9/7/20, 10:36 AM - Messages to this chat and calls are now secured with end-to-end encryption. Tap for more info. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI Shimfida Malam Auwalu dan asalin kauyen Badume ne dake jiyar Kano. Manomi ne kuma dan kasuwa a lokaci daya da Allah ya azurta da rufin asiri. Kafin rasuwar su shida matar shi Balaraba da tsiran su duka shekara biyu ne, dan shine ya rigata rasuwa. Allah ya azurta su da yara shidda. Da yake daga baya sun dawo cikin garin Kano da zama, hakan yasa duka yaran samun wadataccen ilimin addini dana boko. Dukkan su mazan harkar kasuwanci ta kayan abinci sukeyi da mahaifinsu ya rasu yabar su a kai, banda Aminu da son boko ya shiga ranshi sosai, dan bayan ya kammala Degree din shi ta farko a fannin siye da siyarwa, yana gama bautar kasa ya samu aiki a wani kamfani da yake Kaduna, da yayi aure ma can yaci gaba da zama. Duk da aikin shi bai hana shi cigaba da karatu ba da ya nemi izini suka kuma bashi dama da alkawarin cewar zaici gaba da aiki tare dasu dan mutum ne mai hazaka. Lokacin daya kammala degree din shi ta biyu ya kuma sake cigaba dan yana son karatun shi yakai matakin da zai zama farfesa, ga aure daya kara rungumowa. Sai yayi dabarar bude gidajen gona har guda biyu anan garin Kaduna din. Inda yake kiwon kaji, zabi, talotalo harda kifin tarwada da a turance akafi sani da catfish. Allah ya saka mishi nasibi da yake mutum ne mai wadata iyali. Cikin wasu yan shekaru kusan duk wasu masu gasa kaji a Kaduna a wajen shi suke siye. Gidan shi daya dauki shekaru yana ginawa suka koma da yake a unguwar Barnawa nan wajen station road a garin Kaduna. Shima Allah ya azurta shi da samun yara. Auwalu Musa - Balaraba Tukur -Yaran su •Mannir •Rabi'u •Humaira •Aminu •Khalil •Salim Aminu Auwal Musa (Baba) -Matan shi Rashida AbdulMannir (Mama) -Yaran ta •Muhsin •Huzaifa •Salamatu •Halima •Khadija •Junior •Amna Karima Sani (Anty) -Yaran ta •Zaid •Jafar •Hindatu •Khalil •Asma'u Kawayen Hindatu Al'amin •Zainab (Biebee) •Aina'u (Dimples) •Yasmin •Hajarah •Hawwa * Malam Abbas bafullatani ne daga shiyar jahar Katsina, kauyen Marake. Auren da ake kira na gata shi akayiwa Abba da matar shi Amina, dan lokaci bata shige shekara sha shidda ba, shikuma yana da ashirin da uku. Haka suke rayuwar su babu yabo babu fallasa har suka sami yara biyar inda a haihuwar ta karashen, Allah yaiwa Amina rasuwa. Haka yaran sukaci gaba da tashi cikin maraicin uwa kafin su rasa mahaifi suna yawo tsakanin dangi. Cikin hakan ne Abubakar ya shiga Kaduna ko zai sami sana'a inda ya fara aikin katakaye har Allah ya hadashi da matar shi da sadakar yalla ce da tayo gudun hijira saboda hatsaniyar da ake a yankinsu na Sudan sukayo najeriya, garin Kaduna, ita tayo Kaduna tana aikatau a wani gida, ko hausar kirki bataji lokacin. Da yake bashi da dangin da suka damu balle suyi magana akan rashin tabbaci na asalin Mariya, basu sami wata matsala ba sukayi aure ya kama haya anan unguwar Tudun Wada, sukayi zaman su yana cigaba da aikin katakayen shi ciki suke duk wata hidimar su. Mal. Abbas - Mama Amina -Yaran su •Abdallah •Ahmad •Abubakar •Maryam •Rabi'atu Abubakar Abbas (Appa) - Mariya (Anna) -Yaran su •Hamza •Abid •Faruk •Jamila (Auta) Abokan Hamza Abu Abbas •Usman Ayoob (Fodio) •Muhammad Kamal (Arafat) •AbdulHafiz Ashir •Abdallah Nuhu 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 1. Wani irin shiru ne mai cike da firgici da tsakiyar dare kadai kan samar, badan ta duba agogo ba, amman tana da tabbacin karfe biyun dare zata iya yi, wata walkiya akayi da ta sata sake rakubewa jikin bangon wajen saboda akwai hadarin da yake nuna alamar saukar ruwa ko wani lokaci, da babu taimakon hijabi haka zata kasance daga ita sai rigar bacci, kafin wata irin gigitacciyar tsawa ta sata dafe cikinta da yaron da yake kwance a ciki sai da ya motsa mata da alama tsoratar da tayi ta tabashi shima. Runtsa idanuwanta tayi wasu irin hawaye masu ciwo na tsiyayo mata, batasan inda zata nufa ba a cikin tsohon daren nan. Tsayuwa ta sake gyarawa tana dafe da cikinta har lokacin, hannunta na rike da bakar leda da take a kulle da alamun wani abu a ciki. Tafi mintina talatin a tsaye bakin kofar gidanta, gidan auren ta bayan ta saurari kashedin da Hamza yaima maigadi da fadin "Wallahi idan ka bude mata kofar gidan nan, ba aikin ka kadai zai zo karshe ba, sai nasa an rufe mun kai, ka fadi dalilin da yasa ka bude ma wata gidana" Mamaki ne karshen abinda tayi, tasan Hamza kamar yunwar cikinta, sai dai batayi zaton rashin mutuncin shi yayi kamari haka ba, idan bai tausaya mata ba, zai tausaya ma halin da take ciki, ina zata nufa cikin tsohon daren a unguwar su da ko da rana saika yini bakaji motsin mutum ba, motoci ma sai jefi-jefi ta baki da akanyi a gidajen, ko kuma su mazauna unguwar. Dakyar ta iya jan jiki tana takawa ta rakube inda take tsaye a yanzun, ko takalma babu a Kafafuwan ta. Ajiyar zuciya ta sauke na kukan da takeyi har numfashin ta na tsaitsayawa, dai-dai lokacin da ruwan sama ya kece kamar da bakin kwarya. Idan Allah ya taimaka duk gidajen unguwar ana kunna generator, a haske take fayau, ba kasafai suke gane ko akwai wutar lantarki ko babu ba. Idanuwanta Hindu ta sake runtsewa, wannan karin ajiyar zuciyar da ta sauke tafi alaka da sanyin ruwan da yake ratsa sassan jikinta, musamman da yake hade da iska mai karfin gaske. Takowa tayi ta dawo jikin gate din tana bubbugawa "Baba Maigadi dan Allah ka taimakamun, ka duba cikin da yake jikina...in samu wajen rakubewa idan asuba tayi ko ruwan ya tsagaita sai in tafi" Hindu ta karasa maganar cikin matukar galabaita da rauni, tana saka hannunta dake rike da yar bakar ledar ta share hawayen da ruwa yake wankewa, jikinta na amsawa cikin kyarma da iskar da ta sake kadawa, sake bubbuga kofar take da karfi, jin alamar motsi yasata dakatawa, dattijon maigadin ne ya bude kofar yana saurin ziro kai kafin ta samu damar shiga "Kiyi hakuri, kinsan halin maigidan, wallahi aikin nan shine rufin asiri na..." Wasu hawaye Hindu taji sun tsiraro mata, aure mai rufin asiri, aure kuma mai tonon asiri, kaddara na zabar inda zata jefaka batare da ta baka wani zabi ba. Yau itace a tsaye tana rokar inda zata rakube, ita Hindatu Al'amin, gaskiyar hausawa, duniya makaranta, duniya kuma juyi-juyi. Yau ta birkice da ita, asalima a shekara daya duniyar ta fara wasan cikar shekara da rayuwar ta. "Dan Allah ka taimakamun, bansan inda zanyi a daren nan ba, ban sani ba" Cewar Hindu, numfashi Baba Maigadi ya sauke, tunda ya koma ciki yarinyar tai mishi tsaye a rai, amman yana tsoron abinda zaiyi sanadin aikin shi "Sai dai ki shigo na minti kadan, in ara miki wayata inda wanda zaki kira" Cikin rawar murya mai alamar kuka ta amsa da fadin "Eh ka aramun" Dan ta manta da wata abu waya, balle tayi tunanin tata da Hamza bai barta da natsuwar dauka ba, mutumin da ko takalma bai bari ta saka ba, ballantana kuma wata waya. Cikin gidan ta shiga da sauri, tana karasawa yar barandar dake gaban dakin baba maigadi ta tsaya tana tsiyayyar ruwa dan tayi sharkaf, kasa tayi dakyar tana dafe cikinta, wani irin sanyi ne yake ratsata har kwanya. "Ungo..." Baba Maigadi ya fadi yana mika mata karamar wayar shi da take daure da kyauro, hannunta na kyarma ta karba, tana kallon shi da yar lemar da yake rike da ita. Wayar ta duba, taji duniya, inka ganta batare da ka latsa ba, zaka iya rantsewa da bata aiki, gwangwan ce. Batama gwada lambar Mama ba, dan tasan kashe wayarta take da daddare, Baba ne zata kira idan ya daga, tunda shikuma ba daga bakuwar lamba yake ba, a duniyar ta lambobin mutum hudu ta haddace, ta Baba, ta Mama, tata, sai kuma ta Hamza da a yanzun babu amfanin da hakan zai mata. Lambar baba ta saka ta kira tana karawa a kunnenta, ringing din da wayar tayi alamar ta shiga na saka ajiyar zuciya kwace mata, kafin wasu hawayen su zubo, wannan karin kuka ne mai sautin alamun zafi da qunar zuciya yake zubo mata. Har wayar ta yanke bai daga ba, sake kira tayi, sai da ta jera kira biyar tana yankewa ba'a daga ba, zuwa lokacin zuciyarta ta kara karaya, amman tasan hakura da kiran wayar na iya ja Baba Maigadi yace ta tashi ta fita tunda ba'a daga ba, kuma ruwan da ake ko alamar tsagaitawa baiyi ba, ballantana tasa ran zai dauke, inda take zaune ma feshin ruwa na samunta, ga sanyin tiles din ya kara mata sanyin da takeji, sai kyarma jikinta yake. Zazzabi ma takeji kamar ya saukar mata. Lambar ta cigaba da kira harta bace lissafi, cike da tausayawa Baba Maigadi yace mata "Ki shiga daga ciki..." Ganin yanda take kara takurewa da alamar sanyin da takeji, a ran shi yake tunanin yanda ba zai sake jin haushi idan mata sukai wa jinsin maza kudin goro na cewar basu da mutunci, basu da tausayi ba. Randa yaji wata ta kira abinda da namiji yayi da akuyanci, kalmar ta kwana biyu tsaye a makoshin shi, dan baiga abinda yai zafi da zata danganta jinsin shi da dabba ba, sai yanzun da kalmar ce ta farko da tazo mishi akan fassara abinda Hamza yaiwa Hindu din batare daya duba tsohon cikin da take tare dashi ba, balle yayi tunanin hadarin dake cikin fitar ko da namiji ne a tsohon daren nan, ko babu hadari, balle kuma mace. Hindu bata jira ya sake mata magana ta biyu ba, ta mike dakyar ta tura kofar dakin tana shiga, da kafet cike da dakin, irin jan nan, sai tarkacen da batabi takan su ba, dan harda katifa irin ta yan makaranta, daga gefe bakin kofa ta zauna tana dan turo kofar, kar Hamza ya fito ya fatattake su daga ita har Baba Maigadi. Dan kadan ne cikin abinda zai iya aikatawa, ita shaida ce. Lambar Baba taci gaba da gwadawa tana karanto duk wata addu'a da tazo ranta, lokaci zuwa lokaci take saka gefen hijabinta da yake a jike tana share hawayenta da sunki daina zuba. ** Bacci suke su duka biyun mai nauyin gaske, da yake babu wuta, tasowar hadari da iska yasa an dauke, ga wani irin zafi da ya dira. Sun jima suna juyi, suna dan taba hira kafin bacci ya dauke su wajen sha biyu. Cikin bacci Alh. Aminu yakejin ringing din wayar daya lalubo yana dubawa da bugawar zuciya, ganin bakuwar lamba yadan nutsar da zuciyar shi "Waye wannan..." Ya fadi, kiran yana yankewa yaga missed calls da lambar har guda ashirin da daya "Subhanallah" Ya furta yana mikewa zaune gabaki daya, dan ya tabbatar ba lafiya ba, baccin na barin idanuwan shi, salatin da yayi shiya tashi matar shi Rashida da yaran gidan duka suke kira da Mama daga bacci, duhun dakin na hanata ganin shi sosai, hasken wayar shi ya tabbatar mata da a zaune yake "Alhaji lafiya dai ko?" Kai Alh Aminu ya girgiza ma Mama yana fadin "Wallahi ban sani ba, wata lamba ce an kirani har sau ashirin da daya fa, bansan irin baccin da muke ba haka yau" Alh Aminu ya karashe yana kokarin sake mayar da kiran da yaki shiga, da alamar matsalar network. Ita kanta Mama tashi tayi zuciyarta na wata irin dokawa. 'Inalillahi wa ina ilaihi raji'un' Take fadi tana maimaitawa cikin ranta, bata son furta abinda zuciyarta take saka mata na camfin da hausawa suke cewar idan wani mummunan abu zai sameka sai baccin asara mai nauyi ya danne ka, dan duk yanda kaso casa'in cikin dari yake kasancewa gaskiya, yau zata kasance da kaso goman. Dan haka bayan Inalillahi jaddada ma kanta kalaman kwarin gwiwa takeyi 'In shaa Allah babu abinda ya faru' Tana kallon Alh Aminu da shima hankalin shi a tashe yake, sai da gabanta ya sake mummunar faduwa da taji yace "Hello.... Waye?" Alamar kiran ya shiga har an daga "Hello..." Ya sake fadi dan bayajin abinda ake fadi, network din na rawa, amman da alamar macece, kashewa yayi ya sake kira, zufa na tsatssafo mishi, a duniya Allah ya dora mishi son 'ya'yan shi, duk albarkar yawan su daya samu, idan yana da iko ba zai bari ko kuda yahau su ba, balle ya taba mishi su, dan sune jigon rayuwar shi, farin cikin ranshi. Akan ce tsakanin da da uwa sai Allah, kaunar su ba abu bace da za'a fassara kan mizanin kalamai, zai karyata hakan, dan kaunar da yake ma yaran shi har iyayen su mata na jinjina mata lokutta da dama. 'Allah ka tsaremun yarana, Allah karka jarabceni ta hanyar su, Allah ka dubeni' Alh Aminu yake fadi yana kara maimaitawa, lokacin da yaji an daga kiran, cikin wani irin raunin murya da shessheka aka ce "Baa... Baba... Baba na" Kafafuwan shi Alh Aminu ya sauko daga kan gadon a gigice, badan yagane muryarta ba, saboda ta fito daga kasan makoshinta a galabaice, ga network din bashida kyau, sai dan ita kadai take ce mishi 'Baba na' duk a cikin yaran kamar ita kadai ya haifa. Har magana sauran sukan yi akan hakan, maganar Hindu a ko da yaushe itace 'Baba na ne, kaunar da take tsakanin mu daban da irin ta ku, nafi ku kaunar shi' Yakan murmusa ko tuna hakan yayi, da gaske ne a cikin 'ya'ya akwai wanda zaka fi jin kaunar shi, Hindu ta kasance itace wannan 'yar, har kasan zuciyarshi shi yake jinta, ko digon hawaye bayason gani akan fuskarta, ko da na farin cikine "Hindatu?" Ya furta da shakku tattare da muryar shi yana sake fadin "Hindu? Hindun Baban ta..." Mama kuwa kallon shi takeyi cikin kaguwa dajin me yake faruwa, amman taga hankalin shi ya tattara wajen sauraron Hindun, fatanta dai Allah yasa komai lafiya. A wahalce yaji muryarta ta sake fita "Baaba ya koreni, Hamza ya kore ni. Yaki hakura gari ya waye..." Wani abu Alh Aminu yaji ya tsirga mishi daga dan yatsan kafarshi zuwa tsakiyar kan shi, kafin ya dunkule yana dawowa ya tattaru a kirjin shi hadi da danne zuciyar shi ya takurata "Ya kore ki?" Ya bukata yanajin dacin da baisan ta inda ya taso mishi ba a makoshi, zai rantse yaga kan da ta daga mishi, gunjin kukan da take na sauka kunnune shi cikin rashin dadin saurare "Cikin daren nan? Cikin dare zai koreki? Kina ina yanzun?" Yanda take maida numfashi na sashi hasashen kalar kukan da take da yake tafasa zuciyar shi, dakyar tana numfarfashi ta amsa shi da "Dakin Ba...Baba Maigadi, shiya aramun waya... Baba kazo karya fito ya koreni..." Zuwa yanzun Alh Aminu ya mike tsaye "Ki tsaya nan, kina jina? Gani nan zuwa, ki tsaya nan karki fito ko ina kinji Hindu... Yanzun zan zo in shaa Allah" Kukan da take yasan ba zata iya magana ba, haka ya jira har sai da yaji tace "To..." Can kasa tukunna ya kashe wayar "Me ya faru Alhaji?" Mama ta bukata, ko kallonta baiyi ba balle ya amsa, dan ranshi in yai dubu a bace yake, ga hankalin shi da yake a tashe. Wajen durowar kaya ya karasa ya bude, doguwar riga jallabiya ya dauka ya dora kan wandon shaddar da ya kwanta dashi sai singileti, yanayi yana kiran wayar Muhsin da taki shiga, dan haka ya kira ta Huzaifa, bugu na biyu ya daga ko sallama baiyi ba balle tunanin gaisuwa yana fadin "Baba lafiya?" Hankalin shi a tashe, kai Alh Aminu ya girgiza, da wani irin zafin zuciya yace "Ka sameni gidan Hindu, ka gwada kiramun Muhsin shima" Duk da Huzaifa yaji shi ta dayan bangaren da wani sabon tashin hankali da yake bayyane a muryar shi yace "Me ya samun Hindun? Baba me ya sameta? Ka fadamun ko zan samu natsuwar tuki" Numfashi mai nauyi Alh Aminu yaja yana fitarwa "Mijin ta ya koreta cikin dare nan, cikin daren nan Huzaifa..." Ya karasa maganar yana kashewa, da fitilar wayar yayi amfani ya lalubi mukullin motar shi, da idanuwa Mama take ta binshi dan ita din bamai yawan magana bace ba, sai da taga zai fice ne tukunna ta bi bayan shi da fadin "Kayi tuqi a hankali dai, Allah ya tsare ya dawo da kai lafiya" Tasan halin shi, shisa bata damu ba, komawa tayi ta kwanta tana jin yanda ruwan yake kara sauka har lokacin, da tunanin barkatai a ranta, ciki harda yanda batasan gaibuba, amman ta hasoso karewar auren Hindun a haka. * Tana sauke wayar daga kunnenta ta mike ta fito daga dakin Baba Maigadi da yana ganin ta ya taso, wayar ta mika mishi "Baba nagode" Ta furta cikin rawar murya tana fitowa daga barandar dan ta nufi kofa "Ina zaki je?" Sai da ta share hawayenta, tana ta kyarmar sanyi har lokacin ga wani ruwan da ya soma dukanta "Za'a zo a daukeni yanzun, kar ya fito in maka sanadin aikin ka" Kai kawai Baba Maigadi ya iya jinjinawa cikin tausaya mata, shiya bude ma Hindu kofar ta fita daga gidan, jikin bango ta samu ta rakube, ruwan na cigaba da dukanta, tanajin Baba Maigadi bai rufe gidan ba har lokacin, da alama yana tsaye bakin kofa, hankalin shi sam yaki kwanciya duk da tace mishi za'a zo daukarta din. Ba zatace ga lokacin da ta dauka a tsaye a wajen ba, amman tabbas bata da lafiya, rashin lafiyar da bata da alaka da Hamza, zazzabine mai zafi yai mata rumfa, har cikin idanuwanta take jin shi da take budewa tana rufewa, ga dan cikinta da yaketa motsi kamar yana son fitowa, wannan karin har bayanta sai da taji ya amsa, tako dafe cikin tana kiran "Yaa Rabbi..." Wata irin azaba na ziyartar kwanyarta, kafin hasken mota ya dirkako ta, daga idanuwa tayi tana jin sabon kuka ya kwace mata da taga motar Baba ce, yanayin parking ko kashe motar baiyi ba ya fito daga ciki yana sauke idanuwan shi kan Hindu da take ta takurewa duk idan iska ta kada, tana hango shi ta fara takowa, yana ganin yanda bata da takalmi, gata rungume da tsohon ciki. Wani abu Baba yaji yana karyewa a cikin zuciyar shi, ga dacin da yai mishi tsaye a makoshi, yama kasa takawa ya karasa inda Hindu take, yayi tsaye ne kamar an dasa shi. A wahalce ta karaso wajen shi tana wani irin kuka kamar zata shide "Baa... Baaba na" Ta fadi muryarta na sarqewa, hannu Baba ya mika ya kama na Hindu da baya tallafe da cikinta, yanajin sanyin daya dauka kamar kankara, shi kan shi da baifi minti biyu da shiga ruwan ba yayi sharkaf, ledar dake hannun nata yake bi da kallo "Ham... Hamza ya bani" Ta fadi dakyar, karbar ledar Baba yayi ya saka cikin aljihun jallabiyar shi yana taimaka ma Hindu da takejin bayanta kamar zai rabe gida biyu, numfashi ma a wahalce take jan shi tana fitarwa, Baba ji yake tamkar zai kama da wuta saboda bacin rai. Mota ya bude yana taimaka ma Hindu ta shiga, dai-dai lokacin da wata motar ta tunkaro wajen, tsaye yayi bayan ya mayar da kofar ya rufe, Muhsin ne da Huzaifa suka fito suna karasowa inda Baba yake "Ina Hindun?" Huzaifa ya bukata dan inba ganinta yayi ba hankalin shi ba zai kwanta ba, murfin motar Baba ya bude mishi yaganta a zaune ta jike sharkaf, numfashi Huzaifa ya sauke cike da nutsuwar da ta saukar mishi "In dai na isa da ku bana so kayanta su kwana a gidan marar mutuncin nan" Baba ya fada yana saka Huzaifa kallon shi cike da tashin hankali "Baba kayi hakuri dan Allah, ka isa Wallahi har kayi yawa ma, amman yanzun dare ne, gashi ana ruwa, ba lallai a samu masu motar da zasu fito ba" Huzaifa ya karasa maganar da sigar lallashi, yana saka Muhsin dorawa da "Kayi hakuri Baba, gobe tunda sassafe, kaga yanzun ya kamata muje gida ta sake kayan nan kar zazzabi ya kamata" Kai Baba ya jinjina wani abu ya tokare mishi makoshi, bai ba Hamza auren yar shi dan yagaji da ita ba, duk da burin kowanne iyaye shine suga yaransu a gidajen mazajen su, amman idan babu kwanciyar hankali da nutsuwa gara ya dinga ganin yar shi cikin gida kullum, zai fi mishi wannan bakin ciki. Dakyar ya iya bude motar ya shiga, dan shima duk ya jike, sai da ya zauna tukunna ya kalli su Huzaifa yace "Ku wuce gida kawai, goben idan an samu motar da zata kwashe kayan ku kirani" Wannan karin su duka suka jinjina ma Baba kai, suna tsaye har saida sukaga ya bace musu, tukunna suka koma mota, gida Huzaifa ya fara sauke Muhsin, tukunna ya wuce nashi gidan shima. * Wani irin sanyi take ji yana ratsata har cikin kwakwalwar ta yana hana mata wani tunanin daya wuce na son rufa da katon bargo ko zataji dumi. Da suka karasa gidama, Baba ne ya bude mata bayan motar, amman tayi galabaitar da ta sakko kafafuwanta wajen motar, amman ta kasa raba jikinta da kujerar. "Hindu?" Baba ya kira ganin yanda take fitar da numfashi a wahalce yana dorawa da "Ko mu wuce asibiti?" Kai Hindu ta girgiza mishi, kwanciya kawai take so taji tayi, ba zata iya zaman motar ba har su sake nufar asibiti. Dakyar, hannunta daya dafe da cikinta, dayan kuma ta rike kofar motar ta raba jikinta da kujerar tana mikewa tsaye hadi da runtsa idanuwanta kafin ta sake budesu cike da gajiyar da take ji. Baba na tsaye yana kallonta zuciyar shi cike da tausayin yar tashi, a gefe daya kuma fal da bacin rai, ita ta fara yin gaba tana karasawa wajen kofar tasa hannu ta murza tana turawa ta saka kafafuwanta cikin falon. Tana karasawa kan kujera ta zauna, Baba kuma ya wuce cikin daki inda yabar Mama, ba bacci takeyi ba tun fitar shi, tana kwance ne tana tunane-tunane, ta kunna fitilar and wayarta tunda babu wuta dan ana ruwa har lokacin Tana jin sallamar shi ta mike tana fadin "Kun dawo? Ina Hindatun?" Hanyar waje Baba ya nuna mata, babu shiri ta sakko da kafafuwanta. Tana daukar wayar ta wuce falon ya rufa mata baya, kallo daya taiwa Hindu taga yanda take a galabaice, tana karasawa taba fuskarta tayi zuwa wuyanta tana jin yanda zazzabi ya rufeta ruf "Alhaji da asibiti aka wuce da ita ai, kaji zazzabin da yake jikinta?" Mama ta fadi kafin ya amsa tana dorawa da "Tashi muje ki cire wannan jikakkun kayan" Saida Hindu ta sa bayan hannunta tana goge hawayen da taji ya zubo mata, tukunna ta kama hannun Mama data riko kafadarta dan taimaka mata, ta mike, dakin Mama din suka nufa tana bata kayanta, ta sake a wajen, dan wata kunyar Mama ce karshen abinda takeji. Sake kama hannunta Mama tayi suka fito daga dakin zuwa dakin baki da yake gyare tsaf, har sauri Hindu take karawa dan so kawai takeyi tajita a kwance, har wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke data kwanta, Mama ta rufa warware katon bargon da yake dakin tana rufa mata. Gefen gadon ta zauna tana kallon Baba daya biyosu ya kasa samun nutsuwa shima tace "Kaje ka sake kayan jikinka kaima ka kwanta, zan zauna da ita zuwa safe in Allah ya kaimu" Dan jim yayi kamar zai musa, tukunna ya jinjina kai yana wucewa ya fita daga dakin, duk da shine karshen abinda yake so yayi. Yafi so ya samu waje ya zauna sai yaga Hindun ta warware tukunna. Da tunanin ko da Hamza ne namijin daya rage a duniya Hindu tagama auren shi har abada Baba yake sake kaya. Shi da an sami mota ma cikin daren za'a kwashe kayan, tunda shi bashida mutunci. Mama kuwa da taga ya fita, jikin Hindu ta sake tabawa taji da zazzabi har lokacin, tana kallon duk da idanuwan Hindu din a rufe suke, hawaye ne kawai yake zubar mata yana sauka ta gefen karan hancinta zuwa kan pillow din da take kwance "Kiyi hakuri ki daina kukan nan Hindu, kinga bake kadai bace, karki jama kanki wani ciwon kinji ko?" Kai kawai Hindu ta daga mata badan tana da wani iko akan zubar hawayen nata ba, su suke fitowa da kansu saboda kwanciyar da tayi da dumin bargon da ya rufe jikinta ruf yaba kwakwalwar ta damar tunanin asalin halin da take ciki. Ba tayi mamaki dan Hamza ya koreta tsakiyar dare da tsohon ciki, ana kuma ruwan sama ba, tana da tabbacin yana can kwance yana baccin shi a nutse, dan babu wani abu da yake shiga tsakanin shi da baccin shi. Yakan ce 'Koma meye zai iya jira, bacci na ba zai jirani ba' Sake runtsa idanuwanta tayi gam, har radadi suke mata da tasan kukan da tasha ne a daren, kukan da ba yanzun ta fara yin shi akan Hamza ba, bata dai san ranar karshe da zata daina ba, da gaske takeyi lokacin da tace mishi 'Na manta ranar karshe da hawayena suka zuba akan wani abu da ba kai ba' Sai takejin kamar tun tana yarinya rabon da wani abu ya sakata kuka sai bayan ta hadu da Hamza, daga ranar ta fara kukan da ya kawota inda take yanzun "Ko dai sai munje asibiti a daren nan?" Mama ta tambaya cike da damuwa, dan ita kam bataso taga mai ciki a wani hali. Tunda tasan shi kanshi daukar nauyin cikin idan aka barka dashi batare da an kara maka wani ciwon ba ya isheka. Cikin disashiyar murya tace "A'a Mama, bacci nake so inyi" Bawai dan tana jin baccin ba, kai Mama ta jinjina "In kawo miki ruwa" Kai kawai Hindu ta iya girgiza mata da alamar a'a. Kyaleta Mama tayi a zuciyarta tana mata fatan samun sauki, ta hau kan gadon tana jan mayafi ta rufe kafafuwanta sannan ta kwanta, dan kanta harya fara ciwo, gara ko baccin kasa da awa biyune ta samu kafin asuba, fitilar wayar ta kashe tana lumshe idanuwanta. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 7 Shekara daya bayan gama diploma dinta, ta sake samun gurbin karatu na HND ana Polytechnic din ta Kaduna, duk da Baba yaso ta gwada Direct Entry ana KASU, amman sam makarantar ta gama fita daga ranta, haka kawai take son cigaba dayin Poly din saboda tana sakata jin wani kusanci na daban da Hamza. Ita kanta zuwa yanzun tasan inda a kasar wajene idan Hamza zai kai kararta tsaf za'a kamata da laifin bibiya, wato stalking a turance, a shekara daya da wani abu duk wani hoto da Hamza zai saka akan idanuwanta, tana liking ta kuma yi mishi comment a shafin shi na Instagram, dan ta tabbatar Hamza ko dan wasan film ne ko kwallon kafa, yanda take bibiyar shi yaci ace ya kula da ita, ko da sau dayane ya tanka. Amman ko inda take Hamza bai taba kallo ba, har haushin kanta take ji wasu lokuttan idan ta gama yi mishi dogon sharhi musamman akan gine-ginen da yakan dora. Ranar da taga ya dawo Najeriya ji tayi kamar an mata albishir da kujerar Hajji, kamar Hamzan zai kulata saboda suna jaha daya, kuma taga dan Kaduna ne daga yanayin wajajen cin abincin da suke hotuna a ciki shida abokan shi. Amman ko like bai taba dannawa akan comments dinta ba. Ta kuma kasa daina yi saboda yanda yake bala'in burgeta. Zuwa yanzun Samari takeyi kala-kala, ta kasa tsayar da hankalinta akan guda daya, dukkan su saita sami abinda ta kushe a jikin su, duk nasiha da Anty take zaunar da ita tana mata, ta kunnen dama take shiga ta fita ta haggu, daman ita kadai ta rage a gidan da take mata magana akan maganar tsayar da Saurayi daya, Baba kam da Anty ta gwada yi mishi zancen, ca yayi 'Ki kyale yarinyar nan dan Allah, duka Hindatun nawa take da kikabi kika dami kanki akan ta? Ba karatu takeyi bane wai? Ko kin manta shi auren nan lokaci yake dashi?' Daga ranar kuwa Anty bata kara daga mishi zancen ba, amman yana damunta matuka, tana kuma addu'a akai. Ita kanta Hindu abin na damunta, yanda har yanzun ta kasa tsayar da hankalinta akan saurayi daya, ta kasa samun wanda zai kwanta mata. Ba sosai take hawa manhajar WhatsApp ba, balle kuma facebook da take dauka sai gidadawa suke yinshi yanzun. Dimples ta koya mata zaman Twitter ba kadan ba. Da yake ita Dimples can tafi ganewa, ko kace ka mata magana a whatsapp bata amsa ba zata ce maka 'Baka dubani a Twitter bane ba' Itama Hindun tunda tagane kan Twitter tasan cewa nan din wata duniya ce ta daban, ta hada duk wasu manyan gayu da kake tunani, babu kuma karya kamar yanda akanyi a Instagram. Akwai manyan yaran da suke burgeta sosai a Twitter, yaran attajirai ne daga yanayin shigarsu da motocin da zaka gansu a ciki, duk da kyawun su bai kai mata inda take so ba. Takan shiga wasu lokuttan a dama da ita, kusan tafi Dimples shige-shige a Twitter, ita Dimples idan ma bata sanka a gaske ba, ba zata taba sakar maka fuska har kuyi wata hira ba, ko kabita ma, ba zata amsa gayyatarka ba. Kalar hotunan da Hindu take sakawa a Twitter yasa take da tarin Mabiya, duk da shigace ta mutunci a jikinta, duk da abaya, sosai ake mata kallan Babbar yarinya. Watan nan daya kama aure akeyi kaca-kaca a twitter, sai kaga matan sunce daga mazan sun tura musu DM wato sako ta inda su kadai zasu iya gani, su kuma suka amsa shikenan soyayya ta ƙullu tsakanin su, yanzun gashi har dunyi aure. Kuma sai taga mazan sun haɗu, ga kuɗi suna dashi, inta duba shafin su sai ta samu basu da wasu mabiyan kirki kuma basa saka hoto ko ɗaya. Abin na matuƙar burge Hindu, ita duk wanda suke mata DM tarkace ne. Haka kawai saita fara ji a jikinta kamar itama mijinta zai fito daga Twitter ne,tunda taɗan rage burin nata, tanajin kamar ko gajerene indai yana da kuɗi sosai wataƙila ta haƙura taga abinda Allah zaiyi. Lokaci ɗaya ta fara ganin Musbey da suke following ɗin juna yana kwaso mata shafin wani Jalil idan yayi retweet ɗin posting ɗin Jalil ɗin da yake siyar da kayan sawa na maza wato kaftan. Daga yanayin kayan zaka fahimci irin kuɗin da yake dasu, duba shi tayi taga mabiyan shi kaɗan, ko data duba hotunan shi duk tallar kayane da suka ji sirfanin hannu da alamu suka nuna zaiyi tsada matuƙa. Saita tsinci kanta da following ɗin shi kafin ta sauka daga kan Twitter ɗin. * "Usztaz kasan dai ya kamata kayi aure ko?” Abokin sa Adam yace mishi. "Wai meyasa kuke ce mishi Usztaz ne? Bafa ustazu bane, rashin kaya ne kawai ke ɗawainiya dashi." Aliyu yai maganar yana takaicin Ustaz din da ake kiran Jalil dashi, saboda ko kusa bai hada hanya da Ustazai ba. Jalil wanda aka fi sani da Ustaz baice komai ba, maganar mutane bata damunsa. Ba yau bane rana ta farko da mutane da abokan sa suke mishi maganar aure. Amma ta ina zai iya aure tunda ba shida sana'ar kirki. A shekaru arba'in da biyu sana'ar aikin hannu yakeyi. Yana saƙa design a riguna. Shima shagon ba nashi bane. Na wani wan mahaifinsa ne wanda ya gaji da ganin sa yana zaman banza. “Haka kurum kuyita ce mishi Ustazu kamar abin arziki, daga namiji yana saka manyan kaya shikenan ya zama na kirki?” Aliyu ya cigaba da sababi. Da Adam da Aliyu yan biyu ne yan shekaru ashirin da bakwai. Sabbin zuwa ne a shagon kuma jininsu ya haɗu dana Jalil, saidai idan ka fita kace mishi Jalil babu wanda zai sani. Anfi saninsa da Ustaz wanda ba'a san inda ya ɗauko laƙabin ba. Shi Jalil yana san gayu amman bashida hanyar da zaiyi, haka ya haƙura abinshi. Tunda yake jikinsa bai taɓa marhaba da English wears ba, toh saidai na haihuwa. Tun tashin shi ya saba saka kwabɗa kwabɗan yadi ko mai kwabo kwabo. Duka kayansa sunyi mishi girma. Gashi bala'in siriri baida faɗin kirji. Yana yanayi da ɗan shekara talatin da biyu yasa yake yarintar sa babu kama hannun yaro. Dan Jalil irin mutanen nan ne da sun girma basu san sun girma ba. Gashi idan yana tafiya saboda girman kayan shi da rashin kiba sai yayi maka kamada tuta. Cima zaune ne na bugun jarida. Yan kuɗaɗen sa dayake samu baya komai dasu sai siyan data domin yaga kyawawan mata sannan kuma idan an dace ya samu wanda zata aure shi a yadda yake. Yanada NCE wanda yayi a FCE Zaria inda ya karanta English and Literature. Wannan ɗan turancin ne yake ma yan mata bagu dashi. A manhajan Twitter yaji labarin cewa akwai wasu manyan yaran attajirai, tun lokacin ma ta Web yake shiga, bashi da wayar da take sauke application, sai dai yana cikin mutanen da ake ma laqabi da Low-key a Twitter. Baya shiga duk wani rikici ko drama da za'ayi, kawai dai idan abu yayi mishi, sai yayi liking ko retweet, mabiyan shima basu da yawa, amman akwai wanda ake ganin girman su a Twitter da suke bin shi, sosai Jalil ya iya kama girman shi a Twitter ba kamar a fili ba. Kasancewar Ustaz Jalil a Twitter yasa shi kara wayewa ta fannin da baka tunani, duk da rashin gayun na nan, kafin Twitter yaji yanda ake fadin fararen kaya girma ne, daga lokacin ko dan yadi zai siya sai ya siyi fari, naya saka wani kaya face fari, kuma idan aka ce farin kaya bawai ana nufin farin da mutane suka sani ba. Duk sun koɗe sunyi dariya ta wajen wuyan. Gashi yanada wani farin half cover wanda ya koma kalar madara. Ya saba idan manyan mutane sun kawo ɗinki saiya ɗauki hoton kayan ya wallafa, sannan yace shagon sa ne yanzu yaran ciki sukayi mishi aikin. * Zata ce kusan sati biyu da tayi following ɗin Jalil amman baiyi follow back ba, hakan ya sakata tunani barkatai, sai taita ganin kamar ita ce take bin arziƙi shikuma yana ƙinta. Hindu bata taɓa mashi magana ba, tunda dai duk matan da takeji dun sami mijin aure a Twitter duk mazan ne suke fara musu magana, amma tana kallon duk wani rubutun da zaiyi, ya kuma iya turanci ba kaɗan ba. Yanayin sa yana burgeta. Babu ruwan shi. Saidai ya watsa hotunan da yaran shagon sa suka yi kamar yanda yake cewa ya tafi. Akwai wani kwarjini dayake mata na rashin dalili, bawai ta taɓa ganinsa bane tunda yana cikin mutanen da ko kadan basa saka hoton su,amma kuma yana bala'in birgeta. Wata Isha datayi aure kwanaki tace mijinta a twitter suka haɗu kuma baida followers sosai. Watau attajiran ba'a sansu ba. Gashi kuma mijin Isha ya haɗu cikakken namiji, Allah bai rage shi da komai ba ta fannin halitta. Hindu ta kasa gane dalilin daya sa take ganin cewa Jalil yana cikin wannan sashen. Kuma idan wannan manyan kayan dayake wallafawa daga shagon sa ne. Toh ai kakanta ya yanke saƙa. Dan kullum da kalar wanda zai saka. Yau haka kawai ta tsinci kanta da yin liking ɗin hoton kayan da ya saka. Ko wayar bats ajiye ba taga yayi following ɗinta, wani irin murmushi taji ya ƙwace mata. Shi kuma Jalil ana shi ɓangaren dan ƙarfin hali su Adam suna mashi magana ko jinsu baya yi dan sam sai yau ya kula da Hindu tayi following ɗin shi,satin ba'a sami wani aikin kirki ba, yanata lallaɓa data din shi karta ƙare da wuri,shisa baiyi wasu shige-dhigen rashin dalili ba sai yanzun da yaga tayi liking hotunan daya saka, nan take yai follow back yana shiga profile ɗinta. Bin hotunan Hindu yayi yana kallo, ta bala'in birge shi. Bawai aurenta yakeso yayi ba, kawai dai ko gaisuwa su rinƙa yi ana mutunci. Tunda shi kanshi yasan bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane. Sallama yayi mata, abin kuma yayi mugun bata mamaki. Kamar yasan yanzu tayi tunanin ko ita tayi mishi sallamar, Har ga Allah nan take Hindu ta fara hasaso yanda bikinta da Jalil zai kasan ce, tasan shine zai zamo uban yaranta. Batayi jan aji ba ta amsa. “Wohoho... Maraba garsarshe!” Jalil yace da ƙarfin tsiya. Yana saka Aliyu ɗagowa cikin ƙunar rai “Ya dai Ustaz meye haka muna aiki kana mana ihu, kamar wani ƙaramin yaro" Dama cikin tagwayen yafi zafin kai. Kuma bayason yanda Ustaz bashida kamun kai Kallonsa Ustaz yayi yana dariya, saiya kara masa wayan a fuska “Kalli abinda ya faru, nayi kamu jama'a" Yace sannan ya miƙe ya soma taka rawa. Irin rawar nan da Ibro keyi da kafa ɗaya bayan yaci ɗammara. Haka yayita ji yana zufa, Aliyu haushi ya gama ƙume shi “Ai ba nan gizo ke saƙar ba, yanzu me wannan yarinyar zatayi dakai? Jibe ka fa. Rigar ka kwara ɗaya, gashi duk ta koɗe bata kama omo" Aliyu yai maganar, Adam da sauran yan shagon na bushewa da dariya. Bai kula suba, ya koma gefe ya soma chatting da Hindu gadan gadan. Sai ya zamana a duka satin babu abinda Jalil yake banda hira da Hindu da ta saki jiki ta biye mishi, duk yanda Dimples tayi mata kashedi tabi a hankali, sai ta bagarar da zancen Dimples din na cewar a low-key Twitter tabbas akwai attajiran masu kudi, akwai kuma attajiran amman tantiran yan duniya masu bin mata, kuma zai iya yiwuwa akwai yan yankar kai ma, tunda yanar gizo yanzun ta zama abinda ta zama. Sai Hindu ta alakanta maganar Dimples da rashin son mutanen ta, in da mutane zasu biye mata sam zata wuce su wuce kamar ba daga jinsi daya suka fito ba. Ko kadan bata da yarda, zaku shekara tare da ita kafin ta sakar maka fuska, kullum girarta a sama take, bata shiga harkar kowa, ba kuma zataki kowa karya shiga harkarta ba, shisa sai ta daina mata zancen Jalil din, duk da tana so ta tambayi Dimples ko zata iya cema Jalil ya turo mata da hoton shi kar a karayin ta Elias, amman kuma nan ba 2go bane ba, Twitter ne, bata taba ganin wata ta fito tace ta hadu da gurgu ba, kuma tana ganin suna ma juna bangajiyar ziyara da kuma godiya a tsakanin su. Ga ajin Jalil din ya burgeta, har lokacin ko lambar wayarta bai karba ba. Wata safiyar asabar da ta kasance bata da aikin makaranta sosai, ta kuma tambayi Anty Dimples zata zo suje gidan Maman Amrah Yayar Dimples din batajin dadi zata dubo ta, sanin kusancin da ke tsakanin Hindu da Dimples shisa Anty ta amince da kashedin kar Hindun ta kai dare. Ranar kuma tayi dai-dai da lokacin da Jalil ya bukaci yana son ganinta su gaisa. Nan ta shaida mishi cewa bata gida yau zasu fita ita da Kawarta. Ya tambayi unguwar tace mishi wajen Lagos Street ne, kafin wani lokaci Jalil ya amsata da cewa shima zaiyi ta area din sai su hadu 'Briefly' su gaisa, yanda yai amfani da kalmar a gayance ya kara burge Hindu. Sosai taji daɗin wannan maganar, a cikin rana ɗaya tayi babban kamu. Watau Jalil shiru shirun twitter zai ziyarce ta. Kwalliya ta fesa sosai, data karbi jikin ta, tasan cewa harga Allah tayi azkar da kyau. Kuma dama Allah yana tare da mai hakuri. Wulakanci da Hamza yake ta mata ne, da kuma kalar tarkacen Samarin da tayi yau Allah zai wanke mata duk wani bakin ciki da ta kwasa. Tunani kala kala ya rinƙa rikito mata. Ita bata san gajeren namiji kamar an kifa kwando. Fata takeyi kada Jalil ya zamto gajere. Sai kuma ta tuna cewa yanzu kai ya soma wayewa, tsawonka shine aljihun ka. Idan dai yanada kuɗin sa kawai zata aure shine ne amma bazata taɓa barin ƙawayenta suga mijinta ba. Zata ce mashi bata san snatching, kafin ayi mata dariya ace taci baya. Haka tayita tunani kala kala tana kokarin ta kawo kamannin Jalil wanda take kyautata zaton shine zai zama mijinta. Da wannan tunanin Dimples ta sameta, suka yi ma Anty sallama suka fice, a hanya ne take ba Dimples labari "Ba zaki rufama kanki asiri da mazan Twitter ba ko Hindu? Bakiji me nace miki ba" Kai Hindu take girgiza ma Dimples "Wallahi ina ji a jikina Dee" Ta kirata kamar yanda take ce mata tana dorawa da "Ki yarda dani, zuciyata ba ko yaushe take mun karya ba, ina da good feelings akan Jalil. Ina jin kamar shine zai zama mijin da zan aura" Wani irin kallo Dimples takeyi mata, su duka sunsan halinta, ba akan komai take magana ba, amman idan taji bata yarda da abuba to karshe sai abin nan ya zamana baizo musu da dadi ba "Hmmm..." Kawai ta furta suna cigaba da takawa zuwa titi inda zasu hau adai-daita sahu da zata kaisu gidan Maman Amrah * "Nifa inada abin yi, ku ce ma Kawu na fita" Jalil yace tareda miƙewa. Su Adam kallonsa sukayi sai suka cigaba da hirarrakin su. Gida ya koma yana cire kayan jikinsa, wankewa yayi sosai da omo dan yayi haske clean ya saka. Daman ya siyo bula domin ya ƙara ma dan yadin da yake matukar ji dashi armashi. Dayake yadin mai laushi ne kuma ana iska nanda nan ya bushe. Aikam saiya goge da kyau yana mishi karin guga na mutunci. Takalmin sa wanda ya ɓare ya soma dariya ya ɗauko, yana saka gam da baya rabuwa dashi dan yan liqe-liqe, nan ya gyara tareda gogewa fes. Yanayin Hindu bai mashi kamar wadda zatayi wulakanci ba. Kuma ai ba santa yace yanayi ba, idan sun haɗu bayan yau zai soma binta da kalamai wanda zai sa ta soshi. Bai taɓa budurwan kirki ba, ya dai saba cema yan talla yana sansu saboda su rinka bar masa kaya kyauta. Musamman masu doughnut ko gyada. Su kuma idan suka gane halinsa su zage shi tas suyi gaba. Karfe huɗu Hindu ta bashi damar ya ziyarce ta, inda ta faɗi yanada ɗan nisa da inda yake. Maimakon ya hau mashin sai Ustaz yace bari yaje da ƙafa tunda akwai sauran lokaci, yan kudin Machine din yayi amfani dasu ya kara siyan data. Inda yake gani babu nisa saida ya kwashi fiye da awa ɗaya yana takawa. Ga rana ana barbaɗawa ranar kamar zai soye. Duk zufa yakeyi ta ko'ina hammatar rigarshi duk tayi dabbara-dabbara da wajen wuyan sa musamman tunda kayan akwai bula. Ya isa inda ta faɗa mishi sai nishi yakeyi zufa tana karyo mishi. Sai yayi mata text ta twitter ta fito gashi. Hindu kuwa har nuna ma Dimples tayi tana wani murmushi dan taga kalar ajin da Jalil yake dashi, mikewa Dimples tayi batare da tace komai ba ta dauki mayafinta, daman Kimono ta dora akan riga da wandon da yake jikinta, sukace ma Maman Amrah zasu ga wani a waje, yanzun zasu dawo. Jalil yana cikin jira ta fito sai gari ya juye hadari ya haɗu, anan iska ta ɗauke mishi hular da ta Kawu ce ta aro ta kuwa cilla cikin unguwa. Haka yayita bi yana “Wait! Wait!!” shi kaɗai kamar mahaukaci. Dan ya san halin Kawu tunda ya hana shi taba mishi kaya, Hular bata tsaya ba saida ta shiga cikin wata muguwar kwata. Haka ya saka hannu ya tsamo ta. Nan yayi dama dama da hannunsa. Zare ido yayi ya soma dube-dube. Sam baisan nan ne kofar gidan Maman Amrah ba, dama Dimples ta hana Hindu bashi asalin address din tace mata kada ta bashi asalin address ɗin, koda baiyi masu ba zasu iya yi mishi fuska kamar basu bane. Nan su Hindu suka fito suka ganshi tsaye kamar mahaukaci sai zufa yakeyi ga kaya duk datti, balle kuma kayan sunyi mugun koɗewa. Bai gane Hindu ba tunda hotuna kan bambamta. Balle ita da tafi kyau a fili fiye da hoto. Saiya ƙarasa wajensu yayinda suka fito domin su taimaka mashi da ruwa ya dauraye hannun shi harma da bakar leda ya samu ya saka hular kar Hindu ta fito tagan shi Yana isa wajen su, bayan yayi sallama yana ajiyar zuciya saboda gudun dayayi. Dimples na watsa mishi wani irin kallo daya saka shi shan jinin jikin shi, a daburce ya soma magana “Dan Allah kuyi haƙuri, ruwa zaku taimaka mun dashi in wanke hulata data fada kwata...” Ran Hindu yayi mugun ɓaci saboda bata ƙaunar rainin wayau, kar mutumin nan ya ja mata bad luck, batason wani akasi da zai faru kafin taga Jalil, Dimples ce ta riƙe mata hannu domin su saurare shi, bata son mutane, amman kuma hakan baisa tana da wulakanci ba, musamman taga zai girmesu nesa ba kusa ba, ganin haka yasa Jalil murmusawa cikin yanayin da duk idan yayi a mudubi yakan ga yayi matukar kyau “Dan Allah ruwan zaku taimaka mun sai yar bakar leda in saka hulata..." Yai maganar yana dorawa da "Nazo wajen wata abin begena ne Hindu shine hulata ta faɗa kwata" Da yake Allah yayi mishi surutu na rashin dalili "Me?" Dimples ta tambaya tana son taji ko kunnuwanta yaji 'Hindun' da Jalil ya furta. Yana dan fadada murmushin shi ya sake maimaitawa "Hindu, ko kinsanta ne? Wannan karin Hindu da take jin jiri na shirin kwasarta ce tace "Jalil?" Muryarta cike da matukar shakku, dago idanuwa Jalil yayi yana karema Hindu kallo, sai yanzun da ta kira sunan shi tukunna ya ganeta, yanda take kallon shi ya tabbatar mishi da kiris take jira ta kwada mishi mari "Kan uban can" Cewar Hindu tana dorawa da wata ashariya da bata tabayin irinta ba, kafin ta sake wani motsi Jalil ya ari takalman kare ya yanki Hanya da wani irin gudu cikin yadin shi da yake kwasar iska yana hura shi kamar zai tashi sama. Cikinta Dimples ta rike saboda da dariyar da take tattaruwa kafin ta fito fili da wani irin yanayi da yasa Hindu taji idanuwanta sun cika taf da hawaye. 'Wannan wacce irin rayuwa ce' Ta tambayi kanta, me yasa na rana daya abinda yake karbar mutane ita bazai karbeta ba? Me yasa duk wani abin arziqi da idan wasu matan sukayi dangane da samun Mijin aure na gari ita idan ta kwatanta sai yazo mata a baibai? Wacce irin rashin sa'a ce take bibiyar rayuwarta har haka? 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 4 Zatai karya idan tace gabanta baya faduwa. Asali tunda suka fito daga gida wata zufa take tsatssafo mata a saman goshi har zuwa tafikan hannunta, da sukaje gidan su Ummi sam kasa samun sukuni tayi. Biebee na kula da ita, batai mata magana ba saboda ta fada mata daga farko bataji ba, sau daya take gaya maka gaskiya ta koma gefe ta saka maka ido, yanda zataji dadin cewa ta fada maka baka dauka ba idan komai ya kwabe. Bata sake shiga tashin hankali ba sai da Elias ya kira wayarta, jikinta har bari yake "Bie muje...Anty ta fara kirana" Hindu ta furta muryarta na rawa, kai Biebee ta jinjina mata, Ummi ce tace "Wai tun yanzun zaku tafi? Kai dan Allah.... Hindu ba Anty tasan nan kuka zo ba" Murmushin karfin hali Hindu tayi "Zata fitane zan dora girki, yamma nayi shisa" Kai Ummi ta jinjina tana fadin "Bari in dauko Hijab dina in rakaku" Wannan karin Biebee ce ta girgiza mata kai "Dan wahalar da kai? Mu biyune fa, kiyi zamanki dan Allah" Duk da haka saida Ummi ta rakasu har bakin kofar gida, sannan sukayi sallama, da sauri Hindu ta daga kiran Elias daya shigo a karo na ukku "Haba Hinduna, inata kira sai an mun sarautar za'a daga?" Dan murmushi Hindu tayi "Kana ta ina?" Sai da yayi jim tukunna yace "Bakin wani saloon Umtaz..." Kai Hindu ta jinjina dan ta gane wajen "Gani nan karasowa to" Ta fadi tana sauke wayar daga kunnenta batare data jira amsar shi ba, ta kalli Biebee "Wai yana wajen Saloon din Umtaz" Biebee ta jita, bata dai ce komai bane, suka dan kara sauri kowa da abinda yake sakawa cikin zuciyar shi. Suna karasawa kwanar da zata kaisu titin da Elias yace yana tsaye Biebee ta riko hannun Hindu "Zuwa zakiyi, ki kira shi kice yana cikin wacce motar, ki fara hango shi tukunna" Shawarar Biebeen ta zauna mata, wayarta ta danna tana kiran Elias da ya daga a bugun farko "Ban ganka bafa... Kana cikin wacce mota?" Hindu ta fadi kafin ya numfasa "Cikin wata jar golf" Elias ya amsata ta dayan bangaren "Golf?" Hindu ta maimaita cike da mamaki, daga ita har Biebee suna zira kansu suka hanga wajen saloon din, akwai motoci jefe a wajen, amman jar golf din da suke hangowa tayi kama da motar da ake dibar jogon kaji ana cin kasuwar kauyuka da ita, ga wata irin kura da ba zasuce ta kasa bace ko qoqewar da fentin motar yayi bane ba, kallon juna sukayi, Biebee na kokarin ganin bata kwashe da dariya ba, a hankali tace "Kice bari mu duba" Hakan Hindu tace tana sauke wayar da wani irin yanayi da yake fassara 'akwai matsala' bayyane a fuskarta, dariya Biebee takeyi harda rike ciki "Wanne irin iskanci ne wannan Bie? Ya zanyi ni yanzun... Jar golf yace, ni kuma waccen motar kadai ce ma golf a duk motocin titin nan, anya shine? Ko dai wasa yake mun? Aike kinga motocin gidan su" Kai Biebee take girgiza mata "A gidan ubanwa naga motocin gidan nasu?" Tsaki Hindu taja "Ban nuna miki hotunan shi ba?" Wani kallo Biebee tayi mata "Da kika nuna mun hotunan bance miki ni ban yarda dashi ba?" Numfashi Hindu taja ranta a bala'in bace "Ni yanzun ya zanyi? Juyawa zamuyi wallahi..." Kai Biebee take girgiza mata "Zai yiwu wasa yake miki, ki sake kiran shi kice ya fito ko shi zai hango mu, kice kin saka hijabi ruwan toka" Duk da taso su juya din tunda Elias yai mata wannan rainin hankalin, amman kuma ita taga hotunan shi, ta kuma ga kalar motocin da yake hotunan a jikinsu, maganar Biebee zata iya zama gaskiya, kilan shima yaga golf dinne yake so ya gwadata, yaran masu kudi kanyi haka wani lokacin dan suga ko tsakani da Allah kake son su. Shisa ta sake kiran Elias ta fada mishi abinda Biebee din tace su duka biyun suna labe jikin katangar da zata hadasu da titin da Elias din yake. Sai dai ga mamakinta murfin motar aka bude ta mazaunin da bana dire ba bane, kafin taga an ziro kafa daya, ana kama murfin motar, sannan taga ya saka dayan hannun shi kamar zai tattaro wani abu ya fito dashi, a tare suka ware idanuwa ita da Biebee "Butar shayin buzaye..." Hindatu ta fadi dan shine karshen zaginta idan abu yakaita makurar mamaki, Biebee na karbe zance da fadin "Inalillahi... Ke Hindatu mun shiga uku....La haula wala quwwata ila billah.... Kinga me nake ce miki ko?" Cewar Biebee da take a tsorace ganin shanyayyar kaface Elias din ya tattaro ya fito daga ita daga motar yana jingina jikin shi da murfin motar, sannan yai amfani da dayan hannun shi yana fara kiran wayar Hindu da batasan lokacin ma data sauketa daga kunnenta ba, sai da taji ringing dinta, dagawa tayi batare data kara a kunnenta ba, tana hango Elias daya bude baki yana fadin abinda bataji ba ta cikin wayar. Tana godema Allah da duk yanda Elias yayi naci hotonta daya yagani wanda yake a dp dinta na WhatsApp, ca tayi shida zai ganta wata rana harya gaji. Wayar ta kashe gabaki dayanta "Na shiga ukuna ni Hindatu" Ta fadi tana kallon Biebee da mamaki ya hanata dariya, hannun Hindun taja suna komawa baya "Mu zagaya ta baya mu wuce gida" Bata bari Biebee ta sake fada mata ba, da sauri suka nufi inda suka fito dan suyi zagaye zuwa gida. Sauri suke kamar zasu tashi sama, basu fara tsagaita tafiyarsu ba saida suka sha kwanar da zata kaisu gida, sannan Biebee tace "Elias..." Tana jan sunan kamar yanda Hindu takan fada kar suyi mata iskanci cewar sunan shi Iliya, kafin ta kwashe da wata irin dariya tana dorawa da "Yar banza... Daman nabari kin karasa wallahi" Hade rai Hindu tayi tunda ita bataga abin dariya a cikin wannan al'amarin ba, tana da yakinin ita kam yarda da wani namiji da zasu kara haduwa a 2go zai mata wahala, daman Khadee ta fada mata itace taki ji. Tace mata babu kalar tarkacen da babu a 2go "Yanzun meye abin dariya?" Ta bukata tana kallon Biebee din da taci gaba da dariya kamar haduwa da Hindun tayi da gurgu shine abu mafi nishadi da ta taba cin karo dashi a duniya. Dogon tsaki Hindu taja tanayin gaba, Biebeen nabin bayanta da fadin "Haba Kawata ta Eliass" Shiru Hindu tayi mata, duk tsokanar da Biebee take mata bata kulata ba, ko sallama batayi mata ba ta shige gida. Kai tsaye dakin su ta wuce ta cire Hijabinta tana ajiyewa akan gado, ta ajiye wayar da takejin duk yanda ta saba da ita zatayi kwana biyuma bata dauka ba, idan Elias ya kirata ya gaji zai hakura. Zatayi amfani da lokacin tayi karatun jarabawar da yake gabanta. Amman duk da haka bayan ta fito dan taya Anty hidimar girkin dare sai da taji zuciyarta na lugude kamar Antyn zata gane abinda ya faru, a tsorace take har suka gama aikin, duk surutunta ko magana bata son yi sosai. * Duk da girkin Anty ne, bangaren Mama ta shiga tana idar da sallar Magriba, ta kasa hakuri, tunda Huzaifa ya karbi memory dinta yace zai turo mata fina-finai, tun safen bata kara ganin shi ba har yanzun. Halima tagani, batama san ta dawo ba, dan taje gidan Yayan Mama din da yake Unguwar rimi, akwai yar shi da suke KASU tare, suna karatun shirye-shiryen jarabawar su ta zangon karshe a shekararsu ta uku. Dan abokin Baban ne ya manne ma Halima, da Baba yaso sai ta kammala karatunta, Hindu batasan meya faru ya amince aka saka rana ba, gashi yanzun bikin sai kara matsowa yake, sauran watanni biyu, tana kammala jarabawarta da sati daya. Sosai Hindu take fatan samun mijin da yafi Yaa Ahmadi kamar yanda suke kiran shi, zatayi karya idan tace sanda yake zuwa gidan baya burgeta, duk da bai karasa irin tsayin Mijin da take so ba, amman ya iya gayu, gashi yana shigowa zaka fara jin kamshin turarukan shi na tashi. Magana daya zuwa biyu Yaa Ahmadi kan jefa turanci cikin kwarewa. Amman taji dadin auren Halimar da zaiyi, ko ba komai basuyi asarar hadadden gaye ba, a nata tunanin ya zama nasu, ta kuma ji dadi ba kadan ba "Yaa Halima yaushe kika dawo?" Numfashi Halima ta sauke, cikin sanyin muryarta ta amsa da "Da yammacin nan, Anty tace kunje duba kawarku ke da Biebee" Kai Hindu ta daga mata, tana jin yanda zuciyarta tayi tsalle data tuna fitar da ta saka Elias fadowa a ranta, duk saurin karbar memory din ma babu amfanin da zai mata yau, dan ba zata kunna wayar ba. "Eh kam... Yaa Huzaifa ya shigo?" Kai Halima ta girgiza mata, sallamar da sukaji na saka su juyawa su duka suna amsawa, Hindu na dorawa da "Ina wuni" A dakile ganin Musa ne dan Kanwar Mama, ta dauka tana son farin namiji, sai akan shi ta fara gane kalar namiji itace karshe cikin jerin abinda take so a tattare dashi, gajartar Musa ta sa ko kadan baya burgeta, ba ca yayi yana son ta ba, kwata-kwata a tunaninta data kwatanta idan yace yana sonta dinne baiyi mata ba. Ba sau daya ba, ba sau biyu ba, babu wani dalili tana jin mutum baiyi mata ba, amman kiyayyar da takewa Musa dabance, kuma sai ya dinga abu kamar baisan gajere bane, yana daddaga kafadun da takeji kamar ta kwantara mishi wani abu akai dan takaici "Hindun Baba....Ya kike?" Ya fadi cike da iyayin da ita kadai take gani a tare da Musan, ta tsani yanda ta karfi da yaji yake nuna akwai wani kusanci a tsakanin su, sai yashe mata baki yakeyi. Mama tace Baban shi qwara ne, da Hindu ta dauka a bakaken fata kawai akafi samun guntaye, amman saiga Musa ya fito a qwaran shi sak, amman tana hango tsakiyar kan shi "Lafiya..." Ta amsa can kasan makoshi, da Halima bata wajen ko inda yake ba zata kalla ba, amman tasan halin Halima, ta kwada mata mari ba abu bane mai wahala, ko Yayarsu Salma basa tsoro haka kafin tayi aure, Halima bata wasa dasu, a haka sai kaganta kamar tana da sanyi, sai kaji saukar mari akan kuncinta, dan bata son raini, bata kuma so taga kana wulakanta mutum, shisa ba sosai suke shiri da Hindu ba, sau daya ta taba cewa Musa gajere a gaban Halima ta kusan kwada mata mari 'Ko gawayi ba zaki iya yiba, kina kushe halittar da Ubangiji yayi kamar bakije islamiyya ba, idan gajartar shi batai miki ba, sai a samo tsani kihau sama kiji dalili. Wallahi Hindu ki iya bakin ki, ba tun yau nake jin yanda kike kushe halittar mutane ba, idan baki haifa ba, zaki iya aura' Shine abinda Halimar ta fada mata, a ranta ta dinga zabga addu'a kar Allah ya amsa, dan taji haushi sosai. Tunda bakin cikine, ita ta sami me kyau tana mata fatan auren gajere. Ko maza sun kare sai ire-iren Musa gara ta hakura da auren, yanzun ma dakinsu Khadija ta wuce dan taga Musa naso ya karayi mata wata magana. Halima ce taje ta kawo mishi ruwa bayan ya zauna tana fadin "Bari in kira maka Mama" Kai Musa ya daga mata, ba wani dalili bane ya kawo shi gidan sai Hindu, tun randa ya fara dora idanuwa akan yarinyar ta kwanta mishi, yayiwa Mama magana akanta tace ya dakata ta kammala sakandire, amman sosai yaso ace ko sanar da ita Hindun Mama ta bashi dama yayi kar wani yazo yayi masa shigar sauri. Mace irin Hindu ba'a saka wasa a neman auren su, amman duka kasa da shekara daya ya rage musu. Har kasan ranshi yake jinta, lokutta irin haka yakan kasa hakuri sai yazo gidan yaganta sun gaisa, kullum kyau yake kara ganin tana yi mishi da yan matancinta da yake kara fitowa. Dan haka Mama na fitowa suka gaisa yace zai wuce. Murmushi Mama tayi, ba tun yau ta kula yakan zo gidan bane da sunan gaisuwa dan kawai yaga Hindu "Ka gaishe su, dan Allah kace ma Hajiya ta shirya da wuri jibin zuwa sunan yar wajen Jummai... Nima da wuri zan fito in shaa Allah" Kai Musa ya jinjina mata sukayi sallama ya wuce. Zata so yaron da Hindu saboda hankalin shi, kuma duk a gidansu babu wadda ta shaku da ita sama da Hajiya, mahaifiyar Musa, ga Baban shi ma mutum ne na kirki dayake samun shaidar mutane a duk rana, tace ya bari tagama sakandire ne sanin tsarin Baban su Hindun, kuma yaran yanzun ba'a yanke musu hukunci, gara shi Musan ya fara neman soyayya a wajen Hindu kafin manya suce zasuyi katsalandan su sha kunya. * Satin bikin Halima yayi dai-dai da satin da Hindu ta fara kallon film din korean da yayi tashe a shekarar 2010 mai suna Secret Garden da ita sam bata san yanda akayi sai yanzun take kallon shi bayan shekara uku dayin shi ba. Daga farko film din yaso yayi mata wani iri, dan ta saba ganin Lee Min Hoo da ya samu wajen zama a zuciyarta yayi kane-kane yana saka duk wasu sauran jaruman fina-finan korea sai take ganin su daban, tamkar kyawun su da soyayyar su bata kai tashi ba. Sai da ta rasa abin kallo, da yake yanzun a wayarta take yin kallon, sai ta saka earpiece ta dade kunnuwanta yanda babu wanda zai dameta. Yanzun ma saida ta tabbatar har wanke-wanke tayi, tayi sallar isha'i, bata da wani assignment tukunna ta saka earpiece tana kwanciya kan kujera dan daren jiya har mafarkin film din ta dinga yai saboda yanda ta saka shi a ranta. Soyayya ce irin wadda take so, zuwa yanzun ta daina ganin fuskar jarumar, dan ta jima da daukar tata fuskar ta makala a jikin jarumar, ya zamana tanajin kamar da ita ake zuba madarar soyayyar da take faruwa cikin film din. Daman haka rayuwa take, sai kaga mijinka ya fado ta inda baka tunani. Tasan hakan na faruwa a Najeriya, kawai ba sosai ba. Yanda jarumin duk kudin shi, da ajin shi ya bada kai bori yahau wajen soyayya ya gama tafiya da Hindu. Haka take so ta kasance da ita, dukkan kudin shi ya zama nasu ne, store dinsu da ya kusan rabin barnawa jarumin ya dauki jarumar dan ta zabi dukkan kayan da take so, amman ta watsa mishi kasa a ido tana nuna bata so, ta juya tana fara tafiya, amman duk irin wulakancin da tayi mishi sai ca yayi 'Nal tteona jima (Karki barni)' Cikin yanayin daya burge Hindu, bata san lokacin da ta mike ba, tana tsayar da film din, idanuwanta ta lumshe tana bude su, tana jinta tamkar a kasar Korea lokacin data maimaita kalaman da jarumin ya fada, tana watsa hannayenta, ji tayi kamar ba dai-dai tayi ba, haka ta shiga maimaitawa, sai ta girgiza kanta ta sake maimaitawa, ko kadan bata kula da Zaid daya shigo ba yanata magana dan ta tare mishi hanya, sai da taji ya dala mata wani duka a gadon baya hadi da tureta "Dalla matsa...wawiya kawai" Ya furta a kufule yana shigewa ciki, dan zai tambayi Anty aron wayane ya kira Baba, katin shi ya kare, kuma yana bukatar magana dashi kan lemukan daya aike shi siyowa da za'ayi amfani dasu wajen bikin Halima din. Sosai dukan ya shigi Hindu, saida ta cire earpiece din ta samu waje kan kujera ta zauna, tana tuna yanda ko kusa batayi hanyar Korea ba, da Zaid bai dala mata dukan da yayi mata ba yanzun, shisa komai na kasashen ketare yake burgeta, yanayin 'yancin da suka samu na rashin kwaba kansa ta hasashen itace a wannan matsayin. Ka kwanta sanda kaga dama, ka fita lokacin daka ga dama, amman duk gidan Khadee ta dauka zata fahimci wannan fannin, data gwada mata magana tsaki taja tana fadin 'Sai a sakeka kamar tunkiya, shisa kike ganin ga rayuwar su nan, babu kan gado, musulunci ma Rahma ne wallahi' Shiru Hindu tayi ta kyaleta, dan ita ba maganar musulunci takeyi ba, maganar zamantakewar rayuwa takeyi. Wayaki irin wannan 'yancin, ka kula duk kalar saurayin dakaga dama, kaje party babu wanda zai hanaka, har tsakar dare fita sukeyi. Amman sukam a gidansu, mazan ma akwai shekarun da zaka kai kafin ka fara fita bayan Magriba idan ba masallaci zakaje gabatar da sallar isha'i ba. Balle su kuma da in suka dawo daga islamiyya shikenan sun gama fita sai dai in su duka gidan zasuje wani waje. Ko aiken su ma ba'ayi tunda akwai maza a gidan. Gajiya tayi da tunani kan abinda ba zata canza ba, hakan yasa ta mike tana nufar daki, da niyyar idan Allah ya bata aron rayuwa, ta sami kalar mijin da take mafarki, zasu gina rayuwar su kamar ba daga yankin Najeriya suka fito ba, har yaransu zasu zamana daban, zasu taso cikin yancin duk da ta rasa a yanzun. Shisa Baba yake da waje daban a zuciyarta, shi kadaine mutum daya a yanzun da yake da cikakken ikon da zai takurata amman baiyi hakan ba. Kwanciya tayi tana fasa yin kallon, gara tayi bacci kawai, dan bama lallai tunani yabarta ta nutsu kan kallon ba. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 15 Cikin sati daya, ko idanuwanta ka kalla sai kaga yanda tayi zuru-zuru. Anty da ta tambayeta haka kawai tace mata "Karatun ne ya kara zafi Anty" Jinjina kai kawai Anty tayi, da damuwa a cikin idanuwanta "Ki dinga hutawa dai" Murmushi ta tsinci kanta da yi, Anty na daya daga cikin iyayen da basu cika bayyana kaunar su a fili ba, amman a cikin duk wani motsi da zatayi sai ka karanci tsantsar kaunar da take yiwa yaranta. Su kansu suna mamakin yanda take gane wani abu yana damun su, ko ya canza a tattare dasu. Hindu ba zata iya gayawa Anty asalin abinda yake damunta ba, batasan ta inda zata fara ba ko da zata iya. Jaruman litattafan hausa kan sha gwagwarmaya a ciki labaran su, kafin su samu cimma burin su, amman sunayin hakanne tare da Samarin, suna nuna musu wata irin zazzafar kauna a duk wani motsi da zasuyi. Samarin basu taba zama matsalarsu ba, sai dai dangi, ko wani abin daban. Amman cikin sati daya, Hamza ya zame mata matsalar da ki a mafarki bata hango faruwarta ba, ga soyayyar shi da ta samu waje tayi mata zaune. Ta dauka tana da rikici, ta dauka ta iya rigima, ta kuma dauka ta gama gane cewar shi Hamzan yana da rikici, sai a satin nan daya, tunda ya fara kiranta da budurwar shi, ko wayarta ya kira yaji busy saiya tsareta da tambayoyi akan wa take magana da shi, idan wani da ba dan uwanta bane ya fara tashin hankali kenan, wani irin kishi take gani tattare da shi daya fara bata tsoro. Yanzun kiri-kiri yayi mata blocking din Ahmad daga Instagram har Twitter din ta, harda fadin "Allah ya isa idan kika kara magana da shi, dan bakya son shi baya nufin shi din baya jin wani abu a kanki, ko da bayaji ni baimun ba, bana son shi, bana so kina magana da shi" Ahmad din har kiranta yayi, bata daga ba saboda batasan me ma zatace mishi ba, taga text din shi 'Naga kinyi blocking dina Hindu, bansan ko nayi miki wani abu bane ba, na kira baki daga ba' Goge text din tayi saboda kunyar Ahmad din da takeji, yana da hankali da matuqar kirki, da ta gwada cewa Hamza "Ba zai yiwu ka dinga mun blocking din mutane ba, wasu abokan karatuna ne, idan ina bukatar tambayar su wani abu fa?" Yanda ya fadi "Ni? Ni kike fadama ba zai yiwu ba?" Sai da tadan raba wayar da kunnenta, kafin ta mayar tana jin shi yana cigaba da fadin "Kome zaki tambaye su, ni ki tambayeni, ni kadai na isheki, banda yan uwanki, ni kadai ne namijin da zai kasance a rayuwar ki, gara ki saba tun yanzun" Kafin ma ta sami fadin wata magana harya kashe wayar shi. A kwanaki bakwai rana daya ce basuyi tashin hankali da shi ba, sai ya hau Instagram dinta, ya zaqulo tsohon chat ya tisa mata rigima a kai, ba karamin tashin hankali tagani wajen shi ba, akan hirar su da ya gani da Jalil, inda yasan yanda zancen ya qare ma da bai tashi jijiyar wuya a kai ba. Ita kam tunda ya bata password din shi ta hau sau daya, bata ma sami nutsuwar da zata koma ba. Sai yanzun da batada abinda zatayi, bata da wani assignment saboda jarabawa data qarato, sai project din zangon kawai, da a hankali take bin zanen. Da yake asabar ce, a daki ta wuni, Anty ma bata sakata aikin komai ba, dan yanda taga tayi zuru-zuru sai ta kyaleta, taji dadin hakan har ranta. Yanzun ma tunda ta idar da sallar la'asar ta koma kan gado tayi zamanta. Hamza yace mata yana da aiki, idan anyi Magriba zai zo ya ganta, tunda duk satin basu hadu ba, sai dai video call kawai da sukeyi. Yau din ma tun safe, sai text din shi bayan la'asar "Azkar din yamma" Ta amsa shi da tayi, ko tana makaranta ne haka yake mata wannan tunin, yanzun da Asuba duk baccin da yake idanuwanta in batayi karatun Qur'ani ba sai yasa ta tashi, wani lokacin video call zai kira yaga ko ta tashin, yakan ce mata "Ranar ki zata tafi dai-dai idan kika fara ta da sallar Asuba a kan lokaci, kiyi karatunki koya ne, kiyi azkar, sai ki rufe da sallah raka'a biyu idan rana ta fito" In ta nemi yi mishi musu saiya ja mata ayoyin da zasu kashe mata jiki, sosai da duk rana Hamza yake kara samun waje a zuciyarta, lamurran shi kuma na bata mamaki sosai da sosai. Twitter din ta hau tana cin karo da tarin notifications da ta fara budewa, taga Mansy ce da tayi ma Hamza magana, ba gane me tace tayi ba tunda da fulatanci ne, wani irin tsaki taja, tsanar da tayi mata na dawowa farko "Tsohuwar banza mai tallar goro" Ta furta a fili tana kara dorawa da wani tsakin, ta tafi DM din Hamzan ta bude, nan ma na Mansy ne a farko "Nawan ina kaje ne yau haka?" Ta karanta sakon da tayi da harshen Hausa, wato munafunci ne yasa take mishi yare a bainar jama'a, anan kuma takeyin magana da wanda kowa zai iya fahimta. Shiga sakon tayi, zuciyarta nayin tsalle ta dawo makoshin ta, kafin ta koma kirjinta inda taci gaba da dokawa da wani irin ciwo da yasata yin tari, idanuwanta har yaji suke da abinda ya wuci hawayen da taji sun taru cikin su, hotunan da Mansy ta turo mishi ne tana dorawa da "Wanne yafi kyau?" Rigar mama ce mai hade da wani wando da Hindu takan ga turawa sun saka a bakin ruwa, bata ga dalilin da zaisa Mansy ta turo ma Hamza irin wannan hoton bane ba, ko da soyayya sukeyi abune da bai kamata ba sam-sam. Amman kamar yanda Dimples kan fadane "Ni banga dalilin da zaisa mata suje suna fada da yan matan mazajen su ba, ko ke budurwa da bakima shiga gidan shi ba ki fara tsanar matan da suke tare da shi ba, saboda koma me yake faruwa a tsakanin su, shi ya bada fuska" Amman hakan bai hanata jin kamar ta soka ma Mansy mashi ba, sama tayi tana karanta hirarrakin su da ko kadan babu kintsi a ciki, sam batasan hawaye take ba sai da taga digar su saman screen din wayarta, sosai kirjinta yake mata zafi, bata taba jin ciwon zuciya irin wanda takeji ba yanzun. Kwata-kwata tashin hankali bakonta ne, fitowa tayi daga hirar, tana cigaba da bude sakonnin sauran matan, da suke ma Hamza tallar kawunan su, sai dai amsar shi daya ce ga duk wadda ya amsa "Digits" Ma'ana lambar wayar kenan, in suka ajiye kuma babu wani abu da yake sake hadasu, amman hirar su da Mansy ta gama tabbatar mata da abinda yake faruwa a tsakanin Hamza da sauran matan. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ta tsinci kanta da furtawa tana sauke wata ajiyar zuciya saboda kukan da takeyi. Hamza na bin mata, ko baya bin sauran matan yana tare da Mansy. Wannan ba zargi takeyi ba, hirar su ce ta tabbatar mata da hakan. Wayar ta ajiye kan cikinta, tana saka tafukan hannuwanta duka biyun ta rufe fuskarta da su. Kuka takeyi da ba zata tuna ranar da tayi irin shi ba, sosai zuciyarta take ciwo kamar zata fito. Tana nan kwance, tayi kuka har fuskarta ta kumbura, kafin ta iya mikewa tana shiga bandaki, ta wanke fuskarta, tana dauro alwalar Magriba. Tana fitowa ana kiran sallah, lokacin da yayi dai-dai da shigowar Asma dakin da sallamarta da Hindu ta amsa murya a dishe. Tana kuma yin sauri ta kabbara sallah, tana jin Asma ta shiga bandaki, tana fitowa kuma ta fice daga dakin. Tana idar da sallah, dakyar ta iya yin azkar, da ta daga hannuwanta sai ta rasa addu'ar da zatayi, tana tsaka tsakiya neman wani canjin ba Hamza ba, ko kuma nema mishi shiriya, kafin ta yanke hukuncin tsayawa a nema mishi shiriya, dan zuciyarta ta karyatata wajen tunanin cewa abinda tagani akan Hamzan ya canza abinda take ji, yana nan daram a ranta kamar komai bai faru ba. Wayarta data fara ruri ta mika hannu ta dauka tana ganin shine, dagawa tayi ta kara a kunnen ta "Ina cikin gidan ku" Ko magana batayi ba ta sauke wayar daga kunnenta, tana mikewa. Ko fuskarta bata duba a mudubi ba, hijabin jikinta kawai ta sake, tana daukar ruwan toka, da ta Asma ce ta zira a jikinta. Ba zata tsaya shafa wani abu ba, shiya sakata kuka, ya kamata yaga haka, ba zata boye mishi tana cikin yanayin damuwa ba. * Komai sabone a wajen shi, inda wani a cikin abokan shi zaice mishi a shekarar nan zai kira wata yarinya da budurwar shi zai karyata. Ba zaice ga yanda akayi ya ce Hindu ta saka shi a layin samarinta ba, yafi ta'allaqa hakan akan yanda tunaninta da wani saurayin yasa shi ganin wani hadarin kishi na gilma mishi ta cikin idanuwan shi, kirjin shi har zafi yakeyi. Bayason kowanne namiji a kusa da ita banda shi, bayason wani yaji muryarta, balle yaji yana son ya riketa kamar yanda yakan ji duk idan tana magana. Aikin daya sakko su gaba bai hana shi tunanin halin da take ciki ba, da wa tayi magana a makaranta, wayai mata magana, waya tare ta a hanya. Shi kadai sai ya tsinci kan shi da jan karamin tsaki, yanzun tunda ya shiga Instagram dinta rabon daya shiga nashi, yana kai kullum yana ganin yanda ta sake tana hira da maza da yake bala'in bata mishi rai. Yau ma duk da ya yanke hukunci ajiye komai yaje ya ganta, haka ya shiga Instagram yana dudduba sauran chats dinta, dan duk wanda ya karanta saiya goge gabaki daya, yayi blocking idan namiji ne. Matan baya bi ta kansu sam, tsaki yaja ganin wani yayi mata sallama tafi biyar "Wawa kawai" Ya fadi yana saka AbdulHafiz da yake shan shayi yana aiki a system din shi ya dago da ido ya kalle shi "Me yasa maza basu da aji ne?" Hamzan ya tsinci kan shi da tambaya, yana saka AbdulHafiz yin murmushi "Me yasa wasu mazan basu da aji zaka ce. Me ya faru?" Tsaki Hamza ya sake ja, duk satin nan baya rabuwa da ciwon kai, akan Hindu ne kuma, ita ce sabon ciwon kan da ya shigo rayuwar shi "In kaga mazan da suke DM dinbHindu suna mata magana zakayi mamaki wallahi, kamar basu da wani aiki banda bin yaran mutane" Shayin AbdulHafiz ya kurba, sannan ya ajiye kofin a nutse, ba sosai yake saka kananun kaya ba, yanzun ma dan suna gidane, anan suke ta aikinsu tun safe, tracksuit ne a jikin shi, riga da wandonsu, yaja zif din rigar har wuyan shi a rufe yake ruf, dago da idanuwan shi yayi yana saukewa kan Hamza da yake girgiza kan shi cike da dana sanin subutar bakin da yayi akan Hindu din. Banda Fodio babu wanda yasan da maganarta, shima Fodio din ya dauka Hamza ya sami abinda yaje nema ya barta. "DM? Screenshot ta turo maka?" AbdulHafiz din ya fara tambaya, Hamza ya riga yasan ba zai iya kaucewa maganar ba, ya riga yayi subul da baki, kuma yanayin fuskar AbdulHafiz din ya nuna mishi ba zai bashi wannan damar ba yau, gashi su kadai ne, Arafat da su Fodio suna kamfanin su. Daga shi sai AbdulHafiz din a gidan, da saiya sake maganar, AbdulHafiz zai dauka bayason yayi a gaban su Arafat a lokacin, zai kyale shi. Kai ya girgiza ma AbdulHafiz din "Da kai na nake gani" Shayin AbdulHafiz ya sake kurba yana ajiye kofin "Abu biyu zan fada maka, ban san me kakeyi a Instagram ko Twitter din ta ba, amman hakan zai saka rashin yarda a tsakanin ku, idan ka yarda da kanka, ka yarda da soyayyar da take maka, sauran mazan bai kamata su dame ka ba" AbdulHafiz ya fadi yana dorawa da "Ka zama Sarki a masarautar yarinyar da kake tare da ita, sauran mazan duk da zasu zo fadawa ne, ba su da wani muhimmanci, da kanta zata baka labari kuyi dariya. Karka fara dora alamar tambaya akan zaman ku, in bata baka dalilin yin hakan ba" Yana jin kalaman AbdulHafiz dinne, amman bai yarda dasu ba, badan bai yarda Hindu tana son shi ba, kawai dai yana so yaga dawa take magana ne. "Wacce Hindu din?" AbdulHafiz ya tambaya, tunda maganganun da yayi basa bukatar amsa, kawai saurare ne, idan Hamza yaga dama ya dauka, idan baigani ba ya rigada yayi nashi bangaren. "Yarinyar da ka amsa a DM dina" Kai AbdulHafiz ya jinjina, yagane ta, yana son yaji tabbaci ne daga wajen Hamzan. Sosai ya gyara zaman shi yana tattara duka nutsuwar shi da hankalin shi akan Hamzan, dan maganar da yake son fadi na da matuqar muhimmanci a wajen shi "Nasan kaddara zata hadaku idan Allah ya rubuta hakan ko da ban amsata ba, kaddarar tazo da ni ne sanadi. Ka jini Hamza, saboda zan fada maka sau dayane, kamar dan uwa kake a wajena, kasan hakan, ba yau ne na farki dana fada maka ba, ina maimaita maka ne...." Numfashi Hamza yaja yana fitarwa, tun kafin AbdulHafiz din ya karasa maganar ta tsinci kanshi da son tashi ya gudu yabar dakin, dan ya kauce ma jin koma meye zai fada "Kusancin da yake tsakanin mu ba zai sa ka darsa mun kokwanto a neman lahirata ba Hamza. Kana jina, idan ba da niyyar aure kake tare da yarinyar nan ba, idan babu alkhairi a tare da niyyar ka, ka yanke koma menene a tsakanin ku, bazan zama silar baka ticket din da zaka sakata a layin matan da kabi ba. Baka isa kai mun haka ba, wallahi baka isa ba, kaji na rantse, ban isa in hanaka abinda kakeyi ba, shisa nake binka da addu'a, amman banda ita, banda Hindu....ba rokon ka nakeyi ba, fada maka nayi. Bazan yafe maka ba wallahi..." AbdulHafiz ya karasa maganar yana so Hamza ya fahimci da gaske yake, idan ya bata musu yarinya zai yanke alaka da shi, maganar farko tayi mishi yanayi da Nabilar shi, batayi kama da matan da Hamza ya saba bi ba sam, ba zai zama sanadin da zata lalace ba. Ba zai yafe ma kan shi ba idan Hamza ya taba ta, kamar yanda ba zai yafe ma Hamzan ba. Kofin shayin shi ya dauka yana tura kujerar da yake kai baya, hadi da mikewa dan yaje ya karo wani shayin da yake kitchen cikin kettle. Nan yabar Hamza a zaune yanajin kamar an mishi wanka da ruwan kankara. Shi bai shirya yin aure ba, sam babu wannan tsarin a rayuwar shi nan da shekaru biyu ma, ko gidan shi bai gama ba. Bai san yanda AbdulHafiz din yake so yayi ba, yanajin dai yanzun ko Hindu bata isa ta raba shi da kanta ba, balle kuma wani. Har ran shi yanzun ba zaice ga abinda yake da niyya akan ta ba, yana son kasancewa da ita, amman shi bai shirya aure ba sam. Kamar yanda bai shirya yanke alakar da take tsakanin shi da AbdulHafiz ba, zai iya hakura da Hindu ko da aurenta zai idan hakan zai shafi alakar da take tsakanin su da AbdulHafiz, yana jin shi kamar dan uwan shi, sun wuce matakin abokantaka. Sosai kan shi yake mishi ciwo, AbdulHafiz ne ya dawo "Kai ba zaka sha shayin ba?" Ya tambaya kamar bai gama hargitsa mishi dukkan lissafin shi ba, ammam AbdulHafiz ne, ya riga ya gama maganar kenan, ba zai maimaita ba. Yabar komai a hannun Hamzan, zabin nashi ne. Kai kawai ya girgiza mishi da yake jin yana kara ciwo. Su dukan su aikin da sukeyi suka cigaba. Kafin AbdulHafiz din ya fara waya da Nabila, ya saka earpiece a duka kunnuwan shi, hirar tasu na saka Hamza jin kewar Hindu da ta danne shi, tun la'asar rabon daya ji motsinta. Aikin da yakeyi yai saving yana kashe laptop din ya mike, zuwa yai yadan watsa ruwa ya dauro alwalar magriba ya fito, kaya ya sake zuwa manya, wani farin yadi daya karbi jikin shi, bakar hula da takalmi ya saka. Ya dauki mukullin mota yana fita falon Wayar shi ya dauka da take kan tebirin da suka ajiye daga can gefe inda suke ayyukan su, dining ne ba zama suke suci abinci ba, ya zame musu kamar Office din gida. Harya kai kofa AbdulHafiz yace "Hamza..." Juyawa yayi "Allah yasa alkhairin ka ce" Dan murmushi Hamza yayi yana ficewa daga gidan,wasu lokuttan AbdulHafiz kanyi mishi kamar babban Yaya, duk da watanni biyar ne tsakanin su, shisa yake kasa zagin shi kamar yanda yake zagin su Fodio. Yanayin kusancin su daban ne, kuma su dukan su yana musu kamar Yaya fiye da yanda yake aboki a wajen su. A hanya ya tsaya nan masallacin da yake station round about, yayi sallar magriba, kafin ya karasa gidan su Hindu, maigadi na bude mishi kofa ya shiga da motar shi, bai fito daga motar ba ya kira wayarta, tana dagawa yace "Ina cikin gidan ku" Batace komai ba, shima bai jira amsarta ba, ya kashe wayar daga bangaren shi, yana ajiyeta a cikin motar. Wani irin sama-sama yake jin shi, ga kan shi da yake ciwo har lokacin, duk da wani bangare na zuciyarshi na cike da jin dadin zaiga Hindun, yau maganganun AbdulHafiz da yake ji sun dabai-baye shi sun kashe mishi jiki tsaf, a karo na farko tun daya hadu da Hindu da yazo wajenta batare da yanajin kamar inta fito bai riketa ba zai mutu. Bai fito daga motar ba, sai da yaga Hindu da ta ajiye musu kujeru bayan motar shi, da murmushi a fuskar shi ya zagayo yana jan kujerar ya zauna. Sai dai tana zama ya sauke idanuwan shi kan fuskarta, murmushin da yakeyi ya dishe "Hindu..." Ya kira ganin fuskarta da take a kumbure har cikin idanuwanta, ai kamar hakan take jira taji wasu hawaye da ta kasa tarbewa sun zubo mata, yana fitowa taji kamar ta rufe shi da duka, kallon da yake mata cike da damuwa shiya karya mata zuciya yasa hawayenta zuba "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Me ya faru? Menene?" Hamza ya fadi yana kai hannu ya riko na Hindu data fisge tana goge hawayen fuskarta "Dan Allah kiyi mun magana" Numfashi taja tana sake goge fuskarta, zuciyarta take ji tana ciwo kamar zata fado "Me yasa kabani Password din ka?" Ta tambaya tana tsare shi da idanuwanta da suke cike da wani yanayi da yaji bayaso "Saboda bani da abinda zan boye miki" Ya fadi da dukkan gaskiyar shi "Har hirar ku da Mansy?" Ta bukata tana jin kirjinta na gab da budewa, numfashi Hamza yaja, yana huro iska ta bakin shi, ya dauka wani abinne daban akayi mata, ko shi yayi mata bai sani ba. A hankali ya daga mata kai, tunda ta rigada tagani baiga dalilin da zai mata wani boye-boye ba. Cikin sanyin murya saboda kan shi da yake ciwo yace "Me kike so ince miki?" Dariya Hindu tayi da bata da alaka da nishadi "Kana da karfin halin yimun wannan tambayar Hamza? Bakasan abinda ya kamata ka ce mun ba? Akan abinda kukeyi da Mansy har kana ce mun baka da abinda zakace mun?" Idanuwan nan nashi ya kafa mata, irin wannan dalilin na daya daga cikin dalilan da zasu saka shi kinyin aure nan kusa, ba zai yiwu ana tsare shi da tambayoyi haka ba "Karkiyi mun ihu, karki fara cewa zakiyi mun fada. Dana baki password dina nace ki karanta mun chats? Na aikeki karanta hirar mu da Mansy? Da kika fara karantawa kikaga ba zaki iya jurewa ba me yasa kika ci gaba?" Bakinta a bude yake tunda ya fara magana, dariyar ta sakeyi duk da idanuwanta da suke cike taf da hawaye "Kana da karfin hali, wallahi kana da karfin hali Hamza" Daga mata gira yayi cike da masifa, kan shi ciwo yake kamar zai rabe biyu. Tana kuma kara mishi ciwon kai kan abinda ita taga zata iya karantawa, shima haka ya jure bin chats dinta da garadan duk da suke mata magana, harda Jalil, baiyi kuka ba duk yanda zuciyar shi tayi mishi ciwo, sai ita da take da hawaye a kusa zatayi amfani da su ta cuce shi, haka mata sukeyi daman ya sani, abu kadan sai su fara kuka, idan wani yagani zai baka rashin gaskiya kamar kayi musu wani babban abu. "Na karanta hirar ku da Jalil tun daga farko har karshe, saboda bani da hawaye shine zaki fini fada" Kai Hindu take girgiza mishi "Karka hada wannan da Mansy, ni banbi Jalil ba, bakama san ya muka kare da shi ba" Cikin idanuwa Hamza yake kallonta "Zunubina ne, me yasa zai dameki?" Mikewa tayi, ba zata iya ba, zuciyarta fadowa zatai idan taci gaba da sauraren Hamza, taci gaba da ganin yanda yake nuna zina a wajen shi ba wani babban abu bane ba. Hannunta ta kama yana janta ta koma ta zauna babu shiri, hannunta ta fisge "Karka sake tabani, abinda ya kawoka kenan daman. Wallahi ba zaka taba samu ba, saboda ni ba Mansy bace ba, kasani dai ka cutar dani....Allah kuma ba zai barka ba" Hindu ta karasa wasu irin hawaye masu zafi na zubo mata, zuciyarta ciwo take har cikin makoshin ta, ga wani tsoro marar misaltuwa daya lullubeta na ma'anar kalamanta, ba ta shirya ba, bata san ya zatayi idan suka rabu ba, amman ba zatayi ma kanta karya ba wannan karin, ba zata iya ba Hamza abinda yazo nema ba. "Ni zaki hada da Allah Hindatu?" Hamza ya tambaya yanajin tashi zuciyar na tafasa shima, duk abinda zaiyi a rayuwar shi bayaso yaji an hada shi da Allah, yana kokarin ganin zunuban shi tsakanin shi da Ubangiji ne, bai hada da hakkin mutane ba "Me ma kike so kice mun? Bari na zakiyi?" Ya karasa maganar muryar shi na wani irin sauka, kan shi naci gaba da sarawa, a karo na farko a tsayin lokaci a rayuwar shi da yaji tsoro ya dabai-baye shi da tunanin cewa zata bar shi. "Ya kake so inyi? Ba zan iya ba, wallahi ba zan iya baka abinda ka zo nema ba" Ta karasa maganar tana rufe fuskarta da hannuwanta saboda kukan da takeyi, baisan lokacin daya kama hannuwan yana rabasu da fuskarta ba, ya dumtse su cikin nata, kai yake girgiza mata "Baki isa ba, wallahi baki isa ki rabani dake ba, Hindu baki isa kisa in fara sonki ba kibarni, ni ban tsara soyayya a rayuwata ba koda aure zanyi, saboda bana so in wahala, ba zaki barni ba, kina jina" A hankali ta zame hannuwanta daga rikon da yayi mata, dan ya fara karya mata zuciya fiye da yanda take a karye. Mikewa tayi, ta goge fuskarta sosai tana tashi, dai-dai lokacin da aka kira sallar isha'i, muryarta a dishe tace "Kaga an kira sallah" Kai Hamza ya girgiza mata, shima yana mikewa "Dan Allah ka barni, zuciyata ciwo takeyi, in ba kasheni zakayi ba yau, kabarni haka" Numfashi ya sauke "Karki barni to, kice ba zamu rabu ba" Kai Hindu ta iya daga mishi, gida kawai take so ta shiga, ko zatayi kuka har sai zuciyarta ta rage mata ciwo "Okay.... Koma menene karki barni, ina son ki" Ya furta kalaman na sauka kunnuwan shi da tabbaci kan abinda yakeji a kanta. Kafin tayi wani abu taji ya riketa a kirjin shi, sosai wannan karin ta ture shi "Kagani ko? Abinda kake so kenan bani ba" Kai Hamza ya girgiza mata, ya riketa ne dan ya rage jin tsoron da yakeji, yau ko abinda take tunanin ma bayaji sam, tashin hankalin da yake ciki ya girmi wannan "Nasan abinda nake so, kuma duka biyun ne" Numfashi Hindu ta sauke, ta mika hannu taja kujerar daya tashi daga kai, ta dagota tana hadata da dayar. A wajen tabarsu tana wucewa ta shige gida, tsaye Hamza yayi a wajen, gabaki daya gwiwoyin shi sunyi sanyi. Dakyar ya iya zagayawa da nufin ya bude motar shi ya shiga, yaji an mishi sallama, juyowa yayi yana mika mishi hannu suka gaisa, ya gane hoton shi, Hindu tana yawan saka shi a status dinta, Zaid tace mishi, Yayanta ne, tace likita ne. Kare mishi kallo Zaid yakeyi, akwai inda ya taba ganin Hamzan, ya rasa ko ina ne, amman haka kawai yaji baiyi mishi ba. "Idan kana son ta da gaske, ka turo ayi magana kafin ka sake zuwa" Zaid ya fadi, ko bai tuna ina ya taba ganin Hamza ba, bayason irin su a kusa da kanwar shi, sam bayaso. Idan da wata niyya yazo Zaid nada tabbacin daga yau ba zai sake dawowa ba, hakan ma zaifi mishi, dan ko turowa yayi har unguwar su zaije da kan shi yayi bincike a kan shi, ba kullum yake yankewa mutane hukunci batare da yasan labarin su ba, amman kuma zuciyar shi kanyi gaskiya akan mutane da yawa, in har yaji kamar baka da hali me kyau sai hakan ya kasance gaskiya. Wucewa yayi kafin Hamzan yace wani abu, dan karma ya samu fuskar ganin wasa yake da shi. Motar shi Hamza ya shiga, yau dai kowa so yake ya raba shi da Hindu, harda ita da kanta, kuma zai nuna musu basu isa ba, kamar yanda yace ne, yana son ta, da a rabashi da ita gara yayi abinda bai shirya ba, duk sai su sama mishi lafiya su daina kokarin ganin sun rabasu. Hanyar da zata kai shi Tudun Wada ya nufa, gara yayi magana da Appa. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 2 Hamza na daya daga cikin mutanen da ba karamin sha zaiwa giya kafin ta bugar dashi, yasan ba ita bace ta saka shi bacci, duk da ya kwankwada daren jiya saboda yanda ranshi yake a bace, dan haka da wani irin ciwon kai ya tashi, kan na shi ya kara sarawa saboda aman da yayi na giyar. Shisa baya so yasha ta da wannan yawan, ran shi a bala'in bace yake jin shi har lokacin. Dan bayan ciwon kan da yake har wani dumi yaji ya dauka na bacin rai, dan karamin kitchen din da turawa sukafi yiwa lakabi da kitchenette ya shiga, dan wajen girkine da zaka iya dafa abin kari ko wani abu dai marar nauyi. Jikin shi sanye da gajeran wando, amman ya saka riga mai dogon hannu hadi da hula ya saki hular a bayan shi, ya riga yayi wani irin sabo da riguna masu dogon hannu, komin zafin da akeyi kuwa, sai yaji iska na shigar mishi hannuwa duk idan ya saka riga mai gajeran hannu, ko a gida baya zama da ita, da daddare ma ba kullum yake kwanciya da singlet ba, dan ma zai lullube jikin shi tunda da AC. Coffee ya hada ya zuba a kofin tangaran da yake rubuce da Arc Hamzy a jiki, da yake bayason zaki ko da can, ballantana da yasan illar da yake da ita a jikin dan adam idan yayi yawa, haka ya fito da Mug din a hannun shi. Kurba yayi yana hadiye shi dakyar saboda zafi "Oh shit..." Ya furta yana furzo iska ta bakin shi, babu shiri ya koma kitchenette din ya dauko cokali ya saka a ciki yana jujjuyawa cikin son yadan sha iska ko yayane, kan mudubin dakin baccin ya ajiye kofin yana duba agogon dakin yaga karfe takwas da kusan kwata, yana da dan sauran lokaci, dan karfe tara zai fita, kuma yayi wanka. Wajen drawer din gado ya karasa yana zama tukunna ya janyo, paracetamol ya dauko ya balli guda biyu yana daukar robar ruwa da take ajiye a gefe ya jefa maganin a bakin shi tukunna yabi da ruwa. Ya sake mikewa ya dauko Mug din ya kurba yaji zafin ya mishi dai-dai. Bai dauki wani lokaci ba ya shanye yana zuwa ya wanke kofin tukunna ya mayar da shi inda ya dauka. Gyara gadon yayi tsaf, dan a rayuwar shi bayason ganin waje a hargitse, bakuma ya son kazanta koya take. Ko wajen ajiye kayan shi ka bude a tsare yake sai abin ya burgeka, kowanne kalar kaya wajen su daban, boxers din shi da singlet kan su a tsari suke. Shisa ya tsani wani ya shigar mishi daki, idan akwai abinda yafi saurin bata mishi rai shine wani ya shigo mishi daki ya taba wani abin, dan koya akai kokarin mayar dashi yanda aka gani yana shigowa saiya gane. Saida ya gama tukunna ya taka wajen wardrobe din da take cike da bango daya na dakin saboda girmanta. Wani farin yadi ya dauko da babu aiki a jiki, sai maballan ne kawai da aka saka mishi blue, links ya dauko kalar maballan, sai agogo, hula da takalmi duka blue. Lokacin da ya gama shiryawa da wahala ko namiji dan uwan shi yai mishi kallo daya bai sake kallon shi ba, ya hadu kamar ba daga jinsin bil'adama ya fito ba. Saida ya feshe jikin shi da turarukan Oud dan yafi son su, tukunna ya dauki mukullin motar shi yana takawa ya fita daga dakin ya sauko daga bene zuwa kasa. Yana zuwa bakin kofa yaja kyauren yana gyara labulen sosai yanda zai datse, bai damu da yasa mukulli ba tunda yana da maigadi kuma yasan babu wanda zai bari ya shigo mishi gida, zai kara mishi kashedi idan zai fita. Yana karasawa wajen motar shi kirar Toyota corolla CE 2010 ya saka mukulli a jiki ya murza yana budewa, shiga ciki yayi ya kunna yana fitowa daga ita daga jerin motocin shi hudu in har da wadda yake ciki cikon ta biyar, tukunna yai kwana cikin tanqamemiyar harabar gidan na shi yana shirin fita da motar yaga shigowar wata, hakan yasa shi fasa fitar da tashi yayi zaune a ciki yana son ganin kowaye. Parking akayi daga gefe daya kara bata mishi rai saboda ba wajen da aka ware dan yin hakan bane. Yana kallon Huzaifa ya fito daga cikin 406 din shi da duk taji duniya, Muhsin na bude dayan bangaren ya fito shima. Ganin su biyun a tare yasa Hamza kashe motar shi ya bude ya fito shima. Ganin su na kara harzuqa shi "Lafiya?" Ya tambaya cikin yanayin da yasa Huzaifa kallon shi da mamaki bayyane a fuskar shi, Muhsin ne ya iya cewa "Kaya zamu kwashe" Tunda ya kula babu alamar mutunci a fuskar Hamzan "Zan duba in saka muku rana" Cewar Hamza din yana shirin juyawa "Bangane zaka duba kasa mana rana ba" Huzaifa ya fadi yanayin fuskar Hamzan na saka shi son dauke shi da mari, a duniya baya kaunar wulakanci ko ya yake, bama shida hakuri ne gabaki daya, shisa ba sosai yake shiga mutane ba, ballantana wani ya harzuka shi. Cikin idanuwa Hamza ya kalle shi yana amsa shi da "Hausa nai maka bawani yare ba, meye baka fahimta daga ciki ba..." Wata yar dariya Huzaifa yayi yana cewa Muhsin "Kayi magana da shi" Ya juya yana takawa wajen motarsu ya jingina bayan shi, dan idan ya tsaya bazai san lokacin da zai kaiwa Hamza naushi ba. "Mun zo da masu mota da mutanen da zasu kwashi kayan, suna waje suna jira" Muhsin yayi kokarin yima Hamza bayani dan su fahimci juna, su ba rashin mutunci bane ya kawosu, duk da abinda yaima kanwar tasu, tarbiyar da suka samu wadatacciya ce, kai Hamza yake girgizawa tunda Muhsin din ya fara magana "Fita zanyi, ba kuma zan barku ku kadai a cikin gidana ba gaskiya, gobe ma ina da abinda zanyi. Idan na saka rana zan fada ma Hindun sai ta sanar muku" Sosai Muhsin yake kallon shi, akwai dalilin da yasa tun ranar daya fara ganin shi tsaye da Hindatu yaji bai mishi ba, a lokacin ya nema bai samu ba, sai jiya daya kwana yana juyi, yana fada ma kan shi yanda bazai kara bata rai idan yaji wata mace tayi wa maza kudin goron zagi ba. Da matar shi rike a kirjin shi tana bacci, darajarta na karuwa a idanuwan shi, baiga riba a wulakanta mace ba, balle wadda ta kasance a karkashin kulawar ka. Tun jiyan ya rasa kalar zuciyar da take kirjin Hamza da har zai iya korar mace tsakiyar dare batare da tunanin halin da zata shiga ba, macen ma da tsohon ciki. "Kaga ba tashin hankali ya kawo mu ba, kaya kawai zamu kwashe mu tafi" Inda Muhsin din yasan yanda Hamza yake kokarin ganin ba suyi tashin hankali ba, daya wuce ya sami Huzaifa sun shiga motar su sun bar mishi gida. Tsayuwar da suke, lokacin shi da suke batawa da maganar kwashe kayan da take dawo da Hindu tunanin shi kara harzuqa shi sukeyi ba kadan ba "Idan baka da abu mai muhimmanci ni ina da shi" Ya fadi yana bude motar shi, kafin ya shiga ya juyo ya kalli Muhsin din "Wallahi kuka shigar mun gida karar ku zan kai wajen yan sanda, saboda ina da dukiya a cikin gidana.." Tukunna ya shiga motar shi, ya tayar yana fisgarta da akwai tsautsayi saiya takama Muhsin da mamaki yagama cikawa kafa. Jikin shi da wani irin sanyi ya karasa wajen Huzaifa yana fadin "Wallahi mutumin nan bashida mutunci, ko kadan bashida mutunci bansan ya akayi bamu kula da hakan ba kafin mu bashi Hindu, kaji abinda yake gayamun? Wai zai kira yan sanda idan muka shigar mishi gida" Jinjina kai Huzaifa yayi cike da bacin rai, yana kasa furta wata kalma "Muje kawai mu sallami mutanen nan, sai mu biya ta gida, kar muyi wani abu ko da sauran zama a tsakanin su" Sai lokacin Huzaifa yace "Da wa? Ai kasan Allah ko zata mutu ba zata dawo gidan wannan mutumin ba, daman shegiyar kafiyarta ce, da Baba daya goya mata baya" Dan murmushi Muhsin yayi yana bude motar ya shiga ya zauna. Huzaifa ya bude dayan bangaren mazaunin direba yaja suka fice daga gidan, masu manyan motocin har biyu suka sallama tare da karbar lambar wayar su da cewar zasu sake neman su azo a kwashe kayan. Tukunna suka kama hanyar gida, Huzaifa har lokacin zuciyar shi a makoshi yake jinta "Inda na mari yaron nan da zuciyata tadan yi sanyi" Dariya Muhsin yayi dan baka raba fuskar shi da fara'a ko da yaushe "Allah dai ya rufa asiri, idan ka biye halin mutane abinda yafi mari ma sai kayi musu. Ni yanzun Baba ma nake tunani wallahi, ran shi ya baci jiya tunda kaji yace a kwashe kayan a daren. Me zamu ce mishi?" Dan kallon shi Huzaifa yayi kafin ya mayar da hankalin shi kan tukin da yake "Me zamu ce mishi daya wuce mu fada mishi gaskiya? Yace ba zamu shigar mishi gida baya nan ba, idan kiran shi Baban zaiyi sai yayi" Numfashi kawai Muhsin yaja yana fitarwa batare da ya sake cewa komai ba. Duk da shine sama da Huzaifa din, bai ja maganar ba saboda bayason ya kara tunzura shi. Yafi so yaga anbi komai a hankali, duk yanda zasu kai da kin Hamza idan zaman su bai kare da Hindu ba yasan haka zasu hakura suna gani ta koma. Sam ba zai so su biye mishi ya kara zubar da mutuncin shi a idanuwan su ba, ko babu rabon komawa akwai ciki a jikin Hindu. Haka suka karasa gida babu wanda ya sake cewa dan uwan shi komai. * Baba da kanshi daya dawo sallar Asuba ya shiga bangaren Anty yana fada mata abinda ya faru. Da yake uwa daban ce tun a daren jiyan taji a jikinta, dan haka kawai bacci ya kaurace ma idanuwanta, sai tunanin Hindun daya cika mata zuciya. Kuma ta kasa tashi tayi sallah ko da raka'a biyu ce, jin Mama na tare da Hindun yasa tayi alkunya tana kasa shiga duk yanda zuciyarta take son ganin halin da take ciki. Da yake ita bafullatana ce, lokaci zuwa lokacin fillon na motsa mata. Tana zaune a daki, ta saka wannan ta kwance har karfe bakwai na safe. Kafin ta fito daga dakin tana shiga kitchen, kowa girkin shi yakeyi tun suna da kuruciyar su. Sai dai yaran duk abinda sukaji suna marmari da aka dafa a gidan shi suke ci, cikin ikon Allah da yake Baba tsaye yake akan gidan nashi, kishin dake tsakanin matan da ba'a iya kauce mishi baisa kan yaran ya rarrabu ba, duk da zaka gane yan daki daya daga yanayin shakuwar su, amman suna kamanta zaman lafiya dai-dai iyawar su, kuma suna kokarin ganin ko da sun sami sabani basu saka yaran a ciki ba. Asma'u da suke kira da Asma ta samu harta tashi tana soya dankalin turawa "Ina kwana Anty" Ta fadi tana daukar soyayyen dankalin guda biyu ta saka a bakinta "Lafiya kalau... Harkin tashi" Kai Asma ta jinjina wa Mama tana dorawa da "Ina da Test da safen nan" Ta sake saka hannu cikin dankalin ta dauki guda daya "To ko kibari in karasa kije ki shirya karki makara" Murmushin jin dadi Asma tayi dan inta tsaya karasa suyar dankalin zata iya makara, tunda karfe takwas da rabi malamin yace. Bata tsaya jan magana ba ta fice daga kitchen din tana wucewa dakinta. Tsaye Mama tayi a kitchen din komai baya mata dadi, kafin taji sallamar Hindun da ta sakata juyawa cikin hanzari tana fadin "Hindu..." Itama da ta samu tayi sallar Asuba, bacci ne ya dauketa sai yanzun nan ta tashi, wanka kawai tayi tana zira doguwar rigar da Mama ta ajiye mata kan gado, son ganin Anty taji tanayi ta kuma son halinta, sam ba zuwa zatayi inda take ba, shisa ita ta lallaba ta taho. Ganin Antyn da yanda ta kira sunanta suka hadu suna kara karya mata zuciya, batasan lokacin da wani irin kuka ya kwace mata ba tana karasawa ta fada jikin Anty da duk damuwar da take ciki bai hanata fadin "Karki kayar dani Hindu, kinga ga mai a wuta. Kiyi hakuri kinji ko" Ai kamar hakurin Antyn take jira wani sabon kuka ya sake kwace mata, duk yanda taso ta boye halin da aurenta yake ciki saida Hamza ya kure duk wani zabi da take da shi,a hankali Anty ta dagota daga jikinta tana fadin "Kinci abinci?" Kai Hindu ta girgiza, ko kadan ta manta da wani abinci, da gaske yunwa ma sai kana cikin kwanciyar hankali kake jinta. Sai yanzun da Anty tayi mata maganar abincin ne ma taji yaron cikinta ya juya mata da alamun yunwa, shisa dazun data mike taji jiri na shirin dibarta, bayan hannuwanta tayi amfani dasu wajen goge fuskarta "Kije ki zauna in zubo miki" Kai Hindu ta iya dagawa Anty, tana wucewa falon ta samu kujera ta zauna, dan inta zauna kasa wajen tashi wahala take sha saboda cikin da yake jikinta. Tana zama Asma na fitowa daga daki ta shirya tsaf cikin kayan da Hindu bata gani saboda Abaya da Asma ta dora a kansu, kanta sanye da bakar hula mai duwatse, tayi kyau cikin kwalliyarta mai sauki, da sauri cike da farin ciki ta karaso inda Hindun take tana fadin "Yaa Hindu" Kafin tadan dakuna fuska cike da tunanin da yazo mata na me Hindun takeyi a gida da sanyin safiya haka, tukunna ta kula da idanuwan ta da dukkan fuskarta da suke a kumbure da alamun kuka, walwalar fuskar Asma ce ta dishe, damuwa na maye gurbinta "Asma..." Hindu ta kira sunan kanwar tata cike da duk wani karfin gwiwa da zata iya tattarowa wajen ganin bata fashe da kuka ba. Gefenta Asma ta zauna tana jin gabaki daya komai yai mata tsaye, kafin tace wani abu Anty ta fito daga kitchen hannunta rike da faranti da dankali a ciki, dayan hannunta da ruwan shayin da ta hada "Ke ba makaranta zaki tafi ba kika sami waje kika zauna" Kallon Anty tayi, da bata furta suna da test ba, ita kam batajin zata tafi tabar Hindun cikin wannan damuwar da take gani shimfide akan fuskarta, turo labbanta tayi tana sa Hindu fadin "Ki tashi karki makara Asma... Ina nan ai har ki dawo" Idanuwanta Asma ta dauke daga kan Anty tana dawo dasu kan Hindu cike da alamun tambayar dake fassara 'Kinyi alkawari?'. Kai Hindu ta daga mata tana dorawa da "Da gaske" Tukunna Asma din ta mike, kitchen ta wuce tana dan dibar dankalin ta zuba a murfin kular da yake ciki dan ba zata iya tsayawa daukar wani kwano ba, tea ta hada tana shan shi a tsaye cikin sauri kafin Anty ta shigo taganta ta zageta tana cin abinci a tsaye. Tana gamawa ta mayar da kular ta rufe tana fitowa da gudu-gudu ta shiga dakinta tana dauko mayafin Abayar ta nada a saman kanta sai jakarta ta gefe, ta zira takalma tana fadin "Saina dawo" Fatan alkhairi Hindu da Anty sukayi mata, ko amsa basu samu ba saboda saurin da takeyi. Kofin shayin da Anty ta bata ta karba tana fara kurba, hadi da dibar dankalin tana ci, ko rabi batayi ba taji yaron cikinta ya harba tamkar abinda taci din harya isar mishi. Jin da tayi komai ya hargitse mata lokaci daya yasata ajiye kofin hannunta tana kiran sunan Allah kafin ta mike cikin hanzari tana nufar bandakin baki da yake cikin falon hadi da tsugunnawa kan gwiwoyinta tana fara kelaya amai tamkar zata amayar da hanjin cikinta, ko sannun da Anty take mata bayan ta shigo bandakin bata iya amsawa ba. Amai take babu kakkautawa har mamakin ta inda yake fitowa takeyi dan tana da tabbacin iya dan abinda taci yanzun nan ya gama fitowa. Baba ne ya shigo dan yaje bangaren Mama baiga Hindun ba, hankali a tashe ya tsaya daga kofar bandakin yana fadin "Subhanallah... Me ya sameta?" Dan rausayar mishi da kai Anty tayi, mai ciki ai ba'a rabata da laulayi kala-kala, mai dalili da akasin haka. Damuwa ce fal a ran Anty da take kokarin boyewa a fuskarta. Ita ta zubama Hindu ruwa tana kuskure bakinta ta kuma wanke fuskarta. Kafin ta dafa sink din tana mikewa dakyar "Ki dauko mata hijabi mu tafi asibiti... Harda ruwan jiya daya daketa" Baba ya fadi yana karasa maganar da wani yanayi a fuskar shi, a kasan ran shi yanajin yanda bazai taba yafewa Hamza wannan rashin arziqin ba, murya cike da rauni Hindu tace "Baba ba sai munje asibiti ba, tunda daman gobe in shaa Allah zan koma awo..." Kai Baba yake girgiza mata "Ki kalli yanda kike magana dakyar Hindatu, kice ba sai anje asibiti ba? Kina wasa da lafiyarki ko?" Dan murmushi Hindu tayi, a fuskar Baba take ganin shine namiji daya a rayuwarta da ba zai taba karya mata zuciya ba, namijin da bai taba karya alkawurran da bai ma daukar mata ba amman yake cikawa a duk rana. Tana kuma jin yanda shi kadai ne dalilin da zai sa ba zataiwa mazan yanzun jimlar marassa mutunci, marassa adalci, marassa tausayi ba. Wata irin kaunar Baban taji cike fal da zuciyarta da take ciwo "Baba Allah ba sai munje ba, da nayi bacci shikenan" Badon ran shi yaso ba, sai don bako yaushe yake iya matsama Hindun ba, ko da kuwa a yanayi ne irin wannan. "Allah ya kyauta, ya kawo sauki...ki kwanta ki huta kinji ko? In dai kika karayin amai asibiti zamu je" Murmushin karfin hali Hindu tayi tana dan dagama Baba kai, Anty kuwa kallon su takeyi, kaunar dake tsakanin su ba sabon abu bane a wajen ta, lokutta da dama idanuwa take binsu dashi. Baban da kan shi ya taka ya raka Hindu har dakin Asma tukunna ya fito yana kallon Anty da fadin "In ta sake yin aman ki kirani mu tafi asibiti...zan karya in kira su Muhsin dan nace su kwaso kayanta" Kallon shi Anty tayi, cikin taushin murya tana fadin "Alhaji anyi saurin kwaso kaya? Da an bari an kira shi anji me ya hadasu tukunna" Wani irin kallo Baba yakewa Anty "Yazo aji me? Ya korar mun yarinya tsakiyar dare, da tsohon ciki tukunna in kira shi? Yace mun me? Ni ince mishi me? Bafa gajiya nayi da kulawa da ita ba, ba kuma kasa ciyar da ita nayi kafin yazo ya tsugunna ya nemi aurenta in dauka in bashi ba, ya wulakanta mun ita haka kice mun in saurari me ya hada su" Ganin yanda ran Baban yake a bace yasa Anty fadin "Kayi hakuri" Dan tasan halin shi, idan ran shi ya baci babu abinda zai saurara, musamman kuma yanzun an taba yar gaban goshi Hindu. Ai tasan sai abinda Allah yayi, ita bataso a yanke hukunci ba'a duba duka bangare biyu ba, dan hakan ne adalci, dan kyautawa ko kadan Hamza bai kyauta ba, ko ita ranta yana kan sosuwa da abinda yayi din, amman zai iya yiwuwa tayi mishi wani abin ne, batajin namiji zaiyi irin wannan hukunci batare da kwakwwaran dalili ba. "Kawai dai ina jinjina yanda zaiyi irin wannan hukuncin batare da wani dalili bane, shisa nake so aji nashi bangaren" Antyn ta sake fadi ganin kamar Baba zai saurare ta, karamin tsaki yaja yana ficewa daga dakin kawai, dan idan ya tsaya fada zasuyi da sanyin safiyar nan. Baisan me yasa Antyn take magana kamar ba mace ba, da ya kamata tayi kishin abinda akaiwa yarta, baice kar a kyautata ma dan adam zato ba, bai kuma ce abinda take so ayi din ba mai kyau bane ba, asalima hakan shine adalci. Amman baiga dalilin da zaisa a kowanne yanayi sai anma jinsin shi na da namiji uzuri ba, ko wanne irin abu namiji zaiyi sai an so juya abin ya koma kamar ita macen ce da laifi. Na rana daya ya kamata a kalli mace cikin kuncin da namiji ya kunsa mata a karbi korafinta batare da kokarin gano me tayi da ya ba namijin dalilin yin abinda yayi. A ganin shi babu wani uzuri da zai karba akan abinda Hamza yayi, kowanne irine kuwa. Daya rufe idanuwan shi Hindu yake gani tsamo-tsamo cikin tsakiyar ruwa da tsakar dare, inda maigadi bai taimaka ta kira shi ba haka zata kwana cikin ruwa, a kofar gida. Ko da wani bai cutar da ita ba, sanyi kadai ya ishi yai mata illa mai girma, ga cikin da yake jikinta. Kirjin shi ma zafi yakeyi ba kadan ba, idan baiga an kwaso kayan Hindu daga gidan marar mutuncin nan ba hankalin shi bazai kwanta ba, indai harya isa yana kuma da cikakken iko akan yar shi ba zata taba komawa gidan Hamza ba. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 17 "Baba ni ina son shi" Hindu ta furta kalaman da ko a mafarki batayi tunanin zata iya gayawa Abba su ba, duk kuwa kusancin da yake tsakanin su, saboda kunya. Anty ma tun satin daya fita sai ta whataapp ta tura mata sakon cewa tayiwa Abba magana Hamza yace zai turo. Amman yau tura ce ta kai bango. Kiri-kiri take ganin yanda duka yan gidan suka juya mata baya kan maganar Hamza. Kuma Zaid ne, duk shi yaja da zancen binciken shi, batama ga matsalar shi akan maganar aurenta ba, yanzun ma da take tsugunne a gaban Baba idanuwanta cike suke taf da hawaye "Mahaifiyar shifa ba'a san asalinta ba" Zaid ya fadi, bayan wannan, har kauyane su Appa saida yasa aka bincika mishi, kuma ya samu tabbacin labarin su, kasancewar mahaifin Hamzan maraya. Amman ita mahaifiyar kanta batasan inda danginta suke ba tunda ta dawo Najeriya. A ganin Zaid ta fannin uwa da uba Hamza bashi da wasu dangi tsayayyu, sai yan uwan shi guda biyu. Duk da kowa a unguwar ya bada shaida me kyau akan mahaifin Hamza, haka shi kanshi Hamzan duk da ance yana da zafin rai, amman abin hannun shi bai rufe mishi ido ba tun bayan samun shi. Kawai akwai wani abu tattare da Hamzan ne da yaki kwantama Zaid shisa ya labe bayan rashin tsayayyun dangin da Hamza bashi dasu ya cewa Anty ayi mata magana ta hakura. Amman ta kafe, shisa ma yazo da maganar wajen Baba. "Kai da bakin ka kace kowa ya fada maka iyayen shi mutanen kirki ne" Hindu tayi maganar tana share hawaye "Ta shi kije abinki" Baba ya fadi, ta kuwa mike dan bataga wanda ya isa yasa ta rabu da Hamza akan wannan dalilin ba, balle yanda yake nuna mata kauna a cikin satin. Kusan kullum sai yazo makarantar su, dan ma batada wani lokacin da zasu fita, haka suke takawa cikin makaranta suna hira, tana bala'in jin dadin yanda ake binsu da kallo cike da sha'awa. Tana kuma jin dadin yanda ko abu ya sai musu shi yake rikewa, kuma har kofar aji yake rakata, su gaisa da wasu cikin Malaman da suka san shi, dan ya farfada musu ita ce zai aura. Da yawa a ciki kuma sun nuna jin dadin su da maganar. Shine Zaid zaiyi mata kafar ungulu a cikin lamarinta. Ita zata zauna da Hamza, idan rashin tsayayyun dangin shi bai dameta ba, bataga dalilin da zaisa ya dami kowa ba. "Yana da asali me kyau Zaid, tana kuma son shi. Babu wani dalili mai kwari na hana mishi aurenta..." Baba ya fadi, numfashi Zaid ya sauke "Wallahi Baba akwai wani abu a tattare dashi da baiyi mun ba, na rasa menene, amman har raina bana son shi da Hindu, in dai za'a bi shawarata a hakura. Allah ya kawo mata wanda yafi shi" Murmushi Baba yayi, yana da tabbaci duk yanda Zaid yake kaunar Hindu bai kai shi ba "Babu wani abu a tattare dashi banda kaunar kanwar ka da kakeyi, kuma wannan shine soyayyar da zaka nuna mata, kasan tunda macece dole irin ranar nan zata zo daman....da zaka mikama wani amanarta" Kai Zaid ya jinjina, Allah ne shaidar shi, yayi duk kokarin da zai iya. A wannan matakin yanajin addu'a ce kawai take rage mishi "Allah yasa hakan ne mafi alkhairi" Ya furta "Amin. Yawwa, ko kaifa" Mikewa kawai Zaid yayi ya fice daga dakin Baban yana nufar nasu Hindu, kwankwasawa yayi hadi da sallama, sai da yaji ta amsa mishi tukunna ya tura dakin ya shiga. Tsaye yayi a bakin kofa yana kallonta, yanayin fuskarta ya tabbatar mishi da cewar kuka tayi "Nasan kina jin haushina, kina ganin kamar na shiga abinda na hurumina ba, ba ko yaushe nake jin abu akan mutum bai zamana gaskiya ba. Ina miki fatan alkhairi a ko da yaushe, Allah ne shaida bayan Anty da Baba, kece ta farko a cikin jerin sunayen da suke fita bakina duk sujjadar da zanyi..." Haka kawai tunda ya fara magana take jin hawaye na zubar mata, da batama yi kokarin goge su ba, tunda taji suna tukundedeniya da juna wajen fitowa tasan bata isa ta tsayar da su ba "Yanzun ma bazan daina ba, Allah yasa shine alkhairin ki. Nasan kuna tsorona, kuna ganin kamar ba zaku iya tunkarata da kowacce magana ba, Hindu wayata kawai zaki kira idan kina bukatata, kina jina? Kar halina ya taba nisantaki da neman taimakona idan kina bukatar hakan" Bai jira amsarta ba ya fice daga dakin, saboda bayason kukan da takeyi. Gabaki daya sai taji maganganun shi sun karya mata zuciya, tana so ya yarda da zabinta, tana so ya yarda tayi hankalin da zata san abinda ya kamace ta da akasin hakan. Ta jima tana kuka kafin taje ta wanko fuskarta. Tana dawowa taga wayarta tayi haske, dauka tayi ta duba, taga Baba ne yai mata text "Ranar juma'a ko asabar, sai su zabi daya. Ki sanar dani" Murmushi tayi, zuciyarta na samun natsuwa, itama text din ta tura ma Hamza "Baba yace ko juma'a ko asabar" Dan ya matsa mata da maganar har fada sukayi da tace mishi Baba yace a dakata tukunna "Ki fada musu, Hindu ki fada musu bazan iya rabuwa dake ba gara ma su bani dama in turo" Shine abinda ya fada mata, yaki kwantar da hankalin shi duk yanda take kokarin ganin ta kwantar mishi da shi "Yau baccin da zanyi daban ne" Ya dawo mata da shi yana dorawa da "Zan kira ki" Suna Kano tun ranar alhamis, yau litinin, kwanan su hudu, sosai tayi kewar shi, duk video calls din da sukeyi, duk kuma aikin da yakeyi sai ya mata ko da text ne. Haka ta wuni a daki, daman karatun jarabawa takeyi, Hamza yace karta bashi kunya, mutane biyu kenan yanzun a rayuwarta da bataso suga gazawarta ta fannin karatu, shi da Baba. Basu kara waya da shi ko magana ba har dare, tunda ta fita taga irin kallon da Anty take binta da shi ta rufama kanta asiri tayi zamanta a daki. Abincin dare ma Asma ce ta zubo musu, Hindu na ganin ita Anty tabi maganar Zaid batare da ko Hamza tagani ba, balle ta bashi dama ya nuna mata yanda suke kaunar junan su, kuma ba haka bane ba, kamar yanda Zaid yakeji Hamza yaki kwanta mishi haka itama Antyn, sai dai tana addu'a sosai akan maganar. Gajiya tayi ta yanke hukuncin lekawa whatsapp dinta taga ya ake ciki, ko group din ajine ma ta shiga, ba za'a rasa abinda zai sakata dariya ba, dan shaftar su bata karewa sam. Haka suke fama kullum, status ta shiga, ta ga Hamza ya saka minti daya daya wuce, ba sosai yake saka status ba, yana iya sati daya bai saka ba, idan yasa ma bazai wuce zane ba, ko hoton su shi da su Fodio. Budewa tayi tana cin karo da hoton AbdulHafiz da Nabila, tana sanye da alkyabba, shikuma da manyan kaya, kanshi nade da rawani, sunyi mata kyau na gaske, har ranta tana son ganin fuskar Nabila gabaki daya. Yanzun ma idanuwanta kawai take iya gani "Wedding bells" Hamza ya rubuta, yana saka Hindu tambayar "Bikin shi ya matso ne?" Kafin tayi gaba tana sake ganin wani hoton "Saraki na Fulani. Allah ya kaimu lokacin" Sai take ji kamar ta janyo juma'a ko asabar, tasan ranar da zata fara duba kasancewar irin hakan a tata rayuwar, sauran hotunan ta gama gani da sukai matukar yi mata kyau, kafin taga Hamza ya amsata "Eh saura kwana talatin, sun sa ina jin kamar ace namu ne" Murmushi Hindu tayi, kafin ta amsa shi ya sake fadin "Nace ma AbdulHafiz sai munfi su yin kyau, yana mun musu" Sosai ta murmusa yanzun, ya sosa mata inda yake mata kaikayi, tunda suka fara maganar aure tagane Hamza na da burin biki dai-dai da nata. "Ka kyale shi, zamu bashi mamaki in shaa Allah" Ta amsa "Allah yasa alkhairi, kace ina mishi fatan alkhairi" Ta fara rubutu, kiran shi ya shigo, ta daga ta kara a kunnenta "Ga AbdulHafiz din ki fada mishi da kan ki" Hamza ya fadi, kafin ta numfasa taji sallamar shi data amsa a kunyace "Ina wuni... Ya aiki?" Ta fadi muryarta can kasa "Alhamdulillah. Ya makaranta?" Amsa shi tayi da "Mungode Allah. Allah yasa alkhairi ya kaimu lokacin lafiya" Bata taba tunanin murya zatai mata kwarjini haka ba sai yanzun da taji ta AbdulHafiz, kuma a cikinta zaka fahimci natsuwar da take tattare da shi "Amin thumma amin. Nagode. Allah ya kaimu naku. Ga Hamzan" Tana jin muryar Hamza tace "Ban shirya ba kawai ka mika mishi wayar" Dariya yayi "Wai me yasa AbdulHafiz yakewa mutane kwarjini haka?" Wannan karin ita tayi dariyar "Yaushe zaka dawo?" Zata iya rantsewa girar shi ya daga mata kafin ya amsa "Bawani nan, sai yau? Ba kinayi kamar ni kadai nake kewarki ba" Runtsa idanuwanta tayi tana sake budesu, ta tsokalo ma kanta rikici "Yi hakuri, ina kewarka Allah. Yaushe zaka dawo?" Saukar da murya yayi "Ban sani ba fa, kinga bikin AbdulHafiz ba'a saka da yawa ba, idan mun dawo zamu fara hidimar tafiya Gombe ne, gara mu rage aiki sosai sosai. Gobe dai zanyi magana da Appa, sanda zan dawo in shaa Allah muna kirga kwanakin bikin mu" Murmushi tayi "Allah ya kaimu, yanzun zan kara wasu satika ban ganka ba?" Tayi maganar, kewar shi na danneta, kamar tayi fuka-fuki taje Kano tagan shi ta dawo "Zaki ganni harki gaji idan na dawo, In shaa Allah. Idan bakiyi bacci ba zamu karayin magana, yanzun zamu fita dasu AbdulHafiz" Kai ta jinjina mishi tana dan sauke wayar daga kunnenta taga tara da rabi "A dawo lafiya, ka kula da kan ka, kace Fodio ya kulamun da kai" Tanajin dariyar shi ta cikin wayar kafin ya kashe, yanzun harta saba da yanayin yanda Hamza ya kare wayoyin shi, baya jiran sallama, daya gama fadar abinda zai fada yake kashewa. Sauke wayar tayi da murmushi a fuskarta, Instagram tahau dan tasan yau zata ga soyayya, tana hawa shafin AbdulHafiz din ta fara zuwa, ta kuwa ci karo da hoton daya dora, na Nabila din, an saka shi a baki da fari, da alkyabba a jikinta, da alamu a zaune take, ta daga hannunta ta kare rabin fuskarta da shi "Allah ya bani aron rayuwa mai tsayi a tare da ke Fulani, ban tana tunanin kwanaki talatin zasuyi mun yawa har haka ba" Zuciyarta Hindu taji ta cika fam, kamar ta sace AbdulHafiz din haka take ji, wani irin burgeta kalar soyayyarsu takeyi, amman ko da wasa har yanzun Hamza bai taba saka hotonta ba, kwanaki ya saka na Mansy a avi din shi, tabi ta cire, ta jira yayi mata magana yanda zasuyi tashin hankali, sai baice mata komai ba. Ranta yayi matukar baci, har yanzun idan ta tuna sai taji ran nata ya kara baci. Musamman idan tazo taga AbdulHafiz din yanda duke gurzar soyayyar su shida Nabila, ta tabbata ita take kara musu yawan mabiya a Instagram din. Fita tayi tana komawa shafin Nabila, hotuna biyu ne ma ta saka, wani jiya, wani kuma yau. Na jiyan ta fara dubawa, AbdulHafiz ne zaune a cikin mota, da murmushin nan har dimple din shi ya fito sosai "Bacci ya kaurace ma idanuwa na, ina jiran wayewar garin da zata kusanta ni da zama taka" Bude comment section din tayi, tana lalubo na AbdulHafiz da tasan dole ne sai yayi magana. "Soyayyar ki alkarya jikar Shehu" Tashi zaune Hindu tayi, tana tunanin yanda za'ayi su fara wannan soyayyar da Hamza. Hoto na biyu ta shiga, ita da AbdulHafiz dinne,a wani falo, tana zaune akan kujera ya tsaya daga bayanya ya daga yatsun shi guda biyu yana dariya "Saraki" Kawai ta rubuta sai hoton zuciya. Shima kuma da hoton zuciyar ya bata amsa, ko da bata saka komai ba, yanayin hoton zai fada maka kalaman da basu rubuta ba. Sai take jin kewar Hamza ta danneta fiye da kullum. Twitter din shi taje tana kai daman, taga Mansy tayi tagging din shi a wani abu da yaren fulatanci, tsaki taja, ta duba DM din shi tana ganin sakon Mansy din "Na kira ka baka dauka ba. Ina kewar ka sosai" Wannan karin tsakin da Hindu taja sai da Asma da take kwance, kunnuwanta manne da earpiece ta juyo tana cire guda daya ta kalli Hindun "Ba dake nake ba" Hindu ta fadi, Asma ta mayar da earpiece dinta, dan mp ce ma, ta saka karatun Qur'ani tana bi dan yafi mata sauri wajen rikewa, kafin lokacin da zasu bayar da hadda yazo sai taga har taci karfin karatun "Wawiya kawai, mata sai kace mayya" Hindu take fadi kasa-kasa kafin ta goge sakon. Yanzun haka takeyi mata, in dai zata ga sakonta sai ta goge, idan tayi unfollowing da blocking da Hamza yahau yake sake following ya budeta, sai ta kyale shi, sakone in ba ya rigata hawa ba sai dai suyi waya. Gabaki daya Mansy ta gama bata mata rai, tana cikin farin cikinta, da ta sani ta tsaya ma taci gaba da kallon soyayyar su AbdulHafiz da yafi mata, addu'a tayi tana juya kwanciya, taja ma Hamza, ba zata jira shi ya dawo ba. Baccinta tayi cike da mafarkin bikin su da Hamzan. * Basu dawo Kaduna ba sai satin bikin AbdulHafiz, washegari zasu wuce Gombe, shisa suna isowa ya fara sauka gida dan yaga Anna, ruwa kawai ya watsa, yaci abinci ya bar gidan, sallar Magriba ma a hanya ya tsaya yayi. Hindu kawai yake son gani har wani iri yake ji saboda kewarta. Ranar da yayi wa Anna maganarta, tambayar farko da tayi mishi shine "Yar gidan wacece ita din?" Dan bataso ya dauko yarinyar da zata saka mishi ido a abinda yake da shi, yarinyar da kudin shi zai zame mata abin alfahari, tafi son yarinyar duk da zai dauko mata a matsayin suruku, kudi ya zama dalili aqalla na biyu na auren shi, hakan zai rage mata tsoron za'a shiga tsakaninta da danta. Duk bayanin da Hamza yayi mata kasa samun natsuwa tayi, har sai da Appa ya tabbatar mata da cewa yarinyar yar mutunci ce, kuma suna da tasu wadatar dai-dai misali. Auta ce ma ta tsare shi da tambayoyi sai da ya zageta Yana son su, Allah ne shaida zaiyi komai saboda kannen shi, sune dalilin farko na sakashi jajircewa wajen ganin ya samu kudi, saboda bayaso su sha kalar wahalar dashi ya sha, yana so komai yazo musu da sauki, amman ba zai dauki su saka mishi ido akan abinda na huruminsu bane, ko hotonta da Auta tace ya nuna mata haka yace mata "Me zakiyi da shi? Saurin me kikeyi?" Dan murmushi Autar tayi "Kawai zan ganta ne, ko ta dace da kai" Girar shi ya daga mata duka biyun yana daure fuska sosai "Kina so ki bani kunya ne Auta? Kina so ki zama irin kannen mijin da suke kushe zabin Yayyen su ko? Ni ban san abinda ya dace dani ba sai kin tayani? Bana so, kina jina? Zamuyi fada dake sosai idan kika fara wannan halin" Ko Anna da ta dinga mishi tambayoyi akan Hindu dole ce ta saka shi amsawa, Anna ce, babu yanda zaiyi da ita. Amman ya tsani yanda ake magana akan dangin miji, bayason yanda suke yankewa yaran mutane hukunci batare da sun basu damar nuna asalin halayen su ba, sai kaji daga ganin hoto ana fadin "Ga idon ta na a tsaye, da ganin wannan yarinyar fitsararriya ce" Sai anje lahira an saka su a layi su farayi kamar masu ciwon asma, babu wata kwakkwarar shaida sai suyita yanke ma yaran mutane hukunci, ba tun yanzun ya saka a ran shi soyayyar da yake ma su Auta ba zata sa ya basu fuskar da zasu raina mishi yarinyar duk da zai kawo a matsayin mata ba, koya take kuwa, idan harya ce itace zabin shi dole su girmama hakan. Da Appa ya nemi zabin shi akan ko wata nawa ya kamata a saka, haka yace a tambayi Anna daman, ita kuma tace ko wata uku ko biyu, dan ta kaqu taga Hamzan ya nutsuwa waje daya. Wata ukkun kuwa akasa ana dai-daita shi dana Khadee, sosai Hamza ya natsu akan karasa gidan shi, da suka tafi Kano ma Abdallah yabari kan komai tunda batare dashi akaje ba, kuma ginin yana tafiya kamar yanda ya tsara abin shi, tare kuma da kudaden da suke ajiye a bankin shi. Tunda aka saka ranar kullum cikin maganar yanda bikin zai kasance sukeyi shi da Hindu, dan biki yake so ayi na kece raini, tunda harya yanke hukuncin yin aure, kowa zai shaida yayi aure. Wani numfashi ya sauke da yayi parking din motar shi a cikin gidansu Hindun yana kiran wayarta ya fada mata ya iso. Kafin ta karaso ya fito daga cikin motar, tana ajiye kujerun da ta dauko musu taji ya rike hannunta, kafin tayi wani yunkuri ya riketa a jikin shi yana sauke numfashi "Nayi kewarki..." Kwacewa tayi jikinta na bari, sai ware mishi idanuwa takeyi har yaja kujera ya zauna, sai da ya sake kama hannunta yana zaunar da ita. Gani takeyi kamar wani yagan su, ga wa'azin da Khadee ta turo mata shekaranjiya kan yan mata da samarin da suke wannan 'yan rungume rungumen zamanin kafin aure. Sai taji kamar dan ita da Hamza akayi wa'azin, ko da hannunta ne sai ya rike duk yanda zata nuna mishi bataso, tun da aka sa ranar kuma tayima kanta alkawari daman ba zai sake tabata ba, balle da taji yanda albarkar auren duk take zirarewa tun kafin ayi shi, ga tarin rashin yardar da yake biyo bayan auren. Banda zunubin da in ba tuba sukayi ba, sahihin tuba irin wanda ta dingayi kafin ya dawo yanzun nan cikin wasu dakika ya kwance mata hannun agogo yana dawowa da shi baya, tayi niyyar har sai ta zama mallakin shi inda duk wani riko da zaiyi mata zai zamana cike da lada "Bansan sau nawa kake so ince maka ka daina tabani kafin kaji ba, kana ta zubar mana da albarkar auren" Numfashi Hamza ya sauke, da tasan yanda yake kokawa da kanshi a duk rana akanta da bata ce mishi haka ba, da tasan irin matan da yabi a Kano dan in yazo karya riketa da bataga gajen hakurin shi ba, itace mace ta farko da yake kasa controlling kan shi a kanta "Bana so inyi fada dake nikam, nayi kewarki da yawa" Ya fadi yana gyara zaman shi hadi da zuba mata idanuwan shi, hakan yasa ta danyin murmushi, itama batason yin fadan da shi "Nima nayi kewarka ai" Dan tabe mata baki yayi, tana ganin yanda yanayin ya kara mishi kyau "Bawani, saura kwana 72 a daura mana aure" Dariya Hindu tayi "Kai ko?" Ta fadi, yana dakuna mata fuska "Ke baki damu ba shisa bakya lissafawa, nikam dana damu kinga ina kirgawa ai" Ya karasa maganar yana saka hannu a aljihun shi ya cire zoben daya siya. Azurfa yaso siya, Fodio yace ya sai mata gold zaifi duk wani tarkacen tsaraba da zaiyi mata, yaga mata naso, dan kanwar Fodio din suka kira suka shiga kasuwa tare. Dubu dari da goma wanda ya siya, badan bashi da halin siyan wanda yafi shi ba, kawai sauran sun mishi girmane sosai, wannan din dai yafi mishi kyau sosai, in an tashi hada lefe ya saka mata wani a ciki, Anna ma tace mishi za'a saka. Hannunta ya kamo, kafin tayi magana taga ya kama yatsanta na biyun yana zira mata zobe, kasa mishi magana tayi, ta ware idanuwanta ganin yanda zoben yake daukar ido a cikin hasken lantarkin dayake gauraye da gidan. "Bansan me zan siyo miki ba" Ya furta yana dago hannunta ya kalli zoben a jikin yatsanta "Karki cire, nasan karami ne, zan sai miki wanda ya fishi girma" Kallon shi tayi, wata irin soyayyar shi na cika mata zuciya fam, kafin a hankali ta zame hannunta daga cikin nashi, tana dago yatsunta, gyara ma zoben zama tayi, tana dan kara matse shi dan mai adjusting ne, ya zauna mata daras kamar dan hannunta akayi "Ban san me zance ba" Ta furta, dan godiya tayi kadan "Kice kina sona" Ya furta yana sake rike hannunta "Ina son ka" Ta fadi, tana saka shi dan dumtsa hannunta da yake rike da shi "Bai fito daga zuciyarki ba" Murmushi tayi "Ni na fada maka haka?" Kai ya jinjina "Ni ne naji a muryar ki... Ki sake fadamun, ya fito daga zuciyar ki kamar yanda nake fada mishi" Numfashi Hindu ta sauke "Ina son ka" Murmushi yayi yana sumbatar hannunta hadi da mikewa, ya tabbatar wayar shi daya bari su Fodio sun mishi kira yafi goma, tunda akwai abubuwan da zasuyi kafin goben su wuce Gombe "Ina zaka je?" Ta bukata tana shagwabe mishi fuska "Kin gani ko? In rike ki kice nayi laifi, bayan ke kike karamun son ki" Hamza ya fadi yana kallonta, murmushin da tayi na saka shi sauke numfashi "Su Fodio na jirana, zamuyi abubuwa da yawa. Zan kiraki, dan Allah kiyi hakuri, dana dawo zaki samu lokaci na" Kai kawai Hindu ta iya daga mishi, ya mika mata hannun shi, duk yanda zuciyarta take mata ihu, sai da ta mika mishi nata hannunta ya taimaka mata ta mike "Ki kulamun da kanki. Ina son ki da yawa, kin san hakan ko?" Kai ta daga mishi, hannunta ya sumbata kafin ya saki yana zagayawa ya shige motar shi, kujerun ta hade waje daya tana jansu gefe, kafin ta wuce gida. Sai da safe zata nuna ma Anty zoben, dan tasan yanzun tana wajen Baba, zatayi fada tace ita duk irin wannan gara yabari saiya aureta, amman abune da ko an sami matsala za'a iya mayar mishi da abin shi tunda ba siyarwa za'ayi ba, tasan Anty zata bar mata abinta, wayama da Hamzan ya sake mata, Anty ta fara fada, Zaid da kanshi yace ta kyale mata wayar, idan biyane ma Allah ya rufa musu asiri za'a iya biyan shi. Haka tayi zaune tana kallon hannunta, sai da ta hau whatsapp dan ta fada mishi yanda taji dadin kyautar, tana lalubo lambar shi, zuciyarta tai tsalle, ware idanuwa tayi tana bude profile din shi. Ba gizo idanuwanta sukayi mata ba, hotonta ne a dp din Hamza, a karo na farko daya saka hotonta, da sauri ta wuce Twitter din shi tana ganin ya saka hotonta a header din shi, bai dai saka a avi ba. Kwanciya tayi kafin shauqi yasa ta narke, ita kadai take murmushi, ta kasa daina kallon kanta a header din shi na twitter, ta tabbata Mansy zatayi kwana bakin ciki yau "Tsohuwar mai tallar goro yau za'a kwana ana juyi" Ta furta a ranta, tanajin kamar taga Mansy din ta fada mata yanda Hamza yayi mata nisa har abada, yanda Hamza nata ne ita kadai, ba kuma zata rabashi da kowace mace ba, sai dai su kalla daga nesa subar mata abinta. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 12 Bashi ya sami kan shi ba sai wajen karfe goma na daren ranar, wata irin gajiya yakeji har cikin kasusuwan jikin shi. Ko da Fodio yayi mishi tayin zuwa club, kai kawai ya iya girgiza mishi. Yanzun yana shigowa gida, ruwa ya watsa ya sake kaya yana fitowa falon gidan jin cikin shi da ya tattare ya kulle gefe daya saboda yunwar da yakeji. Wata zuciyar na mishi Allah ya kara da bai wuce gidansu ba, da yaci abincin Anna. Tunanin hakan kawai ya kara mishi yunwa. AbdulHafiz kadai ya samu a falon yana zaune kan kujera ya jingina kan shi, idanuwan shi a lumshe da earpiece a kunnuwan shi. Dan tabashi Hamza yayi dan yasan ko yayi magana ba jin shi zaiyi ba, kunne daya na earpiece din AbdulHafiz ya cire yana kallon Hamza da fadin "Meye ne?" Saboda yanda ya takura shi, karatun Qur'ani yake ji cikin muryar Sheikh Abdullahi Abba, da Nabila ce ta koya mishi son qira'ar mutumin, lokutta da dama idan ya zauna shi kadai bayaso tunanin duniya ya dame shi yakan saurara, nutsuwar da take saukar mishi daban take, sam bayason ayi mishi magana a lokaci irin wannan "Me kaci?" Hamza ya tambaya, numfashi AbdulHafiz ya sauke, shisa yayo musu take away, wanda zaici yaci, wanda ba zaici ba ya saka a fridge, idan yunwa ta koro wani zai dunduma a microwave din da shi ya siya. Lokutta da yawa yana mamakin yanda zasuyi inda baya nan. Yasan yanzun haka kowa zai dawo da yunwa tunda ya rigasu barin wajen aiki, da tunanin shi din ya nemar musu abinda zasuci "Ka duba Kitchen" Ya fadi yana shirin mayar da earpiece din shi "Me ka siyo? Meye?" Harara ya watsa ma Hamza "Karka dameni, kaje ka duba, idan bakaci ka ajiye. Dan Allah ka kyaleni" Murmushi Hamza yayi, yasan magana ce AbdulHafiz din bayason yi, yana sane shisa yake son saka shi yinta dole "Uban me kake ji?" Hamza ya tambaya yana kai hannu ya cire earpiece din da yake hade da wayar AbdulHafiz din, sai dai zarewar da yayi ya saka karatun shiga Pause, numfashi AbdulHafiz ya sake saukewa, ya danna play, karatun na gauraye shirun da dakin yayi, kafin ya kalli Hamza, kallon da yake fassara 'Sai kuma me?'. 'Yar dariya Hamzan yayi yana girgiza mishi kai "Ustaz AbdulHafiz, yau kuma Ash-Shura ake ji kenan. Allah ya bada lada" Earpiece din AbdulHafiz ya mayar, yakan yi mamakin Hamza, babu inda zaka ja a Qur'ani bai cigaba ba, babu kuma inda yake mishi wuyar fahimta, yanda zai zauna yana ja maka ayoyi yana fassarawa, zakace bashi bane idan kuka hadu a wani club din da mace rungume a jikin shi, shisa duk a cikinsu yafi jin haushin lalacewar Hamza, gashi da sanin da zai amfani al'umma ba kan shi kadai ba, sam yabari shaidan yayi galaba a kan shi. Hamza kuwa kitchen ya wuce yana daukar take-away guda daya cikin wanda suke jere a kitchen din, ya bude fridge ya dauko coke ta gwangwani, ya dawo falon ya zauna kasa kan kafet yana budewa, soyayyen danlalin turawa ne, plantain, kwai sai naman kaza. Sai da ya fara ci tukunna yai tunanin cire wayar shi daga flight mode din daya sakata dan kar wani ya dame shi da kira yana aiki. Duk yinin ranar tun da suka rabu da Hindu ta kara samun waje ta manne a cikin kan shi, zai rantse da Allah har yanzun yanajin yatsun hannunta a cikin nashi. Sai dai a cikin idanuwanta ya karanci bakuntarta a kalar tashi rayuwar, ta waye ta yanayin hirarta da maganganunta, amman ba kalar wayewar shi ba, idanuwanta ba'a bude suke ba, zai kuma ji dadi ya zama na farko daya bude mata su. 'Ya gajiyar ki, kin ga ban kira ba ko? Sai yanzun na shigo gida ma, abincin zanci, nagaji har cikin kasusuwan jikina Allah' Ya tura mata ta text, yana shiga tana biyo shi da amsa 'Gajiya tana wajen ka ai, sannu. Sai ka kwanta ka huta' Kai ya jinjina yana kurbar coke din shi 'Sai naji muryarki tukunna' Ganin ta dauki mintina bata dawo mishi da amsa ba, ya tabbatar da batasan yanda zata amsa maganar da yayi ba 'Ke me kike yanzun?' Ya bukata, ga mamakin shi ta whatsapp ta mayar mishi da amsa 'Na dan yi karatu, ina da test. Ina zaune kawai' Amsa ya fara rubuta mata, kafin tunanin kudinta ne zai iya karewa shisa tayi mishi magana ta whatsapp maimakon ta amsa mishi ta text ya fado mishi, sauka yayi daga whatsapp din, AbdulHafiz kance 'Sai kayita chatting da yarinya, kasa ta turo maka hotuna ko video, ko kai ka tura mata. Na rana daya ba zakayi tunanin data dinta da kake kararwa ka tura mata da kati ba. Saboda rashin sanin ya kamata' Duk shi ya koya musu wannan dabi'ar, Hamza ma ya rigada ya saba, ko ba budurwa ba, in yana tunanin ba wasu kudin kirki gareka ba, zai tura maka kati yace kayi sub da shi. Shisa yaran da kanyi aiki a karkashin shi suke yabawa da yanda bashi da mugunta, hannun shi kuma yake a bude. Yanzun ma bankin shi ya shiga yana tura ma Hindu katin dubu biyar. Kafin ya fita ma yaga sakonta ya shigo ta saman wayar. Budewa yayi yana ganin emoji din mamaki da ta turo mishi 'Kai ka turomun da kati ko?' Kafin ya amsa ta dora da 'Har dubu biyar, katin dubu biyar. Yayi yawa' Murmushi yayi, dan shikam bai dauki katin dubu biyar wani abu ba 'Karkiyi 'dan karatu'. Kiyi da yawa, ina son inga test score din idan kun gama' Ya tura maimakon amsa abinda tace, da gaske yake kuma har ran shi, yana son gani, batayi mishi kama da marar kokari ba, tunda take Architecture, amman zaisa ta kara dagewa in har hakan zai yiwu. 'Kar ka canza maganar nan' Wannan karin shiya tura mata emoji din harara 'Kar kiyi kamar baki gane bana son maganar ba, zan sauka idan kika sake mun' Bayason godiya, shine lokaci daya da yakan tabbatar da yana da kunya. Musamman kan karamin abu kamar katin dubu biyar. 'Yi hakuri. Nagode sosai sosai' Haka kawai yaji ba zai iya hakuri ba, muryarta yake son ji har tsikar jikin shi tashi takeyi. Sauka yayi daga whatsapp din yana kiranta, bugun farko ta dauka, muryarta da ta daki kunnen shi na kara mishi yanayin da yake ji "Da gaske jikina ciwo yake" Ya sake fadi yana gyara zaman shi, yar dariya taji "Na cika lalaci ko?" Ya tambaya, yanaji a jikin shi kai ta girgiza mishi "Ka gama cin abincin sai ka kwanta" Dankalin ya diba yana sakawa a bakin shi ya tauna "Bana son magana ina cin abinci, amman gashi na kira ki" Yayi maganar da dukkan gaskiyar shi, hakan bai taba faruwa da shi ba, amman yanda yake son jin muryarta, da bai kira ba, abincin ma ba zai ciyu ba. AbdulHafiz da yake zaune ne ya kula da kamar waya Hamzan yake. Hakan yasa karatun da yake ji na karewa, kafin wani ya shigo ya tsayar yana zare earpiece din daga kunnuwan shi hadi da kallon Hamzan da matukar mamaki. Dan yanayin maganganun ya tabbatar mishi da ba Anna bace ba. Kuma yaga abinci yake ci, dan rankwafowa yayi yana kai hannu ya taba fuskar Hamzan daya janye yana fadin "Zan kira 'yan Hisba, lafiya? Ya kake taba mun fuska da daren nan?" Dariya kawai AbdulHafiz yayi dan yaji lafiyar Hamzan kalau, babu zazzabi a jikin shi, coke din da yake ajiye a gaban shi ya dauka yana shinshina wa yaji ko ba zallar coke bace ba, dan sosai yake mamakin yanda akai Hamza yake magana yana cin abinci, bai damu da harar shi da Hamzan yake yi ba, ko yanda ya fisge gwangwanin coke din yana ajiye cokalin da yake hannun shi cikin abincin hadi da mikewa. Rigar shi AbdulHafiz ya janyo ta baya yana nuna mishi kwanon daya bari "Dan Allah AbdulHafiz ka kyaleni, ban gama ba ai, abu zan dauko in dawo" Hamzan ya fadi yana dakuna fuska, kitchen ya koma ya bude fridge, akwai section guda daya daga gidan saman, tunda fridge din na tsaye ne da babu mai taba mishi, karamar kwalbar giyar shi ya dauka yana kwancewa, a kitchen din ya tsaya, har lokacin da wayar shi manne a kunnen shi, yanajin Hindu na mishi bayanin tambayar da yayi mata, dan ta gaya mishi akan me test din da za'ayi "Dubawa kikeyi ko? Bana son cheaters" Dariyar da tayi na saka tsikar jikin shi ta shi, akwai babbar matsala, yai wannan tunanin yana daga kwalbar shi ya sha kusan rabi tukunna ya ajiye. "Allah ban duba komai ba, inda ka tambaya tun jiya nake karantawa" Kai Hamza ya jinjina mata yana sake daga kwalbar ya tuttula ma cikin shi, yanajin yanda jikin shi ya soma daukar dumi na daban, amman yaki dishe wanda muryar Hindu yake haifar mishi. Numfashi ya sauke mai nauyin gaske, yana saka Hindu fadin "Gajiya ko? Ka kwanta dan Allah" Kai ya jinjina mata "Yanzun nan....zamuyi magana da safe?" Sake ji yayi kamar ta daga mishi kai, kafin tace "In shaa Allah. Allah ya hutar da gajiya. Nagode sosai" Wayar ya sauke daga kunnen shi batare da yace komai ba, tukunna ya dauki kwalbar yana karasa shanyewa, ya jefa cikin kwandon shara, falon ya koma, yanajin idanuwan AbdulHafiz na bin shi da kallon tuhuma, a karo na farko da yaji dadi AbdulHafiz ne, ba zai taba tambayar shi ba, duk yanda yake so yaji kuwa, in dai bashi ya bude bakin shi yai mishi wani bayani ba, a cewar shi 'Idan mutum naso kaji abu, zai fada maka da kan shi, lokacin daya shirya, ba saika matsa mishi da tambayoyi ba. Kuma babu kyau jin kwaf' Gabaki daya rayuwar AbdulHafiz akan tsarika yake tafiyar da ita. Yau dai Hamza ya godema hakan sosai, saboda baya cikin yanayin da zai iya tsayawa bayani, robar da sauran dankalin yake ciki ya dauka da murfin yana mayarwa kitchen ya rufe ya ajiye. Sannan ya wuce dakin shi. Kayan jikin shi ya canza. Bacci ya kamata ace yayi, kafin ya kira Hindu ya sake rikita kan shi abinda yake da niyyar yi kenan. Amman yanzun kam labari ya sha banban. Akwai yarinyar daya kamata su hadu tun satin daya fita, ya tsaya yana mata yanga. Saboda ba ta wani yi mishi bane ba, balle kuma yanzun da idanuwan shi basa ganin kowa Sai Hindu, baya son kasancewa da kowa sai ita din. 'Zamu iya haduwa nan da mintina talatin?' Ya tura mata text din da yana shiga ta dawo mishi da address din inda zai dauketa din. Zai iya karasawa wajen cikin kasa da mintina sha biyar ma, in dai ba ya sami cunkoso a hanya ba. Mukullin mota ya dauka yana fitowa "Komai zai iya faruwa da kai a hanyar zuwa din kafin ka karasa, ko idan ka karasa koma ina ne kake shirin zuwa. Zaka iya mutuwa a kowanne lokaci wallahi, tun da sallama takeyi ba" Hanci Hamza yaja da yake jin kamar wani yaji a cikin hancin nashi da maganganun AbdulHafiz suka haifar mishi, kafin ya juyo ran shi a bace "Me yasa kake son shiga rayuwa ta ne haka AbdulHafiz?" Cikin takaici AbdulHafiz yake kallon shi, ya tsani kalar rayuwar nan daya zabar ma kan shi, ba kadan ba, har kasan zuciyarshi yake jin dacin hakan "Na fada maka, mutuwa bata sallama, zata iya daukar ka ko me kakeyi" Tsaki Hamza ya ja yana sa AbdulHafiz fadin "Karka sake, bana so, karka sake mun tsaki Hamza, karka sake" Yana sane yayi, bata mishi rai yake sonyi kamar yanda na shi yake a bace, duk da yasan ko me yasha ba zai sake din ba, baya kure hakurin AbdulHafiz din, ya tabayi sau daya, dakyar suka koma dai-dai. Bai sake ba, baya fata ya sake kuma. Juyawa yayi yana ficewa daga gidan. Yaji dadi da motar AbdulHafiz dince, ya ma manta bai karbi mukullin shi ba. A ciki zai dauki yarinyar, da ita kuma zaije hotel din da yayi niyya. Yasan dai inya dawo sai AbdulHafiz yasa an wanke mishi motar daga cikinta har wajenta, kamar wanda ya kwaso mishi wani mugun abu a jiki. Baice ba zai daina halayyar da yakeyi ba, amman AbdulHafiz din yakan saka shi jin kamar lokaci zai iya kure mishi a ko da yaushe kafin ya tuba. Bayan shi bama kwana zaiyi ba, yana gama abinda yakeyi zai zare jikin shi, ya fito ya dawo gida, komin dare kuwa, bai taba kwana da wata yarinya a waje daya ba, idan ita bata kama hanya ba, shi zai kama, ko da a cikin hotel dinne, idan bayason komawa gida, zai fita ya sake kama wani dakin daban. Shi bama yason jin mutum a kusa da shi idan har bacci zaiyi, ko da macece kuwa, duk yanda yake son mata, baya iya bacci kusa da daya daga cikin su. * Ranta kal take jin shi tana gama waya da Hamza, duk yau taki sakewa ta fita falo ta zauna. Sai take ganin kamar Anty zata gane ta fita da wani, kamar zata gane Hamza ya rike hannun ta, ko da ta shiga alwalar la'asar bayan ta dawo, sai da ta saka sabulu ta wanke hannunta, ta jima a sujjadarta, cikinta ta dinga neman yafiyar Ubangiji, ko sallar isha'i da tayi hakan ya kasance, bata dago goshinta sai taji kafafuwanta sunyi sanyi. Saboda so take zunuban da take jin nauyinsu su kakkabe su fado. Sai dai zuwa yanzun da suka gama waya da Hamza, ba tunanin zunubanta takeyi ba, tunanin shi takeyi. Muryar shi na amsa kuwwa a zuciyarta, koya ta juya sai taga fuskar shi a zuciyarta, murmushin rashin dalili takan ji ya kwace mata cike da wani irin shauki, sanin babu wani abin da zata iya tabukawa, yasa ta shiga manhajar Instagram dan ta more kallon hotuna, tana kuma son duba shafin teloline, har yanzun bata gama yanke hukuncin telan da zai mata dinkunan bikinta ba, so takeyi ta sami ko guda ukune, in yaso daga baya saita zabi guda daya. Haka kawai take jin kamar bikin nata ya matso kusa duk da ba'ayi maganar shi ba, zuciyarta bata taba gaya mata karya ba. Gara ta zaba da wuri kafin lokacin ya kure mata tazo tana hanzari a al'amarin. Tana refreshing shafin tana cin karo da Nabila da ta saka hotuna har guda uku, tsayawa tayi na farkon ya bude. Sai taga AbdulHafiz ne, akan wani doki mai fari da ratsin baki, dokin kan shi koshin da yayi abin kallo ne, yana sanye da kayan sarauta a jikin shi, kan shi nade da farin rawani daya rufe rabin fuskar shi, da alamun murmushi cikin idanuwan shi, daga kasa ta saka caption din 'Tafiya dai kwaro, bajimi sai horo, diyan ka basu ruwa. Jikan Shehu mai hidima, Allah ya kare mun kai Dikko na' Sauran hotunan biyu takai da sukayi mata kyau matuka. Ita kam ba zasu daina burgeta ba, tana duba comments kuwa sai ga na AbdulHafiz a farko. 'Gaba ke, baya ke, babu kamar ke Fulani' Sai taji kamar fitilar Hamza nason dishewa a ranta. Akwai wani abu tattare da Sarauta da yake burgeta har cikin kasusuwan jikin ta, lokutta da dama takan ji daman ace ita din ta fito daga gidan Sarauta ne. Kasa duba shafikan telolin tayi, ta saka wayar a key tana yin addu'ar bacci, tukunna ta juya hannu tana lumshe idanuwan ta, da fatan Allah ya taimaketa ta samu bacci. Aikam baccin tayi cike da mafarkin Hamza ya zama sarki, ita kuma ta zama Sarauniya, tana gefen shi tsaye ana zuba musu kirari. Ita kanta da safe da ta tashi sai da dariya ta kamata. Yau saboda tana cikin farin ciki kitchen ta wuce ta fara sharewa, babu ma wanke-wanke, da alama Asma tayi da dare. Doya ta fere ta dora, sannan ta fito ta share falon ta gyara ko ina. Ta koma ta tace doyar, lokacin Asma ta fito itama "Sannu da aiki. Ni me zan tayaki?" Kai Hindu ta girgiza mata "Kije kiyi shirin islamiyya abunki, doya kawai zan soya mana" Dan tsaye Asma tayi "Ko ki kawo in soya doyar to" Dan murmushi Hindu tayi, tana da tabbacin Asma ta gyara musu daki kafin ta fito "Asma ki wuce ki kyaleni, kullum ba ke kikeyin aikin ba?" Dariya kawai Asma tayi tana wucewa ta koma dakin su. Ita aiki bata dauke shi komai ba. Doyar kuwa Hindu ta fara soyawa, ta kunna karatun Qur'ani da take tabi a hankali, Zaid ya shigo kitchen din "Me kike soyawa? Ina ci... Yunwa nake ji" Dan juyowa tayi ta kalle shi "Yaya... Ina kwana. Doya ce fa, amman ban dafa ruwan zafi ba tukunna, bari in duba maka a flask ko akwai saura" Kai Zaid ya girgiza mata, tashi yayi cikin shi kamar anyi sata. "In da miya ki saka mun, idan babu kibani a haka nikam, kyale ruwan zafin nan" Plate ta dauka ta dibi doyar ta zuba mishi, tana karasawa ta bude tukunyar miya da take ajiye ta zuba mishi a gefe. Sannan ta mika mishi, ya karba da fadin "Nagode sosai" Ya fice, duk baudadden halin shi, koya kayi mishi abu sai ya nuna maka yaji dadi. Ko shara ya saka idan kayi, ko da baya kusa ya dawo yagani sai yazo ya sameka yace maka ya gode. Akan ce maza basu cika nuna jin dadin su akan al'amura ba, ita kam ta yarda maza nada banbanci halayya, kowa da yanda na shi yake, dan Zaid kawai yasa ta karyata wannan fadar da mutane kanyi. Ko Anty tana cewa matar shi zata sha wahala da halayen shi da yawa, amman idan ta fahimce su zasu dade basu sami matsala ba, dan shi mutum ne mai saukin kai. Kuma kamar yanda zai nuna maka yaji dadi in kayi mishi abu, haka zai nuna maka baiji dadi ba idan kayi mishi ba dai-dai ba. Tana karasa soyawa, ta gyara takardar ta rufe kular, dan kar zufa ta koma cikin doyar shisa ta saka takarda a kasa. Tasu ita da Asma ta dauka tana kai musu daki, sannan ta dawo ta duba flask, akwai ruwan zafi, shayinta kawai ta hada, tunda tasan bai dami Asma ba, shisa ma ta saka musu miya a gefe. Tare suka karya yau suna dan taba hira, har suka gama cin doyar. Asma ta dauke plate din da kofin da Hindu tasha shayi ta mayar kitchen, hijabi ta dauka da jakarta tana fadin "Ni kam na wuce" Hindu na amsa ta da "Kina da kudine a hannun ki?" Dan yini sukeyi ranakun asabar da lahadi "Ina da Naira dari" Tsaki Hindu taja a fili, dan tasan Asma ba shiga wajen Baba zatayi ba kafin ta wuce din, tana rasa kalarta wasu lokuttan, ko kudine idan ba'a dauka an bata ba, ba zata taba bude bakinta ta tambaya ba. "Ki mikomun jakata din can, ke ba zaki taba bude baki ki tambaya a baki kudi ba, banza kawai. Uban me zaki siya da Naira dari? Salon ulcer taje ta kamaki a banza" Asma dai batace komai ba, murmushi kawai takeyi, ita abubuwa irin haka basa bata mata rai. Jakar ta mika ma Hindu, ta bude tana bata dari biyar. Dan ita ko ranar juma'a sai da Baba ya bata kudi. "Nagode sosai" Asma ta fadi, tana saka Hindun sake jan wani tsakin. Dariya kawai tayi ta fice daga dakin. Hindu kuwa wayarta ta dauko ta duba taga ko Hamza yai mata magana, amman shiru. Tana tunanin ko ta tura mishi sako taji ya tashi lafiya. Ko kuma ta kyale shi, duk da Dimples kance mata 'Matan Hausawa na da matsala, sun ma jan aji mummunar fahimta. Su a ganin su jan aji shine namiji ne kawai zai dinga kiranki, idan shi bai miki magana ba ke ba zaki taba mishi magana ba, idan chatting kuke ki dinga amsa shi dai-dai. Kowa fa nasan kulawa, idan bai kira ki ba, ba wani abu bane dan ke kin kira kin duba shi, aji na cikin kama mutuncin ki, karki taba rokon shi wani abu, kisan me kikeyi. Amman ina amfanin bakiyi mishi magana ba, amman yana kira kina makale murya kina fadin sub dina ma ya kare' Yar siririyar dariya Hindu tayi yanzun ma, babu yanda za'ayi kai mintina biyar da Dimples bakayi dariya ba. Amman a cikin abinda da yawa kan dauka rashin hankalinta, akwai maganganu masu tarin ma'ana, text tayiwa Hamza 'Ka tashi lafiya? Ya gajiyar ka?' Sannan ta ajiye wayar tana shiga tayi wanka ta fito. Duk da babu inda zataje bai hanata yin kwalliya ba, ta feshe jikinta da turaruka masu karfi tunda tana gida. Doguwar riga ta saka ta material ja da baki daya karbi jikinta, ta sami hula kalar kayan ta saka a kanta tana dan turata baya. Tayi kyau dai-dai ita, sannan ta dauki wayarta tana dorawa kan drawing table dinta, ta dibo kayan zanenta, ta saita takarda, sai da ta saka earpiece a kunnuwanta ta hada da wayar tana sauraren wakokin Ed Sheeran, sannan ta fara zanenta. Jin alamar shigowar sako yasa ta mika hannu ta dauki wayar tana dubawa, Hamza ne 'Alhamdulillah. Ke ya kika tashi? Vid call?' Tana karanta ta zare earpiece din daga kunnenta da sauri, ta tura kujerar da take zaune kai baya tana mikewa, mayafi ta dauka ta nade kanta dashi tana gyara mishi zama. Tukunna ta tura mishi 'Sure' Tana komawa manhajar whatsapp, saiga kiran shi ya shigo, kunne daya na earpiece din ta makala tana daga kiran, kyakkyawar fuskar shi na cika screen din wayarta, tana saka ta tunanin yanda mutum zai kasance da kyau haka. Hannu yadan dago mata yana murmushi, a kunyace tace "Ina kwana" Maganar da alama ta dade bata kai mishi ba "Lafiya lau, kin yi kyau" Ya furta yana sakata ware idanuwa, dan tasan idan yana waje babu wanda zaice tana da kyau "Zolaya ko?" Hakoran shi ta fara gani kafin taji yayi dariya, sai dai kafin tace wani abu taga ya juya yana kokarin ture wani da yake son leqowa, amman sai da ya leqo din "Hello, Fodio ne" Tana kallo Hamza ya kauda fuskar wayar dan taga alamun kujeru, batajin me yake cewa dai, yakai mintina biyu sannan ya dago taga fuskar shi "Kiyi hakuri, zakiyita ganin kalar abubuwan nan, abokai na sai hamdala" Yar dariya Hindu tayi "Bakomai. Ka gaishe da Fodio din" Kai ya jinjina mata "Zan fita yanzun. Amman zamuyi magana anjima. Ki kula da kanki" Ta bude baki tace mishi shima ya kula da kan shi ya kashe kiran, kai kawai ta girgiza tana rubuta maganar ta tura mishi, sannan ta ajiye wayar tana cire mayafin ta cilla kan gado. Zanen ta cigaba da wani nishadi na daban wannan karin. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 10 Gabaki daya satin wani irin sama-sama take jinta, kamar wadda take yawo a saman gajimare, ko tafiya takeyi sai ta dinga jinta kamar reshen bishiya saboda nishadin da take ciki. Babu rana daya a cikin satin da ta wuce batare da tayi magana da Hamza ba, yana kiranta, duk da baya mata wata magana da ta shafi wani abu banda Architecture, jiyane kawai ya bukaci sanin inda take karatu. Ta kuma fada mishi, muryar shi wani irin sanyi take mata, duk yanda take a bude. Hausar shi tafi komai burgeta, bawai bai iya bane, akwai yanda yakan fitar da wasu haruffan da zasu tabbatar maka da cewa ba Hausa bace yaren da harshen shi ya fara lanqwasawa. Har yan gidan su zuwa yanzun sun fahimci nishadin da take ciki, hatta Zaid da ba shiga harkar kowa yake yiba sai da yace mata "Wai ke uban me yake damun ki kwana biyun nan?" Dan tabe baki tayi tana girgiza mishi kai "Babu komai, me kagani?" Bai sake kallonta ba, ballantana ma tayi tunanin zai furta wata maganar. Duk yanda take son ko Khadee ce ta ba labarin Hamza wannan karin taja bakinta tayi shiru, ba zatayi jinxing din abin ba. Kuma Khadee din ma bata dameta da tambaya ba, dan hidimar bikinta da yake gabatowa, bakomai take mayar da hankali a kai ba. Garama Asma kan bita da kallon tuhuma duk idan tana waya da Hamzan, saboda yanda murmushi sam baya barin fuskarta, haka idan suna chatting dashi. Sosai take son sanin wani abu a tare dashi da ba a kafar sada zumunta ya saka ba. Bataso tayi mishi tambayar da zata saka ya daina mata magana, dan taga har yanzun baya kula duk wani comment da zatayi a kasan posting din shi na Instagram. Ta dauka tunda suna magana ko dan liking ne zaiyi, amman bai ma nuna mata yagani ba, ta dai ga alamun yana WhatsApp ne saboda taga ya saka status kwana uku bayan ya kirata, sai tayi commenting, suka koma magana a can, maimakon Instagram. Yau kam tunda ta dawo gida wajen sha biyu da rabi, sallah ce kawai take rabata da tebirin zanenta, so take ta gama duk wani assignment da take dashi zuwa safiyar gobe asabar, dan ta samu ta fara karatun test din da take dashi ranar litinin. Sai bayan isha'i tukunna ta samu taci abinci, ta koma kan gado ta zauna, tana dora system dinta akan cinya, taji dadin wutar da suka kawo, tana addu'ar su barta har zuwa safe. Wani American film ne take kallo, series, mai suna SUITS. Tana kuma jin dadin shi fiye da yanda tayi tunani, akwai abokinta a Instagram, Ahmad. Shi yace mata ta kalla, har makaranta yazo ya kawo mata daga farko zuwa inda aka tsaya dan ana kanyine, jininsu ya hadu da Ahmad din, yana level 3 a KASU. Shima mayen kallon fina-finai ne, shine ma abinda ya fara asassa abokantakar tasu. Tunda tayi system ta daina damuwa da zaman falo, duk abinda take son kallo zata saka a cikin system din ta, ko kadan film baya yanke mata. Kallon taci gaba daga inda ta tsaya, da earpiece manne a kunnuwanta. Taji zir alamar shigowar sako a wayarta, batare da ta tsayar da film din ba ta dago wayar tana budewa. Hamza ne yai mata magana ta whatsapp 'Hey' Ya fadi, amman sai da taji wani abu na yawo a kasan cikinta kafin ya gauraye zuwa ko ina na jikinta yana karasawa cikin kirjinta yai zaune. Saboda yaune karo na farko da ya fara mata magana batare da ita ta fara mishi ba, shiga WhatsApp din tayi tana amsa shi da 'Hey' Tana fara rubuta gaisuwar da kafin ta tura yace mata 'Me kikeyi?' Goge gaisuwar tayi 'Kallo' Emoji din alamar tambaya ya saka mata, tayi murmushi 'American film, Suits' Ta dora da 'Kai me kakeyi?' Ya dan dauki lokaci kafin ya amsa cikin yaren turanci 'Ba wani abu mai yawa ba' Kallon amsar takeyi tana rasa abinda ya kamata tace, ba hirar da bata shafi Architecture suka cikayi ba, tunanin abinda zata tambayeshi takeyi 'Baka fadamun dan wanne gari bane kai' Cewar Hindu din 'Kaduna' Kai ta girgiza tana murmushi 'Bakayi kama da 'yan Kaduna ba' Wannan karin shiya turo mata da Emoji din murmushi, bai amsata ba, sai ga kiran shi ya shigo. Film din ta saka a pause tana amsawa da "Hello" Muryar shi na dukan dodon kunnenta "Da 'yan ina nayi kama?" Siririyar dariya tayi "Bansani ba, shisa nake tambayarka ai, har Hausar ka batayi kama da ta 'yan Kaduna ba" Tana jin numfashin daya sauke ta cikin wayar "Ann shuwace, Appa bafullatani, amman ni dan Kaduna ne tunda anan aka haifeni" Wannan karin ita ta sauke numfashin, batayi mamaki ba sam, dan batama yi tunanin baban nashi zai kasance dan kasa ba saboda kamannin shi, duk da ba haske ya cika can ba. "Kace kana jin yarika da yawa" Zata rantse taji girgiza kan da yayi duk da bata ganin shi "Guda hudu ne kawai, babu wani yawa" Dariya tayi cikin yanayin da yake nuna alamar ya burgeta sosai. Kafin ta amsa yace "Zan danyi abu, muyi magana anjima" Ya kashe wayar, yana sakata sauketa daga kunnenta tana dakuna fuska, haka yake mata wannan kashe wayar, ko ba zaiyi wani abu ba, da shi ya gama maganar da yake sonyi da ita yake kashewa batare daya jira amsarta ba. Amman kuma kalar ajin shi yayi mata, saboda yayi dai-dai da kyawun shi, tana hango musu abinda batason furtawa ita da shi, addu'a kawai ta karayi, dan yanzun bata asarar gabaki daya darenta a wajen zane, tunda Hamza ya amsata, ko yayane sai tayi sallah dan tana da tarin bukatu. Alamar shigowar sako taji, ta duba taga text ne wannan karin Hamza yayi mata, bata WhatsApp ba 'Zamu iya haduwa mu gaisa?' Batasan ta saki wani ihun murna ba sai da taji sautin cikin kunnuwanta, zufa takeji ta wajajen da bata taba zaton suna fitar da ita ba. Yau ita Hamza Abu Abbas yake tambaya ko zai iya haduwa da ita su gaisa, ba tun yanzun tasan Allah ya amshi addu'arta ba, kawai lokacine baiyi ba sai yanzun, daman Allah yana tare da mai hakuri. Yau kuma taga ribar hakurin takaicin duk tarkacen samarin da ta dinga kwasa a baya. 'Babu wata damuwa' Ta amsa shi, kafin ya sake tunani, kafin ya tuna cewar shine Hamza Abu Abbas, gayen da matan Instagram suke tururuwa a kanshi 'Lunch?' Gabanta taji yayi mummunar faduwa, kafin ya gama luguden ya kara mishi gudu ta hanyar fadin 'Ki saka time ki turomun address in zo in daukeki' Wannan karin fankar dakin bata hana gumi jiketa sharkaf ba, tabbas wannan shi Hausawa ke kira ga koshi ga kwanan yunwa. Hamza na tambayar su fita abinda turawa ke kira da 'Date' ne, yanayin shi bai nuna mata yayi kama da wanda zaizo kofar gidansu ta saka musu kujerun roba su zauna ba, batasan me yasa tayi tunanin hakan zai faru ba tun daga farko. Tasan ko mutuwa tayi ta dawo, Anty ba zata taba barinta fita da Hamza wani waje ba, kullum cikin maganar lalacewar da ta sami al'ada irin ta Malam Bahaushe take, tunda taga wani video na yawo a whatsapp na wata matashiyar budurwa da saurayinta ya hadama patin cikar shekara ashirin da uku, ya kuma tsugunna ya mika mata zobe yana tambayar ko zata aure shi kamar a kasar waje. Anty bataga komai ba, saka mata zoben kawai yayi, sai abokanan shi da nata da suke tafa musu, matan na fitar da wasu sautika da Anty ta kira da kukan mage, cikin nuna alamar yanda abin ya kayatar dasu, amman kwana tayi tana fada kamar zata ari baki, ita Hindu taga cikakken video din, har rungume juna sukayi, suka kuma sumbaci junansu, sosai ita kanta abin yayi mata wani iri, duk da bangaren da aka bada zoben da yanda wajen ya kawatu ya matukar burgeta. Balle kuma yanzun ita Hindu ta dauki kafafuwanta ta fadama Anty cewa Saurayi zaizo ya dauketa su fita cin abinci. Tasan magana ce da ko shaye-shaye tayi ba zata taba fara kwatantawa ba, ballantana kuma cikin hankalin ta, amman kuma ba zata bari wannan damar da ta samu ta wuce ta ba. Batare da sanin ya zatayi ba ta turama Hamza address dinta tana dorawa da 'Bayan azahar yayi?' Emoji da yake nuna 'ok' ya turo mata. Ta saka hannu tana goge zufar da take tsatssafo mata, kafin ta lalubo Dimples, dan tasan Biebee tsaf zata sami Anty ta gaya mata ga abinda yake faruwa idan ta hanata bataji ba, inma fada zasuyi suyi, sun shirya daga baya. Amman zatace da wani abu ya sameta gara sun daina magana. 'Dee saurayi nayi haka. Ya hadu da komai dai, so yanzun yana tambayata zamu fita cin abinci, kinsan Anty ba zata taba bari ba, bansan karyar da zan ba wallahi' Tana ganin kawunan hararar da Dimples din ta turo mata 'Babu shinkafa a gidanku ne halan?' Yar dariya Hindu tayi duk da batajin nishadi 'Kefa banza ce matsalar, me zance mishi?' Harar dai ta sake turowa 'Ki fada mishi gaskiya, yazo kofar gidan ubanki ya sameki, kuna da shinkafa a gidanku, idan ita yake marmari ki zuba mai a plate ki fitar mishi da ita. Amman karki fara bin saurayi yawon cin abinci, ba kowacce wayewa bace abin kwaikwayo' Sauka Hindu tayi daga whatsapp din, Dimples ba zata taba ganewa ba, Hauwa ta kira tana fada mata abinda ta fada ma Dimples din "Babe... Yazo gida zaifi fa" Kai Hindu take jinjinawa "Nasani wallahi, amman banason blowing wannan chance din, Hauwa yamun, irin yamun ba kadan ba. Dan Allah ki taimaka mun" Tana jin Hauwa ta sauke numfashi, kafin su tsayar da magana akan dabarar da zasuyi Hindu din ta fita ko da na awa dayane. Ta sauke wayar da murmushin nutsuwa a fuskarta, tana tsintar kanta da kashe system din gabaki daya, bata da wata natsuwar da zata cigaba da kallo, gara suyi hira da Hauwa ta tayata zaben abinda ya kamata ta saka, tsikar jikinta sai mikewa take saboda excitement, ta kasa yarda da cewar itace zata ga Hamza Abu Abbas gobe. * "Wai murmushin me kakeyi?" Fodio ya tambaya da mamaki bayyane a fuskar shi, sai da Hamza ya gyara zaman shi akan doguwar kujerar da yake zaune ya mike kafafuwan shi, hannun shi da kofin da ya zuba giyar da turawa kema laqabi da beer. Saboda bayaso ya rike kwalbar, a samu akasi AbdulHafiz ya shigo. Tun randa yasha wiwi a cikin gidan yana nan, har yanzun baya sakar mishi fuska. Wata magana mai tsayi ma bata hadasu ba, gara jiya da suka hadu wajen aiki sunyi magana kan project din da suke kanyi na zanen Estate a jahar Kano da ya samo musu daga gwamnatin tarayya. "Ba zaka gane ba" Cewar Hamza yana cigaba da danna wayar shi, hira yake da Hindu, abinda a sati daya ya fara zame mishi jiki, duk yau sau daya sukayi magana tace mishi tana makaranta, yanda yaita duba wayar shine yasa ya yanke hukunci fara yi mata magana. Dariya yayi yanzun kam mai sauti, bakomai yakan saka shi dariya haka ba "Allah mai iko" Fodio ya fadi yana kallon Hamza daya daga waya ya kara a kunne da alamun kira yakeyi, tashi wayar Fodio ya sauke daga kunnen shi yana sauraren hirar da Hamzan yakeyi da shigowar kiran Anna yasa shi yima Hindu sallama yana kashewa, ya kira Ann din yaji ko lafiya "Mai gyara ya kawo mun mota ta yanzun" Ta sanar dashi, ya jinjina kai, dan sunyi waya, ya rigada ya bashi kudin gyaran tun kafin ma ya gama "Yawwa to, ki hau kiji, in batai miki yanda kike so ba saiki fadamun" Hamza ya fadi kafin Anna ta kashe wayarta. Ya siyo motoci har biyu da kannen shi zasu dinga yawon su a ciki, amman baisan me yasa suke son daukar mata mota ba. Duk da bayason musu fada, amman wannan karin ya sauke musu sosai, idan suka gama aikin da sukeyi aka basu kudinsu, zai sai mata sabuwar mota, sai su karata da wannan din da suke naci. "Zaka fara magana ko sai na nemo wanda zai mun hacking wayarka?" Kallon 'Baka da hankali' Hamza yaima Fodio daya daga mishi girar shi duk biyun "Kayi budurwa ban sani ba" Kai Hamza yake girgizawa "No... Nope.... Ba budurwata bace ba, kawai muna magana ne" Dariya Fodio yayi mai sauti "Kai? Hamza, kai? Kake magana da mace, kiranta kayi fa. Banda Mansura ka fadamun macen da kake magana da ita?" Dan dakuna mishi fuska Hamza yayi "Ina magana da wasu mata mana" Ganin Fodio na mishi kallon 'Nine fa, karka raina mun hankali'. Shisa ya dora da "Ok, naji, ina magana da ita saboda tamun kyau, ba budurwata bace, ina so in tasting ne kawai" Sosai Fodio yake dariya irin ta gogaggun yan duniya "Yanzun ka fito mun a mutum, me yasa ka tsaya kana wani boye-boye to, ka taya kawai" Kai Hamza ya girgiza mishi "Ina ganin ta ba kamar sauran ba, ina so mu hadu ma bansan ta inda zan fara ba, ni ban saba neman su ba kasani, su suke nemana" Kai Fodio yake girgizawa yana mika ma Hamza hannu, da bai musa ba ya mika ma Fodio wayar yana furta "Hindu" Fodio ya jinjina mishi kai, ko mintina biyar baiyi ba ya mikama Hamza tare da fadin "Ga address dinta nan, zaku fita cin abinci gobe" Dan ware mishi idanuwa Hamza yayi yana amsar wayar ya duba hirar "Woo Maza..." Tashi wayar Fodio ya dauka yana dafa kujera ya mike, dan zaune yake kan kafet "Kai ni yunwa nakeji, in zaka taso muje" Kai Hamza ya girgiza mishi "Kamun take away. Zan danyi abu" Wucewa Fodio yayi batare daya amsa ba, Hamza kuwa murmushi yayi, da gaske yake da yace ma Fodio yana son dandano ne kawai a tare da Hindu, saboda yanda ta manne mishi a kai, yana son fitar da ita, bashida lokacin wannan a yanzun. Akwai matakin da yake son kaiwa tukunna, ginin da yakeyi ma bai karasa ba, saiya kammala tsaf, yaji wasu miliyoyi a account din shi, saiya nemo wata 'yar ustaziya ya kawo ya ajiye dan Anna ta kwantar da hankalinta da maganar aure da ta fara yi mishi. * Wasu kayoyi takeji sun mata tsaye a cikinta tun da ta tashi, gashi ko baccin kirki bata samu tayi ba, saboda tunanin yanda yau din zata kasance, dakyar ta samu bacci da safe, shima zuwa goma da rabi harta tashi, ta fita kitchen ta samu Asma har tayi wanke-wanke ta wuce Islamiyya abinta. Ko da suna gida, ko da Hindu bata da wani abin da zatayi, Asma bata jiranta, sam basa raba aiki, ita Asma bata da son jiki, ko Anty na fada. Hindu kam in zata iya gujema aiki tsaf zata guje mishi. Shayi ta dan sha da biredi kadan, dan sam batajin yunwa, ta koma falo tana zama, daga Anty sai Khadee suna kallon Hanyar Kano da aka saka a tashar Arewa. Itama zama tayi suna yin kallon tare, lokaci-lokaci take kallon wayarta da tabar ma Hauwa sakon ta kirata tana zaune kusa da Anty. Zuwa can kuwa Hauwar ta kirata, daga wayar tayi tana sakawa a speaker "Yan mata, ya ake ciki?" Hindu ta fadi "Lafiya kalau, ya su Anty da kowa?" Hauwa ta amsa ta dayan bangaren "Suna lafiya, tana ma jinki" Ta karasa tana mikama Anty wayar suka gaisa da Hauwar, tukunna ta sake miko ma Hindu "Ke kinji Aboje wai yau zaiyi lecture din shi ko? Karfe daya ne ko biyu, banma duba ba sosai" Dakuna fuska Hindu tayi tana cire wayar daga speaker ta kara a kunne "Kice mun wasa kike, dan ban niyyar zuwa makaranta ba yau, ni zan rage zane ne ma fa da in danyi karatun test" Cewar Hindu tana jin yanda Anty take binta da idanuwa kamar ta gane shirine duk maganganun nasu, amman da gaske ne akan saka musu lecture ranaku irin haka. Ko idan suna presentation, yakan kai daga Alhamis har zuwa Asabar, ba bakon abu bane ba daman. Wata rana ma in sun kai Magriba wani a gidan kanzo ya dauketa su dawo. Bata taba karyar tana da aji ba sai yau, shisa ta tsargu, tana sauke wayar ta zabga uban tsakin da yasa Khadee yin dariya "Yarinya sai a tashi a fara shiri" Hararta Hindun tayi "To Hajiya, ai sai da azahar akace ba wai yanzun bane, bari in tashi in rage wani abin kawai" Hindu ta karasa tana mikewa kamar ranta ya baci da maganar fitar da zatayi "Karatu sai da hakuri daman ai, wata rana sai kiga kamar ba'ayi ba" Anty ta fadi, dan wani lokacin har tausayin Hindun takeji, duk idan taga alamar haske a dakin su idan ta fito, ko ta shiga dubasu taganta tsakiyar dare tanata faman zane da takardu a gabanta, karatunsu ba mai sauki bane ba. "Allah dai ya nuna mana mu gama din mu huta" Hindu tai maganar tanajin wani bargon rashin gaskiya daya lullubeta da karyar da tayiwa Antyn. Kafin Anty da Khadee su amsa da "Amin..." Hindu na wucewa daki tabarsu anan, tana shiga ta tura kofa ta tsugunna tana mayar da numfashi, zuciyarta na harbawa kamar zata fado daga kirjinta saboda tsoron da take ciki "Wooo... Allah nagode maka" Ta furta tana mikewa, sun gama magana da Hauwa, tace mata ta saka wandon pallazo, sai ta saka dogon hijab da takalma masu tsini, ta dauki jaka da zata tafi da shigar, ta dora tabaranta, karta cika wata kwalliya mai yawa, jambaki ma zaiyi, dan zai iya dauka cewa tayi kwalliyar ne kawai dan zasu hadu. Shisa take bala'in jin dadin kawancen su da Hauwa. Ba magana ta cika ba, asalima randa yan miskilancin nata suke kanta, tana iya wuni da fuskar nan tata a murtuke, kawai tasan kayane, ta kuma yarda da shigar alfarma, wanda basu santa ba zasuce ko tana karyane, kuma ba haka bane, da dukkan gaskiyarta take gayu, saboda bata son harkar zubar da girma. Bata da hijabi, amma Asma nada su kala-kala, dan ita duk shigarta da Hijab takeyi, kuma doguwa ce sosai, tama danfi Hindun tsayi. Harma ta zabi hijabin da take so din ta dauko ta ajiye, sauran kayan ta fito dasu tana hadawa waje daya. Ganin lokaci yaki mata saurine yasa ta yanke hukuncin yin zane, dan yafi komai sa taga saurin lokaci. Aikam kafin kace wani abu har karfe daya ta saura kwata. Ta mike tana kara watsa ruwa ta dauro alwala, lokacin data dan murza mai da hoda a fuskarta har an kira sallah. Gabatar da azahar tayi tana yin azkar din bayan sallah tayi addu'a tana dorawa da 'Allah Ka san duk abinda yake a zuciyata, Ka san Hamza ne kalar mijin daya dace dani, Allah Ka tabbatar mun da mafarkina. Allah kasa wannan karin shine karshen wahalata, Allah Ka haskani a zuciyar shi, idan yana da wata ma ta fice fit daga ran shi, Allah kasa gabas, yamma, kudu da arewa idan Hamza ya juya kar yaga kowa, kar yaga komai saini' Sabonta ne, shisa ta maimaita sau uku tana rufewa da Salati dan ya tunkuda mata addu'ar tayi saurin karasawa da sauri. Sannan ta mike tana sake kaya. Batasan ko ita kadai bace, ko dan ba zata ga muninta ba, amman tayi ma kanta kyau a mudubin data kalla, alamar shigowar text taji ta karasa ta dauki wayar 'Zan karaso nan da mintina sha biyar ko sama sa haka kadan' Murmushi tayi tanajin wani abu ya kulle a cikinta duk da farin cikin da take ciki. 'Ok' Ta amsa shi, dan batasan meya kamata tace ba, mintina goma ta bashi, tukunna ta saka hijab din da ruwan kasa ce mai haske, yadin mai yashi, sai roba da aka saka a jikin hannun, sosai taga tayi kyau, ba kadan ba Asma take mata kyau a cikin shigar hijabanta, kawai dai ita tafi jin dadin saka abaya ne. Tunda duka biyun sun rufe jiki yanda ya kamata. Tabaranta ta dauka na gayu ruwan kasa mai cizawa tana sakawa, sai taga ta fito a yar gayu sak yau, fiye da kullum, sannan ta saka takalminta baqi tana daukar bakar jaka ta sakala a jikin tsintsiyar hannunta, turare mai kamshin sauki ta fesa, ta cire tabaran tana rikewa a hannu, daman duk ta saka abinda take bukata a jakar harda wayarta, sannan ta fito. Taji dadi sosai da taga Anty na sallah, dan haka ta furta "Na wuce Anty, saina dawo" Tana jan kofar ta fice daga gidan tana sauri, dan gani takeyi kamar Anty zata idar da sallah ta fito tace mata ta dawo tasan karya takeyi, sai da tabar gidan tana karya kwana sannan ta saka tabarau din a fuskarta tana takawa zuwa bakin hanya, sannan ta ciro wayarta daga jaka dan ta kira Hamza tace mishi ya tsaya a bakin hanya karya shigo kwanar gashash street din, ta fito. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 14 Daya koma gida kwanciya ya sakeyi, saboda yanda yakejin jikin shi, har wani zazzabin wahala ya rufe shi. Ya dauka inya sami wata zai rage abinda yakeji, amman fuskar Hindu ya dinga dorawa a ta yarinyar. In za'a yanka shi har ya baro hotel din ba zaice ga kalarta fuskarta ba, ballantana yanayinta, gangar jikin shi ce kawai ta kasance da ita, tunanin shi da ganin shi duk Hindu ce tayi kane-kane. Sosai abin yake tsorata shi, da ace baije gidansu ba, zai dauka ko aljana ce ya hadu da ita shisa ta dabai-baye rayuwar shi haka. Yanzun ma duk abinda ya durama cikin shi, bai daina ganinta tana gilmawa ta cikin idanuwan shi ba, bai kuma daina jin duminta a jikin shi ba. Giyar yau taqi tasiri ballantana ta disar mishi hasaso lokacin daya rike Hindu a kirjin shi, daya rufe idanuwan shi sai yaji kamar har lokacin tana rike a kirjin shi. Ya rasa kalar jarabar data same shi haka. Dakyar ya iya zuwa sallar isha'i. Yaga text dinta ya share bau amsa ba, kamar yanda yaki daga kiran daya biyo bayan text din, muryarta wahala kawai zata kara mishi. Har tunanin yaje gidan su yaganta yayi, amman bayajin idan yaje zai iya controlling kan shi da abinda yakeji, kuma yana da yaqinin basuyi nisan da zai nuna Hindu asalin maitar shi ba. A hankali yake so ya jata, lokacin da zai ajiyeta ba zata san me ya faru ba, ko ya akayi ya faru. Yanzun ma a kwancen yake a falo, kan doguwar kujera, dakin yana nan yanda su Fodio suka fita da safe suka barshi, sai robar coke da yasha rabi, yaje ya bude daya daga cikin giyar shi yana karasa cika robar da shi ya dawo falo ya ajiye. Arafat ke siyan abin zuqar lemo ya ajiye a gidan, ya dauka ya saka cikin robar coke din, bayajin dadin jikin shi, tun abincin rana rabon shi da wani abu, sai giyar da yaketa kwankwada. TV nata aiki, amman hankalin shi baya kai, tunanin shi na tare da Hindu, da abinda takeyi, sai robar coke din da yake dan dagowa yana zuqa daga kwancen a hankali, a hankali. A haka su Fodio sukayi sallamar daya amsa can kasan makoshi, AbdulHafiz na dorawa da "Ka gyara kwanciyar ka Malan" Dan ya tsani yaga daya a cikinsu yayi ruf da ciki, sai yaita ganin kamar mutuwa zata iya dirar musu cikin wannan kwanciyar da batada kyau a addinance. Numfashi Hamza yaja yana saukewa da fadin "Arafat baku gaji bane?" Dakuna mishi fuska Arafat da yake cire jacket din jikin shi yayi, ya jefa kan kujera, yana kwance agogo kafin ya amsa Hamzan "Asalin gajiya ma, kaji kasusuwan jikina kuwa" Numfashi Hamza ya sake ja "AbdulHafiz naga yana da sauran karfin takura mun" Dariya Fodio yayi, AbdulHafiz ya dauki jacket din da Arafat ya cire yana jefa mishi a fuska "Wai me yasa zaku dinga baza kaya ko ina?" Cire rigar Arafat yayi daga fuskar shi yana rikewa a hannun shi "Dan Allah karka fara dani, wai mu ba Maza bane ba? Me yasa ba zamu dinga baza kaya inda muke so ba. Fodio...." Arafat ya karasa maganar yana mayar da hankalin shi kan Fodio daya sunkuya zai dauki robar lemon da Hamza ya janye "Ba lemo bane kawai" Ya fadi dai-dai kunnen Fodio din, daya jinjina mishi kai, sannan ya sakar mishi robar "Fodio kana jina fa" Zuqar lemon yayi sosai, ya mayar ma Hamza, tukunna ya kalli Fodio da yake harar shi "Nan gidanka ne, kai ya kamata ka fadama AbdulHafiz ya dinga kyalemu muna barbaza kaya yanda muke so" Dagowa AbdulHafiz yayi, dan kofuna yake tattarawa, a gajiye yake, koma bayajin gajiya ba zai bata bakin shi akan Hamza ba, yasan ko dan ya saka shi magana zai iya qin dauke kwanonin. Da sauri Fodio ya daga mishi hannuwa alamar bada kai, wato 'surrender'. Yanayin da ya saka Arafat zagin Fodio din yana dorawa da "Matsoracin banza kawai" Dariya Fodio yayi yana wucewa dakin shi dan ya watsa ruwa. Arafat dinma wucewa yayi, AbdulHafiz kuwa sai da ya tattara duka kwanonin da suke cikin dakin yakai kitchen, tukunna ya dawo yana wuce Hamza batare da yace komai ba, kara gyara kwanciya Hamza yayi yana zuqar lemon shi har lokacin. Wayar shi da yaji kararta alamar shigowar sako, yasa shi miqa hannu ya lalubota daga gefen shi, yana dubawa. Hindu ce 'Ina ka shiga haka? Kana lafiya dai ko?' Birkitawa yayi, yana kwanciya kan bayan shi "Bana lafiya wallahi, ke nake bukata a kusa dani" Ya furta a fili, yana tura mata 'Inata hidima, kuma banama jin dadi dai' Wayar ya saka a silent, yana sakata a key ya ajiye a gefen shi, text din da sukai musaya kawai na neman sake birkita shi. Sauran lemon ya karasa shanyewa, yanajin kan shi yayi nauyi sosai. Idan ya kara zai iya buguwa fiye da yanda yake so. Ba zai iya hada abu biyu a lokaci daya ba, tunanin Hindu kawai ya ishe shi, ba saiya hada da fadan AbdulHafiz da bazai kare ba, idan ya gan shi a buge. Da zai sha har sai ya daina gane abinda yakeyi. Ba zaice ga iya lokacin daya dauka ba, yanajin shige da ficen su Fodio duk da idanuwan shi a lumshe suke. Sai da yaji Fodio na kiran "Kai ba zaka ci wani abu ba?" Idanuwan shi ya bude da yakejin sunyi mishi nauyi sosai "Banajin yunwa nikam" Ya furta yana kara gyara kwanciya, Fodio nashi ya dauka yana fadin "Sai da safen ku" Arafat daman a fridge yaje ya saka, shi yaci samosa da lemo a hanya. Bacci kawai yake son yi, AbdulHafiz suka bari da yake zaune akan kafet yana cin abincin suna hira da Nabila da take mishi rikicin aiki yasa basuyi magana da yawa ba, ganin lallashi ba zai aiki ba, yasa shi nuna mata jan ido yasa ta sauka ta kwanta, tunda tace mishi tana da makaranta da sassafe. "Kai me kaci?" AbdulHafiz din ya bukata, dan ya san ba bacci Hamza yakeyi ba "Ka kyaleni dan Allah" Hamza ya fadi cikin bacin rai, bayason wata takura koya take a yanda yake jin shi, amman AbdulHafiz ne, in baiyi niyya ba, babu wanda ya isa ya saka shi barin abu, ko ranshi kake son ganin ya baci, sai yayi niyya ne zai nuna maka "Me yake damun ka?" Hamzan yasan inba maganar sukayi ba, AbdulHafiz zai share duk wani abu da zai fada yaci gaba da maimaita tambayar har saiya amsa "Bana jin dadi" Ya amsa a taqaice yana mikewa zaune, ya runtsa idanuwan shi saboda dakin dayaga ya wulwula mishi "Ok" AbdulHafiz ya furta yana dan ture robar take away din da take gaban shi, dan ya koshi. Yana karantar damuwa a fuskar Hamzan, ya kuma kula da yanda yake komai a hankali, kamar yanda yakanyi duk idan yasha wani abu, bayaso AbdulHafiz din ya gane. Yana kyale shine, saboda addu'a ce kawai zata fi saurin tasiri akan shi, tunda yana kokarin boyewa, hakan na nufin akwai sauran imani a tare da shi, akwai kuma yiwuwar shiriya zata same shi a kowanne lokaci. Kai Hamzan ya girgiza "Ka daina mun haka" Fuska AbdulHafiz ya dakuna mishi cike da alamar tambaya, yana saka shi nuna shi da dan yatsa "Gashi nan, abinda kakeyi ne bana so, ka daina yi kamar ni nake so in fada maka matsalata, bayan kaine ka tambayeni" Mikewa AbdulHafiz yayi, ya dauki robar take away din "Sai da safe, idan kana son shawarata, kasan zaka iya kwankwasa mun kofa" Ya karasa maganar yana wucewa abin shi, numfashi Hamza yaja, yana komawa kan kujerar ya kwanta, bayajin karfin tashi ballantana ya wuce yaje ya kwanta, kuma shi bashi da matsala da kwana akan kujera, balle Fodio ya zuba kujeru masu fadi, yana jin dadin kwanciya a kai sosai. Ya lumshe idanuwan shi, yana addu'ar samun bacci, ko zai daina tunanin Hindu da son kasancewa tare da ita. * Kwata-kwata batajin dadin jikinta, duk motsin da zatayi sai taji kamar wani bangare na Hamza na liqe da ita. Sai take ganin kamar ta makara wajen tuban da tayi, kamar Allah ba zai amshi tuban nata ba, shisa takeji tamkar an tsaga fatar jikinta an tura mata zunuban da takejin nauyin su har lokacin 'Allah Kabani karfin gwiwar ko da ture shine idan ya sake kwanta irin hakan. Allah Kaa yafe mun Ka karemun imanina' Shine abinda take maimaitawa duk juyin da zatayi, zanen ma ganin layukan na hade mata yasa ta hakura, ga rashin maganar da basuyi ba da Hamzan ya kara sakata shiga yanayi. Lokaci zuwa lokaci take tsintar kanta da duba wayarta ko ya mata magana, itace bataji karar wayar ba. Har kallo ta fara data kwanta, ko zai dauke mata hankali, amman ta kasa, tunani ne kala-kala a ranta, musamman yanda zatayi ma Hamza magana karya sake tabata, ya hakura suyi aure tukunna, kafin ta fara tunanin ai har yanzun baima ce yana sonta ba ballantana magana irin wannan ta shiga tsakanin su. Ganin tunani zai dameta ya sata shiga Instagram, tana ta kallon kwalliya tunda tana da wadattaciyar Data, Hamza na tura mata kati har ta rasa abinda zatayi da shi. Sai dai ta siyi data ta shiga YouTube ko taje Instagram taita kallon shagalin bukukuwan da ake sakawa a shafin 9ja weddings. Abin yana kayatar da ita, wasu bukukuwan kan sata hasaso yanda nata zai kasance. Yanzun din ma abinda takeyi kenan, tana hango dinkin da za'ayi mata, sai taga notification na cewa an mata sako, da sauri ta duba ko Hamza ne, dan sha biyun dare, sai taga Ahmad ne yayi mata sallama, duk sai taji haushi ya kamata, dan har ranta ta saka ran Hamza ne. Kamar ta share shi, saita bude ta amsa sallamar 'Wai kinga abinda ya sami Mike?' Da sauri ta fara bashi amsa 'Wallahi Ahmad karka bani labari, karka batamun kallona, ka kyaleni' Kawunan dariya ya turo mata, kafin suci gaba da hira, yana dan debe mata kewar Hamzan da takeyi. Batasan lokaci na ja bama, dan in suka fara hirar films ita da Ahmad din, ko waya sukeyi hakan ne yake kasancewa, kan abu daya daya faru a film din zasu iya kwanaki suna gardama a kai, kamar yanzun da ta dake babu abinda Mike zai nuna ma Harvey sai kwakwalwar shi, amman Ahmad din yaki yarda. Wajen daya saura, taji idanuwanta sun fara mata yaji, ta fita daga chat din su da Ahmad din taga Hamza yayi mata magana a Instagram din, kuma baifi mintina biyu da sauka ba. Amsa Hello din shi tayi, sakon na shiga tana ganin ya turo mata alamar tambaya a whatsapp. Sai ta koma can din, kafin ta amsa shi ya sake turo 'Bakiyi bacci ba? Me kike yi? Zane?' Ya jero mata tambayoyin yana sakata yin murmushi 'Aa, ina kwance ne ma, yanzun dai zanyi baccin, kai ma bakayi ba, ko aikin ne?' Tana kallon yana rubutu 'To me kikeyi? Bakiyi bacci ba har yanzun' Ya turo yana share tambayar ita da tayi mishi, tasan halin rikicin shi 'Naje Instagram ina kalle-kalle, sai kuma na tsaya muna hirar film ni da Ahmad' Tana ganin ya dauki lokaci yana typing 'Ahmad? Waye shi din? Har tsakiyar dare kina hira da shi? Me yasa zaki dinga magana da shi da daren nan? Akan me? Shi me yasa zaiyi hira dake da daren nan?' Yau kam ji tayi tagaji da kishin da yake nunawa a kanta ba soyayya suke ba, baice yana son ta ba, amman ya dinga tsareta da tambayoyi, yanzun bata isa ta amsa wani a comment section ba sai sunyi rigima, ko hoto ta saka nata sai yace ta cire. 'Kai ga shi ina hira da kai, menene dan nayi da shi? Abokina ne' Gani tayi yana typing, yakai mintina biyu, amman sako bai shigo mata ba, har tayi tunanin ko network dinta ne, kafin taga kiran shi na shigowa, sai da taji gabanta ya fadi, da sauri ta danna gefen malatsin wayar tana sakata a silent, tashi tayi ta sakko daga kan gadon tana zuwa ta duba kofar dakin, taga Asma bata rufe ba, ita ta murda mukullin, sanda ta koma kiran harya yanke, saiga sakon shi ya shigo 'Ki daga wayar nan Hindatu' Kafin ta amsa ya sake kira, dagawa tayi muryarta can kasa tana fadin "Hello" Ta dan runtsa idanuwanta jin yanda muryar shi ta daki kunnenta a fadace "Ni da shi daya ne? Me yasa zaki hada mu kamar muhimmancin mu a wajen ki iri daya ne? Akan me zaki ce dan kina magana dani ko da yaushe shima zakiyi magana da shi haka?" Tashi zaune tayi dan taga alamar rigimar Hamza yake so suyi, abinda bai sani ba shine ita kanta ta iya rigimar, kawai dai bata nuna mishi ne, tana lallaba shi, idanuwan shi kawai idan ya kafa mata sai taji duk jikinta yayi sanyi, amman yanzun bata ganin shi, zata iya tattaro kwarin gwiwarta ta fada mishi duk abinda take son fada "Kasan ko bashi ba dole zan kula wasu ai..." Tana jin hucin da yake har ta cikin wayar "Saboda me?" Numfashi ta sauke "Saboda ni macece, budurwa kuma, ko ba abokai ba, zanyi samari" Tana jin shirun daya biyo bayan maganarta, dan saida ta ciro wayar daga kunnenta dan taga bai kashe ba, tana ta reading, kawai shiru yayi da yasa zuciyarta cigaba da dokawa kamar zata fito daga kirjinta "Bana so" Ya fadi can kasan makoshi, yana sa ta sauke muryarta "Haka zakayi hakuri... Dole zanyi samari Hamza, kaima abokina ne" Tayi maganar da wani irin ciwo da taji ya fito daga zuciyarta, tasan karya takeyi, tana kuma addu'ar baiji yanda muryarta take rawa ba, yanda ya wuce matsayin aboki a wajenta, tana son shi, tana son shi fiye da yanda take tunanin soyayya take, tana son shi har mamaki abin yake bata. "Kibari, bana so, karki sake hadani layi daya da abokan ki" Cike da gajiyar da takeji har a kasusuwanta, da kuma kukan da take son tarbewa tace "Ina kake so in ajiyeka? Ka fadamun inda kake so in ajiyeka" Shirun ya sake biyo baya, fiye da na dazun, kafin kamar wanda aka shaqe yace "Ki ajiyeni a saurayin ki, karki hadani da kowa, bana so, karki hadani da kowanne namiji. Wallahi zamu sami babbar matsala" Murmushinta da wasu hawaye masu zafi ya bayyana, tasa ka hannu tana share su, tana jin yanda zuciyarta take tsalle-tsalle "Ahmad da wa kike hira cikin daren nan?" Kai ta girgiza tana danyin gyaran murya kafin tace "Shi kadai ne" Da sauri ya amsata da "Ban yarda ba" Kafin ta amsa ya sake cewa "In gani" Yana kashe wayar, Hindu ta sauketa daga kunnenta tana binta da kallo, kafin sakon shi ya shigo mata ta whatsapp "Menene Password dinki?" Tsintar kanta tayi da tura mishi 'HAlamin' Tana cigaba da kallon wayar, baifi mintina biyar tsakani ba, ta sake ganin ya mata magana "Jibi tarin mazan da kike magana da su, Hindu kina so ki kasheni ko?" Murmushi tayi, bata san abinda zatace mishi ba, can ta sake ganin yayi magana "Kina Twitter daman? Me yasa wannan banzan yake tambayar handle dinki?" Batama san waye yake magana akai ba, ikon Allah kawai take kallo, kafin taga notification din twitter alamar anyi following dinta, tana dubawa taga Hamza dinne, shisa ta neme shi bata gan shi ba a Twitter, HAbuAbbas ya saka a handle din. Bin shu tayi itama, tana fara duba tweets din shi, duk yawancin hirarrikin shi da abokan shine, sai wata Mansy_ da taga suna magana, ta bude profile dinta tana duba hoton ta, sai da taji gabanta yayi mummunar faduwa ganin hoton jikin Avi din Mansy din ita da Hamza ne, da alama ita ta dauka, dan Hamzan yana bayanta ya daga girar shi duka biyun da murmushi a fuskar shi. Da sauri ta koma tana sake duba hirarrikin nasu da bata fahimta, dan yawanci da yaren fulatanci duk maganganun da sukayi yake. Handle din Mansy din ta sake komawa tana shiga gabaki daya hotunan ta da sun kai dari takwas, tana kuma matuqar mamakin ganin wajen kala talatin duk tare da Hamza ne, sai wasu da yawa kuma nashi ne shi kadai. Zuciyarta ta so gaya mata kanwar shi ce, amman kuma yanayinta ya nuna zata iya zuwa shekaru daya da Hamzan, dan ba yarinya bace ba, kuma kanwar shi ba zata saka hoton su da caption din 'Me and Mine' ba. Ta kira shi nata a yawancin duk hotunan da ta saka nasu, kuma bata ga inda ya gyara mata ba. Kanta taji ya fara sarawa saboda tashin hankali, tsintar kanta tayi da dawowa Whatsapp inda Hamzan yabar mata tarin saqonni yana mata tambayoyi akan mazan da suke DM dinta na Instagram din 'Wacece Mansy?' Ta tambaya, bai ko numfasa ba ya dawo mata da amsa 'Qawata ce' Yana dorawa da 'Mariya24' Kafin ya sake cewa 'Shine password dina na Twitter, ki duba kigani, banda abinda zan boye miki' Numfashi Hindu ta sauke da batasan tana rike da shi ba, duk da ta sami waje a layin mutanen da ta tsana ta saka Mansy a saman dukkan su, zata hau twitter din tagani kamar yanda yayi ikirarin bashi da abinda zai boye mata. Gara ta tabbatar dai, amman ba a daren nan zatayi haka ba. Sai da safe, zuciyarta gara ta nutsu waje daya. Kar ta buga da irin tsallen da taketa faman yi, yau zata kwanta da nasara guda daya, zata iya nuna ma kowa Hamza ta kuma kira shi da saurayinta, wannan kadai ya isheta, shine kuma abinda zatayi tunani, Mansy da komai zasu iya jira sai da safe. Hakan kuwa tayi tana lumshe idanuwanta, ko sallama batai ma Hamza ba, bacci yayi gaba da ita cike da mafarkin shi. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 13 Idan akace maka a kasa da wata daya Hindu da Hamza sukai kalar shakuwar da sukayi zaka karyata hakan. Idan basa manne da juna ta waya, suna manne ta chatting, dan ma lokutta da dama karatu yake tayata yi, amman ko zane takeyi, maimakon ta saka waka ko karatu yanda takanyi wani lokacin, sai suyi waya. Ko aiki yake yakanyi mata text. Sai dai kamar yanda tagani tun a haduwar su ta farko, yana da rigima, sosai yana da rigima fiye da yanda take tunani. Zuwa yanzun Hauwa kadai tasan suna tare da Hamzan, batason ta cika yawan magana akan shi din, tunda bawai yace yana sonta bane ko wani abu. Ko kadan bata wasa da addu'a kan hakan ya kasance. Dan har ranta take jin Hamzan. A lokacin kuma sau uku kadai suka hadu, zai wuce hidima ne sai ya biyo makaranta yaganta, ko mintina biyar baya cikawa, saboda yace mata sosai aiki ya rincabe musu. Yaune dai sukayi dashi zaizo har gida ya ganta. Dan ta ma sanarma da Anty, ta kuma gaya mata baya tashi aiki da wuri, ba zai samu zuwa da yamma ba. Ita kanta wani sama-sama take jinta, duk da yana kokarin kiranta video call, ba kamar tana ganin shi ba, yayi mata alkawarin ana idar da Magriba, zai bata awa biyu cikakku "Ina so in ganki" Shine abinda ya furta mata "Da gaske ina so in ganki, Video call din nan baya mun" Dariya kawai tayi, sai gashi kuma ya samar musu lokaci. Yau kam kwalliya tayi sosai, tana saka Abaya, a harabar gidan ta same shi a tsaye jikin motar shi. Jikin shi sanye da shadda sai maiqo takeyi, fara kal da ita, sai hular shi da takalmin kafar shi ruwan toka, yayi mata kyau kamar ta sace shi ta boye kar wata ta kallar mata shi. Murmushi yayi mata "Sannu da zuwa" Ta furta tana ajiye mishi kujerar data dauko, ta rabasu da yake guda biyune a hade, itama ta ajiye daya a gefe. "Ina zuwa" Cewar Hindu tana komawa, a bangaren Mama ta tsaya tana shiga kitchen ta dauko mishi ruwa roba daya, sai coke da tagani a ciki, batasan waya zuba ba. Ta dai dauki guda daya ta sami plate mai kyau, sannan ta koma. Plate din ta ajiye a kasa, tana dora ruwan da coke din a kai. "Ga ruwa" Hannu Hamza ya kai yana daukar coke din dan lemon shine "Ke dai ki sha ruwan, nikam na dauki coke" Yai maganar yana bude robar yakai bakin shi ya kurba "Kin san yanda nayi kewar ki kuwa?" Sadda kanta kasa tayi a kunyace, tana jin dadi idan yace yayi kewarta, sai taji kamar tana da wani muhimmanci mai girma a wajen shi "Nima nayi kewar ka ai" Ta tsinci kanta da furtawa, tana saka shi girgiza mata kai "Da kinyi kewata da kin kalleni, tunda kika fito idanuwanki suke a kasa" Dariya ta danyi, ba kallon shi bane batason yi, kunya take ji, yayi mata kyau na gaske, idan bai sani ba. "Hindu..." Ya kira can kasan makoshi, saboda ganinta ya birkita mishi lissafi gabaki daya. Ba karamin kokari yayi ba wajen kokawa da zuciyar shi ganin bai rungumeta a cikin harabar gidan su ba. Yanzun ma kokari yakeyi na ganin bai kamo ko da hannunta da take ta wasa da wayarta da shi bane ya rike a cikin na shi. A hankali ta dago kai tana sauke idanuwanta cikin na shi, amman yanayin da take gani a cikin su ya sakata sauke nata babu shiri. Numfashi ya sauke yana runtsa idanuwan shi hadi da bude su a kanta "Me yasa duk wanda yai miki magana sai kin amsa shi a Instagram?" Ya tambaya da wani yanayi a muryar shi yana kuma tsareta da idanuwan shi, tambayar tayi mata bazata, Hamza kuma amsarta yake jira, har ranshi yake jin wani irin kishin yaga garadan banzan nan suna mata magana. Bayaso sam, ba wai soyayya suke ko wani abun ba, amman yanajin tashi ce shi kadai, har kuma ranar da zai daina jin hakan, bayason kowanne namiji a kusa dashi, shisa sam bayabin mace sau biyu, saboda ba zai taba iya rabata da wani ba, yanada wannan kishin, ballantana kuma Hindu da ta sami waje tayi kane-kane a rayuwar shi. "Haka kawai" Ta amsa dan batasan me ya kamata tace mishi ba "Bana so, bana so kina magana da su" Ya furta cike da ikon da ya bata mamaki, a gefe daya kuma yana mata dadi, dan ya daga mata burin da take da shi a kan shi, a cikin muryar shi take son karantar kamar kishi yake son nunawa. Dan murmushi tayi "Ki kalle ni Hindu... Da gaske nakeyi bana so, ki daina magana da su" Kai ta jinjina mishi, ya sauke numfashi, kafin yace "Nagode..." Hadi da mika mata hannun shi, bataga komai da take rike dashi ba sai wayarta, dan daga mishi wayar tayi cike da alamar tambaya, ya jinjina mata kai, daga mukulli ta cire sannan ta mika mishi, Instagram dinta ya shiga yana goge hoton da ta saka jiya, baka ganin komai sai fuskarta da hular da take kanta, ta saka da caption din 'Work, work, work'. Sai dai alamun bacci da gajiyar da take cike da idanuwanta yasa tayi mishi wani irin kyau kamar ya lasheta. Tarin mazan da suke kasan comment section dinta yasa ya tabbatar shi kadai yaga tayi kyan ba. Hindu kuwa tsayawa tayi tana kallon ikon Allah, dan Hamza ya wuce Mijin Novel, duk yanda take hasaso mazajen, shi yana nuna mata kyawun shine kawai yayi dai-dai da nasu, amman ya fisu rikici da baudadden halayya. Kawai shi ba miskili bane, ba kuma shuru-shuru bane. Yana magana sosai sosai, duk wani hoto da bayason wasu kartin banza suna gani, suna kalle mishi ita suna hadiyar miyau yabi ya goge. Tukunna ya mika mata wayar da fadin "Bana so, bansan me yasa kike yawan saka hotunan ki ba" Duba Instagram din tayi taga ya goge mata hotuna masu yawan gaske "Duk ka cire mun hotuna, wasu fa bani da su a wayar yanzun" Hindu ta fadi kamar zatayi kuka, akwai hotunan da ta dora ne ko da zata rasa wayar. Kafadu yadan daga mata yana hade fuska. Akan ta yake mamakin kan shi sosai, bai taba daukar wayar ko da cikin abokan shi ya goge musu wani abu ba, amman ikon da yakeji akan Hindu mai girma ne "Ki dinga turo mun kafin ki saka, kowanne wawa zai bude bakin shi yayi magana kinyi kyau. Bana so" Kallon shi tayi tana sauke numfashi, tama rasa abinda ya kamata tace mishi "Kina jina kikayi shiru" Ya sake fadi, kai ta iya daga mishi kawai, dan lamarin ne take ganin yafi karfinta. "Thank you" Ya furta yana kai hannun shi ya dan murza goshin shi, kafin ya sauke shi yana kamo na Hindu da zuciyarta tayi wani irin tsalle kamar zata faso kirjinta ta fito, kar wani ya fito yagan su, ko wani ya shigo yagan su "Na cika rigima ko?" Ya fadi yana lankwasa yatsun hannunta hadi da sake budesu ya hada cikin nashi ya dumtsa, kafin ya sauke idanuwan shi cikin nata da yake ganin bayanannen tsoro a cikin su, kome tayi kara birkita mishi lissafi takeyi "Haka zakiyi ta hakuri dani" Ya fadi muryar shi can kasan makoshi. Hannunta take son zamewa daga cikin nashi, so take tace ya sakar mata hannu kar wani ya fito, amman sam ta kasa. Bakinta yayi mata wani irin nauyi, kuma kallon da yake mata batajin zata iya tabuka wani abin kirki, da kan shi ya sakar mata hannu bayan yadan dumtsa shi, hadi da sauke numfashi yana mikewa, da idanuwa Hindu ta bishi, motar ya bude ya mike hannu yana dauko agogon daya siya wajen Mansura. A status dinta yaga ta dora, yayi mishi kyau sosai. Bata tsare shi da tambayar wa zai bama ba, dan tasan halin shi da kyauta. Dawowa yayi ya zauna, yana jin dadin samun wani dalilin da zai rike hannunta. Agogon ya fara kwancewa sannan ya kama hannunta yana dago shi, ya daura mata agogon, sai yaga hannun yayi mishi kyau. Yana ganin agogon ya hango shi cikin hannunta. Itama dago da hannun tayi, zuciyarta ta shiga wani yanayi da ba zata iya misaltawa ba "Nagode..." Ta furta a hankali, kai kawai Hamza ya iya daga mata, yanajin dadin sallar isha'i da yaji an fara kira "An kira sallah" Ya furta yana saka Hindu ware mishi idanuwa kafin ta shagwabe fuska "Tafiya zakayi ko?" Ta bukata tanajin kewar shi na danneta tun kafin ya tafin "Ki kasheni kawai, Ki kasheni" Ya fadi cikin yaran fulatanci yana sakata dakuna mishi fuska cike da rashin fahimta "Zan dawo ai, in kina da lokaci gobe zanzo muje muci abincin rana tare" Kai ta jinjina mishi, a cikin kanta tana tunanin lakcocin da take dasu goben. Hamza daya mike yana katse mata tunanin da takeyi "Da gaske tafiya zakayi ko?" Tai maganar cikin muryar da ta saka shi son sumbatarta, amman hannunta ya rike ta fara zare mishi idanuwa kamar yana zare mata rai, zai dauke shi lokaci mai tsayi kafin yazo wannan matakin, lokacin da bayajin yana da hakurin jiran shi, saboda yanda komai tayi yake kara kwadaita mishi ita. "Hindu so kike ki hanani tafiya ko?" Yar dariya tayi tana girgiza mishi kai "Zan ganki gobe In shaa Allah" Mikewa tayi itama, kawai saiya tsinci kan shi da sake kamo hannunta, yana share tsoron da yake gani a cikin idanuwanta, hannun yakai yana goga shi akan fuskar shi, kafin ya sumbaci cikin tafin hannunta "Bye..." Ya iya furtawa yana sakar mata hannun da taji yayi wani irin nauyi. Harya shiga mota ta kasa cewa komai, tana kallo yayi baya da motar shi yana fita daga gidan, juyawa tayi, duk da bataji alamar akwai wani a bayanta ba. Sai take jin kamar anga abinda tayi, kamar wani yaga hannunta a fuskar Hamza, zuciyarta cike fal da tsoro ta samu ta dauki kujerun ta hade su waje daya. Anan tabar su ta dauki plate din da ruwan da bai shaba ta shige gida, zuwa kitchen din Mama tayi ta ajiye mata plate, ta mayar da ruwan mazaunin shi. Sannan ta wuce bangaren su tana sakun Khadee a zaune "Shikuma menene laifin shi? Gajere ne? Ko katon hanci?" Khadee ta tambaya cike da zolaya, zagayawa Hindu tayi ta zauna kan kujera, bata cikin yanayin da zata biyewa tsokanar Khadee din, yanayinta yasa Khadee fadin "Lafiya? Me ya faru?" Kallon Khadee tayi da wani irin yanayi a fuskarta tace "Ina son shi Khadee..." Ware idanuwa Khadee tayi, ita kanta Hindu mamakin kalaman takeyi, amman daga zuciyarta suka fito, mikewa tayi "Ke dai ki mun addu'a. Allah ya tabbatar mun" Khadee da kallon mamaki take bin Hindu harta shige daki tana barinta a wajen, da tunanin ko dai wani dan wasan fim dinne Allah ya jeho Najeriya suka hadu da Hindun. * A gidan su ya kwana, duk da bai shiga da wuri ba sai wajen sha daya na dare. Yanzun kuma karfe tara harya gama shirin shi, ya fito falo yana samun Anna da Auta a zaune "Hamma na ganka rannan... Kai da wata ta wajen Byblos... Mantawa nayi in fada maka" Wani kallo ya watsa mata "Uban ki kike a wajen? Kuma baki iya gaisuwa ba?" Yar dariya Auta tayi "Ina kwana... Allah da gaske na ganka. Ni Anna ta aikeni ai ranar, kafin inje in maka magana harka shiga mota" Numfashi Hamza ya sauke, yana jin idanuwan Anna a kan shi, amman yaki kallon ta, sai da tace "Wacece ita?" Dan kallon Anna yayi "Ni banma tuna ranar bafa Ann, bazai wuce abokan aiki ba" Ya fadi yana ganin yanda Anna bata yarda ba, amman ba zata fada mishi hakan bane kawai. "Ko ita ce? Ban ga fuskarta ba sosai" Auta tace tana saka Hamza watsa mata wani irin kallo da yasa ta fadin "Allah ya baka hakuri. Ni shirin makaranta zanyi daman" Ta karasa maganar tana tashi tabar dakin. Da idanuwa dai Anna take bin shi "Ban san sau nawa zanyi maka magana kan nutsuwa waje daya ba, kana da aiki me kyau. Na rasa abinda kake jira" Dakuna fuska Hamza yayi yana turo labban shi "Ni zan fita wajen aiki" Yai maganar yana nufar hanyar kofa, inda yaci karo da Appa dayai wa magana cikin harshen fulatanci, Appan na tambayar yanayin aikin Hamzan, shikuma yana amsa shi "Maganar aure nayi mishi shine zai fita yabar mun gidan" Dan juyawa Hamza yayi "Anna mana" Ya furta, yana wuce Appa ya fice daga gidan dan karma su hadu su biyun suna mishi maganar aure. Bai hango shi a wannan kejin ba dan nan kusa, babu wanda zai kulla mishi yarinyar mutane ya rasa yanda zaiyi da ita, haka kawai a takura shi a hana shi sakewa. Kullum dole ka koma waje daya ka dinga kwana, ba zai kwana a waje yanda yaga dama ba, saboda yayi aure. Bai shiryama wannan matsatsin rayuwar ba, kuma bai gama ginin shi ba, shine uzurin da yake amfani dashi wajen sakawa Anna tana saurara mishi da maganar auren. Yana fita daga gidan ya tsinci kan shi da kiran wayar Hindu, ko muryarta yaji. Ga mamakin shi, kashewa yaji tayi, sai ga text tayi mishi "Ina aji" Tana sake turo wani "Sha biyu da rabi zan fito, zan kiraja" Titi ya kalla, kafin yadan kalli wayar shi yana fara rubutu "Ok. Zan zo sai mu fita lokacin" Ya tura mata, tukunna ya nufi hanyar da zata kaishi gidan Fodio. Yana karasawa ya samu suna karyawa, waje ya samu ya zauna shima yana cin dankalin da kwai, hannu yakai zai dauki kofin yoghurt da yake gaban AbdulHafiz ya doke mishi hannu "Wallahi nayi brush" Hamza ya fadi, yana saka Fodio da Arafat kwashewa da dariya "Brush shine abinda zai tsarkake maka bakin ka?" AbdulHafiz ya bukata yana daukar kofin shi ya rike a hannu, tuntuni ya gaya musu ya daina hada irin wannan abubuwan da su, ya siyo kofina daban yana kaiwa dakin shi "To ni ina ma naje?" Hamza ya tambaya yana dorawa da "Dan Allah kabani in kurba" Fodio ne ya sakeyin dariya, fadan AbdulHafiz din da Hamza baya gajiyawa wajen saka shi nishadi "Karbi..." Arafat ya fadi yana mika mishi kofin da yake hannun shi, lekawa Hamza yayi "Kai ni bana shan tea dalla" Bude baki Arafat yayi cike da mamaki, kafin ya jinjina kai yana furta "Laifina ne da nayi maka tayi" Banza Hamza yayi yana kyale shi, Yoghurt din ce ranshi ya biya "Ido guba AbdulHafiz, ba kyau wallahi" Ko inda yake AbdulHafiz bai kalla ba, yasan ba bashi zaiyi ba, saida yasha fiye da rabi tukunna ya tura ma Hamza kofin yana fadin "Dan Allah Arafat ka tashi, yanzun yaushe zamu shiga Kano har mu gama mu sake kamo hanya? Bafa naso mu kwana" Kofin shayin Arafat ya daga yana shanye na ciki, hadi da maida numfashi kafin ya mike "Ba zaka bar mutum abinci ya narke mishi ba. Kaya fa kawai zan sake" Harar shi AbdulHafiz yayi "Daka wuce ai da yanzun ka sake kayan... Ka zauna mayar mun da magana" Wucewar Arafat din yayi kuwa. "Ko in shirya mu tafi tare?" Fodio ya tambaya yana daga hannun shi ya kare fuskar shi "Hararata yake ko?" Ya tambayi Hamza daya daga mishi kai yana dariya "Wanne wulakanci ne wannan? Sai ka tashi ai" Da sauri Fodio ya mike yana wucewa daki dan ya watsa ruwa, idanuwan shi AbdulHafiz ya tsayar kan Hamza "Kai ba zakaje ba?" Kai Hamza ya girgiza mishi, ai yaji suna maganar zuwan tun jiya da rana, ya riga ya saka ma ran shi ganin Hindu yau. Ko ya bisu tunaninta damun shi zaiyi, gara dai yaganta din "Kuje abinku" Dan kallon shi AbdulHafiz yayi, yasan Hamza baya wuce tayin yawo, ko marar muhimmanci, balle kuma yanzun da aikine zai kaisu, kuma su dukan su, dan zasu biya su dauki Abdallah. Shi kadai zasu bari, yasan akwai dalilin da yasa ba zaije din ba "Ka shiga uku AbdulHafiz, ka tambayeni dalili mana, nasan kana so ka tambaya, ina jin idanuwanka na mun rami a bayan kaina..." Hamza yai maganar da wani yanayi tattare da muryar shi. Shiru AbdulHafiz din yayi, idan Hamzan na so yaji zai gaya mishi, ba zai fara saka hancin shi cikin abinda bai shafe shi ba "Nabila na da aiki" Hamza ya fadi yana saka AbdulHafiz fadin "Jibi yanda kake kiran sunanta gatsau dan Allah" Dariya Hamzan yayi "Kana jina ashe, kayi banza ka kyaleni" Shirun AbdulHafiz ya sakeyi mishi, har su Fodio suka fito suka wuce, Hamza yana karasa cinyewa nan ya tsallake yana barin kwanonin, zai tabbatar sanda zasu dawo baya gidan, ballanta AbdulHafiz ya sauke mishi fadan ba zai iya gyara waje ba. Kwalabe biyu ya dauka na vodka, duk da yasan yayi safiya ya bulbula ma cikin shi abu mai karfi haka, sai dai ita kadai ce zata taimaki yanayin da yake ciki, rabin kwalba yasha yana jin kan shi ya fara nauyi, hakura yayi ya kwanta, sai da ya saita alarm din wayar shi zuwa sha biyu da rabi, tukunna ya kwanta, yana lumshe idanuwan shi yabar baccin da yake son daukar shi yin aikin shi. * Karamin tsaki yake ja a mota, yana tuqi kamar zai tashi sama, kwata-kwata baiji karar alarm din wayar ba, sai bayan ya tashi wajen daya da kwata, sannan ya kula wayar a silent take gabaki daya. Yaga Hindu ta kira shi har sau biyu, ruwa ya watsa a gaggauce yana sake kaya ya fita. A hanya ya tsaya ya siya mata shawarma da kaji, sai lemuka, yasan ko yaushe in dai tana makaranta to zaiji tana tare da Hauwa, shisa yayi ledoji biyu. Yana shiga makarantar ya samu waje yayi parking, tukunna ya kira wayarta, bugun farko ta dauka "Dan Allah karkice komai, kiyi hakuri, wallahi bacci nayi, wayar kuma tana silent, ki fito ina wajen parking din motoci..." Hamza ya fadi muryar shi cike da ban hakuri, batace komai ba, shima wayar ya sauke yana jin babu dadi, saba alkawari ba sabon shi bane ba, balle shi yace ta jira shi zaizo. Ji yayi an kwankwasa motar, hakan yasa shi mika hannu ya bude mata, kai ta leqo tana mishi murmushin daya kasa mayar mata "Kiyi hakuri..." Ya furta kamar zai mata kuka, dariyar ta sakeyi tana shiga motar ta zauna. "Ki rufo kofar akwai rana" Hamza ya fadi, dan baima kashe motar ba, saboda AC din. Batayi musu ba ta rufo mishi murfin, sai take jinta wani iri saboda gilasan gabaki daya a rufe suke, kuma motocin duk da take ganin shi dasu tinted ne. "Ya kike?" Ya fadi yana yawata idanuwan shi akanta, yana ganin gajiyar da take fuskarta, yasan kuma karatune, ga ranar da ake kwallawa. Haka kawai yaji bayason ta koma cikin zafi "Alhamdulillah.... Da baka zo bama" Idanuwan shi ya kafe ta dasu "Baki so ganina ba kenan?" Da sauri ta girgiza mishi kai "Aa wallahi, ba haka nake nufi ba, da kayi baccin ka dai" Ledojin da suke ajiye a gefen shi ya dauko yana mika mata "Bansan ko kunci wani abu ba, ke da Hauwa... Bari kar in rike miki sauran lokacin cin abincin" Murmushi tayi, suna ma masallaci ita da Hauwa din, sanda ya kiratane suke tunanin zuwa suci abinci, dukkan su a gajiye suke. Hannu ta saka ta karbi ledojin tana fadin "Mungode sosai" Kai ya jinjina mata, yana kwance seatbelt din da yake daure a jikin shi, kafin tayi wani kwakkwaran motsi ya gyara zaman shi, bata san me ya faru ba, ba zatace ga yanda akayi ba, sai jinta tayi gabaki daya a jikin shi ya rungumeta hadi da fadin "Yau nayi laifi, dan Allah kiyi hakuri" Duka da rungumar da sakinta bai wuce minti daya ba, amman wani zazzabi taji ya saukar mata, da kan shi Hamza ya bude bangaren shi ya fita, ya zagaya yana bude mata nata bangaren, kafafuwanta ta janyo dakyar tana dire su a kasa tukunna ta fita daga motar. "Ki kula da kanki dan Allah" Ya furta, kai kawai ta iya daga mishi, tana jin kamshin turarukan shi da suka manne mata, dakyar take daga kafafunta tana takawa ta nufi hanyar da zata kaita masallacin da take tunanin shiga saboda zunubin da takeji a jikinta. Hamza kuwa daya koma motar yana rufe murfin, kan shi ya hada da abin tuqin yana maida numfashi, baisa ya akayi ba shima, kawai ji yayi idan bai riketa ba komai zai iya faruwa, yanajin bugun da zuciyar shi takeyi a cikin kirjin shi, numfashi kawai yake mayarwa kamar wanda yayi gudu. Baisan abinda yake damun shi ba, yasan yanda yake akan mata, amman abinda yakeji akan Hindu yayi yawan da ya fara bashi tsoro, yakai mintina goma anan zaune cikin motar, kafin ya iya tashin motar, yana juyata ya fita, a bakin gate din ya tsaya yana ba masu gadin dan katin shigar da suka bashi, hadi da dubu biyu, yaja gilashin motar shi, bai damu da godiyar da suke ta faman yi mishi ba, da fatan sauka lafiya. Garama wannan, dan yana bukatar shi a halin da yake ciki. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 5 A karo na farko a rayuwarta da taji bata dokin hidimar biki, yan gidan kansu mamakin rashin kazarniyarta da rawar kan da ta saba duk idan taji maganar bikin yan uwa, balle kuma wannan da akeyi a cikin gidan su, abinda basu sani ba shine littafi hausa ta samu daya dauke mata hankali daga kan komai. Tun da ta kunna waya tayi mamaki sosai da bataga sakkonin Elias ba, da hannunta ta goge 2go din daya gama fita daga ranta. Banda kallo babu abinda tafi yi da wayar, tunda bata da wanda zatayi hira dashi sosai a whatsapp sai kawayenta da kusan kullum suna tare a makaranta, hirar da zasuyi a gida bata da wani yawa. Sai yanzun data samu littafin Hausar da Dimples ta tura mata. 'Tana Tare Da Ni' na Miemiebee. Gabaki daya littafin ya gama tafiya da ita, Anas yayi dai-dai da kalar mijin mafarkin ta, bata tsammani ko a cikin fina-finan da take kallo, daga na Indiya harna kasar Korea ta taba cin karo da jarumin da taga yayi dai-dai da tsarinta irin shi. Duk da ba ganin wannan tayi ba, amman an haska mata shi ta yanda zuciyarta ta zayyana mata mutum sak, fari, dogo, mai faffadan kirjin da ba zata taba gajiya da kwanciya luf a cikin shi ba, gashin kanshi bakine wuluk, a kwance luf-luf kamar na mutanen kasashen ketare, ga fatar shi nada wani irin haske kamar gilashi saboda rashin wani kurji ko tabo a jikin shi, labban Anas ruwan hodane da zaka iya rantsewa yana shafa musu janbaki. Babu abinda yafi tafiya da imaninta a tare dashi irin idanuwan shi,blue ne masu hasken da zata iya misaltawa da sararin samaniya. Gashi miskili ajin gaske, magana ma sai kayi da gaske zakaji ya furtata, ajin shi wani irin ajine da yake wahalar samu, sai da Fannah ta shigo rayuwar shi. Ta hargitsa komai tana canza shi, kalar son da yake mata, yanda ta sake shi, kuma ita kadai take ganin canjin yayi dai-dai da ra'ayin Hindu. Anas ne duk ajin shi da jiji da kai yake kuka wiwi tamkar yaro dan wata biyu a gaban Fannah. Duk idan yace 'Flower' Sunan da yake kiranta dashi sai Hindu taji wani abu ya tsirga mata tun daga tsakiyar kanta zuwa dan yatsar kafarta saboda shauqi. Da ace Anas zai fito daga littafin ya tsaya a gabanta ya furta mata kalmar so, zata amsa shi batare da wata gargada ba, ko baice yana sonta bama in dai zai aureta bata da wata matsala, dan in suka zauna zasuyi ta fada daga farko, amman tasan zasu shirya daga baya, zai fara son ta, wahalar abin ta fito daga wanka ayi dai-daito ya shigo dakin daga ita sai towel, ba zata jira tsautsayi ya kwance towel din ba, da kanta zata san yanda zatayi ya subuce. Sanda zai hargitse ta manne a zuciyar shi babu wanda zaiji labari. Zuwa yanzun Hindu tayi wani irin zurfi cikin tunani, sam bataji maganar da Anty take tayi mata ba, sai da ta fisge wayar hannunta tana dorawa da "Dan ubanki baki da wani aiki yanzun a rayuwar ki saina waya? Kinsan Allah na kusa haramta miki wannan shegiyar wayar tunda naga alama ke baki da hankali..." Da hanzari cikin wata irin faduwar gaba Hindu take kallon Anty "Dan Allah Anty kiyi hakuri, banji bane Wallahi" Harara Anty ta watsa mata "Daman ya za ayi kiji, kin saka kanwar uwarki a gaba... Mutane na can kinzo nan kin lafe kina danna waya sai tambayarki akeyi" Anty ta karasa maganar tana dorawa da "Ki tashi kibar mun daki ni..." Mikewa Hindu tayi tana kokarin bata nuna bacin ran da take ciki a fuskarta ba, wayarta Anty ta miko mata "Saura in shigo inga kina danna waya, idan na karba sai an gama hidimar bikin nan tas zan baki" Karba Hindu tayi tana wucewa dakinsu ta saka wayar a caji dan tayi kasa sosai, mukulli ta dauka ta kulle dakin, shisa bata ganin laifin kawarta Aina'u da suke kira da Dimples da take cewa bata son mutane, saboda suna da bala'in sa ido da takurama yan uwan su mutane. In ba takura ba me zatayi musu, kamu ne an riga anyi, sunje sunyi kunshi da kitso, gobe Asabar daurin aure za'ayi tare da walima sai akai amarya tunda anan garin Kaduna zasu zauna. Bata ga me zataje tayi musu ba da suke faman tambayarta, inba salon son su shiga rayuwar ta ba. Da sallama ta shiga bangaren Mama tana wucewa dakin su Halima da take jiyo hayaniyar hirar su, ta leka da sallama, Halima ce da kawayenta, sai wasu cikin yan uwansu da kusan sa'annin Halima din ne, wasu kuma duk da auren su ma harda yara daya zuwa biyu. Murmushi ta dora saman fuskarta tana gaishe dasu, kafin ta juya dan ba wajen zamanta bane, su Khadee ta nemo, suna zaune da yan uwan su, yaran kannen Baba da kuma na Mama da Yayyenta, sun kacame sunata hira. "Ke banza ina kika shiga tun dazun anayi babu ke?" Mimi ta fadi tana matsama Hindu ta zauna a kusa da ita, hadi da leqa wayarta tana ganin hoton Halima da Yaa Ahmadi, ya leko wajen kamun na yan mintoci akai musu hotuna "Wallahi sunyi kyau ba kadan ba" Mimi ta fadi tana mikawa Hindu wayar dan taga hoton sosai, zata iya rantsewa Halima har wani kyalli-kyalli takeyi da batasan ya akayi ba, wani irin kyau take mata tun satin bikin naban mamaki, ita batayi haske kamar su ba, ta biyo duhun Mama, amman tana jerin masu kyawun gidan "Shisa auren namiji me kyau ma girma ne" Hindun ta fadi batare da tasan maganar ta fito fili ba "Kibari kawai yar uwa, namiji me kyau fa duniya ne, ba ka auri mummuna ya bata maka hotunan biki ba" Saddika ta amshe zancen, dariya sukayi su dukansu, Khadee ta kalle da murmushi a fuskarta "Allah ya shiryaku Wallahi" Hannu Hamida ta daga mata "Amin. Amman ki rantse har kasan ranki bakya son auren me kyau? Mijin da ba zaki boyema kawayenki ba" Wannan karin Hindu ce take dariya sosai, dan an tabo mata inda take so, shisa wani lokacin tana son yan uwanta na bangaren Baba saboda wayewar su, ta dauka zasuce wani abu da tayi maganar Miji me kyau, ashe duk sun gane kan al'amarin. A wannan zamanin me akeyi da namiji mummuna. Khadee kai kawai ta girgiza musu, tana sa Hamida juya idanuwanta "Kinji zancen ko? Hajiyata Allah ya bamu masu kyau" Kai Mimi ta jinjina "Masu kudi kuma" Hindu na saurin amsawa da "Amin thumma amin" Fati da take gefe sai lokacin ta tsoma musu baki "Banji kunce mafi alkhairi ba" Tana sa Hindu amsa ta da "Wannan ai itace karshe, in dai yana da kudi, yana da kyau... Ai da alkhairin shi yazo" Sosai suka cigaba da hirarsu akan maza masu kyau da irin yanda zasu zaba su darje. Hindu ta jima tana mamakin dalilin da zaisa ka daga hannu wajen rokon Allah miji ka tsaya a iya 'mafi alkhairi'. A ganinta hakan babbar wauta ce, ka bude bakinka ka zayyana kalar shi tun daga sama har kasa, kai a zuciyarka kasan kalar mai alkhairin da kake so. Tun da ta fara hankali, ta fara fahimtar akwai wani abu soyayya da kuma aure take addu'ar namiji me kyau mai kudi, ita shine mafi alkhairi a duniyarta. Indai yana da abubuwan nan biyu babu wani abu da zata nema. Yanzun ne ma addu'ar kan canza lokaci zuwa lokaci. Ganin lokacin sallar isha'i yayi yasa da yawansu tashi. Hindu bangaren su ta koma, duk da daga farko bataso fitowar ba, taji dadin hirar su, ta kuma ji dadi da Anty tasa ta ajiye waya taje. Tana idarwa ta daga hannuwanta sama, bayan tayiwa Baba addu'a da Anty da yan uwanta, tata addu'ar ta fara, neman lahira da mutuwa me sauki dan tana firgitata, tukunna ta fara fadin 'Allah Kai Kace mu roke Ka zaka amsa mana, Allah kabani miji kyakkyawa, dogo, ko bakine ina so, Allah idanuwan shi su zama irin na Anas din Tana tare da ni. Mai kudin da zai kaini hajji da umra, ya sai mun mota ya bani kyautar gida. Miskili na gaske, mai aji, wanda zai so ni fiye da komai a rayuwar shi. Allah kabani yara masu kama dashi sak' Maimaitawa tayi sau bakwai tukunna ta rufe da Salatin Annabi SAW dan addu'ar tayi saurin zuwa. Mikewa tayi tana komawa bangaren Mama san suci gaba da hirarsu, tasan in sun gama wasu zasu dawo nan bangaren Antyn su kwana, kamar yanda akayi jiya. * Washegari da sukaje wajen kai amarya, Hindu taji dadin hirar novel din da suka dingayi ita da Mimi, dan ta saka ta bude facebook account, ta kuma shigar da ita groups da yawa da zata dinga samun litattafan hausar a saukake. Suka kuma yi musayar lamba da alkawarin Mimi zata dinga turo mata litattafai masu dadi. Gidan Halima yayi mata kyau duk da ba wani girma gare shi ba, daki biyune, amman filat ne yasha tiyal masu daukar ido. Ga Baba yayi kokari matuka wajen zuba mata kayan alfarma. Kyawun da gida yayima Hindu bai hanata rokon wanda ya linkashi girma kamar sau goma ba, tafi son gidanta ya kasance da bene, yanda mijin inya daukota zai sauko bene da ita. Ba irin wannan dan gidan ba, tana kuma so ta shiga wannan falon yau, ta shiga wancen gobe. Burinta me girma ne, ta daina maganar ko da Khadija saboda yanda take mata kallon marar hankali wasu lokuttan, ita kuma bata so ko kadan, dan ra'ayin su ya banbanta baya nufin ta dinga kallonta kamar ba zata sami abinda take buri ba. Ko babu komai, hausawa kance in da rai da rabo. Kusan Hindu zatace da duk ranar da take wucewa da yanda burinta yake kara girma, ta dauka da tagama sakandire ta samu damar da take bukata tayin zance da samari zata tara su kamar layin markade, sai ya zamana burinta ya katange hakan, gashi yanzun ita da kanta tanajin canjin da tayi a jikinta na bayyanar cikar yan matanci. Tunda Khadee da kanta kan yabata idan tayi kwalliya lokaci zuwa lokaci ta fara yarda da tana da kyau. Ta dibo hasken fatar Baba, a dakinsu kaf itace tayi dogon hanci irin na Mama. Ga bakinta dai-dai fuskarta, tana da matsakaicin tsayi, tana kuma da kyawun da zaka fahimta a kallo daya. Jamb tayi mata rashin darajar da kan faru da dalibai masu burin zuwa jami'a. Sosai take hasaso kanta a KASU kafin jamb tayi mata yankan kauna. Gashi Baba baya bari ka zauna, ya tsani zaman shekara dayar da zakayi a gida baka wani abu, zaice ko FCE ce ka farayi, karatu karatune, duk ta inda dama ta baka ka fara, a hankali in kayi hakuri zaka kai inda kake so. Dari da saba'in da hudu taci, ya kai yanda Kaduna Polytechnic suke so, amman tayi sashin kimiya da fasaha da akafi sani da Science ne a sakandire. In ka tambayeta dalilin da yasa ta zabe shi ba zata fadi guda daya ba. Ba zaka kirata mai kokari ba, ba kuma zaka sakata a layin marassa kokari ba, ta kasance a tsaka-tsakiya, inka raba ajinsu gida uku, tana cikin kaso na tsakiya, sakamakonta baya wuce C ko da can, da wahalar gaske kaga B, tana cikin mutanen da turawa kan kira 'average' ta fannin karatu. Har ranta aikin likitanci bai taba burgeta ba, saboda shi Zaid yake karanta, kusan duka gidan daliban Science ne, asalima tana son karantar abu daban da wanda kowa a gidan yake karanta, karshen abinda take so shine a fara gwada kokarinta da wani a cikin gidan. Ko kuma azo ana mata wani iyayi na daban, sai dai ta duba ta rasa kwas din daya kamata ta karanta, ta kasance tana matukar sha'awar zane-zane tun da karancin shekaru, duk litattafanta baka rabasu da zane, tayi shawara da Baba kan ko zata koma Art ne, saiya bata shawara mai zai hana ta koma fannin Technology saita karanci Architecture fannin zanen taswirar gidaje, amman kwas ne da yake matukar bukatar jajircewa dan ba sosai ake samun mata a fannin ba. Ko da bata so ma zatayi tunda Baba ya nuna yana sha'awar kwas din, a yanayin fuskar shi taga alfahari a kwance data yanke shawarar yin kwas din. Baima saka kowa a gidan ba, da shi da ita suka dinga zuwa hidimar siyan form da sauran duk wani abu da ake bukata. Cikin ikon Allah ta sami gurbin karatu a Kadpoly, sai taji dadin kasancewar babu nisa da gida, in taso ma da kafarta zata iya takawa. A haka Hindu ta fara karatun ta a shekarar 2014. A lokacin ne komai ya fara canza mata. Zatayi karya idan tace Architecture baizo mata da bazata ba, sam duk wahalar shi ta wuce yanda Baba yake fada mata. Amman kuma tana jin dadin yanda mutane kanyi mamaki in sukaji abinda take karanta, sukan kuma jinjina mata, hakan ba karamin dadi yake mata ba. Da gaskiyar Baba, ajin su bakwai ne kacal mata, sauran duk maza ne. Har zuwa yanzun da suke a zangon su na farko bakowa take magana dashi ba, asalima kullum da earpiece manne a kunnuwanta dan kar ayi mata magana, kawarta daya duk ajin itace Hauwa, a haduwa ta farko zaka dauka Hauwa nada bala'in girman kai, saboda kullum fuskarta a hade take, saika zauna da ita zaka gane saukin kan da take dashi. Kusan duk inda zasuyi a cikin makaranta tare suke zuwa, hatta da cin abinci, kafin wani lokaci sunyi wata irin shakuwa da zata baka mamaki. A bakin Malamai Hindu ta fara jin Hamza Abu Abbas, dalibin da ya kafa tarihin da ba'a taba kafashi a makarantar ba tunda aka bude department din, haka kawai ta tsinci kanta da son sanin kowaye shi, sosai take jin son sanin Hamza Abu Abbas din da kowanne Malami yake musu kwatance dashi. Amman wanda zata tambaya a ajinsu duk bakine, yanda taji labarin shi a bakunan Malamai, haka suma sukaji. Ta gwada yiwa Hauwa zancen a shekararsu ta farko, ta tabe baki tana dan daga mata kafadu cikin halinta idan bata dauki abu da muhimmanci ba "Koma waye nikam harya gundure ni, bana so ana maimaita mun abu daya kullum, Hamzan nan sun mayar dashi kamar wani abin bauta" Murmushi Hindu tayi, da tunanin Hamza lokaci zuwa lokaci ta kammala shekararta ta farko ta shiga NDII, tasan ko hasken Hamza ba zata kamo ba a wajen karatu balle ta kwatanta, inda take yanzun yayi mata, kawai tana son sanin ya yake, ko kadan ne taga kamannin shi, taso tambayar yan HNDII dinsu da suka fita, kawai batasan yanda zata fara kawance da wani a cikin su bane a lokacin, da ko mai hoton Hamza tagani. Har Khadee tasan labarin Hamza a bakin Hindun, tunda kaf abinda ya faru a makaranta inta dawo saita bata labari. Anty kanta takan ji zancen Hamza, Hindu na mita wata rana idan sunyi abu an kushe. Da wani yace mata zata so Kadpoly har haka zata karyata, amman zuwa yanzun da project dinsu na kammala NDII yake ta matsowa sai take jin tana son taci gaba a makarantar. Maganar Samari kuwa babu kalar da bata haduwa dasu, na farko basuyi mata ba daga shigarsu zuwa abin hawansu ballantana harta saurare su, na biyu kuma ko kadan bata da cikakken lokaci, kallo ma saitayi wata bata gama film daya ba, gara dan karatun Hausan takanyi shi a manhajar Wattpad data gano yanzun, tunda tayi wayar hannu ta Android. Zuciyarta da wani irin nauyi take takawa zuwa gida, duk gajiyar da tayi a yammacin ranar bai sa ta nemi abin hawa ba, kafin ta tashi daga makaranta sukayi hira da Dimples ta WhatsApp tana bata labarin saurayinta Faisal da ake ma inkiya da Fash, harta turo mata hoton shi, gaye ne na kwatance, duk da Hindu tayi mata murna, a can kasan zuciyarta taji wani iri, ga kawayenta duk sun sami Samari tsayayyu, dan Biebee har ana maganar kawo kudin gaisuwarta da Usman, sai itace har yanzun wanda zai kwanta mata a rai ma bata gani ba, ballantana ayi wata tsayayyar magana. Zatayi karya idan tace abin baya damunta, zuwa yanzun sai take ganin kamar dole ta sassauta burinta, kamar da wahala ta sami mijin da take mafarki, tafiya take kan titin da zai kaita gidansu, amman hankalinta ma sam baya jikinta, koya ta rufe idanuwanta ta bude su sai taga zanukan Hamza na zangon karshe da yayi sun gilma mata, dan suna gama magana da Dimples ta tsinci kanta a hanyar Data room, ta nemi ganin zanukan shi, aka kuma dauko mata. Zuwa shekarar a cikin ajinsu, a ajin manyansu, a internet taga zanuka babu adadi, batasan me yasa nashi ya zamana daban ba. Hannu tasa tana shafar rubutun shi na cursive daya rubuta sunan shi dasu, cikin salon da zaka iya rantsewa da Allah ba hannu ne ya rubuta ba, babu kala ko daya a zanen shi, bakine, banda wajen sunayen da yayi amfani da maka ja da baka wajen yin design. Zanen kan shi kamar da injin aka buga. Lallai dole Malamai suyita magana a kan shi. Daga zanen shi tagane banbancin da yake dashi da sauran mutane, taji wani Malamamin su yace Hamzan ya sami gurbin karatu a South Africa, duk da bai tsallaka kasashen ketare ba, South Africa a wajen Nigeria take, akwai maza irin Hamza a duniya, akwai Maza irin Fash din Dimples, akwai irin Murtalan Hauwa, batasan me yasa ita ta kasa samun kalar nata namijin ba. Ranta a bace take jin shi, tana gab da gida taji wata mota a baya tana ta mata hon, bata juya ba duk da tasan da ita yake, abinda ya saba faruwa ne zai faru yau din ma, zata tsaya, shikuma zai fito daga motar, tun daga yanayin fuskar shi zai zamama bai mata ba, balle kuma ta tsaya ta karema yanayin shigar shi kallo, lokacinta zata bata kamar yanda ta saba, su kansu Samari zuwa yanzun ya kamata su gane ita din ba ajinsu bace ba, Hindu ba matar mummuna bace ba, matar me kyau ce, su daina binta, amman ba zasu tabayin wannan abin arziqin ba. Inda duk zata shiga sai an sami mutum daya ko biyu mummuna da zai bude bakin shi da sunan tayi mishi. Wata zuciyar ta saqa mata, ta tsaya, ta saurare shi, dan tsayawa tayi, kamar hakan yake jira yayi parking, babu laifi motar shi za'aje da ita ko shopping ne in ba'a shiga taron biki ba, a tunanin Hindu. Cikin hanzari ya fito yana yi mata murmushin data runtsa idanuwanta tana sake bude su "Guntu ne" Wani sashi na zuciyarta ya ayyana mata, duk da tsayin shi daga inda yake zaifi nata kadan, fuskar shi babu yabo babu fallasa, sai da ya ketaro yana karasowa kusa da ita taji yana warin ajiyayyen quli-quli. Sosai ranta ya kara baci, ta hade girar sama da ta kasa, ta rasa abinda yake damun wasu mazan da ba zasu saka turare ba, jibi irin motar daya fito daga ciki, da maza zasuji shawara da sun dinga karanta litaffafan Hausa, watakila idan sukaji yanda Mazan Novel suke tashin kamshi kamar waliyyai zasu fara neman turare. Haka mazan gidan su, basa wari, amman kuma batajin kamshin turaren su na kama waje bayan sun tashi. Fuskar shi ta kalla da take ta naso, inda za'a tsaya a tatse man dake fuskar zai soya wainar kwai "Hajiya..." Ya fadi yana wani dashe mata bakin dayasa hancin shi bajewa kan fuskar shi yana dishe dan kyawun da taga yayi mata "Sannun ka" Ta fadi a dakile tana karema kayan jikin shi kallo, wandone ya saka baki mai ratsin ja da fari, sai wata jar riga daga ciki, ya kawo kwat ruwan toka ya dora, sai irin hana sallah da take ganin tsofaffin inyamurai na sakawa a fina-finan kudu. Bai kara fita daga ranta ba sai da takai dubanta zuwa takalman kafar shi da sukayi mata kama da jirgin kwale-kwale. Sunyi budu-budu da kasa "Sai yaushe ne zan sami kalar saurayin da zai kwanta mun?" Tayi tambayar a zuciyarta, a fili tana jin kamar ta fashe da kukan bakin ciki, da ta sami saurayin har yaushe zata tsaya kula irin wannan "Na tsayar dake kan hanya ko? Kibani lambarki muyi magana" Wani irin kallo Hindu take mishi da yasa shi fadin "Nasan baki sanni ba, Sunana Badamasi, lakcara ne ni a KASU" Lumshe idanuwanta Hindu tayi, tana budesu cikin godiyar Allah da bai kaita KASU ba, indai haka lakcarorin su suke, gara da bataje ba. So takeyi ma tabar wajen kar ace saurayin da take mafarki yazo giftawa yaganta tsaye da Badamasi. Wayarta ta dago tana fadin "Ka gayamun taka lambar, ina sauri ne zan karasa gida" Cike da fara'a Badamasi ya gaya mata lambar shi, Hindu tayi kamar tana sakawa, tukunna ta dago kai da dan guntun murmushi tana fadin "Banda kati yanzun, ina karasawa gida zan kiraka...." Dan jim Badamasi yayi da kokwanto shimfide a fuskar shi, amman murmushin da Hindu tayi saiya dan bashi hope akan cewar zata kira din, yana juyawa ta zabga mishi harara "Allah kaci gaba da gina katangar karfe irin ta kurkukun kiri-kiri tsakanina da irin wannan bayin naka, Allah ka kawomun saurayi irin wanda nake so" Hindu take fadi kasa-kasa tana kara baza sauri, tasha kwanar da zatayi zagaye sosai kafin ta karasa gida dan kar Badamasi yayi tunanin biyo bayanta, duk da haka tanayi tana wai-waye harta shiga gida. * Godewa Allah takeyi da bata da assignment a ranar tunda satin jarabawarsu ta karshe ne zai kama, sun kuma yi presentation dinsu na karshe sai bayan jarabawa, a gajiye likis take jinta. Tunda sukaci abincin dare tana bangaren Mama ita da Khadee suna hira "Kinsan yau naga zanen Hamza... Inalillahi... Wallahi ban taba ganin zanika masu kyan nashi ba... Kinga rubutun?" Ta karashe tana cire wayarta daga key tana kokarin shiga gallery dan ta nuna ma Khadee hotunan zanen da ta dauka "Ai tunda kikaji Malamanku na maganar shi, duk yanda kike fadar kushen su kan ayyuka, kinsan ba karamin kwaro bane" Kai Hindu ta jinjina tana mikawa Khadee wayar "Kalli fa" Ware idanuwa Khadee tayi cike da mamakin ganin wai hannu ne yayi wannan zanen "Karki ce mun da hannu ne wannan" Dan murmushi Hindu ta tsinci kanta yi, cike da alfahari kamar tasan Hamzan, ta dangwala screen din wayar tana nuna ma Khadee sauran hotunan da fadin "Ai danma baki gansu a fili ba, rubutun kawai abin kallo ne" Kai Khadee ta jinjina tana mamaki matuka, sosai suke hirar Hamzan, kafin taje ta kwanta, haka kawai Hindu najin wani kusanci tare dashi da ba zata iya misaltawa ba, sai take tunanin ko yana wanne halin, ko zai taba dawowa Nigeria ma oho, ko sau daya zata so taga fuskar shi "Zai iya yiwuwa mummuna ne" Zuciyarta ta ayyana mata, tana sakata yin murmushi. Shafin twitter ta shiga dan ganin diramar dake wakana ta ranar, babu wani abu a TL din nata na nishadi sai ta sauka tana komawa facebook, zuciyarta taji ta doka da tunanin ta duba Hamza ko a facebook ne, da sauri taje search tana rubuta 'Hamza Abu Abbas' Jerin mutane wajen goma suka fito, na farkon da ta ga hoton profile din shi an rubuta ARC ta shiga. Tana kuwa bude ta ga description dinshi taqaitacce ne, inda yayi sakandire, Kadpoly, sai University of Johannesburg da take da tabbacin nan yake karatu yanzun. Zuciyarta na wata irin dokawa ta tura mishi da Friend request, kafin ta shiga wajen hotunan shi har wata zufa takeji tana karyo mata, hotuna ne sunfi 800+, gyara kwanciya tayi tana dubawa daya bayan daya, hotunan zanukane wanda akayi da hannu da kuma na kwamfuta, sai zanen da akafi kira da rough sketches a turance da su kansu suke a tsare. Hoto daya taci karo dashi na Hamza, yana tsaye ya juya baya, da riga mai hade da hula a a jikin shi, rigar mai dogon hannu, da alama hannuwan shi na cikin aljihun rigar ta gaba daga yanayin tsayuwar shi, rigar fara ce kal da bakin rubutu daga kasa an saka HAMZY_ da manyan baki. Dogone sosai, irin tsayin da take so, ji takeyi kamar tace mishi ya juyo taga fuskar shi. Komawa tayi tana duba maganganun dake kasan kowanne hoto daya saka wato comments, mutane nata yabawa da zanen nashi, cikin harshen turanci, harshen hausa, sai kuma yaren da ta kasa karantawa, amman babu ko godiya daya da yayi musu, like yake dannawa shima ba'a kowanne comment ba. Yanzun kam Hindu har a zuciyarta take jin ta fada abinda turawa kan kira da 'Obsession' akan Hamza. Sosai take son sanin komai da ya dangance shi, taje ta saka sunan shi a twitter bata ga ya fito ba, ta nema harta gaji, har yanda taga ya saka a bayan rigar shi ta saka, amman bata gani ba, ji take kamar kanta zai tarwatse saboda tunani, ta hasaso fuskoki sunfi kala hamsin tana dorawa a jikin hoton shi data hani a facebook, amman sai take ganin kamar bata dace dashi ba. Tunanin taje Instagram ta duba shine ya fado mata, ga wayarta da take nuna mata battery dinta saura biyu, generator dinsu ya sami matsala, kuma sunki kawo wutar dare yau. Data sani ta saka caji a makaranta. 'Hamza Abu Abbas' Ta saka, tana ganin wasu mutane sun fito da ta bubbude amman bata ganshi ba, bata tunanin yana cikin su, dan wasu ma larabawa ne. Sai ta sake duba 'HAMZY_' Shima bai fito ba, gyarawa tayi zuwa 'Hamzy_' Aikam sai gashi ya fito, da wannan hoton nashi na facebook a jikin profile din shi. Tana budewa taga tarin followers dinshi har dubu arba'in da yan kai, taga mintina biyu da suka wuce ya saka hoton da network ya hanashi ya bude mata da wuri, ga wayarta zata iya mutuwa gabaki daya. Budewa hoton yayi tana saka idanuwanta cikin na Hamza da yake kamar yana kallonta, zuciyarta nayo tsalle ta dawo makoshin ta, dai-dai lokacin da wayarta ta dauke...! 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 16 Tunda ya shiga gida, kayan jikin shi kawai ya sake, yana saka wando iya gwiwa sai wata riga mai dogon hannu hadi da hula ruwan madara. Yaja hular yana dorata saman kan shi, tukunna ya dauki wayar shi, earpiece ya duba ya hada a jikin wayar, ya maqala ma kunnuwan shi batare daya kunna komai ba, magana ce bayaso yayi da kowa, kuma akwai aikin da bayaso ya kwanar mishi, da bazai fita falon ba. Yana karasawa ya dauki system din shi daga kan tebirin da take yana jan cajar da take hade da system din ya koma kama cikin falon in da su Fodio suke zaune suna hira. System din ya kunna yana jira ta gama budewa gabaki daya, saiya tsinci kan shi da lulawa duniyar tunani, har lokacin yana kasa yarda da abinda ya faru "Appa aure zanyi, sunce in tura manya na" Shine maganar farko daya fara furtawa bayan sun gaisa da Appa din, sosai kuma yake karantar mamakin da yake shimfide a fuskar Appa "Aure?" Appa ya jinjina maganar yana dorawa da "Ma shaa Allah, Allah yasa albarka, sun fadi ranar da zamuje ayi maganar?" Kai ya tsinci kan shi da girgizawa Appa "Su saka mana ranar da zamuje sai ka fadamun" Kan ya sake jinjinawa, yana kasa furta wani abun "Hamza" Appa ya kira, duk da yana dadewa bai kira sunan shi kai tsaye haka ba, ba kunya bace ta dan fari, kawai Appa bai cika kiran sunayen mutane ba "Auren nan fa ba abu bane da zaka wayi gari kawai kace zakayi saboda kana da halin yi, ba kudin bane shiri, wannan yana daya daga cikin abubuwan da ake bukata, idan har a zuciyarka baka shirya ba, karka dauko yarinyar mutane, yau da gobe tafi karfin tunanin ka, duk yanda za'a gaya maka aure idan bayi kayi ba sam ba zaka fahimta ba" Cewar Appa yana dorawa da "Hakurin da kakeji anayi, shi kan shi akan wayi gari a neme shi a rasa, abubuwan da suke rike da aure sunfi karfin kudi, karka sakani zuwa karbo maka amanar da ba zaka iya rikewa ba" Idan akwai abinda yake bata ma Appa rai bai wuce yanda ake ma aure rikon sakainar kashi ba a yanzun, kwata-kwata daga Samarin har 'yan mata basu san menene auren ba sukeyin shi. Kusan ya zama gasa, wane yayi, bai kaini samun kudi ba, wane na bashi shekara biyu gashi yayi aure harda yaro, amman ni ina nan zaune. Sam suna mantawa da yanda tsarin rayuwa yake tafiya akan cikar lokaci. Sai ayi auren a kasa hakuri da yanda rashin dadi da jarabtar da take cikin shi lokutta da dama kan rinjayi jin dadin ciki. Shisa bai taba yiwa Hamza maganar yai aure ba, ko kuma ya tambaye shi yaushe zaiyi aure. Saboda yasan ba a samun kudin abin yake ba, idan har bai shirya a zuciyar shi ba, auren zai zo mishi a baibai. Yanzun ma sai yake karantar shakku a idanuwan Hamzan, shisa yayi mishi magana, yafi so ya zamana dari bisa dari ya tabbatar da ya shirya ma auren "Idan har akwai wani bangare na zuciyarka da bai natsu da maganar nan ba, ka hakura Hamza. Karkai gaggawa, aure ne, lokaci yake da shi kamar mutuwa, indai an rubuta maka yin shi, zai zo ya sameka, ba saika neme shi ba" Numfashi Hamza ya sauke, zai kuma yi karya idan yace maganganun Appa basu taba zuciyar shi ba, zai kuma yi karya idan yace ya shirya yin aure har a zuciyar shi, abu daya kawai ya shiryama a halin yanzun, bin duk wata hanya da take karkashin ikon shi dan ganin ba'a raba shi da Hindu ba, yana son ta, tunanin rabuwa da ita na wanzar da wani irin tsoro hadi da firgici a cikin zuciyar shi, balle kuma ya hasaso ta da wani da bashi ba, kan shi har sarawa yake saboda tashin hankali "Na shirya Appa" Ya furta da muryar shi can kasan makoshi, kai Appa ya jinjina mishi "Allah yasa hakan ne mafi alkhairi" Mikewar da Appa yaga Hamza yayine yasa shi sake fadin "Ka gayawa Annarka ne?" Kai Hamza ya girgiza mishi, yasan ya kamata yaje yayi ma Anna maganar, amman kuma a yanayin da yakeji, sam ba zai iya amsa duk wasu tambayoyi da yake da tabbacin Anna zata jero mishi ba "Akwai aikin da zan karasa Appa, gobe In shaa Allah sai in dawo in fada mata, kasan Anna" Murmushi Appa yayi cike da fahimta, yana sakeyi mishi addu'a, kafin ya wuce, dan yaji dadin samun Appa shi kadai a falon, shisa ya jashi bangaren shi, ta baya ya fice daga gidan. Ko gaisawa da Anna baije yayi ba, yasan Appa bazai ce mata komai ba. "Sai magana nake maka, Banza kawai" Arafat ya fadi yana dukan kafadar Hamzan daya sa hannu ya zare earpiece daya daga kunnen shi "Shine zaka cire mun kafada? Dan ubanka baka ga earpiece bane a kunne na?" Hamza ya karasa maganar yana kara hade fuska "Ina flash dina?" Arafat ya bukata "Ka duba cikin jakar system dina" Hamza ya amsa shi yana shirin mayar da earpiece din shi "Jakar ka na ba flash ko kai? Ka tashi ka dauko mun" Kai Hamza ya jinjina, yana mayar da earpiece din shi hadi da fadin "Ka zauna ka jirani in dauko maka" Kafin ya cire wayar shi daga key yana cigaba da dannawa, yanajin zagin da Arafat din yayi mishi kafin ya mike, bai damu bane ba. Lambar Hindu yake ta kira tunda ya baro wajen Appa, amman tunda tayi ringing din farko ba'a daga ba, yana sake kira a kashe yaji ta, har yanzun kuma a kashe take, yabar mata sako yakai goma, yanzun ma sakon ya sake tura mata "Me yasa zaki kashe wayarki? Idan caji ne ya kusan karewa me yasa baki fadamun ba? Ki kirani muyi magana" Baisan me yasa ya sake binta whatsapp yana tura mata "Kina ina wai?" Tunda yaji wayar a kashe, tick daya dayaga sakon yayi alamar baije mata ba yasa shi jan karamin tsakin da yayi shi babu a dadi a cikin yan dakikan daya kirata zuwa tura sakonnin. Earpiece din ya zare yana ajiye su tare da wayar akan system din shi, kafin ya dafe fuskar shi da hannuwa yana fitar da wani numfashi mai nauyi, sannan ya sauke hannuwan, bayan shi ya jingina da kujerar falon, da wani nisantaccen yanayi a muryarshi yace "Aure zanyi" Coke din da Fodio yake zuqa da straw yaji ta bi mishi ta wata kafar daban, kafin ya soma tarin da yasa shi sake zuqar wata coke din ko zai samu kafofin iskar shi da suka toshe su bude, Arafat kuwa fasa maqala flash din da yake shirin yi a jikin system yayi yana dago idanuwa ya kafe a kan Hamza, bakin shi yaki rufuwa cikin tsananin mamaki. AbdulHafiz da yake zaune kan kujera bayan Hamza sai da ya gyara zaman shi ya miko hannu yana taba fuskar Hamzan daya doke hannun AbdulHafiz din "Lafiyar shi kalau?" Fodio ya tambaya yana cigaba da tari, kai Arafat yake girgiza "Haba Fodio, ya maka kama da mai lafiya? Bakaji me yace ba? Ko ni kadai naji? Dan Allah kuma kuce mun kunji" Kai AbdulHafiz yake jinjina ma Arafat "Bakai kadai ba, nima naji" Numfashi Hamza ya sauke, ya tsammaci fiye da abinda sukeyi yanzun, shi kanshi bai gama mamaki ba, ballantana kuma su "Ina zaune fa" Ya furta ganin yanda su Fodio suke maganar shi kamar baya wajen "Da gaske aure zanyi" Ya fadi yana kallon Fodio daya sake zuqar coke din shi yana hadiyewa "Dan Allah ka daina wannan wasan mana" Kai Hamza ya girgiza mishi "Wallahi ba wasa nake ba" Wannan karin AbdulHafiz ne yace "Wai da gaske kakeyi?" Yasan sunyi maganar Hindu da shi "Ka manta abinda kace mun?" Hamzan ya tambayi AbdulHafiz cikin yaren fulatanci, yana saka Fodio daukar filon kujerar da yake gefen shi ya jefa mishi "Uban me kace mishi?" Ya tsani Hamzan yayi ma AbdulHafiz fulatanci, dan ma da yawan lokutta AbdulHafiz baya mayar mishi, sai dai ya bashi amsa da Hausa, kuma Hamzan mantawa yakeyi tunda AbdulHafiz yana ji, shikuma inba da su ba, sai kuma mutane, amman indai yana cikin gida yare suke "Shine yake nufin me? Zakayi aure?" AbdulHafiz ya bukata cikin harshen Hausa, Hamza bai juya ba, amman yanajin idanuwan AbdulHafiz din na yawo a bayan kan shi, kamar suna neman hanya su leqa ciki suga duk wani abu da yake boyewa "Ku daina yi kamar kunsa ran bazan taba yin aure a duniya ba..." Hamza ya fadi yana mikewa, so yake ya fada musu daman ko zaiji maganar ta daina tokare mishi makoshi. Amman yanda sukeyi na kara mishi shakku, yasan bai shirya ba, suna kara nuna mishi yanda bai shirya din ba da gaske, system din shi da waya ya dauka yana wucewa daki yabar su anan. AbdulHafiz na bin shi da kallon da yake cike da alkawarin cewar basu gama maganar ba, tunda bai bashi amsar tambayar da yayi mishi ba. Dan yace karya taba Hindu, baya nufin yace mishi ya aureta dan kawai ya tabata. Wani irin shirune ya biyo bayan tashin Hamzan, kafin Arafat ya kore shi da maganar kwallon kafar Laliga ta shekarar, kafin suci gaba da hirar suna aikin su, AbdulHafiz ya fara tattara kayan shi wajen sha biyun dare yana wucewa daki. Idanuwan shi yakejin yana dagawa dakyar saboda baccin da yake cikin su. Yana kai wayoyin shi da system ya ajiye a daki, ya zauna gefen gado, wayar Hamza ya kira daya daga a bugun farko "Ka shigo muyi magana" Ya furta yana kashe wayar, yana kokarin ganin bai shiga dakin Hamzan ba, dan karya ga abinda zai bata mishi rai, ko mintina biyar ba'a yi ba Hamzan ya shigo dakin yana tsayawa bakin kofa "Karka tambayeni me yasa zan aureta, karka cemun ban shirya ba AbdulHafiz na sani, ita kanta ban shirya zan so taba, ka kalleni yanzun" Kallon nashi AbdulHafiz yakeyi "Kayi istikhara, karka kara wani abu akan maganar nan baka nemi zabin Allah ba" Kai Hamzan ya jinjina mishi, alwala ya dauro daman, zai saka dogon wando ne AbdulHafiz din ya kira. Sallah yake so yayi ko raka'a hudu ce, tunda har lokacin yana kiran wayar Hindu amman a kashe yake jinta. Batare da yace komai ba ya kama hannun kofar ya murda yana janta ya bude "Kar sha'awa ta zama jigon yin auren ka Hamza" Cewar AbdulHafiz din, ficewa daga dakin Hamza yayi yana ja mishi kofa. Koma menene jigon yin auren bashida wani muhimmanci tunda ba zai hana ba. * Da zazzabi ta tashi da safe, dakyar ta iya shan ruwan shayi, tukunna ta hadiyi panadol. Anty ma sai da tace ta hakura da zuwa makaranta, tace mata test zatayi, tana gamawa zata dawo gida, ba wani abu bane yake damunta, bacci ne. Kuma tasan kukan da tayine yasa mata zazzabi, sunyi waya da Dimples, ta kira zata tambayeta wani film taji tana kuka, duk da ta fada mata Hamza ne, bata dai gaya mata ga dalili ba kawai "Tun baki aure shi ba harya fara sakaki kuka? Hindu anya wannan mijin aure ne kuwa? Bai sameki bama bai san ya lallabaki ba, me zai faru idan ya sameki?" Bata samu amsar da ta bata ba, tadai tsinci kanta da kin dagawa daya kirata, gabaki daya wayar ma a kashe take tun jiyan. Ta dai sakata a caji ta cika, ta zare ta jefa a jakarta. Tayi kwalliya sosai dan ta boye yanayin da yake kan fuskarta. Tun jiya bata ko gwada yima kanta karya ba, ba zata iya rabuwa da Hamza ba in dai hakan ya zama zabinta. Abu dayane zai faru, ya gama tabata bai aureta ba, dole ya jira, ko kuma batasan me zai iya faruwa ba idan yaki, hango rabuwa dashi bata cikin tsarin abubuwan da suke zuciyarta. Iya jiya ta tabbatar da Hamza ya zama bangare na rayuwarta, kuma tasha ganin jarumai na canza halayen wanda suke soyayya dasu, daga film har a littafi, ko a korean films, cikin Secret garden ma yar talakawa ce fitik, dan da gani ma yake yafi karfin yayi soyayya da ita, sai gashi zance yasha banban, rabuwa yayi da mahaifiyar shi akan yarinyar, sukai auren su harda yara ukku, a cikin The Heirs ma sai da soyayyar yarinyar tasa azzalumin film din yayi laushi tubus, tana da yakinin idan ta dage tsaf zata sakewa Hamza hali, balle taga soyayyarta a cikin idanuwan shi. Da wannan tunanin ta tashi, har addu'a tayi a sujjada Allah ya bata karfin gwiwar yin wannan jahadin, dan rabashi da neman mata idan tayi nasara ba karamin jihadi bane ba "Zan canzaka Hamza, soyayyata zata canza ka" Take fadi tana kara maimaitawa a cikin kanta harta fito daga gida, tana mike hanyar da zatayi kwana ta nufi makaranta. Tana shan kwanar kuwa tana ganin motar Hamza daya taka wani irin burki yana sauka gefen hanya ta dayan bangaren, zuciyarta takeji tana wani irin tsalle, da alama ko motar bai kashe ba ya fito yana zagayowa ya tsallako inda take, tun kafin yayo gab da ita take ganin tsantsar rikicin da yake shimfide a fuskar shi da tayi mata wani irin kyau, sportswear ne a jikin shi, riga da wando baqaqe "Me yasa zaki kashe wayar ki?" Ya tambaya yana dorawa da "Kinsan aikin da na ajiye na taho? Saboda kin kashe wayar ki?" Cikin idanuwa take kallon shi "Ai bance ka ajiye ba, ban kuma ce ka zo ba" Numfashi ya sauke, yanajin wani abu na tsirga mishi daga tafin kafar shi zuwa tsakiyar kan shi, kallonta yake yi, komai nata yayi mishi, kamar yanda ita da kanta din tayi mishi "Kinyi kyau" Ya tsinci kan shi da furtawa, yanajin yanda duk wata masifa daya kwaso ta bace mishi, tun da asuba yake kiran wayarta a kashe. Har sun fita wajen aiki tun karfe bakwai, ya kasa zama ya taho ya dubata "Ni makaranta zanje" Cewar Hindu da takejin ganin shi ya taso mata da tuquqin kishin duk wasu yan mata da ya kasance da su "Hindu" Ya kira cike da kashedi, yana runtsa idanuwan shi ya bude su a kanta "Karki batamun rai fiye da yanda yake a bace, ki kunna wayarki. Kizo in sauke ki sai in koma wajen aiki" Kai ta girgiza mishi "Kaje abinka zan karasa" Kafin ta sake magana ya kama hannunta yayi mata rikon da batayi tunanin kwacewa ba, ya jata suka tsallaka dayan bangaren "Ka sakar mun hannu, wallahi ka sakeni" Take fadi cike da masifar da Hamza baibi ta kai ba, ya bude murfin motar "Zaki shiga da kanki ko in dauke ki in saka?" Ya tambaya yana tsareta da idanuwa, dariya tayi me sautin da bashi da alaka da nishadi "Karki gwadani Hindu, zaki sha mamaki wallahi" Ganin da gaske babu alamar wasa a fuskar shi yasa ta fisge hannunta tana shiga motar ta zauna, dan tsilli-tsillin mutane na wucewa "Nagode" Hamza ya fadi yana rufe murfin motar, ya zagaya ya shiga shima, yaja motar yana samu yayi kwana dan ya fita titi "Ya kika tashi?" Ya bukata "Lafiya" Ta amsa a taqaice, kai ya jinjina hadi da sauke numfashi "Ba zaki tambayi ya na tashi ba?" Shiru tayi ta kyale shi "Nai ta kiranki jiya, nayi magana da Appa azo a tambayar mun auren ki" Zuciyarta taji tayi wani irin tsalle kamar zata bar kirjinta, da sauri ta kalli Hamza, wani murmushi da bata sani ba ya kwace mata, tun ba'aje ko ina ba, ta dauka akwai aiki shimfide a gabanta kafin ta canza shi, kafin suzo wajen nan, amman kashe wayarta tayi na rana daya gashi ya rikice har yana maganar aurenta, ina ma zata ga wanda suke karyata faruwar rayuwar cikin litattafai, tayi musu misali da kanta "Shine yace daga gidan ku za'a fadi ranar da za'a zo" Dan gyaran murya tayi, tana kokarin boye tsantsar farin cikin da take ciki "Ni nace ina so in aure ka bayan jiya?" Dariya Hamza ya danyi "Ni ina so in aure ki, ya ishe mu" Harar shi tayi, tana saka shi karayin dariya, yanda take da karfin bata mishi rai ta kuma batar dashi cikin kankanin lokaci na bashi mamaki. Hira yake janta da ita har suka karasa makaranta, duk da tana ta kokarin share shi kamar tana fushi har lokacin, bayan ya gama wanke mata duk wani bacin rai da yayi sanadi. "In dawo muje muci abinci da rana?" Ya bukata, kai ta girgiza mishi "Ina yin test din nan gida zan koma inyi bacci, sai dai gobe" Shagwabe mata fuska Hamza yayi "Dan Allah, bansan ko zan samu in ganki anjima ba..." Numfashi ta sauke "Karki ce mun a'a" Kai ta tsinci kanta da jinjina mishi, yako yi mata kyauta da wani rantsatsen murmushi da taji har kasan zuciyarta, kafin suyi sallama tana wucewa aji. Da wani irin nishadi take duk wata hidima ta ranar, tana jin yanda data koma zatayi wa Anty maganar dan ta fadama Baba a saka masu Hamza ranar da zasu zo. Da zata samu ma a saka lokacin bikin daya dana Khadee, tunda ita gidan mijin sunzo sun roki alfarmar a kara musu wata biyu, bai karasa ginin da yakeyi ba, saura fenti, tayal da kuma wayarin din wuta. Baba baiyi musu ba, yayi gini, ya kuma san wahala da kashe kudin da yake cikin hakan. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 8 Ita kanta ba zatace ga asalin abinda yake damunta ba, amman sai da ta kwana biyu ko makaranta bataje ba, da yake kowa a gidan ya santa da nacin zuwa makaranta, babu wanda ya takura mata, duk kyaleta sukayi da tace bata jin dadin. Ranar na ukkun ne da taje ta sami assignments sun tarar mata kamar tayi wata daya bataje makaranta ba, da sanyin jiki hadi da dana sani marar misaltuwa ta dawo gida. Ta rasa ta inda zata fara taro kwanaki biyun da ta rasa a makaranta. Tana cin abinci ta watsa ruwa, hadi da alwalar magriba duk da akwai sauran mintina talatin, bata so idan ta zauna ta sake tashi, har hijab din da zatayi amfani da shi ta dauko. Assignments din ta fara ragewa na rubutun, tana barin zanen sai da tayi Magriba tukunna ta hau kan drawing board dinta, zanenta takeyi tana sauraren wakokin Ed Sheeran da yake bala'in burgeta saboda kalaman da yake amfani dasu wajen wakar, gajiya tayi wajen tara ta mike tana zuwa ta sake yin alwala tayi sallar isha'i, akwai abinda ya daure mata kai a zanen, ta kasa fahimtar shi, tasan ba za'a rasa wanda ya gane ba cikin yan ajin nasu, zata iya bari da safe in taje makaranta, dan haka tabi lafiyar gado, da yake tana zanen tana ciye-ciye kamar yanda yake sabonta, bata jin yunwa. Wayarta ta janyo tana shiga Instagram, kafin ma tayi refreshing taci karo da hoton AbdulHafiz, ko tace hannuwan su shi da yarinyar da alama ita zai aura, ba rike suke da junan su ba, nashi hannun akan cinyar shi, nata ma a kan tata cinyar, yasha jan lalle, zoben su iri daya, hakama agogon hannun su, irin wanda masoya suke siye, ya saka caption din 'Mine' Sai yayi tagging din handle dinta da tuntuni Hindu tayi following din yarinyar dan ba karamin burgeta sukeyi ba ita da AbdulHafiz, wata irin soyayya sukeyi mai sanyin gaske. Zuwa yanzun tasan cewa AbdulHafiz jinin sarauta ne, amman batasan dan Sarki bane ko hakimi, itama kuma Nabila din, budurwar tashi a jikin profile dinta ta rubuta 'Royalty' kuma tana yawan daukar hotuna akan doki, ko cikin gidan Sarauta da Hindu ba zatace Masarautar wanne gari bace ba, ko yaushe baka raba hotunan da Hindu take sakawa da Alkyabba a jikinta, masu kyau, duk da fuskarta zakaga da nose-mask da yake hana maka ganin gabaki daya fuskarta, shi kan shi yaci ado dai-dai da duk wata alkyabba da zata saka. Garama kwanaki taga AbdulHafiz ya saka wani hoton Nabila da rabin fuskarta ne kawai, kuma an saka hoton a baki da fari, ta hadu harta gaji. Lokaci da dama Hindu kanji kishin Nabila na rashin dalili, saboda yarinyar ta sami duk wani abu da take mafarkin samu, namiji hadadde jinin sarauta ma, ga shi ya iya soyayyar da take sakata cire Nabila tana dora kanta a madadinta lokutta da dama. Ko Hamza takan ga ya saka abinda ya danganci su AbdulHafiz din da caption din 'Couple crush'. "Hmmm...." Hindu ta fadi a fili da ta shiga shafin Nabila taga ta saka hoton AbdulHafiz din da yake dariya ya daga hannu yana kokarin kare fuskar shi kamar bai shirya hoton ba aka dauka, ga dimple din shi daya bayyana yana saka zuciyarta dokawa, Nabila din ta saka caption din 'Allah ya kai fata Mizani Dikko Na' Gyara kwanciya Hindu tayi, duk da zuciyarta ta furta mata 'Wata miyar sai a makota' Batason barin wannan tunanin yayi tasiri a tare da ita, In shaa Allahu yanda take addu'a babu dare babu rana, itama miyar makotan nan a gidanta za'a dinga yinta. Bata san ko ganin su AbdulHafiz bane ba, ko kuma kalar Samarin da ta dinga haduwa da su, ciki harda Jalil ya sata yin abinda takeyi yanzun ba, kawai tsintar kanta tayi da shiga DM din Hamza tana mishi sallama hadi da rubuta 'Ban san ko zaka ga sakon nan ba, ban ma san ko zaka karanta ba' Tukunna ta tura mishi matsalar da bata gane ba, dangane da assignment dinta tana dorawa da 'Watakila sanda zaka ga sakon nan ma har na gama. Duk da haka nagode' Ta karasa tayi minimizing tana tashi zaune, har wata zufa takeyi kamar wadda tayi gudu, zuciyarta na mata sake-sake kala-kala. Sake kwanciya tayi tana komawa tayi screenshot hadi da komawa whatsapp ta turama Dimples 'Nama Hamza DM' Ko mintina biyu batai ba, sakon ya nuna alamar yaje an karanta, harma Dimples din na rubutu 'Wanne Hamzan?" Numfashi Hindu taja tana fitarwa, zagin da tasan zata sha wajen Dimples shisa ko da wasa bata taba bata labarin Hamzan da yanda take bibiyar shi ba, yanzun ma kawai ca tayi mata 'A Instagram nake ganin shi, yana burgeni sosai, kuma Architect ne' Tsaki Dimples din ta turo mata 'Allah yasa ya watsa maki zagi tunda ke baki da tunani, halan Jalil bai koya maki hankali ba? Kinsan ni bana wani yin Instagram, saboda nasan makaryata sunyi yawa a wajen. Kilan ma duk abinda yakeyi yana burgeki din Fake ne, Hindu ki rufama kanki asiri da mazan social media, kiyi addu'a Allah ya kawo miki wanda zaki natsu da shi' Kai take girgizawa tana karanta sakon 'Ke shi ba karya yake ba' Emoji din harara Dimples din ta aiko mata 'Kici gaba dai, tunda baki da hankali har yanzun. Ni dai na fada miki, Wallahi ki kiyayi mazan Social Media' Sauka kawai Hindu tayi daga whatsapp din, daman abinne taji ba zata iya barma cikinta ba shisa ta fadama Dimples din, duk da tasan halinta da kuma yanda sam bata da yadda, mutanen da take gani ma bata yarda dasu ba, ballantana na Social Media, bama mutane Dimples take so ba, lokutta da dama zakaga ta daga girarta in tana danna waya, duk idan ka tambaya zata ce 'Mutane ne suke mun magana, me yasa mutane suke mun magana ne wai? Halan basu san ni ba son su nake ba' Har dariya take ba Hindun, sai dai duk baudadden halinta tana da dadin zama, saboda tana da wani irin kirki da ba ko yaushe ake samun mutane masu irin shi ba yanzun, sai dai tana cikin mutanen da ake kira 'kai fi daya' kuma cikin wanda ake cewa su 'tsaye' suke, shisa sai kayi tunanin magana Dimples ta fada maka wasu lokuttan, amman har ranta hakikanin gaskiyarta ta fadi, bata damu da ya zaka dauki hakan ba. Shisa suke fada da Hindu wasu lokuttan, saboda tana mata fadan gaskiya. Wayar Hindu ta saka a key zata ajiye sai taji 'dit' alamar sako ya shigo, da sauri ta danna ta cire key din ganin notification din na Instagram ne, shiga tayi tana budewa, zuciyarta na wani irin tsalle ta dawo wuyanta, kafin ta koma kirjinta tana cigaba da dokawa kamar zata fito, ganin da tayi Hamza ne ya amsa sallamarta, ya dan dauki mintina kafin taga ya turo hoton da tayi saurin budewa tana ganin 'Rough sketch' daya warware matsalar da ta kasa na zanen nata, sai dogon sharhi cikin gamsashen bayani daga kasa. Wani irin murmushine ya subuce mata, tayi wani tsalle tana dawowa kan gadon, hadi da mirginawa tana jin kamar an mata albishir da kujerar hajji da duk wani cikar burinta saboda farin cikin daya lullubeta, tuntuni inda tasan maganar Architecture itace zata saka Hamza ya kulata a DM da tafi shekara da tura mishi, yanda in tayi mishi a comment section yake yin biris da ita yasa bata taba tunanin zai amsa mata magana ta private ba. Hamza fa, Hamza Abu Abbas ne ya zauna yayi mata bayani harda zane yanda zata fahimta sosai. Rubutu ta soma yi tana tura mishi 'O. M. G, wallahi ban taba tunanin zaka amsani ba, banma san me zance ba, na rasa ta ina zan fara, har yanzun ina ganin kamar mafarki nakeyi ka amsani, Nagode, Nagode, Nagode' Baifi minti daya ba ya turo mata gajeriyar amsa 'Uw' Daya nuna alamar da wahalar gaske ya sake cewa komai, amman a hakan ma ita ce da dubban godiya, dan yau ya gama mata komai, ya wanke mata bakin cikin da ta kwasa a watannin nan, ranta kal take jin shi, dan tashi tayi ma ta koma kan zanen da takeyi. So takeyi ta gama ta dauki hoton ta tura mishi, tana jin alamar ko da zata kwana tana zane yau babu gajiyar da zata saukar mata, sakon Hamza ya zame mata kamar 'Energy drink'. ** Zaune yake kan doguwar kujera ya jona cajar system din shi a jikin extension din dake falon ya janyo wayar yana kokarin hadawa. Fodio ya fito daga daya daga cikin dakunan baccin, kugun shi daure da towel, sai wani karami yana goge kan shi da shi, ya zo tsallakewa yayi ciki da cajar Hamza din da ya buga wani tsaki yana dorawa da "Wawa ne kai Allah... Wanne iskancine ma zaka fito tiqi-tiqi da towel kana goge mana kai a falo?" Arafat da yake zaune yayi dariya mai sauti, Fodio kuwa towel din ya sauke daga kan shi "Ni da gida na? Sai a hanani yin abinda nake so? Kaji mun wani karfin hali dan Allah" Tsakin Hamza ya sake ja yana rankwafawa ya dauko cajar tashi ya jona hade da system din. Da gaskiyar Fodio, gidan shine da yake nan Malali, shi dan asalin garin Kano ne, Mahaifin shi dan kasuwane da zai shiga cikin jerin manyan yan kasuwa da ake sarin kayan masarufi a wajen su a garin Kano, matan shi hudu, mahaifiyar Fodio itace ta biyu, kuma shi kadai ta haifa kafin Allah yai mata rasuwa tun yana da karancin shekaru, ya sha gwagwarmayar rayuwa, shisa yaci burin karatu dan ya zama wani abu ya daga ma gidan nasu ko zai huta da yan ubancin da ake nuna mishi kiri-kiri. Da yake mahaifin shi ba wani damuwa yayi dasu ba, sun kai su arba'in a wajen shi, kudine duk idan ka tambaya zai dauka ya baka tunda ba matsalar shi bane ba, ko karatu Bauchi Fodio ya zaba, can kuma yaje ya karancin bangaren gini, ya fita da sakamakon da makarantar suka so rike shi, sai dai tuntuni yake burin zama garin Kaduna, hakan yasa shi yayi cuku-cukun da bautar kasa ta kai shi Kaduna, ya kuma yi zaman shi da yake yayi sa'a kamfanin sun yaba da kwazon shi suka kuma rike shi. Tsarin baban sune duk yaran shi Maza yakan siya musu gidaje, Fodio ya zabi a siya mishi na shi anan garin Kaduna, bai kuma sami matsala ba, ba zaice ga ranar shi ta karshe da yaje garin Kano ba. Arafat dan nan Kaduna ne, duk da asalin su dan garin Kaduna ne, Structural Engineer ne, su ukkun sun hadu wajen IT, shi da Hamza da kuma Fodio din, a wani construction company a garin Abuja, jinin su ya hadu suka kuma zama aminnai kafin wani lokaci, duk da karatu ya watsa su wajaje daban-daban, sun ma kan su alkawarin duk zasu zauna a Kaduna suyi nasu kamfanin na qashin kan su komin shekarun da hakan zai dauke su. Abdallah ne kawai a cikin su abinda ya karanta ya banbanta da nasu, tunda shi aikin Banki yakeyi kafin daga baya ya dawo karkashin su Hamzan da aiki, kuma shi kadai ne talaka a cikin su, ya hadu da Arafat da Fodio ta sanadin Hamza, sun taso unguwa daya tun suna yara, da ya zama wani kuma ko kadan bai yarda zumuncin da yake tsakanin su ba. Sosai Abdallah yake samun rufin asiri ta fannin Hamzan dan shi mutum ne da hannun shi yake a bude, kuma irin mutanen da zasuyi komai dan abokan su. AbdulHafiz da Civil Engineer ne, kuma jinin Sarauta gaba da baya, daga garin Gombe, Sarautar garin da wahala taje hannun mahaifin AbdulHafiz din, dan anfi saka ran idan Allah ya dauki ran Sarki maici na yanzun babban yaron shi za'a ba, kuma shine Wan mahaifin AbdulHafiz din, a takaice dai jikane shi wajen Sarkin Gombe. Wajen taron da akeyi na manyan Architects da Hamza ya ziyarta yana shekarar shi ta ukku a makaranta suka hadu da AbdulHafiz ya rako Yayan shi da yake cikin manyan baki a wajen taron. Da yake Hamza mutum ne mai shiga rai lokaci daya, jinin su sai yayi wata irin hadu Hamza din, a haka su biyar suka zama abokan da suke jin junan su tamkar yan uwa. AbdulHafiz shiya dinga samo musu ayyuka daga manyan mutane har sukai kudin da suke da shi yanzun, aka kuma san su a wajaje da dama cikin fadin Nigeria, kamfanin su yana nan garin Kaduna na HAF constructions. Kalmomin farko na sunan su sukayi amfani dashi, sannan abokantakar su bai hanasu kafa kamfanin akan duk wasu ka'idoji da ya kamata ba, har da lawyoyi da kowa yake da shi, saboda halin rayuwa, ko ba da babu mutuwa. Duk da a tafiyar tasu ko kadan basa hango rabuwa ta sanadin samin matsala. Basu zo inda suke yanzun ba sai da fahimta sosai, duk a cikin su ma AbdulHafiz ne halin shi ya fita daban, ko magana sai kayi da gaske zaka ji tashi, suna iya tashin dakin da surutu sai dai ya bisu da idanuwa, ko zage-zagen da akeyi tsakanin abokai, sai dai su din su zage shi, amman shi ba zaka taba jin zagi a bakin shi ba, idan Sarautar ta motsa mishi ma, ko hayaniyar zakaga baya so, sai dai ya tashi yabar musu dakin, in sun ishe shi yabar gidan gabaki daya. Su dukkan su babu wanda bashi da gida da komai na bukata a ciki, sunfi zama gidan Fodio ne kawai. Abdallah kuwa da yake yana da matar shi, sai dai yazo su danyi hirar da zasuyi ya wuce, idan aiki bai sha musu kai ba kenan. Yanzun ma duk maganar da suke ya lafe cikin kujera da wayar Hamza a hannun shi, su duka suna daukar wayoyin juna, amman sun san iyakarsu a kai, duk kusancin su ba zaka tsinci daya daga cikin su na bude sakon wani ba sai da izini. Kome zasuyi da wayar kuwa, zasu iya shiga banki tunda duk sun san lambobin sirrikan juna su tura kudi, ko su siyi kati, amman ba zasu duba sakon da bai shafe su ba, suna girmama junan su, dan waya sirri ce, duk yanda kake ganin kusancin ka da mutum kuwa, akwai wani sirri a ciki da ba lallai yaso kagani ba. Ko AbdulHafiz din daya shiga Instagram, Hamzan yace ya dora mishi wani zane daya gama. Sai ya tsaya kallon hotunana, yana ganin yanda sakonni ke ta shigowa "Kai baka duba sakonnin ka ne" Ya bukata, Hamzan na girgiza mishi kai "Instagram ne fa" Fodio daya zauna gefen Hamzan ya amsa da "Instagram din fa, kasan aiki nawa na samar mana ta Instagram din?" Dan daga kafadu Hamza yayi dan shi kam bashi da lokacin tarkacen Instagram, ya dauke shi wajen ajiye hotunan shi, in yanajin kwiyar mayar dasu kan system. Ga shi da yarda waya kamar me, idan bai yardar ba za'a sace tunda duk inda zaije haka yake barin gilasan mota a bude. AbdulHafiz kance 'Rashin adani na cikin almubazzaranci Hamza, saboda kana da kudin siyan wata wayar baya nufin ka dinga sakaci da wadda kake da' Amman haka zai sake bari a sace, kusan indai da AbdulHafiz za'ayi fitar shi yake rufema Hamzan gilasan mota, tun yana fada harya gaji ya saka ma Hamzan ido "Da gaskiyar Fodio, ana samun clients a Instagram fa" Arafat ya fadi, kafadun Hamza ya sake daga musu wannan karin hadi da fadin "Hafiz ka shiga kagani, tarkace ne fa" Shigar kuwa Hafiz yayi, yanata duba sakonnin, da gaskiyar Hamzan, tarkacen su suka fi yawa, yawanci sakon gaisuwa, yan mata ma sunfi yawa, suna saka AbdulHafiz jinjina ma kokarin su, bawai yaga rashin ajin su ba, dan sun yiwa Hamzan magana, kawai dai yana ganin kokarin su wajen sake yi mishi magana bayan bai amsa waccen ta baya ba "Hindun Baban ta" AbdulHafiz ya karanta a fili, yana saka su ukkun kallon shi, kafin kowa yaci gaba da abinda yakeyi, sunan ne yayi mishi wani iri, sakon ya bude, yanayin murmushi, yanayin shiriritarta tayi mishi kama da ta Nabilar shi, yarinyar da ya dinga dakon soyayyarta tun kafin tayi hankalin da zata san yanayin ta, har Allah ya taimake shi ta fahimta, ta kuma amsa tayin shi, yanzun gashi har manya sunsan da maganar, da yake abu na cikin gidane, abokiyar wasan shice, basu kuma sami wata matsala ba. Hakan kawai yasaka shi amsa ma Hindu sallamarta, yana karanta sakonta, duk da ba fannin shi bane, matsalar tata ba wata babba bace ba, mikewa yayi yana zuwa dakin da indai zai kwana a gidan nan yake kwana, dan shi baya son jin hayaniyar komai in har yayi shirin kwanciya, ko da ba baccin zaiyi ba, ya dauko littafin da yakan yi zane-zane a ciki, sannan ya dawo inda yake ya zaina yana zana mata yanda taswirar matsalar take, ya dauka hoto ya tura mata, tukunna ya hada dayi mata bayani dalla-dalla, sai yaji ta burgeshi, dan karatun da takeyi din bakowacce mace bace zata iya. Lokacin da yan makaranta da yawa, harda masu nacin karatu zasu kai sha biyun dare su kwanta, Hindu zata kai asuba kan abin zanenta tana aiki, washegari kuma ta tafi makaranta, asalima zata iya sati daya a kowanne dare da wahala ta sami baccin awa biyu cikakke, lokacin da sauran dalibai suke tafiya gida duk idan an gama jarabawa, lokacin Hindu zata fara zuwa makaranta dan yin presentations na project dinta na wannan zangon. Dalibai kanyi project daya tal bayan shekaru hudu ko biyar, Hindu kanyi guda biyu kwarara a shekara daya, banda kananun da ba zasu kirgu ba. Duk da Hamza kance mishi ko a mafarki yaga zai karanci Civil Engineering idan ya tashi zaiyi sadaka, dariya kawai AbdulHafiz din yakan yi, dan yana da tabbacin babu wani abu da zai gagari Hamza in dai ya sa kan shi, domin yana da kwakwalwa da AbdulHafiz kan gani a fina-finai na kasashen ketare, yakan kuma ji labarin mutanen da ake ma laqabi da 'gifted'. Bai taba cin karo da su ba sai da ya hadu da Hamza. "Me kakeyi haka?" Fodio ya tambayi AbdulHafiz din "Wata yarinya na amsa" Ya fadi a takaici yana saka Hamza dagowa daga zanen da yake a laptop din shi ya kalli AbdulHafiz din "Me yasa zaka amsa ta? Da nace ka duba nace ka amsa ne?" Idanuwa AbdulHafiz ya kafe Hamzan dasu da ya saka shi kauda kai da cewa "Ni dai da baka amsa mun ba" Hankalin shi AbdulHafiz ya mayar kan wayar da yake dannawa, su dukan su yana musu wani irin kwarjini, ba ko yaushe maganganun su ke da amsa a wajen shi ba, kallon su kawai yakeyi sai kowa a cikin su ya kama kan shi, sun san AbdulHafiz, ba ko yaushe yake wasa dasu ba, yana karasawa ya ajiye wayar yana mikewa, dan lokacin wayar shi da Nabila yayi, yana barin wajen Hamza yace ma Fodio "Dan miko mun wayata dan Allah..." Wayar Fodio ya mika mishi, shima yana tashi yabar wajen, dan ya fita zaiyi ya siyo musu abinda zasuci, shi kam yunwa ta fara naniqar shi, har tara da wani abu. Sakon da AbdulHafiz ya amsa Hamzan ya duba yana shiga profile din Hindu, hotunanta ya shiga yana tsayawa kan wani da take sanye da farin Hijab "Woow" Ya tsinci kan shi da furtawa, ta mishi kyau badan bai tana ganin yan matan da suka fita din ba, kawai ya manta ranar karshe da mace tayi mishi kyawu a idanuwan shi har haka. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 3 Kamar yanda Zahra Tabi'u, marubuciyar Mai Tafiya, cikin alkalamin ta a rubutun Farin wata: "_Kowane labarin duniya yana da tushe. Kowanne yana da mafari. Me ke nan? Wani abu da ya faru har ya zama sanadin wanzuwar jirkitattun al'amura_" Labarin Hindu ya fara a shekarar 2012 a lokacin tana aji biyar a sakandire. Tun bayan haihuwar ta, tun ranar da Baba ya dora idabuwan shi a kanta tana a cikin shawul, aka mika mishi ita dan yayi mata hudu ba, Anty zatace taga wani yanayi a fuskar shi da bata taba gani ba a game da sauran yaran nashi, ba wanda ta haifa tare dashi ba kawai, har wanda suka haifa da abokiyar zamanta, dan tana wajen duk yawanci sanda ake bashi yaran yayi musu huduba. A lokacin da yake rike da Hindu zaka iya rantsewa ita ce yarinya ta farko da Allah ya nufe shi da samu bayan tsayin shekaru, kuma a lokacin yana da yara bakwai kafin ita. Ya kuma kara samun yara hudu bayan ita din, jimlar yara goma sha biyu da Allah ya albarkace shi da samu. Amman ya riketa a jikin shi ko bayan daya gama yi mata huduba, daga ranar kuma har zuwa yanzun zaka gane yanda wajen Hindu daban yake a zuciyar Baba. Akwai dalilin da yasa Malamai da yawa suka karkata ra'ayin su da kafa hujjoji masu karfi akan cewa iyaye su boye yaron da yafi soyuwa a ransu, karsu nuna a fili saboda hakan zai iya saka kishi a zukatan sauran yan uwan su, idan da kaddarar shaidan ya darsa musu wani tunani zasu iya cutar da juna ma. Sai dai a gidan Baba hakan bai faru ba, saboda bokon shi ta rinjayi ilimin addinin shi ba kadan ba. Duk yanda Anty taso ta nusar dashi akan yanda yake nuna kaunar Hindu karara sai ya nuna mata bacin ran shi, ya nuna mata shi duka yaran shi yana kaunar su. Da dukkan gaskiyar shi yakan yi maganar, yana kaunar yaran shi, zai iya komai a kan su, yana kula dasu, yana kare musu duk wani hakki har wanda bai rataya a wuyan shi ba indai zasuyi farin ciki. Da iyayen su mata basa tsaye akan tarbiyar su, tabbas da yaran gidan Baba zasu taso cikin wata irin sangarta taban mamaki, dan shi in ba Hindu aka taba ba, baisan ya kwabi yaro ba, wannan itace kalar fahimtar da Baba yayiwa kaunar yara. Ita kanta Hindu tana girma tana kara fahimtar yanda ita dince raunin Baba, ko da ana so a roke shi abinda ba ayi tunanin zaiyi ba, ita din ake turawa, da ta shagwabe fuska tace "Baba na" Kamar yanda take kiran shi, ko wacce bukata zata furta bayan kiran sunan nashi, dai-dai kun ranaku ne yake iya ce mata a'a shima badan zuciyar shi taso hakan ba. Ba zaka ce babu kishin kalar kaunar da Baba yake ma Hindu a tsakanin yan uwanta ba, dan lokutta da dama a fuskokin su zaka gani. Sai dai su kansu akwai wata irin kauna da shakuwar zaman yau da gobe hadi da karfin jini ta saka musu akan junan su, shisa kishin kaunar da Baba yake mata din baya damun su na tsayin lokaci, zasu nuna a lokacin da hakan ya faru, ita kuma tayi musu dariya dan har ranta take jin Baban nata, idan kaunar shi a gareta daban ce, tana da yakinin kaunar da take mishi daban ce da ta sauran yan uwan ta. Bawai dan Anty bata da halaye masu nagarta ba, ba kuma dan batajin mahafiyarta har karkashin zuciyarta ba, haka kawai ta taso da son zama kamar Baba, ta taka matakin karatu kamar shi, taso yaranta kamar yanda Baba yake son su, dukkan rayuwarta tana kwatanta ta akan son zama kamar mahaifin nata. Yau tun da akaje daukosu daga makarantar su ta Zamani College dake nan garin Kaduna, Hindu take jin ranta kal, farin ciki takeyi tunda satin ya kama, bawai dan kasancewar yau din ranar alhamis ba, ranakun da take matukar so fiye da kowanne a cikin satika shine Alhamis da juma'a, dan babu islamiyya, zata samu tayi kallo yanda ranta yake so. Musamman idan Allah ya dora ta akan Yaa Zaid ya ara mata kwanfutar shi kirar laptop tayi kallon a ciki. Akwai faifan cd din data siya har biyu, daya fina-finan indiya ne da baka raba rayuwarta da kallon su, dayan kuma korea ne da bata jima da fara kallon fina-finansu ba, ta kuma sami sunyi dai-dai da ra'ayinta. Zuwa yanzun tana da tabbas duk kudaden da zata samu wajen siyo su zasu kare. Tana son soyayya, tun bata kai haka ba take hasaso kalar mijin da take so, ballantana yanzun da take kan ganiyar shekarun yan matancin ta. Duk da kullum saita canza ma mijin da take ra,ayi siffa ko launi a cikin kanta, amman dai a kowanne yanayi, kyakkyawa ne na kwatance. Sai dai alhamis din yau ba murnar kallo bace kawai a ranta, harda murnar Baba zai cika mata alkawarin wayar da yayi mata. Kusan duk kawayenta a makarantar boko suna da wayoyin hannu, shekarar da tazo ana yayin Nokia daga kan Express zuwa C2 da kuma X2 da take tashe tsakanin yan mata, samari harma da masu aure, idan kuma akazo wayoyin Nokia na symbian series da bakowanne bama yasan darajarsu balle yagane dadin amfanin da suke dashi da yanda a lokacin suka shallake ma duk wani samfuri na wayar hannu da kamfanin Nokia suka kaddamar. Saboda haka dai-dai kun mutane ne suke da ita. Ita kam Hindu ba wannan tunanin bane a ranta, waya take so ta mallaka kawai. Yanda yan ajin su ke hirar manhajar sada zumunta ta 2go bata so a barta a baya. Dan haka ta addabi baba cewar suna duba aikin gida da za'a basu a makaranta a wayar ta google. Kuma yana da kyau ace ta mallaki tata saboda jarabawar da karshe da zata shirya su shiga aji shidda da take gabato musu. Kuma ta fada mishi idan ya hado mata da memory card har karatun Qur'ani kamalalle za'a tura mata, zata dinga kunnawa tana sauraro saboda haddar da sukeyi a islamiya. Duk da Baba yaso sai Hindun ta gama sakandire, dan shine tsarin shi ga matan na rike waya. Mazan kuwa kusan yanzun da wayar ta yawaita duk ya siya musu, har Khalil da Junior suna da yan Nokia dinsu kananu. Ita ce mace Babba a gidan tunda Amna da Asma'u yanzun suke tasowa, wayar hannu ita ce karshen abinda yake ran su. Sosai Khadija take mata yanga da Nokia Express dinta, tana kara kwadaita mata son wayar, kawarta Zainab da duka suke kira da Biebee, makociyar su ce, tare suka taso tun yarinta, duk da ba makarantar bokon su daya ba, amman islamiya daya suke zuwa, itama satin daya wuce Babanta ya sai mata X2 yar yayi. Naci da rokon da ta dinga yiwa Baba ne yasa shi amincewa. Yace har sim da memory duk zai hado mata dashi, ran alhamis yace mata, tana kuma lissafe da ranakun. Yau a sama take jinta tana yawo kan gajimaren farin ciki. Har fina-finai ma sai ta dinga bayarwa ana tura mata a memory dinta, kallo zata dinga yi a nutse babu takura, bamai zuwa falo yai mata iko da rimat. Sosai take cikin nishadin da ko fuskarta kagani saika fahimta. Suna shiga gida kai tsaye bangaren su ta wuce tana shigewa dakin su ita da Asma. Kai tsaye bandaki ta wuce dan babu wutar lantarki, ga wani irin zafi da taji ya saukar mata, ruwa ta watsa tunda tayi sallah a makaranta, tana fitowa ta saka riga da zani na Atamfa tukunna ta fice daga dakin zuwa kitchen dan ta zuba abinci. Duk da batajin yunwa, cikinta a cike take jin shi da murna, tuwon shinkafa ne da miyar taushe da tasha lawashin albasa tana ta zuba kamshi, ga wadataccen naman rago da ya kara taimaka mata wajen yin kyau. Rabin malamala ta zuba tana saka miya a kai ta dauka ta fito falo ta zauna, bata nemi Anty ba dan tasan bacci take a irin wannan lokacin, ko da zata tashi sai zuwa la'asar. Asma kuma tana da tabbacin tana bangaren Mama. Ta fara cin abincin kenan Khadija da suke kira da Khadee ta shigo falon, duk da yanda suke furta nasu sunan a gayance Kha din daban sai Dee din da take fitowa a gajarce D, in wasu suka kira sai suna gyara musu da cewar ba haka bane ba. "Banza ashe kin dawo, yau Baba zai kawo miki wayarki ko?" Khadee ta fadi tana samun waje kan kujerar da Hindu take ta zauna, kai Hindun ta daga mata dan ta cika bakinta da tuwo, hadiyewa tayi kafin tace "Eh yau yace in shaa Allah... Zaki tura mun 2go" Dan karamin tsaki Khadee taja "Ke ba zakiyi addu'a ba ya siyo miki mai yin WhatsApp, yanzun shi ake yayi ba wani 2go ba" Dan turo baki Hindu tayi, duk da yanayin ya zame mata jiki, fuskarta kusan ko da yaushe a shagwabe take, da harda muryarta kafin tsokanar yan makaranta yasa tayi kokarin gyarawa, amman duk da haka, magana kawai zatayi ka fahimci tsantsar sangarta a tattare da ita "Ni dai ina son 2go" Ta fadi, dan kuwa shi yan ajinsu suke labari kullum, suna hirar rooms, Nigeria room1, Kaduna room1, da Comedy room1. Duk da shi Comedy room din monitan ajinsu taji yana maganar shi, akwai masu account biyu ma a ajin, da garin Kaduna da kuma garin Kano, dan ance sosai ake buga dirama a BUK room1. Tama ji kawarta Yasmin na fadin zata bude, dan rannan wasu yan Kano su B2 sun shigo Kaduna room din sunyi fadan turanci da akafi sani da brawl da su Curious su Zeegee, dan daga baya fadan ya koma BUK room, taso ta kalli yanda aka kare. Labarai irin wannan su suke kara kwadaita ma Hindu 2go din, ita whatsapp din bawani burgeta yake ba, dan taji Khadija tace yafi rashin hayaniya. Saima kana da lambar mutum tukunna zaka gan shi. A kunnuwan Hindu hakan ba abu bane da zaiyi mata dadi, tunda duk kawayenta sunfi yin 2go, bata da waya amman duk wata dirama da za'ayi suna bata labari, da yanda suke fadar turancin samarin Kaduna room1 tasan dole akwai hadaddu a cikin su. Zata je itama a gabza da ita, a santa a Kaduna room1 dan duk wanda yai mata ba barin shi zatayi ba, da alama Yasmin yar kallo take zama dan ta cika tsoro, takan ce mata tana gudun tayi turanci su Qwaro ko Curious suja mata layi alamar batayi dai-dai ba. "Ke kika sani, meye a 2go banda hayaniya, da shirme, kowa sai yace zai turo maka friend request, aita maka shirmen banza da wofi" Cewar Khadee dan sam bata san hayaniya, duk gidan ita da Zaid sun fita daban. Gara ita Khadee ma ana hira da ita idan taso, Zaid kuwa zuciyar shi a wuya take kullum, da wahala ayi hirar mintina goma bai watsama wani zagi ba, dan zaka fadi wani abin da bai mishi ba sam-sam. Kusan a yayyen maza yan gidan sunfi shakkar shi, yana musu dariya, amman hakan baya hana shi hukunta su idan bukatar hakan ta taso. Karasa cinye tuwon ta Hindu tayi ta dauke plate din takai kitchen ta wanko hannunta, dai-dai lokacin da suka kawo wutar da ta sakata wani ihun murna tana fitowa daga kitchen din da gudu. "Allah ya sambada muku albarka yan nepa" Yar dariya Khadee tayi "Kafin anjima ki tsine musu in sun dauke ba" Kayan kallon dakin Hindu ta kunna tana dauko remote ta dawo ta zauna, kafin su gama kawowa tace ma Khadee "Anya akwai wanda suka fi yan Nepa shan tsinuwa a kasar nan?" Kai Khadee ta girgiza mata "Bayin Allah, ko yan sanda basu kaisu shan zagi ba, duk in suka kawo wuta suka dauke fa sai kinji an zage su, ko kwana nawa wutar zatayi" Dariya sukayi su biyun, suna mayar da hankalin su kan tv din, Hindu na canza channel din zuwa ta indiya sun saka film din Ishq, duk da ta kalla, tana son film din har lokacin, saboda soyayyar da aka shimfida a cikin shi, ita ta saka Ajay ya kara burgeta matuqa, daman yanayin miskilancin shi ya mata, haka take son namiji karya cika dariya ta rashin dalili, abu kadan ya bude hakora cike da rashin aji. Kallon sukeyi suna dan taba hira kan film din, kafin a kira sallar la'asar data tashe su, Khadee na wucewa bangaren su, ita kuma Hindu tayi daki abinta. * Da yake sun saba cin abincin dare tare da Baba, yamma nayi suka tattaru bangaren Mama kasancewar ranar ta fada girkinta. Su biyar ne a dakin. Huzaifa, Khadee, Jafar, Hindatu sai Junior da ya shigo da sallama yana zama gefen jafar da ya lafe cikin kujera mai mazaunin mutum biyu da wayar shi makale a kunne, da alama ya gama nutsuwa cikin wayar da yakeyi, banda murmushi babu abinda yakeyi, muryar shi ma can kasa, Junior din ma da yake kusa dashi ba zaice ga abinda yake fada ba. Muhsin ne ya fito daga bangaren su, da sai daga baya aka gina musu, boys quarters din da yake bayan gidan ne Baba ya rushe aka sake ginin ya hade bangaren da cikin gida, a ra'ayin shi bai yarda shi yana cikin gida yara dan maza ne suna can wani bangare kofa ta raba su ba, duk da a ko ina suke cikin gidan ba zai hana abinda Allah ya kadarta samun su ba. Amman zasu iya fita yawon rashin dalili sukai dare a waje bazai sani ba, ba lallai maigadi ya fada mishi ba. Idan anan ciki suke, dole zai san karfe nawa suka dawo, in fitar dare ce zasuyi sai da sanin shi, hakan yafi mishi kwanciyar hankali. Kallon Jafar yayi da yake ta zabga murmushi tukunna ya kalli Huzaifa yana fadin "Shi kuma wannan me yake yi?" Cike da rashin kulawa Huzaifa yace "Waya" Girgiza kai Muhsin yayi dan yana da tabbacin da budurwa Jafar din yake waya, rigimar yaran na bashi mamaki, idan yana da yarinya kamar su Jafar na zuwa wajenta, da kan shi zai fito yace ya turo manya. Yasan daga nan bazai sake ganin shi ba, yara basu da ko sisi wai soyayya. "Jafar da muryarka na sauka haka kake mana hayagaga" Cewar Muhsin din cikin jimami, dariya Huzaifa yayi "Me yasa zai kashe maka murya?" Dan rausayar da kai Muhsin din yayi yana samun kujera ya zauna "Hakane kuma..." Ganin zasu dame shi yasa Jafar mikewa har lokacin da wayar a kunnen shi dan yabar musu falon, yana kan fadin "Jiya ko baccin kirki banyi ba ina tunanin ki" Suna cin karo da Mama da tayi karaf tace "Kaji shegiyar karya, ba ina jin Babanku harya dawo masallaci ba yana faman tashin ka..." Da gudu Jafar din ya wuce dan yasan Mama zata ballo mishi aiki, gabaki dayan su dariya suke, Mama kam kai take jinjinawa "Haka kuke samun yan mata kuyita gillara musu karya, sai kiji yaro yana fadin ya kasa cin abinci, bayan ya share faranti biyu yana neman kari" Sosai Huzaifa yake dariya "Mama banda ni fa" Hararar shi tayi "Kai din? Allah dai ya shiryaku kawai" Ta karasa maganar tana shigewa kitchen ta dauki kofi ta koma daki abinta. Hira suke dan tabawa kafin ayi kiran sallar magriba, mazan su wuce masallaci, su Hindu duk anan bangaren Mama sukai sallah. Kafin Baba ya shigo da sallamar da suka amsa su dukan su, dan sauran mazan ma sun dawo sanin Baban na gab da shigowa, murmushi ne najin dadin ganin yaran nashi bayyane a fuskar shi da take cike da dattako, kasumbar da furfura ta fara fitowa ta kara mishi wani kwarjini naban mamaki, kallo daya zakaiwa Baba kasan dan boko ne, ga gayu ya samu wajen zama tattare dashi. Yakan saka manya da kananun kaya duk randa ra'ayin hakan ya motsa mishi. Su duka sukayi mishi sannu da zuwa, ya amsa yana dorawa da "Hindu" Murmushi Hindu take ganin ledar dake hannun Baban, cike da shagwarta ta amsa "Baba na" Karamin tsaki Zaid yayi "Wai Baba na, kamar ke kadai kike da Baban" Shagwabe fuska Hindu tayi sosai, dan Zaid ne shiya hanata furta wani abin, ko a gaban Baba ne zai iya kwadeta sai dai yayi mishi fada, ledar hannun shi Baba ya mika mata yana dorawa da "Ga alkawarin ki" Cikin hanzari ta mike tasa hannuwa biyu tana karba hadi dayin wani ihun murya tana rungume Baban kamar zata karya shi "Nagode Baba na, Allah ya kara arziqi ya kare mana kai" Wani karamin tsakin Zaid yaja yana takaicin yanda Hindu ke abubuwa kamar wata yar shekara hudu, ita kuwa bata ma bi takan shi ba, Baba ya gama mata komai yau. Nan Baba yabar su yana shigewa ciki, Muhsin ya kalli Hindu da fadin "Zo muga wayar Yar Baban ta" Kamar yanda yakan kirata in yanajin tsokana, da sauri ta karasa wajen shi "Babban Yaya ai kaine ma zaka bude min daga kwalin" Hadi da mika mishi ledar, ya karba ta fito da Nokia C2 dal a kwalinta. Murmushi yakeyi, da gaske Hindun yar Baban ta ce, dan ko shi wayar hannun shi bata kai tsadar wannan ba, shiya bude ya saka mata sim din da memory ya mika mata. Murna fal ranta, inda Huzaifa yake ta karasa "Yaa Huzaifa kaga" Karba yayi, wayar ta mishi kyau yana fadin "Ma shaa Allah, aikam idan na fita zan siyo miki kati. Sai a kiyaye banda abinda bai kamata ba, nasan ban isa in hanaki chatting ba, ki dai saka Allah a duk wani abu da zakiyi da wayar nan Hindu..." Huzaifa ya fadi yana kallon sauran kafin ya dora da "Ku dukan ku ma, wayar nan da kuke rainawa zata iya halakar da ku Wallahi, kuyi chatting dinku, bashida wani aibu in dai kuka tsarkake zuciyar ku, duk da hanya ce ta shagala da ta same mu, yana dauke hankali sosai daga muhimman abubuwa, dan Allah ku kula" Kai Hindu ta jinjina mishi, nasihar tashi na zauna mata "In shaa Allah Yaya" Wayar ya mika mata, ta karasa tana nuna ma sauran, kafin ta wuce bangaren su ta nuna ma Anty, fadan da Huzaifa yayi mata shi Anty ta sake maya mata. Caji ta saka tana komawa suka ci abincin dare, ko da akayi isha'i anan sukayi. Baba yace jikin shi ya mishi nauyi a gajiye yake, Junior yaja musu sallah, shine ustazun gidan, ya kusan hada haddar shi ta Qur'ani, yaro ne da kallo daya zakai mishi ka fahimci nutsuwar da take tattare dashi da annurin fuskar shi wanda hasken karatun Qur'ani ne kawai yake zaunar dashi. Huzaifa ana idar da sallah ya fita, baifi mintina sha biyar ba ya dawo, ya mika ma Hindu katin dari biyu, sosai tayi mishi godiya tana jan hannun Khadee suka nufi bangaren su "Dan Allah kizo ki turamun..." Hindu ta fadi, nan suka zauna suka kunna wayar, Khadee ta tayata suka saita komai. Tukunna ta fice daga dakin, kan gado Hindu ta koma, tana jin ranta kal, ta siyi go credits daman, shiga 2go din tayi tana fara saka user name din duka kawayenta tayi adding dinsu. Biebee ta fara ansa mata tana turo sakon "Kawata kin shigo gari, kice Baba ya miki komai yau" Dariya Hindu tayi a bayyane suna fara hira da Biebee din. Kafin ta shiga Kaduna room1 din, yar kallo ta zama saboda tayi magana tafi sha biyar babu wanda ya kalli ko inda take, abin daya kona mata rai sosai. Dawowa private tayi tana fadama Biebee data turo mata kawunan dariya "Banza baki ga star dinki a Novice take ba, waye zai kula ki? Haka zaki ci gaba da dagewa har adan fara ganin ki" Jikinta Hindu taji yadan yi sanyi da maganar Biebee din, da tayi mata sallama dan tace bacci take ji zata kwanta. Fita daga room din Khadee zatayi taga an turo mata friend request. Da kamar ba zata amsaba ganin Elias aka rubuta a jiki. Sai kuma ta amsa, sannan ta fita daga room din. Sallama yayi mata da tasa ta duba profile din shi, zuciyarta na dokawa saboda ganin hoton nashi, ya hadu iya haduwa, bashi da hasken fata, amman yana da kyau, ga kasumba luf-luf kwance a fuskar shi, yasha shadda ruwan kasa da hula. Da alama a zaune yake da mota a bayan shi, sosai yayi ma Hindu kyau. Sallamar shi ta amsa suna gaisawa, yake ce mata sunanta yayi mishi dadi da harshen hausa, dan tunda suka fara hirar da turanci sukeyi "Kana jin Hausa daman?" Ta tambaya, tana saka shi turo mata dariya "Sunana Illiyas Abdallah. Bahaushe ne ni, ko dan kinga Elias, haka abokai suke kirana" Dakuna fuska Hindu tayi, sam sunan nashi bai mata ba, dan ita tafi son sunan yan gayu. Meye wani Iliya? "Yayi kyau, sai da safe" Ta fadi tana sauka daga kan 2go din batare da ta jira amsar shi ba, WhatsApp din da bata bude ba, ta shiga ta saka lambarta tana yin register. Tukunna ta sauka da kudirin da taje makaranta da safe zata amshi lambobin yan ajin su, itama su san ta faso gari yanzun. Danne-danne ta shiga yi na son ganin komai na wayar. Da Asma ta shigo dakin dakyar ta bata wayar tagani na wasu yan mintina. Har wajen sha daya na dare tayi kuri tana danna waya. Jin motsin Anty yasa ta tura wayar karkashin pilo zuciyarta nayin tsalle har cikin makoshin ta saboda tsoro. Dan Anty ta mata kashedi banda chatting din dare, tasan kuma tsaf zata iya dinga karbe wayar duk dare inta kula Hindun bata ji maganar da tayi mata ba, Anty na sakar musu fuska yanda ya kamata, amman suna bala'in shakkarta, bata da wasa ta fannoni da yawa. Baccin da bata shirya ba ya dauketa cike da mafarkin wayar tata. * Cikin sati biyu yanayin surutun da Hindu take da kuma tsoma baki a cikin duk wani fada da zata gani yasa aka fara ganeta a Kaduna room1 harma wanda ake ji dasu a group din kanyi mata magana, zuwa lokacin request take samu kaca-kaca. Takan amsa wasu, wasu kuma bata amsawa, tunda wanda take so suyi mata request din su Curious ne da su Rugi, amman taqi samu, dan ance mata Rugi ma zaku iya shekara kuna hira a room bai maka request ba. Gashi turancin shi na tafiya da ita. Duk a tarkacen da tayi babu wanda suke magana dashi sosai kamar Elias, wata irin shakuwa sukai a satika biyu, har sun koma da hirar su ta WhatsApp, yakan kirata da daddare ta shiga bandaki ta amsa a tsorace kar Asma ta farka taji ta, tasan bakar shaida irin tata, tsaf zata kwashe ta gayawa Anty, tayi mata sanadin wayar gabaki daya. Hankalinta a tashe takanyi wayar na mintina ta kashe. Dan dai taga hotunan Elias din, ya tuttura mata, ya kuma yi mata kyau sosai, dan ya iya daukar wanka. Cikin wata daya kuwa, kaf kawayenta babu wanda baisan labarin Elias ba, wasu suna dan ganin shi a room, amman da yake bai cika magana ba, ba wani sanin shi akayi ba. Sosai sukan yi hira, wani lokaci tana assignment suna taba hirar su. Lokaci daya Elias ya nuna ma Hindu yana so su hadu, hankalinta ya tashi, amman bata so ta nuna mishi ita din ba babbar yarinya bace kamar yanda ya dauketa. Ranar juma'a da daddare yai mata maganar, washegari Asabar tace ma Anty zata shiga gidansu Biebee dan suyi assignment din Nahwu, tunda anyi hutun kwana uku a islamiyar, daya cikin Malaman su ya rasu, sai ranar Monday za'a koma. Anty bata hanata ba, gidansu Biebee dasu kusan an zama yan uwa, tana shiga suka gaisa da Hajiya mahaifiyar Biebee din Hindu tajata suka shiga daki "Ke wajen ki nazo fa, Elias naso mu hadu, wallahi na rasa yanda zanyi" Wani irin kallo Biebee takeyi mata da yasa ta fadin "Dan Allah Bie, ki fadamun me ya kamata inyi" Gyara zama Biebee tayi "Me ya kamata kiyi banda ki fada mishi ba'a barinki zance a gida, sai kin gama secondary, in zai iya jira ya jira. In bazai jira ba yai gaba" Dafe kai Hindu tayi, Biebee ba zata gane ba, matsalarta daya da ita kenan, komai a tsaye takeyin shi babu wata kwana, yanzun ma dorawa Biebee tayi da fadin "Ni nace miki baiyi mun bama, hoton shi duka a waje daya, kuma yanayin pattern daya, me yasa ba zai turo miki hoton shi a tsaye ba? Ke ni bai mun ba" Langabar da kai Hindu tayi "Bie ki rufamun asiri dan girman Allah, so kike yaje room yana fada musu yarinya ce ni, ina tunanin da mu hadu wani wajen... Sai muje dake kice ma Anty zamuje dubiya... In dake ne ba zata hana ba" Tunda Hindu ta fara magana Biebee take girgiza mata kai "Ku hadu ina? Idan dan yankar kai ne fa? Hindu ki rufama kanki asiri" Hannunta Hindu ta kamo tana fadin "Bie mana.... Dan Allah kimun wannan abin daya. Ki taimaki rayuwata" Hannunta Biebee ta fisge tana mikewa, bada ita za ayi wannan rashin hankalin ba, ko bakomai tana jin tsoro, yanzun duniyar babu gaskiya. Shisa inda duk tace zataje bata biyawa wani guri, tana tsoron kar taje wani abu ya sameta, ko babu mutuwa akwai hatsari, akwai rashin lafiya da take dirar maka babu sallama. Idan tace zataje tudun wada a gida, sai ta wuce Malali, wani abin ya faru, ko mutuwa haka iyayenta zasu kasance cikin tunanin me ya kaita malali har karshen rayuwar su. Tunani irin wannan yana hanata abubuwa da dama. Amman Allah yayiwa Hindu wata baiwa ta samun abinda take so a wajen mutane, bai dauketa mintina talatin ta shawo kan Biebee ba, amman da sharadin inda sukace zasuje nan zasu. In yaso sai Elias din ya same su a bakin hanya su gaisa su wuce. Hakan yayi ma Hindu, hira suka dan karayi tana tashi ta wuce gida ta fadama Elias gobe zasu hadu, amman zata fada mishi ko karfe nawa da safe, sukayi hira dashi tukunna ta kwanta tana jin yanda zuciyarta take lugude, gani take kamar Anty zata shigo dakin ta dauki wayar in tayi bacci, tashi tayi zaune ta dauki wayar tana goge chats dinsu duka, ta goge kiran wayar sannan hankalinta yadan kwanta. Ta samu bacci ya kwasheta. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 11 "Na hango ki" Hamza ya fadi yanda ya sauke kalmar 'G' din da take cikin 'Hango' din na fito da fulatancin da yake harshen shi, ita kam ta cikin tabaran fuskarta take yawatawa da idanuwa ko zata hango shi "Ban ganka ba ni kam" Cewar Hindu tana danne tambayar da take sonyi mishi ta kowacce irin mota yake ciki. Bataso ya fassara tambayar da ko tana so tajini dan tasan darajar da zata dora motar tashi a kai "Zaki ganni nan da mintina biyu, zan yo kwana ne..." Titi take kallo sosai, zuciyarta na lugude kamar zata fito daga kirjinta "Gani nan afuwan....yanzun nan" Hamza yake fadi cikin sigar da yasata yin yar siririyar dariya, tana jin wani irin shauqi na lullubeta da batasan daga inda yake tasowa ba. Kafin ta hango wata mota ruwan madara kirar Range Rover da baqin gilasai da akema laqabi da tinted, ta tsaya a gabanta "Gani nan na karaso" Taji muryar shi a kunnenta ta cikin wayar, kafin ya sauke gilashin motar hadi da sauke wayar daga kunnen shi, yana saka Hindu jan wani numfashi da taji yaki kai mata inda ya kamata. Da alama suspenders ne a jikin Hamzan, dan tana ganin belt din kayan dayake a kafadun shi ya zagaya zuwa bayan shi inda take da tabbacin yana maqale a mazaunin shi jikin wandon shi, rigar shi fara kal mai dogon hannu, ya dora hular hat daya dan tura baya, idanuwan shi kal-kal dasu kamar bai taba cin karo da hayaqi ba, tamkar hawaye basu taba zama a cikin su ba balle su bata asalin hasken da suke dashi. Yanayin fatar shi yafi komai ba Hindu mamaki, batasan ko idanuwanta bane kawai suke ganin salqin da yakeyi saboda kyawun da yai mata. Bata taba yarda da cewa mutum na maka kyau har kaji numfashinka na tsai-tsayawa ba sai yau, sai yanzun da ta rasa yanda zatayi ta dauke idanuwanta daga kan Hamza 'Kice wani abu mana Hindu' Wata murya ta fada mata a cikin kanta 'Ki daina kallon shi kamar wata sakarai, kice wani abu' Muryar ta sake fadi, amman ta kasa ko motsin kirki balle ta iya furta wani abu. Hamza kuwa tun da ta fada mishi kalar Hijab din da take jikinta ya fara hangota, daga farko zai karya idan yace kalmar 'Hijab' din data furta bai mishi wani iri ba, fita yace zasuyi suci abinci, ba wajen wa'azi yace mata zasuje ba. Duk da hotunan da take dorawa da Abaya a jikinta, banda dankwalin kanta wasu lokuttan ba zaice ga kalar kayan da yake kasan Abayarta ba. Amman 'Hijab' ta mishi wani iri sosai. Bayason harkar rashin wayewa, tashin farko da suka fara magana batayi mishi kama da local ba. Sai da ya zagayo ya hangota sosai, sai yanzun kuma daya sauke gilashin mota yake kare mata kallo, bai taba tunanin mace zata saka Hijabi tayi mishi kyau har haka ba, duk da zaiyi komai dan ya daga hijabin yaga abinda take boyewa a kasan shi, amman tayi mishi kyau babu karya. Tabaran da ta sakane ya hana mishi ganin idanuwanta. Murmushi ya tsinci kanshi da yi hadi da fadin "Muje?" Sai lokacin Hindu ta iya daga mishi kai, tana samu ta motsa kafafuwanta dakyar ta zagaya ta bude murfin motar ta shiga. Wani irin kamshi mai sanyi na dukan hancinta. Haka kawai ta tsinci kanta da yin murmushi, zuciyarta take so ko yayane ta tsagaita da dukan da takeyi. Amman kamar da Hamza yaja motar ma zuciyarta kara dokawa tayi "Kin san yunwar da nake ji? Banyi breakfast bafa" Hamza ya fadi saboda shirun motar yayi mishi yawa. Kuma da gaske bai karya ba, wani irin bacci yayi, sanda ya tashi kuma ana jiran shi a wajen aiki. A gurguje ya shirya ya fita, yanzun ma sai da yazo zai taho yaga AbdulHafiz ya daukar mishi mota yabar mishi wannan da yake ciki, baisan me yasa yake son daukar mishi mota ba, ta AbdulHafiz din har tsada da komai tafi, sai yace ta mishi girma, dan Yayan shine ya bashi kyauta shisa yake dauka, bawai dan yana so ba. "Me yasa?" Hindu ta tambaya tana wasa da yatsun hannuwanta, rage gudun motar Hamza yayi yana dan kallonta kafin ya mayar da hankalin shi kan tuqin da yakeyi "Ba zamuyi haka dake ba, ba zaki fara mun kunya-kunya ba, bana so, ba zamu shirya ba idan kikace zaki fara jin kunyata" Wannan karin dago kai tayi tana dan juyar dashi ta kuwa yi sa'a shima ya juyo da nashi kan suka hada idanuwa, nata zata sauke yadan girgiza mata kai "Bance kunya ba abu bane me kyau, bana sone kawai. Don't be local mana Hindatu" Dan tari tayi kadan tana hadiye yawu saboda tunda take ba'a taba furta sunanta cikakke da yanayin da Hamza ya furta ba, tsallen da zuciyar ta tayi sai da tajita a makoshinta. Har wani zazzabi takeji yana shirin saukar mata. Kuma shi gaskiya ya fada mata, shisa duk tunanin shi, duk yanda ya hango da wahalar gaske ya iya auran cikakkiyar bahaushiya, bayason gidadanci, idan tace wannan sunkuyar da kan, amsa mishi magana dai-dai zata dingayi, yaune ranar karshe da zata sake ganin shi, zai kokarin hadiye kwadayin shi a kanta dan ba zai iya ba. Kuma zai karya idan yace bata burgeshi ba, kominta yayi mishi, komai nata yasa shi son daga hijabinta yaga sauran sirrikan da suke tattare da ita. Amman hakan ba zai yiwu inta fara da jin kunyar shi ba. Itama kokari takeyi taga tadan ce wani abu, amman yaune karo na farko da ta taba kebewa haka da wani namiji da ba muharraminta ba, a mota su kadai suna nufar inda bata ma sani ba "Ina zamu je?" Ta bukata, tana saka Hamza sauke numfashi, yadan daga mata kafadun shi "Ina kike so muje? Na fada miki yunwa nake ji ko?" Yar dariya tayi tana daga mishi kai "Good... Ina ya kamata muje?" Dan jim Hindu tayi, ita ba wani wajajen cin abinci ta sani ba "Duk inda kake so" Dan kallonta yayi yana daga girar shi duk biyun "Kin tabbata?" Ta jinjina mishi kai, yanda yake kallonta duk da na wasu dakika ne ya sa gwiwoyinta kamar an bubbuge su da guduma, duk sunyi mata wani irin sanyi. Yanda yake abubuwa kamar baisan komai kara mishi kyau yake ba na kara sakawa ya burgeta matuka. Numfashi ya sake saukewa, yana yanke hukuncin zuwa Byblos Restaurant da yake Abakpa, ta wajen Waziri Ibrahim Crescent. Suna da abinci kala-kala na kasa Najeriya, Lebanese harma da Mediterranean. Indai ba sauri yake ba yakan zo nan, wasu lokuttan kuma yai order tunda suna kaiwa har gida. "Kin gama assignment din jiya?" Kai Hindu ta girgiza mishi "Na ajiye, Electric nake son karasawa in huta" Murmushi Hamza yayi "Oye ko?" Hindu ta daga mishi kai suna dariya su biyun "Mutumin nan ya bata mana lokaci ba kadan ba" Idanuwanta ta juya "Kai ma kenan daka gama, kuma ance zai mana Settlement ne ko meye next semester" Sai da Hamza yadan kalleta cike da tausayawa yana girgiza kai sannan yace "Hindu" Wannan karin ita ta dan kalle shi "Oye zai kashe ku" Yanda yayi maganar ya bata dariya sosai, hira suke zaka rantse da Allah sunyi shekaru da sanin juna, ba yau bane haduwar su ta farko. Hamza na cikin mutanen da zasu sa ka sake dasu lokaci daya, bashida wahalar magana, kuma yasan yanda zai jaka da hira ko da bakayi niyya ba. Ba Hindu kadai taga haka ba, abokan shima sunfi so yayi magana da mutane a wajen aiki, musamman idan akace cinikin kudin aikinsu za'ayi. Sai kayi mamakin kudin da Hamza zai caji mutane kuma su biya suna fara'a. Yana da wannan baiwar ta samun abinda duk yake so a wajen mutane, saboda zai nuna maka kana da wani irin muhimmanci da bakasan kana da shi ba. Yanzun a yan mintina kasa da ashirin daya dauke su zuwa Byblos Restaurant, Hamza yasa Hindu tanajin kamar tana da wani muhimmanci mai girma a wajen shi, a cikin hirarsu ya tabbatar tasan irin aikin daya tsallake ya fito, har saida taji kamar bata kyauta ba, kamar ita dince ta roki ya fito bashi da kanshi ya nemi ganinta ba "Da ban sa ka fito ba, ba zaka sami matsala a wajen aiki ba dai ko?" Hindu ta tsinci kanta da fadi lokacin da Hamza ya sami guri yayi parking din motar, dan gabaki daya yasa taji bata kyauta mishi ba daya fito. Sai da ya murza mukullin motar yana kashewa, ya daga gilasan tukunna ya girgiza mata kai "Karki damu, it's worth it, nagan ki fa, shine abu mai muhimmanci yanzun" Murmushin jin dadi Hindu tayi, tana kallo ya bude murfin motar, itama hakan yasa ta bude nata bangaren tana fita. Sosai take jinta sama-sama. Tunda take babu wanda ya taba fada mata magana mai dadin wanda Hamza ya gaya mata yanzun. Ta jira Hamza ya zagayo, tana karema shigar shi da tayi matukar burgeta kyau, duk da takalman da suke kafarta ko kafadun shi kanta bai kai ba, dogone, tsayin shi fiye da wanda take mafarkin samu, hannun shi ya mika mata yana kankance idanuwan shi kamar yana so taga yanda girar shi take a ciki, da mamaki ta dakuna fuskarta, dan batasan me zata bashi ba, sai da taga ya matso dab da ita yana saka zuciyarta wani irin dokawa Jakar da take sakale a hannunta yadan kama, tana amfani da dayan hannunta ta zare jakar cikin sauri, dan batason abinda zaija ya tabata, sosai zuciyarta take mata wani irin lugude. Hamza nazarin duk wani motsinta yakeyi, amman baya iya ganin idanuwanta ta cikin tabaran balle ya fahimci kadan cikin abinda take tunani. Da dayan hannun shi ya rike jakar yana jerawa da ita hadi da fadin "Muje?" Kai Hindu ta daga mishi, duk da bugun da zuciyarta yakeyi a cike take taf da wani irin yanayi. A film kadai ta taba ganin namiji ya karbarma mace jaka, ko a tarin burinta bata tsawwala da abinda ake kira 'Public affection' ba, wato nuna kulawa ko kauna a bainar jama'a. Saboda abune da bai saba faruwa a Najeriya ba, duk kuwa kalar kaunar da take tsakanin masoya, ta hasaso faruwar abu irin haka idan suna kasar waje lokacin honeymoon dinsu, inda zasu barji soyayyar su batare da fargabar sa idon al'ummar Najeriya ba. Jerewa sukayi har cikin wajen, Hindu najinta kamar wata Sarauniya, musamman yanda Hamza yake janta da hira kadan-kadan suna murmushi. Sai ta hango hannunta sakale cikin nata, ta hango yara biyu, daya a gefen shi daya a gefenta, a lokaci daya tana hasosu yanda rayuwar auren su zata kasance, kafin taji muryar Dimples na katse ta da 'Sannu Hindatu Khan Bachaan' Kamar yanda takan fada mata idan tana wani zancen soyayyar, ko tana fadar abinda zasuyi ita da mijinta. Dimples kance indiyawa sune karshe dai a soyayya. Kuma Hindu batajin hakan, dan Korea sun shallake indiyawa ta wannan fannin, nesa ba kusa ba, amman gaddama da Dimples babu riba, shisa bata taba kwatantawa ba. Ko da zasu zauna ma, Hamza da kanshi yadan janyo mata kujera bayan ya ajiye jakarta akan tebir din da yake gabansu, yana zama ya kama bayan kujerar yadan tura, sannan yaja tashi ya zauna yana fuskantarta kamar bai lalata mata duk wata fita da zatayi da wani namiji da bashi ba har karshen rayuwarta. Dan sosai zata dinga auna duk wani abu da zai faru da wanda ya faru a tsakanin su. Hamza take kallo da har lokacin yaki nuna alamun yayi mata wani abu, asalima yanda yake nunawa kamar abinda ya faru ba bako bane a wajen shi, kamar abune da yakeyi yau da kullum, ga restaurant din ya kawatar da ita. Waiters din gurin tsaf-tsaf dasu, daya daga ciki yazo yana kawo musu Menu, amman sam Hindu ta rasa abinda zata ce a kawo mata, dan bama taji yunwa kwata-kwata, hakan yasa ta yanke hukuncin zabar hadin salad. Sai a zabin abin sha ta dauki cocktail. Gira Hamza ya daga mata da yasata dauka hakan sabon shine, dan yayi yafi a kirga daga haduwarsu zuwa yanzun "Me kike nufi? Iya abinda zakici kenan?" Kai Hindu ta jinjina mishi tana dorawa da "Banajin yunwa" Yanda ya tsareta da idanuwa yasata dan shagwabe mishi fuska "Da gaske" Kai ya girgiza mata "Ba zaki kalleni ina cin abinci ba aikam" Da kanshi ya kara cewa a hado mata da kaza sai spaghetti. Sannan ya zabi nashi shima, waiter din na tafiya dan ya kawo musu abubuwan da suka zaba din, gyara zama Hamza yayi "Is not fair kina ganin gabaki daya fuskata ni bana ganin taki" Murmushi Hindu tayi a kunyace, kafin tayi wani yunkuri Hamza ya mika hannun shi ya kama tabarau din fuskarta ya zare, yana sauke idanuwan shi cikin nata da suka firfito da alamar tsoro, tana tabbatar mishi da zaton da yakeyi a kanta. Ita din ba kamar sauran matan bace ba, Hindu dabance da duk wasu mata da ya taba cin karo da su, kan tebir din a kusa da ita ya ajiye gilashin yana fadin "Hakan yafi" Yasa ta sauke idanuwanta daga cikin nashi, wayarta taji tayi vibrating alamar shigowar sako, hakan yasa ta daukar jakarta tana ciro wayar. Bude sakon tayi ta whatsapp tana ganin a class group dinsune wani ya turo zanen da yakeyi dan a duba mishi ko da kuskure. Hamza ita yake kallo, bai saba yana zaune da mace hankalinta na wani waje banda kan shi ba, bama yaso kwata-kwata "Baki san ba kyau kina tare da mutum ki dinga danna waya ba?" Cike da sabon mamakin shi Hindu ta raba idanuwanta da wayar tana kallon shi "Ko waye ya jira sai bama tare, karya shigar mun lokacina dake, bana so..." Ya karashe maganar cike da ikon da kyawun da yai mata bai hanata ganin karfin halin shi ba, data dinta ta kashe tana mayar da wayar a jaka "Nagode" Hamza ya fadi yana sata cewa "Kana da rigima" Dan daga mata kafadu yayi "Nasani, kawai bai dameni bane tunda rigimar nasani samun abinda nake so" Siririyar dariya tayi, ko a littatafai kuwa bata tunanin ta taba ganin kalar shi, tunda yawancin mazan novel basa magana, ita ya kamata ace tanata mishi surutun da tasan ba zata iya ba, amman shi yake ta mata magana bai damu ba, ta dauka tana son namiji shiru-shiru sai yanzun da Hamza yake zaune a gabanta. Abincin su da ya saukane ya ceceta, dan batasan amsar daya kamata taba Hamza ba. Kallon abincin takeyi tana ganin kamar daga Instagram aka ciro shi aka ajiye a gabansu saboda yanda ya qawatu. Robar ruwa Hindu ta bude tana dan kurba saboda yanda taji makoshinta ya bushe. Tana kallon Hamza ya fara cin abincin shi a nutse kamar bashi da wani abu mai muhimmanci daya wuce cin abincin, itama salad din ta faraci kadan, tana jin yanda yake dira cikinta da wani irin yanayi. Hamza na kallonta ta kasan idanuwan shi, sai dai baya surutu idan yanacin abinci, bama yaso wani yai mishi wata magana, yasan bai isa ya zabi hanyar da zai mutu ba, yana dai kokarin kaucema faruwar hakan ta hanyar shaqewa da abinci. Shi bai ga dalilin da zaisa a dinga magana ba idan anacin abinci. Ita kuma ta saba tana cin abinci tana danna waya, yanzun sai shirun yai mata wani iri, tana ganin kamar hankalin Hamza na kanta, lokaci zuwa lokaci take dago idanuwa ta kalle shi, amman sai taga abincin shi yakeci a nutse. Dakyar taci rabin salad din da yake gabanta, dan kar yace yasa an kawo mata abinci bataci ba, shisa tadan dibi taliyar tasa a bakinta, ta kuma yi mata dadi, ba zata iyaci bane ba kawai. Kazar ma kadan ta gutsira, ta ajiye cokulan tana ci gaba da kurbar lemon gabanta. Har Hamza ya gama dan kadan ya rage a tarkacen abubuwan a aka kawo mishi, wasu ma bata taba ganin su ba balle tasan sunayen su. Masu kudi na sha'ani da rayuwar su, ta fadi a ranta "Karki ce mun kin koshi" Hamza ya bukata, kai tadan daga mishi tana murmushi "Hmm..." Ya furta yana dorawa da "Kin kyauta" Ya dauki wani dan kati da take tunanin kudinsune a rubuce ya duba, hannu taga yakai aljihun shi yana fito da wallet din shi, sai dai tayi mamakin yan dubu-dubun da taga yana kirgawa yakai na dubu goma sha, ya bude dan katin ya saka a ciki, sannan yadan kalleta "Muje?" Ta bukata, ya jinjina mata kai, a tare suka mike, Hindu na daukar jakarta, da tabarau ta makala a fuskarta,har lokacin tana mamakin yawan kudin da kuma dan abinda sukaci. Suna shiga motar yaga wayar shi na ta haske, dauka yayi ya duba "Dammn" Ya furta yana mayarwa ya ajiye. Yaga Hindu bata wani ci abin kirki ba, yaso su biya ko Havilah ne. Yasan mata bakowa kecin abinci irin haka ba, sunfi jin dadin ci a gida, amman Murjanatu, Autar su tasa yasan mata akwai san kayan zaki, duk da shi baya ta'ammali da kayan zaki, amman tana son desserts sosai "Wajen aikine..." Yai maganar kamar yayi mata wani laifi yana dorawa da "Nayi alkawari I will make it up to you, In shaa Allah, zamu kara samun time da aikina ba zai shigar mana ba, kina jina?" Kai Hindu ta daga mishi tana murmushi "Karka damu, babu komai" Wani numfashi ya sauke yana fadin "Nagode" Kafin yaja motar, yanzun ma hirar sukeyi, yana bata labarai kananu da suka shafi aikin shi, yana sa tana karajin dadin kasancewa da tayi tana karantar Architecture saboda yanda take fahimtar hirar tashi. Inda ya dauketa suka karasa yasa shi cewa "Ina zamu bi?" Tun kafin ya karasa Hindu take girgiza mishi kai, bugun zuciyar data samu ya tafi ya dawo mata sabo, ta ina Hamza zai fara shiga lungun gidan su da ita, idan wani daga cikin gidan ya fito yaganta ta ina zata fara musu bayanin dalilin da yasa take cikin motar shi "Karka damu, ka saukeni anan" Kallonta yayi da yake fassara 'kice mun wasa kike' Ganin bata da shirin ce mishi wasan takeyi yasa shi fadin "Saboda me?" Hadiye yawu tayi tana sauke numfashi, ta rasa abinda zatace mishi "Kayi hakuri kai dai, kabarni zan karasa, kaga kaima ana jiran ka" Badan yaso ba, ba kuma dan da gasken ana jiran shi ba, amman baiji dadin yanda zai ajiyeta a bakin hanya ba "Zamuyi waya. Ki kula da kanki" Ya karasa maganar yana dan sauka gefen titi dan suyi sallama da kyau, kai Hindu take jinjina mishi "Nagode sosai" Hannun shi ya mika mata, sai dai wannan karin sauka zatayi balle tayi tunanin jakarta zata bashi, ga idanuwan shi daya kafeta dasu, haka kawai yaji idan bai rike ko da hannunta bane komai zai iya faruwa, yanayinta da komai nata yasa wasu kusoshi kwancewa cikin kan shi, ganin kallon da take mishi yasa kama hannunta, yana share yanda take kallon shi kamar shine karo na farko da wani namiji ya taba rike mata hannu, dan matsa yatsunta da yaji cikin nashi yayi. Ko ba nata ba yana son yanda hannuwan mata suke, sirara, yana son jin yatsun mace a cikin na shi, balle nata da haka kawai yake ji kamar an halicci nata yatsun ne don ya rike. Tunda take a tunaninta tasha hango lahira, amman bata taba hangota wani sashi na jikinta a wuta ba, tana neman tsari daga wuta sau bakwai da safe, bakwai da dare a rana, idan tadan kone ko yayane takan yini tana neman tsari daga azabar wutar da batasan zata iya ba, amman yanzun kam har kaurin konewar da hannunta zaiyi a wuta takeji a hancinta, ta hango shi gashi can an kama an tsoma yana babbakewa, ta kuma rasa abinda ya daskarar da ita ya hanata yin wani yunkuri wajen hana Hamza rikewa, da ya murza yatsunta har ranta taji girman zunubin. Tana kallon shi ya kama hannun nata yana saka labban shi cikin tsakiyar tafin hannunta ya sumbata, muryar shi can kasan makoshi ya furta "Sai munyi magana" Hadi da sakin hannun nata kamar komai bai faru ba, kamar bai manni zunubai a labban shi ba, dakyar ta iya daga mishi kai tana bude motar ta fice. Hanya ta mike, lungun da zai kaita gida tana ta kokarin ganin hannun da Hamza ya sumbata bai taba ko ina na jikinta ba, karta goga tarin zunubin da taji yasa hannun yayi wani irin nauyi na ban mamaki "Allah ka yafe mun... Oh Allah na... Me ya faru haka" Take fadi ita kadai kamar sabon kamu, a gefe daya na zuciyarta tana jin inda Hamza ya samu sabon waje ya manne. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 26 Duniyar tayi mishi tsaye waje daya, kallo daya zakai mishi kasan baya cikin kwanciyar hankali, damuwar da take tare da zuciyar shi shimfide take kan fuskar shi "Me yake damun ka?" AbdulHafiz ya tambaye shi, kai kawai ya iya girgiza mishi yana fadin "Babu komai" Ya kuma ji dadin yanda bai matsa mishi da tambaya ba, saboda bashi da wata amsa tsayayya da zai iya baiwa AbdulHafiz din. A watanni biyun nan cikin Hindu ba karamin wahala yake bata ba, bata kwana biyu ba'a kara mata ruwa ba. Gara cikin satin nan yaga ta fara warware wa, watannin nan sune masu tsayi a rayuwar shi tunda ya mallaki hankalin shi da yayi su batare da mace ba. Shisa a satin nan har cikin idanuwan Hindu yake ganin yanda ko kusa da ita ya zauna a tsorace take da shi. Wuni yake bulbulawa cikin shi giyar da yakejin tana dakushe mishi abinda yake ji. Abu daya Hindu ta kula da shi yanzun, in har yana gida, yana manne da wayar shi, ita kanta ba dadin take ji ba, sati daya kenan da take samu taci abinci ya zauna, duk tayi wata irin rama. Duk abin Anty sai da suka zo suka duba ta, Baba kuwa zuwan shi hudu, duk idan ya dawo aiki yakan biyo ya dubata, duk da sau daya ta samu ya shigo cikin gidan harya zauna ya sha ruwa. Sauran a tsaitsaye suke gaisawa, ya bata tarin siyayyar kayan ciye-ciyen da take lodawa a fridge, wanda zasu lalace ta baiwa mai aikinta, tunda ita ba iyaci takeyi ba. Yau ta rasa abinda zatayi, da Dimples tace zata shigo ta saka mata films, saboda zataje gidan su Biebee da bikinta sauran satika uku, suna kan hidimar da ake ta faman yi babu Hindun saboda laulayin da take fama da shi, ta kuma kira cewar ba zata sami shigowa ba, dan wajen aiki basu barta tashi da wuri kamar yanda tayi tsammani ba. Tata wayar ta dauka, yanzun ta zama yar kallo a twitter saboda bakin kishi irin na Hamza, da tayi tweet ma idan yahau yaga maza sun yi magana baya ce mata komai, sai dai ta nemi tweet din ta rasa, ya goge. Tasan duk inda yake yana gab da dawowa yanzun tunda har anyi sallar magriba. A nan inda ta idar da tata sallar take zaune tana danna wayar. Fita tayi daga nata account din tana shiga na Hamza da taga tarin Notification, ga kuma sakonni da yawa ta DM. Shiga tayi duk yanda zuciyarta take fada mata karta yi hakan, karta jama kanta abinda zai daga mata hankali, amman kuma wani bangare na zuciyar yana fada mata ta duba, tasan Mansy na nan tana bi mata miji, tana kuwa shiga, sakon farko nata ne "Shegiya mai tallar taba" Ta furta a fili, wani tuquqin bakin ciki na danne ta, shiga tayi tana ja ta koma daga farkon hirar da tayi mishi magana, tana duba lokaci, jiyane ma, karfe biyu na dare, saboda ita batasan darajar 'ya mace ba. Karfe biyu zata fara yi mata magana da miji, amsar Hamzan tagani, farko hira ce sukeyi mai tsafta, kafin Mansy din ta fara mishi wata magana da ta canza gabaki daya akalar hirar tasu, jikin Hindu babu inda baya bari saboda munin abinda ta kasa daina karantawa "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ta furta ganin yanda Mansy take cewa Hamzan ya duba whatsapp din shi ta tura mishi hotunan da video din da ko ita da yake mijinta batajin zata taba iya tura mishi su, ko dan tsoron kar wayar tashi ta fadi, ko a sace da irin wannan abubuwan a ciki da ya kamata ace idanuwan shine kawai zasu gani. Kife wayar tayi, ko ina jikinta bari yake saboda tashin hankali. Ga hawayen da suke cike da idanuwanta sunma ki zubowa saboda zafin da zuciyarta takeyi, daukar wayar tayi tana fara rubutu "Dan uban babanki duk hotunan da kika tura mishi suna wayata, da screenshot din wannan hirar gabaki daya. Idan bakiyi blocking din shi, kin daina mishi magana ba sainayi posting hirar nan da duka hotunan har da videos din a TL kowa yaga karuwancin da kike bin mazan mutane kina yi. Wawiya, jaka, ballagaza da batasan inda yake mata ciwo ba, tsohuwar banza kawai" Sai taji zuciyarta tayi mata dan sanyi, da ace zata ga Mansy din ido da ido ta kamata ta jibga kamar ganga sai tafi hucewa, sau biyu tana sake sallar isha'i saboda ta farkon bata da tabbacin ga abinda ta karanta a ciki saboda tashin hankali, tana sallar tana kukan wannan jarabtar da take ciki, batasan ranar da Hamza zai bar zuciyarta ta samu hutun kirki ba. Ta dauka yanzun cikin jikinta yasa shi ya nutsu, duk tunanin da takeyi ya daina shan koma meye taga yasha a daren ta na farko a gidan, saboda bata kara ganin shi cikin maye irin wannan ba. Addu'ar da ta duqufa tana mishi ta karbu ta wannan fannin. Duk da ta fara dora laifin wannan abin da taga sunyi da Mansy a kanta, watakila da ace bata nuna mishi gazawarta a satin nan bayan hakurin da yayi da ita na watanni biyu ba da bai komawa Mansy ba, da abinda ya faru bai faru ba. Tana sallame sallama sallah yana bankado dakin kamar zai karya kofar hadi da fadin "Hindu!" Yana hanyar dawowa, kan shi yayi bala'in nauyi saboda abinda yasha mai karfine, kuma babu wani abincin kirki a cikin shi, so yake yana shigowa gida ya watsa ruwa ya kwanta tunda yayi isha'i. Ya kusa gidan ma yaga kiran Mansy, harya yanke bai daga ba, sake kira tayi bai daga ba. Ganin tayi mishi kira na ukku yasa shi dagawa, dan ya tabbata akwai dalili me karfi da yasa take kiran shi, kukan da yaji tanayi ne yasa shi sauka daga titi yana yin parking gefe, yanda kan shi yayi nauyi ba zai samu nutsuwar yin tuqi da amsa wayar a lokaci daya ba "Ki natsu kimun magana Mansy, bana gane me kike fadi, me ya faru? Me akai miki?" Ya karasa tambayar da fulatanci, itama da shi take mishi magana "Matar ka, matar ka taga hirar mu jiya, ka duba whatsapp kaga me tace mun. Hamzy ka rufamun asiri ka bata hakuri karta doramun hotuna a tl, in dai kaine na hakura wallahi..." Cike da rashin fahimtar abinda take fadi yace "Bangane ba..." Amman kuka takeyi sosai, abinda bai taba gani ko jin tayi ba tunda yasan ta da shi "Kai kasan a duniya kai kadai kake da wannan hotunan, ko na taba kasadar turawa duk iskancina saboda na yarda da kai. Wallahi ba zan yafe maka ba idan suka bazu, kayi mata magana" Mansy ta karasa cike da kashedi tana kashe wayar, hakan yasa shi duba whatsapp din shi ko zai fahimci abinda take fadin, screenshot ne na sakon da Hindu ta tura mata "What the fuck!" Ya furta a harzuqe yana sauka daga whatsapp din ya kira lambar Mansy "Bata da hotunanki ko daya, chats dinne kawai da ta gani. Ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru" Yana jin ajiyar zuciyar da take saukewa "Dan Allah Hamza..." Kai yake girgizawa "Na fada miki karki damu, babu abinda zai faru, akwai dalilin da yasa kika yarda dani tun daga farko, ki sake yarda da nace miki babu abinda zai faru" Ya fadi, kafin tace wani abu ya kashe wayar, Allah ne kawai ya karasa kawo shi gidan lafiya saboda yanda yake fisgar motar. Bai aiki Hindu duba mishi chats ba, baiga dalilin da zaisa tayi abinda tayi ba, saboda bata da wata alaqa da Mansy, da shi take da, shikuma shine yake da alaqa da Mansy, shi ya kamata ta zaga ba ita ba. Idan mutuncin shi yake bukatar ya zube zaiyi da kan shi ba saita yi mishi ba "Me kike tunanin kinyi?" Ya tambaya yana kallonta, itama kallon nashi takeyi cike da tsantsar mamaki "Me kake tunanin nayi?" Ware idanuwan shi yayi yana wani murmushin takaici mai sauti "Ki amsa mun tambayata, akan me zaki tura mata wannan sakon? Me tai miki da zaki zageta?" Mikewa Hindu tayi tana son saka idanuwanta cikin na Hamza, tana son ganin da gaske ne maganganun da yake fada mata "Idan da kunya a idanuwan ka zaka tsareni da wannan tambayar dan na zagi karuwar ka?" Ta furta, kalmar karuwar shin na fitowa daga wani lungu na zuciyarta da yake mata ciwo na gaske "Kin taba ganin alamar kunya a idanuwa na?" Ya tambaya yana hade space din da ya rage a tsakanin su yana tsareta da idanuwan nashi "Karuwa ta ce, shisa nake tambayar dalilin da zaisa ki zageta tunda baki da alaka da ita, ni ya kamata ki zaga ba ita ba inda kina da hankali" Wata irin dariya taji ta kubce mata mai hade da wani sautin kuka, duk abinda yake faruwa, duk fadan da sukayi akan sauran yan matan shi, musamman Mansy da ta zame mishi wani bala'i da Hindu ta rasa ta inda zata fara tarbar shi, yaune karo na farko da take jin dana sani na tasowa daga dan yatsar kafarta yana tattarowa daga dukkan gabbanta kafin ya samu wajen zama a kirjinta "Kaine babban marar hankali wallahi, da kana da hankali ba zaka tsareni kana fadamun wannan maganganun akan wata ballagaza ba, kaine babban mahaukaci Hamza" Da mamaki yake kallonta, a tsayin rayuwar shi banda AbdulHafiz babu wanda ya taba kallon shi ya kira shi da marar hankali cikin raini haka "Ni kike kira mahaukaci?" Ya tambaya, kai ta daga mishi tana saka hannuwa ta goge fuskarta da wasu hawayen bakin cikin suka sake zubowa "Na kiraka mahaukaci, wallahi yaune na fara tir da mugun halin ka Hamza, na dauka zaka canza, na dauka zan iya canza ka, meye a jikin Mansy da ni bani da shi? Me take maka da ni ban iya ba?" Tayi mishi tambayar da ta dade tana yiwa kanta, yau ta bari ta fito fili saboda da gaske a tsorace take, tsoro bana wasa ba da halin Hamzan, a karo na farko tanajin kamar bata isa ta canza shi ba, kamar shi din bayason canzawa, in kuma bayason canzawa ita bata isa ta canza shi ba "Ka fadamun abinda take dashi da bani da shi, ka fadamun me kake nema a jikin ballagazar nan!" Juyawa yayi da nufin fita yabar mata dakin, saboda sosai kalamanta suke kara harzuqa shi, musamman da yakejin tana gab da fada mishi tayi dana sanin auren shi, idan shi bai gaya mata yayi nata ba, ba zai jira ta fara fada mishi ba "Ina zaka je? Ka amsa ni inji, ka fadamun abinda yake jikin karuwar taka da bani da shi" Juyowa yayi, muryar shi can kasan makoshi yace "Idan ba zaki iya karanta chats dina kiyi kukan ki ke kadai ba, karki sake shigar mun. Karki sake mun makamancin abinda kikai mun yau, wallahi zan baki mamaki, baki sanni ba har yanzun" Sosai take kallon shi tana sake sa bayan hannunta ta goge fuskarta "Wallahi idan yanzun na sake hawa saina zagi uban uwar Mansy, kana jina, saina zageta, akanta ne kake fadin zaka bani mamaki. Allah ya baka iko....na zageta, Hamza na zageta ka..." Bata karasa ba saboda marin daya dauketa da shi, wata irin walkiya na giftawa ta cikin idanuwanta, da gaske ne, littafi bai mata karya wajen rubuta kalar marin nan ba, ta runtsa idanuwanta tana bude su yafi sau hudu dan ta tabbatar da kwayar idonta bata fado ba. Kafin ta dafe kuncin, ta nemi hawaye ma ta rasa dan azaba "Na fada miki zan baki mamaki kinqi yarda ko?" Ya furta da wata irin murya dashi kanshi ta sauka kunnuwan shi da wani yanayi, jikin shi har bari yake saboda bacin rai, ya dauka Auta ce mace daya a rayuwar shi da zai taba dagama hannu. Saboda bai hango Hindu zata tunzura shi haka ba, zata saka shi jin son ya jibgeta har saiya daina jin nauyin da kanshi yayi "Mar... Mari, ni ka mara? Akan Mansy ka mareni?" Tsaki yaja mai sauti, yana wucewa hadi da jan kofar da karfi, kafafuwanta da taji suna rawa suka sakata zama, amman jikinta bari yake, dole ta kwanta, tanajin hawayen da suke bin gefen fuskarta, ga kirjinta da yayi nauyi kamar zai bude, mutanen da suka taba marinta basu da yawa a rayuwarta, ta kuma manta ranar da hakan ta faru. Mijin da take karkashin inuwar aure da shi, ko a mugun mafarki bata taba hango zai daga mata hannu ba, ko da hakan ta faru ba'a kan karuwar shi ba. Ba akan ballagazar da ko kira ta 'ya mace ba zata nuna mata ba, ballantana kuma daraja. Ta sha jin labarai na cin mutunci irin na da namiji, amman nata ne mafi muni da taci karo da shi a tsayin rayuwarta, yau ita Hindu, ita Hamza ya daga hannun shi ya dauke da mari saboda karuwa...! *** "Ban gane yace zai saka ranar da za'a kwashi kaya ba, sai ku ka taho kukuma?" Baba yake fadi ranshi a matukar bace yana kallon Muhsin da Huzaifa "Baba bana so in biye mishine ni, saboda kar ayi abinda za'aji kunya ko da sauran zama" Huzaifa ya fadi a tausashe "Wanne sauran zama? Shi da wanene zasuyi sauran zaman?" Shiru su Huzaifa sukayi, cikinsu babu wanda baisan halin Baba ba idan ranshi ya baci "Ya kore muku 'yar uwa cikin dare da tsohon ciki har kuyi tunanin akwai sauran zama a tsakanin su. Halan bakwa kishin ta ne?" Kai Huzaifa ya girgiza, yana shirin magana Muhsin yadan zungure shi alamar yayi shiru, tsaki Baba yaja "Ku koma ku kwasomun kayan yarinya dan banason su kara kwana a gidan wannan marar mutuncin" Muhsin ne ya fara mikewa yana ma Huzaifa ido, shima ya mike suka fice daga falon "Kasan halin Baba babu abinda zai saurara yanda ran shi ya baci, kuma Hindu aka taba, ni wajen aiki zan wuce, zuwa anjima watakila ya huce yanda zai iya fahimtar mu" Kai Huzaifa ya jinjina "Allah dai ya rufa asiri. Ni naso inga Hindun ma wallahi" Dan murmushi Muhsin yayi "Ka rufawa kanka asiri ka wuce, anjima ka dawo kaganta. Yanzun wallahi Baba kaniyar mu zaici" Shi Huzaifa ma sam ya kasa yin ko da murmushin ne saboda takaici. Shi kan shi idan za'abi shawarar shi za'a hakura da maganar Hindu ta koma gidan Hamzan nan. Tare da Muhsin din suka fice daga gidan, da shawarar duk idan kowa ya dawo daga neman halal dinshi zasu sake dawowa suyi ma Baba magana ko zai fahimci abinda suke son ya fahimta din. Cikin gidan kuwa, Anty najin duk abinda yake faruwa, idan ta gwada yiwa Baba magana ita kanta ranta ne zai kara baci fiye da yanda ya baci yanzun. Shisa ta nufi dakin Asma tana samun Hindu a kwance ta zubawa bango idanuwa, sai taji tausayin ta ya cika zuciyarta "Hindu..." Ta kira da wani irin yanayi a muryarta, tana saka Hindun tashi dakyar ta jingina bayanta da gadon, karasawa Anty tayi tana shiga cikin dakin sosai. Ta zauna gefen gadon "Hindu ke kadai kikasan meya hadaki da mijin ki, kamar yanda ke kadai zaki taushi zuciyar Babanku yayi hakuri abi komai a hankali..." Tunda Anty ta fara magana taji idanuwanta sun ciko da hawaye "Anty ki kyale shi kawai, ni ba zan taba komawa gidan shi ba, wallahi nagaji, tunda na fito na fito kenan da yardar Allah" Ta karasa maganar tanajin wani zogi da ba sabo bane a zuciyarta. Karfin tahowa gidane bata da shi daman tun watanni biyun da suka wuce, da tuni ta kamo hanya ta gudo daga gidan auren daya zame mata qangin da bata tana hangowa ba, daga auren mijin da kowa zau kira da kyakkyawa amman a idanuwanta sai da ya juye ya koma kamar dodo. Ba auren Hamza kawai take son gujewa ba, gabaki daya kalmar aurene bata son ji "Hindatu..." Anty ta kira da wani irin yanayi a muryarta, kai Hindu take girgiza mata, tana wani irin gunjin kuka me sauti "Anty karkice inyi hakuri, ya rigada ya sakeni, komawa ba zabi bane ko da ina so..." Hindu ta karashe, ballantana tunda ta shigo gidan takejin tana shakar wata irin iska mai sanyi da ta kwana biyu bata shaqi irinta ba. Ya saukake musu auren daya zame musu karfen kafa. Da kan shi ya sauke aurenta daya kira da kaddara "Kaddarar auren ki ce kaddara ta farko da nayi dana sanin ta Hindu a duk kaddarorin da suke cikin rayuwata" Ko kadan baya dana sanin kaddarar bin mata, kaddarar shaye-shaye sai ita, sai aurenta. Hamza ya gama cire mata duk wani kyale-kyale na aure da take tunani, taso MIJIN NOVEL, a sujjadarta ta roki MIJIN NOVEL, sai dai bata roka da kalar halayyar shi ba, har a zuciyarta idan ta hasaso, kudin, kyawun da soyayyar kawai take gani. Ta dauka ita kadai ta isa ta rike auren su, bata dauka aure ya wuce duk wannan ba. Hamza ya bude idanuwan ta, ya wanke tunaninta tas, ya dasa mata neman asalin dalilin da yasa aka saka aure a cikin jerin ibadu "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Anty ta fadi, wani irin daci na zauna mata a zuciya, kalmar saki abuce mai muni a duniyar ma'aurata komin karfin dalilin yin hakan kuwa. Ko labarin saki taji sai zuciyarta ta tsinke, yanzun da labarin ya fito daga bangaren ta, daya faru akan 'yarta ji take zuciyarta ta matse a cikin kirjinta tana wani irin ciwo "Allah Kai Kadai Kasan me Ka boye a cikin wannan lamarin. Allah Ka bamu juriyar cinye dukkan jarabtar da ka tsara mana" Anty take fadi a cikin ranta, kafin ta dora da "Alhamdulillah ala kulli halin" Tana cigaba da maimatawa, hannu Hindu tasa tana share hawayenta "Ya sakeni Anty..." Ta sake fadi, kalaman na zauna mata, ba kukan rabuwa da Hamza takeyi ba, kukan tarin abubuwan da ta hadiya a karkashin auren shi da tunanin zata iya gujema kawowa inda take yanzun. Kamota Anty tayi, a karo na farko da hakan ya faru, gyara zamanta tayi tana kwanciya ta dora kanta a cinyar Antyn, kuka take kamar zuciyarta zata fito, kuka take yau da take samun lallashin da ta dade bata samu kalar shi ba, kuka tayi har baccin wahala yai gaba da ita...! * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 6 Zufa take da bata da alaka da zafin gari tana girgiza ma wayarta kai, dan bata ga dalilin da zatayi mata abinda tayi mata ba, ya kamata ta tabbatar da abinda take tunanin idanuwanta sun gani. Ga Asma bata da waya balle ta dauki tata, da dare baiyi ba tabbas bangaren Mama zataje ta karbo wayar Khadee "Dan Allah.... Dan girman Allah ku kawo wuta. Ku taimaki rayuwata" Take fadi kamar wadda ta sami tabin hankali, har a kasusuwan jikinta take son tabbatar da fuskar da tagani a jikin Hamza take, fuskar da ta sami waje tana zaunawa a zuciyarta. Lumshe idanuwanta tayi tana ganin nashi da ruwan kasane mai cizawa sosai, duk da kalace da ake samu a tattare da yan Nigeria, yankan idanuwan nashi abin daukar hankaline, shisa take so su taimaketa su kawo wuta, taga idanuwanta ne ko da gaske labban Hamza ne wani irin ruwan hoda da ba kasafai ake ganin su ba, ko a fina-finan kasashen ketare. Gashin kan shine bata kula ba, saboda askin shi buzz cut ne kamar, akwai hular rigar da take jikin shi. Tsaki taja tana juya kwanciya, ba karamar cutarta yan Nepa sukai ba, duk kalar zagin da yazo ranta shi take auna musu, caji ta jona tana kunna socket din, da sun kawo ba saita tashi ba, ta lumshe idanuwanta, fuskar Hamza na dawo mata kamar yana tare da ita, kafin barawon bacci ya dauketa. Duk da haka a daren bata san adadin farkawar da tayi ba, tana ganin basu kawo wuta ba har lokacin, sai ta sake komawa bacci, a haka har aka kira sallar asuba, Asma ta tasheta, saboda ba wani wadataccen bacci ta samu ba, ta dai godewa Allah bata da lakca sai sha daya, dakyar ta idar da sallah, zata fara Azkar suka kawo wuta, dan casbin hannunta tayi cilli dashi gefe tana nufar wayarta kamar zata kifa "Ikon Allah...." Asma ta furta, ko inda take Hindu bata kalla ba, wayarta take kokarin kunnawa, amman taki kamawa, dan tsayawa tayi tana kallon wayar har tayi 1% tukunna ta kunna tana cire mukullin sirrin da yake rufe da wayar. Data dinta a kunne take amman wayar bata gama loading ba, ji take kamar tayi me dan zumudi. Tana samu wayar ta fara loading ta shiga Instagram tana komawa shafin Hamza, sai da ta fara danna 'Follow' tukunna ta bude profile din shi, yanda na Facebook yake haka wannan din yake shima. Hoton farko da taci karo dashi da dare ta fara budewa, tana jin bugun zuciyarta a cikin kunnuwanta. Tafukan hannunta har wata zufa suke. Duk da ma'abota lafazi kance zuciya ita take ganin kyawu ba idanuwa ba, zata rantse tunda take kalle-kallen fina-finai bata taba ganin wanda yai mata kyawun Hamza ba, kamar komai nashi shiya zaba, daga hancin shi, idanuwan shi, girar shi da take a cike, da kasumbar da take kwance a fuskar shi data kara mishi wani kyau naban mamaki. "Oh Allah na" Hindu ta fadi zuciyarta cike da shauki, dakyar ta iya danna Back tana fita daga cikin wannan hoton. Wani hoton takai tana ganin su shida abokan shi, rigar shi wannan karin babu hula, amman mai dogon hannu ce, gabaki daya abokan shi sun hadu iya haduwa, babu wanda ba zata iya aure ba indai suna da kudi, kyawun su yayi mata, amman a hoton zaka gane yanda kyawun Hamza ya bambanta dana sauran. Yayi tagging din abokan a kasan hoton, bubbude tags din tayi tana following su duka hudun. Fodio, Arafat, AbdulHafiz, sai kuma Abdallah. Sannan ta dawo kan hotunan Hamza tana cigaba da dubawa, idanuwanta na tsayawa kan wani hoto shida wata mata mai matukar kyawu. Ya rubuta 'Ann❤'. Duk da sunyi kama dashi sai taga kamar tayi yarinta data haifi Hamzan, watakila babbar Yayar shi ce. Fita tayi tana shiga wani da ya saka 'Barka da Sallah' jikin shi sanye da farar shadda kal, har hular kanshi fara ce, kasa hakuri tayi ta zare wayar daga cajin tana share 'low battery' din data rubuta, da zumbuleliyar hijabin sallarta ta fice daga dakin zuwa bangaren Mama, tana shigewa dakin su Khadija ta sameta zaune da Qur'ani a hannunta "Khadee kinga Hamza kuwa? Tafdin... Kinga Hamza" Ta karashe maganar tana mikama Khadee wayar, data karba tana rikewa sai da takai karshen ayar da take karantawa, tukunna ta dago ido tana kallon Hindu da take numfarfashi kamar taga wani waliyyi, magana zatai ma Hindun ta dago wayar tana kallon hoton da yake kai "Allahu Akbar....Allah mai halitta" Ta fadi cike da jinjina Girma na Ubangiji da yake wanzar da halitta kala-kala a tsakanin yan adam, wasu kagansu munana, wasu tsaka-tsakiya, wasu masu kyau, wasu kuwa kyawunsu kamar ba mutane ba, kamar sun fito daga jinsin aljanu, Hamza na cikin kalar wannan mutanen "Hmm... Kibari kawai, wallahi na kasa yarda cewar shi dinne" Cewar Hindu, Khadee na dorawa da "Sai kace aljani, Ikon Allah kenan...." Wayar Hindu ta karba "Bari kiga sauran abokan shi ma" Tana komawa baya ta kai kan hoton Hamza da abokan nashi tana nunawa Khadee "Jiba rashin adalci, shi yana da kyau duk saiya kwashe masu kyau yake abokai dasu, jiba wannan bakin... Inalillahi... Duk yafi su kyau harda Hamzan" Leqa kai Hindu tayi "AbdulHafiz ne" Nata kan Khadee ta daga tana kallon Hindu cike da mamakin yanda akayi ta san shi "Duk na duba sunayen sune, kuma wallahi baifi Hamza kyau ba, tafdin, dan dai yana da dogon hanci shima" Sake dubawa Khadee tayi "Kai mun handle din shi ingani, kin san Allah yafi Hamza kyau, hasken fata kawai zai nuna mishi" Da sauri Hindu ta nemo sunan AbdulHafiz din suna shiga hotunan shi, na farkon da yayi murmushi har dimple din dake gefen fuskar shi ya loba ciki kamar ka saka dan yatsa "Haba Hajiyata... Kiga gaye iya gaye... Haske fa Hamza zai nuna mishi" Wayarta Hindu ta fisge "Ban wayata ni, ke baki san kyau ba sam, ni karki batamun rai dan Allah" Ta karasa maganar tana mikewa ta fice daga dakin, murmushi Khadee tayi kawai. Hindu taki yarda ne, amman AbdulHafiz duk yafi sauran kyau, amman dai-dai wani karkataccen wani, hankalinta ta mayar kan Qur'anin da take karantawa, dan shi yafiye mata alkhairi da maganar kyawun mutanen da basu san da zaman su ba, Khalifanta bashi da kyau kamarsu tasani, ba zatayi karya ba, amman shi dinne zabinta, kuma shidin take fatan ya zama alkhairinta. Hindu kuwa daki ta koma ta mayar da cajinta dan wayar ta samu sosai. Tasan halin yan Nepa, sam basu da wata daraja. Zasu iya dauke wutar duk da basu kwana da ita ba. Bandaki ta shiga ta watsa ruwa dan karta fara bacci ta farka a makare. Tana shafa mai ta kwanta. Tun tanajin motsin Asma da ita karfe bakwai da wani abu na safe za'a kaisu makaranta harta daina ji, bacci ya saceta, wani irin bacci cike da hargitsatsen mafarkin Hamza, da bayan ta tashi duk yanda taso ta tuna me ya faru a mafarkin ta kasa. Kiran Hauwa tagani har biyu, sai kuma text din data bude 'Ke kinji Arc Aboje ba zaizo ba, ya bada handout dai, ki karbar mun in kin shiga school dan Allah. Idan baki shiga ba kuma shikenan' Numfashi ta sauke, taji dadin rashin zuwan da Malamin nasu ba zaiyi ba. Amman dai ko wajen sha biyu zata shiga ta karbar musu Handout din, gara ta kwana a hannunta sai tafi samin natsuwa. Ita bama sosai take printing ko photocopy ba, tunda Huzaifa na da shagon da akeyi irin abubuwan nan, sai dai ta aro na wani a aji, sai ta bashi yayo mata, yanzun ma duk da yana kwana gida ba sosai take ganin shi ba, tunda aka saka mishi ranar biki yake wahalar gani, dan lokacin da baya wajen aiki tasan yana can zance. Duk wasu sun kwace musu Yayye suna gani, haka Muhsin ma da haduwa da yarinyar da maganar auren duka kasa da wata hudu, abin ya jima yana bata mamaki. Ko dan itama in dai wanda take burine ta samu bataga jiran da zata tsaya yi ba. Da wannan tunanin ta koma Instagram tana shiga shafin Hamza. Ya saka sabon hoto yana wajen cin abinci, daga kasan hoton cikin harshen turanci ya rubuta 'I can't wait to be home' Haka kawai sai taji zuciyarta ta kumbura ta cika fam, ba zai zauna acan kamar yanda duk wanda ya ketare daga Nigeria sukeyi ba, da alama Hamza na sha'awar dawowa gida Najeriya, hakan kuma yayi mata dadi da bata da dalilin shi. Hoton tayi liking ta shiga comment din tana ganin matan da suke ta cewa yayi kyau, kuma yayin, jar riga ce a jikin shi mai dogon hannu, da hula kamar ta sanyi itama ja, yadan turata baya, gashin kan shi ya fito, kunnuwan shi a rufe ruf da hular, sai dai kana ganin farin zaren earpiece din da alamu suka nuna yana manne cikin kunnuwan shi "Shegu mayu" Ta tsinci kanta da furtawa, a gefe daya tana jin dadin yanda Hamzan ko like bai danna akan comments din nasu ba ballantana ya kula su. Tana fitowa daga comments din tayi refreshing taga ya saka sabon hoto na wani gini, da alama shi yayi, bayan tayi liking sai tayi comment da hotunan zuciya har guda uku, dan duk yanda taso ta fadi wani abu daban ta kasa, ta rasa abinda ya kamata ta fadi da sauran mayun matan da suke ta mishi magana basu riga da sun fada ba. Ganin haka kawai comments din nasu yana neman bata mata rai yasa ta tashi tana some shirin fita makaranta. Tana gama shiryawa tsaf, ta dora baya akan kayanta tana yafa mayafin abayar saman kanta, yar jaka ta dauka ta saka wayarta a ciki, tana da kudi, tunda Baba na sati daya yake bata ta rike a hannunta, wani lokacin kuma yana kara mata kafin satin ya kare. Sai da ta shiga dakin Anty dan tayi mata sallama ta samu tana bacci, fitowa tayi taja mata kofar a hankali ta wuce makaranta. Handout din daya kaita kawai ta karba, da yake batai breakfast ba, yunwa takeji har wani jiri-jiri takeyi, karasawa tayi restaurant din su Elizabeth da yake nan cikin makaranta, taci doya da kwai da plantain. Sannan taji tadan samu nutsuwa. Ganin azahar har tayi yasa ta biya masallaci tayi sallah, tukunna ta fita daga makarantar zuwa gida. Tana shiga da sallama ta sami Anty zaune a falo "Sannu da gida" Ta fadi, Antyn na amsawa da "Yawwa... Yau da wuri?" Kai Hindu ta jinjina mata "Ai bamuyi komai bama, Handout kawai na karbo" Ta karasa maganar tana wucewa dakin su dan tasan da wahala Antyn ta sake cewa komai. Kayan jikinta ta rage, ta zauna kan gado tana zaro wayarta daga jaka, kiran Huzaifa tagani dayasa ta tunanin ko lafiya, dan haka ta danna tana bin kiran, yana dagawa da sallama "Yaa naga kiranka ne, ina dawowa daga makaranta wayar na cikin jaka" Dan jim yayi kafin ya amsa da "Nabar miki sako a whataapp, ki duba" Ya kashe wayar, da mamaki a fuskarta ta kunna data. Sakkonin ta bari suka gama shigowa tukunna ta bude na Huzaifa din tana soma karantawa: 'Akwai abokina Kamal, shagon shi kusa da nawa yake, ya taba zuwa gida, amman ba lallai ki gane shi ba. Tunda yaganki ya matsamun sosai, nayi miki magana ne yanzun saboda na yarda da hankali da nutsuwar shi. Duk da nasan shi wajen shekara hudu, sai da na kara bincike a kan shi kafin na yarda in hada ku. Bance sai kinso shi ba, amman ki bashi dama dan Allah. Zai zo anjima da yamma' Sake karanta sakon tayi tana dakuna fuska, duk da yaune karo na farko da wata magana data danganci Samari ta taba hadata da Huzaifan, watakila shisa taji zancen yazo mata daga sama. A wani bangaren kuma tana jin Kamal din bai mata ba tun kafin tagan shi, saboda tana da yakinin ko kafar Hamza bai kamo ba, ita kuma yanzun a zuciyarta Hamza yayi mata setting din wani standard da ba zata dinga auna duk wani namiji da zai kalleta da sunan soyayya. 'Allah ya kaimu' Ta amsa Huzaifan da taga yazo online 'Nagode Kanwata. Allah ya tabbatar mana da alkhairi' Sauka tayi kawai, ba zatace Amin a abinda bata gani ba, babu wani alkhairi ita idan ba ganin shi tayi ba. Tashi tayi ta fito tana fadama Anty zatayi bako da yamma "Daga ina? Waye shi?" Anty ta tambaya tana tsare Hindun da idanuwa "Bansan shi ba nima, abokin Yaa Huzaifa ne, yanzun yake fadamun" Kai Anty ta jinjina, fuskarta na saki da alamun yarda, tasan sukan taba kishin su a tsakaninta da Mama, amman babu ayar tambaya a kaunar da ke tsakanin yaran, Huzaifa ba zai taba aminta da yazo wajen Hindatun ba sai idan ya yarda da tarbiyar shi. Yanzun Hindun ce matsalarta, dan haka fafur duk yanda Anty taso ta da Musa kai tsaye tace bata son shi guntu ne. Tana kula da yanayin 'yartata, zuwa yanzun kuma addu'a take mata babu dare babu rana, Allah yai mata zabin alkhairi ya tsayar da hankalinta akan mutum daya, tagaji da dauka da saukewar da Hindu takeyiwa Samari, zata so tayiwa Baba maganar amman zai goyi bayan Hindu ne, tunda bata laifi a idanuwan shi. "Ki bashi dama Hindu, karki duba wani kyawu na halitta, ina fada miki bashi yake rike aure ba" Kai kawai Hindu ta jinjina ma Anty tana wucewa ta koma daki,bawai dan maganar ta shigeta ba, kyawu kam shine ginshiqin komai a wajenta, ita kanta Antyn Baba ta zabo, kuma bashida muni. Babu dalilin da zaisa ta saurari mummuna, shisa ma take addu'a babu gajiyawa. Kyakkyawa, fari, dogo, mai kudi na fitar hankali. Ba zata zo tana kwana a duhu ba, ko ta fito tana kikiniyar shiga kitchen, gara tasan aure tayi, taga banbanci daban dana gidansu, tana daki a dafo a kawo mata. Ba zataki ta auri mijin daya iya girki bama, tana bacci ya tasheta ya hada musu breakfast yanda akeyi a littafin Hausa. Ai soyayya dabance, in batajin shi har bayan zuciyarta babu abinda zaisa ta aure shi. * Karfe biyar taga kira da bakuwar lamba, dagawa tayi tana karawa a kunnenta "Assalamu alaikum..." Muryar shi ta daki kunnenta da wani irin sanyi da yasata gyara zama tana amsa mishi sallamar "Kamal ne, ya kike?" Sosai muryar shi tayi mata dadi, da dan murmushi a fuskarta tace "Alhamdulillah. Ina wuni" Amsawa yayi yana dorawa da "Afuwan, kinganni sai yanzun. Ina cikin gidan ku" Mikewa tayi "Gani nan fitowa" Ta fadi tana neman Hijab din data fito da ita, ta Asma ce ma, ita ba ma'abociyar saka hijabi bace, lokaci zuwa lokaci takan saka, bata dasu da yawa ma, tafi saka abaya, yanzun da zamani yazo saita dora Kimono wasu lokuttan. Bata dai san dalilin da yasa ta zabi hijabin ba yau. Ruwan toka ce da ta haskata ba kadan ba, fita tayi zuwa falo tana zira takalmanta da suke kofar daki, tana fita ta kitchen din gidan ta zagaya, dan akwai hanya ba saita bi ta falon Mama ba, daga nesa ta fara hango shi kan machine roba-roba a zaune "Tafdin...Machine..." Hindu ta fadi tana tabe baki, lallai zata sallame shi ya koma inda ya fito, karasawa tayi tana mishi sallama hadi da kare mishi kallo cikin raini, bataga dalilin da zaisa shi zuwa mata da jallabiya da hula tashi da kwakwa kamar sabon ladani ba, ga wani gemu da zata iya kirgawa tsai-tsaye kamar dole akace saiya ajiye gashin da yaki bashi hadin kai. Murmushi yayi hakoran shi na bayyana, guda daya ya karye, bashida muni, amman sam baiyi mata ba. Duk da jallabiya ce a jikin shi tana iya gane siririne ba kadan ba. Duk yanda tayi kokarin ganin tayi mishi fara'a ko dan Huzaifa saita kasa. Dan gaisawa sukayi, Kamal duk yanajin wani iri, shi yana zaune akan Machine ita tana tsaye, hakan yasa ya sauko daga kan Machine din shima ya tsaya, duk da yaga kujeru irin na robar nan a cikin gidan, amman Hindu batayi mishi tayin zama ba, yana ganin kamar baiyi mata ba daga yanayin fuskarta, ko kuma dan zuwan farko ne shisa, shi yake ta kokarin janta da yar hira, amman sai amsa shi take da "Umm..." Ko "Ai kam" Duk jinshi yake a takure, Hindu kuwa daya sauke daga Machine din taga hannuwan shi kamar bulala, dogone babu laifi, amman bazai kai Hamza tsayi ba, sai dai sam batason ganin namiji siriri haka, ita da take son dirarren namiji da zai dauketa bai sauke numfashi ba, faffadan kirji da zata kwanta luf kamar jaririya a kirjin mahaifiyarta. Ina zata kai irin Kamal, bai cire rigar shi ba, amman tasan babu komai a kirjin shi banda kasusuwan da intayi bacci akai zata tashi da tambarin da kasusuwan shi zasu bar mata a kunci kamar bagobura. Ganin da Kamal yayi ya rasa gane kan Hindu, ga yamma na karayi yasa yai mata sallama da fadin "Zamu yi waya" Shima kai ta jinjina mishi, tana kallo yaja jak din Machine din shi da bata tsaya ya tayar ba ta juya tana nufar cikin gida, badan Huzaifa yace mata yana da shago kusa da nashi ba, in a hanya tagan shi zatace Malamin Islamiyya ne, ko kuma irin matasan nan masu jan baqi a wajen tafisir. Yanzun ma tanaji a jikinta robobi yake siyarwa a shagon...! 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 22 Yafi mintina goma da bude idanuwan shi, amman sam yaki ko da motsawa ne, komai nauyin shi yakeji, dakyar yayi sallar asuba, itama a cikin daki, sabo ne kawai abinda ya tashe shi a yanda yakejin shi kamar marar lafiya. Karatun Qur'ani ma, da kai ya karanta abin da ya sawwaqa, yaja jikin shi ya koma kan gado ya kwanta. Baya gane hasken rana ta cikin dakin saboda gabaki daya labulayen a sake suke, kuma ya kashe wutar dakin, akwai dalilin da yasa yayi zanen taswirar dakin a haka, saboda bayason haske sam idan bacci yake son yi. Dakyar ya iya juya kwanciyar shi, yana daukar wayar shi ya latsa, sha biyu saura mintina tara. Dan ware idanuwan yayi ganin rana tayi har haka, sako yagani ta saman wayar, ya cire daga mukulli yana budewa. AbdulHafiz ne "Basu dauki yarinyar su sun baka dan sun gaji da ita ba. Kamar yanda wani bai maka dole kaganta kace kana so ba, karka wulakanta musu yarinya Hamza, karka ci amanarta da ka dauka. Allah ba zai barka ba, ka zauna da ita kamar yanda kake so mijin Auta ya zauna da ita, ka riketa kamar yanda kaga Appa ya rike Anna, ka kula da ita kamar yanda zaka so a kula da naka yaran wata rana. Allah ya baku zama na aminci, Allah ya kauda fitina a tsakanin ku, Allah baka ikon fin karfin zuciyarka a kowanne yanayi" Wani abu Hamza ya hadiye da yazo yai mishi tsaye a makoshi, yanajin jikin shi ya kara nauyi da maganganun AbdulHafiz din, a lokaci daya kuma suna bashi karfin gwiwar mikewa zaune. Dan dafa kan shi yayi, kafin ya sauke wani numfashi mai nauyin gaske yana mikewa gabaki daya ya nufi bandaki, ruwa ya watsa ya fito, zuwa wani dan lokaci ya shirya kan shi tsaf cikin wani yadi ruwan kasa mai haske, sai kamshi yake bazawa. Idan kagan shi zakace wani waje zaije, dan har hula ya saka a kan shi, ya daura agogo a hannun shi, takalma ya zira da za'a iya kira da silipas, bakake, tukunna ya fito daga dakin, a hankali yake sauka kasa. Tsaye yayi bakin kofar dakin Hindun yanajin jikin shi a sanyaye, ko kadan bayason tuna abinda ya faru a daren jiya, yasan shi din mai tarin laifuka ne, amman laifukan shi tsakanin shine da Ubangiji, nauyin da yakeji yau na da alaka da rashin kyautama Hindu da baiyi ba, ko kadan bayason hada laifukan shi da hakkin kowanne mutum, musamman ita, musamman matar shi. Numfashi ya sauke da kalmomi biyun karshen "Matar shi". Shi dinne yau karkashin inuwar aure da wata, shine da mata, da gaskiyar Hausawa da sukace "In da ranka ka sha kallo". Kwankwasa dakin ya farayi, sannan ya tura a hankali, a tsaye ya hangota, daga inda yake baya iya ganin fuskarta, bata kuma juyo ba, jikinta na sanye da doguwar riga ruwan kwai, bayan a bude, bata kai da zage zip din ba, tanata kokarin daura dankwalin ta, takalman shi ya zare daga nan inda yake tsaye, ya saki kofar yana rufeta, a hankali ya taka har inda Hindun take tsaye, hannun shi yasa yaja mata zip din, kafin ya mika shi yana kama dankwalin da take kokarin daurewa, yana kallo ta sakar mishi, dubawa yake yana tunanin ta inda ya kamata ya fara daurawa dan baisan me take son yi ba, baima san me yasa yayi kokarin tayata ba. Tunda ya shigo taji shi, taji shigowar shi, wani irin wahalallen bacci tayi tun bayan asuba, ta kuma tashi da wata irin yunwa, ga alamar zazzabi da takeji, ta dai godewa Allah da kanta baya ciwo, duk da ta kwanta da shi, amman bata tashi da shi ba, da sanyi-sanyi take komai tun tashin nata, sai da ta fara gyara gadon tukunna ta shiga wanka. Ba zatace ga halin da zuciyarta take ciki ba, balle kuma kalar tunanin da takeyi, a karo na farko da hatta tunaninta ya kwace mata, bata da karfin kokawa da komai, dan haka batayi kokarin janyo shi ba. Shisa tana fitowa wanka ta shafa mai, ta sami riga ta saka a jikinta, Hamza ya kwace mata abubuwa da yawa a daren jiya, ba zata bari ya kwace mata shigar da tayi niyyar yi yau ba, dan bata cikin walwala baya nufin ba zatayi kwalliya ba, ko ba komai shirin zaisa kadan cikin ranar yau tayi mata saurin wucewa. Da taji shigowar shi sai da zuciyarta ta doka, wani sabon tashin hankalin daya daga mata kafa tun tashinta taji ya dawo, jikinta ya fara bari, tana rasa yanda tayi niyyar daura dankwalin kafin shigowar shi. Badan bataso juyawa bane, kafafuwanta taji sun daskare a waje daya, har ya karaso yana kama zip din rigar da take jikinta yayi sama da shi. Ko ta cikin mudubin ta kasa kallon shi, zuciyarta dokawa take har zazzabinta ya bayanna sosai, dan tanajin zafin da jikinta ya dauka. Tana jin shi ya kama dankwalinta, shisa ta sakar mishi, sai yanzun ta sami karfin gwiwar kallon shi ta cikin mudubi, da yanayin fuskar shi daya nutsar akan dankwalin, zaka rantse bashida abu mai muhimmanci daya kamata yayi, numfashi ta sauke, tana mika hannunta ta dora akan nashi cikin son karbar dankwalin, makale mata kafada yayi yana saka dayan hannun shi ya tutture nata "Kibar ni, ina tunanin style ne" Yanda yayi maganar sai ta tsinci kanta dayin dan murmushi, yafi mintina biyar, har saida taji kafafuwanta sun fara gajiya da tsayuwa, sannan ta dan tsugunna tana zame kanta daga cikin dankwalin, ta sake mikewa, ta mika hannu ta fisge dankwalin daga cikin hannuwan Hamza, bude baki yayi ta riga shi da fadin "Ka kyaleni, kafafuwana sun gaji da tsayuwa" Ta karasa maganar tana daura dankwalinta mai sauqi ta hanyar lanqwasa shi, ta kuma tura ta baya, daurin da akanyiwa laqabi da ture kaga tsiya. Ya kuma yi mata kyau, ta cikin mudubin suka hada idanuwa, tayi saurin sauke nata, tana sa Hamza zagaya hannuwan shi a qugunta ya rikota jikin shi hadi da lumshe idanuwan shi "Idan nace kiyi hakuri yayi kadan, idan nace ba zai sake faruwa ba zanyi miki karya...na rasa abinda ya kamata ince miki, kiyi hakuri, ban kyauta miki ba, kiyi hakuri Hindu" Ya karasa maganar yana bude idanuwan shi cikin nata da take kallon shi ta mudubin, nata idanuwan cike taf da hawaye, batasan ko yanayin muryar shi bane ba, ko hakurin da yake bata, amman koma meye yayi tasiri a zuciyarta, tunda bata tsammaci hakan daga wajen shi ba, asalima batayi tunanin komai ba, dan a tsorace take "Kiyi hakuri..." Hamza ya fadi da dukkan gaskiyar shi, yana sakinta, hadi da kamata ya juyo da ita ta fuskance shi, yasa hannuwa ya tallabi fuskarta "Dan Allah karkiyi mun kuka" Ajiyar zuciya ta sauke, hawayen na zubo mata "Ka bata mana daren mu na farko" Ta fadi muryarta na rawa, kai yadan daga mata, yasani ba saita fada ba, shisa yasan bai kyauta mata ba "Shisa bansan ya zan fara baki hakuri ba, naji dadi da muna da darare da yawa a tare damu, I will make it up to you, na miki wannan alkawarin" Wannan karin ita ta daga mishi kai, yasa hannu yana goge mata fuska, kafin ya rankwafa ya sumbaci goshinta cike da ban hakuri, tukunna ya rungumeta tsam a jikinta. Ta zagaya hannuwanta a bayan shi, tasani daman, jiya dai zuciyarta ta fara karyatata, amman yanzun Hamza ya tabbatar mata ita yake bukata a rayuwar shi dan ta canza shi, tasan zata iya canza shi daman. Ba zaizo da sauqi ba, saita jajirce, amman tana ji a jikinta ko bajima ko ba dade hakan zai faru. Sunkai mintina biyu a hakan kafin yace "Yunwa nake ji sosai..." Tana lafe a kirjin shi ta amsa shi da "Nima haka" Dagota yayi "Dauko mayafin ki mu fita" Itama sai taji ya kara mata yunwar, gani yake kamar bata sauri saboda hanjin shi da yake kullewa "Nikam bari in fito da mota, kafin ki karasa shiryawa" Hamza ya fadi yana juyawa ya zira takalman shi ya fice daga dakin, hanyar waje ya nufa, ya kama kofar ya bude, ga mamakin shi, katon kwando mai hannuwa yaci karo da shi a bakin kofar dakin, tunanin farko daya fara zuwa ranshi ko jaririne a ciki, yanda kwandon yake a lullube, sai da kirjin shi ya doka, dan yasha ganin haka na faruwa a fina-finai, amman inda jaririne zaiyi kuka ai dole. Ganin yar takarda a maqale yasa shi tsugunnawa ya dauko takardar yana dubawa, kafin ma ya karanta yagane rubutun AbdulHafiz ne. "Eng. AH" Kawai aka rubuta a jiki, daukar kwandon yayi yana shigowa dashi cikin gidan, cike da mamaki, tsugunnawa yayi ya fara bude ledar da akayi amfani da ita aka lullube kwandon, yana cin karo da kuloli a shirye tsaf. Fiffito dasu yayi, ya bude na farko, dankaline soyayye da wainar kwai sai kamshi ke tashi, yana kara mishi yunwa, ya sake bude wata, farfesun kayan cikine "Allah ne kawai zai saka maka AbdulHafiz" Hamza ya fadi yana godema Allah da kyautar AbdulHafiz a rayuwar shi. Sai yakejin kamar AbdulHafiz bai taba mishi wani abu da yaji dadin shi irin yau ba. Mikewa tsaye yayi yana zaro wayar shi daga aljihun shi, AbdulHafiz ya kira da bugun farko ya daga yin sallama "AbdulHafiz...." Hamza ya kira yana rasa abinda ma zaice, yanajin karamin tsakin da AbdulHafiz din yaja "Menene?" Ya bukata, yar dariya Hamza yayi "Nagode, Nagode AbdulHafiz" Yanda yayi maganar yasa AbdulHafiz fadin "Kai kam baka da hankali dama" Ya kashe wayar daga dayan bangaren "Kamshin me nakeji?" Hindu data fito ta fadi yawunta na tsinkewa "Abinci AbdulHafiz ya aiko mana" Hamza ya bata amsa, abayar da ta saka a jikinta ta cire tana cillawa kan kujerar dake falon, tare suka tattara kulolin suna dawowa falon, suka zauna dirshen, babu wanda yake maganar dauko plate, akwai cokula a ciki, da babu hannuwan su zasu saka, ita kam Hindu batasan ko yunwar da takeji bace ba, amman ta kwana biyu bataci abinda yayi mata dadi ba haka. "Hindu mun kusan cinyewa" Hamza ya fadi da mamaki a muryar shi "Kasan yunwar da nake ji kuwa?" Hindu ta amsa shi tana saka nama a bakinta "Bamuyi Bismillah ba, ko ke kinyi?" Ya sake tambaya, kai ta girgiza mishi, dariya yakeyi yana sakata dariyar itama, cikin nishadi suka karasa cin abincin, suna zaman su a falon dan su dan sami natsuwa, kowa da tunanin da yakeyi a ran shi. * Tare sukai sallar azahar, Hamza yayi ja musu sallar. Suna gama azkar dinsu ta gyara zamanta, tanajin wata gajiya na saukar mata, Hamza take kallo da yake karatu a hankali da wayar shi, muryar shi na nutsar da abubuwan da batasan suna tashe ba a zuciyarta, tana kara jinjina ikon Allah da kalar jarabtar Hamzan. Gashi yayi mata wani irin kyau, sai da ya idar tace mishi "Kayi kyau" Kallon kanshi ya danyi, yana kashe mata ido daya "Kwalliya nayi miki" Murmushi ta danyi, duk da taji dadi har ranta "Ko dai zaka fita ba" Kai ya girgiza mata "Babu inda zanje Allah, sai za'a je wani waje ake kwalliya?" Ya tambaya, shi zai iya yin wanka ya saka manyan kaya harda hula kuma yayi zaman shi a daki. Mikewa yayi yana hawa kan gadon ya zauna ya mike kafafuwan shi, itama Hindu mikewa tayi, inda taga jakar system dinta su Anty sun ajiye mata ta nufa ta dauko, akwai socket ta gefen Hamza, ta fara saka cajar, sannan ta hada da system din tana janta zuwa kan gado ta ajiye, ta dayan bangaren ta zagaya ta zauna. "Me zakiyi?" Ya bukata cike da son sani, yasan tana da sauran sati biyu kafin ta koma makaranta, zangon karshenta. "Kallo..." Da ido yake binta harta kunna system din, tana zama a gefen shi, matsawa yayi kusa da ita sosai, ta kunna korean film din da bata fara kallo ba, Biebee ta tura mata shi. "Bride of the century" Hamza ya karanta sunan, yana mamakin inda suke samo sunaye haka, kashi na farko Hindu ta kunna, tana gyara zama, ta kwantar da kanta a kafadar Hamza, tasha mafarkin faruwar hakan, har a ido biyu tana hasasota zaune da mijinta suna kallo haka a system suna taba hira. Yanzun da abin ya faru sai take ganin kamar a mafarki, kamar wani zaizo ya tasheta. Hannun Hamza taji ya kama nata yana hade yatsun su waje daya ya dumtsa, tana jin yanayin har cikin zuciyarta. Kallon suke a nutse suna son fahimtar inda film din ya dosa, har kashi na farko ya kare, Hamza ya mika dayan hannun shi ya shigar musu na biyun, film din ya fara daukar hankalin shi sosai "Yarinyar nan na da kyau" Ya furta a fili, shiru Hindu tayi mishi batace komai ba, sai da akayi wajen mintina sha biyar a tsakani aka sake nuno jarumin film din tukunna tace "A haka ba lallai kaga kyawun shi ba, sai ka natsu tukun..." Bata karasa ba saboda zungurinta da Hamza yayi da gwiwar hannun shi a hakarkarinta "Wallahi zaki fasa kallon nan, me yasa zaki natsu kina kallon shi?" Dariya Hindu tayi "Oh ashe babu dadi" Hararta yayi kafin ya mayar da idanuwan shi kan laptop din "Ni ai ba har zuciyata na fada ba, kinga kinja banga me aka ce ba" Ya karasa maganar yana mika hannu yadan mayar da episode din baya. Kallon suka cigaba dayi, ko da sukayi sallar la'asar ma kallon sukaci gaba dayi, suna tattauna abinda yake faruwa a film din, batasan yanda akai Hamza ya koma jikinta ba, ita da take jikin shi a kwance, wajen biyar da rabi ta miqe ta sauka daga kan gadon "Ina ka kai mana kazar mu ta jiya?" Saida ya tsayar da film din tukunna ya kwashe da dariya "Menene abin dariya? Bakajin yunwa kai?" Kai ya girgiza mata "Ina ji wallahi, tun dazun" Kallon shi takeyi "Bana so in fara yin magana ne kawai. Tana cikin fridge a kitchen..." Ya karasa maganar yana sauka daga kan gadon, tare suka fita kitchen din, komai na mata bakunta, tana mamakin kitchen dinta ne haka. Tukunya ta dauka tana daurayewa ta dora akan gas ta kunna dan ta dunduma musu kazar "Kisa a microwave mana....ina da a kitchen din sama" Hamza yai maganar, ita ta manta da wani abu microwave, akwai a gidan yayarsu Babba, amman basu da shi a nasu gidan, shisa tunanin tayi amfani da shima baizo mata ba, duddubawa takeyi a nata kitchen din ko itama an kawo mata. Bata gani ba, tasan wasu kayan sai a hankali zata dinga fiffito dasu. Aikam saman suka hau, lokacin duk da tagama dumama musu ana kiran magriba, anan bangaren Hamza sukayi sallah, suka dauki kazar da sauran shawarmar su da burger suka sake komawa kasa, fita Hindu zata sakeyi yace mata "Me kuma zaki dauko? Allah zanci gaba da kallo idan kika dade" Murmushi tayi "Lemo fa zan dauko mana" Ta fadi tana ficewa, wani irin sama-sama take jinta saboda nishadin da take ciki, gabaki daya yau din ya wanke mata bakin cikin data kwasa a daren jiya. Shi kan shi Hamzan yau da sauqi yake jin shi, kamar zai iya zaman auren, kamar babu wani abu mai wahala a ciki kamar yanda yake tunani. Kallon sukaci gaba dayi har isha'i, da suka idar ne ya sake jansu sukayi nafila raka'a biyu ta godiya ga Allah daya kamata su gabatar tun a jiya, amman hakan bai faru ba. Kallon suka ci gaba dayi har wajen goma na dare, kafin zancen ya fara sauyawa. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 20 Hannu tasa tana kara gyara qullin lafaya din da yake daure a kugunta, hawayene da batasan inda suke sauka ba, saboda kanta da yake a sadde. Har Anty ta gama mata maganar da takeyi mata, sam bataji komai ba, hankalinta baya jikinta, bata kara shiga tashin hankali ba sai da taganta tsugunne a gaban Baba, sai da taji muryar shi ta dira kunnuwanta cike da bankwana, tabbas aure ba mutuwa bane ba, amman tana jin kewar Baba har cikin kasusuwan jikinta "Haka muke cinye kwanakin mu Hindatu, sai makusanta cikin jimami suyita ganin kamar munyi gaggawa, suna manta yanda su dinma basuyi jinkiri ba" Baba yayi maganar yana kasa yarda yau shine Hindu take tsugunne a gaban shi, yau shine zaiyi sallama da ita, ya mika kulawarta da amanarta a hannun Hamza. Iyaye mata kance rana irin tayau kanzo musu da farin ciki hadi da firgicin rashin sanin makomar gobe akan auren yaran su mata, abinda basu sani ba, shine firgicin yafi yawa a tattare da iyayensu maza, ka dauki amanar 'yarka da tayi shekaru karkashin kulawarka, kana duk wani kokari da kake da iko a kai na ganin wani abu bai cutar da ita ba, rana daya zaka mika ma waninka ita, duk kuwa da tarin kokwanton da yake ranka na ganin babu wanda zai iya kula maka da ita kamar kai. "Zance kiyi hakuri saboda yana daya daga cikin manyan jigo a cikin zaman aure, amman bance kiyi hakuri idan ya hada da cutarwa ba, na dage akan islamiyar ku saboda ki fahimci darajar da musulunci ya baki a matsayinki na 'ya mace, idan har hakurin da zakiyi a gidan aure ya nemi taka wannan darajar, Hindu ina da wajen zamanki, karki taba bari al'ada ta tauye danne miki 'yancin da addinin ki ya baki..." Cewar Baba, yana dorawa da "Allah yai muku albarka..." Yanayin muryar shi da yanda ta sauka ya kara haduwa ya karyama Hindu zuciya, batasan ta zauna ba, saida taji kanta ya jingina da kafafuwan Baba, kafin wani kuka daya fito daga kasan zuciyarta ya kwace mata, kuka take na barin gida, kuka take cike da firgicin rashin tabbas din da take cikin aure, kuka takeyi saboda yanzun ne take jin kamar bata shirya ma zama da Hamza ba, yanzun ne takejin wani bayanannen tsoro ya lullubeta. Sai da Mama da wata kanwar Baba sukazo suka janyeta dakyar suna fitowa da ita daga bangaren Baba. Kuka takeyi har yanzun da aka fito da ita. Ko da kanta ba'a lullube yake da lafayan jikinta ba, ba lallai taga hanya ba saboda kukan da takeyi, batasan waye ya kamata yana sakata a mota ba. A wani irin gigice take jinta har suka karasa gidan da yake a unguwar Malali, ta wajen KAD Academy. Batasan waye yake ce mata tayi addu'a kuma ta fara saka kafarta ta dama ba, ita banda sallama babu abinda ya iya zuwa kanta, addua kullum cikin yinta take, fiye da yanda zasu taba fahimta, saboda haka su kyaleta kawai taji da abinda takeji. Tanajin suna rike da ita har aka shiga wani daki, tukunna aka zaunar da ita akan gado. Har lokacin fuskarta a rufe take, danma tanajin sanyin AC din da ya gauraye dakin yana ratsata, banda ajiyar zuciya babu abinda take saukewa, kayansu da zasu saka anjima wajen zuwa Dinner yana wajen su Aina'u, su suka harhada komai, tasan kuma sun taho dasu, kilanma suna cikin gidan. Tana jin shige da ficen mutane da masu yi mata fatan alkhairi, da masu yi mata nasiha, ita kam banda hayaniya batajin komai, ba zatace ga awannin da aka dauka a haka ba, sai da taji muryar Hauwa data kama mayafin da yake rufe da fuskarta tana fadin "Ke bude kisha iska, duk sun tafi" Numfashi Hindu ta sauke hadi da ajiyar zuciya, tana kama mayafin ta kara goge fuskarta da shi, kafin Dimples ta shigo da plate din abinci a hannunta tana kallon Hauwa "Ba zakici abincin ba? Bie na kitchen..." Dan yatsina fuska Hauwa tayi, ita ba wata yunwa take ji ba, amman taga kamar da hadin salad, zataci wannan "Jiba gulma, yanda kike damun uban kowa da Hamza shine kika garji wannan kukan, kinga fuskarki? Ki tashi ki wanke ko zai sauka kafin lokacin Dinner" Dimples ta karasa tana zama gefen gadon, ta fara juya abincin da yake rike a hannunta "Wallahi duk fuskarki ta kumbura" Hauwa ta fadi tana nufar hanyar da zata fitar da ita daga dakin, ta fice "Ki tashi Allah, kinsan dai dole a zageki tunda ango yafiki kyau, gara ki wanke fuskar ko zai taimaka miki" Dan murmushin karfin hali Hindu tayi tana saukowa daga kan gadon, sai dai kofa biyu tagani a cikin tanqamemen dakin baccin, na farko ta fara budewa tana ganin dakin sake kayana, saita rufo ta dawo ta bude dayan, dan ware idanuwanta tayi ganin kayatuwar da bandakin yayi "Ke kinga toilet din nan kuwa?" Hindu ta fadi, tana saka Dimples kusan shakewa da shinkafar da take bakinta "Banza yanzun ranki har yayi sanyi, saboda bandaki" Dimples ta karasa tana kwashewa da dariya, itama dariyar Hindu tayi, tana shiga bandakin, komai ta karewa kallo, kamar an ciro shi daga film an ajiye mata, har bango saida ta dafa, yanayin tayal din ruwan gwal yayi matuqar daukar hankalinta, lokaci daya ta nemi damuwar da take ciki ta rasa, alwalar magriba ta dauro, dan bata lokacin da aka tsaya yi, sai bayan la'asar aka taho kawota, tasan inba dai babu masallaci a kusa dasu ba, tabbas ana gab da kiran sallar magriba, kuma karfe bakwai sukayi da mai kwalliya zatazo tayi mata, kafin su fara kama hanyar zuwa wajen dinner. Tana fitowa ta sami su duka ukkun a dakin suna cin abinci "Ke ba zakici wani abu ba? Tun dazun kike yawo kamar ganga" Kai Hindu ta girgizawa Biebee, ko yunwa bataji ballantana taci wani abinci. Tana zama ana fara kiran magriba "Wai Magriba har tayi?" Hauwa ta fadi cike da mamaki "Saiku tashi kuyi sallah, ni nayi sub" Hararar Biebee din Dimples tayi "Abin nan baimun dadi ba, yanda na wanke kwalliyata naso kowama ya wanke tashi wallahi" Dariya Biebee tayi sosai "Dan bakin ciki dai baiji dadin rayuwar shi ba" Dimples din bata ko kulata ba, ta mike, ita ta tattara kwanonin da su duka sukaci abinci "Allah sarki Kawata, dadina dake baki da matsala" Biebee din ta fadi tana sake kwashewa da dariya, fita daga dakin Dimples tayi tana kin biye mata, tana dawowa itama alwala ta dauro ta fito, duk sallah sukayi banda Biebee da take zaune tana danna wayarta. Basu dade da idarwa ba saiga mai kwalliyar na kira tazo kan street din, Hauwa ta karbi wayar Hindu ta fita tana dawowa da ita. Batare da wani bata lokaci ba ta tsarama Hindu kwalliyarta da tayi matukar karbar fuskarta, suma yi musu aka sakeyi, Biebee kuwa dan gyara mata akayi, tunda bata bata tata ba. Kafin kace wani abu har sun kammala shirinsu tsaf, Hindu na sanye da material da dinkin doguwar rigar kawai zaka kalla kasan amarya ce. Wine color kamar yanda bature yake kiran kalar kayan da suke jikinta, tayi wani irin kyau da har Hauwa sai da tace "Oh Allah, Hindu kinga yanda kikayi kyau?" Murmushi Hindun tayi, tana mata godiya, hotuna suka dinga yi mata, ta mika musu harda wayarta, su material dinsu ruwan madara ne, duka dogayen riguna. "Ni kadai ce nayi kama da muburkin miya" Dimples ta fadi tana saka dukansu kwashewa da dariya "Zan tayaki addu'a kawata, yar kibar nan Allah ya dubeki" Tsaki Dimples taja "Bie bana son iskanci, kuma anma fi yayin kalata kiji, yarinya siririya, ga kyau ga dimples" Wata dariyar Biebee ta sake kwashewa da ita, Hauwa nata kallon su da murmushi a fuskarta, yanayin kawancen su yana burgeta, tun jiya sunyi fada yafi sau ashirin, kamar kaji haka suke, Dimples saurin kulewa, Biebee kuma tsokana. Hindu kuwa kiran Hamza ta daga, tun bayan wayar da sukayi da aka daura aure, sai da suka zo gidansu akayi hotuna, shima magana ko daya bata hadata da shi ba, sai take ganin wani nisantaccen yanayi shimfide a fuskar shi da batasan na menene ba, basu wani dade ba suka wuce, basu sake neman juna ba kuma, yanzun ma tana karawa a kunnenta yana furta "Kun shirya?" Kai tadan daga mishi tana dorawa da "Eh..." Cikin sanyin murya "Kaji wai sun shirya..." Hamza yayi maganar daga dayan bangaren da alama wani yake yiwa magana, kafin taji ya kashe wayar a kunnenta, saukewa tayi tana kallon su Biebee a zahirance, a badini kuwa batama ganin su, wani abune yazo dai-dai kirjinta yai tsaye, ba tasan akwai wani yanayi a tsakanin tsoro da tashin hankali ba, sai yanzun data tsinci kanta a cikin shi male-male. "Sauran yan gidan su Hindu fa? Wa zaije ya dauko su?" Fodio ya bukata "Dan Allah Fodio ka kira AbdulHafiz, nifa ban sani ba, bana ji yace ya tura ba?" Hamza ya fadi yana kara saka comb cikin sumar kanshi ya taje, kafin ya dora hular shi, farar Getzner ce kal a jikin shi sai daukar ido takeyi, duk da babu aiki a jikin riga da wandon da yake sanye dasu, kallo daya zakayiwa yanayin dinkin saiya burgeka, zaman agogon shi ya gyara, yana daukar babbar rigar shi ya rike hannu, dan bazai sakata tun yanzun ta yamutse ba. Turarukan da suke baje kan gado ya shiga dauka yana kara feshe jikin shi da rigar da take hannun shi. "Ka cakar dani Hamza" Fodio ya fadi yana mikewa tsaye, kan shi harya fara juyawa saboda karfin turarukan, ko kallon shi Hamza baiyi ba, ya mika hannu ya dauki wayar shi da mukullin mota, ficewa yayi daga dakin yana shiga kitchen, yanda yake jin shi idan baidan kara shan wani abu ba, rayuwar shi zata shiga wani yanayi kafin a gama dinner din nan. Kwakbar vodka ya dauka yana samun kofi ya zuba fiye da rabi a ciki, ya rufe kwalbar ya mayar, duk da akwai dan sanyi, saida ya dibi kankaru ya zuba, tukunna ya kwankwade. "Uban me kake sha? So kake ka fara slow cikin jama'a?" Fodio ya karasa maganar yana dariya "Kaina yamun nauyi ne, kawai abinda zai taimaka mun a gama dinner din nan" Dariyar Fodio ya sakeyi yana girgiza kai kawai "Idan nace maka kayi kuskure kamar na makara ko? Tunda an riga an daura" Numfashi Hamza ya sauke yana kara bude fridge din da nufin dauko kwalbar ya sake kwankwada, Fodio yayi saurin karasowa yana mayar da fridge din ya rufe "AbdulHafiz zai kasheni wallahi, ka wuce mu tafi..." Runtsa idanuwan shi Hamza yayi yana sake bude su, yanda kanshi yayi dim yana da tabbacin gab yake da fara buguwa fiye da misali "Ya isa Hamza, ya isa haka, ba a karkashin kulawata zakayi wannan shirmen ba" Yasan da gaskiyar Fodio, amman a wani irin takure yake jin shi kamar ya saka ihu. Duniyar ta hade mishi waje daya, ga wuyan shi da duka jikin shi da yakeji kamar an shaqe, tamkar wanda aka garkame a dakin da babu window, kofar ma an kulle an cillar da mukullin haka yake jin shi, iskar da yake shaka tun bayan da aka daura auren kanta da kauri yake jin tana mishi zirga-zirga. Kafin ya fara neman mukullin da zai warware wannan kullin da ya jama kanshi yake so yasha giyar shi harsai ya daina gane komai. Amman hakanma ba zai yiwu ba saboda zaije dinner, dinner din bikin shi "Me nayi haka?" Ya tambaya yana kallon Fodio "Komai zaiyi dai-dai, calm the fuck down Man. Ka natsu fa" Fodio yake fadi muryar shi na rawa saboda yanayin Hamzan ya fara bashi tsoro kuma, tun yana dariya, yanzun abin tsoro yake bashi, da AbdulHafiz yana nan shi yasan yanda zaiyi da Hamza, amman koma meye bazai barshi ya bugu ba tunda taro zasu shiga. "Kazo mu tafi" Numfashi Hamza yaja yana fitar dashi da nauyin gaske, kafin ya jinjina kai, yana saka Fodio sauke numfashin da baisan yana rike da shi ba "Nagode" Ya furta yana nuna ma Hamza hanyar fita daga kitchen din, baiyi musu ba ya fito, harabar gidan inda motocin su suke suka karasa, har wajen motar Hamza ya raka shi "Zaka iya tuqi?" Ya tambaya, Hamzan nayin wani irin shiru, saboda ya nisa cikin tunanin da bazaice ga na menene ba, dan taba shi Fodio yayi tukunna ya daga ma Fodio din girar shi duka biyun "Hamza, Hamzaaa" Fodio ya karasa cike da roko "Nayi yarinta da ciwon zuciya, Hamza ka bari in mayar wa AbdulHafiz kai lafiya sai kayi duk abinda zakayi" Sai lokacin Hamzan yayi dan murmushi "Bana son iskanci Fodio" Sharce goshin shi Fodio yayi "Kana tsoratani yau din nan" Murfin motar shi Hamza ya bude yana shiga, saida ya rufo tukunna Fodio ya wuce yana shiga tashi motar, su duka suna fita daga gidan, dayake Fodio baima dade da samun maigadi ba, su suke jigilar bude gate dinsu da rufewa da, yanzun ko gidanma bai damu daya kulle ba. Malali suka nufa dan su zasu dauki su Hindu, gudun da Hamza yakeyi da mota, Fodio addu'a kawai yake a ran shi su dauke su, su karasa wajen dinner din lafiya "Karka bari yayi wani shirme" AbdulHafiz ya jaddada mishi kafin ya fita, bayajin yasan wani abu shakka, ko kuma shayin wani tun tasowar shi, ko Yayyen shi tunda ya kawo karfi babu wanda zai daga mishi dan yatsa bai lankwasa ba, amman AbdulHafiz na mishi wani irin kwarjini naban mamaki, akan AbdulHafiz din yasan me ake nufi da samun Babban Yaya da har ranka kake da tabbacin zai kula dakai da duka zuciyar shi, har a kullum yana godema Allah daya kadarta kasancewar AbdulHafiz din a rayuwar su, dan shi Alheri ne tare dasu gabaki daya. Suna karasawa, Hamza ne ya fara shiga da motar, ya samu waje cikin harabar gidan yayi parking dinta, a jiki yabar mukullin yana fitowa, cikin gidan ya shiga kanshi tsaye, duk da bazai ce ga dakin da Hindun take ciki ba, amman yaji hayaniyar su, dan haka ya nufi dakin da yake anan kasa, tunda gidan hawa biyune. Kwankwasawa yayi, yana tattaro duk wani karfi daya rage mishi ya dora murmushi akan fuskar shi "Waye?" Yaji muryar Dimples da yanajin ita kadai zai iya ganewa duk a kawayen "Ku fito" Hamza ya fadi, yana gani aka murda hannun kofar ana budewa "Ango kasha kamshi" Dimples ta furta, murmushi ya karayi "Ku fito ko zasuyi wata magana, kafin suce mun saka musu ido" Dimples ta fadi tana raba Hamza ta wuce, su Biebee ma wucewar sukayi, Hamza ya taka yana shiga cikin dakin, hadi da mayar da kofar ya rufe, a tsaye ya hangota, tayi wani irin kyau naban mamaki, jira yake yaji abinda yakeji duk idan ya ganta, musamman yanzun da take halalin shi, amman sai takeyi mishi kamar abincin da ya dade yana jira bayan matsananciyar yunwar da har taci shi ta cinye, saboda haka duk wani zumudin da yakeyi ya fita daga kan shi. Takawa yayi ya karasa inda take, kamshin da takeyi na saka shi lumshe idanuwan shi, kafin ya kara bude su a kanta. Itama yawatawa takeyi da nata idanuwan akan fuskar shi,duk da sai da ta daga kanta saboda tsayin shi, yayi mata kyau matuqa, hular kan shi kalar kayan jikinta. Magana take sonyi, amman batasan abinda ya kamata tace mishi ba, ga zuciyarta da take ta dokawa kamar tana son fitowa ta nuna ma Hamzan abinda harshen Hindun ya kasa furta mishi, hannun shi ya dago yana saka yatsan shi ya taba janbakin da yake kan lebenta da yayi mishi kyau matuqa, kafin ya sauke hannun yana amfani da duka biyun ya kamo kowanne cikin nata. Dago dasu yayi, ya ware tafukan hannuwanta yana dorawa kan kuncin shi hadi da runtse idanuwan shi yana sauke numfashi "Lafiyar ka?" Hindu ta bukata a tsorace, yanayin shi yana saka gwiwoyinta yin sanyi, hannun shi yana kan nata da yake kuncin shi, har lokacin idanuwan shi a lumshe suke, ya girgiza mata kai "Ko ma maka wani abu?" Ta bukata cike da son gano inda matsalar take, dan wannan ba Hamzan ta bane ba, Hamzan da yake nuna mata ya kasa jira hannuwan shi su sauka a kanta, yanzun gata a gaban shi a matsayin tashi, amman ta nemi duk rawar kan nan ta rasa, sai lokacin ya bude idanuwan shi yana sauke su cikin nata "Bake bace ba, babu abinda kikayi mun" Kai tadan daga mishi tana sauke numfashi, kafin a hankali ya sauke hannuwanta daga kan kuncin shi, yana dan dumtsa yatsunta, kafin ya saki hannuwan nata, wani irin mayafine yake gani kamar alkyabba, amman daga kafadarta yake manne, ya sauka har kasa yana baje, yayi mishi kyau, kamawa yayi yana kara gyara mata "Kinyi kyau" Ya furta da wani irin sanyin murya da yasa kai kawai ta iya daga mishi "Muje?" Ya bukata, ta daga mishi kai, jakarta ta dauka tana rikewa a hannunta, wayarta na hannun Biebee. Tare suka fita, Hamza ya bude mata mota ta shiga, yana tayata tattare rigarta da mayafin ta shigar cikin motar sosai, kafin ya zagaya ta dayan bangaren yana shiga shima. Tayar da motar yayi, yana fita daga gidan, a hankali yake tuqin, su dukan su babu mai cewa komai, kowa da abinda yake sakawa a cikin zuciyar shi har suka karasa wajen dinner din. * Littafina na siyarwa ne, #250 da hamsin ne kawai, zaka iya samu idan kai mun magana ta WhatsApp dina a lamba: 08074545149. #250 baya nufin ka siya ka karanta da wasu, yana nufin ka siya ka karanta kai kadai, zabinka ne idan hakan yayi maka ka biya. Idan baiyi maka ba dan girman Allah, dan darajar iyayenka idan kasanta kana kuma mutuntata, ka barmun littafina. Nagode. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 18 Ta dauka lokaci zaiyi mata tsaye,kalaman AbdulHafiz da Nabila bayan saka ranar su ya zauna mata daram, amman sai tasha mamaki, dan lokaci bai taba yi mata gudu irin wannan karin ba, ko dan jarabawar da sukayi da gujumniyar project din karshen zangon, duk da lokacin Hamza ya karba yayi mata tracing. Ta samu sauki, amman sam ta kasa yarda da cewa kwanaki kasa da ashirin suka rage a daura aurenta, sai take ganin komai ya cakude mata, ga Hamza sam aiki ya wani irin rike shi, komai ya bari a hannunta. Dan Dimples da Biebee su sukayi hidimar fito da anko, sun sha wahala kafin su yanke hukuncin anko kala biyu, atamfa da za'a saka wajen Kamu, sai kuma leshi da za'a saka a wajen dinner. Wannan ma batabi ta kansu ba, nata kudin ma su taba, Ita tun sauran wata biyu bikin take duba leshina a Fabrique Castle, harma ta dauki lambar Waheedah Shu'aib Haroon da itace mai mallakin shafin, kuma da alama mutane sun yarda da kayanta, taga hotunan amare da dama da suka siyi kaya a wajenta cewar abinda suka siya shi aka aika musu da shi. Dan ba sosai take yarda da siyayya online haka ba, amana tayi karanci a cikin mutane yanzun. Amman tabbas akwai kayayyaki daga leshi zuwa atamfofi irin wanda bako ina ake samun su ba, yanda take son komai nata ya fita daban. Anan tayiwa Waheedah magana ta tura mata kalaluwan leshina da atamfofi, Hamza ya tayata zabe, tunda shima duk shaddojin daya siya tare suka zabi wanda zai dace da kayan da zata saka. Babu yanda Anty batayi da ita ba kan a siyi kayan anan Kaduna, itama tasan mutane, amman Hindu taqi "Anty harfa nayi magana da Baba, yama bani kudi" Cewar Hindu, dan Baba ya kirata yaji ita dame-dame ta zaba, ta kuma nuna mishi, da Antyn tayi mishi magana ca yayi "Ki kyale yarinya da zabinta dan Allah, ke abinda zaki so ba lallai yayi mata ba, kuma kinsan kayansu na zamani" Shisa Anty ta koma gefe ta saka musu ido, kiri-kiri Baba yake nuna yanda Hindu tafi mishi kowa a gidan, har saida Antyn ta dinga jin babu dadi, tunda da Hindu da Khadee za'a yi bikinsu lokaci daya. Amman kai tsaye Baba yake kiran Hindu yana tambayarta zabinta akan abubuwa da dama, ko da Khadee take nuna hakan ba komai bane, Anty tasan Mama ba zataji dadi ba, kawai dai in akace Baba da Hindu ne, babu wanda ya isa yace wani abu. Shisa kowa ya dauki ido ya saka musu. Yanzun ma Hindu na daki a zaune ta shiga Instagram, wani biki ta fara cin karo da shi, ita yanzun gabaki daya bikin AbdulHafiz ya dakushe mata kyallin duk wasu bukukuwa da take cin karo da su, badan bata taba ganin bikin da yafi nasu AbdulHafiz ba, tunda Allah yayita da bin shafukan manyan mutane, amman nasun ne anyi shi cike da natsuwa, ga kuma irin kalar shigar da sukayi. Akwai kudi dan kudi, amman sarautar da take tattare da shagalin bikin na daya daga cikin abinda ya qawatar sosai da sosai. Kuma lokacin dan rashin tausayi, duk da a Kaduna yake da zama da matar shi, amman sai su Hamza suka bashi sati biyu, tunda aiki suke a Kano lokacin, shi yake kular musu da sauran ayyukan su na nan Kaduna, shida Abdallah. Ita Hindu sai take ganin sati biyu yayi kadan, dan tana so idan nasu yazo a basu fiye da haka. Tasan yanda Hamza yake rawar kafa a kanta, ko wata daya aka basu wuni zaiyi cikin gida, yanda zata zuba sangartarta, tafiya ma a cikin gidan ba sosai zata dingayi ba, sai dai ya dauketa. A ganinta idan mata basu more wannan damar da Allah ya basu ta lokacin amarci ba, ai an gama sha dasu, indan Hamza ne yanayin soyayyar su ma, harsu tara yara ba zata wuce sunguma a wajen shi ba. Murmushi tayi ita kadai tana dan sadda kai cike da kunyar kalar tunanin da sake-saken da take yawan tsintar kanta a ciki tun bayan da aka tsayar da lokacin auren su, balle kuma yanzun da abu ya matso kusa, sosai take hasashen yanda rayuwar auren nasu zata kasance. Ta gama da maganar dinki, Doka plaza takai, da aka lissafa mata kudin dinkunan gabaki daya sai da taji kanta ya sara, dan har kasan ranta take tausayin Baba, balle taga kudin da yake kashewa, tun daga kayan kallo dana kitchen, komai aka shigo dashi gidan guda biyu ake siyowa. Ranar tana shigowa gida sunayin waya da Hamza, yake tambayar me tayi ranar, ta fada mishi takai dinki, sukai hirar, sai gashi ya turo mata kudin dinkin, taji dadi har ranta. Idan baba ya bata kudin dinki, ko nawane sai tayi maganar kwalliya dasu, taga yanda abin zai kasance. Ta dai ajiye lambar Nadine da Meemie Beauty, amman ranar Kamu dai zataje colors of Meena da yake safaha plaza anan kwato road, tayi gyaran kai, wankin kafa sai kuma suyi mata kwalliyar fitar bikin ranar acan. Khadee tayi musu booking din mai kunshi da zatazo tayi musu har gida. Shiga tayi tana duba masu yin cake din biki, dan Hamza yayi mata maganar jiya, amman shi ba wasu abubuwa yakeyi da yawa ba, dinner ce kawai da zasuyi, kuma Fodio da shi kadai take da lambar wayar shi duk a cikin abokan Hamzan, da bikin ya gabato "Nikam kaina na ciwo, haka biki yake da wahala daman? Kuyi magana da Fodio ni dai, nagaji wallahi" Hamza ya fadi ranar da suke maganar wanda zai musu hotuna a wajen bikin. Yanzun ma alamar shigowar sako tagani ta whatsapp, tana budewa taga Fodio dinne yayi mata sallama, ya tura mata wasu hotuna da ta bude, wajen event ne har guda uku. Yana dorawa da "Ki zabi daya" Zabar kuwa tayi, inda yafi kowanne yi mata kyau a cikin hotunan, tana hasaso yanda zasu kawatu sosai, har saukowa daga gado tayi tana tashi tsaye, dan sosai wajen yayi mata kyau "Castle event center, daman nima duk yafi mun kyau" Ai bata ma ba Fodio amsa ba, ta sauka daga whatsapp din tana shiga Instagram dan ta duba su, wani irin tsalle tayi ganin sosai yanda wajen ya qawatu, tana da tabbacin zaiyi tsada sosai da sosai. Dan Big city events center ma nawa aka ce musu, dan anan zasuyi kamun bikin, da yake wajen babu laifi shima ya qawatu, da wuri sukayi booking, kar a fara gaya musu labaran da zasu karya musu zuciya. Murmushi kawai takeyi ita kadai, a tsayen Asma ta shigo dakin ta sameta "Ke zo kiga inda za'ayi dinner din bikina" Tace ma Asma cike da farin ciki, da gudu Asma ta karasa tana karbar wayar daga hannun Hindu "Inalillahi.... Kai... Wallahi wajen nan yayi mugun kyau, amman da tsada ko?" Kai kawai Hindu take dagama Asma, murmushi take har kumatunta sun fara mata ciwo, amman ta kasa dainawa saboda tsantsar nishadin da take ciki, wayarta ta soma ruri, kafin tayi wani yunkuri Asma ta daga, muryar Hamza na dukan kunnenta da fadin "Babe..." Cike da gajiyar da yake tattare da ita, dariya Asma tayi "Ba ita bace ba" Shima dariyar yayi, tun bayan saka ranar su da Hindu sukayi wata irin shakuwa da Asma din, dan Hindu batajin a gidan akwai mai yin Hamza bayan ita, sai Asma, takance yana da kirki sosai, haka kawai zai turo ma Hindu kati yace taba Asma, tayi sub ta duba assignment, ko zuwa yayi wajenta yakan taho da kayan ciye-ciye yace a bata, sosai in kana tare da shi zaka fahimci yanda hannun shi yake a bude kamar ganyen magarya, ba kamar samarin yanzun ba da Dimples kance "Ki godema Allah Hamza nayi miki kyauta, yanda samari suke kamar kwalta, sam basa banbaruwa" Godiyar Allah kullum a cikinta take dan ta sami cikar burinta, addu'arta bata fadi a banza ba, jinkirin da ya sameta yazo da alkhairi "Asma, ina Babyna?" Hamza ya fadi, dariya Asma ta karayi, kafin tace wani abu Hindu ya fisge wayar tana kai mata dukan data kauce tana fita daga dakin, dan har lokacin dariya takeyi "Hello..." Hindu ta fadi, tana jin yanda Hamza ya sauke numfashi "Nagaji sosai, Fodio yake cemun kun zabi wajen da za'ayi dinner ko?" Kai ta daga "Eh yanzun ya turomun, sannu da gajiya, su AbdulHafiz ba zasu kyalemun kai kadan huta ba ko?" Numfashin ya sake sauke mata cikin kunne "Kibarsu, kuma wai zamu shiga Kano gobe, gashi yanzun suna so su kara jana mu fita, ni zan watsa ruwane inyi Magriba inzo wajen ki" Zama Hindu tayi, jin kafafuwanta sun fara gajiya "Dan Allah zaka zo? Karka sakamun rai fa" Yar dariya yayi "Jibi yanda kike magana kamar da gaske kinyi kewata, bayan nine nace zanzo" Itama dariyar tayi "Da gaske ina kewar ka, bana so ince yaushe zan ganka dan kar in kara takura ka" Tunda tasan aikin da yake fama dashi "Sau nawa zan fada miki duk aikin da nakeyi idan da gaske kina son ganina zan ajiye in zo? Sai dai in bana garin" Murmushinta ya fadada, tanajin yanda soyayyar shi take kara cika mata kirji "Sauran 'yan kwanaki dai, duk mu huta da wannan wahalar" Ya fadi, yar dariya tayi a kunyace "Ba zaki daina mun wannan kunya-kunyar da kika san bana so ba ko?" Tasan yanda yake a gajiye, rigima zai iya yi mata, tana kuma cikin farin ciki, sam batason abinda zaija suyi rikici "Ka tashi ka watsa ruwan, yamma na karayi, nima alwala zanyi" Zata rantse kai ya girgiza mata "Ni um um, ban gama jin muryarki ba" Mikewa tayi "Yi hakuri, kai da zaka zo muyi hira ma, tashi ka watsa ruwa dan Allah, kaji" Shiru yayi na yan dakika kafin taji ya sauke numfashi me nauyi "Baka tashi ba fa" Ta fadi "Yanzun zan tashi ai" Yayi maganar yana karasawa da hamma "Bacci ko?" Ta bukata muryarta na sauka kasa, cike da kulawa "Ummm, bari dai inyi wankan" Ya karasa maganar yana kashe wayar, kan gado ta cillata, itama tana shiga bandaki. * Zuwa yanzun Hindu gani takeyi kamar da ta tashi da safe dare yake sakeyi ta kwanta, saboda yanda lokacin yakeyi mata sauri. Gidansu Biebee taso shiga, amman suna wajen suna, zaifi mata sauqi akan zuwa unguwar su Dimples, amman babu yanda zatayi, dole can din ta tafi, saboda za'a kawo lefen su, gidan ma akwai wasu cikin yan uwan su, tacewa Anty a can zata kwana, idan ta kira Hamza tsaf zaije ya dauketa ya mayar da ita gida. Ko Baba Abba ma Yayan Dimples idan yana gida, dare kuma yayi tasan zai taimaka ya sauketa. Tunda taje suka gaisa da Mama tana dakin Dimples suna zuba labari, tana kwance akan gado, ita kuma Dimples din tana kan keken dinkin ta "Dee rashin mutuncin ki bashi da na biyu, jibi rigar da kike dinkawa kan ki" Idanuwa Dimples ta juya mata tana cigaba da abinda takeyi kafin tace "Kinfi kowa sanin ban koyi dinki dan kowa ba sai kaina, kuma nama tsani abin yanzun wallahi, sam baya raina. Su Mama ma sun cire rai, tela suka samu suna kai dinkin su" Dariya Hindu tayi, tasan halin Dimples, tunda Mama ce ba zata ce mata ba zata dinka ba kai tsaye, amman ayi watanni ko yankawa batayi ba, Mama kuma irin mutanen nan ne da basa son a ja musu rai, tunda ta gwada sau biyu, bata kara bata dinki ba. "Allah ya shiryeki wallahi, amman ke banza ce, da kudin da zaki samu Allah kadai yasan yawan su" Dankwalin da Dimples ta karasa lafewa ta jefa kan gado tana fadin "Naji...yanzun zamuyi wata maganar mai muhimmanci ko baki gaji da bata bakin ki ba?" Sosai Hindu take dariya, kafin ta daga wayarta da Hamza ya kira "Nifa ina inda kika ce, ki fito, tun dazun nake kiran wayarki ban samu ba" Mikewa tayi tana fadin "Dee bari inga Hamza" Kai Dimples ta daga mata "Ki gaishe da shi" Wucewa Hindu tayi, tasan Dimples, ko catayi ta fito su gaisa ba zataje ba, haka ma zatace "Bana son shegen gulma, kibarni" Shisa batayi asarar maganarta ba, fita tayi tana kuwa ganin motar shi da yayi parking a gefe. Karasawa tayi ta bude tana shiga, ya jingina sosai da jikin motar, ya juyo da kanshi yana sauke mata idanuwan shi da take ganin sun sake launi, takan ga hakan wasu lokutta, sai yace mata bacci ne da gajiya. Murmushi tayi mishi, yana sake shagwabe mata fuska "Gajiya?" Ta tambaya, ya daga mata kan shi da yakejin yayi wani irin nauyi, kuma yasan abinda yasha ne, da bacci zai kwanta yayi, kawai yaji yana son ganinta. Shisa ya kara bulbula ma cikin shi vodka, ko zai samu ta dishe mishi abinda yake ji, yanzun sosai take mishi rigima idan ya nemi ko hannunta ne ya rike, kuma ran shi na baci ba kadan ba, shisa yake kokarin ganin yayi controlling din kan shi, kamar yanda tace ne "Saurin me kakeyi?" Kuma AbdulHafiz yace mishi "Idan kana son ta, da gaske idan kana son ta, ba zaka tayata tara zunubi ba, ba zaka nemi wasa da kwanciyar kabarin ta ba" Kuma tunda aurenta zaiyi, zai jira, yana azabtuwa da hakan ne fiye da yanda ita da AbdulHafiz zasu taba fahimta, ba wasa yake so yayi da kwanciyar kabarinta ba, dan shima nashi yana kan layi, ita dince take barazana da nutsuwar shi. "Ya kike?" Ya tambaya muryar shi a dishe "Ni ina lafiya, kai zan tambaya ya kake... Ka karbo dinkin?" Kai ya daga mata, yanda itama take zaune cikin kujerar ta kwantar da kanta na sakashi sauke numfashi "Kinsan kina da kyau ko?" Yar dariya tayi "Kai baka ganin naka kyan? Dan wanda na samu shine baka gajiya da magana a kai" Numfashi ya sauke, idan zai kwana yana mata bayani ba zata taba gane abinda yake nufi ba, ko magana takeyi sai yaji tsikar jikin shi na mikewa, wani irin kyau take mishi na ban mamaki, jin yayi shiru, ga wani irin kallo da yake mata yasa ta fadin "Ya turo hulu nan?" Wayar shi da take ajiye cikin gaban motar ya mika hannu ya dauko, cireta yayi daga mukulli yana shiga WhatsApp din shi, yakai kan inda yayi saving lambar mai hular, ya mika mata, shiga tayi tana dubawa, gabaki daya sunyi kyau, kuma zasu shiga da kayanshi "Dubu arba'in da takwas?" Ta fadi tana ware idanuwanta, ganin kudin daya daga cikin hulunan, amman dai daga zanen ma ta fita sosai, tana dai jinjina kudin, sai taga sauran ma suna da tsada sosai, guda dayace dubu sha biyar. Fita tayi daga kan lambar mai hulunan, tana ganin wadda take saman tashi da akayi saving da 1. Anyi sako, baima bude ba "Naga alert din. Nagode" Tagani, batasan me ya kaita ba, kawai ta tsinci kanta da bude sakon, haka kawai taji tana son sanin kudin menene ya tura, kuma waye ya tura ma, chat din ma baiyi tsayi ba, sama tayi tana fara ganin na farko daya tura "Hi" Kafin a amsa shi, zuciyarta tayi wata irin dokawa "Sunan hotel da kuma kudin ki" Ta karanta, tana ganin yarinyar ta turo kawunan mamaki da kuma alamar tambaya "Karki bata mun lokaci. Ba zan maimaita tambayata ba" Anfi awa biyu a tsakani kafin ta turo "Assa pyramid hotel. 100k" Wannan karin shiya tura mata kawunan mamaki "100k? Sake turomun hoton ki ingani" Tasan ya kamata ta daina karantawa, amman ta kasa dainawa, duk da zuciyarta na mata barazanar tarwatsewa a cikin kirjinta saboda zafin da takeyi, hotunan ta shiga, yarinyar da wahala idan musulma ce, dan kanta yasha kitson gashin doki, kuma riga da wandone a jikinta da suke bayyana duk wata halitta da take da ita "Meye abin 100k anan? 15k idan zaki iya" Sai da ta duba mintinan da suke tsakani kafin yarinyar ta amince, zuwa lokacin idanuwan Hindu cike suke taf da hawaye. Tana karasa karanta hirar da lokacin da suka saka zasu hadun, kuma jiyane, baizo yaganta ba. Ya samu lokacin da zai hadu da wata a hotel, har ranta ta dauka ya daina, saboda bata ganin maganar shi dasu a twitter, har Mansy tun bayan saka musu rana bata ganinta, ta dauka sun rabu itama, yanzun kuwa ya dawo mata da shakku da kokwanto, ga wani zafi da kirjinta yakeyi. Hamza na kallonta, yana kallon yanda hannuwanta suke rawa, yasan wani daga cikin chat din shi ta shiga. Gudun ruwanta ya tsaya kallo, dagowa tayi tana kallon shi da hawayenta da sai lokacin ya samu damar zubowa, dagowa yayi daga jikin kujerar motar yana mika hannu ya fisge wayar shi, ya duba yaga abinda ta karanta, dan bata fita daga kai ba, fita yayi, ya saka wayar a key, ya mayar da ita inda ya dauko "Hulunan sunyi kyau?" Ya bukata, yana saka Hindu kai hannuwa ta goge fuskarta "Huluna sunyi kyau? Shine abinda zaka ce mun? Hamza karka raina mun hankali, wallahi karka nuna mun kamar baka san abinda ya faru ba" Hindu ta fadi a masife, kallonta yakeyi a kasalance "Me kike so ince miki?" Yanayin yanda yake very calm, yana kallonta kamar baiga wani abin tashin hankali cikin abinda tagani dinba na kara tunzurata "Wow.... Da gaske? Da gaske baka san abinda zaka ce mun ba?" Komawa yayi cikin kujerar ya kwanta, yana karkato jikinshi ya zuba mata idanuwa "Hula na baki kigani, me yasa zaki bude mun wani abin daban? Na aike ki? Nace ki duba? Me kike so ince miki bayan ban saki duba mun waya ba?" Hannu takai zata bude motar ta fita, yayi saurin rufe murafun motar gabaki daya "Ke kin isa ki fita kibar mun mota Hindu?" Cikin idanuwa take kallon shi, kirjinta kamar zai bude "Ka bude mun mota in fita, bana son ganin ka" Wani irin kallo yake mata, dan yaga alamar nata rikicin wasa ne, bai aiketa ba, baice ta duba mishi waya ba, yana mamakin mata, idan kinsan ba zaki iya jurewa ba me yasa zaki duba tun daga farko? "Wallahi zan baka mamaki, ka bude mun mota" Hindu ta fadi, dan yanda takeji komai zai iya faruwa, gara ya bude mata motar ta fita tayi kukanta ko zata samu saukin tuquqin bakin cikin da take ji "Karki mun fada, karki fara cewa zaki mun fada. Ya kike so inyi? Hauka? Kince in daina tabaki, duk kokarin da nakeyi bakya gani?" Sosai take kallon shi, mamaki da takaici duk sun hadar mata waje daya "Dan nace ka daina tabani shisa kake bin wasu matan? Abinda ka fada ya maka kama da uzuri? Ya maka kama da dalilin da zai saka yin abinda kayi?" Ta karasa maganar tana kokarin mayar da hawayen da suke cike taf da idanuwanta, cike da rikici shima yake kallonta yanzun "Idan ban bisu ba zaki bani?" Sake jinjina murfin motar tayi dan ta fita, bata son ganin shi, ko kadan batason ganin shi, amman a rufe yake, hannu ta mika da nufin ta dauki mukullin motar da yake jiki, ya damqe hannunta yana saka dayan nashi ya cire mukullin motar ya saka a aljihun jeans din da yake jikin shi, sannan ya saki hannunta yana tsare ta da idanuwa "Karki gwada hakuri, kinga yanzun ke kika sa na tabaki, ki bari ki huce sai in bude miki ki fita. Ba zaki koma gidan mutane a haka ace na miki wani abu ba" Fuskarta ta rufe da hannuwanta, wasu hawaye masu dumi na zubo mata "Babe ki bari, ki daina kukan nan, kina sa inajin ina son in rikeki in lallasheki, kuma bakya so, ki daina kure hakurina, yanzun inbi wasu kice zakiji haushi" Sosai yasan yana bin mata tun kafin su hadu, amman bashi da wannan jarabar haka sai bayan ya hadu da ita, rashin samunta yasa shi son kashe wutar da take kunna mishi da duk macen da ta tari gaban shi, amman a daddafe yake lallaba rayuwar shi, ita dince taki fahimtar shi, taki gane halin da yake ciki, gyara zaman shi yayi cikin motar, yana sauraren sautin kukanta, harta dago fuskarta, ruwan da yake cikin motar ya dauka ya bude yana mika mata, harar shi tayi da idanuwanta da sukayi ja "Yi hakuri, ki sha ruwa to dan Allah" Karba tayi tana shan ruwan, ya duba agogon shi, shidda harda arba'in "Are you calm? Kice mun idan na tafi ba zaki sake yin kuka ba" Shiru tayi ta kyaleshi tana kauda kanta gefe, har lokacin kirjinta kamar an zuba garwashin wuta takeji "Babe... Kinsan a gajiye nake, kaina na ciwo wallahi, karki karamun, karki mun fushi. Ba laifina bane ba, bansan ya zanyi bane ba" Ya fadi yana wani irin sauke murya da ya kashe mata jiki, kallon shi tayi "Bana so, zuciyata na ciwo wallahi, dan Allah ka daina" Ta karasa maganar muryarta na karyewa, kai ya jinjina mata yana hade hannuwanshi waje daya "Karki mun fushi to, kinji" Kai ta jinjina mishi, tasan idan har tanaso ta canza shi, dole sai tayi kokarin fahimtar shi "Nagode... Kinsan ina sonki ko?" Kai ta sake daga mishi, kuma soyayyar nan da yake mata ita zatayi amfani da ita wajen kokarin canza shi, mukullin ya dauko daga aljihun shi yana bude mata murfin motar "Baki ce kina sona ba" Ya fadi yana daga mata gira, murfin motar kawai ta bude tana ficewa, yau bazai sami wannan na tunda laifi yayi mata. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 19 "Hello" Ta furta muryarta can kasan makoshi, kallo daya zakaiwa fuskarta ka fahimci yanda take cikin damuwar da tun jiya kowa yake dauka jimamin rabuwa da gidane "An daura, Hindu an daura" Hamza ya fadi daga dayan bangaren, runtsa idanuwanta tayi tana bude su, hadi da sauke wani irin numfashi, tun dazun take kallon agogo tana jiran karfe goma tayi, tana jiran taji canjin da marubuta kan fadi duk idan an daura auren ka, sai dai shiru, bataji komai ba, bataji a jikinta cewa an daura ba, da bai kirata ba sai dai idan taga dawowar wani daga cikin mazan gidan, yanzun ne dai muryar shi da tsantsar dokin da yake ciki yasa zuciyarta wani irin zirga-zirga a cikin kirjinta. Amman a kasan wannan akwai wani ciwo da yaki fitar mata tun jiya. "Okay..." Ta furta, tana jin hayaniya daga dayan bangaren kafin ta sauke wayar daga kunnenta tana katse kiran ta ajiyeta kan mudubi "Ke anata neman ki, kin karya?" Biebee data leqo dakin ta bukata, dan su sun tafi wata hidimar, kai Hindu ta girgiza mata "Sugar bana jin yunwa wallahi" Cewar Hindun kamar yanda takan kira Biebee wani lokaci, dan kallonta Biebee tayi "Zaki zauna ulcer ta kamaki, aure fa akayi miki ba wani mugun abu ba, is not like ba zaki dinga zuwa gida ba" Murmushin karfin hali kawai Hindu ta iya yiwa Biebee din, tana tsintar kanta da kasa furta komai "Ni dai zan hado miki tea" Ta karasa maganar tana juyawa, numfashi Hindu ta sauke, tana saka hannu ta gyara zaman dankwalin da yake nade a kanta, ba wata kwalliya bace mai nauyi a kan fuskarta, amman tayi kyau matuka, ba kunshin hannunta ba, yanayinta kawai idan ka kalla zaka gane itace amaryar, taji dadin kasancewar ita kadai a cikin dakin. Biebee batafi mintina biyar ba ta sake dawowa, wannan karin tana shigowa har cikin dakin, ta mika ma Hindu kofin shayin data hada shi da kauri sosai yanda zai rike mata ciki. Sannan ta fice daga dakin, kofin Hindu ta daga takai bakinta ta kurba a hankali, sai taji idanuwanta sun cika taf da hawaye "Oh shit..." Sune kalman farko da Hamza ya furta a daren jiya da misalin karfe tara da rabi na dare, bayan ya daga video call din da tayi mishi da alama babu shiri, bai kuma yi nufin ya daga ba, abin yazo mishi a shammace, yanda take ganin yanayin hoton na rawa, da alama so yakeyi ya kashe, amman a rikice yake "Ka sallameni dare nayi" Ta sake jin muryar yarinyar da ko idanuwanta ta rufe tun jiyan tana sake dawo mata, kafin Hamza ya kashe video call din yanata maimaita "Oh shit" Abinda ya taso yai tsaye bayan zuciyarta har yanzun tana jin shi, yaki fitowa, kuma yaki wucewa, hotunan kwalliyar da akayi matane da ta tura mishi taga baice komai ba, kuma tun da yamma basu kara magana ba, shisa ta kira shi video call din, dan tayi kewar shi a yinin ranar ba kadan ba, tana kuma da tabbacin ba bacci yakeyi ba, har yanzun tana dana sanin kiran shi da tayi. Yafi mintina talatin tsakani kafin ya kira wayarta, zuwa lokacin hawaye ma ta neme su ta rasa, harabar gidan ta fita dan ta samu sararin yin video call din dashi, jikinta babu inda baya rawa lokacin da ta kara wayar a kunnenta "Bansan me zance miki ba" Ya furta daga dayan bangaren yana ba hawayen da take ta nema damar zubowa "Ran daren auren mu? Hamza ranar daren auren mu? Me kake nema? Me yake damunka da ba zaka iya jira ba? Awanni nawa suka rage mana? Me yasa zakai mun haka?" Tana jin yanda yake sauke numfashi "Bansan me zance ba" Ya sake furtawa "Karka kara cemun bakasan me zaka ce ba, wallahi karka kara" Tayi maganar a masife "Idan nace miki bazan iya jira bane zaki yarda?" Numfashinta taji yana mata barazana, Hamza so yakeyi ya kasheta taga alama, inda wani yace mata wata rana kirjinta zaiyi kamar an dora dutse haka ba zata yarda ba, amman yau har wuta take ji kamar tana ci a cikin shi saboda zogin da yake mata "Bazan iya jira ba Hindu, in ba mutuwa kike so inyi ba" Bakinta ta bude tana neman iska ko zata samu tayi numfashi, kafin dakyar ta iya cewa "Kai zaka kasheni Hamza, so kakeyi ka kasheni" Tana jin numfashin daya sauke "Karki karamun abinda nakeji, dan Allah yau kawai, yau kawai ki kyaleni. Awanni kadan ya rage mana kamar yanda kika ce, ki kyaleni inyi abinda zan samawa kaina sauki kafin su cika" Ya karasa maganar yana kashe wayar, saukewa tayi daga kunnenta, wasu hawaye masu dumi na zubar mata lokacin da take danna wayar tana kiran shi, bata saka a kunne ba sai da taga ya daga "Babe" Ya kira da wani irin yanayi a muryar shi "Wanne bangare na ki kyaleni ne baki gane ba?" Hannu tasa ta goge fuskarta "Baka isa ba, wallahi kayi kadan kaimun abinda kai mun sannan kace in kyaleka" Ta karfi da yaji Hamza ya koya mata masifa, duk da bawai bata fada bane ba, na yanzun ne yafi na da, bala'in shi yasa bata shakkar gaya mishi magana lokutta irin haka "Idan baki kyaleni ba ya zakiyi dani? Na zaba miki abinda yafi sauki ne amman kina so ki karama kanki ciwon kai" Dariya tayi da bata da alaka da nishadi sam, zuwa yanzun batajin akwai wani abu, ko wata magana da zai fada ta bata mamaki sam "Babu yanda zanyi da kai, amman batamun ran da kayi sai Allah ya saka mun" Ta furta muryarta na rawa, bata jira mai zaice ba saboda kukan da takeji yana neman kwace mata, ta kashe wayar. Kan cinyarta ta dora tana hade kanta da gwiwa wani irin hawaye masu dumi na zubo mata, kamar yanda ta hada shi da Allah yanzun, haka zataci gaba da hada shi da Allah har saiya canza, tana da yakinin zai canza, ba zaizo mata da sauki ba, amman zata jure, zatayi wannan jahadin, zata canza shi. Idan tana gidan shi hakan zaifi saurin faruwa, zata tabbatar da ita kadai ta ishe shi, saboda zatayi mishi duk wani abu da yake so. Kiran shi ne ya shigo, sai da taja hanci, tana sake goge fuskarta, tukunna ta dago kai, tana daukar wayar da ta yanke, ajiyar zuciya kawai take saukewa, sake kira yayi, ta daga ta kara a kunnenta "Ni zaki hada da Allah? Hindu ni zaki hada da Allah? Tashin hankali kike nema dani ko?" Dafe kanta tayi tana furta "Kai! Kai jama'a, oh Allah na" Saboda batasan me kuma yake so tayi ba, batasan ina yake so ta tsoma ranta ba, shi yayi mata laifi, amman yana neman yafita rigima akan abin, zuciyarta ciwo takeyi, baisan ya bata hakuri ko zataji sanyi ba, dan lallashi ma bata samu ba, amman shi yake so ya fita hayaniya "Me kike nufi?" Kai take girgizawa "Babu komai, Hamza babu abinda nake nufi, sai da safe" Har ranta wayar tayi niyyar kashewa, bata da karfin biye mishi, abinda takeji kawai ya isheta "Babban kuskuren da zakiyi ki kashemun waya, wallahi karki kashe mun waya Hindu?" Wasu hawayen taji sun sake zubo mata, kashedin shi na zauna mata "Ya kake so inyi? Me kake nema dani? Baka tausayina ne? Baka san me nake ji ba ko?" Tayi maganar muryarta na karyewa, tana jin yayi shiru, kafin cikin sanyin murya yace "Kece bakya tausayina saboda bakisan halin da nake ciki ba, da kinsan me nakeji a daren yau da baki nemi hadani da Allah ba, kamar zunuban da nake dauka da kaina basu min yawa ba, shine kike son karamun wani" Kara karya mata zuciya yake, balle cikin yanayin da yayi maganar kamar shima zaiyi mata kuka "Ko dan kin fini saurin kuka? Shisa duk abinda zai faru nine mai laifi?" Batasan me zatace ba "Ki bani hakuri, kin batamun rai bayan banajin dadi, Babe ki bani hakuri" Numfashi Hindu ta sauke "Kayi hakuri" Ta tsinci kanta da furtawa ko wayar zata zo karshe, numfashi mai nauyi ya sauke mata cikin kunne "Ya wuce, ina son ki, kinsan haka ko?" Kai kawai ta daga, kafin tace wani abu ya rigata "Sai da safe, ki kulamun da kanki" Yana kashe wayar kamar shikenan, kamar idan abinda yake ikirarin tayi mishi ya wuce a wajen shi itama abinda yayi mata ya wuce a wajen ta, kamar yarinyar da yabi yau laifinta ne shisa baiga dalilin da zai bata hakuri ba, takai awa daya a zaune a wajen, sai da taga bayan ciwon zuciya, zazzabin ciwon sauro na gab da kamata tukunna ta tashi ta shiga cikin gida, baccin kirki ma bata samu ba, dan duk yanda zata rufe idanuwanta sai taga Hamza da wasu matan. Haka ta tashi safiyar yau komai bayayi mata dadi, shisa bata ma neme shi ba, shima din daya kira tsintar kanta tayi da rashin son yin magana da shi. Hawayen da takeji suna shirin zubo mata takai dan yatsa tana sharewa. Kukan zai jira, nan da yan wasu awanni zatayi mai dalili, dan da wuri za'a kaisu. Tea dinta ta kara kurba, tun da yan uwan Baba dana Anty, harda ma wasu cikin na Mama sukaje jere suka dawo suke maganar gidanta, kujeru saiti biyu Baba yai mata, Hamza ma yaso subar maganar kayan dakin, tadai fada mishi Baba bazai taba bari ba, amman taji suna cewa dakunan suna da yawa, ko falo guda hudu ne a cikin gidan, a biyu kawai sukayi jere, sauran ma duk an kawo kayan daki suna lullube a cikin ledoji ko bude su ba'ayi ba. Kowa maganar gidan yakeyi, har ranta wannan yayi mata dadi, gidan da take mafarkine, ko a hoto Hamza bai taba nuna mata ba, basu ma tabayin maganar gida dashi ba har saida akazo maganar yin jere tukunna. Ance gidan Khadee ma babu laifi, duk da karamine, daki biyu, amman a iya karfin shi, yayi kokari matuka, ko ina yasha tayal. Khadee dinma da kanta sai da tazo cikin murna tana fadin "Ke banza kinga yanda ake maganar gidan ki? Ance ya hadu wallahi, kina zuwa kiyumun video" Murmushi kawai tayi, Hamza ya rage mata walwalar da ya kamata ace tanayi, ya kamata ace tana tunanin Dinner dinta da za'ayi karfe takwas na ranar. Amman zuciyarta ciwo takeyi mata, dakyar ta samu ta karasa shanye shayin, tana barin kofin nan kan mudubi, ta mike ta karasa kan gado ta sami waje tayi zamanta, tana kallon yanda Aunties dinta suke shigowa sunata tsokanarta da fadin "Yarinya zuwa sha biyu zamu tattaraki mu kai ki" Da sun fadi haka sai taji zuciyarta tayi wani irin tsalle, ba'a fadi wannan fargabar da tashin hankali na tunanin barin gida ba a littafi, kwanciya tayi jin alamar zazzabin tashin hankali da yake shirin rufeta. * Bai taba gajiya da daukar hoto ba sai yau, babbar rigar da take jikin shi ta ishe shi, yana fitowa daga motar da tayi parking cikin gidan Fodio ya fara cire babbar rigar jikin shi, yana cire hular ya rike hannu ya taka zuwa bakin kofar da zata shigar dashi gidan, yana jira AbdulHafiz da mukullin yake a hannun shi ya karaso yazo yana bude gidan. Shigewa Hamza yayi hadi dayin sallama, ya jefe babbar rigar akan kujera ya samu waje ya zauna. Tun karfe goma aka daura aure, amman azahar ma a hanya suka tsaya sukayi, sai yanzun ne suke shigowa gida. Ko karin kirki bai tsaya yayi da safe ba, tun jiya yake jin shi a hargitse Daya motsa sai yayi kamar wasu sarqoqi ne suke biye dashi suna jiran lokaci ya cika su daure shi waje daya, zuciyar shi taki aminta da cewar auren shine aka daura, badan sarkokin da yakeji sun dabaibaye shi ba, zai dauka ko mafarki yakeyi, da suka fito daga wajen daurin auren ma, yana kula da kallon da Fodio yake yi mishi, kamar shima yana mamakin yanda akayi Hamza yai wannan wautar, yanda ya yarda ya daukar ma kanshi gagarumin nauyi kamar aure. Har a kasusuwan jikin shi yakeji bai shirya ba, shine abinda yasa shi sulalewa ya fice daga gidan jiya ya nemi yarinyar da Hindu bata tashi kiran shi video call ba sai da suna tare. Ba kuma zaice ya akai ya dangwalo wayar ya amsa video call din ba, ga kan shi da yakeji da nauyi sosai tamkar an dora dutse, giya ta fara dira cikin shi a safiyar yau, sai shayin daya kurba dakyar, kamar kayoyi ne a cikin shi ko wasu itace haka yakeji. Ana fadin "Amin" Sai da yaji wani abu ya tsirga mishi har zuciya yana sa hanjin cikin shi kullewa waje daya. Shikenan an daura, shikenan an mishi katanga da abubuwa da yawa a rayuwar shi, abubuwan da bai shirya bankwana dasu a yan wasu shekaru masu zuwa ba, yanzun ma mikewa yayi yana nufar kitchen, AC din dakin bata hana zufa tsatsafo mishi a goshi ba, yana shiga kitchen din fridge ya nufa ya bude, giyar ta gwangwani ya dauka ya bude yana dagawa ya kwankwada, sanda ya sauke gwangwanin yasha fiye da rabi, numfashi yake mayarwa kamar wanda yayi gudu. Yasa hannu ya balle maballin rigar shi guda biyu, dan yanajin kamar sun taimaka wajen shaqe mishi wuya suna barazana da kaikawo na iskar numfashin shi. Motsin da yaji sai da ya zabura, juyawa yayi yaga AbdulHafiz da yake kallon shi, gwangwanin ya daga yana karasa shanye abinda yake ciki, saida ya matsa shi da hannun shi tukunna ya jefa cikin kwandon shara, yana kallon AbdulHafiz din ya saka hannu a cikin aljihun shi ya zaro wata farar takarda yar karama yana karasowa ya ajiye mishi akan kantar kitchen din, ya mika hannu ya bude fridge din ya dauki ruwa yana ficewa. Idanuwan shi Hamza ya runtsa yana bude su akan yar takardar da take dauke da rubutun da akayi da pensir "Isra'i:32" Runtsa idanuwan shi Hamza ya karayi, fassarar ayar na yawo a cikin su "KADA KU KUSANCI ZINA, DOMIN ITA ALFASHA CE KUMA TAFARKI NE MUMMUNA" Bude idanuwan shi yayi yana ganin rubutun da yake kasan na farkon "Nur:02" Wannan karin numfashi Hamza yaja mai nauyi yana fitarwa "MAZINACIYA DA MAZINACI, TO KUYI BULALA GA KOWANNE DAYA DAGA GARE SU, BULALA DARI. KUMA KADA TAUSAYI YA KAMAKU GAME DA SU A CIKIN ADDININ ALLAH IDAN KUN KASANCE KUNA YIN IMANI DA ALLAH DA RANAR LAHIRA. KUMA WANI YANKIN JAMA'A DAGA MUMINAI, SU HALARCI AZABAR SU" Yakai mintina biyar yana kara jin shi a hargitse, tun jiya AbdulHafiz yake mishi wannan abin, yana kara hargitsa mishi lissafi, ya manta ranar karshe dayaji zunuban shi nabin shi kamar zasu kayar dashi sai bayan yarinyar jiya. Daga ayoyin da sukayi magana akan hukuncin zina, sai kuma wanda sukayi magana akan muninta da yanda take ragargaza imani tare da ayyuka. Yau tunda safe ya ajiye mishi ayar da tayi magana kan a jefe wanda yayi zina da aure. Yana da tabbacin da yawa AbdulHafiz din ya samo ya rubuta yana ajiye mishi duk wadda hannun shi yakai ya dauko. Baiyi magana ba, baice mishi komai ba, saboda bashida abin fada, tunatarwa ce AbdulHafiz yake yi mishi, kuma daga ranar daya fara bin mata ya rigada ya hango barin hakan duk ranar da aka daura mishi aure, saboda bai shiryama daukar wannan gagarumin zunubin ba, da kan shi dai bayajin yana da karfin daukar hukuncin zina da aure, a lokaci daya kuma yanzun shaidan na kallon shi a gefe, yana saka shi tunanin yanda zai kare gabaki daya rayuwar shi da mace daya tal. Tunda aka furta Amin din data kulle shi karkashin inuwa daya da Hindu ya kiraya ta amsa shi da "Okay" Ta kashe sai ya kara jin duk wani zumudi da yake ya fita kan shi, tsoro da firgici sun maye gurbin shi, ga AbdulHafiz da bai taimaka wajen samun nutsuwar shi ba, asalima so yake ya karasa firgitar da shi. Dakyar ya iya dafa bango ya fito daga falon, ya samu Abdallah ya dawo, tunda shi gidan su Hamzan ya wuce, Anna ta kira suzo su karbi abinci, har ya fara zuzzuba musu, waje Hamza ya samu ya zauna. Yanajin hirar da suke kamar zasu tashi dakin, amman sam hankalin shi ba'a kansu yake ba, abincin kawai yake kaiwa bakin shi yana hadiyewa badan yana gane dadin shi ba. AbdulHafiz ne ya mika mishi robar ruwan daya dauka da sauri yana budewa ya sha, sai lokacin yaji abincin da yaketa hadiya ya karasa cikin shi inda ya zauna da wani irin yanayi. "Ka ajiye idan ka koshi" AbdulHafiz din ya fadi da harshen fulatanci, yana saka Hamza dagowa ya kalle shi "Kamar ka damu da lafiyata" Ya amsa yana cigaba da hadiye abincin shi, yayi niyyar ajiyewa, maganar da AbdulHafiz din yayine ta saka shi karasa cinye abincin da yake cikin plate din, aikam ji yake kamar zai mutu saboda cikar da cikin shi yayi, ga shinkafar tayi mishi tsai-tsaye. Ajiye plate din yayi yana mikewa "Ina zaka je?" Arafat ya bukata "In da ka aike ni" Hamza ya amsa shi yana tsallake Fodio ya wuce kitchen, gwangwanye hudu ya diba na giyar shi yana dawowa ya wuce daki, ya doko kofar kamar zai karyata, yana saka Arafat runtse idanuwan shi da karar "Ni kadai ne ko yanayin Hamza da gaske ya canza tun da aka daura auren nan?" Arafat ya tambaya yana kallon su "Kai mun alfarma daya Arafat, da kaji na fara maganar aure, ka kamani, ka girgizani, idan banji ba, ka daukeni ka tsoma kaina a bokitin ruwa, kayi komai daya kamata, amman ka duba abokantakar mu, karka barni inyi kuskuren da Hamza yayi" Dariya Abdallah yayi yana kallon Fodio "Auren nan fa dadi gare shi, ka koma gida a gajiye ka samu wadda zatayi maka sannu ma da dadi, koya aka bata maka rai a waje in ka koma gida yaranka zasuyi wani abin da dole saiya sakayi dariya" Zuciyar shi Fodio ya dafe yana girgiza kai "Abdallah ina magana da wanda zasu fahimta, gabaki daya rayuwar ka akan iyali ta kare, duk zaman da zakayi maganarka kenan" Murmushi Abdallah yayi yana ajiye plate din abincin shi, dan ba wani mai yawa yaci ba, zai koma gida suci, bayason ya cika cikin shi. Fodio ba zai taba fahimtar yanda aure yake ba, in zai kwana yana mishi bayani, kuma yasan rayuwar gidansu Fodio din ta taimaka sosai wajen saka mishi kokwanton nan. "AbdulHafiz ba zakace wani abu ba?" Abdallah ya tambaya, AbdulHafiz din na girgiza mishi kai "Bazan bata bakina akan Fodio ba, zan mishi addu'a da maganganun" Ya karasa yana mikewa shima, gara ya watsa ruwa ya canza kaya, yanzun zasu kara fita daukar yan kai amare, inya dawo saiya duba Hamza, bashi da kalaman da zaiyi amfani dasu ne, har ran shi yakejin kamar akwai kuskure a auren nan da Hamza yayi, saboda ta kowacce fuska yau Hamza ya nuna sam bai shirya daukar nauyin daya dorama kan shi ba. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 23 Tunda Hamza ya tashi wajen karfe hudu tana jin shi, sai da ya fice daga dakin tukunna ta bude idanuwanta, akwai wani abu da yazo yayi mata tsaye da bashi da alaqa sam-sam da abinda ya faru shekaranjiya. Tasan jiyane ya zame mata daren farko, da shima yazo mata ba'a yanda ta tsammata ba, har ranta taso jin yanda ita din take daban da sauran matan da take da tabbacin Hamza yayi mu'amala da su a baya, taso ya fada mata ita din daban ce, ko dan mutuncin ta da ta kawo mishi, ta so jin tarin alkawurra a bakin shi, a kasan irin wahalar da tasha, kunnuwanta a bude suke cike da shirin jin duk wannan abubuwan. Batace sai ya bata kujerar makka kyautar kawo mutuncinta ba, duk da tasan yana da halin hakan, amman idan ya fada mata yanda ita din daban ce, yanda baisan abinda ya dingayi da rayuwar shi kafin ita ba zataji dadi, gaya mata ya samu duk abinda yake nema a jikin mace a tare da ita, yayi mata alkawari cewa tunda gata, shi da wasu matan sai dai kallo daga nesa, yanda ta tsammaci zai rikice a kanta ba haka taji abin ba sam-sam. Ga labaran da ta dinga ji da wanda ta dinga karantawa kala-kala, sam basu ko da kusan karya gado yanda ta hasaso ba, bata majin idan akwai mutum a dayan dakin zaiji su. Jin shigowar Hamza yasata saurin lumshe idanuwan ta. Shikam kaya yaje ya dauko daga bangaren shi, a kan gadon daga gefe ya ajiye su yana wucewa bandaki. Da gaske ne akwai nutsuwar da tazo mishi tare da macen da ta kasance ta shi, halalin shi, bai tashi da Hindu manne a kirjin shi yanajin wata irin dauda ba, kuncin da kan jiyarce shi duk lokacin da yabi sauran matan da dana sanin da yakeji sam babu su yau, asalima sai yake jin shi daban, ita ma Hindun sai yajita daban. Ba sai wani ya fada mishi dan ita din halalin shi bace ba. Sai dai a kasan duk wannan yana tunanin ace ya sami mata masu yawan gaske da zasu zama halalin shi. Sai dai tunda shi ba basarake bane ba, musulunci hudu ya halarta mishi zai iya samu ta wannan hanyar, ko a mafarki kuwa bai hango kan shi da mata hudu ba, yana da halin rike su, amman ba zai iya ba, da ace kwana bibbiyu ne, idan yayi hudun za'a kwashe su a zuba mishi wasu kamar yanda ake kiwon kaji zai so hakan. Har cikin kasusuwan jikin shi yake jin wani irin tsoro na ziyartar shi, sau daya ya kasance da Hindu, amman kamar ba zata rike shi ba, ita din kadai ba zatayi mishi ba. Ba kuma yason inda tunanin shi yake kai shi, shisa ya sakar ma kanshi ruwan sanyi, yana yin tsalle gefe babu shiri, hadi da mika hannu ya kashe shawa din yana maida numfashi. Ruwan yayi mishi bala'in sanyi, dole ya dai-daita zafin. Bai fito ba saida ya dauro alwala, ya zame towel din jikin shi yana sake kaya, zuwa lokacin yana jin kiran sallah kasa-kasa. Kafar Hindu ya fara bubbugawa a hankali, su duka ba wani baccin kirki suka samu ba, amman idan tayi sallah sai ta sake komawa, shima idan ya dawo ya gama tilawa da azkar din shi bacci zai koma. "Hindu..." Ya kira a hankali yana sake dan dukan kafafuwanta, tana jin shi tunda ba bacci takeyi ba, wani malolon bakin ciki ne taji ya taso mata, ya za'ayi a darenta na farko ya dinga tashin ta kamar tana gidan su, ko Asma tasan ta tsani a bubbuga mata kafa in za'a tasheta, tama tsani a bubbuga mata ko ina, tunda ba nauyin bacci gareta ba, idan ka kira sunanta ma zataji. Ya yake so tagane banbancin auren da tayi da kuma gidansu, ita yanzun tana da miji, yanda ta hasaso zai dinga tashin ta daban da yanda yazo yana tashinta yanzun. Ta dauka daya fito wanka zaizo gefenta ya zauna, saukar ruwan da yake digowa daga sumar shi zata fara ji a wani bangare na fuskarta, kafin lausasan labban shi kan goshin ta yana kiran sunanta cike da soyayya, bayazo yana bubbuga mata kafa yana kiran sunanta gatsau irin haka ba. "Hindu..." Tana jin shi sarai, idanuwanta sun fara tara hawayen bakin ciki "Hindu ki daure ki tashi, in kikayi sallah saiki koma baccin" Hamza ya fadi yana balle maballan jikin rigar shi, kafin ya kara matsawa yana zama gefen gadon, taji shi, ashe ya iya irin wannan zaman yai mata qerere. "Hindu..." Ya kira a hankali yana dora hannun shi a jikinta hadi da dan girgizata, sai lokacin ta bude idanuwanta a hankali tana sauke su cikin nashi, kwan fitila daya ya kunna, babu wadataccen haske a dakin, amman ya isa taga yanda yayi wani irin kyau, fuskar nan fayau da ita, kamar ta kai hannu ta shafi sumar da take kwance luf-luf akan fuskar shi "Wani abu na miki ciwo?" Ya tambaya cikin taushin murya, kai ta dan daga mishi a hankali "Sannu, tashi ki samu kiyi sallah" Ya karasa maganar yana mikewa, hadi da kama hannunta, ya taimaka mata ta mike daga kan gado, hannunta na cikin nashi harta tashi, tana kokarin langabewa a jikin shi ya tare ta "Karki karyamun alwala Hindu" Shagwabe fuska tayi, idanuwanta cike taf da hawaye, bai kamata sam yace ta samu tayi sallah ba, ina laifin ma tunda ta tashi ya dauketa ya kaita bandakin, wankan ma daya jirata sunyi tare "Ni jikina ciwo yake mun" Kallonta yayi, yasan dole jikinta zai mata ciwo, amman ba kamar yanda take nuna mishi ba, shagwaba ce kawai take son yi mishi ba wani abu ba, yasan me yakeyi, ba ita bace cikakkiyar macen daya fara kasancewa da ita ba. Hannunta ya dumtsa yana janta zuwa hanyar bandaki, gabaki daya sai langabe mishi takeyi, a dole dakyar take iya taka kafafuwanta. "Hindu masallaci zan tafi fa..." Hamza ya fadi, haka kawai yaji dariya nasan kubce mishi, inda yasan wannan rainin hankalin zatayi mishi, daya bata dalili mai karfi nayin hakan. Kallon shi tayi, sosai idanuwanta suke cike da hawaye, shi da yake da sabuwar amarya ina yaga ta fita masallaci "Ban hanaka ba ai" Ta karasa maganar muryarta na karyewa, numfashi ya sauke, yana rasa abinda ya kamata yayi, after care din nan sam ba sabon shi bane ba, mace ma bata dade mishi harya tsaya yana lallabata, bai saba ba, komai yana mishi wani iri. Hannun shi ya zare daga cikin nata tunda yana da tabbacin babu abinda ba zata iyayi da kanta ba "Yanzun zan dawo, kisa ruwa mai dumi sosai kiyi wankan" Ya karasa yana juyawa, cike da mamaki Hindu take binshi da kallo, da gaske ficewa Hamza yayi daga dakin, da gaske ba zai tayata yin wankan ba, balle tasa ran zai nadota da towel ya daukota ya kawota ya kwantar. Hawayen da suka silalo mata tasa hannu ta share, ta lallaba tana shiga bandakin, shawarar shi ta dauka tayin amfani da ruwa mai dumi sosai. Kafin ta fito kam har jikinta yayi mata dadi. Doguwar riga ta samu ta saka, ta gabatar da sallar asuba, tana zaune tana azkar, harta idar ta karanta Qur'ani shafi biyu Hamza bai shigo ba. Hakan yasata jan jikinta ta mike, hijab din ta cire ta ninke, tana komawa kan gado ta kwanta. Duka yanda ta hango safiyar yau ba haka tazo mata ba, itama ta hango bayan Hamza ya nadota ya fito da ita, ya sami kaya ya saka mata ya kums gama lallashinta, ta mike tayi sallah, kanta tsaye gaban mudubi zatayi ta tsantsara mishi kwalliyar da zata sake rikita shi, amman ko mai bata shafa ba, turare ma sabo dayine yasa tadan fesa ta cikin rigar jikinta tun kafin tayi sallah. Amman baccin da takeji a idanuwanta da kuma disappointment din da ya danneta bai barta da wani zabi ba. Zata dora laifin akan Hamza, daya bata kwarin gwiwa da tayi kwalliyar, tana wannan mitar a ranta bacci yayi awon gaba da ita. * Sosai take jinta daban, komai nayi mata wani iri, da sanyi-sanyi takeyin komai, jiyan batazo mata da wani yanayi ba. Sun fita da rana sukaci abinci ita da Hamza, amman fitar da sukayi da dare tayi mata dadi ba kadan ba, har Havila ya biya da ita ya kwaso mata ice cream. A bangaren shi suka kwana, bata samu dukkan abinda tayi tsammani ba, amman ta sami wani abu daban. Yau kuma tunda sukayi asuba suka koma bacci, basu tashi ba sai wajen goma da rabi, dukkan su wanka sukayi, tunda da dare ya fada mata zasu je su gaishe da Anna. Haka kawai sai zuciyarta ke mata rawa, fargaba na saukar mata. Ta zabi kaya sunfi kala biyar tana mayarwa, har saida Hamza yace mata "Ki kwantar da hankalin ki, Anna bata da matsala" Kallon shi tayi "Me zan kai mata? In kai mata turare?" Dan jim yayi, kafin ya daga ma Hindu kai, yasan Anna da kamshi, zataso turare. Kai Hindu ta jinjina mishi "Dan Allah ki saka kowanne kaya, kinga yunwa nakeji ni..." Riga da skirt ta dauka na atamfa, ta wuce tabar shi a zaune, sakawa tayi, ta fito da wata Abaya da Baba ya siya mata, baifi sau biyu ta saka ba, saboda tana bala'in ji da ita, natsuwa tayi ta daura dankwalinta, ta feshe jikinta da turaruka masu saukin kamshi, shi kanshi Hamzan kallonta yakeyi saboda yanda tayi mishi kyau, banda jan janbaki da eyeliner babu wata kwalliya a fuskarta. Saida ta samu leda ta zuba turarukan wuta da aka kawo mata, dana sakawa a cikin kaya, da ma wasu ta ajiye a gefe tukunna ta dora abaya din, tana daureta ta zauna mata das, mayafin ta dauka ta dora a saman kanta tana yafashi ta baya. Bata wani dauki takalmi mai tsini ba, flat ta saka sai jaka data dauka fara, kalar takalmin. "Muje?" Ta furta tana kallon Hamza da yakejin kamar su fata fita, dan dai ya fadama Anna zasu zo, amman Hindun tayi mishi kyau ba kadan ba "Kinyi kyau" Murmushi tayi "Kaima haka..." Ta furta, ya saka shadda, golden mai haske, sai daukar ido takeyi, ga kamshin shadda mai tsada daya hadu dana turarukan shi, mikewa yayi "Ina wayar ka?" Ta bukata, hannu yasa a aljihu, haka kawai yasan hoto zata dauke su, cire wayar yayi daga key yana matsawa kusa da ita ya daga camera din yana daukar su, sosai sukai hotuna wajen kala goma, dan wani ma saida ya sumbaci kuncinta tukunna suka dauka, dariya sukeyi idan sukayi wani style din, kafin bikin Hamza yayi kara "Ke yunwa fa nakeji, ki wuce mu tafi wallahi" Dariya tayi tana daukar ledar dayasa hannu ya karba suka fita tare, har mota shi ya bude mata, haka kawai sai take jinta da wani irin muhimmanci a wajen shi, bakomai dan har yanzun bai nadota a towel ba, tasan dabarar da zatayi hakan ya faru, bari dai ta samu ta kama zuciyar Anna. A nutse Hamza yake tuqin shi har suka isa gidan, yayi parking yana fitowa. Kallon gidan Hindu takeyi, yayi mata kyau matuqa duk da baikai na Hamzan ba. Shi ya fara yin gaba suna shiga cikin gidan da sallama, sosai gabanta yake faduwa, kafin matar da tasha ganinta a hotuna, kuma bata gajiya da mamakin cewa itace mahafiyar Hamza ta amsa musu sallamar "Ann" Hamza ya fadi yana karasawa da fara'a a muryar shi, dan rike mata kafadu yayi yana sumbatar kuncinta "Ina kwana..." Ya furta, Hindu na tsaye tana kallon su "Kai ba zakace ta zauna ba" Ann ta fadi cikin yaren shuwa, duk da Hausa Hamzan yayi mata, tana mayar da hankalinta kan Hindu hadi dayin murmushi "Ina kwana" Hindu ta fadi, da alama tanajin Hausa, kafin ta amsa Hamza ya karaso inda Hindu take yana fadin "Ki zauna" Batayi musu ba ta sami kujera ta zauna, dan kafafuwanta sun mata wani irin nauyi, kujerar da take fuskantar ta Hindu, Anna ta zauna "Nifa yunwa nake ji" Hamza yai maganar da harshen Anna din, duk suna saka Hindu jin wani iri "Karki damu da shi kinji ko, kin tashi lafiya?" Sai dai kafin Hindu ta amsa, wata siririyar yarinya da Hindu taga hartafi Hamza kyau ta fito, jikinta sanye da doguwar riga irin ta mutanen saudiyya, kanta daure da jan dankwali ta rigata da "Inalillahi.....Ann tayi Hausa...." Kusan a tare Hamza ma dayake tsaye baki a bude yace "Ann!" Ko kallon su Anna batayi ba, Hindu kuwa ta kasa daina murmushi, kafin yarinyar ta karaso ta zauna gefen Hindu "Matar Yayan mu" Kallonta Hindu tayi "Yaaya kagama boye mana ita, yau gata har gida" Dariya Hamza yayi "Daman kune da gajen hakuri ai" Gaisawa Hindu tayi da Auta, data mike daga inda take zaune tana fadin "Nikam ban karya ba" Hamza da sauri yace "Wallahi nima" Wannan karin Anna ce ta mike "Ku gama karyawa, ina zuwa" Dan taga Hindu a takure take, yarinyar tayi mata kyau, ta kuma burgeta matuqa, sam batayi mata kama da irin tsagerun yaran zamanin nan ba. Tana bar musu wajen, Auta na kama hannun Hindu ta mikar da ita "Ki zo muje muci abinci" Ba shiri Hindu ta ajiye jakarta tana binsu, har wajen cin abincin, suka zauna. Da kanta yarinyar ta zuba ma Hindu plantain da soyayyen dankali, ta kuma hada mata Tea "Auta baki ganni bane halan" Hamza da harya gaji da jira ya fadi yana mika hannu ya dauki kofin shayin Hindu, Auta ta kuwa rike mishi hannu "Sake mun hannu" Kallon shi tayi "Kabar mata nata dan Allah, zan hada maka yanzun" Da fulatanci tayi mishi maganar, saboda sam ba sabawa sukayi da yiwa juna Hausa ba. Ajiyewa yayi kuwa, ta hada mishi nata, ita Hindu duk da yunwar da takeji a kunyace take, sukam hira sukeyi kamar bata wajen, da alama itace ta takura kanta. Auta ma nan tabar su, sai lokacin Hamza yace "Ke ba zakici abinci ba ko? Karki cemun kina jin yunwa Allah" Murmushi tayi, da sauri-sauri take cin dankalin kafin su kara fitowa, sai dai harta gama babu wanda ya fito, falon suka koma suna zama ita da Hamza, da alama flashing yayiwa Anna, sai gata ta fito "Tafiya fa zamuyi Anna" Hamza ya fadi, kallon su tayi "Ayita hakuri kunji, Allah ya baku zaman lafiya" Hindu sunkuyar da kanta tayi, Hamza ne ya mike yana daukar ledar daya ajiye ya karasa ya mika ma Anna "Wai a baki Anna" Da murmushi tasa hannu ta dauki ledar "Ma shaa Allah, nagode sosai. Allah yasa albarka" Mikewa Hindu tayi "Mungode Anna, Allah ya kara girma" Sannan sukayiwa Anna sallama, tace musu Appa ya fita, dan haka suka wuce kawai. Suna fita daga gidan Hindu na sauke wani numfashi da batasan tana rike da shi ba. "Matsoraciya" Hamza ya fadi yana dariya "Nace miki Anna bata da matsala baki yarda ba" Murmushi tayi "Nagani aikam, na dauka kana da kyau sai da naga Auta" Dariya yayi sosai wannan karin "Faruk yafi kowa kyau, duk zaki gansu a hankali, mu biya mu siyi abinda zamuci da rana?" Kai ta daga mishi "Har dare ma, mu saka a fridge..." Kai kuwa ya jinjina mata, suka biya Chicken Republic, sannan suka wuce gida. * Sati biyun nan a jigace tayi su, ta dauka zaiyi mata kadan, yanda ta hasaso satika biyu babu inda zasu kaisu, amman yanzun da kanta take neman hanyar da Hamza zai fita daga gidan ko na yini dayane ko zata samu sauki "Ba yau zaka koma aiki ba?" Ta bukata, ganin ya bude system din shi, kallonta yayi ta kasan idanuwa "Kingaji dani ne?" Kai ta girgiza mishi a hankali, amman yasan karya takeyi, a idanuwanta yake karantar hakan. Kuma dole ta koyi hakurin zama dashi tunda a yanzun ita kadai yake da ita, ganin yayi shiru ya bata karfin gwiwar yi mishi tambayar da take ta cinta a rai "Ba zamuje honeymoon din mu ba?" Saida yayi kamar baiji taba, tukunna ya dago idanuwa, kafin ya kwashe da wata irin dariya, ganin tana zaune dai tana kallon shi yasa shi fadin "Wai da gaske kike?" Kallon shi dai takeyi har lokacin, dan sam bataga abin dariya a maganar da tayi ba "Da gaske kikeyi" Ya furta yana tabbatar ma kanshi "Hindu anan ma harkin gaji dani, idan muka tafi wani waje wallahi ba zaki iya ba, kuma kin kusan komawa makaranta ma..." Dan turo mishi labba tayi, da gaskene ta kusan komawa makaranta, amman hakan baya nufin zai hana musu zuwa honeymoon dinsu in yayi niyya, kasar wajen a kwana nawa ma za'a iya zuwa a dawo "Ni dai ba wani, a kwana nawa zamu bar kasar mu dawo" System din shi Hamza ya ture gefe, saboda har ranshi ta fara saka shi nishadi "In zamuje da wacce kasa zamu tafi to?" Da sauri ta amsa da "Paris" Jinjina kai yayi, sosai kasar take burgeta, akwai wata Hawwaty a Instagram, can taga sunje da mijinta, kalar hotunan da suka kashe a wajaje daban-daban sun bala'in burgeta "To yaushe ya kamata mu tafi, tunda kinga Monday zaku koma makaranta" Dan shiru Hindu tayi, ranta yayi wani irin qal "Ko gobe da safe haka" Sosai Hamza yake kokarin danne dariyar shi, amman ganin da dukkan gaskiyarta yasa shi kwashewa da wata dariyar, system din ya dauka yana mikewa, Hindu ba zata kashe shi ba "Ko Abuja zamuje ai sai haka Hindu, kinsan samun visa kuwa? Kina magana kamar zamuje Barnawa.... Kibar ni aiki zanyi" Hamza ya karasa yana dariya, kafin ya fice daga dakin, sai dai a gabaki daya maganar da tayi bataga abin dariya ba. Yana magana kamar ba zai yiwu subar kasar a gobe ba, a littafi sau nawa ta karanta, rana daya za'a yanke tafiya kasar waje, sai dai a shirya a wuce airport, yanda wasu ma suka mayar da fita kasashen ketare kamar dakinsu, akwai littafin data karanta, gayen ciki duk juma'a a Madina yake sallar juma'a, duk da wannan suna da nasu private jet din, amman ai ba abin mamaki bane ba. Kwanciya tayi tana daukar wayarta, gara ko hira su danyi da Dimples, Hamza ba zai gaji da disappointing dinta ba sam-sam. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 9 Dan baccin da ta samu bai shige awa biyu ba, sai taji kamar tana rufe idanuwanta ne aka kira asuba ta sake bude su, cikin yan dakika zuciyarta tai wani irin tsalle daya tuna mata akwai abinda ya faru da ita a daren jiya, kafin tai wata irin mikewa daga kan gado tana daukar wayarta, dan ko addu'ar tashi bacci ma batayi ba. Duk da daukar wayar da sassafe haka dabi'arta ce, Dimples kan ce 'Daga tashi da safe sai ka janyo waya, baka duba ko zaka iya magana ba, ka taka kafafuwan ka kaji ko suna nan lafiya ba, ka dauki waya. Baka ma godema Allah daya dawo maka da ranka ba, tsabagen rashin hankali. Sai ranka ka gama latsa wayar kayi ka mike ka kasa tukunna zaka dawo hayyacin ka' Kuma maganar Dimples din tayi tasiri a ranta ba kadan ba, wasu lokuttan da tazo daukar wayar ta tuna sai ta ajiye ta fara yin addu'ar tashi, wata rana har alawala ma sai tayi indai da wuta, in babune zatai amfani da fitilar wayar. Amman yau baiyi amfani ba, dan so take ta tabbatar da cewa da gaske ne tayi magana da Hamzy. Tayi magana da Hamza Abu Abbas, Instagram din ta koma tana bin gabaki daya hirar hadi dayin wani murmushin nishadi, kafin ta tashi har Asma ta rigata mikewa ta shige bandaki, zaune itama Hindun ta tashi tana tunanin dalilin da zatayi amfani dashi wajen sake yiwa Hamza magana. Mikewa tayi tanayi shiga bandaki, ganin lokaci ya kure yasa tai alwala ta fito tana gabatar da sallah, tadan yi karatun Qur'ani, ta gabatar da azkar din safe, tana kuma bin shi da addu'arta, ta yau da kullum. Wannan karin tana ji har a ranta tamkar addu'ar ta gama amsuwa. Sai da tayi wanka ta shafa mai, sannan ta sake kwanciya tana komawa wani baccin sanin cewa sai karfe goma da rabi take da lacka a safiyar. Sanda ta tashin ma goma tayi, fuskarta ta wanke, tana gyarawa ta sake kaya tayima Anty sallama ta fita, ko yunwa ma bataji, in sun fito sha biyu da rabi sunje restaurant ita da Hauwa. Tana fita harabar gidan tana cin karo da Musa daya fito daga motar shi, yana sata jan karamin tsaki, duk da taji Mama na fadama Anty an saka bikin shi, bai hana mata haushin shi da take ji ba, manyan kayane a jikin shi ruwan omo, yana rike da hular kayan a hannun shi, ga kan yasha aski sal, sai taga yayi mata kama da dan ta'adda saboda kasumbar daya tara ya kuma salle kai tas, dan dai bata jin akwai gajeru kamar shi a cikin su, saura kiris taji ya cire mata son da takema kasumba a fuskar maza, tahowa yayi bigil-bigil, gajartar da askin na haduwa su saka shi yi mata tamkar kwalbar roll on. "Hindu..." Ya kira yana mata murmushin da yasa ta kara tamke fuskarta tana furta "Sannun ka" Ta rabashi ta wuce karma ya kara samun damar da zai mata wata magana da sanyin safiyar nan, ita bama kullum take son yawan haduwa da gajerun mutane tunda sassafe ba haka, Musa kuwa kai ya girgiza, ance zuciya bata da kashi, kuma masoyi baya laifi, shikam ya yarda da haka, dan har yanzun da sa ranar shi amman yana jinta har ran shi. Soyayyar da yake mata ba karama bace, haka dai Allah ya kadarta ba zai sameta ba, ya kuma rungumi kaddarar shi da hannuwa biyu. Tunda yanzun in ba wani dalili mai karfi bama, baya zuwa gidan sam-sam. Da ta isa makaranta taji haushi sosai jin cewa Malamin ya fasa zuwa, ta kuma san ganin Musa da tayine ya shafa mata rashin sa'ar nan, Hauwa ta kira tana fada mata "Taf... Kinga saurin da nake, kice inyi zamana" Kai Hindu ta girgiza "Banza kizo dan Allah... Ni banajin komawa gida ma sam" Tana jin dariyar da Hauwa tayi "Ashe in zo, bacci zan koma wallahi, kinji kaina yanda yayi nauyi" Ita kanta Hindun da tasan ba zaizo ba kwanciyarta zatayi tai baccinta, ko ma ta kara rage assignment din da yake gabanta "Ai shikenan, bari in koma kawai. Sai munyi magana, ki gaishe da Anty" Tana sauke wayar daga kunnenta bayan Hauwa din ta amsa. Kamar yanda tace mata, gidan kuwa ta koma, sai dai batayi sauri ba, dan bata son komawa ta sake haduwa da Musa, kar ya kara shafa mata wata rashin sa'ar Hamza yaki kulata. Da ta shiga gidan ma a falo ta cire abayar dake jikinta tana ajiyewa da jakar, ta shiga kitchen. Dankali ta fere ta soya ta dauko ta fito, kayanta ta tattara tana shigewa daki dasu. Kan tabirin zanenta ta dora plate din dankalin ta linke abayar sosai ta mayar da ita inda ta fiddo da dan mayafin nata. Sannan ta dauki plate din da wayarta tana komawa kan gado. Twitter ta leqa ta samu ana cece kuce kan maganar yawan sakin aure, mata na ba maza laifin, su kuma suna kin karba. Ta sauka ta koma Instagram tana shiga shafikan kwalliya, a nutse take duddubawa sosai, dan ita bakowacce mai kwalliya bace zata taba mata fuska idan bikinta ya tashi. Dinki kan shi tana da telolin da take hari, tasan duk yanda Baba yake sonta, bashi da kudin da zai mata kalar bikin da take mafarki, amman tare da hamshaqin mijin da zata samu, abin bazai wahala ba sam. Tunda tana da yakinin zai bata wadatattun kudi da zata gudanar da hidindimunta a cikin tsanaki. Dabara ce ta fado mata a rai, tana sakata ajiye plate din dankalin a gefe tana mikewa, zanikan da tayi daren ta dauko, ta warware su tana dauka hoto daya bayan daya, guda shidda ne daman ta gama, sannan ta bude Instagram dinta. Sallama ta fara yima Hamza sannan ta tura mishi hadi da dorawa da 'Bansan ko nayi dai-dai ba' Sannan ta ajiye wayar tana nannade zanen ta mayar inda ta fito dasu kafin ta koma kan gadon tana addu'ar Allah yasa kar Hamza yaki yi mata magana, ko da kalma dayace ya fada mata zataji dadi. * Da sallama ya shiga gida, Anna na zaune ta nade kafafuwanta akan kujera, ta amsa mishi, amman ko inda yake bata kalla ba, murmushi yayi, yasan bata kaunar yanda yake kwana a wani waje ba gida ba, duk da Appa ya goya mishi baya da fadin 'Namiji ne shi, kuma ya kai munzalin da zai fita ya nema har wata kasar ma' Abin baima Anna dadi ba kwata-kwata. Tafi son yaje ya dawo gida ya kwana. Wani lokacin sai ta kira shi ta zage shi tukunna yake dawowa gida. "Ann" Hamza ya furta yana zagayawa ya zauna gefenta. Hararshi tayi, tana saka shi yin dariya "Haba mana Ann... Aikine fa ya rikeni" Ya fadi da harshen Hausa, duk da yasan Ann din ba zatayi mishi Hausa ba, kwata-kwata bata musu Hausa, asalin yaren kasarta take musu, larabci ne gurbatacce, duk da shi Hamza yanajin larabcin na kwarai, yana kuma yima kannen shi cikin kokarin ganin nasu ya gyaru kamar na shi. Kishin abinda Anna din takeyi yasa ta karfi da yaji Appa ma ya daina musu hausa yake yara musu fulatanci, sai suka taso suna jin yarikan duka biyu, ita kuma Anna a tsakaninta da Appa suna fahimtar kome zasu fadama juna da yarukan su, amman kowa bayayin na kowa. "Hmm, ka kyauta dai, in kasa kafa ka fita daga gidan nan sai an ganka". Dariyar ya sakeyi dan bayason maganar tayi nisa "Ina Auta? Bakowa gidan? Appa fa?" Kai ta jinjina mishi "Auta na makaranta, su Abid sun dawo sun kara fita" Sake gyara zaman shi Hamza yayi "Me kika dafa? Yunwa nake ji Allah" Mikewa Anna tayi batare da tace mishi komai ba, ta shiga kitchen din tana zubo mishi dambun shinkafa da yaji kayan hadi ta dawo ta kawo mishi "Shisa nake son ki Anna" Hamza ya fadi yana karbar plate din daga hannunta, hira suke kadan-kadan harya gama cin abincin. Da kanshi ya kai plate din kitchen ya fito yana wucewa dakin shi, samun shi yayi a gyare tsaf, ya kuma san aikin Auta ne, bayan ya sai musu gidan da suke ciki, yaso ya daukar musu mai aiki, saboda babu kalar wahalar da su Anna basu sha ba kafin rayuwa ta kawosu inda suke yanzun, idan dubu daya yake da ita, dari takwas daga cikinta a kansu take karewa, yana kokarin kyautata musu da dukkan wani abu daya mallaka. Ba wani dangi gare su ba, garama Appa akanta, sune komai nata, da wahala ta saka mishi doka ya tsallake. Ita kanta tana alfahari da Hamza, tun yana karami kalar kwakwalwar da yake da ita yasa takeji a jikinta dan nata zai iya zama wani, yanzun kuma gashi zatonta ya tabbata. Shisa take da buri akan Hamza, bakowacce kalar mata bace zata bari ya aura, sai yar manyan mutane da suka san mutunci, wadda ba zata shiga tsakaninta da danta ba, dan yanzun rayuwa ta canza, mutane babu Allah a ransu. Sai ka samu iyaye da yaran su, kayi kokarin rabasu dashi, ta karfi da yaji ka fara adawa da kyautatawar da yake musu, saboda rashin tsoron Allah. Shiga yayi yana karasawa kan gadon shi ya kwanta, tun jiya yake tunanin Hindu batare da wani dalili ba, kawai ta samu waje a cikin kanshi ta manne, kaf duk wani hoto da ta saka sai da ya duba, da yanayin yanda take magana da mutane daya bata mishi rai haka kawai. Dan har yau da safe sai da ya sake dubawa yaga tana hirar film da wani kato, shisa mata suke kamar hula a wajen shi, sai ya zaba ya darje, in ya dora na wani lokaci ya cire ya ajiye, yawancin duk matan daya taba mu'amala dasu, su suke kawo kan su wajen shi, da bakin shi bai taba neman mace ba, baima taba nuna ta mishi ba ko da ta mishi din. Duka halin su daya, idan ba kyawun shi suka biyo ba, to kudin da sukaga yana da shi ne, garama Hindu yaga ita maganar Architecture tayi. Shisa shima baya kasa a gwiwa wajen amfani da wannan damar da suka bashi, in dai zasu mori juna to shikenan, daya gama yayi gaba abin shi, da wahalar gaske ya koma ma mace sau biyu. Har iskanci Fodio yake mishi, cewar yana tsoron attachment. Kuma da gaskene, duk wani abu da zai takura shi baya kaunar shi. Abdallah ne ya kula ya kasa gajiya da yi musu nasiha akan mata shi da Fodio, AbdulHafiz ya dauki idanuwa ya saka musu yanzun. Basa dai hirar a gaban shi ne, tun ranar da yayi musu hauka sosai yafi sati hudu ko waya bata hadasu ba, sai suke taka tsantsan da yanda suke hirar mata, daman shi da Fodio ne kadai. Kusan Hamza zaice yanda matan suke yawan kawo mishi kansu ne ya fara jan ra'ayin shi, tun yana ND kuma wasu cikin abokan karatun shi da suke kwana studio tare suka koya mishi fara shaye-shaye. Tun yana mamakin yanda bacci baya kamasu har suka sanar dashi wiwi ce, a indomie suke dafawa, ko su zuba a shayi, in zaka kwana idanka kyam, ga yanda yake jin kwakwalwar shi har wani kaifin tunani take karawa. Sai kuma ya samu Fodio ma yana dan sha, duk da shisa ce abinda yafi bulbula ma cikin shi, Arafat ma na shan shisa. Hamza zuwa club ya fara koya mishi daga kwalba, sai kuma yaga kan shi na rike wuta, bata bugar da shi kamar yanda yake ganin tana yiwa sauran mutane. AbdulHafiz kan ce 'Kana cutar da kanka Hamza, akwai kuskuren da kakeyi a cikin sallarka, shisa bata hana maka aikata wannan abubuwan... Wallahi ka gyara kafin lokaci ya kure maka' Nasihar kanbi ta kunnen shi na dama ta wuce a ta haggu ne, abinda yasani kawai shine komai yana da lokacin shi, idan lokacin barin yayi zai bari. Kuma azumin litinin da alhamis baya wuce shi sam, in ba rashin lafiya ba, safiyar yau saboda yasan zai zo gida, bai niyyar shan wani abu ba, amman hirar Hindu da wannan 'katon banzan' kamar yanda ya fadi ta saka shi kunna wiwi, hakan kuma yasa shi yin fada da AbdulHafiz da bayason jin warin ta, shisa bayason damuwa ko kadan, haka kawai daga ganin hoton yarinya kamar jaraba ta manne mishi a kai. Shisa har wajen sha daya tukunna yayi wanka ya fito. Yanzun ma tsintar kanshi yayi da komawa Instagram, yana duba hotonta da yake na karshe da ta saka, dan yatsa yasa yana shafa kan fuskarta, na rana daya idan ya sameta ma yayi mishi, zai cireta daga kan shi kwata-kwata. Yana da wannan yakinin, sakkonni ya shiga yana ganin sunanta a sama alamar ta mishi magana "Sai yanzun zakiyi mun magana?" Ya fadi a fili kamar tana jin shi, tun da ya tashi yake dubawa, baisan me zaice mata ba, shi daya fara mata magana, kuma bai saba yima mace magana ba sam, bude sakonnin yayi yana shiga hotunan, badan abinda tayi din ba dai-dai bane a zanen, akwai dai gyara da yawa, kuma layikan basuyi mishi yanda yake so ba. Sallamarta ya amsa sannan ya ce 'Akwai gyara kam, bazan iya dogon typing ba. Zan kiraki' Sai da ya tura yai tunanin bashi da lambarta balle ya kirata din, baima san dalilin da zaisa yace mata haka din ba, kawai zuciyar shi ce ta darsa mishi son jin muryarta, ko zatayi dai-dai da kalar fuskarta. Sauka zaiyi daga Instagram din yaga alamar tana rubutu 'Da gaske? Like da gaske zaka kirani?' Kafin ya amsa yaga alamar ta sake cigaba da rubutun 'Kaifa zaka kirani, dan Allah karka ce mun wasa kake mun' Dariya yayi mai sauti, yana fara rubutu 'Ki ajiye lambarki kafin in canza ra'ayina' Bai taba ganin saurin rubutu kamar yanda ta turo lambar ba, kwafa yayi yana saving da Hindu. Sannan ya danna kira, ta daga yayi mata sallamar da ta amsa shi yana jin farin cikin da yake tattare da muryarta hadi da wani irin excitement da duk basu hana muryar sauka cikin kunnen shi da wani sauti na daban ba, bai tambayi ya take ba, ko ya makaranta, kawai abinda yake so ta gyara a jikin zanen ya fada mata, ko godiyarta bai jira ba ya kashe wayar shi, dan yana ganin kamar duk sakokin da yake kara magana da ita, da yanda take sake manne mishi a kai, da yanda zuciyar shi ke kara kwadaituwa da ita. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 21 Lokaci zuwa lokaci take dan juyawa tana kallon Hamza da yake tukin shi hankali a kwance, ko sau daya bai juyo ya kalleta ba tunda aka tashi daga dinner din da ta kawatu daga wajen shirin kujerun, ko hotunan da aka dinga yi musu sai dai yadan yi murmushi, wani ya rike hannunta, wani ya tsaya a bayanta. Da aka kira su filin ma, hannunta ya rike sukayi tsaye. Tasan daga shi har abokan shi suna da kudi, amman yau sun nuna mata kudin nan da suke dashi basa jin komai wajen liqasu. A cikinsu mutum dayane taga yana liqa dari bibbiyu ma. Amman daga dubu sai dari biyar, sosai sukayi ta ruwan kudi, duk da taron awa biyu akayi, daga takwas zuwa goma na dare. Kalma ko guda daya bata hadata da Hamza ba, zuciyarta take jin tanayi mata rawa, ta dauka babu wani abu da zai shiga tsakaninta da farin cikinta a rana irin ta yau, ga dinner ta samu irin wadda take mafarki, dan tana da tabbacin zata tsinci hotunan su da Hamza a shafuka daban-daban na Instagram. Amman zuciyarta a jagule take, duk da tabbacin daya bata na cewa babu abinda tayi mishi, kowaye yai mishi wani abu yau bai kyauta mata ba sam, kuma bai mata adalci ba. Duk da fiye da rabin hankalinta akan Hamza yake, tana kula da hanyar da suke komawa bata nan suka biyo ba wajen zuwa. Kanta ta jingina da kujerar motar tana sauke wani irin numfashi mai nauyin gaske. Idanuwanta na kafe kan titi, amman hankalinta yana can wata duniya da take bakuwa a wajenta, jin Hamza yayi parking yasa ta dago kai tana kallon shi, kafin ta kalli inda yayi parking din, Barcode Lounge, sai take ganin kamar a Barnawa suke, amman batajin ko hanya ta taba biyowa da ita ta wajen. Da matukar mamakin dalilin tsayawar su ta juya ta kalli Hamza da yake tattare babbar rigar jikin shi, kafin ya dan daga yana zarota daga jikin shi ya cireta gabaki daya, duqunquneta yayi yana jefawa bayan motar. Kafin ya fara dube-dube jikin gaban motar yana bude wani waje ya zaro ATM. Ficewa yayi daga motar, baice mata komai ba. Ya kusan mintina sha biyar, dan tanayi tana duba wayarta data karba bayan sun fito daga wajen dinner din, tana jin Dimples nayiwa su Fodio mita "Me kuke nufi wai? Yanzun kudin siyan bakin ne ba kwaso ku fitar shine kuke so a rabu tun nan?" Ta kuma ji AbdulHafiz na fadin "Dan kudin siyan baki, ku fadi ko nawane ni in biya. Amman ku taimaka mun, dare nayi..." Da alama sauri yakeyi tunda da matar shi yazo, yanda take nunawa kuwa a takure take, duk da idanuwanta kawai ake iya gani saboda face mask din daya rufe fiye da rabin fuskarta. Tayi wani irin kyau cikin alkyabbar ta silver. Dan juyawa baya tayi jin Hamza ya bude murfin motar wajen yana saka wani abu da duhun cikin motar bai bari taga ko menene ba, amman kamar lemuka da alama, tunda harda kiret taji alamar kacafniyar kwalabe. Juyawa ta sakeyi tana gyara zamanta, harya gama saka abubuwan da zai saka ya zagayo ya shigo, yana tayar da motar suka bar wajen. Waje biyu suka kara tsaya, tukunna suka karasa gida, sai lokacin Hindu ta samu ta karema gidan kallo daga waje, yayi mata kyau har saida murmushi ya kwace mata duk da damuwar da take ciki. Da kanta ta bude murfin motar tana fitowa, ganin Hamza nata sauko da kaya, yasata mika hannun dan takarbi ledojin da ya tattaro "Kibar shi zan shigo da shi" Yayi maganar da wani irin yanayi a muryar shi "Kayan da yawa, ka kawo in tayaka" Mika mata ledojin yayi, saboda bayason doguwar magana, bayama son yin magana gabaki daya, ji yake kamar zai kurma ihu ko zai samu saukin takurar da yakeji rayuwar shi tayi. Idan har zai samu ya daure zuciyar shi ya kwana a gidan nan yau batare daya fito ya koma gidan Fodio ba, to yana bukatar ya sha wani abu. Yasan bashi da komai a cikin gidan, shisa ya biya ta Barcode ya siyo kalaluwan giyar daya kan sha. A hankali ya dinga dauka yana shiga dasu gidan, baiga inda Hindu tayi ba, shi dai sama ya haura yana kai kayan part din da nashi ne, dan har furnitures da komai ya zuba. Har kayan sawar shi ya dibo wasu ya kawo nan gidan. Fridge din bangaren ya shirya komai yana cika shi taf, tunda harda coke ya siyo. Saida ya gama sannan ya balle links din rigar shi yana cire shaddar, daga shi sai singlet a jikin shi yaji kamar ana murda hannun kofar dakin da yake ciki, runtsa idanuwan shi yayi yana bude su a hankali hadi da juyawa, Hindu yagani data bude kofar tana tsayawa a bakin kofar, rigar da suka dawo da itace a jikinta, amman ta cire mayafin, sai dankwali. Bayason yanda take kallon shi idanuwanta cike da maikon hawaye. Ita kuma tunda ta shigo, saita wuce dakin da aka fara ajiyeta nan kasa, ledojin ma duk a dakin ta ajiye, wayarta da jakarta ta jefa su akan gado, ta kwance mayafin daga wajen da yake maqale a kafadunta tana ajiye shi, ta zame takalman kafafunta, ta karasa ta zauna gefen gadon, wani irin shiru daya gauraye gidan ya saukar mata da kadaici na ban mamaki, ga kuma bakunta da zullumin sabuwar rayuwa duk suka hadar mata. Haka kawai taji idanuwanta sun cika da hawaye, suna zubo mata, musamman da taga Hamza yaki shigowa, sosai hawaye ke zubar mata, wani na ture wani, ba haka ta hango daren farkon ta ba sam. Wani irin tsoro taji ya tsirga mata da batasan daga inda ya taso ba yana sakata mikewa babu shiri, waje ta fara lekawa ko takalma bata saka ba, sai dai ta hango motar Hamza inda ya ajiyeta, ko ina a rufe kuma, babu kowa, ko maigadi bata iya hangowa daga inda take, sai tarin shuke-shuken da suke a tsare. Dawowa tayi tana fara bin dakunan gidan na nan kasa gabaki daya tana neman Hamza, har kitchen sai da ta shiga. Tana dubawa, hawaye na sake zubo mata, dan batasan koya fita yabarta ita kadai a wannan tanqamemen gidan ba. Da kuwa bai kyauta mata ba "Kar kaimun haka, dan Allah Hamza" Ta tsinci kanta da furtawa, wasu hawayen na sake zubo mata, tuntuni ta yanke shawarar kiran shi da sunan shi, saboda duk wani suna da tayi tunani, taga tarin yan mata sun kira shi dashi, bataso kuma ta zama kamar su, ko sunan shi a wayarta sai daga baya ta sake zuwa 'Hilwatee'. Shima din shiya taba kiranta da hakan, ta tambaye shi ma'anar yace mata 'My sweet' da yaren Annar shi. Da yake saitama jima ko sunan nashi bata kira ba. Ganin duk ta duba dakunan kasan baya nan, ta yanke hukuncin hawa sama, shima daki biyu ta bude tana leqawa, kafin ta shiga wani dan lungu daya sadata da falon da bai kai na kasan girma ba, a hankali take kawa harta sake yin wani dan lungun tana ganin kofa, murzawa tayi ta tura a hankali. Ta kuwa sauke idanuwanta kan Hamza da yake tsaye daga shi sai singlet da gajeran wando, saurin sadda kanta kasa tayi, tana kai hannu ta share kwallar da ta taru a gefen idanuwanta, kafin ta sake dagowa ta kalle shi, tana kokarin tsayar da idanuwanta a iya fuskar shi, muryarta na rawa tace "Ban ganka ba, inata duba ka" Idanuwan shi Hamza yadan murza, yanayin da karara yake nuna mata yanda shigowarta dakin ta takura shi, tana jin wani abu ya bude a cikin kirjinta da ba zatace ko menene ba, amman ciwon shi yasa idanuwanta sake cikowa da hawaye "Wanka zanyi Hindu, dan Allah a gajiye nake, kije ki watsa ruwa kema. Zan zo idan na fito" Wannan karin batayi kokarin tsayar da hawayen nata ba, barin su tayi suka zubo yagani, yana jin kan shi ya kara nauyi da kukan da tayi tsaye tana mishi kamar yai mata wani abu, ko kwana basuyi ba karkashin inuwa daya, amman a wuyan shi yake jinta ta tokare, ko iskar kirki baya iya shaka sam. "Na tambayeka ko nayi maka wani abu, tun dazun, duk yau kanata bani attitude, idan ma bayau ba, ko wani lokaci a baya nayi maka wani abin daka rike a ranka ka zabi kabari sai yau ka horani, ka dubi girman Allah ka fadamun sai in baka hakuri....amman... Am..." Hindu ta kasa karasa maganar saboda kukan daya kwace mata, bata baro gidansu tazo nashi dan ya dinga yi mata wannan abin ko kwana batayi ba, amare nawa ne ta karanta, ta kuma ji labarin yanda angwayen ke lallabasu a dare irin nayau, suna lallashin su yayin da suke kukan rabuwa da gida, amman yanzun ita gata a tsaye nata hawayen na zuba akan wani dalili daban, amman ko motsi Hamza baiyi ba, ballantana ya nuna alamar zai karaso inda take ya lallasheta. Kallonta kawai yakeyi, inda zai iya shima kukan zaiyi saboda abinda yake ji, kawai so ta tafi ya dan jishi shi kadai na wani lokaci. Amman taqi tafiya, neman dalili takeyi bayan ya gaya mata babu, maganar da bayason yi take so ta saka shi dole-dole saboda rashin son zaman lafiya "Karya kike so inyi miki? Nace miki bake bace ba, dan girman Allah ki kyaleni inji da abinda yake damuna mana, haba dan Allah" Hamza yake fadi yanajin idan ya karasa inda take, turata waje zaiyi ya rufe kofar, bayason haka ta faru, bayason yin abinda su duka bazai musu dadi ba, tunda har ranshi yake jin babu abinda tayi mishi, abinda yakeji bashi da alaka da ita, yanzun ne take so ta hada mishi abinda yakeji da ciwon kanta, su zame mishi biyu "Me yasa dan Allah Hindu na zaki kyaleni in shaki iska ni kadai ba?" Hannu takai tana share hawayenta da kamar taba wasu hanyar zubowa ne, ta bude bakinta tana shakar iska, dan wadda take zarya ta hancinta da wani irin zafi take jin shigarta, ga kirjinta abinda ya bude dazun takeji yana kara budewa, batasan wanne laifi ta aikata mai girma haka da ta cancanci wannan abin ya faru da ita a darenta na farko ba. "Wow..." Ta furta tana sake kai hannu ta goge fuskarta. Kafin ta juya, ko kofar bata rufe mishi ba, tana da tabbacin tsoron da takeji bazai mata komai ba, amman yanayin Hamza da maganganun da yake fada mata na barazana da numfashinta, kafar benen bibbiyu take hadawa wajen sauka, da gudu ta koma dakin da ta fito, tana doko kofar, jikinta ko ina bari yakeyi, dankwalin kanta ta fisge tana jefa shi kasa, kafin ta fara kiciniya tana samu ta zuge zif din rigarta, ta zameta tana tsallaketa a wajen, bandaki ta shiga, da sauran kayan da suke jikinta ta bude ma kanta shawa din da ko a film bata taba ganin irin ta ba, ruwan yadan fara zubo mata, tana fita babu shiri jin ruwan zafi ne sosai, anan bandakin ta tsugunna, tana kokawa da numfashinta. Kuka takeyi kamar ranta zai fita, kafin ta samu dakyar ta mike, dubawa tayi sosai tana samu ta dai-daita zafin ruwan ta watsa. Ta cire sauran kayan tabarsu anan bandakin, tana dauro towel ta fito. Tanajin yanda fuskarta ta kumbura har idanuwanta, dakin sake kayan data gani dazun ta shiga, ta kuwa samu kayanta a shirye a cikin wardrobes din, na cikin ta fara sakawa, ta tsaya tunani kafin ta sami wata rigar bacci mai yanayi da kimono ta saka a jikinta tana daure madaurin akan cikinta, duddubawa tayi ta samu wata farar hula, sai da ta saka towel din ta goge kanta, tana jin dadin shawarar Aina'u data dauka, tayi kitso. Sannan ta saka hular, saboda yasa tadan turata baya, dakin ta fito ta karasa kan gadon ta kwanta daga can karshe. Kanta kamar zai bude saboda ciwon da yakeyi, ga cikinta ya daure waje daya saboda rashin abinci. Tunda ba wani abin kirki bane a ciki, banda ajiyar zuciya babu abinda take saukewa, zuciyarta kanta tayi wata irin natsuwa a cikin kirjinta, su dukansu biyun a gajiye suke da rayuwa gabaki dayanta. * Kwalbar hannun shi ya daga yana sake kafawa a bakin shi, sai da yaji baya iya numfashin kirki tukunna ya sauke kwalbar, a zaune yake dirshen kasa kan kafet, tunda Hindu ta fita daga dakin, yafi mintina goma a tsaye. Yasan wanka ya kamata yayi, amman kanshi ya cunkushe, gabaki daya lissafin shi ya kwance. Ya kasa tsayar da tunanin shi waje daya sam, shisa ya dauko abu daya dayake da tabbacin zai batar mishi da komai, kwalbar ya ajiye yana dafa gado ya mike, ji yayi lum, kan shi yayi wani irin juyawa, wasu taurari na giftawa ta cikin idanuwan shi. Dakyar ya samu ya dai-daita tsayuwar shi, kafin ya fara takawa yana dan tangadi ya fita daga dakin. Baisan ya bugu ba saida ya fara gwada taka benen yaga yana rabe mishi biyu, kama karfen gefe yayi, amman ya gwada faduwa Allah na tsayar dashi yafi sau biyar, kafin ya samu ya karasa sauke, komai bibbiyu yake ganin shi, saiya runtsa idanuwan shi ya sake budewa yake dan ganin dai-dai. Dakin da Hindu take ya karasa yana tura kofar, ya hangota a kwance, bata koyi motsi ba, ballantana ta dago, dakyar ya karasa cikin dakin sosai, ya kuwa yi tuntube da ledojin da suke ajiye da sam bai kula dasu ba, kafin jiri ya dibe shi yana katantanwa cikin dakin, karar faduwar shi Hindu taji saboda hankalinta sam baya tare da ita. A firgice da wani irin matsanancin tsoro ta mike gabaki daya, tana sauke idanuwanta kan Hamza cikin tashin hankali, tana kallon yanda yake kokarin tashi, dakyar ya mike zaune, tsaye yake so ya tashi amman saiya kara zamewa ya koma ya zauna, da wani irin tashin hankali da bata taba sanin akwai shiba a duniya take kallon Hamza, kafin ta sauke daga kan gadon tana jinta kamar a gajimare take yawo, itama jirin taji yana neman kwasarta, saita tsugunna tana rarrafawa ta karasa inda Hamza yake, kafin tayi wani abu harya riko hannunta "Bakiyi mun komai ba, ina so in zauna ni kadai ne.... Hindu ki taimaka mun, ya zanyi in kwance sarkar da ta daure ni? Ya zanyi? Bana so, ban shiryaa ba, wallahi ban shiryaa ba, ki taimaka mun" Idanuwanta cike suke taf da hawaye, hannunta dayake rike dashi ta dago tare da nashi, tana dumtsawa a cikin nata, ganin a buge yake, kamar baima san me yake ce mata ba "Hamza....me ka sha? Me kake sha? Kar kayimun haka, dan Allah ka rufamun asiri, ka rufamun asiri" Take fadi, wani irin gunjun kuka na kwance mata, tana saka shi zame hannunshi daga cikin nata, ya kama fuskarta yana fadin "Shhhhh.... Ban sha da yawa ba, ban sha da yawa ba, ban sha da yawa ba" Yake fadi yana kara maimaitawa, amman ta kasa yin shirun, batasan yanda zata fara yin shiru ba a wannan halin, so takeyi idan yau mafarkine ta farka, dan zuciyarta zata tarwatse, tasan yana neman mata, wannan abune da take da yakinin zata iya canza shi a kai, saboda tana da abinda zata bashi, amman wannan, wannan abin da take gani batasan yanda zata fara ba, yarda da abinda yake gabanta ma na mata barazana, balle tasan yanda zatayi da shi, ga wani irin wari da batasan meye ba daya cika mata hanci yana kara dagula mata lissafi. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ta furta tana dora hannayenta kan na Hamza da yake fuskarta, wani sabon kukan na kwace mata, kafin taga ya lumshe idanuwan shi, yana yi mata wani irin nauyin dayake neman rinjayar su biyun, yana sakata sakin hannuwan shi babu shiri, faduwa taga yayi ya kwanta, yana kara mata tashin hankalin da take ciki "Hamza..." Ta fadi, tana girgiza shi "Hamzaa" Ta sake fadi, tsoro da firgici bayyane a muryarta, sosai take girgiza shi, amman ko motsi baiyi ba, kuka take har sautin shi baya fita saboda tashin hankali. Hannunta ta dora kan kirjin shi tana jin bugun zuciyar shi daya nutsar da abinda yake mata tunanin ko mutuwa yayi, kafin ta dora kanta a jikin shi tana kuka kamar ranta zai fita. Tabbas labarin tashin hankali take ji, yaune tasan yanda yake. Ko kadan ba wannan bane abinda ta shirya, a mugun mafarki bata hangoma kanta irin haka ba, yanzun lokacine daya kamata ace suna more soyayyar su, ba wannan tashin hankalin ba "Babe ji nake kamar in janyo satika biyun nan da suka rage. Bacci ni kadai yana mun wani iri yanzun, saboda ina tunanin yanda zan fara yin shi tare dake" Maganganun shi suka fado mata "Da zasu mun adalci, sai suce inzo in dauke ki, bama sai sun rakomun ke ba Hindu, in zo in dauki matata mu taho gidan mu" Wani irin numfashi takeyi, ko shima zai taimaka ya farkar da ita, taga wannan abin da yake faruwa mafarkine "Na kagu lokaci yayi da zan farka daga bacci in ganki a kusa dani, kece mace ta farko da take gwada hakurina haka" Dago da kanta tayi, kan daya sara mata yasa ta mayar da shi a jikin Hamza, zuwa yanzun hawayenta ma sun daina zuba, banda wani yaji-yaji da idanuwanta sukeyi mata, kokarin kirjinta take gani, batasan yana da kwari haka ba, sai da taga har yanzun bai tsage dan abinda yake cikin shi ya fado ba. Ciwo dai yake mata na ban mamaki. Batasan ya lokaci yake tafiya ba tunda na ganin shi takeyi ba, duk da yanzun bata tunanin akwai wani mamaki da rayuwa zata bata, sai da baccin wahala ya dauketa mai nauyin gaske. Ko motsin Hamza ba zatace taji ba, kawai farkawa tayi cikin wani irin yanayi, kanta kamar dutse saboda nauyin da yayi mata, kafin komai ya dawo mata, zuciyarta na wata irin dokawa, hanyar bandaki tagani a bude, ta kuwa mike tana shiga, Hamza ta samu yana kwara amai kamar zai fitar da hanjin cikin shi. Shima farkawar yayi, inda sabo ya kamata ace yanzun ya saba, duk da basai wani ya fada mishi ba, yasan yasha takai mishi karo, Hindu ma da take jikin shi hankadeta yayi, da rarrafe ya fara yana samu ya mike da gudu yana shiga bandakin, da kofar a rufe take zai fara amai a waje, hakan ma ba bakon abu bane a wajen shi. Saida ya tabbatar ya gama aman tukunna ya dago kan shi, yana tarba hannun shi a jikin fanfo ya kuskure bakin shi, kan shi kamar zai rabe biyu saboda ciwon da yakeyi. Hindu na tsaye a bandakin ta zuba mishi idanuwa cikin rashin sanin abinda ya kamata kayi, singlet din shi ya kama ya cire, ya jefar a kasa, kafin ya mike, ganin ya dora hannun shi a kugun shi, yasata fita da sauri daga bandakin tana janyo mishi kofar. Sai dai tayi tsaye a bakin kofar, tana jin ya sakarma kan shi ruwa, alamar wanka yakeyi. Daga shi sai gajeran wando ya fito yana dafe da kan shi, tana kallon shi ya fice daga dakin, nan ta zame tana zama, hawaye take nema amman sunki fito mata. Kafin ta ga an turo kofar, Hamzan ne ya dawo, ya saka gajeran wando da riga mai dogon hannu, karasawa yayi inda take ya tsugunna, baisan me yakeji ba, baisan me zaice mata ba, ya tabbata tagan shi a halin da Fodio ne kawai ya taba ganin shi tunda yake a rayuwar shi. Bai kuma san yanda zai dauki hakan ba, abu daya yasani, bata cancanci wannan abin dayake faruwa da ita ba, kawai baisan yanda zai gyara hakan bane ba, ga kanshi da yake ciwo, hannunta ya kama, yana mikewa ya mikar da ita, janta yayi har tsakiyar dakin, yana kamata suka sake zama, kafin ya janyota ta matso sosai, yana hadata da kirjin shi ya riketa sosai. Sai lokacin kukanta da take nema ya fito, baice mata komai ba, riketa yayi sosai, har saida yaji tayi luf a kirjin shi, alamar ta gama kukan, sannan ya mike da ita, yana jan hannunta suka shiga bandakin, ruwa ya dinga tarba da hannun shi yana zuba mata a nata ta wanke fuskarta da bakinta, sannan suka fito daga bandakin. Zaman suka sakeyi, ya mika hannu ya janyo ledojin da suke ajiye, ya siyo kaji, burger da shawarma, yana da tabbacin bata taba ko daya ba, budewa yayi duka "Kici wani abu" Kai take girgiza mishi, batajin zata iya cin wani abu, har yanzun sama-sama take jinta "Kar kisani doguwar magana Hindu, kaina ciwo yake mun. Kici..." Ya fadi muryar shi babu alamar wasa, batasan me yayi tasiri a kanta ba, burger daya ta dauka tana faraci kamar magani, dakyar taci rabi tana ajiyewa, baice mata komai ba, duk ya tattara yana fita dasu, fridge din kitchen ya bude ya saka. Ya dauko mata ruwa daya gani yana dawowa ya bude ya mika mata, sha tayi tana bashi, ya karba yasha shima sannan ya rufe robar ya ajiye a gefe, kamata yayi ya dago, suka nufi kan gadon su dukan su, saida yaga ta kwanta, ya kama mayafin da yake kai ya lullubeta. Sannan ya mika hannu ya kashe mata kwan dakin yana takawa ya fice, tana jin rufe kofar shi, ta lumshe idanuwanta, zuciyarta na wani irin ciwo. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 25 Shi kan shi wanda yake koya mata tuqin yayi mamakin yanda ta iya cikin yan kwanaki, saboda bata zaton ta taba mayar da hankalinta akan wani abu irin haka. Ko Hamza yaji dadin yanda ta iya tuqin, da yake kudi ne suke aiki, harya gama hada mata duk wani abu da take bukata, an bata lasisin tuqinta. "Banda kudin sai miki sabuwar mota yanzun Hindu, mu fita kiga cikin nawa ki dauki daya, banda Corolla din" Ita kam ranta kal, bakar ta dauka kirar BMW 330i, saboda tun ranar daya fara zuwa da motar wajenta ta bala'in tafiya da ita, gata kal-kal babu inda wani abu ya sameta, shima Hamzan ita yayi niyyar bata, dan tafi sauran motocin shi haske, kuma bata koyi shekara da siye ba, bama sosai yake hawanta ba. Ya dai bari ta zabane da kanta. Ko baccin kirki bata samu ba ranar daya bata motar, ya kuma tabbatar mata da mallakinta ce, duk yanda take sonyi da ita zata iya. Ranar farko da ta koma makaranta da motarta ta koma, taji dadin yanda tayi parking ta fito, duk ga wasu cikin yan ajinsu suna ta kallonta, an ga ta zama Hajiya. Danma Hamza bai fara mata zancen zuwa Hajji ba har yanzun, zata san yanda tayi ta sako maganar cikin hirar su, ta keta hazo itama, ta dawo manne da hakorin makkanta, inda duk zata shiga ana kiran Hajiya Hindu. Tunanin kawai na sakata nishadi na daban. Sai dai ba nan gizo ke sakar ba, cikin watanta na biyu a gidan Hamza, taje makaranta da safe, ana tsakiya da daukar darasi wani dan ajinsu da yazo a makare ya ratsa ta gefenta yana wucewa, kamshin turaren shi na cika mata kofofin hanci. Lokaci daya taji komai ya hargitse mata har jiri-jiri take ji. Cikin tashin hankali, ko excuse bata iya dauka wajen Malamin ba, ta mike tana fita da saurin gaske, dakyar takai bakin kwalbatin da take gaban ajin, kafin ta tsugunna tana fara kelaya amai kamar zata fitar da hanjin cikinta. Hawwa ce ta fito tana taimaka mata, har ruwa ita ta siyo mata, ta kuskure bakinta, ta wanke fuskarta tana kuma samu ta sha, bata mike daga wajen ba sai da wani irin zazzabi mai zafin gaske daya lullubeta. Dole ta tarkata jakarta tana nufar gida "Anya Hindu zaki iya tuqi kuwa? Dakin bari na sauke ki, sai in hau Napep in dawo" Hauwa tace cike da damuwa a muryarta. Ita dince dai taqi, aikam a jigace ta shiga gida, a bandakin baki na cikin falon taci birki saboda wani sabon amai daya sake taso mata, amman kakari kawai takeyi a wahalce tunda duk wani abu da yake cikinta ta gama fito da shi, anan kan kafet ta kwanta, tana rashin lafiya. Ba zata iya kirga yawan lokutta da ta kwanta asibiti ba, amman zata rantse bata taba ciwo irin wannan daya kamata farat daya haka ba. Jinta take kamar ba'a duniyar take ba, kamar ta shiga wata irin duniya da bata taba tunanin akwai irinta a rashin lafiya ba. Ko numfashin kirki bata iyawa, ga amai da takeji yana taso mata har lokacin. Ta kai mintina talatin anan kwance, idanuwanta a lumshe, amman sam ba bacci takeyi ba, ganin kamar mutuwa zatayi idan bata samu taimako ba, ya dan bata karfin gwiwar mikewa, taja jiki tana janyo jakarta data cillo tsakiyar dakin tun shigowarta, wayarta ta dauko daga ciki, tana samu dakyar ta kira lambar Hamza, da bugun farko ya daga da fadin "Har kun fito ko bai zo ba yau din ma?" Muryarta can kasa tace "Ya zo..." Kafin ta samu furta wani abin, daga dayan bangaren Hamza ya rigata "Hindu? Lafiya? Me ya faru? Ya naji muryarki haka?" Dan gyara kwanciyar tayi "Bani da lafiya, na dawo gida ne ma" Tana jin yai magana cikin yaren da bata fahimta ba kafin yace "Ina zuwa kinji, yanzun zan zo" Bai jira amsarta ba ya kashe wayar. Mai musu aiki sau daya take zuwa, da tayi share-share sai dan wanke-wanke da bama kullum suke da shi ba, sai in Hindun tayi girki, sauran tarkacen da sukaci, Hamza kance in tazo a fito mata dashi ko ansa a fridge ta tafi dashi, kuma Hindu ta dinga bata kudin mota, ko dubu dayane. Yanayin kyautar shi na mata dadi, ko yau da zata fita dubu goma ya bata, a cewar shi ko zata bukaci siyan wani abu a makaranta, ko takardu ba saita kira shi ba, kuma akwai kudi a account dinta. Baba ma satin daya fita taga ya tura mata dubu goma, tasan kuma na makaranta. Shisa Baba yake daban a duniyar ta. Sanin tana karkashin kulawar Hamza yanxun bai hana shi sauke nauyin da yake tunanin har yanzun yana kan shi na hidimar makarantarta ba. Bata san iya lokacin da ta dauka ba, dan bacci ya fara daukarta taki muryar Hamza daya dago ta yana tana fuskarta, wuyanta da duk wani waje da hannun shi zai iya sauka a jikinta da zaiji yanayin zazzabin daya rufeta. "Wanne irin zazzabi ne wannan?" Ya fadi cikin tashin hankali, shi sam bayason yaga wani bashi da lafiya. Hankalin shi yakan tashi, musamman yanda yaga duk ta langabe mishi, zuciyar shi banda dokawa cike da tsoro babu abinda takeyi "Hindu... Hindu" Yake kira yana mikar da ita zaune, shi ya mike tsaye ya kamata, tana tashi dakyar saboda wani irin jiri da taji yana shirin dibarta, ga amai daya taho mata, da sauri ta kwace hannunta daga rikon da yayi mata tana rugawa bandakin, amman babu abinda ya fito sai wahala, Hamza yayi tsaye a kanta yana mata sannu, shiya taimaka mata ta mike, suna fitowa ya zaunar da ita, da kan shi ya zame mata abayar da take jikinta, ya shiga dakinta ya dauko mata hijab, yana kamawa ya saka mata. "Ta shi muje asibiti" Yanda take jinta motsin kirki ma dakyar takeyin shi "Dan Allah kabari in kara hutawa" Ta fadi kamar zata fashe miki da kuka, kan shi yake girgiza mata "Kalli yanda kike fa, kina cemun in tsaya ki huta. Ki tashi wallahi mu tafi asibiti..." Hamza ya karasa yana kamo hannuwanta duka biyun ya mikar da ita tsaye, amman gani yake kamar zata bata mishi lokaci, sakin hannuwan nata yayi yana dan rankwafawa ya sungumeta ya sabata a kafadar shi kamar bai dauki komai ba, bata da lafiya amman bai hanata jin wani abu ya motsa a zuciyarta ba. Da tasan rashin lafiya ce zata sa Hamza ya dauketa haka, da ko ta karyace tayi tuntuni, luf tayi a kafadar shi har suka karasa bakin motar shi daya samu ya ajiyeta, yana amfani da hannun shi daya ya riketa gam, kamar yana tsoron inya saketa zata iya faduwa, gaban motar ya bude mata, sai daya taimaka mata ta shiga, ya rufe, tukunna ya zagaya ya shiga. 44 Nigerian Reference Hospital da akafi sani da 44 NARHK ya nufa kan shi tsaye, Anna da duka yan gidan nasu nan suke zuwa yanzun in dai basu da lafiya. Ya yarda da aikin su da kuma yanayin kulawar su, duk da tsadar da mutane suke kira asibitin na da shi. Amman yana da halin, kuma wani kyale-kyale ma yake kashe kudin shi a kai, ballantana neman lafiya. Suna shiga kuwa ana zuwa aka taimaka ma Hindun, sannan ya fara maganar bude mata nata katin, sosai aka shiga bata taimakon gaggawa, dan yanda suka ga ta galabaita har sun bata daki ma, an daura mata ruwa ko zata samu karfi a jikinta, ruwan da takeji kamar yana sake takalo mata ciwon da take jine. Hamza ya zauna tare da ita, da yake an dibi su jini ayi gwaji, har fitsari suka sa tayi a wata yar roba, bayan jerin tambayoyin da sukayi ta mata. Dan lokacin da results din suka fito bacci takeyi, Hamza ne zaune yana danna wayar shi. Har ofishin likitan ya bishi, inda aka tabbatar mishi da Hindu na da shigar cikine. Tashin farko ba zai ce ga asalin yanda yaji saukar maganar ba, dan daga ofishin yana fitowa, Hindu ya fara leqawa, yaga baccin takeyi. Tukunna ya fita yana shiga motar shi, masallacin farko daya samu ya tsaya ya gabatar da sallar azahar da yaji ana kira, sannan ya sami wani karamin restaurant, ya zauna. Dankali da kwai sai kaza yace a kawo mishi, su hado mishi da coke. Abincin yakeci ba dan yana gane kan shi ba, bama yunwa yakeji ba, jikin shine ya bashi cewar lokacin da zaici abinci yayi. Wani irin sama-sama yake jin shi, kan shi kamar an dora dutse saboda nauyin da yayi mishi. Aure gare shi, matar shi ce dauke da cikin shi. Yau shine mace take dauke da cikin shi, baisan me ya kamata yaji ba, amman tsoro na daya daga cikin abinda yakeji, tsoron da bai tabaji ba tunda yake a rayuwar shi. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya furta yana ajiye cokalin cikin plate din shi, fuskar shi ya dafe da hannuwan shi biyu yana sauke numfashi, kafin ya budeta yanajin yanda zuciyar shi take bugawa har cikin kunnuwan shi. Ko da yake hango kan shi da mata, ba zaice ya hango shi da yaro ba, bai hango wannan dawainiyar ba dan baisan ta inda zai fara ba "Kana zaman ka lafiya ka janyowa kan ka wannan bala'in Hamza, kana zaman ka" Shine abinda zuciyar shi take furtawa tana kara maimaita mishi. Mikewa yayi yana ajiye dubu biyu akan tebirin duk da abinda yaci dubu dayane da dari biyu. Sannan ya fice, motar shi ya shiga yana komawa asibitin, amman inda yayi parking nan yayi zaune cikin motar, yana kasa fitowa, ko ina jikin shi kyarma yakeyi saboda tashin hankali. Wayar shi ya zaro daga aljihun shaddar da yake sanye da ita, yana lalubo wayar Fodio ya kira, AbdulHafiz zai janyo mishi wasu ayoyi na yanda cikin jikin Hindu kyauta ce da Allah yake zabar bayinsa wanda zai ba, da sauran wa'azikan da basu yake bukata ba a halin yanzun. Wanda zai fahimci tsoro da firgicin shi yake so "Hey..." Fodio ya fadi ta dayan bangaren "Ciki take da Fodio. Bansan me zanyi ba wallahi, I'm fucking terrified" Hamza ya karasa muryar shi na rawa "Shit.... Da gaske?" Fodio ya tambaya, Hamza najin tsoron da yake muryar shi shima "Abinda nake fadi kenan, kaima ka tsorata ballantana ni, muna asibiti tun dazun. Ina cikin mota a zaune. Fodio ban shirya ba, wallahi ban shirya ba" Wani irin zagi Fodio yayi mishi da yasa shi fadin "Fodio" Cike da mamaki "Ka jini ai, dan ubanka me kake nufi da baka shirya ba? Kana da hankali kuwa Hamza? Ita ka dai kabari a cikin asibitin bayan an fada muku? Ita kadai kabari ka fito?" Kai Hamza yake girgiza mishi "Bacci takeyi sanda na fito" Ya furta a raunane, yanajin Fodio ya sauke numfashi "Kasan me yasa ban taba tunanin aure ba? Saboda ba zan dauko yarinyar mutane ban shirya daukar nauyin ta ba. Ka jini Hamza, sai da na fada maka karkayi, nace maka wahala ce a cikin shi, na fada maka aure bana kowa bane ba shisa ba'a tilasta shi bama" Runtsa idanuwan shi Hamza yayi yana sake bude su "Inda baka shirya haihuwa ba, kafi kowa sanin yanda zaka kauce ma samun cikinta, bakayi ba. Me yasa kake mun magana kamar baka taba hango cewar zata dauke shi ba? You step the fuck up kayi abinda ya kamata..." Maganganun Fodio din yake ji har kasan zuciyarshi, yasan ya fahimci tsoron shi, amman ya manta asalin waye Fodio, ya manta in akazo maganar daukar nauyi ta fannin aure da kula da iyali, suna da ra'ayin da yasha banban da Fodio. Tsoron su ba kala daya bane ba "Karka bani kunya Hamza" Fodio ya karasa yana kashe wayar, numfashi Hamza yake fitarwa yanajin kamar iskar cikin motar bata kai mishi inda ya kamata. Hakan yasa shi fitowa babu shiri yana jingina a jikin motar "Ko da wata rana zan taba aure bazan haihu ba, yara ne karshen abinda zan kawo a duniyar nan. Ba zan mutu in barsu su wahala kamar yanda aka mutu aka barni ba, kudin duk da zan tara musu in babu kulawa aikin banza ce..." Maganganun Fodio suka dawo mishi "Me yasa zaka auri yarinya kasan baka shirya kula da ita ba? Ina fada muku aure bana kowa bane kuna dariya kamar wasa ne magana ta" Fodio din ya fada wata rana da Abdallah ke basu labarin wani mutum a unguwar su da yayi aure bashi da tsayayyar sana'a, karshe sai sakin matar yayi saboda ya kasa riketa. Sosai halayen su da yawa suka banbanta da na Fodio. Ko ranar farko daya fara ganin shi da kwalbar giya tsayawa yayi yana kallon shi "Menene? Ka daina kallona kamar baka shan wani abu kaima" Kai Fodio ya girgiza mishi "Idan yau zan samu bacci batare da taimakon komai ba zan daina sha. Kai kasan me ya fara sakani shan wani abu tun daga farko, kana da zabi Hamza, kana zagaye da mutanen da zasuyi komai saboda kai, in ba zaka iya dainawa saboda kan ka ba, ka duba Anna, ka duba me zataji in ta sani ka daina" Shiru yayi wa Fodio din a wancen lokacin "Ni ba AbdulHafiz bane ba Hamza, ba zan iya jure tunasar da kai kullum ba, na fada maka abinda ban samu wanda ya fada mun ba lokacin da nake da damar bari. Zabin duk da kayi bayan wannan naka ne" Kuma daga ranar bai sake mishi magana akan shan wani abu ba, ko kiran shi yayi ya biya ya sai mishi zaiyi. In kanata tare da Fodio, shawarar duk da zai baka ka bude kunnuwanka ka saurara, saboda ba zai sake maimaita maka ba, ko da kanka ka bukata ba zai maimaita ba. Kallon ka kawai zaiyi yaci gaba da abinda yake. Ajiyar zuciya mai nauyin gaske ya sauke yana takawa ya shiga cikin asibitin, yana nufar dakin da Hindu take, a zaune ya sameta, ruwan da aka saka mata harya kare, tana murza hannunta. Yau kawai duk tayi wani irin zuru-zuru. "Kanki babu dankwali" Ya fadi wani irin kishi na tsirga mishi, wani katon banza ya shigo ya ganar mishi mata da kai a bude. Shisa bai bari ta cire hijabinta ba tunda ba dogo bane har kasa "Yanzun na cire hijab din zanyi fitsari" Ta amsa shi da dan murmushi a fuskarta, kai ya jinjina mata yana shiga dakin sosai, ya kama hannun da take murzawa ya dago shi, yana shafa inda yayi alamun fasawar allura, harya dan kumbura "Sannu..." Ya furta yana kamata ta mike, har kofar bandakin ta shiga, fitsari tayi ta kara wanko fuskarta tana fitowa. "Wai zasu sallameni ne fa, ance kana ina" Kai Hamza ya jinjina yana fadin "Ina zuwa" Tunda yasan yanda duk tsarin asibitin yake, yakai mintina sha biyar kafin ya dawo yana, da yar leda a dayan hannun shi, ya kama nata hannun yana fadin "Muje..." Kallon shi takeyi, ko takalma babu a kafafuwanta, saboda sungumarta yayi da zasu fito "...You step the fuck up kayi abinda ya kamata" Muryar Fodio ta dawo mishi, dan murza goshin shi yayi yana sauke numfashi a hankali, kafin ya zare takalman da suke kafafuwan shi yana tsugunnawa ya tura su saitin nata kafafuwan, kallon shi takeyi, zuciyarta na wata irin dokawa. Kafin ta daga kafafuwanta ta saka takalman, ya kama hannunta yana janta, bin shi take tana kallon yanda yake taka cikin asibitin suna nufar hanyar fita, babu takalma a kafafuwan shi. Kallon shi takeyi kamar har abada ba zai taba bata mata rai ba, kamar ko satin daya wuce basuyi tashin hankali da shi akan Mansy ba. Wani lokacin yana mata kamar yana da iska in ya juye haka. * Duk fadan da Hamza yayi da tace ya sai mata soyayyar doya ta bakin titi da taga wata mata nata soyawa, yayi parking din ya fita ya siya. Haka kawai taji doyar tayi mata, yawunta har tsinkewa yakeyi, tun a motar ta faraci, har suka karasa gida tana samu waje ta zauna. Kamar jira aman daya taso mata yakeyi ta karasa cinye doyar, gabaki daya saida ta dawo. Shi kan shi Hamzan hankalin shi yayi bala'in tashi, da kan shi ya taimaka mata ta watsa ruwa, ya dauko mata kayan da zata saka, sai rawar sanyi takeyi duk da ruwan mai zafine tayi wanka da shi, rigarta ya kama yana taimaka mata dan ta saka "Me yake damuna haka? Naji sauqi fa kafin mu fito daga asibitin, me sukace ya sameni?" Take tambayar shi "Ba abinda ya sameki, ciki kike da Hindu" Maganar shi ta sauke cikin kunnuwan shi da wani irin yanayi "Ciki?" Ta tambaya da murmushi a fuskarta, kai ya daga mata yana juyata, ya zage mata zif din rigar. Hannunta takai saman cikinta, tana lumshe idanuwanta, hadi da jero kalmomin godiya ga Allah da wannan kyautar da yayi mata, kyautar da tasan mata da yawa na raba dare suna addu'ar samu. Kwanciya tayi, ya ja bargo ya rufa mata, idanuwanta kawai ta lumshe. Bashi yake rashin lafiyar ba, amman a gajiye yake jin shi sosai, maganin da kala biyune kawai ya ajiye gefe yana fita. Robar ruwa ya dauko mata, yazo ya ballo magungunan yana tsugunnawa "Ta shi ki sha" Batayi musu ba ta mike, ta karbi maganin ta sha tukunna ta koma ta kwanta. Shi nan ya zauna kan kafet din yana jin wata irin gajiya na saukar mishi. Wayar shi ya dauko da yaga bacci ya dauketa yana kiran Auta, bugun farko ta daga "Yayaa" Ta fadi "Auta kina ina?" Ya tambaya "Yanzun na fito daga makaranta, ina kan komawa gida. Ya naji muryarka can kasa?" Numfashi Hamza ya sauke "Hindu batajin dadi, ko zaki zo ki zauna da ita. I promise ba wani aiki zakiyi ba. Kawai kar a barta ita kadai, akwai abinda zanyi a wajen aiki" Ya karasa, dan yaga Arafat nata kiran shi, tunda AbdulHafiz kadai yasan ya fito, shima bai fada mishi dalili ba, bai kuma tambaya ba "Okay, bari in siya abu sai in taho" Kai Hamza ya jinjina "Nagode" Ya fadi yana sauke wayar daga kunnen shi. Zama yayi har saida yaga Auta na kiran wayar shi, yasan ta karaso ne kuma, ba zata shigo ba. Ta tsaya a falo tana kiran shi, mikewa yayi ya leqa kai, yaganta a zaune kuwa tana warware mayafin da yake nade da kanta "Nagaji wallahi" Kai kawai Hamza ya girgiza, lalacinta bashi da na biyu, yana da tabbacin babu abinda tayi duk yau banda shiryawa ta fita makaranta "Bacci takeyi, in ta tashi da wani abin ki kirani" Kai ta jinjina mishi "Ka fadama Anna ina nan, kaine kace in zo. Kaji" Wannan karin shiya jinjina mata kai yana ficewa. Yasan tana so tazo gidan nashi, amman Anna tace me zata zo tayi, har karar Anna ta kawo mishi, ta hada su biyun ta zage. Da gasken babu abinda zatayi, kawai tana so tazo ne, itama tace taje gidan Yayanta, kamar yanda sauran kawayenta suke fadi. Anan falon tayi zamanta tana kunna tv, ta tsayar da channel din a MBC 2 da suka saka film din Step Sisters, ta kalla yafi a kirga, kawai bata gajiya da film dinne. Ice cream din data biya ta siya ta fara sha hankalinta a kwance tana kallon, dan sosai ta kwaso tarkacen ciye-ciyen da Anna kance suna tafiya a banza tunda ko yar kiba basa sakata. * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 24 Wani irin shiru take jin gidan tun fitar Hamza, bata gane akwai wutar lantarki ko babu, kasancewar solar da yake gidan, kullum a cikin wuta suke. Bata taba tunanin zata gaji da kallo ba sai yanzun da take da wadattacen lokacin yin shi. Tun karfe goma ta gama bacci, har sharar rashin dalili ta takalarwa kanta, duk da Hamza yayi maganar cewa za'a kawo mai aiki, a cewar shi Anna tayi mishi maganar, yace kuma ta samo musu. Riga da wando ne a jikinta, sai ta daura farin dankwali, zakayi tunanin fita zatayi saboda kwalliyar da take fuskarta. Tun satinta na farko wani ya kwankwasa kofa, ta saka hijab ta leqa, yace mata "Oga yace kibani kayan wanki" Matashine wanda da wahalar gaske ya girmeta, nata dakin ta shiga ta kwaso mishi kayan wankin da ta tara, ta shiga dakin Hamza ma, da kayan suke a cikin wani kwando duk ta hada, washegari suna tare dashi ma aka kawo kayan a wanke tsaf, sun sha guga, har cikin wasu ledoji aka saka su, ta jima tana mamaki, tunda an kawo mata injin wanki, da alama ba wani amfani zaiyi mata ba, haka ma ran asabar din shekaranjiya data cika sati biyu cif akazo aka amsa, sai ta saka a ranta cewa duk sati za'a dinga zuwa karbar wankin nasu kenan. Hamza ya tashi da azumi safiyar litinin din, ya fada mata shi baya suhoor, da yaci abinci da dare ya sha ruwa shikenan. "Daman kana azumin litinin ne?" Ta bukata daya fada mata zaiyi azumi, kafadu yadan daga mata, yana amsawa da "Wasu lokuttan..." Da gaske yakan yi azumi duk sanda Allah ya bashi ikon yin hakan, yanzun dai zaiyi azumin ne dan ya daga ma Hindu kafa ta dan huta, a idanuwanta yake ganin yanda ta gaji da shi, in ba hakan yayi ba gashi can tare da wata tun kafin suyi nisa. Tun daren auren shi rabon shi da wani kafar sada zumunta, ko yanar gizo zai hau da laptop din shi yake amfani, bayason cin karo da duk wani abu da zai tunzura zuciyar shi, yana son yin iya kokarin shi na danne abinda yakeji, Hindun ita kadai ta ishe shi rayuwa, shine abinda yake fadama kan shi, amman yanajin abu mai wahalar gaske ne, sosai zuciyar shi take karyata shi. Yayi ma jikin shi wani irin sabo da canjin yanayi. Ko abinci kala daya bai cika gamsar dashi ba, ya fiso ko da guda biyu ne ya hada a lokaci daya, balle kuma mace da yake dauka yana ajiyewa a duk lokacin da yaso, rana daya ace hakan ya sauya, abune mai wahalar karbuwa a wajen shi, amman zaiyi dukkan kokarin shi, ko dan AbdulHafiz da harya daina bude sakonnin shi yanzun, tun bayan auren shi, kullum saiya turo mishi da tunasarwa kan illar shaye-shaye da neman mata, kamar bai sansu ba, kamar yace mishi ya manta da tarin laifin hakan. Yana saka shi jin dauda a jikin shi fiye da wacce yake ji batare da tunatarwar shi ba. Dan AbdulHafiz ne, shi kadai ne yake mishi wannan shiga hanci da qudundunen. Zama tayi a falon sama, Hamza yace ta dawo nan taqi, tunda dai duka ko ina gidanta ne, kuma inda duk taso kwana zata kwana, da ace ma zai dinga daukarta yana sauko da itane, hakan zai mata dadi, amman taga Hamza bashi da wannan tunanin sam-sam, har Korean film tasa suka kalla da hakan ya faru ko zai sanar dashi wani abu, sai ma ca yayi "Dan Allah jibi yanda suke daga matan su, da yake su ba wani kayan nauyi suke ci ba, amman a Najeriya ba yanda zaka juya matarka yanda kake so, nauyin tumbinta kawai yafi na irin yarinyar nan hudu" Tashi tayi ma ta shiga bandaki, badan zatayi wani abu ba, sai dan takaicin daya rufeta, ita din ba siririya bace ba, amman kuma bata da wannan jikin da yake magana, tana kuma da tabbacin ba wani nauyi zatayi ba. Kuma Hamzan ai yana motsa jiki, duk girman shi yanzun take kula da mugun lalaci yayi mishi yawa, shisa har yake tunanin ba zai iya daukar kamarta ba. A yanda yake ganin shi, ta dauka ko yini yayi yana yawo da ita a cikin gidansun nan sam bazai nishi ba. Shisa ta lallaba zuciyarta, tunda Hamza sam ba zai gaji da basu kunya ba. Tun jiya tace mishi yayo musu cefane tayi girki, har da dankali ya siyo musu, shima ta soya tayi musu sauce da dare. "Soya dankali da wahala haka daman? Kinga da kin bari mun siyo abinmu" Hamza yace, da yake kitchen din ya sameta yayi tsaye, har saida ya gaji sannan ya koma falo ya zauna, ita kuma haka kawai taji tana so ta dafa wani abu taci, ta gaji da abincin waje. Kuma gara ma da tasa yayo cefanen, yanzun sai ta yi mishi kayan buda baki, tun da tazo ta zauna take tunanin abinda ya kamata tayi mishi, tunda ita da safen nan shayi ta hada tasha da cincin dinta na gara da sai yau dinma ta bude shi. Hamza ya kamata ace abokan shi sunzo, ta diddibar musu, amman zatayi mishi magana, su Dimples ma sunqi leqota har yanzun, a cewar su saita gama amarcinta. 'Yan gidansu kuwa batama saka ran ganin su yanzun ba, suna dai waya kusan kullum. Kuma sukan yi chatting, amman tasan ba barinsu zuwa za'ayi yanzun ba. Sai ta kara kwana biyu. Tasan yau aka koma makaranta, ko za'a fara wani abu sai wata litinin din, Hamza ya sani shisa batayi mishi maganar tana son zuwa ba, ca zaiyi zata wahalar da kanta. Kawai abu dayane yake mata dadi har ranta, da safe kafin ya fita yace zai nemo makarantar koyon tuqi, a koya mata. Yana so ta koma makaranta da motar ta, duk idan ta juya sai wani nishadi na daban ya lullubeta, ita din, Hindu Al'amin zatayi mota, sosai ya faranta mata rai, shisa itama zatayi kokarin ganin ta faranta mishi rai a yau din nan. * Wanka ta sakeyi tana dauro alwalar sallar Magriba, sunyi waya da Hamza sau daya, shima kawai yaji ya ta wuni ne, sai text da yayi mata bayan la'asar "Nikam nagaji, yunwa nakeji" Murmushi tayi kawai, dan lokacin harta gama farfesun kaji, tayi miya, ta fere dankali ta zuba mishi ruwa. "Sannu da aiki, Allah ya dawomun da kai lafiya" Bai bata amsa ba, kitchen ta wuce taci gaba da aiki abinta, bata kammala komai ba sai gab da magriba. Yanzun ma kwalliya tayi mai sauqi, ta saka riga da skirt na atamfa, ta zauna gefen gado tana jiran a kira sallah, tayi saita daura dankwalin ta, wayarta ta dauka, taga Hamza ya kira wajen biyar saura, tana kitchen, sai kuma text daya turo "Karfa ki wahalar da kanki, ba sai kin dafa mun wani abu ba" Murmushi tayi, tanajin dadi data ajiye qwiya a gefe ta shirya mishi kayan buda baki, tasan zaiji dadi. Ta kula in zasu fita kullum suci abinci a waje ba zai damu ba, idan ya bata kunya ta wani bangaren, sai yayi wani abu kuma da zai zo dai-dai da mafarkinta. Ana kiran sallah tana mikewa dan ta gabatar da sallar ta. Da Hamza manne a ranta lokacin da ta idar, sai takejin kamar motsi a falon kasa, yanke azkar dinta tayi tana mikewa ta daura dankwalinta ta fita, aikam Hamza ne zaune kan kujera, hannun shi ya mika mata, tasa nata a ciki, ya kama ya zagayo da ita tana zama gefen shi, sumbatar gefen fuskarta yayi "Nayi kewar ki" Ya furta da wani yanayi a muryar shi da yasa ta fadin "Buda baki fa zakayi" Murmushi yayi, sai lokacin ta kula da kwandon da yake ajiye a kan kafet. Da mamaki take kallon kwandon, kafin ta kalli Hamza "Yunwa nake ji" Ya furta, yana fita daga nan da safe gidan Fodio ya wuce, duk acan ya sami su AbdulHafiz. Arafat ne kawai yaje musu Abuja, Fodio nacin indomie, ko Hamza bai tambaya ba yasan AbdulHafiz ma yana azumi, tunda shi kusan duk litinin da alhamis din duniya yana azumi. Sai dai ko in rashin lafiya, kusan ranar duk aiki sukayi, har sai da suka dawo masallaci sallar azahar, yana shigowa Mansy na kiran shi, ya daga ya kara a kunne, maganar farko da ta fara yasa shi yatsina fuska "Mansy azumi nakeyi ni, bana son iskancin banza" Dariya tayi ta dayan bangaren "Kai da kake da amaryar da ko sati uku batayi ba, me ya kaika yin azumi?" Numfashi ya sauke "Ya kike?" Ya bukata cikin son canza maganar, yana da tabbacin in tayi tsayi, Mansy zata saka shi fadin abinda bai kamata ba yana azumi, amsa shi tayi suna dan yin hira "Yau banajin zuwa aiki, ban fita ba, ko in maka kayan buda baki?" Kai yake girgizawa tun kafin ta gama magana "Ba zan stressing dinki ba, zamu fita da Madam" Ko ma basu fita ba, inya kira Anna yasan za'a kawo musu abinci idan na gida yake jin ci, ko daga gidan AbdulHafiz duk yana da wannan alfarmar, Abdallah ma zai iya sakawa a dafa mishi. Duk da yau din ba shi bane ranar farko da Mansy take mishi girki, sosai yana son kalar abincinta, da yawan ranaku idan yayi azumi tana hada mishi kayan buda baki, ko tazo ta kawo mishi, ko yaje ya karba, duk da baya bari ta shigo har cikin gidan saboda AbdulHafiz, tunda akan abincin ma yana mishi fada "Kai baka tsoron a zuba maka wani abu? Gara ka siyi abinci a hotel ko restaurant akan ka dinga karba daga wasu mutanen" Murmushi kawai Hamzan yayi "Mansy ce AbdulHafiz, ba zata zuba mun komai ba" Ba tun yanzun yasanta ba, inda zata zuba mishi wani abu, tuntuni da tayi, duk iskancin ta bai kai nan bangaren ba, ita ce mace ta farko daya fara nema fiye da sau daya, kuma ta farko da zai kira da kawar shi bayan su Fodio, bafullatana ce, a yanda take fada mishi marainiya ce, ta taso hannun kawunta da tsantsar rayuwar boko ake gudanarwa, babu wanda ya damu da abinda duk takeyi, tana gama makaranta daga service, wajen da take aiki a Kaduna suka riketa, ta kuma kama haya take zaman kanta, yan wanda suka damu a dangi sun mata magana tayi biris dasu, saboda ita ba zata yanke yancin da ta samu saboda surutun mutanen da bayan rasuwar iyayenta babu wanda ya damu da ita ba, su biyu suka haifa daman, yayanta ya rasu tunda karancin shekaru. "Babu wani stress, dan zan maka girkin shine zai zama wani abu, daman zan dafa nima. In zaka wuce gida saika biyo ka karba" Kyaleta yayi tayi din, suka karasa magana kafin suyi sallama kan cewa zai biya ya karba din. Lokacin da taji labarin auren shi, ta daga hankalinta ba kadan ba, abinda ko a takalmin Hamza, ya jima da sanin Mansy na son shi, yana jinta har ranshi, amman ba irin wannan soyayyar ba, kuma tayi mishi tsufa, ko ba haka ba, bazai iya auren mace irin Mansy ba, kishin shi ba zai taba bari ba, ko zai bari Anna zata mutu kafin ta yarda da auren. Shisa kai tsaye yace "Karki mun rigimar rashin dalili Mansy, ke kinsan ba zan taba auren ki ba, ba tun yanzun ba, kuma kinsan dole rana irin ta yau zata zo. Babu macen da zata daga mun hankali banda Anna a rayuwar nan, zabinki ne muci gaba da abokantaka ko kuma akasin haka" Kwana biyu basa magana, kafin daga baya kuma ta dawo kamar da, dan shi tsaf zai yakice ta gefe. Kamar yanda ya fadane, har ranshi mace ba zata daga mishi hankali ba, Hindu ma da ta nemi barazana da zaman lafiyar shi, aurenta yayi, gashi nan yanzun komai ya lafa mishi. Shisa ya kira Hindu yace mata karta wahalar da kanta, tunda za'ayi musu abinci. Sai bata daga ba, amman yabar mata text, yasan kuma tagani. Suna gama aikin su da ya dauke su har yamma liqis gidan Mansy ya wuce, ko shigar da motar shi baiyi ba, anan kofar gida ya jirata ta miqo mishi ya wuce. A hanya ya tsaya yai sallar magriba, kafin yanzun ya karaso gida "Ka biya wajen Anna ne?" Hindu ta bukata, tana kallon Hamza daya zame jikin shi ya sauko daga kan kujera, yana janyo kwandon, kafin ya girgiza mata kai "Gidan AbdulHafiz?" Ta sake tambaya, saboda tana son jin inda yaje ya shigo da kwando haka, a iya sanin ta dai restaurant ba zasu hado shi da kwando ba, kuma ta shirya mishi kayan buda baki, kulolin ya fara fito dasu, sai wasu robobi masu murfi, yana fara bubbudewa, pepper chicken ne, soyayyar doya da kwai, plantain, sai wata irin jalof din taliya da taketa baza kamshin daya cika wajen, ita kanta sai ta raina dan abinda take tunanin ta hada mishi. "Nima fa na hada maka kayan buda baki" Ta fadi da wani yanayi a muryarta da yasa shi kallon ta "Na miki text fa, nace kar kiyi" Dan rausayar da kai tayi gefe "Ina ka samo duk wannan? Na tambaya ko gidan AbdulHafiz kayi mun shiru" Cikin idanuwa Hamza ya kalleta yana sauke numfashi "Ba daga can bane, kibarni ni kam, yunwa nakeji" Tasan ya kamata tabarshi din, amman wani abu na azalzalar zuciyarta "Ina ka samo abinci?" Cokullan da suke nade ya warware yana daukar mai yatsu yasa a cikin taliyar yayi Bismillah yana fara ci, ba amsa bane bayason bata, ko ba zai iya bata ba, a gajiye yake jin shi, wani abu kuma na gaya mishi in ya fada mata daga inda abincin ya fito maganar ba zata kare dan yanzun ba. Kwalin Exotic ya dauko ya bude yana kurba, yanajin idanuwan Hindu a kan shi tana kallon shi "Me kika dafa?" Ya bukata, duk da bayason yin magana ko kadan idan yana cin abinci "Koma me na dafa baka shigo da wani ba?" Hindu ta amsa shi ranta a bace, ita bawai girki ya dameta bane tun farko, shisa abin yake kara bata mata rai "Ina ka samo abinci? Siyowa kayi?" Cokalin hannun shi ya ajiye cikin kular taliyar yana kallonta shima nashi ran ya soma baci "Ban baki amsa bane saboda inajin ba lallai kiso amsar ba, ba siyowa nayi ba Hindu, Mansy ta dafamun, daga gidanta na samo abinci" Ya karashe maganar yana daukar cokalin shi yaci gaba dacin taliyar a nutse, kallon shi takeyi wani irin abu na tasowa ya tattaru yayi mata tsaya a kirjinta. Mansy, abinci daga gidan Mansy, daga gidan wata tsohuwar banza shisa har yake mata text kar tayi abinci saboda Mansy zata dafa mishi "Wow.... Like wow, saboda Mansy zata dafa maka shisa kace ni kar inyi kenan ko?" Banza yayi ya kyaleta kamar ba dashi takeyi ba, yana cigaba da cin abincin shi, dan harya fara dibar plantain din yana hadawa da doyar "Akan me zata dafa maka abinci? Saboda kana tunanin ni ba zan iya dafawa ba ko me?" Hindu take fadi tanajin kamar ta rufe shi da duka, ga hawaye sun fara cika mata idanuwa "Me yasa zaka dauko abincin wata banza ka shigomun da shi cikin gida?" Abincin shi yake ci har lokacin ko dagowa baiyi ba, saboda ita bata isa ta hana shi cin abincin shi ba tunda yunwa yakeji, bata kuma yi shiru ba, surutai ta cigaba dayi, sai da yaji ya koshi, sannan ya rufe kulolin yana mayar dasu mazaunin su, ya mike ya dauki kwandon da nufin kaiwa Kitchen, itama Hindu ta mike "Ba zaka mayar dani kamar bansan abinda nakeyi ba H..." Yanda yai wata irin juyowa yana hade space din dake tsakanin su yasa maganar koma mata, cikin idanuwa yake kallonta "Idan kina so mu zauna lafiya a cikin gidan nan zaki koyi yanda zaki dinga mun magana. Zakuma ki koyi girmama ra'ayoyina. Dan na miki shiru baya nufin ina gudun rigima dake ne ko wani abu Hindu..." Numfashi yaja "Zan shigo da duk abinda nayi niyya cikin gidan nan saboda gidana ne, zanci kuma abinda nayi niyyar ci, ke baki isa ki hanani ba wallahi, tun kafin in aureki nake cin abincin Mansy, dan na aureki me yasa hakan zai canza? Idan kinga zaki iya ci in nazo dashi kici, idan ba zaki iya ba ko ki fita ki siya, ko ki dafa bai dameni ba, amman ba zaki takurani ba, kina jina? Wallahi baki isa ki takurani ba" Ya karasa maganar yana juyawa ya nufi kitchen din, hannu tasa tana share wasu hawaye masu zafi da suka zubo mata, yana fitowa daga kitchen din ta gefenta ya raba ya wuce, tana jinshi ya haura sama, ranta in yayi dubu a bace yake, ashar din da batasan ta iya ba, shi ta dibo tana aikawa Mansy data ja mata wannan bacin ran, kuma sai ta nemota ta zagi ubanta, in bata kyale mata miji ba, tabbas zasu kwashi 'yan kallo. Ta kai mintina biyar a wajen tana tsiyayar da hawayen bakin ciki, kafin ta shige daki, fuskarta ta wanke, tukunna ta fito tana nufar dining din data shiryama Hamza, yanda baiki cin abinci ba, itama ba zata fasa ba. Tana cikin ci, ya fito ya sake kaya daga manya zuwa kanana, sai baza kamshi yakeyi, ko inda take bai kalla ba, hannu da taga ya kawo cikin plate din dankali da kwan ta, yasata janyewa "Ba akwai ragowar na Mansy ba?" Ta fadi tana watsa mishi harara, murmushi yayi, duk yanda take tunanin ta iya rigima bata kai shi ba, da wurin nan ya kamata tasan ita din bata isa tasa shi ko ta hana shi ba, ya tabbatar ma da kan shi auren nan ba zai takura shi ba, shisa ya daina jin kamar an daure shi da sarkoki, ba kuma zata dawo mishi da yanayin nan ba. Zagayawa yayi, ta sake janyewa, hannuwanta ya kama duka biyun ya rikesu da nashi guda daya, yasa karfi ya karbi plate din yana ajiye shi "Wallahi ka kyalemun abincina, Hamza bana so, kaje kaci na Mansy, karka taba mun" Sakinta yayi yana daukar cokali ya caki dankalin yasaka a bakin shi "Ke kin isa ki hanani yin abinda nayi niyya?" Ya furta yana wucewa yabarta a wajen, tunda ba yunwa yakeji ba, fita yayi ta kuma san masallaci zai tafi, hannu takai ta share hawayen da taji ya zubo mata, itama mikewar tayi, ta shiga daki tayi alwala, ta gabatar da sallar isha'i, karatun Qur'ani ta farayi, ta mike tayi nafila raka'a biyu, tana cikin yi taji Hamza ya shigo, ya zauna gefen gado, tana idarwa ta daga hannayenta biyu, kawai sai taji wasu sababbin hawayen sun sake zubo mata "Tafdi jan..." Hamza ya fadi yana karasa maganar cikin yaren da yasa bata fahimci me ya karasa fadi ba, kafin taji ya kama damtsen hannunta yana kokarin mikar da ita "Tashi wallahi, kuka kike? Kin kalli gabas kin daga hannu kina sharara hawaye zaki hadani da Allah?" Cike da mamaki take kallon Hamza da yasa karfi ya mikar da ita, kiciniyar cire mata hijabi ya fara ta kama hannuwanshi tana tutturewa amma a banza tunda ya fita karfi saida ya cire mata hijabi, kafin tayi wani motsi ya hade bakin su waje daya. Zuciyar shi sai bugawa takeyi, sosai hankalin shi ya tashi, inya barta tayi addu'ar nan da wuri Allah zai iya amsawa, duk da yanajin baiyi mata komai ba, amman dai bayason wani dan Adam daban ya nemi hada shi da Allah. Hindu ikon Allah take kallo kirikiri, mamaki ya hanata yin wani kwakkwaran motsi. 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 26 Duniyar tayi mishi tsaye waje daya, kallo daya zakai mishi kasan baya cikin kwanciyar hankali, damuwar da take tare da zuciyar shi shimfide take kan fuskar shi "Me yake damun ka?" AbdulHafiz ya tambaye shi, kai kawai ya iya girgiza mishi yana fadin "Babu komai" Ya kuma ji dadin yanda bai matsa mishi da tambaya ba, saboda bashi da wata amsa tsayayya da zai iya baiwa AbdulHafiz din. A watanni biyun nan cikin Hindu ba karamin wahala yake bata ba, bata kwana biyu ba'a kara mata ruwa ba. Gara cikin satin nan yaga ta fara warware wa, watannin nan sune masu tsayi a rayuwar shi tunda ya mallaki hankalin shi da yayi su batare da mace ba. Shisa a satin nan har cikin idanuwan Hindu yake ganin yanda ko kusa da ita ya zauna a tsorace take da shi. Wuni yake bulbulawa cikin shi giyar da yakejin tana dakushe mishi abinda yake ji. Abu daya Hindu ta kula da shi yanzun, in har yana gida, yana manne da wayar shi, ita kanta ba dadin take ji ba, sati daya kenan da take samu taci abinci ya zauna, duk tayi wata irin rama. Duk abin Anty sai da suka zo suka duba ta, Baba kuwa zuwan shi hudu, duk idan ya dawo aiki yakan biyo ya dubata, duk da sau daya ta samu ya shigo cikin gidan harya zauna ya sha ruwa. Sauran a tsaitsaye suke gaisawa, ya bata tarin siyayyar kayan ciye-ciyen da take lodawa a fridge, wanda zasu lalace ta baiwa mai aikinta, tunda ita ba iyaci takeyi ba. Yau ta rasa abinda zatayi, da Dimples tace zata shigo ta saka mata films, saboda zataje gidan su Biebee da bikinta sauran satika uku, suna kan hidimar da ake ta faman yi babu Hindun saboda laulayin da take fama da shi, ta kuma kira cewar ba zata sami shigowa ba, dan wajen aiki basu barta tashi da wuri kamar yanda tayi tsammani ba. Tata wayar ta dauka, yanzun ta zama yar kallo a twitter saboda bakin kishi irin na Hamza, da tayi tweet ma idan yahau yaga maza sun yi magana baya ce mata komai, sai dai ta nemi tweet din ta rasa, ya goge. Tasan duk inda yake yana gab da dawowa yanzun tunda har anyi sallar magriba. A nan inda ta idar da tata sallar take zaune tana danna wayar. Fita tayi daga nata account din tana shiga na Hamza da taga tarin Notification, ga kuma sakonni da yawa ta DM. Shiga tayi duk yanda zuciyarta take fada mata karta yi hakan, karta jama kanta abinda zai daga mata hankali, amman kuma wani bangare na zuciyar yana fada mata ta duba, tasan Mansy na nan tana bi mata miji, tana kuwa shiga, sakon farko nata ne "Shegiya mai tallar taba" Ta furta a fili, wani tuquqin bakin ciki na danne ta, shiga tayi tana ja ta koma daga farkon hirar da tayi mishi magana, tana duba lokaci, jiyane ma, karfe biyu na dare, saboda ita batasan darajar 'ya mace ba. Karfe biyu zata fara yi mata magana da miji, amsar Hamzan tagani, farko hira ce sukeyi mai tsafta, kafin Mansy din ta fara mishi wata magana da ta canza gabaki daya akalar hirar tasu, jikin Hindu babu inda baya bari saboda munin abinda ta kasa daina karantawa "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ta furta ganin yanda Mansy take cewa Hamzan ya duba whatsapp din shi ta tura mishi hotunan da video din da ko ita da yake mijinta batajin zata taba iya tura mishi su, ko dan tsoron kar wayar tashi ta fadi, ko a sace da irin wannan abubuwan a ciki da ya kamata ace idanuwan shine kawai zasu gani. Kife wayar tayi, ko ina jikinta bari yake saboda tashin hankali. Ga hawayen da suke cike da idanuwanta sunma ki zubowa saboda zafin da zuciyarta takeyi, daukar wayar tayi tana fara rubutu "Dan uban babanki duk hotunan da kika tura mishi suna wayata, da screenshot din wannan hirar gabaki daya. Idan bakiyi blocking din shi, kin daina mishi magana ba sainayi posting hirar nan da duka hotunan har da videos din a TL kowa yaga karuwancin da kike bin mazan mutane kina yi. Wawiya, jaka, ballagaza da batasan inda yake mata ciwo ba, tsohuwar banza kawai" Sai taji zuciyarta tayi mata dan sanyi, da ace zata ga Mansy din ido da ido ta kamata ta jibga kamar ganga sai tafi hucewa, sau biyu tana sake sallar isha'i saboda ta farkon bata da tabbacin ga abinda ta karanta a ciki saboda tashin hankali, tana sallar tana kukan wannan jarabtar da take ciki, batasan ranar da Hamza zai bar zuciyarta ta samu hutun kirki ba. Ta dauka yanzun cikin jikinta yasa shi ya nutsu, duk tunanin da takeyi ya daina shan koma meye taga yasha a daren ta na farko a gidan, saboda bata kara ganin shi cikin maye irin wannan ba. Addu'ar da ta duqufa tana mishi ta karbu ta wannan fannin. Duk da ta fara dora laifin wannan abin da taga sunyi da Mansy a kanta, watakila da ace bata nuna mishi gazawarta a satin nan bayan hakurin da yayi da ita na watanni biyu ba da bai komawa Mansy ba, da abinda ya faru bai faru ba. Tana sallame sallama sallah yana bankado dakin kamar zai karya kofar hadi da fadin "Hindu!" Yana hanyar dawowa, kan shi yayi bala'in nauyi saboda abinda yasha mai karfine, kuma babu wani abincin kirki a cikin shi, so yake yana shigowa gida ya watsa ruwa ya kwanta tunda yayi isha'i. Ya kusa gidan ma yaga kiran Mansy, harya yanke bai daga ba, sake kira tayi bai daga ba. Ganin tayi mishi kira na ukku yasa shi dagawa, dan ya tabbata akwai dalili me karfi da yasa take kiran shi, kukan da yaji tanayi ne yasa shi sauka daga titi yana yin parking gefe, yanda kan shi yayi nauyi ba zai samu nutsuwar yin tuqi da amsa wayar a lokaci daya ba "Ki natsu kimun magana Mansy, bana gane me kike fadi, me ya faru? Me akai miki?" Ya karasa tambayar da fulatanci, itama da shi take mishi magana "Matar ka, matar ka taga hirar mu jiya, ka duba whatsapp kaga me tace mun. Hamzy ka rufamun asiri ka bata hakuri karta doramun hotuna a tl, in dai kaine na hakura wallahi..." Cike da rashin fahimtar abinda take fadi yace "Bangane ba..." Amman kuka takeyi sosai, abinda bai taba gani ko jin tayi ba tunda yasan ta da shi "Kai kasan a duniya kai kadai kake da wannan hotunan, ko na taba kasadar turawa duk iskancina saboda na yarda da kai. Wallahi ba zan yafe maka ba idan suka bazu, kayi mata magana" Mansy ta karasa cike da kashedi tana kashe wayar, hakan yasa shi duba whatsapp din shi ko zai fahimci abinda take fadin, screenshot ne na sakon da Hindu ta tura mata "What the fuck!" Ya furta a harzuqe yana sauka daga whatsapp din ya kira lambar Mansy "Bata da hotunanki ko daya, chats dinne kawai da ta gani. Ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru" Yana jin ajiyar zuciyar da take saukewa "Dan Allah Hamza..." Kai yake girgizawa "Na fada miki karki damu, babu abinda zai faru, akwai dalilin da yasa kika yarda dani tun daga farko, ki sake yarda da nace miki babu abinda zai faru" Ya fadi, kafin tace wani abu ya kashe wayar, Allah ne kawai ya karasa kawo shi gidan lafiya saboda yanda yake fisgar motar. Bai aiki Hindu duba mishi chats ba, baiga dalilin da zaisa tayi abinda tayi ba, saboda bata da wata alaqa da Mansy, da shi take da, shikuma shine yake da alaqa da Mansy, shi ya kamata ta zaga ba ita ba. Idan mutuncin shi yake bukatar ya zube zaiyi da kan shi ba saita yi mishi ba "Me kike tunanin kinyi?" Ya tambaya yana kallonta, itama kallon nashi takeyi cike da tsantsar mamaki "Me kake tunanin nayi?" Ware idanuwan shi yayi yana wani murmushin takaici mai sauti "Ki amsa mun tambayata, akan me zaki tura mata wannan sakon? Me tai miki da zaki zageta?" Mikewa Hindu tayi tana son saka idanuwanta cikin na Hamza, tana son ganin da gaske ne maganganun da yake fada mata "Idan da kunya a idanuwan ka zaka tsareni da wannan tambayar dan na zagi karuwar ka?" Ta furta, kalmar karuwar shin na fitowa daga wani lungu na zuciyarta da yake mata ciwo na gaske "Kin taba ganin alamar kunya a idanuwa na?" Ya tambaya yana hade space din da ya rage a tsakanin su yana tsareta da idanuwan nashi "Karuwa ta ce, shisa nake tambayar dalilin da zaisa ki zageta tunda baki da alaka da ita, ni ya kamata ki zaga ba ita ba inda kina da hankali" Wata irin dariya taji ta kubce mata mai hade da wani sautin kuka, duk abinda yake faruwa, duk fadan da sukayi akan sauran yan matan shi, musamman Mansy da ta zame mishi wani bala'i da Hindu ta rasa ta inda zata fara tarbar shi, yaune karo na farko da take jin dana sani na tasowa daga dan yatsar kafarta yana tattarowa daga dukkan gabbanta kafin ya samu wajen zama a kirjinta "Kaine babban marar hankali wallahi, da kana da hankali ba zaka tsareni kana fadamun wannan maganganun akan wata ballagaza ba, kaine babban mahaukaci Hamza" Da mamaki yake kallonta, a tsayin rayuwar shi banda AbdulHafiz babu wanda ya taba kallon shi ya kira shi da marar hankali cikin raini haka "Ni kike kira mahaukaci?" Ya tambaya, kai ta daga mishi tana saka hannuwa ta goge fuskarta da wasu hawayen bakin cikin suka sake zubowa "Na kiraka mahaukaci, wallahi yaune na fara tir da mugun halin ka Hamza, na dauka zaka canza, na dauka zan iya canza ka, meye a jikin Mansy da ni bani da shi? Me take maka da ni ban iya ba?" Tayi mishi tambayar da ta dade tana yiwa kanta, yau ta bari ta fito fili saboda da gaske a tsorace take, tsoro bana wasa ba da halin Hamzan, a karo na farko tanajin kamar bata isa ta canza shi ba, kamar shi din bayason canzawa, in kuma bayason canzawa ita bata isa ta canza shi ba "Ka fadamun abinda take dashi da bani da shi, ka fadamun me kake nema a jikin ballagazar nan!" Juyawa yayi da nufin fita yabar mata dakin, saboda sosai kalamanta suke kara harzuqa shi, musamman da yakejin tana gab da fada mishi tayi dana sanin auren shi, idan shi bai gaya mata yayi nata ba, ba zai jira ta fara fada mishi ba "Ina zaka je? Ka amsa ni inji, ka fadamun abinda yake jikin karuwar taka da bani da shi" Juyowa yayi, muryar shi can kasan makoshi yace "Idan ba zaki iya karanta chats dina kiyi kukan ki ke kadai ba, karki sake shigar mun. Karki sake mun makamancin abinda kikai mun yau, wallahi zan baki mamaki, baki sanni ba har yanzun" Sosai take kallon shi tana sake sa bayan hannunta ta goge fuskarta "Wallahi idan yanzun na sake hawa saina zagi uban uwar Mansy, kana jina, saina zageta, akanta ne kake fadin zaka bani mamaki. Allah ya baka iko....na zageta, Hamza na zageta ka..." Bata karasa ba saboda marin daya dauketa da shi, wata irin walkiya na giftawa ta cikin idanuwanta, da gaske ne, littafi bai mata karya wajen rubuta kalar marin nan ba, ta runtsa idanuwanta tana bude su yafi sau hudu dan ta tabbatar da kwayar idonta bata fado ba. Kafin ta dafe kuncin, ta nemi hawaye ma ta rasa dan azaba "Na fada miki zan baki mamaki kinqi yarda ko?" Ya furta da wata irin murya dashi kanshi ta sauka kunnuwan shi da wani yanayi, jikin shi har bari yake saboda bacin rai, ya dauka Auta ce mace daya a rayuwar shi da zai taba dagama hannu. Saboda bai hango Hindu zata tunzura shi haka ba, zata saka shi jin son ya jibgeta har saiya daina jin nauyin da kanshi yayi "Mar... Mari, ni ka mara? Akan Mansy ka mareni?" Tsaki yaja mai sauti, yana wucewa hadi da jan kofar da karfi, kafafuwanta da taji suna rawa suka sakata zama, amman jikinta bari yake, dole ta kwanta, tanajin hawayen da suke bin gefen fuskarta, ga kirjinta da yayi nauyi kamar zai bude, mutanen da suka taba marinta basu da yawa a rayuwarta, ta kuma manta ranar da hakan ta faru. Mijin da take karkashin inuwar aure da shi, ko a mugun mafarki bata taba hango zai daga mata hannu ba, ko da hakan ta faru ba'a kan karuwar shi ba. Ba akan ballagazar da ko kira ta 'ya mace ba zata nuna mata ba, ballantana kuma daraja. Ta sha jin labarai na cin mutunci irin na da namiji, amman nata ne mafi muni da taci karo da shi a tsayin rayuwarta, yau ita Hindu, ita Hamza ya daga hannun shi ya dauke da mari saboda karuwa...! *** "Ban gane yace zai saka ranar da za'a kwashi kaya ba, sai ku ka taho kukuma?" Baba yake fadi ranshi a matukar bace yana kallon Muhsin da Huzaifa "Baba bana so in biye mishine ni, saboda kar ayi abinda za'aji kunya ko da sauran zama" Huzaifa ya fadi a tausashe "Wanne sauran zama? Shi da wanene zasuyi sauran zaman?" Shiru su Huzaifa sukayi, cikinsu babu wanda baisan halin Baba ba idan ranshi ya baci "Ya kore muku 'yar uwa cikin dare da tsohon ciki har kuyi tunanin akwai sauran zama a tsakanin su. Halan bakwa kishin ta ne?" Kai Huzaifa ya girgiza, yana shirin magana Muhsin yadan zungure shi alamar yayi shiru, tsaki Baba yaja "Ku koma ku kwasomun kayan yarinya dan banason su kara kwana a gidan wannan marar mutuncin" Muhsin ne ya fara mikewa yana ma Huzaifa ido, shima ya mike suka fice daga falon "Kasan halin Baba babu abinda zai saurara yanda ran shi ya baci, kuma Hindu aka taba, ni wajen aiki zan wuce, zuwa anjima watakila ya huce yanda zai iya fahimtar mu" Kai Huzaifa ya jinjina "Allah dai ya rufa asiri. Ni naso inga Hindun ma wallahi" Dan murmushi Muhsin yayi "Ka rufawa kanka asiri ka wuce, anjima ka dawo kaganta. Yanzun wallahi Baba kaniyar mu zaici" Shi Huzaifa ma sam ya kasa yin ko da murmushin ne saboda takaici. Shi kan shi idan za'abi shawarar shi za'a hakura da maganar Hindu ta koma gidan Hamzan nan. Tare da Muhsin din suka fice daga gidan, da shawarar duk idan kowa ya dawo daga neman halal dinshi zasu sake dawowa suyi ma Baba magana ko zai fahimci abinda suke son ya fahimta din. Cikin gidan kuwa, Anty najin duk abinda yake faruwa, idan ta gwada yiwa Baba magana ita kanta ranta ne zai kara baci fiye da yanda ya baci yanzun. Shisa ta nufi dakin Asma tana samun Hindu a kwance ta zubawa bango idanuwa, sai taji tausayin ta ya cika zuciyarta "Hindu..." Ta kira da wani irin yanayi a muryarta, tana saka Hindun tashi dakyar ta jingina bayanta da gadon, karasawa Anty tayi tana shiga cikin dakin sosai. Ta zauna gefen gadon "Hindu ke kadai kikasan meya hadaki da mijin ki, kamar yanda ke kadai zaki taushi zuciyar Babanku yayi hakuri abi komai a hankali..." Tunda Anty ta fara magana taji idanuwanta sun ciko da hawaye "Anty ki kyale shi kawai, ni ba zan taba komawa gidan shi ba, wallahi nagaji, tunda na fito na fito kenan da yardar Allah" Ta karasa maganar tanajin wani zogi da ba sabo bane a zuciyarta. Karfin tahowa gidane bata da shi daman tun watanni biyun da suka wuce, da tuni ta kamo hanya ta gudo daga gidan auren daya zame mata qangin da bata tana hangowa ba, daga auren mijin da kowa zau kira da kyakkyawa amman a idanuwanta sai da ya juye ya koma kamar dodo. Ba auren Hamza kawai take son gujewa ba, gabaki daya kalmar aurene bata son ji "Hindatu..." Anty ta kira da wani irin yanayi a muryarta, kai Hindu take girgiza mata, tana wani irin gunjin kuka me sauti "Anty karkice inyi hakuri, ya rigada ya sakeni, komawa ba zabi bane ko da ina so..." Hindu ta karashe, ballantana tunda ta shigo gidan takejin tana shakar wata irin iska mai sanyi da ta kwana biyu bata shaqi irinta ba. Ya saukake musu auren daya zame musu karfen kafa. Da kan shi ya sauke aurenta daya kira da kaddara "Kaddarar auren ki ce kaddara ta farko da nayi dana sanin ta Hindu a duk kaddarorin da suke cikin rayuwata" Ko kadan baya dana sanin kaddarar bin mata, kaddarar shaye-shaye sai ita, sai aurenta. Hamza ya gama cire mata duk wani kyale-kyale na aure da take tunani, taso MIJIN NOVEL, a sujjadarta ta roki MIJIN NOVEL, sai dai bata roka da kalar halayyar shi ba, har a zuciyarta idan ta hasaso, kudin, kyawun da soyayyar kawai take gani. Ta dauka ita kadai ta isa ta rike auren su, bata dauka aure ya wuce duk wannan ba. Hamza ya bude idanuwan ta, ya wanke tunaninta tas, ya dasa mata neman asalin dalilin da yasa aka saka aure a cikin jerin ibadu "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Anty ta fadi, wani irin daci na zauna mata a zuciya, kalmar saki abuce mai muni a duniyar ma'aurata komin karfin dalilin yin hakan kuwa. Ko labarin saki taji sai zuciyarta ta tsinke, yanzun da labarin ya fito daga bangaren ta, daya faru akan 'yarta ji take zuciyarta ta matse a cikin kirjinta tana wani irin ciwo "Allah Kai Kadai Kasan me Ka boye a cikin wannan lamarin. Allah Ka bamu juriyar cinye dukkan jarabtar da ka tsara mana" Anty take fadi a cikin ranta, kafin ta dora da "Alhamdulillah ala kulli halin" Tana cigaba da maimatawa, hannu Hindu tasa tana share hawayenta "Ya sakeni Anty..." Ta sake fadi, kalaman na zauna mata, ba kukan rabuwa da Hamza takeyi ba, kukan tarin abubuwan da ta hadiya a karkashin auren shi da tunanin zata iya gujema kawowa inda take yanzun. Kamota Anty tayi, a karo na farko da hakan ya faru, gyara zamanta tayi tana kwanciya ta dora kanta a cinyar Antyn, kuka take kamar zuciyarta zata fito, kuka take yau da take samun lallashin da ta dade bata samu kalar shi ba, kuka tayi har baccin wahala yai gaba da ita...! * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 27 Ran shi in yayi dubu a bace yake, shisa ko sallama baiyi ba ya shiga gidan Fodio. Shi ya hadu da mutumin da zaiwa zane a Office yau, suna karasa magana kan shi tsaye nan yayo. Shi kan shi yaga kokarin da yayi har yai magana da mutumin batare da an samu wata matsala ba. "Ina ta kiran ka baka daga ba" Arafat da yake tsaye ya furta, kallon shi Hamza yayi yana daga girar shi batare da yace komai ba, tunda baisan neman me Arafat din yake mishi ba. In dan client din sune, ya rigada ya gama magana da shi "Fodio ne daman..." Arafat din ya fadi muryar shi na rawa, hakan yasa Hamza cewa "Me ya faru? Me ya sami Fodio din?" Kai Arafat ya girgiza "Nima ban sani ba, tun jiya wajen karfe biyu na dare ya kirani naje na dauko shi, ko motar shi bansan ina ya kai ba, ya kulle kan shi a daki, duk yau fa bai fito ba" Da mamaki a fuskar Hamza yake kallon Arafat din, baice komai ba ya nufi hanyar dakin Fodio din, Arafat na bin bayan shi. Kwankwasawa ya fara yi "Fodio..." Ya kira yana cigaba da dukan kofar, dai-dai lokacin da AbdulHafiz ya karaso hadi dayin sallama yana dorawa da "Yanzun nake ganin text din ka Arafat, me yake faruwa ne? Me ya sami Fodio din?" Kafin Arafat ya amsa, Hamza ya riga shi da fadin "Da mun san me ya same shi ba zaka ganmu anan tsaye ba" Sosai AbdulHafiz din yake kallon Hamza, yayi watanni yana ganin yanayin da yake shimfide a cikin idanuwan shi yanzun, abu kadan yaje bata mishi rai, duk da ba hakuri gare shi ba tun da can, amman na yanzun ya wuce misali, yasan Hamza, ya san shi kamar yunwar cikin shi, yau neman taimako yakeyi, yana kokarin boye damuwar shi a bayan bacin rai "Ko me yake damun ka ya jira" AbdulHafiz ya furta, yana karasawa ya kwankwasa dakin "Fodio bamu da duk rana, ka bude kofar nan, nasan kana ciki, kana jinmu kuma, idan waje kake so duk mu baka, ka bude ka fada mana sai mu tafi..." Shirun dai ne amsar da suka samu "Idan na sake kwankwasawa zan dauka wani abu ya sameka, zan karya kofar in shigo Fodio..." Wani shirun ya sake ziyartar wajen, kafin suji alamar motsi, ana murza mukulli, tukunna Fodio ya bude dakin, kallo daya zakayi mishi kasan baya tare da nutsuwa ko kadan, ga idanuwan shi sun canza launi, sun rine sunyi wani irin ja "Me yasa ba zaku kyaleni ba?" Arafat ne ya fara wucewa cikin dakin, kafin Hamza yabi bayan shi, runtsa idanuwan shi Fodio yayi yana wani irin sauke numfashi, takawa yayi da nufin fita daga dakin, AbdulHafiz da yake bakin kofar ya hankada shi yana mayar da shi ciki, shima ya shiga, sannan ya tura kofar yana jingina bayan shi a jiki "What the fuck? Meye haka wai? Naji... Ku fita ina bukatar ku bani waje, kun ganni ai, babu abinda ya sameni, bana son magana ne da kowa" Fodio ya fadi muryar shi a dakushe "Baka san magana da kowa, tunda ka bude kofar kai kadai kake surutu Fodio" Arafat daya sami waje gefen gadon dakin ya zauna ya fadi, AbdulHafiz na dan daga kafadun shi cikin yarda da maganar Atafat din yana kallon Fodio, kafin ya zame takalman kafar shi yana shiga cikin dakin sosai shima. Kallon su Fodio yakeyi, sosai yake kallon su, Hamza na zaune ya saka hannuwan shi ya dafe fuskar shi. Arafat ya hau saman gadon sosai yana jingina bayan shi da bango hadi da mike kafafuwannshi, sai AbdulHafiz da yake zaune shima, ya dora kafar shi daya akan dayar. Ya san su, ba tun yanzun ba, kamar yanda yace bayason magana da su, ba zasu ce mishi komai ba, in zasu wuni zaune a dakin, ko a tsakanin su ba zasuyi hira ba, amman ba zasu taba barin shi ya zauna shi kadai ba a yanayin da suka gan shi. Tsikar jikin shi yaji ta tashi, kafin tsoron da ganin su yasa ya tafi ya dawo mishi yana cika mishi zuciya taf, idanuwan shi ya runtse yana jin shi a hotel din, yana jin kamar yana tsakiyar mata suna cashewa a hall din da aka kama dan gudanar da bikin cikar shekara na abokin shi da karatu ya hada su, shi kan shi kuma ya shigo Kaduna ne musamman saboda taron bikin. Zai iya cewa, kafin su Hamza, Ashir ne abokin da yake da shi, kuma abokin shi tilo da suke waya, suka san gidajen juna a garin Kano. Kuma har su Hamza sun san Ashir din, dan in ya shigo Kaduna suna haduwa duk a gaggaisa, har fita sukanyi tare. Idan yana hasaso wani lokaci da zai tuba ya daina rayuwar da yakeyi, yakan yi zaton kowanne mutum na duniya mai irin halayen shi ma yana da wannan tunanin, amman banda Ashir. Ko maganar akayi mishi tunda lalacewar da gidansu sukaga yayi ne yasa su yi mishi aure ko zai kintsu, maganar shi daya ce "Mai rabon shiryuwa fa zai shiryu, kana zaune in kana da rabo, ba sai ka wani wahalar da kanka ba, ku barni inyi shagalina" Ashir na rayuwa kamar an mishi alkawarin shekaru masu tsayi, yana rayuwa kamar yana da tabbacin me goben shi zata haifar. Haka daren jiya ya kasance musu. Ko Fodio bai fita daga gida ba sai karfe sha daya da rabi na dare, tunda ance musu shagalin har asuba zai kai, kuma haka suka cigaba da rallewa bayan an yanka cake, misalin karfe daya da rabi na dare, da shi da Ashir sun saka wata yarinya a tsakiya suna tiqa rawa ta rashin mutunci, Ashir din na mishi alamu da ya ganar mishi yanayin fuskar budurwar shi ko tana kishi. Dariya Fodio yayi yana girgiza kai, lokacin da yayi dai-dai da canjin daya bayyana a fuskar Ashir din yana dakatawa da rawar da yake hadi da dan dakuna fuska yana dafe kirjin shi "Ashir?" Fodio ya kira, amman sautin kidan da yake tashi bai bar muryar shi ta karasa fuskar Ashir din ba, kafin Fodio yai wani yunkuri har Ashir din ya yanke jiki ya fadi. Yanayin da yasa hankulan mutane da yawa komawa kan shi. Kafin wani lokaci gabaki daya hall din ya hargitse. Fodio ba zaice ga asalin abinda ya faru ba saboda tashin hankalin, abinda zai iya tunawa shine kalaman wani da baisan wanene ba yana fadin "Wannan ai ya rasu fa" Kalaman da suka gigita gabaki daya rayuwar shi, suka jefashi cikin wani irin firgici marar misaltuwa, wanda bashi kadai ba, dan da yawa mutane har an fara gudu ana fita daga hall din, cikin wannan tururuwar fitar ya tsinci kanshi da binsu, ya manta sam da mota yazo wajen, a haka ya samu ya fita daga hotel din zuwa titi ya fara tafiya, sai da ya karasa gidan man farko da yake hanyar tukunna ya iya tsayawa yana dan tsugunnawa cikin son neman numfashin shi da yake kokarin kwacewa. Jikin shi babu inda baya rawa, ko da tunanin ya ciro wayar shi ya kira kowa ya fara samu yazo mishi, sau hudu tana subucewa ta fadi daga hannun na shi. Sai da ya tsugunna tukunna ya samu ya kira Arafat, muryar shi ma bata fita sosai, kalamai yake kokarin hadawa kamar mai koyon magana "In zaka iya Fodio ka turomun location din da kake" Arafat din ya fadi, hakan ya samu yayi, tukunna yazo ya dauke shi. Basuyi wata magana ba har suka karasa gida, kan shi tsaye daki ya shiga yana mayarwa ya rufe. Kayan jikin shi ya fara cirewa, yana wanka ya tsarkake jikin shi, ya fito ya nemi wasu kayan ya saka, zuwa lokacin har zazzabi ya rufe shi. Mutuwar bata kara gigita shi ba saida ya kwanta, tukunna wani irin tsoro ya shige shi "Mutuwa na binku fiye da yanda tunanin ku yake baku wallahi, ba jiran ku zatayi ba, kuna tare da ita a duk takun da zakuyi, a duk inda zaku shiga tana jiran umarni, ku dinga shiga inda ba zakuyi dana sani idan mutuwa ta riske ku ba" Kalaman AbdulHafiz da yake fada musu a duk rana suka dawo mishi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya furta muryar shi na karyewa, da gaske AbdulHafiz yakeyi, mutuwa bata jiran kowa. Koya ya rufe idanuwan shi Ashir yake gani, yana kasa gasgata cewar a gaban idanuwan shi, a cikin hotel, da kida yana tashi mutuwa ta dirkar mishi. Ba abinda Ashir zai cewa Ubangiji Fodio yake tunani ba, shi abinda zai fada, baisan lokacin daya dirko daga kan gadon ba yana zama dirshen ya janyo kafafuwan shi, ba zai iya tuna ranar karshe da hawayen shi suka zuba ba. Duk kuwa bakar wahalar da yasha a gidan su, tunda ya fara gane kwayoyi ma ko dukan shi sukayi da ya jefa hudu ko biyar komai yake bace mishi, amman yau kuka yake kamar karamin yaro, kuka yake yana rasa kalaman da zai amfani da su wajen neman yafiyar Ubangiji, balle kuma ta inda zai fara dan ganin ya kankare tarin zunuban da suke kan shi. Gani yake kamar ba zai tashi daga inda yake ba mutuwa shima zata dirkar mishi kamar Ashir. Haka ya kwana anan wajen, bacci ko na dakika, asuba ma anan yayita, kan shi yake ji kamar zai bude. Har zuwa yanzun da su AbdulHafiz suka shigo, kafin suzo din yanajin kiran da Arafat ya dinga mishi, amman bayason ko da motsawa ballantana yaje ya bude kofar. Yanzun ma kallon su yakeyi "Inalillahi... Wai Fodio me yake faruwa ne?" Arafat ya fadi, ganin hawayen da suka zubo mishi, yana saurin saka hannu ya goge su. Hamza ma dagowa yayi da sauri, kafin yaji cikin shi ya hargitsa da tashin hankali "Fodio" Ya fadi cike da mamakin ganin da gaske kuka yakeyi, nan wajen ya durkushe, baya kunyar kuka a gaban su, ba lallai su fahimci kalar tashin hankalin da yake ciki ba, Ashir bai mutu a gabansu ba, basu ga yanda ran shi yabar jikin shi cikin wasu yan dakika ba, su dukan su tasowa sukayi suna rasa abinda ya kamata suyi banda tsayuwa akan Fodio din. "Ashir.... Ashir... Ya... Ya rasu" Fodio ya kakalo maganar dakyar, su duka ukkun kowanne da kalar salatin daya fito daga bakin shi "Fodio..." Arafat ya fadi cike da tausayawa "A hotel... Ya rasu a hotel" Fodio ya karasa maganar yana tsayar da rinannun idanuwan shi akan Hamza "Bamu da lokacin da muke tunani.. Hamza bamu da wannan lokacin" Kan shi Hamza ya saddar kasa, tsoron dake cikin idanuwan Fodio na taba shi ta fannonin da bai taba tunani ba, fannoni daban da yanda suke taba Fodio, dan bacin ran da yake tare da shi ya nema ya rasa, hakan na bude mishi kofar da yayi amfani da bacin ran ya rufe, hakan na ba wasu abubuwa daban ziyartar shi, kamar wanda aka dokama guduma a kai ya kalli AbdulHafiz, kafin ya furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Amman daga Fodio har Arafat sun dauka shima mutuwarce ta taba shi, AbdulHafiz ne kawai ya fahimci damuwar da take tattare da Hamzan bata da alaka da mutuwar Ashir. Kai Hamza ya dafe yana dan murza goshin shi, kafin ya sauke hannun hadi da furzar da iska ta bakin shi, yasan yanda yake idan ranshi ya baci, ya kuma san yanda yanke hukunci cikin fushi yake abokin tarayyar shi. Musamman idan yasha wani abu da ya kara taimakawa wajen tunzura shi. "Hindu..." Ya furta kasan numfashin shi, hanjin cikin shi na hautsinawa, hannun kofar da yake tsaye a kusa da ita ya kama, hakan nasa Fodio janye jikin shi ya matsa, Hamza ya bude kofar ya fice, su dukan su suna binshi da kallo kawai. Kafin Arafat ya zauna a gefen Fodio, AbdulHafiz ya zauna a dayan gefen, lallashin juna ba halayyar maza bace a yankin Najeriya, zasu zauna tare da shi har ya samu natsuwar da zai iya jinyar ciwukan shi da kan shi. Shine kawai abinda zasu iya yi mishi. * Yana zaune a mota yake gwada kiran lambar Hindu, tunda yayyenta suka zo gidan shi maganar kwasar kaya ya tabbata tana gida. Yasan yanda take a wajen Babanta, duk yanda zai dauki zafi, ita din zata iya lallaba shi, tunda tasan shi, tasan yanda yake idan ran shi ya baci, daya huce shikenan zasu shirya, yanzun ma da ta hakura har safe ta dawo gidan ya huce komai zai wuce musu kamar bai faru ba. Ba wannan bane gagarumin fadan da sukayi, kuma ko wancen dinma sun shirya, babu wanda yaji sunyi, sirrin su ya zauna a tsakanin su. Sai dai har tayi ringing ta yanke ba'a daga ba, ya sake kira har sau hudu "Bafa kabari ta dauki wayar ta ba" Wata murya ta furta kasan zuciyar shi tana saka shi dukan abin tuqin da karfin gaske, kafin ya dora kan shi a jiki "Bamu da lokacin da muke tunani..." Maganar Fodio ta dawo mishi da yanayin da yake fuskar shi lokacin daya furta mishi wannan kalaman. Tunasarwar AbdulHafiz ta kullum ce, amman duk idan Fodio ya bude bakin shi, saiya fadi maganganun da Hamzan zaiji sun shiga cikin fatar jikin shi suna tsikarin shi a wajaje da dama hadi da barazana da zaman lafiyar shi. Lumshe idanuwan shi yayi, kafin wani abu ya tsirga mishi, Ashir ya rasu, fuskar Ashir din yake gani da ranar karshe da suka hadu, yanda yake maganganun shi cike da buruka masu tarin yawa "Ba zaka gane rayuwar nan ba komai bace, sai kayi kokarin juya kwanciya bayan Allah ya mayar maka da ruhinka a gangar jikin ka, kaji kamshin kasa ya cika maka hanci, kana tunanin mafarkine, saika bude idanuwa kaga dundum, kafin mala'iku su dirar maka da tambayoyin da baka da yakinin zaka iya amsawa" Dagowa Hamza yayi da sauri yana bude idanuwan shi, kan shi ya girgiza ko muryar AbdulHafiz da tsoron dake muryar zasu fice mishi daga cikin kai. Da ya sami Hindu ya lallabata zata dawo, tsautsayina yasa fadansu yakai kunnuwan yan gidansu. Ta dawo ya riketa a jikin shi ko zai batar da abinda yake faruwa da shi yau. Samu yayi ya murza mukullin motar shi, kan shi tsaye gidan su Hindu ya nufa, ya dade ko bayan an bude mishi kofar yayi parking a zaune cikin motar yana rasa ta inda zai fara. Bawai yana ta'ammali da kunya bane ba, kawai baisan ta inda zai fara ba. Fitowa yayi daga motar "Kuskure ne kayi Hamza, idan su basu fahimta ba ita zata fahimta. Tana son ka, zata yafe maka kamar kullum" Ya furta ma kanshi a hankali yana kara samun kwarin gwiwa. Gidan nasu ba bakon shi bane, tunda bashi da wanda zai aika ya kira mishi ita, kan shi tsaye ya taka har ciki hadi da yin sallama yana shiga, da yake yasan gidan, baibi ta falon Mama ba, zagayawa yayi yana shiga falon Anty kai tsaye. Ita kuwa ta amsa mishi sallamar tana karasawa cike da bayanannen mamaki a fuskarta da ma muryarta ganin Hamza ne "Anty ina wuni" Ya furta yana sadda kan shi kasa, dan haka kawai yaji yau tayi mishi kwarjinin fiye da ko yaushe "Lafiya kalau" Ta amsa tana kallon shi cike da mamaki, dan bata tsammaci ganin shi yau ba, ko dame yazo kuwa. Zuwa tayi tana wuce shi, numfashi mai nauyi ya sauke ya sami waje ya zauna, da zaiga Hindu, da zata fito komai zaizo mishi da sauki, ko Asma ma, sai ta kira mishi ita. Yana wannan tunanin yaji muryar Baba kamar daga sama yana fadin "Me yazo yi?" Sai da zuciyar shi ta doka, baisan bashi da confidence ba sai ranar daya fara dora idanuwan shi akan Baba, muryar shi har rawa yaji tanayi, kuma gaishe shi kawai yaje yi wancen lokacin. Yanzun kam sai abinda Allah yayi, amman koma meye yayi laifi, wannan karin ya sani, laifin nashi ne daya bari rigimar su ta kawo gida "Lafiya? Me ya faru?" Baba ya furta yana zagayowa ya tsaya yana kallon Hamzan da har karfin halin zauna mishi cikin gida ya samuyi. "Baba ina kwana" Hamza ya furta yana wani irin sauke murya "Me ya faru?" Baba ya sake furtawa kamar baiji gaishe shin da Hamza yayi ba. Numfashi Hamzan yaja yana saukewa "Ni mai laifine Baba, dan Allah kayi hakuri. Zuwa nayi in bada hakuri" Wani irin kallo Baba yayi mishi "To madallah....ka tashi ka koma, kar su Muhsin su karasa gidan kuma a kulle, bana son kayan nan su kara kwana" Dagowa Hamza yayi yana kallon Baba cikin tashin hankalin jin maganar da yayi, abin babbane, yaga borin namiji ne "Babaa...." Ya fara, Baban na dakatar da shi "Ka tashi ka ficemun daga gida...ba zan sake maimaitawa ba" Yanayin muryar Baba ya saka shi mikewa, dai-dai lokacin da suka hada idanuwa da Hindu da ta fito daga dakin Asma da nufin ta dauki ruwa, ko muryoyinsu bataji ba saboda hankalinta na wani waje daban, aikam zuciyarta tayi wata irin mummunar faduwa, ji tayi kamar taga dodo, iskar da ta fara shaka ta daban na bace mata. "Baba me yakeyi? Ni ba zan koma ba, dan Allah karku ce in koma" Ta karasa muryarta na karyewa "Hindu..." Hamza ya fadi wani abu na matsewa a zuciyar shi ganin da gaske take furta maganganunta, har matsawa takeyi kamar zai karasa ya kamata su koma dole, kai take girgiza mishi "Zaka fice mun daga gida ko saika kara firgitamun yarinya?" Sosai ya kara kallon Hindu, kafin ya juya yana ficewa daga dakin, ita kam inda ta fito ta koma da saurin gaske, badan cikin jikinta da yayi mata nauyi kamar yana shirin fitowa kowanne lokaci ba, tsaf da gudu zata karasa cikin dakin. Anty ma nata dakin ta wuce, kome zata tsaya tacewa Baba bata bakinta zatayi, batace a saurari Hamza yanzun ba, koba komai dole su kwatarwa Hindu 'yancinta kafin su bari ta koma, amman yanda Baba ya dauki zafi idan tai mishi zancen komai ma zai iya faruwa, dan haka kai tsaye bandaki ta shiga tana daura alwala, abin yafi karfinta, ba zata wahalar da kanta ba, addu'a zatayi, tana da yakinin komai zaizo musu da sauqi. * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 28 Jin shi yake kamar an watsa mishi ruwan kankara, sanda ya koma gidan Fodio a falo ya sami AbdulHafiz. Tun fitar Hamzan suna tare da Fodio, panadol yasa Arafat ya dauko ya bashi. Da kan shi ya shiga kitchen ya hada mishi ruwan shayi mai kauri ya bashi ya sha, suka fito suka bar mishi dakin. Sai bayan sun dawo sallar azahar ne ma ya leqa ya ga yana kwance, sake janyo mishi kofar yayi ya dawo falo ya zauna. Addu'ar neman Rahma yake ma Ashir da ko jana'izar shi ba zasu samu suje ba, zai so suje din, amman Fodio bashida wannan nutsuwar. Arafat ya fita ya samo musu abinda zasu ci, hakan na nashi damar kiran Nabila, da maganar farko da yayi yasa ta fadin "Me ya sameka? Me ya faru?" Kai yadan girgiza "Bani bane ba, Fodio ne...." Duk da ajiyar zuciyar da tayi, bai hana wata damuwar bayyana a muryarta ba sai da ya ce mata rasuwa aka mishi, abokin shine ya rasu tukunna yaji ta nutsu "Kaci wani abu?" Kai ya girgiza kamar tana ganin shi "Kaci wani abu dan Allah, karka zauna da yunwa" Kan ya sake jinjina mata, yasan ta fishi rashin son magana, lokutta da dama yakanyi shiru ne dan yaji tata maganar "Ke ma kici wani abu, na kira ne inji muryar ki" Ko bai ganta ba yasan murmushi tayi "Ka kular mun da kanka. Allah ya tsare ya dawo da kai lafiya. Ina ma Fodio gaisuwa" Sallama sukayi, ya sauke wayar daga kunnen shi kenan Hamza ya shigo. Kujerar da take kallon ta AbdulHafiz din ya zauna yana dafe kan shi "Me kayi?" AbdulHafiz ya tambaya, yana sa Hamza dagowa ya kalle shi, hadi da dan girgiza kai "Ba zan sake tambayar ka ba, bana cikin yanayin Hamza, damuwar ku ba za taimun illa ba..." AbdulHafiz ya karasa maganar yanajin shi a gajiye "Bazan dinga neman damuwa a fuskar ku kamar kananun yara ba, kana jina, wallahi ba zan sake tambaya ba Hamza..." Ran shi yake ji a bace, ba tun yanzun yake ganin damuwa a fuskar Hamzan ba, ya tambaye shi yafi a kirga yana ce mishi ba komai, nauyi ya mishi yawa. Lokutta da dama yanajin kamar ya girmi shekarun shi, ko a gidansu bashi bane babba, amman matsalar kowa da shi yake rabawa, ga kuma ta su Hamza. Sosai ya gaji har cikin kasusuwan jikij shi "Duk wani kokari nayi, nayi Hamza..." Dan babu yanda za'ayi ka taimaki mutumin da bayason taimakonka, ko ya kake son yin hakan kuwa. Ba wai magana bace Hamza bayason yi, ba kuma fada mishi bane ba zai iya ba, asali ya tara abubuwa da yawa da ya kamata ya fada mishi baiyi ba. Bai saba daukar laifukan shi ba, yanzun da hakan ya zame mishi dole, baisan ya zaiyi ba, ko ta ina zai fara "Nayi kuskure..." Ya furta da wani nisantaccen yanayi a muryar shi "Ba jiya bane kawai" Ya sake fadi, daga randa ya fara dagama Hindu hannu ne farkon kuskuren shi, a ranar kuma yaji a jikin shi yayi kuskure, dan ko idanuwa bayason hadawa da AbdulHafiz, satin da yaje gida sai yake ganin kamar Anna zata gane abinda yayi, musamman da yaga Appa, kamar zai gane ya samu rauni a matsayin shi na namiji tunda ya dagawa matar auren shi hannu. Sai dai me, tsintar kan shi yayi da kasa dainawa, ko cikin da yake jikinta baya dubawa, karamar gardama da wahalar gaske su karasa bai daga mata hannu ba "Karka sake dukana, dan Allah karka sake dukana Hamza, idan zamuyi fadan mu muyi, amman ka daina dukana, zan tafi gidan mu" Muryar Hindu ta dawo mishi wani lokaci bayan ya hankade ta tayi wata irin faduwa, har taso samun matsala saboda cikin jikinta, tsoron da yaji bayan sun dawo asibiti, ya dauka zaisa ya bari. Sai da ya sake, sosai wasu lokuttan yake binta da idanuwa yana neman dalilin da yasa take mishi uzuri, yana rokonta da ta taimaka mishi, ko barin shine tayi ko zai dawo hayyacin shi, ya rasa abinda yake damun shi haka. Sosai yake daga kwalba fiye da da, cikin son rage damuwar da ta zame mishi abokiya. Kwata-kwata bashi da farin ciki. Inda wani yace mishi zai kai tsayin lokacin nan da mace daya zai karyata. Amman ko rage zafi ya fita yi da wata yarinya sai maganganun AbdulHafiz sun bishi inda duk ya shiga, wasu lokuttan kamar mai aiki da aljanu, yana dakin hotel din text din tunasarwar AbdulHafiz zai shigo mishi ya kashe duk wani abu daya shiga dakin da shi. Mansy ce kawai ta san yanda take tana samar mishi natsuwa ko da baya tare da ita. Hakan yasa shi duk ya watsar da sauran matan, da ita kawai yakan yi chat yanzun, yana kuma kokarin ganin hirar tasu ta tsaya iya whatsapp din shi, yana gogewa duk idan sun gama, in ba tsautsayi da rabon suyi tashin hankali da Hindu ya gifta ba, ta dauki wayar tagani. Yau ma kamar kullum, uzurinta ta kawo mishi kamar yanda take yi duk satin nan, sai tace mishi bayanta kamar zai bude. Hakuri take hada shi da shi, hakurin da baisan yanda zai fara yin shi ba, tunda bai saba ba, bar mata dakin yayi tunda ya riketa a jikin shima sai faman hakuri take bashi. Bayason suyi tashin hankali shisa ya hau sama yana wucewa ya dauko kwalbar giyar shi, ya bude ya ajiye, ya mike ya dauko kofin daya zuba kankaru a ciki ya dawo ya bulbula. Kirane ya shigo wayar shi, yana dubawa yaga Mansy ce ya daga "Hamzy... An shigo gidana... An shigo gidana yanzun" Ta karasa tana wani irin kuka kamar zata shide "Hey...kina ina yanzun?" Ya tambaya yana mikewa tsaye, amman kukan da takeyi ta kasa magana, hakan yasa shi yi mata magana cikin fulatanci "Basu tabaki ba ko?" Dakyar ta iya amsa shi da "Eh...kudi kawai suka dauka da gold, sai su tv...bansan iya abinda suka dauka ba" Kofin shi ya dauka yana karasa kwankwadewa "Ki kulle dakin da kike ciki....bari in zo" Yanajin kukan da takeyi har lokacin "Dan Allah ka zo... Bansan wazan kira ba, kai kadai... Kai kadai ka..." Kai yake jinjina wa "Shhh.... Gani nan zuwa yanzun" Ya karasa yana kashe wayar, ya duba agogo yaga karfe sha biyu saura. Mukullan mota ya dauka, kan shi ya danyi nauyi saboda vodka ya sha, tana da karfi, amman zai iya tuqi. Ficewa yayi daga gidan ya dauki mota, kan shi tsaye gidan Mansy ya karasa, ya sha mata magana kan ta sami ko maigadi ne, saboda yanayin shirun unguwar su, amman taqi ji. Aikam tana jin muryar shi ta bude kofar ta fada jikin shi. Riketa yayi sosai yana dan jijjigata a jikin shi "Ba zan iya kwana a gidan nan ba, ka kaini wani waje... Dan Allah ka kaini wani waje" Dan har ranta ta dauka mutuwarta ce tazo yau, yanayin su da makamai har su biyar ya firgitata, tazo rufe gida kenan suka afko mata. Kamata yayi suna fita daga gidan zuwa wajen motar shi, sai lokacin ya kula da tata motar ma bata gidan, kuma yasan su suka dauka. Inda zai nufa da ita yake tunani, yanda take a firgice ko hotel ya kaita yasan ba zata zauna ita kadai ba, shikuma ba zai iya kwana tare da ita ba saboda Hindu ita kadai ce a gida, ga tsohon ciki. "Dan Allah karka barni ni kadai, yau kawai karka barni ni kadai, kana da mata nasani..." Ta karasa cikin kuka. Kai ya jinjina mata yana nufar gidan shi kai tsaye, akwai dakuna da yawa inda zata kwana, yau kawai. Zuwa gobe sai acan yanda za'ayi. Ko ba komai kawar shi ce. Haka suka karasa gidan, yayi niyyar saiya fara kaita inda zata kwanta, sannan ya shiga wajen Hindu, in batayi bacci ba yasan yanda zaiyi ya fada mata Mansy zata kwana a gidan yanda ba zasuyi rikici ba. Amman sai hakan bai yiwu ba, saboda suna shiga tana saukowa daga sama. Haka kawai bayan yabar dakinta take ganin kamar zai je yayi waya da Mansy, batasan ya haihuwa take ba tunda bata tabayi ba. Amman har a kasusuwan jikinta takejin tana gab da sauke abinda yake cikinta, duk da asibiti sunce mata tana da sauran satika uku, ko sama da haka, amman yanda bayanta yake amsawa kawai yana karyata likitocin. Amman Hamza yaki fahimta, kamar ranta zaibar jikinta haka takeji duk idan ya kasance tare da ita. Yanda ya fita a fusace har kwalla tayi, jarabar shi ta isheta, har auren ma ya fita a ranta, a hankali komai ma take tsintar kanta da jin baya ranta. Musamman yanzun da take jin kafarta daya a duniya, daya a lahira, wasu kyale-kyale ne karshen abinda yake ranta, inda wani yace bata fara hauka akan siyayyar kayan baby ba zata karyata. Amman Hamza da yayi mata maganar ca tayi yaba Anna din da ta fara mishi zancen suyi duk abinda ya kamata, ita kam ba zata iya ba, so take kawai taga ta haihu lafiya. Duk da sun yanke hukunci basa son sanin meye zasu haifa din, gara yazo musu a ba zata. Har bandaki ta duba shi bata gan shi ba, dakyar take saukowa daga benen, da hijab din da ta saka bayan ta daura alwala da nufin yin ko raka'a biyu ce ta nafila bayan fitar tashi, saita kasa samun nutsuwa shisa ta fito ta duba shi. Sai gashi ya shigo, da wata mace manne a jikin shi, ko dankwali babu a kanta, asalima rigar jikinta ko gwiwarta bata karasa ba, ita kanta Hindu daga inda take tana ganin duk wata halitta ta jikinta. Harta karasa saukowa daga benen abin na mata kamar a mafarki, saboda tasan duk abin Hamza ko da wasa bai taba shigo mata da wata mace gida ba, yanzun ma yana kokarin boye mata abinda yake faruwa da wannan fannin na rayuwar shi. Ko giyar shi da tagane bai daina sha ba, ya sha yau bata tunanin zata gaya mishi ya shigo mata da wata mace cikin gida haka. Ta kasa yarda harta karasa gab dasu ta tsaya, tana karewa Mansy da ta boye bayan Hamza kallo. Dariya Hindu tayi me sauti tasan mafarkine daman, saboda Mansy tafi tsana duk a cikin matan da yake bi, shisa ta kasance macen da mafarkinta ya hango mata a tare da Hamza "I can explain, ba abinda kike tunani bane ba" Hamza ya fadi yana kallon Hindun, har ranshi ba abinda yasan take tunani bane ba "An shigar mata gidane, bata da inda zataje, kwana kawai zatayi da safe sai tasan ya zatayi. Nasan zaki fahimta" Kallon shi Hindu tayi, tana saka hannu ta taba kirjin shi, taga yana nan dai, itama kanta ta mintsina taga da gaske na mafarki bane ba, wani irin ashar ne ya kubce mata, sam batasan duk zagin da takeji tana adana shi bane sai bayan ta auri Hamza, Mansy da ta kara shigewa bayan Hamza ta mika hannu ta fisgo "Dan ubanki da nace ki kyalemun miji baki jini ba ko?" Hindu ta karasa maganar wani irin kishi na lullube mata idanuwa, dan batasan lokacin da ta daga hannu tana shararawa Mansy mari ba, ko kadan bataji nauyin cikinta ba, niyyar fara jibgar Mansy din takeyi kamar ganga, dakyar Hamza ya banbare Mansyn da ta koma gefe tana rawar jiki, ita iya tashin hankalin da ta gani yau ya isheta, maruka tasha sunfi goma a hannun barayin nan, dan daya sai da yaso keta mata haddi, ogan nasu ya tsawatar mishi, tasan haushin hakan yasa shi shimfida mata wasu marukan. "Hindu... Hindu..." Hamza yake fadi, yasan ta iya rigima saboda ba karamar mace bace zata iya kallon idanuwan shi ta biyema tashin hankalin shi, amman ko dukanta yayi bakinta baya mutuwa, kuma saita fada mishi duk wani abu da tayi niyyar fada ko zai kasheta. A girman jiki Mansy ta fita, amman idan zai barsu, duk da cikin jikin Hindu dukan tsiya zatayiwa Mansy yasani "Ta fitar mun daga gida...dan ubanki ki fitar mun daga gida kafin in karairayaki" Kamata Hamza yakeyi tana zillewa, in bata jibgi Mansy ba sam ba zataji dadi ba, ko kuka ta kasa, haka Hamza yake janta harya samu ya shigar da ita daki "Ina kike so taje? Bakiji nace miki barayi sun shigar mata gida ba?" Kallon shi tayi "Idan baka fitar mun da ita daga gida ba ku biyun zaku ga tashin hankalin da baku taba gani ba" Idanuwan shi ya runtsa, kan shi yayi nauyi sosai, kuma ranshi ya fara baci "Bafa gidanki bane ba, ina da damar da zan kawo wanda duk naga dama...bana son yin rigima dake. Zata kwana da safe zata tafi" Dariya Hindu ta kwashe da ita da bata da alaqa da nishadi ko kadan "Wallahi ba zata kwanar mun a gida ba, ka kawo kowa banda karuwar ka" Kai yake girgiza mata "Ki bari, karki sake..." Ya karasa yana fita daga dakin, ta kuwa bi bayan shi, kitchen ta wuce bata sami wani abu a kusa ba, saboda ta manta ranar karshe da tayi girki, tukwane ne kawai a kusa, guda biyu ta dauko, tana fitowa daga inda take ta fara cillawa Mansy "Dan ubanki ba zaki fitar mun daga gida ba ko?" Dayar tukunyar ta sake dagawa tana nufar ta, da gudu kuwa ta fice daga gidan, Hamza ya tare Hindun yana kokarin karbar tukunyar da take hannunta, dakyar ya kwace, bata nutsu ba duk maganar da yake mata, haukan da takeyi mishi saika dauka tana da aljanu, sai da ya kwashe ta da mari tukunna ta fara dawowa hayyacinta "Ki kiyayeni Hindu, wallahi ki kiyayeni" Ya furta yana ficewa daga gidan, a harabar ya samu Mansy tana kuka kamar ranta zai fita. "Kabani mota in samu ko hotel ne, matarka zata kasheni Hamza" Dan dafe kai yayi, yana komawa cikin gidan ya haura sama, kudi ya dibo da baisan yawan su ba da mukullin dayar motar shi yana komawa ya bata sannan ya dawo cikin gidan "Na fada maka ba zata kwanar mun gida ba" Kallonta yake yana tunanin abinda yasa take kiran gidan shi da nata "Wallahi idan nayi niyya ke baki isa ba Hindu, gidana ne idan ma karuwar zan kawo gidana ne" Kallon shi takeyi tanajin yanda auren shi ya kawo mata iya wuya "Sai dai ke kibar mata gidan idan ba zaki iya zama ba" Kai take jinjinawa wasu hawaye na zubar mata "Ka bani hujja kaga idan ban tafi gidan mu, ka sakeni kagani..." Ran shi yayi matuqa wajen baci, yagaji da auren ta, ya gaji da yanda take nuna mishi saboda ya aureta bai isa yayi abinda yake so ba "Kaddarar auren ki ce kaddara ta farko da nayi dana sanin ta Hindu a duk kaddarorin da suke cikin rayuwata" Sai lokacin hawayenta suka zubo jin yanda kalaman suka fito daga zuciyar shi "Baka ga kaddarar neman mata ba, baka ga kaddarar shan giya ba sai ta aurena? Na tsaneka Hamza, nayi dana sanin da ban saurari Yayana ba na aureka wallahi" Kai ya jinjina mata "Da kin fadamun tuntuni ai, dana saukaka mana duka damuwar mu kinyi gaba" Hannu tasa tana share hawayen fuskarta "Yanzun ma bai baci ba Hamza...ka bani takardata kaga idan ban bar maka gidan ka ba" Yanda yakeji idan ya kara minti daya a wajen rufeta zaiyi da duka. Sama yahau ya samo takarda ya sakko, har lokacin tana nan tsaye tana zubar da hawaye, jinta take da gaske kamar a mafarki, tana kallon shin yana rubutu, harya gama ya ninke yana fadin "Gashi nan, ki fita kibar mun gida" Sosai take kallon Hamza saboda ta tabbatar ba kunnuwanta kadai suke jin alamar ruwan sama ba, hakan yasa ta dan kalli window din dakin "oh karki damu..." Ya furta yana wucewa kitchen din dakin, wata baqar leda ya samu ya kulle takardar a ciki yana janyo hannunta ya mika mata "Sai ki fitar mun daga gida, ba zata jiqe ba, kina da abinda zaki nuna musu in kinje" Kuka take zuwa yanzun, badan sakin yana mata ciwo ba, sai dan ganin da gaske Hamza janta yake zai fitar da ita daga cikin gidan ana ruwan sama, da tsakar daren nan "Duka biyun ka karasa?" Ta bukata tana kokarin kwace hannunta daya rike yana janta kamar zai karyata, tana son tuna mishi bata manta da sakin farko da su kadai suka san da shi ba "Koma nawa nayi ba dawowa zakiyi ba..." Ya karasa maganar yanajin iskar 'yan cin da yake shaka, kawai so yake ta fitar mishi daga gida, duk inda zataje taje. Da ta fara tirjewa sosai tana fadin "Takalmina, ban dauki wayata ba Hamza... Ka bari in dauki takalmana..." Wani irin mari ya kwasheta da shi sai da komai ya tsaya mata na wasu dakika, dan harya jata ya fita da ita, taja jin yanda yake ma maigadi kashedi amman wani irin sama-sama take jinta. Kamar yanda yake jin shi sama-sama, yanda yake jin shi kamar a mafarki yake, duk maganar da yake da yanda sabon tashin hankali yake ziyartar shi gani yake kamar zai koma gida ya gan Hindu. Sai da yaga AbdulHafiz ya mike tukunna yace "AbdulHafiz..." Amman baiko nuna alamar yaji ba ballantana ya kalle shi, wayar shi da take gefe ya dauka ya saka a aljihu, yana daukar hular shi "AbdulHafiz..." Hamza ya sake kira cikin wani sabon tashin hankali, bai kamata yabarshi shi kadai ba. Ba zai yiwu ya gama bude mishi ciwukan shi yayi kamar hakan ba komai bane ba. Wucewa AbdulHafiz din yayi, yana cin karo da Arafat a bakin kofa "Muje..." AbdulHafiz din ya fadi yana sa Arafat kallon shi cike da rashin fahimta "Ka wuce muje, kaima ba zaka so ka zauna da shi ba in kasan me yayi, ka wuce kawai Arafat" Kai kawai Arafat ya jinjina yana wucewa suka fice daga gidan gabaki daya. Suna barin Hamza nan sake da baki, a karo na farko a rayuwar shi da yasan tabbas yayi babban kuskure, in har AbdulHafiz zaiqi sauraren shi haka, da gaske yayi kuskuren da baisan ta ina zai fara gyarawa ba. * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/18/20, 9:50 AM - mmn khalid: 29 Da wani ya tambaye shi me yayi a cikin kwana biyu ba zai iya fadi ba, ko da kudi za'a saka mishi kuwa. Ko masallaci baije ba a kwana biyun, tunda ya hau sama bai sakko ba, kwalaben giyar shi ma dibowa yayi ya ajiye gefen gado, daya mika hannu dauka zaiyi. Ranar farko yana dawowa gida ya sami su Muhsin a kofar gida, bai tsaya gardama da su ba yace su shigo su kwashe kayan, ya sanar musu kayan duk da suke a kasan na Hindu ne, sannan ya hau sama ya shige dakin shi, kwalaben giya ya dauka ya samu waje ya zauna, sai da ya daina gane abinda yake faruwa, bai sauran salloli ba sai cikin dare. Gabaki daya ya daina gane kan rayuwar. Jin shi yake kamar an kama kafafuwan shi an daga su sama an jirkice shi. Dan snacks din da yake dashi a saman ne kawai abinda yake a cikin shi. Ko yau ma daya mike zaiyi alwalar Magriba saida ya koma ya zauna na wasu dakika saboda jirin da ya kwashe shi da bashida alaka da giya sam, tunda bai sha ba duk ranar. Badan sallah ba, motsi ma ba zaiyi ba. Wayar shi na falon kan kujera tun shekaranjiyar, idan an kirama bai sani ba, balle kuma ko da caji a jiki ko babu. Yana samu yayi sallar ishai ya koma ya kwanta, ko kwan dakin da yake ji cikin idanuwan shi bai iya tashi ya kashe ba. Duk tsaftar Hamza a kwanaki biyun nan jikin shi banda ruwan alwala baiga wani ruwa ba, kayama amai da yayi ne ya jikasu garin wanke fuska shisa ya sake wasu. Kallo daya za kai mishi idan kagan shi kasan baya tare da natsuwa sam, dan rigar da wandon basu hadu ba, haka yasa kayan shi. Kamar cikin kunnuwan shi yake jin ana sallama, sake runtsa idanuwan shi yayi yana shigar da kanshi cikin filo. Sosai yake jin sallamar na kara kusantowa kafin a fara kwankwasa kofar dakin da yake ciki "Yayaa" Yaji muryar Auta, kafin ta Abid da cikin yaren shuwa yake fadin "Yayaa...ko dai basa nan?" Da shakku a cikin muryar shi, suna zaune a gida kawai shi da Auta suka yanke hukuncin fita siyan shawarma, Anna ma sai da tace suyi order a kawo musu gida, sukaqi saboda yawon suke so. A hanyar su ta dawowa ne sukayi shawarar su biyo gidan Hamzan tunda kwana biyu basu gan shi ba. Suna da tabbacin aiki ne ya rike shi, idan bai kira su ba, yakan yi musu zuwan bazata makaranta ya duba su. "Wanne irin basa nan, kana ganin wayar shi a kan kujera? Ni jikina na mun wani iri. Kuma falon kasa tas an kwashe kaya fa" Auta ta fadi, kafin ta murza hannun kofar tana turawa "Yayaa" Abid ya kira cikin tashin hankali, su biyun suna turereniya wajen shiga cikin dakin, amman ko dagowa Hamza baiyi ba, basu tabbatar yana da rai ba saida suka hau kan gadon, Abid na kama shi ya juyo da shi "Ka kyaleni Abid" Ya furta yana kwace jikin shi, ko motsi bayason yi. Shiru yake bukata har sai ya samu dai-daito koya yake. "Wanne irin in kyaleka? Me yake faruwa? Me ya sameka?" Abid yake tambaya cikin tashin hankali, dan ba zai tuna ranar karshe da yaga Hamza kwance yana wani ciwo ba tun tasowar su. Baisan ko da yabar kasar ba. Auta ce da ta taba jikin Hamzan tana jin shi kamar wuta tace "Zazzabi ne ma a jikin shi" Kama Hamzan ya sake yi yana dago shi, yama ki bude idanuwan shi "Yaya ka tashi mu kaika asibiti, baka da lafiya zaka zauna a gida. Ina Anty Hindun zata barka haka?" Kai Hamza ya girgiza mishi yana bude idanuwan shi da yakeji sunyi nauyi, jin sunan Hindu na saka tsikar jikin shi tashi, hannun shi daya yasa yana ture na Abid "Na ce ka kyaleni bakaji ba ko?" Kallon juna Abid da Auta sukayi, cikin su babu wanda baisan kafiya irin ta Hamza ba, sauka daga gadon Abid yayi, mutane kance Hamza dogo ne, tsayayyen namiji, amman wanda duk zaiga Abid din saiya dauka shine Yayan Hamza, saboda a tsayi da girman jiki ya fishi. Akanyi mamaki ko da Hausa yayi akaji alamar fulatanci daya zauna a harshen shi, mutane na da yardar cewa fulani na da dan jiki, mafi yawancin su kuma basa girma. Sai su dinga yi kamar Abid dinne bafullatani na farko daya karya al'adar su ta fitowa a siraran mutane "Zaka iya tashi da kanka Yaya... Ko zan dauke ka. Wanda duk ka zaba shi zai faru" Abid yai maganar yana kallon Auta "Ki kira Ann" Kai kawai ta daga mishi tana sauka daga kan gado itama, dan wayarta na cikin mota tabari, duk a zaton su 'yan mintina zasuyi su wuce gida. "In dauke ka din kenan?" Kallon shi Hamza yayi, baya cikin yanayin da zai iya yin wata gardama, dan haka ya mike, jirin da yake gani bai hanashi ture hannun Abid daya mika mishi cikin son ya taimaka mishi ba. A haka suka sauka kasa. Abid ne ya dauki wayar Hamzan yana sakawa a aljihu, a wajen suka hadu da Auta "Babu asibitin da zanje, mu tafi gida kawai" Ya furta yana bude bayan motar ya shiga. Cikin kasa da mintina da suka dauke shi ya fito daga cikin gidan ya shiga motar ya riga ya yanke hukunci daya, ya daina boyewa abinda yake faruwa, fadansu ya riga da ya kai gidan su Hindu, ko zata dawo mishi dole maganar ta kai nasu gidan. Da Anna taji me yake faruwa daga bakin wani cikin manyan Hindu, gara taji daga bakin shi. Ko ba komai ita ba zata bar shi kamar yanda AbdulHafiz yayi mishi ba. Duk a cikin abinda ya faru daga kwana uku zuwa yau, babu abinda yake mishi ciwo har kasan zuciyar shi irin yanda AbdulHafiz ya tashi tsam bayan ya gama bude mishi ciwukan shi, yanda ya mike yana barin shi kamar yana tsoron idan jinin da ciwukan da ya bude mishi suka taba shi wata cuta zata kama shi. Sosai abin yayi mishi ciwo na gaske, sai da suka hada idanuwa da Arafat kafin shima ya zabi bin AbdulHafiz batare da yama san meya faru ba. Har suka karasa gida wannan tunanin yakeyi a ran shi. Auta ce tayi sallama, dan a falo ta sami Anna a tsaye, tun bayan da ta kira ta fada mata Hamzan bashi da lafiya, gashi suna gidan shi ma, ta kasa samun natsuwa sam, itama ta sake kiran Autar, tace gasu nan ma zasuyo gidan. Hatta Appa ta fada mishi, shima yana falon a zaune, idan yace mata ta zauna ma ba zata zauna ba, shisa bai bata bakin shi ba. Appa ya dauka ciwon ba zai wuce zazzabi ba sai da ya kalli yanayin Hamzan kamar wanda ya sami tabin hankali na wucin gadi, ga gashin da yake fuskar shi duk ya cukurkude saboda rashin gyara. Waje ya samu a daya daga cikin kujerun falon yana zama, ba sai wani ya fadama Abid da Auta abinda suke gani ba, sun san koma meye yake damun Hamzan ya girmi rashin lafiya. Dan haka kowa ya wuce dakin shi batare da sunce komai ba "Hamza..." Appa ya kira, dan Anna ma ta rasa abinda zata ce saboda tashin hankali, tunani takeyi barkatai a lokaci daya tana son hasaso abinda ya sami danta haka "Appa ban kyauta muku ba" Hamza ya fadi idanuwan shi kafe a jikin bango, yaki yarda ya kalli fuskokin su, jin yanda kafafuwan Anna suke rawa yasa ta samun waje gefen Appa ta zauna, numfashi Hamza ya sauke mai nauyin gaske, yana sauke idanuwan shi akan su Anna "Na saki Hindu" Ya furta yana jin wani irin shiru daya biyo bayan maganar da yayi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Shine abinda Anna ta fadi, Appa na dorawa da "Subhanallah, saki da tsohon ciki Hamza? Me ya faru haka?" Dan daga kafadun shi Hamza yayi, baisan ta inda zai fara ba, baisan me zai ce musu batare da halayen shi daya dauki shekaru yana boye musu sun fito fili ba "Bansan me zance ba Appa, kawai nasan ba laifinta bane ba...har sun kwashe kayan su" Ya karasa maganar yana gyara zaman shi a cikin kujera. Yanayin shi yasa Appa fadin "Yanzun aini gidan ya kamata inje..." Saboda koma meya faru yanayin Hamzan ya nuna idan fada ya rufe shi da shi babu abinda zai fahimta. Tun ranar da abin ya faru ya kamata ace sun sani, baisan wanne kallo iyayen Hindu suke musu ba, ballantana ga tsohon ciki, haihuwa yau ko gobe, ace ya sakar musu yarinya "Ai bakai kadai ba, harni ya kamata mu tafi" Anna ta fadi tana daukar mayafinta da ta fito da shi da nufin ta bi bayan su asibiti. Ganin Hamza ya kara gyara zama yasa Appa fadin "Kaima kasan ai ba zama zakayi ba ko?" Numfashi yaja yana saukewa, bashi da wani zabi. Haka ya mike yana bin bayan Appa, sannan Anna ta furta "Abid mun fita" Cikin yaren shuwa, tana jin ya amsa mata tukunna itama tasa kai suna ficewa daga gida. Appa ne yaja motar suka nufi hanyar Barnawa da zata sada su da gidan su Hindu. * Wani irin bacci takeyi a kwana biyun nan kamar wadda ta tara gajiya mai yawan gaske. Tun da aka kwaso kayanta sai take jinta wani irin sama-sama, ga ciwon baya da take fama da shi da bata furtawa kowa komai a kai ba, asibiti ma da taje batayi musu magana akai ba. Tana jin yanda tai wata irin saduda da lamurran duniyar gabaki daya. Ko da wayarta da aka kawo mata, drawer ta ja ta jefata a ciki. Batasan karya ta fadama kanta na cewar Hamza da auren shi sun fita daga ranta ba sai da taji zuciyarta na mata wani irin ciwo bayan kwaso kayan. Amman ta mikama Allah lamurranta, hawaye ma a kwanakin nan sun kaurace mata. So take kawai ta juye abinda yake cikinta ko zata rage wani nauyin. Gashi yan gidan kowa yana kokarin ganin murmushi a fuskarta, musamman Asma da ko kwanciya ta juya sai taji ta tambayeta ko lafiyarta. Daren jiya ma sai da tace "Asma lafiyata kalau fa, kiyi bacci kin ji ko?" Anty kanta tana iya lekasu fiye da sau biyar kafin wayewar gari. Yau ma ganin yanda duk idan ta wuce suna binta da ido kamar mai shirin breaking a kowanne lokaci sai ta koma tana tausaya ma damuwar da suke ciki. Shisa tana idar da isha'i bata kwanta kamar yanda takanyi ba, ta fito falo ta zauna ayi hirar da ita, suna kallon shirin "Kwana casa'in" a tashar Arewa24. "Ni fa Mal. Alin nan bala'in kunnani yakeyi" Asma ta fadi, Jafar na jinjina kai "Ai wawane, yanda yakeyi kamar yana da kyau shine abinda yafi batamun rai" Dan murmushi Hindu tayi "Kuji ikon Allah fa, celebrity ne fa" Wani irin tsaki Jafar yaja "Kuyita rage mishi dai kunji" Cewar Anty da take zaune a gefe, da yake girkinta ne ranar. Mikewa ma take shirin yi ta shiga bangaren Baba, sai gashi ya shigo falon "Me ake kallo haka?" Hindu da murmushinta ya fito daga zuciyarta yanzun ta riga kowa amsa shi "Baba..." Ta furta cike da kaunar da takeyi mishi "Hindu... Kinci abinci?" Baba ya tambaya. Ta bude baki zata amsa shi, sallamar su Anna ta katse ta, sai da taji zuciyarta tayi wani irin dokawa kamar zata fito waje saboda wani irin firgici da ta tsinci kanta a ciki, har suka gaisa da Anty, aka basu wajen zama, sam bataji ba, hankalinta na kan Hamza da yake tsaye a gefe kamar magen da aka tsoma a ruwan sanyi. Kanshi sadde yake a kasa, lokacin da Anty tadan taba Hindu ne ta kula da har su Anna sun zauna, Asma da Jafar ma bata ga barin su falon ba "Ina wunin ku" Hindun ta iya furtawa muryarta na karyewa "Lafiya kalau Hindatu, sannu kinji" Appa yai maganar kamar yana neman wata Hausa da ta dace yayi amfani da ita, Anna kuwa duk kunya ta gama rufeta, tama kasa cewa komai, wani irin shiru na ziyartar falon, kafin Appa ya fara magana "Wallahi Alhaji Aminu mu bamu san abinda yake faruwa ba sam sai yau din nan, yana zuwa ya same mu da maganar muna tahowa" Kai Baba ya jinjina "Haba bakomai, ai zance ya rigada ya kare ma. Har an kwaso kaya" Kallon Hamza da ya kara sunkuyar da kan shi Appa yayi, kafin ya mayar da hankalin shi kan Baba "Subhanallah..." Sai dai bai samu damar furta wani abu ba, Baba ya riga shi "Da ya fada muku ya saketa, ya gaya muku cikin dare ya korota waje? Ana tafka ruwan sama?" Wannan karin Anna ce ta kalli Hamzan cike da bayanannen mamaki a fuskar ta, so take ya kalleta, so take ya karyata mata abinda Baba ya fada, dan tasan yaronta mai tausayi ne, Hamzan ta ko mace mai ciki yagani tsakiyar dare ana tafka ruwa zai tsaya ya taimaka mata, dan ta ba zai aikata wannan halin da zata alaqanta shi da na marassa tunani da tausayi ba, dan bata taba jin ko yan unguwa sun mishi shaidar zalunci ba "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Appa ya fadi yanajin lamarin yafi karfin shi, da Baba yace an kwaso kaya sai da ranshi ya sosu da rashin neman su da baiyi ba dan ai kokarin sulhunta lamarin. Yanzun kuma da yaji dalili, sai yaga sunyi mishi matuqar kokari da suka ma basu wajen zama. "Bana so duk mu bata lokacin juna, aurene kaddara ta hada, yanzun kuma ta raba. Sai muyi musu addu'a Allah yasa hakan shine alkhairin su, ba zance zumunci zai kare ba saboda rabon da yake jikinta....aure kam in shaa Allah karshen shi kenan" Baba ya karasa maganar da dukkan zuciyar shi, dan yaga takardar sakin, kuma a rubuce saki dayane Hamza yayi. Hindu tasan yagani, saboda Anty ta fada mata, su duka basu san saki biyu bane ba, har yanzun akwai kome a tsakanin su da Hamza, komen da ko a mugun mafarki bata fatan ya faru da ita balle kuma a gaske "Baba dan Allah kayi hakuri, nayi kuskure nasani, amman kayi hakuri" Hamza ya fadi zuciyar shi na wani irin radadi, ganin kallon da Baba yayi mishi yasa shi kallon Hindu "Hindu ki bashi hakuri, kinsanni, ke kinsan abinda su basu sani ba a kaina. Ba zan sake ba, wallahi ba zan sake ba... Ki basu hakuri" Ya karasa maganar yana takowa ya shigo tsakiyar falon ya tsugunna a gabanta batare daya damu da su Anna da suke zaune ba, ballantana kuma su Baba. Bayajin akwai macen da zata zauna da shi da halayyar shi kamar Hindu, baima san yanda yake son ta ba sai yanzun da yake ganin da gaske raba shi za'ayi da ita, da gaske sukeyi ba zasu hakura ba "Ba zamu bar juna ba, duk abinda zai faru ba zamu bar juna ba, zaki zauna da ni har in canza, zakiyi hakuri dani har in canza..." Hamza yake furtawa yana sauke idanuwan shi cikin na Hindu da suke cike taf da hawaye "Kome zai faru ba zan barka ba, na yafe maka kuskuren ka na baya, zanyi kokari in yafe maka kuskuren ka na gaba" Hindu ta karasa mishi hawaye na zubar mata, wannan shine alkawarin da sukai ma juna bayan ya sake ta, lokacin da yaga da gaske ta janyo akwati tana hada kayanta, hakurin daya bata a ranar tayi tunanin shikenan, ta dauka wani abu ba zai taba sake shiga tsakanin su daya danganci shan giyar shi ko Mansy ba. Shisa ta tayashi suka binne rigimar, babu wanda yaji ko yagani. Hannuwanta duka biyun ta saka tana goge fuskarta, wasu hawayen ne suke sake zubowa kamar an bude famfo "Wannan alkawarina ne, nayi kokarin cikawa, ka manta naka?" Wani abu da yaji ya tokare mishi makoshi yake kokarin hadiyewa "Zaka canza, ba zaka sake dukana ba, ba zaka sake shan wani abu ba, matsalar mata ba zata sake zama dalilin rigima a tsakanin mu ba..." A rayuwar shi ya lissafa abubuwa da dama da zasu saka shi kuka, amman bai hasaso mace bace ba, ko bayan da ya auri Hindu bai dauka rana irin ta yau da hawayen shi zasu zuba a kanta zaizo ba, sai yanzun da yaji idanuwan shi sun cika taf da hawaye "Zan dora alhakin auren ka akan kaddara, amman yi maka uzuri a lokutta da dama kuskurena ne, ba zan sake maimaitawa ba, Hamza bazan sake maimaita wannan kuskuren ba" Kai yake girgiza mata, idan yai magana gunjin kukan da ta karashe zancenta da shi zaiyi shima, fuskar shi ya dafe da hannuwa biyu. Daga Anty da take zaune, Baba, Anna har Appa jikin su ya gama yin sanyi. Kaddarar yaran nasu ce take taba su har kasan zukatansu, bude baki Hindu tayi zata roke shi daya tashi daga tsugunnan da yayi a gabanta, ya daina zubar mata da hawaye karya sa zuciyarta ta karaya, kar ya yaudareta kamar yanda ya saba, wani irin ciwo daya tsirga mata har ranta tayi zaton kashin bayanta ne ya karye "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un.... Baba bayana... Bayana ya karye Baba..." Hindu ta furta cike da wani irin rauni da yasa Anna da tafi kusa da ita kamata, saboda ta kula da abinda yake bin kafafuwan Hindun, tasan naquda ce ta taho mata gabaki daya, ita da Anty suka kamata, banda salati babu abinda yake fita daga bakinta har suka samu suka karasa mota. Anna ce take tambayar Hamza asibitin da Hindu take zuwa, kafin su duka su dunguma zuwa asibitin. 9/19/20, 8:05 AM - mmn khalid: 30 BAYAN AWA GOMA Ya sha kwana zaune, amman wannan ne awanni goma mafi tsayi a rayuwar shi, har Baba da yasan haushin shi yake ji sai da yai mishi magana ya zauna. Tunda duk a asibitin suka kwana, amman yaki, so yake kawai a fito musu da wani labari koya yane, shi baima san mata suna dadewa haka basu haihu ba. Da ba a jam'i yai sallar asuba ba, tabbas da ba zaisan abinda yake karantawa ba. Ruwa ma Anna ce ta bashi ya samu ya kurba yana jiqa makoshin shi. Tunda daddaren Anna da kanta ta koma gida cikin kayan babies din da aka siya ta tattaro duk wani abu da take tunanin za'a bukata ta dawo. Amman ba'a sanar da su ta haihu ba sai karfe bakwai na safe, duk wasu maganganu da ake fadi Hamza bayajin su, kalaman farko kunnuwan shi suka tsinta suka koma suna rufewa ruf "Ta samu 'yan biyu duk mata..." Ba dan baisan yara biyu bane ba, baima san kafafuwan shi sun gaji da tsayuwa ba sai da yaji suna rawa, babu shiri yabi bango yana samun waje ya zauna, numfashi yake fitarwa kamar wanda yayi gudu, ranar da aka fada musu yara biyune ita kadai taje asibitin, tun a hanya take kiran shi in yana kusa su hadu a gida, ba zai manta yanda ta kama hannun shi ta dora cikinta ba "Yara biyu, yara biyune a cikina" Tun da ta samu cikin ranar ne karo na farko da yaji kaunar koma meye a ciki har bayan zuciyar shi, ranar ne yaji kamar yana bangare daya da wani abu mai matuqar muhimmanci "Zamu basu mamaki..." Ya furta da murmushi a fuskar shi "Sai kowa yazo da tunanin yaro daya zasu ga biyu" Kai take daga mishi, sai yanzun yake jin ashe ya adana sautin dariyarta a wani bangare na zuciyar shi. Ya adana abubuwa da yawa a tare da ita, abubuwan da yake kula da su yau da kullum, yanda take zagaya hannuwanta kan cikinshi ta dora fuskarta a bayan shi tana rungume shi duk idan tayi tunanin bai hakura da rigimar da sukayi ba, ko da shine da laifi "Fushi kake har yanzun? Ni na hakura kaine za kai mun fushi" Takan fadi, abubuwa da yawane suka dawo mishi, sosai yayi nisa cikin tunani, dan sai da yaji an taba mishi kafada tukunna ya daga kai yana kallon Anna "Zaka iya zuwa kagan su" Ta fadi farin ciki shimfide a fuskarta, ga yaran Ma shaa Allah, so take ta tafi gida yanzun, tunda hankalinta ya kwanta. Ta watsa ruwa, su sa suke tunanin yaro ko yarinya guda daya saiga biyu. Siyayyar kaya bata kare ba, harta gama tsara yanda jikokin nata zasu ga gatan da basu taba tunani ba. Kai ya daga ma Anna yana mikewa da kyar, dakin ne yake juya mishi, ji yake kamar yana yawo akan gajimare. Dakyar ya iya shiga dakin da Anna ta nuna mishi yanajin tana fadin "Hindun tana hutawa saboda ta sha wahala sosai, amman zaka iya ganin yaran su..." Ko kai bai iya daga mata ba, ya tura hannun shi yana shiga cikin dakin. Karo yaci da wata Nurse daya dan daga ma kai, muryar shi dauke da wani yanayi yace "Ina yaran?" Gaba tayi yana binta a baya, yanzun kam jin shi yake yana yawo akan gajimare, jin shi yake kamar a cikin mafarki. Bai sake jin yana wata duniya ta daban ba sai da Nurse din ta dauko yarinya daya tana sakawa a hannun shi, dokawa zuciyar shi takeyi kamar zata fito waje, ya kasa kallon fuskarta saboda yanda zuciyar shi take mishi rawa. Gyara yarinyar da yake ji tana hannun shi batare da yaji nauyinta ba yayi, yana dan gyara dayan hannun shi ana saka mishi dayar, bai iya kallon su ba sai da yaji fitar Nurse din daga dakin. Da wani irin bugun zuciya ya sauke idanuwan shi akan hannun shi na dama, bacci takeyi. Kiran sallah yayi mata cikin kunnanta, yana juyawa yayi ma dayar yarinyar ma. Kafin ya sake mayar da hankalin shi kan yarinyar da idanuwan ta suke a bude. A duniyar shi kaf ya dauka bayan Anna ba zai sake dora idanuwan shi kan macen da zaiji kaunarta har cikin bargon shi ba, macen da zaiji yana so ya kare daga duk wani abu naqi da Allah ya saka a karkashin ikon shi. Sai ga mata biyu a hannun shi, mata biyu da in yana da iko ko sauro ba zai kusanto inda suke da sunan cutarwa ba. Mutane da yawa sun dauka hawaye shine karshen karayar zuciya, akan yaran da suke hannun shi idan idanuwan duka ake bukatar gani a kasa zai ciro su ya ajiye. "Suhana..." Ya furta daga wani lungu na zuciyar shi yana kallon yarinyar da idanuwanta suke a bude kamar tasan abinda yake faruwa. Fassarar sunan ta shine "Kyakkyawa". Shine kuma suna na farko da yazo cikin kanshi daya kalleta, watakila dan jinin shi ce, dan ta fito daga wani bangare na jikin shi, ko da bata da kyau zuciyar shi ba zata taba yardar mishi da hakan ba. Dakyar ya iya dauke idanuwan shi daga kan Suhana yana kallon dayar yarinyar da take bacci. Akan ce jarirai basu da kama, amman yan biyun da akafi sani da identical a turance tun suna jarirai kamannin su iri dayane. Nashi yaran basu zo a wannan jinsin yan biyun ba, kowacce kamanninta daban yake. Kallon yarinyar da yakeyi ne yasan labarin nutsuwa yake ji, kwanciyar hankali na daya daga cikin abubuwan daya manta yanda ake jinsu, sai yanzun, bai taba cin karo da wata halitta mai nutsuwar yarinyar da tayi kwance luf a hannun shi tana bacci ba, a duniya yara sunfi kowacce halitta yarda, ko idanuwanta bata bude ba, ballantana tasan waya dauketa, ta bashi dukkan yardarta tun kafin tagan shi "Amna..." Sunan ya kubce daga labban shi, sau daya suka taba maganar sunayen yara da Hindu, tace mishi tunda sun zabi barin sanin jinsin yaran har sai sun haifesu, sunayen ma su bari a haihun, ba zai wahala ba. Yasan yayi sonkai daya zabar musu sunaye batare da yaji ko tana da wani zabi nata ba. "Daga yau, zuwa ranar karshe da nake da aron ta, ba zan taba yin abinda zai baku kunya ba, ba zakuyi dana sanin fitowa daga jikina ba" Ya furta a cikin zuciyar shi yana kallon yaran. Kafafuwan shi ciwo suke, amman bayaso ya zauna ya tashi Amna, bayaso ko motsi mai karfi yayi "Ke me yasa ba zakiyi bacci ba? Ko yunwa kike ji?" Yake maganar yana kallon Suhana da yasan karonta ne na farko da taji yaren fulatanci. Dariya yayi me sauti yana sake kallon su. Wani dan labule ne tsakanin inda yake tsaye da gadon da Hindu take a kwance, karasa takawa yayi yana shiga wajen, baisan ko idanuwanta biyu ba ko kuma takun tafiyar shine ya tashe ta, sai lokacin yayi dabara yana zama kan kujera "Hey..." Ya furta yana kallonta, amman idanuwanta ba a kanshi yake ba, yana kan yaran da yake hannun shi. Ta gansu, ta karbe su, dan an saka mata su a hannuwanta tun da sauran jini a jikin su, ta rike abubuwa da yawa masu daraja da hannuwan, amman sune na farko da taji har cikin tsokar jikinta. Bata kara fahimtar kaunar da take tsakaninta da Baba ba saida ta rungume su a kirjinta, sai take hasaso kalar kusancinta da Anty. Tana kara wata daraja ta daban a idanuwanta, tana da tabbacin wannan matakine da mata suke takawa a rayuwar su duk ranar da suka rike nasu yaran a hannuwan su. Ranar zaka kara sanin darajata ta uwa, ranar da zaka fahimci dalilin da yasa take dora duk wani farin ciki naka a saman nata, yanda rayuwarta kacokan take tsayawa saboda taka ta cigaba. Kamar mahaifiya a duniya da zagayenta babu, duk yanda kake tunanin ka fahimci muhimmancinta ba zaka gane ba sai ranar da bayanka yai amsawar farko da ciwon naquda. "Na kasa yarda suna hannuna, yaran mu Hindu, muna da yara" Kai ta iya daga mishi saboda idanuwanta da taji sun cika taf da hawaye, dayan hannunta da babu karin ruwa, duk da akwai plaster a jiki ta dan mika mishi, tana saka shi yin danara ya mike ya taka har bakin gadon, sosai ya rankwafa yana mika mata yarinyar da take bacci har lokacin, tana nade tsaf cikin farin towel yanda ko kayan jikinta baka iya gani "Amna" Ya furta bayan ta karbi yarinyar, hakan yasa Honduras ware mishi idanuwa cike da son karin bayani "Peace..." Ya fadi ma'anar sunan da harshen turanci, dan ya tsaya a tsakanin nutsuwa da kwanciyar hankali, ya rasa asalin ma'anar da yaren Hausar da har yanzun mutane da yawa suke rainata a bakin shi. Har a ranshi ma baiyi niyyar musu magana da wannan yaren ba, Idan Anna taji zatayi kishin yanda ya yanke hukunci yi musu fulatanci. Idan suna da rabon jin nata yaren duk in suna tare da ita zasu tsinta. A bakin shi kuwa da yaren Appa zasu tashi, da jinin fulanin da yakeji har a kasan zuciyar shi Rike yarinyar Hindu tayi tana lumshe idanuwanta, kaunarta na ratsa duk wani lungu da sako na ruhinta. Kujerar Hamza ya janyo sosai yana zama. Hannunta da yagani a kumbure ya mika nashi ya kama, tana janyewa da sauri kamar wanda yake shirin goga mata wani abin, a cikin idanuwanta yake fara ganin abinda yasa zuciyar shi mummunar bugawa, kafin kwakwalwar shi ta fara fahimtar da shi kuskure na biyu mafi girma da yayi bayan na korar ta, shine kin furta kalaman ya dawo da ita kafin ta haihu, ganin ya fahimci hannunta da ta janye yasa ta jinjina mishi kai tana tabbatar mishi da gaske ita ba halalin shi bace yanzun "Zan ma Appa magana, sai a sake daura mana aure, muna da igiya daya a tsakanin mu..." Yake fadi cikin tsantsar tashin hankali, musamman da tun da ya bude bakin shi take girgiza mishi kai, hawaye da yake cikin idanuwanta yana zubowa "Auren mu ya rigada ya kare..." Wannan karin shine yake girgiza mata kai, idan kukan take so yayi shima zaiyi, zaiyi komai dan karta rabashi da kanta "Ya kare Hamza... Ya kare..." Kan dai yake girgiza mata "Ki kalle su, karki raba musu iyaye daga zuwan su" Ko tana da hannun share hawayenta ma ba zatayi ba, tunda basu daina zubowa ba, naquda takeyi da tabbacin ba zata taba komawa auren Hamza ba, Allah ta roka ya bata shi, tana naquda take rokon ya musanya mata da mafi alkhairi idan har Ya kadarta mata sake wani zaman auren, zatayi, zata sake daga farko batare da maimaita kuskuren da tayi a baya ba. Yara da yawa sun tashi batare da iyaye ba, wasu ma mutuwa ce gabaki daya ta rabasu. Tun kafin ta haihu take fadin yanda yara ba zasu taba zama dalilin da zata zauna a auren da batayi niyya ba. Har Mama ca tayi bata da hankaline da taji hirar, bata dandana zafin naquda ba. Yanzun ba naquda ba, ga yarinyarta nan a hannunta, ga dayar nan a hannun Babanta, amman ba zata taba koma mishi ba "Na miki alkawari na saba, nasani, zan canza saboda su, karkiyi tunanin zan kalli yarana inyi musu karya, wallahi zan canza Hindu, karki rabani da ke, kiyimun kowanne hukunci banda wannan..." Kai ta sake girgiza mishi tana saka shi jin wani abu ya bude a zuciyar shi. Mikewa yayi, yana mika mata Suhana da tayi bacci a jikin shi yana juyawa. Idan abinda yakeji kuka ne zai balle da shi ba zaiyi a gaban yaran shi ba, ba zasu fara ganin raunin shi kafin suyi girman fahimtar karfin zuciyar shi ba. Ko daya kama hannun kofar ya bude yana fita, janta yayi a hankali, batare daya kalli inda yake tunanin su Appa suna tsaye ba ya taka yana nufar hanyar da zata fitar da shi daga asibitin. Ko babur ne zai hau zuwa gida, idan yaje ya nemi kudin da zai bashi, sam baima ji Abid da yake kwala mishi kira ba sai da yasha gaban shi "Abid ka kaini gidan Fodio" Ya furta, Abid din na daga mishi kai, suka karasa wajen motar shi, ya bude ya shiga ya zauna yana jan murfin. Har Abid ya zagaya ya shiga baima sani ba, dan ya nutsu yana jin yanda ba tsaga daya zuciyar shi takeyi ba, wajaje ne daban-daban yake budewa yana sanar dashi ba iya kirjin shi ciwon zai tsaya ba. * Babu kowa a gidan sai Fodio, yana zaune kan kujera a falo da Mug a hannun shi da Hamza baisan ko meye a ciki ba. Sallamar Hamzan ya amsa da wani irin sanyi murya. Shima baice mishi komai ba ya wuce daya daga cikin dakunan baccin gidan zuwa bandaki. Wanka ya fara yi yanajin kamar an sake mishi fatar jikin shi saboda iskar da yake ji tana shigar shi ta ko ina. Sai da ya fito ne ya kula da dakin Fodio ne, cikin kayan shi ya sami riga da wando, yasan su duka basa rabuwa da sabon kayan ciki ko dan abokai baqi, ko bukatar hakan ta taso a tsakanin su. Har turare ya samu ya dan fesa, sai da ya dafe kirjin shi saboda ciwon da yaji yana mishi. Sannan ya samu ya fito yana dawowa falon. Waje ya samu ya zauna. Sai yanzun ya kalli Fodio da idanuwan shi sukayi zuru-zuru, abinka da mai hasken fata, kamar jini ne kwance kasan idanuwan shi da yake nuna alamar rashin wadataccen bacci, duk abinda Hamza yake ji bai hana shi fadin "Fodio lafiyar ka kuwa? Kaga yanda ka rame?" Kallon shi Fodio yayi "Me kayi?" Ya tambaya a madadin amsa tambayar da yayi mishi "AbdulHafiz bai fada mana ba, yace ba hurumin shi bane ba, in kana so muji zaka fada mana da kanka. Me kayi Hamza?" Numfashi Hamza yaja yana gyara zaman shi cikin kujerar, da wani irin yanayi a fuskar shi yace "Kuskure, Fodio kuskure nayi" Dan daga mishi kafadu Fodio yayi "Rayuwar mu cike take da tarin kuskure Hamza" Da sauri Hamzan ya kalle shi "Ba za kai mun fada ba?" Kai Fodio ya girgiza mishi "Zan maimaita maka abinda kasani ne, kayi kuskure, baka kyauta ba...duk kasan wannan Hamza" Fuskar shi Hamza ya saka a cikin hannuwan shi yana jin duniyar tayi mishi tsaye waje daya "Kana da sa'a daya, in dai zaka tsarkake zuciyar ka, idan zaka roki Allah da dukkan zuciyar ka zai yafe maka" Bude fuskar shi Hamza yayi, Fodio na jinjina mishi kai "Haka AbdulHafiz yace mun, tunda raina bai zo wuyana kafin in gane kuskuren da nayi ba ina da sauran rabo. Kasan AbdulHafiz, ya jamun ayoyi da Hadisai yana kara kashe mun zuciya" Murmushi Hamza yayi mai sauti, badan ya samu saukin abinda yake ji ba, sai dan AbdulHafiz ne, kaunar shi a wajen su mai girma ce, shisa yake jin abinda AbdulHafiz din yayi mishi har kasan zuci, shi kan shi Fodio din da murmushin a fuskar shi "Hindu ta haihu" Hamza ya furta muryar shi can kasan makoshi, wannan karin murmushin da Fodio yayi har cikin idanuwan shi ya kai "Kace mun ba wasa kake mun ba" Hamzan kan shi baisan murmushi ya kwace mishi ba, murmushi tun daga zuciyar shi "Amna da Suhana..." Yatsun shi biyu Fodio ya daga ma Hamza da ya jinjina mishi kai yana murmushi "Congratulations Man... Allah ya raya mana su" Abinda bai taba faruwa da Hamza ba yaji yanzun, yanayi ne daya dauka bakowa Allah yake halitta da shi ba, kunya, kunyar ma ta Fodio "Amin" Ya amsa da wani yanayi da yasa Fodio kwashewa da dariya, har ran shi ya dauka zai jima wani abu bai saka shi nishadi ba, amman daya daga cikin kyautar da Allah yayi wa dan Adam ita ce mantuwa "Kunya ta kake ji yau?" Hararar shi Hamza yayi, zai magana kenan wayar Fodio da ta hau ruri ta hana shi. Dagawa Fodio din yayi, kwata-kwata Hamza bai gane kan maganar ba tunda bayajin me ake fada daga dayan bangaren "Dan Allah daga nan zuwa gobe ku nemomun duk kauyukan da akace suna cikin wahalar neman ruwa, ko guda nawa aka samu kuyi mun magana ina jira" Shine ma dan abinda ya fahimta a maganganun Fodio, kafin ya sauke wayar daga kunnen shi. Ganin yanda Hamza yake kallon shi yasa yanayin daya gani cikin idanuwan shi tun zaman shi ya dawo, kamar maganar da yake shirin yi na da ciwo tun kafin ya fito da ita "Ina son gina iya rijiyoyin da nake da hali a madadin Ashir...banda wani abu da zan mishi, Hamza ban da shi" Fodio ya karasa maganar muryar shi na karyewa, cikin idanuwa Hamza ya kalle shi "Idan ka gina rijiya ko da daya a madadin Ashir, ina da tabbacin da zai dawo duniya ko na rana daya zai nemoka, zai fada maka yanda kake daya daga cikin masu kaunar shi da bai tabbatar ba sai da ya rasu" Kai Fodio yake girgiza ma Hamza, yanajin idanuwan shi na cikowa da hawaye "A wajen na bar shi, a wajen, Hamza ko gawar shi ban tsaya an dauke ba, wacce irin kauna ce wannan?" Numfashi Hamza ya sauke, shima yana bukatar lallashin nan, ba Fodio bane kawai cikin yanayi "Ban sani ba....ban sani ba Fodio...." Cewar Hamza a gajiye, yana dorawa da "Kawai nasan ina fatan in rigaka mutuwa, abinda ban tabayi ba, saboda ina so in samu abinda Ashir yake shirin samu yanzun... Zunubaina masu yawa ne" Shiru ya biyo bayan maganar Hamzan, ba dan basu da sauran abin fadi ba, sai dan su duka kowa da tunanin da yakeyi, wayar Fodio din ce ta sake yin ruri, wannan karin daya duba mikawa Hamza yayi ganin Mansy ce, ajiyar zuciya ya sauke yana karbar wayar hadi da daga kiran ya kara a kunnen shi "Hello..." Ya furta, jin muryar shi na sa Mansy fadin "Alhamdulillah, ina kaje? Inata kiran wayarka a kashe, na maka text yafi a kirga baka karanta ba ma, lafiya dai ko?" Numfashi Hamza yaja yana fitarwa a hankali "Lafiya kalau..." Yana jin itama ta sauke numfashi "Motar ka zan kawo maka daman, ina kofar gidan Fodio, ko ina zan kai maka?" Mikewa Hamza yayi "Ki shigo ciki" Jin ta danyi shiru yasa shi sake fadin "Ni nace ki shigo..." Sannan ya kashe wayar yana mikawa Fodio daya karba ya ajiye a gefe shima yana mikewa, kitchen ya nufa dan ya ajiye mug din da yake hannun shi. Hamza kuma ya fita daga gidan. Mansy harta shigo da motar ciki, ta bude ta fito. Ganin shi yasa ta karasowa tana samun shi. Sai dai yanayin fuskar shi ya tsorata ta, sosai yanayin fuskar shi yasa zuciyarta dokawa, hannu ya mika mata tana saka mishi mukullin a ciki "Yau ne rana ta karshe da wani abu zai hadamu Mansy, zaki tafi, zaki goge lambata, zaki gogeni a duk wani shafi na sada zumunta da kike dani, kamar yanda zanyi dana dauki wayar ta...." Cikin bayanannen tashin hankali da firgici take kallon Hamza "Ina da yara Mansy, ina da yara har guda biyu yau da safen nan. Ba zan koma baya in goge rayuwar da nayi ba, bama ni da tabbacin laifukana ba zai taba su ba..." Hamza yake fadi wani irin tsoro na shigar shi "Me kake ce mun? Ta ina kake so in fara? Ni bance zaka aureni ba tuntuni, ka fadamun da bakinka ba zaka aureni ba. Bance kai ka fara bata ni ba, amman kana da hannu a ciki..." Mansy tayi maganar hawayenta na zuba, itama tsoron ne bayyane a fuskarta, firgicin inda zata fara daga nan, badan Hamzan ne kawai namijin da ta taba bi ba, ba kuma dan shi kadai ne take tare da shi ba. Duk da ya sha fada mata yanda ba zai taba aurenta ba, ta kuma dauka har zuciyarta ta yarda da hakan, sai yanzun, sai yanzun da yake tabbatar mata rabuwa da shi take jin akwai bangaren zuciyar ta da yake ganin kamar Hamza zai kasance a rayuwar ta har karshe "Ina da laifuka da yawa na yarda, amman ba zan bari ki doramun na bacinki ba Mansy, ba zaki karamun da wannan ba, babu abinda ya faru a tsakanin mu da babu amincewar ki, zamu raba laifin ne dai-dai..." Hamza ya fadi yana dorawa da "Wa'azi ya kamata in miki, amman banda wannan kalaman, laifukana ba zasu barni ba. Karki sake nemana, idan har akwai wani bangare na zuciyar ki da ya taba mutunta abotar mu zaki bar rayuwata" Hannu tasa tana goge fuskarta "Nagode, nagode da komai" Ta karasa muryarta a karye tana juyawa, shine namiji na farko a rayuwar ta da ya taba kokarin kareta batare da alhakin hakan ya rataya a wuyan shi ba, namiji kwara daya da tasan zata kira a kowanne lokaci ya taimaka mata idan bukatar hakan ta taso, namiji na farko da ta jingina kanta da shi batare daya tureta ba. Ko bata ba Hamza jikinta ba a idanuwanta taga yanda zai taimaka mata idan da ta roke shi. Shisa yanzun rabuwa da shi yake jijjiga rayuwarta. Sai dai da gaske akwai bangaren daya wuce zuciyar ta da zai cigaba da mutunta abokantar su har karshen rayuwarta. Zata bar shi, zata bar shi kamar yanda ya roketa, duk da batasan inda rayuwa zata kaita daga nan din ba, zata bar shi. * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/19/20, 9:46 AM - mmn khalid: 31 Ba kirga kwanaki yakeyi ba yanzun, saboda wani irin tsayi da suke mishi wajen wucewa. Rayuwar ma gabaki daya bayajin dadinta, saboda cikin watanni ukun nan ta kowacce fuska rayuwar ta hade mishi waje daya. Su Anna basuce suna fushi da shi kai tsaye ba, amman bayan gaisuwa babu wata magana mai tsayi da take hada su, bai samu fuska har a wajen Appa da zai roki su sake zuwar mishi wajen Hindu ba. Hatta AbdulHafiz har yanzun bai huce da shi ba, ko yayi kokarin fada mishi damuwar shi baya saurare, satin daya wuce ma kai tsaye AbdulHafiz din yace "Ka daina wahalar da mu biyun Hamza, kaga abotar nan mun gwada a baya batayi wani amfani ba, tunda ko shawara ce na baka banda kimar da zaka dauka.....shisa na daina maka shishshigi a lamurranka, kai dai muci gaba da maganar aiki ana gaisuwar mutunci zaifi" Shisa ya kyale su, ya barma Allah lamurran shi. AbdulHafiz ne yake sa ran zaije ya taya shi bama su Anna hakuri daman, shima kuma ta bangaren shi babu wani sauki. Gidan Fodio din ma da yakan kwana yabari, tunda in dai ba yana falo zasu fita shi da Arafat ba sai dai ya fito yaga basa nan. Ko abinci suka siyo basa tahowa da shi "Mantawa nake ka saki Hindu... Sai ina dauka kana da aure har yanzun zaka koma gida kaci abinci" Arafat yace mishi ranar karshe da yai magana sunyo take away basu taho da shi ba. Abin yayi mishi ciwo ba kadan ba, a fuskar shi suke sake goga mishi laifin da ya riga daya karbi yayi, kuma gani yake duk AbdulHafiz ne ya zuga su suke mishi wannan abubuwan. Wai a ciki harda Abdallah ma, jiya da yazo wajen aiki a makare yake tsokanar shi magana ya danqata mishi "Ba zaka gane dalili ba, wanda ya rike auren shi da kyau ne kawai zaifi fahimtar dalilin makarata" Komai ya hade mishi waje daya, babu wanda yake kokarin fahimtar shi, kafar sada zumunta ta WhatsApp kawai yakan hau, shima idan ya roki Hindu yana son ganin yaran shi da zai rantse duk ganin da zai musu a kullum kara girma sukeyi, sai ta turo mishi hotunan su, duk maganar da zaiyi bayan hoton ba zata taba amsa shi ba. Ko kiranta yayi maganar su bata wuce ta wasu dakika, da yaji lafiyar su Suhana take kashewa, har mamaki yake. Hindu da aiki idan ya fita a tsayin rana bai kirata ba sai tayi mita "Idan baka so kaji muryata, ni ai ina so inji taka" Amman yanzun kamar bataso ma take amsa wayar shi, text baisan adadin wanda ya tura mata naban hakuri ba, bayajin ya taba bada hakuri a rayuwar shi mai yawan wanda ya ba Hindu, amsa daya ya samu a tsayin watannin nan "Na fada maka komai ya wuce, wallahi komai ya wuce har raina" Amman kuma taqi amsa tayin auren shi da yake sake yi mata. Idan gidansu yaje dan yaga yaran shi, Asma take bama su ta kawo mishi, harya gama zaman da zaiyi ba zata taba fitowa ba. Idan ma daukar su yayi ya kaiwa Anna, harya dawo dasu sai dai tasa aje a amso su. Ita kanta Anna yafi ganin fara'arta yanzun duk idan ya kai mata su Amna. Yau ma yana zaune a Office shi kadai, daga inda yake yana jin hayaniyar hirar su Fodio, zuciyar shi ciwo takeyi, duk yayi zuru-zuru ya fita hayyacin shi. Wayar shi da take ajiye akan tebir ta fara ruri, jikin shi har kyarma yake wajen dauka da yaga Hindu ce "Hello" Ya furta kafin ta amsa yana dorawa da "Ya kuke?" Yanajin kukan da baisan na waye ba "Amna ce take kuka ko Suhana?" A gajiye Hindu tace "Waka sani rigimammiya?" Murmushi yayi "Suhana..." Dan jim Hindu tayi "Mama da Anty zasu fita yau ana wani suna haka. Ni yanzun ina makaranta, ina da test amman bansan ya zanyi ba" Hindu take fada mishi, baima san ta koma makaranta ba, sam bata bashi labarin komai daya shafi rayuwarta yanzun. Motarta ya jima da kai mata abinta harda takardun, kuma yana jin dadi duk in yaje gidan yaga motar, bayan su Suhana yanzun bashi da wani abu nashi da yake tare da ita sai dai motar. Yana tura mata kudi saboda su, duk da kullum cikin siyayyar duk wani kaya da zasu burge shi yakeyi. Ya gwada sai mata sau daya tai wani irin warware shi, bai kara gwadawa ba. Yanzun tsoronta ma yake ji, tsoron yai wani abu da zai sake tunzutata taqi hakura ta dawo mishi yakeyi sosai. "Karki damu, bari inzo in dauke su" Yanajin numfashin da ta sauke "Nagode..." Kafin ta kashe wayar, mikewa yayi yana fita da sauri, kan shi tsaye ya nufi mota ya bude yana nufar hanyar da zata hada shi da makarantar su Hindun. * A bakin ajinsu ya hangota, takawa yake yana son tabbatar da abinda idanuwan shi suke hango mishi tun daga nesa. Rabon daya saka ta a idanuwan shi tun a asibiti. Watanni ukku cir bai ganta ba, tayi wani irin kyau, tayi jiki. Sai yake ganin kamar ya shekara ukune bai ganta ba, gashi tayi mishi wani irin kwarjini, banda jan jambaki babu wata kwalliya a fuskarta, sosai tayi mishi kyau cikin shigar abayarta kamar ko da yaushe. Sai wani da yake tunanin cikin yan ajin su na yanzun ne yana rike da Amna, ita kuma ta rike Suhana da take jijjigawa a hankali. Ko da ake ce mata raino abune mai wahala bata tabbatar ba sai da yazo kanta, raino harna yara biyu. Danma kowa a gidan yana tayata hidimar su, shisa take samun sauki, Suhana ce take da wata irin rigima, gashi inta fara kuka kome zakai ba zatayi shiru ba sai tayi niyyar hakan da kanta. Amna kuwa in ba yunwa take ji ba ko batajin dadin jikinta da wahalar gaske kaji kukanta. Amman Suhana ko wanka za'ayi har makota sai sun sani. Hannu Hamza ya mika yana karbar Suhana ya sabata a kafadar shi yana jijjigata, magana yake mata a hankali cikin harshen fulatanci yana shafa bayanta, kamar haka take jira kukan ta ya fara rissina. Cikin mintina kasa da biyar hartayi shiru, da alama bacci take shirin yi ma, kallon su Hindu takeyi, tana kallon yanda Hamza yakeyi da Suhana kamar raino na daya daga cikin abinda aka haife shi da iyawa. Suit ne a jikin shi mai guda uku, bai saka ta saman ba, daga ta cikin mai dogon hannu sai kuma yar jacket din saman. Dan murmushi tayi, da gaske takeyi ranar da tace mishi komai ya wuce mata, saboda a sujjada ta dinga zubar da hawayenta tana rokon Allah daya yaye mata dukkan damuwa. Yanzun kam hamdala kawai takeyi saboda yanda komai ya nutsar mata, ita ce yau take kallon Hamza, gashi a gabanta amman kyawun shi bai mata wani abu ba, asalima salaf take jin zuciyarta a kan shi. Sai takejin kamar ba kalar kaunar da ake fadi taiwa Hamza ba, kamar dai-daito da yayi da kalar mijin burinta ne abinda ta so a tattare dashi ba komai ba, yanzun kuma da ya bude mata idanuwanta sai take kallon shi a shi kadai, take kallon shi babu tarin dukiyar nan, babu izza da kyawun shi. Hamza take kallo, Hamza da yai wasan cikar shekara da auren su, Hamza daya shigo mata a buge a darenta na farko. Hamza take kallo daya sa kirjinta daukar zafi kamar ana hura wuta a cikin shi, sosai yanzun idanuwanta suke a bude tana ganin Hamza da yasa ta kuka kamar ba zata daina ba. Sai takejin kamar ba watanni uku bane da rabuwar su saboda inda take hango shi da matukar nisa a rayuwarta. Shi din bakomai bane a wajenta yanzun sai Baban su Suhana, ko dazun da zata fito da Mama take mata maganar yanda zatayi da su Suhana, ko za'a dauko mata yar aikine da zasu dinga zuwa makaranta da ita tana tayata raino idan basa nan, kai ta girgiza ma Anty "Zan kira Baban su yazo ya karbe su, shima ya dana yaji" Ko abu ya kawo sai take tsintar kanta da fadin "Baban su Suhana ne ya kawo" Ya tashi daga Hamza a idanuwanta, saboda idan ta kira shi da hakan zai zamana akwai wani kusanci a tsakanin su da yake ita da shi kadai, amman idan tace Baban su Suhana, kusancin zai biyo ta kan yaran ne tukunna ya hadata dashi. Hakan kuma yayi mata har a zuciyarta. Bata bukatar wata mai raino, courses biyune ta ajiye daman ko da ta dawo makaranta, saboda tana tsoron ga ciki, kamar ba zata iya ba. Tunda project dinma a lokacin kaf zanen Hamza ne yayi mata su, har aka kusan kamata wajen kare kanta, danma yasa tayi rubutun da kanta, kuma yayi mata bayani da yawa a kai, da bata haye ba, tsaf za'a gane ba ita tayi ba. "Muje sai in baka kayan su, suna mota" Ta furta tana mika hannunta ta karbi Amna "Nagode Faruk" Ta furta tana yin gaba, Hamza ya bita a baya, har kasan zuciyar shi yake jin yanda ko arziqin gaisuwa bai samu ba wajen Hindu. Suna zuwa mota ta dauko jakar kayayyakin da tasan duk zasu bukata, har madarar su da sai sunga haza suke sha ta hada musu. Tasan yana da kujerun su a duka motocin shi, na tata motar ma shiya siyo ya kawo. Ta dai raka shi har mota ne ya zaunar da su "Idan Suhana tayi fitsari baka canza mata pampers ba kuka zatayi, bata son jin lema a jikinta ko kadan" Kai ya jinjina mata, yana kallon fuskarta, kewarta na danne shi, yanda take mishi bayani zakai tunanin ba zata sake ganin su Suhana bane ba, murmushi yakeyi "Hindu..." Ya kira a hankali "Amna bataso a kwantar da ita akan bayanta, zata farka..." Gyara tsayuwar shi yayi "Hindu..." Ya sake kira, sai lokacin ta kalle shi "I got this, I got them... Na 'yan awanni ne, ki yarda dani, zan iya" Kai ta jinjina mishi, yanayin fuskarta yana nuna mishi ko kadan bata yarda zai iya kula da su ba, kuma haka dinne, duk da tun suna jarirai suna awa har biyu tare da shi, wani lokacin fiye da haka. Kewar yaranta takeyi tun kafin subar wajen, ko a gida wani ya karbe su, alkunya kawai take, dan ji takeyi inba ita ba babu wanda yake fahimtar abinda suke so, babu wanda zai kula dasu kamar yanda ita din zata kula da su. "Dana fito zan kira ka, in suna kuka ka kirani dan Allah, kaji" Kai ya daga mata "Ayi test lafiya. Allah ya bada sa'a" Kallon shi takeyi kamar zai tafi da wani bangare na zuciyarta. Harya shiga mota yana kallon tana kokarin leqa su Suhana duk da tinted ne gabaki daya gilasan shi. Kai kawai ya girgiza yana dariya, da har yanzun tana karkashin ikon shi, da test din yau an hakura da shi, zai jata su shiga mota su tafi gida, saboda yasan da wahala ta sami nutsuwa harta iya rubuta wani abin kirki. Yana hanya ne yaga kiran Fodio, bai daga ba sai da ya sauka daga titi yai parking, ba zai amsa waya yana tuqi da su Suhana a motar ba "Ina kaje?" Fodio ya tambaya "Hindu na da test a makaranta, shine naje na karbo su Suhana..." Baima karasa maganar ba Fodio ya katse shi da fadin "Ka zo dasu gidana dan Allah, mu ma can zamu tafi yanzun" Numfashi Hamza ya sauke yana daga girar shi "Me yasa? Ni gida zan wuce" Shi suke shama kamshi, duk da yasan su duka suna zuwa ganin yaran, lokutta da dama sai sun dawo su fada mishi, ko Hindu ta dauki hotin abinda suka kai mata ta tura mishi ma yake sanin sunje din. Rayuwa ta hada shi da abokan da mutane da yawa suke addu'ar samu "Bana so inyi zagi saboda kana tare da su Suhana, dan Allah ka kawo mana su, kaji" Dariya kawai Hamza yayi yana kashe wayar. Gidan Fodio din ya nufa kan shi tsaye, sun ma riga shi karasawa, saboda sunfi shi kusa da gidan daga Office, tunda yai parking, yana budewa ya fito yaga Fodio harya bude murfin motar yana rankwafawa ya kwance Amna daga cikin kujerarta ya dauketa, sai yaga kamar ta kara kiba, kumatunta kawai na saka dariya kwace mishi, tafi Suhana haske, yanda yaran suke kama da Hindu suna kuma kama da Hamza batare da sunyi kama da junan su ba yana matuqar bashi mamaki. Hamza kuwa Suhana ya dauka, yana juyawa AbdulHafiz na miko hannu ya karbeta, da Nabila batayi bari ba da yanzun yana rike da nashi shima, amman haka Allah ya tsara, komai na da lokaci. Su Amna dinma jin su yake kamar daga jikin shi suka fito. Wani abu Suhana tayi da baki "Allah karkiyi mun rashin kirki Suhana, ke kullum sai munyi fada ne?" AbdulHafiz ya karasa yana dangwale mata hanci, sake kwabe fuska tayi "Ko kinyi kuka ba ajiye ki zanyi ba...." Yai maganar yana gyara mata zama a kafadar shi, tare suka shiga gidan su duka. Kan su bai dauki caji ba sai da yaran biyu suka kaure da kuka. Su hudun sun rasa yanda zasuyi da su, musamman Suhana da ko fida taqi kamawa. Hakan yasa Hamza fadin "Ko Pampers take so a sake mata" Wani tsalle Fodio yayi yana komawa gefe "Ku cireni a lissafin nan" Ya fadi, yana son su Amna, amman ba zai taba kashin yara ba. Shi a nashi tsarin rayuwar ma sam bai hango yara ba har yanzun, aure ne abinda ya fara sakawa a ciki yanzun, shima ya kasa furtawa a fili wani yaji saboda tsoron da yake ji, amman ya san yana bukatar mace ko dan karya komawa neman su ta hanyar da bai kamata ba. Amman yara kuwa yana da sauran tafiya a gaba kafin ya fara hasaso rayuwa da su "Bari kuga Husband material, yadi goma, riga harda yar ciki" Arafat ya fadi yana fara kokarin cirewa Suhana skirt din da yake jikinta. Su duka tsayawa sukayi suna kallon ikon Allah, batama bata pampers din ba, rigima ce kawai da take ji, yana sabata a kafada kafin a miko mishi wani pampers din tana tsula mishi fitsari "Inalillahi... Suhana kinsan wanne kayane kikai wa fitsari? Kinsan dubu nawa kika fitsare?" Ya fadi kamar zai fashe da kuka, dole Hamza ya karbeta suna mishi dariya. Sai da suka samu duka yaran biyu sukai bacci tukunna Hindu ta kira shi "Na fito yanzun" Kai yake girgiza mata "Wallahi ba yanzun zan dawo dasu ba, kinsan wahalar da muka sha kafin suyi bacci..." Yana jin tayi jim kafin ta kashe wayar, shima pillow ya dauka daga kan gadon yana kwanciya kasa, gefen katifun su Suhana da suke kwance a kai suna baccin su, kamar basu da wata damuwa a duniya. Idanuwa ya kafa musu yana kallon su har shima baccin ya dauke shi. * Links din hannuwan rigar shi ya dauko yana ajiye su akan gado, sannan ya dauki daya ya saka a hannun, yana daukar dayan ma. Cikin wani lokaci ya fito tsaf, cikin yadin shi ruwan madara. Da wahalar gaske ka kalle shi baka kara kallon shi ba. Kallo daya zakayi wa fuskar shi kaga kwanciyar hankalin da take shimfide, zuwa yanzun bayajin shi cikin kuncin da baisan dalilin shi ba, bayajin kirjin shi kamar an danne. Bai dauka zai iya shekara daya batare da mace ba. Azumin shi yake duk Alhamis da litinin yana rokon Allah daya kare mishi zuciyar shi. Da kan shi ya goge Twitter da Instagram. Baice zai daina gabaki daya ba, amman sai ya yadda da fin karfin zuciyar shi da yayi Sau biyu yana kusan komawa ruwa sanadin Instagram, na biyun hotunan su Suhana da Hindu ta turo mishine ya taimake shi, hotunan yagani yasa shi goge manhajojin biyu gabaki daya. Temptation bala'i ne, idan kana fama da kanka abu kalilan, abinda kake ganin bai kai ya kawo ba zai dawo maka da komai baya. Shisa ya goge, babu yarinyar da zata saka shi karya alkawarin daya daukar ma Ubangijin shi, alkawarin tuba sahihi, tuban da yake fatan ba zai koma ruwa ba, bazai karya alkawarin da yayiwa su Suhana na ganin basuyi dana sani kona rana daya daya kasance sun fito daga jikin shi ba. A hankali kwanaki suka tafiyar mishi suna juyewa watannin da suka cike shekara, a cikin wannan lokacin yaga kokarin da yayi ya samar mishi yafiyar su Anna, a cikin lokacin ne ya ajiye duk wata izza da yake ji ya roki AbdulHafiz ya yafe mishi dan yagaji da yanda yake mishi kamar bare, kamar basu da wata alaqa data wuce aiki. Shekara daya daya dauka yana bin Hindu kamar babu zuciya a kirjin shi kan ta sake bashi dama, amman tayi biris da shi, ita kanta harta kammala bautar kasarta. "Ni karatu zanci gaba, ba aure bane a gabana Hamza, na farkon da nayi kaine shaida akan yanda ya kare..." Shine abinda ta fada mishi, ya roki Anna tayiwa Appa magana a taya shi lallashin Hindu, tace mishi "Ba zan shiga maganar nan ba, ba zamuyi amfani da girman mu da yarinyar nan take gani mu tirsasata ba, ka lallabata da kanka, idan kuna da rabon sauran zama zata dawo. Amman kam kayi hakuri, ni da Appan ka mun yanke hukuncin ba zamu shiga zancen ku da Hindu ba" Maganar Anna ta kara kashe mishi jiki, duk da har a zuciyar shi yana son Hindu, yana azabtuwa da rashinta, musamman yanzun da yake ganin yanda ta kara kyau, ba a gane hankali ta fuska, tunda ba'a rubuce yake ba, amman zai iya rantsewa akwai hankalin da yake gani a fuskarta da baya gani a da. Duk da shima AbdulHafiz yace mishi su Suhana sun saka har kunyar mutane ya fara ji yanzun, duk da rikicin shi na banza yana nan babu inda yaje. Yanzun ma Fodio ne ya bashi karfin gwiwar sake tunkarar Hindu, ya dauka yagama ganin abin mamaki sai daren jiya da wayar Fodio na hannun shi yana duba design brief din wani abokin wasan Fodio din da yake son ayi mishi zane ya turo, kiran waya ya shigo. Sosai Hamza yake kallon wayar, ganin Mansy, mikawa Fodio wayar yayi, ba ya manta da ita bane ba, yakan tunata lokaci zuwa lokaci, amman tunani ne na inda rayuwa ta kaita, ba wani abu ba, har ranshi yana mata addu'ar shiriya, ta samu dalilinta kamar yanda ya samu nashi, sosai yake kallon Fodio da yanayin yanda yake wayar da Mansy "Tun yanzun zakiyi bacci kibar ni?" Yanayin yanda Fodio ya ajiye maganar nasa wani abu tsirgama Hamzan da bashi da alaka da kishi, sai tsantsar mamaki da tsoron da baisan dalilin shi ba, har Fodio ya sauke wayar daga kunnen shi Hamza na mishi kallon tuhuma "Karka tambayeni yaushe ya fara, nima ban sani ba" Fodio ya furta yana samun waje ya zauna. Suna dan hira da Mansy sama-sama lokacin da take tare da Hamza, ko in tazo wajen shi, ko idan ya raka shi wajenta. Abu daya yasani tun a lokacin, da badan yarinyar Hamza bace zai taya shima, sai dai su din basa hada nema ko da na banza ne. Ta kitchen din gidan shi ranar da ta dawoma da Hamza mota yaji duk maganganun su. Baisan me yasa ya kirata a ranar ba, yasan labarinta, yasan rashin iyaye har biyu na daya daga cikin tushen lalacewar ta, zai fahimci wannan bangaren fiye da kowa. Bai kirata ba sai karfe goma na dare a ranar, amman kuka takeyi har lokacin, ko muryarta bata fita sosai "Ina tunanin rayuwata Fodio...ina tunanin abubuwan da zasu faru da na tashi da iyayena duk da ba zai taba zama hujja a gareni ba" Har zuciyar shi yaji maganganunta, saiya tsinci kan shi da kiranta a kullum dan yaji lafiyarta. Sai ya sake tsintar kan shi da takawa har inda take dan ya dubata da idanuwan shi. Ya fahimci dalilin Mansy da yayi mata maganar tayi aure "Wa kake ganin zai aureni batare da bincike ba? Wa kake ganin iyayen shi zasu yarda ya aureni bayan sun san rayuwar da nayi? Sirri irin nawa baya boyuwa komin gyaran da akai mishi..." Shisa da yawan karuwai wa'azi baya shigar su, saboda in basuji ba sunga yan uwan su da tuba baiyiwa rana a duniya ba, duk da inda za'a tonosu a basu ikon magana zasu bada labarin yanda tuban ne zabi mafi alkhairi da sukayiwa rayuwar su, duk da mutanen da suke yawo da zunubai mabanbanta basu karbe su ba, ko da malamai suka zama akwai mutanen da zasu furta "Abin da a baya kowa yasan tsohuwar karuwa ce" Kamar zunuban su ba zasu yafu ba, suna manta yanda ba'a shiga tsakanin bawa da Ubangijin shi, suna manta yanda Rahma ta Ubangiji ce, wanda yaso a cikin bayin shi yake nufa da samunta. Shisa da yawa suke zabar zama inda suke tunda ko sun tuban baya wanke laifukan su na baya a idanuwan mutane. Akwai irin su Mansy da yawa, akwai iyaye da yawa da ba zasu taba barin yaransu su auri irin Mansy ba "Ba zaka hadamun zuri'a da karuwa ba" Sukan kafa hujja da zance irin wannan, sosai suke manta a cikin mummuna Allah yana fitar da me kyau, a cikin me kyau Allah yana fitar da mummuna, dan da yawa idan aka bincika asali, iyayen su mutanen kirkine, kaddara ce kawai basu tsallake ba. A ranar Fodio yasan idan aure zaiyi ba zai samu macen da yaji ta dace da rayuwar shi kamar Mansy ba. Bashi da wanda zai damu dayai bincike a kanta ballantana bayanta ya dami wani, indai tana da wakilan da nashi zasu samu da maganar aure shikenan. Yasan rayuwar shi ta baya ba zata hana shi samun macen kirki ya aura ba. "Ka san wacece Mansy, Fodio ka sani" Hamza ya fadi yana son karin tabbacin Fodio din yasan abinda yakeyi. Ya tuba shikam, shisa yake addu'ar Hindu ta dawo mishi, ya yarda da nagartarta, ba zai iya wahalar neman wata matar ba, ba zai iya duk wannan fargabar ba, dariya Fodio yayi da bata da alaka da nishadi "Da in auri macen da zata canza mun, gara in auri macen da zata canza mun" Kallon shi Hamza yayi, dan magana daya ce ya maimaita, kai Fodio ya jinjina mishi "Canji biyu nake magana, mata nawa ne zaka aure su a kintse sai bayan auren su canza maka? Canjin da sai kayi dana sanin auren, gara in auri Mansy da halayenta da zata canza mun, nasan dukan mu da zuciya daya zamuyi, Allah zai taimake mu ba zamu taba dana sanin auren juna ba" Yakinin da yake muryar Fodio shi ya taba zuciyar Hamza fiye da maganganun shi, dan ba fahimtar su yayi ba, har ranshi baiga dalilin da zaisa ya auri Mansy ana zaune lafiya ba. Allah ya shirye su duka ya hada kowa da rabon shi "Sai dai in kana da matsala da aurena da ita, matsala daban da bata shafi halayenta ba" Da sauri ya girgiza ma Fodio kai, daga ranar daya karbi mukullin motar shi ya yanke alaka da Mansy gabaki daya "Bani da wata matsala da Mansy" Numfashi Fodio ya sauke "Mansura, sunanta Mansura" Murmushi kawai Hamza yayi yana girgiza kai, sosai Fodio ya bashi karfin gwiwar sake tunkarar Hindu. Yau zasu gama maganar nan duk yanda take kauce mata, hular shi ya dora saman kan shi yana daukar mukullan mota ya sauko kasa yana ficewa daga gidan. *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/20/20, 1:04 PM - mmn khalid: 32 Wata irin mummunar dokawa zuciyar shi tayi ganin Hindu zaune akan kujerun da suka saba zama, a wajen da suka saba yin zance, amman bashi bane akan kujerar, wani ne zaune a inda ya saba zama, yana magana da Hindu, har tana mishi dariyar nan tata da yake ji a ko ina na jikin shi. Dakyar ya iya yin parking saboda ko gani bayayi sosai, yasan yana da kishi na fitar hankali, ba tun yanzun ba, akan ta yasan kishin shi ya wuce duk yanda kalamai zasu fassara, dan nan take zazzabi mai zafi ya saukar mishi, ko murfin motar bai rufe ba daya fita. Karasawa yayi inda suke yana addu'a kar ya nuna ma Hindu yanda akwai wasu daga cikin halayen shi da ba zasu taba canzuwa ba. Tsaye yayi a kansu yana mayar da numfashi kamar wanda ya sha gudu "Hindu waye wannan?" Ya bukata yana kare mishi kallo, kafin ya tsayar da idanuwan shi da suke cike da tsantsar rikici a cikin nata. Idan zata saurari wasu ma baiga dalilin da zata kula irin mutumin da yake zaunen nan ba, in ba kawai so take zuciyar shi ta buga ta tarwatse ba. Duk da a shekaru bayajin zai girmi mutumin, idan ma bai fi Hamzan ba to zasu zo daya. Numfashi Hindu ta sauke tana dauke idanuwanta daga cikin na shi "Bello ga Baban su Suhana" Ta fadi tana kallon mutumin da ta kira Bello, kafin ta kalli Hamza da fuskar shi har tayi wani ja saboda kishi tace "Hamza ga Bello, shine wanda zan aura" Bude baki yayi da nufin yin magana, yaji wani yawu ya sarqe shi, yana fara tari babu kakkautawa, sosai yake kokawa da numfashin shi, ko bai sarqe ba, maganganun Hindu barazana ne da rayuwar shi. Murmushi Bello yayi "Bari in barku kuyi magana. Zamuyi waya ko?" Kai Hindu ta jinjina mishi, kafin ya mike, Hamza da har lokacin tari yake ya samu dakyar yana furta "Kar... Karka kirata wallahi" Murmushin dai Bello ya sakeyi, Hamza na bin shi da wani irin mugun kallo harya karasa ya hau machine din shi da Samari sukafi yiwa laqabi da roba-roba yana ficewa daga gidan. A nutse Hindu take kallon Hamza da tarin shi ya tsagaita "Ka zauna..." Wani irin kallo yake binta da shi, tabbas ta sami tabin hankali idan tana tunanin zai dora mazaunan shi inda Bello ya tashi "Ba zan zauna ba, Hindu kasheni kike so kiyi? Bana baki hakuri ba? Ya kike so inyi? Titi kike so in bi ina taro mutane dan su tayani baki hakuri ko meye?" Ya karasa maganar idanuwan shi har sun sake launi saboda bacin rai. "Sau nawa zance maka na hakura? Sau nawa kake so in fada maka komai ya wuce a wajena?" Hindu ta fadi a gajiye, dan tagaji da shi, tagaji da nacin shi. Ba wai babu masu sonta bane ba, har mamakin yanda ake Mazan da suke mata tayin aure suke gane ita din bazawara ce takeyi wasu lokuttan, tunda shigarta sam bata nuna bata da aure ba. Amman sai taji zuciyarta na dokawa, a tare dasu take hango Hamza, wani lokaci har a yanayin tsayuwa, agogon da suke sanye da shi, tsadaddiyar mota ko wayoyi, sai take ganin kamar su din ma ba zasu banbanta da shi ta fannin halaye ba. Tana bautar kasa suka hadu da Bello, shima gida yazo wajen Baba, sai daga baya tasan likitan dabbobi ne, aikin da yake a karkashin Baba kamar abinda ake kira da side job ne a turance. Har sukayi musayar lamba tana mamakin kanta, tana jinjina cewar da hannunta ta dauki lamba ta bawa Bello, saboda takowanne fanni shi din ba kalar mijin da ta taba hangowa kanta saurare bane ba. Baya matsa mata da yawan zuwa, sai ta hada satika biyu ma bata gan shi ba. Tun maganar farko ya sanar mata yana da mata da yara har guda biyu. Kusan zata ce abinda ya fara burgeta da Bello shine kusancin da yake da shi da iyalan shi. Yanda baya gajiya da bata labarin Arifa da Khalid, tasan kalar abin, tasan irin farin cikin, dan itama duk wanda zai saurari labarin su Suhana idan zata wuni tana bayarwa abin fada baya qare mata. Soyayyar da kowanne yake yiwa yaran shi ta fara saka shakuwa a tsakanin su, kafin a hankali, cikin watanni shidda take fahimtar kyawawan halayen Bello, tana kuma mamakin yanda da duk rana yake samun waje a rayuwar ta. Bata san inda tafiyar su zata kai ba, Bello baya mata gaggawa, tasan niyyar shi, ya bata dukkan lokacin da take bukata dan ta yanke hukunci, kuma yana nuna mata ba zai riketa da laifi ba a kowanne irin decision ta yanke "Idan alakar mu bata wuce abokantaka ba haka Allah ya kadarta Hindu..." Ya fada mata da take ce mishi tana jin wani iri kar tazo bata aure shi ba, dan sam bata shiryama aure yanzun ba, tafi so ta yaye yaranta, duk da yanzun ma ba damuwa sukayi ba sosai, Suhana ce da fitinarta daman. Amman alamu sun nuna Amna zata yaye kanta ko bata cireta ba. Kuma akwai tarin abubuwan da take hangowa, bai fito ya fada mata ba, maganar bata hadasu kai tsaye ba, da dabara Bello yake nuna mata zai rike mata yaranta, abinda ko auren shi tayi ba zai taba yiwuwa ba. Su Baba ma ba zasu bari ba tasani, balle kuma Hamza da take da tabbacin za ai yakin duniya kafin yabar yaran shi suyi agolanci a gidan wani. Har ranta bawai ta raina samun Bello ba, amman ba zai iya rike su ba. Yanzun a tsorace take da halin maza, tabon guda daya take da shi, amman ya firgitata da sauran ma, alkawurran Bello iya kunnuwanta suke tsayawa, batama bari sun karasa zuciyarta ba ballantana yai disappointing dinta. Daga auren Hamza ta daina daga burinta akan komai na lamarin duniya, bata saka rai ba ballantana ya dameta idan bata samu ba, yaune karo na farko da ta furta shi zata aura, dan ta huta da nacin Hamza, amman zuciyar ta cike take da tsoron kalaman da tayi din "Idan kin hakura me yasa ba zamu koma auren mu ba? Me yasa ba zaki taimaka mun yaran mu su rayu tare da mu biyu ba? Ki kalli irin mazan da kike kulawa Hindu, da gaske baki hakura ba" Numfashi ta sauke mai nauyin gaske, ya katse mata tunanin da takeyi "Nace ka zauna kaqi" Kai ya girgiza mata "Ni bazan zauna inda ya tashi ba" Yai maganar kamannin shi da Suhana na fitowa sosai, duk da ba magana takeyi ba ita, amman abu da yawa zatayi da fuska sai Hindu taga kamar shine a gabanta, sai dai yanzun tana tunanin shi batare da komai ba, yana fado mata a rai bataji ciwo a kirjinta ba sam, da gaske komai ya wuce mata, tabon ne kadai shaidar da take da shi na abubuwan da suka faru. Mikewa tayi daga kan tata kujerar tana tura ma Hamza, taja wadda Bello ya tashi da nufin ta zauna, cikin zafin nama ya fisge kujerar daga hannunta "Saboda baki da hankali ke saiki zauna? Inda ya tashi? Inda wani kato da ba muharramin ki ba ya zauna kema zaki zauna?" Har ranta bataso dariya ta kubce mata ba, kawai ta taho ne batasan ya zatayi ta tsayar da ita ba, saboda dariya Hamzan ya bata sosai, zama yayi a kujerar yana kallon Hindu da take mishi dariya kamar akwai wani abin nishadi a maganar da yayi, kafin itama ta gyara kujerarta tana komawa ta zauna "Na zama mahaukaci ko? Duk hakan bai isheki ba, shisa kike magana da Bello" Yanda ya kara fadar Bellon ya sata yin murmushi, karfin halin shi ba zai daina bata mamaki ba, muryar shi ya saukar sosai saboda yanda kirjin shi yake zafi "Dan Allah karki kara kula shi, nace zan rike ki da kyau, ba zan sake ba. Wallahi rabona da wata mace tun ranar da kika bar gidana...Allah ne shaida ina duk kokarin da zan iya, kiyi hakuri dan Allah..." Kai take girgiza mishi saboda yanda ya saukar da murya sai taji wani irin tausayin shi ya cika mata zuciya "Idan baki duba halin da nake ciki ba, ki duba su Amna, nayiwa Anna magana tace ba zasu baki hakuri ba, tace sai dai in baki hakuri da kaina... Ni kuma kinqi ki saurare ni" Kirjin shi kamar ana hura wuta a ciki haka yake ji "Ba haka bane ba" Hindu ta fadi, bayason abinda yakeji a muryarta sam "Nace maka kom..." Kasa karasawa tayi ganin Hamza ya sauka daga kan kujerar da yake, bai damu da farin yadi bane a jikin shi ya saka gwiwoyin shi a kasa yana kallon ta da idanuwan shi da yake nuna mata alamar kuka zai iyayi kowanne lokaci "Inalillahi.... Hamza menene haka? Dan Allah ka tashi... Ka tashi kar wani ya fito" Cewar Hindu cikin tashin hankali, shekara daya da kusan rabi da suka wuce, Hamza a durkushe a gabanta yana bata hakuri abune da take mafarki, ido rufe harma a bude. Abune da zata so dauka ta dora a Instagram dan duniya taga kalar mijin da take aure, mijine da zai iya saka gwiwoyin shi a kasa ya bata hakuri, ba kamar mazaje yan gargajiya da girman kai zai yanasu ko da furta kalaman ne balle kuma har su tsugunna. Yanzun kuwa abin tsoro ya bata, ko kadan bai burgeta ba, saboda ji takeyi yana son amfani da duk wata hanya wajen tursasa zuciyarta ta koma auren shi, auren shi da yaki fahimtar ya gama fita daga kanta tas "Dan Allah ka tashi..." Ta fadi, amman kai Hamza ya girgiza mata, kome zai dauke shi, indai zata hakura zaiyi, idan ma ca tayi ya kwanta zai kwanta. Koma meye dan karta sake kula Bello, zuciyar shi ba zata iya dauka ba "Kice kin hakura, kice zaki bani wata damar Hindu, ko baki koma yanzun ba a sake daura auren mu, wallahi zan jiraki komin tsayin lokacin da zaki dauka har sai kin yarda da na canza, abune mai wahala a wajena, amman zan jure, zan jure komai banda rabani da ke..." Hamza yake fadi yana wani irin fitar da numfashi kamar zai shide mata "Ni me laifi ne, na yarda, dan Allah karkiyi mun wannan horon, karki horani ta hanyar rabani dake..." Hawayene cike da idanuwanta, ba zata jure ganin shi haka ba, wannan bashi bane Hamzan da ta sani "Ki sake bani dama, ba zanyi wasa da ita ba" Kai take girgiza mishi, hawayenta na zubowa, sunayi kamar sun wanke mishi cikin idanuwanta ne yana ganin abinda takeji tar a cikin su "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ya iya furtawa, kujerar daya sauka daga kai ya dafa yana mikewa dakyar ya koma ya zauna saboda nauyin da jikin shi yayi, da gaske zazzabi yakeyi, dan iskar yammaci liqis data kada shi yanzun har cikin ranshi yajita, tsikar jikin shi na mikewa "Hindu da gaske ba zaki koma ba? Da gaske kin daina so na?" Kai ta daga mishi a hankali, yanayin na fitowa daga zuciyarta, wasu hawayen da tayi saurin gogewa suna zubo mata, batajin komai a tare da shi sai tsoro, sai tsoron komawa a auren shi duk yanda alamu suke nuna mata ya canza "Dan Allah kice mun ban rasaki kenan ba..." Hamza ya fadi da nauyin da zuciyar shi tayi a muryar shi, yanajin kamar an watsa mishi ruwan kankara, idan ita soyayyar da tayi mishi zata iya bacewa shi yanzun yake jin tata, yanzun yake jin wani irin sonta kamar zai mutu idan tabar shi, kai ya jinjina "Ok... Kece kadai kika daina sona, ni ina son ki, zai ishe mu, zan zauna da ke ko bakya son wallahi, dan Allah ki zauna dani tunda ni ina son ki" Hawayen ta sake sharewa da gefen yatsunta "Hamza..." Ta kira muryarta na karyewa, tana so ya dawo hayyacin shi ya yarda da kaddarar su ko da ba haka zuciyar shi take so ba, amman kai yake girgiza mata, bayaso ya yarda ta subuce mishi kenan, bayaso tace ba zata koma ma auren shi ba, wa zata aura to? Hasaso ta da Bello kadai na barazana da bugun zuciyar shi, mutuwa zaiyi tabbas idan ta auri wani, idan ya zauna da sanin tana rayuwa da wani da bashi ba, da gaske mutuwa zaiyi, kishinta ne zai fara kashe shi in har zafin son da yake mata bai kashe shi ba yanzun "Zaki bani yara na, wallahi ba zaki tafar mun gidan wani da yara ba" Hamza ya fadi cike da neman rikici, so yake ya tsoratata ko zata hakura ta dawo mishi, tunda yasan yanda take son su Suhana kamar ranta, idan tasan ba dashi kadai zabinta zai rabata ba har su watakila ta dawo hayyacinta, tagane komama auren shine kawai zabin da ya fiye mata, muryarta a karye, wasu hawayen na sake zubo mata tace "Na sani, bance zanje ko ina da su ba daman" Cikin sabon tashin hankali Hamza yake kallonta, dan bayajin tana cikin hankalinta, abinda yayi mata yai muni har hakane da ta kasa yafe mishi "Ki aureni ki koreni cikin dare to, ki rama ko zaki hakura...." Mikewa tayi da dan murmushi duk da kukan da takeyi, saboda har an fara kiraye-kirayen sallar Magriba. Bai kirata ba, da idanuwa yake binta harta bace mishi, ta falon Mama tabi, sai da ta taka cikin falon sannan kafafuwanta suka zabi suki daukarta, dan a tsakiyar kitchen din ta zauna tana sakin wani irin gunjin kuka da ya fito tun daga ruhinta, batama san Mama tana cikin ba saida ta taji ta kamata, a jikin Mama ta kwanta tana kuka kamar ranta zai fita "Hindu me ya faru?" Mama take tambaya cikin tashin hankali, dakyar Hindu ta iya dago da kanta, tana saka hannuwanta tana goge fuskarta, dakyar take jan numfashi "Nasan zan bashi yaran shi, na sani Mama, tun ranar da nasan ba zan koma gidan shi ba nasani... Amman zuciyata ciwo take, zuciyata kamar zata fashe Mamaa..." Hindu ta karasa idanuwanta cike taf da hawaye "Oh Allah na..." Mama ta furta tausayin Hindun na cika mata zuciya, tana tausaya musu su duka "Da kinyi hakuri kin koma dakin ki Hindu, ko dan yaran da kinyi hakuri" Kallon Mama take da bayananne tsoro, hawayenta na zuba, duk yanda zata so yi musu bayanin emotional abuse din da ta jure a gidan Hamza ba zasu gane ba, haukane kawai ba tayi ba, da kasar waje suke ta tabbata zata dauki wasu shekaru tana ganin likitan kwakwalwa saboda abinda ta hadiya a gidan Hamza, ko bata sami miji ba sai Hamza zata hakura ta karashe rayuwarta a haka "Mama ba zan iya ba, wallahi bashi su Suhana bai kai tunanin zama da shi firgici ba" Kai kawai Mama ta jinjina mata, domin ita uwa ce, ta fahimci Hindu, abinda zaisa uwa hakura da rayuwa da yaranta ba kadan bane ba, ba komai daya faru a zaman su da Hamza ta fada musu ba, iya abinda suka sani ne, sai wanda suka fahimta daga yanda ta dage ba zata koma gidan shi ba "Allah yasa hakan shine alkhairin ku, Allah yai miki canji kinji ko? Kiyi hakuri... Kiyi hakuri" Mama take fadi tana kama hannun Hindun da ta mike. Kan kujera ta mayar da ita, da kanta ta dibo ruwa ta bata tasha, sannan ta mike "Ki bari ki natsu, kinga Antynki ko bata nuna ba zaki sakata cikin damuwa" Kai Hindu ta jinjina "Sallah zanyi Mama" Ta furta tana wucewa bandakin da yake cikin falon. Gara tayi sallar Magriba ko addu'a tayi watakila ta samu saukin abinda takeji, in tama yi karatun Qur'ani zuciyarta zatayi sanyi. * A daddafe ya samu yai sallar Magriba, yasan Allah ne kawai ya kai shi gidan su lafiya. A karo na farko a rayuwar shi da yaji yana bukatar Anna fiye da kowanne lokaci, saboda ciwon da zuciyar shi takeyi. Yana shiga gida bai sameta a falo ba, dakinta ya wuce, tana zaune akan darduma inda tayi sallar Magriba, yanda ya shiga babu ko sallama yai mata tsaye a kai yasa ta fadin "Lafiya? Me ya faru?" Kai Hamza ya girgiza, kirjin shi kamar zai bude gida biyu zuciyar shi ta fado "Kai mun magana..." Anna ta fadi, dan wuyanta harya fara gajiya, ta daga shi tana kallon fuskar Hamzan da yake tsaye har lokacin. Tsugunnawa yayi "Kirjina ciwo yake Ann... Zuciyata na ciwo. Anna mutuwa zanyi" Ya karasa maganar yana wani irin sauke numfashi, cikin tashin hankali Anna take kallon shi "Wai me yake faruwa" Ya kai wasu dakika yana kokawa da numfashin shi kafin dakyar ya iya furta "Ba zata dawo ba... Anna zata auri wani wai" Ya karasa maganar yanajin hawaye cike taf a idanuwan shi, sauki yake nema da baisan ta inda zai fara samun shi ba. Cike da tausayin dan nata Anna tace "Kayi hakuri Hamza, haka taku kaddarar ta zo" Dan daga mata kafadu yayi, a karo na farko yana kasa fahimtar kaddara "Nayi laifi nasani Anna, me yasa ba zata yafe mun ba, me zan cewa su Suhana idan suka nemi dalilin da yasa bana tare da Maman su?" Wani irin kallo Anna takeyi mishi da yake kara karyar mishi da zuciya, batasan me zatace mishi ba, bata da abinda zata fada mishi ya samu saukin koma meye yake ji "Kayi hakuri..." Kai ya girgiza ma Anna, wasu irin hawaye masu zafin gaske na zubar mishi. Kallon shi dai takeyi kaddarar shi na dawainiya da ita, yau danta ne da ko lokacin kuruciyar shi sai kayi da gaske zakaga hawaye a idanuwan shi, shine zaune a gabanta yana kuka da idanuwan shi saboda mace, ita kam da Hindu zata saurareta yau da taje da kanta ta roketa tayi hakuri, ta dawo su karasa rayuwar su tare, duk da tasan Appa ba zai bari ba, ta gwada mishi maganar yace ba zasu shiga ba, su kyale yarinyar tunda ita kadai tasan abinda ta hadiya a zama dashi. Sosai ya zauna kan kafet din yana dora kan shi a kafafuwan Anna, kuka yake yau kamar karamin yaro, yafi mintina sha biyar kafin ya dago da idanuwan shi da suka rine yana furta "Yarana zan karba..." Kai ta jinjina mishi, ita ma ba zata bari jikokinta su zauna a wani gida ba, sai dai in Hindun bata tashi yin wani auren ba, amman in dai aure zatayi zasu karbesu, a dinga kai mata su tana gani. Tunda dai zuri'a ta hada, zumunci ba zai yanke ba. Mikewa Hamza yayi yana shiga bandaki ya bude famfo yana tarar ruwa a tafukan hannuwan shi ya wanke fuskar shi da su, dago kai yayi yana kallon fuskar shi ta cikin mudubin bandakin. A karo na biyu da ya zubar da hawayen shi kan Hindu, yau kam ya hakura "Idan nan kaddara ta kawo mu shikenan Hindu, na hakura, watakila karshen kaddarar mu ya hada da yanda soyayyar ki zatayi ajalina" Yai maganar a zuciyar shi yana fitowa, ganin ko sallama baiyi mata ba yana shirin ficewa daga dakin yasa Anna fadin "Ina kuma zakaje? Ba zaka tsaya kaci abincin dare ba" Ko juyawa baiyi ba ya girgiza mata kai yana ficewa, kallon shi tayi, a ranta tana mishi addu'ar tsari harya karasa gida lafiya. Dan taga bashi da nutsuwar kirki a tare da shi. Yana fita daga gidan ya shiga mota gidan Fodio ya nufa. Ya shiga ciki da sallama, bawai gida bane ba zai iya wucewa ba, kawai bayason zama shi kadai ne a irin wannan yanayin da zuciyar shi take ciki, temptation din ya sha wani abu zai dame shi, shekara daya da barin shi, ba zai warware abinda yasha matukar wahala da bari ba saboda bacin ran kwana daya. Yana kallon yanda Fodio yake fama, da taimakon asibiti da komai sai yayi kwanaki baya bacci da dare, sai dai da rana ya dan samu ko na awa biyu, suna kallon shi kullum yana kokawa da depression din da yake zuwa tattare da insomnia, amman bai karaya ba, shiriyar da ta zo mishi mai karfi ce, kuma sosai yake karawa Hamza kwarin gwiwa. Yanzun ma shi kadai ya samu zaune yana danne-danne da waya, ga tv a kunne, dan raba idanuwan shi da wayar Fodio yayi suna gaisawa da Hamzan daya sami kujera ya zauna "Ba zata dawo ba..." Ya furta a hankali, yana saka Fodio ajiye wayar tashi hadi da kallon shi "Da gaske?" Kai Hamza ya jinjina mishi, sosai kirjin shi yake zafi "Fodio na hakura....kawai ina tunanin abinda zan cewa su Amna ne" Numfashi Fodio ya sauke, maganar batai mishi dadi ba, sai dai ba kowanne shafi da kaddara ta bude maka bane yake maka dadin fuskanta, duk da wasu lokuttan yanda shafin zai kare idan ka nutsu sai kaga shine mafi alkhairi da abinda kai din kaso da farko "Ka fada musu gaskiya idan sun tambaya..." Kallon shi Hamza yake cike da rashin fahimta "Ka fada musu kaddarar da ta hadaka da Maman su itace ta sake sakawa zaman ku ba mai nisa bane ba....ka tabbata baka basu dalilin yin dana sanin fitowa daga jikin ka ba, zasu fahimta...." Kai Hamza ya jinjina mishi, watakila soyayyar Hindu ba zatayi ajalin shi ba, watakila ya samu karfin zuciyar jurewa kaddarar su "Allah Ka bani aron rayuwa mai tsayi da albarka tare da yarana. Allah Ka fini sanin dalilin rabani da Maman su, Allah ka bani juriya" Hamza ya fadi a zuciyar shi yana lumshe idanuwan shi, yana karbar ciwon da zuciyar shi takeyi dan ba zai iya guje mishi ba, idan jinya zai kwanta gara ya fara tun da wuri ko zai samu ya warke, amman tunanin Hindu da wani ko da ba Bello bane zuciyar shi na tafasa "Katon kai gare shi..." Ya furta batare daya bude idanuwan shi ba "Waye da katon kai?" Fodio ya bukata cikin rashin fahimta, yana saka Hamza bude idanuwan shi "Wallahi Fodio in ka gan shi kamar mai tallar doya.... Shine Hindu take cemun zata aure shi" Wata irin dariya Fodio ya kwashe da ita duk da Hamzan ya bashi tausayi "Kishi ne yake damun ka ba wani abu ba" Cewar Fodio, kai Hamza ya girgiza mishi "Allah mummuna ne, ko ba komai idan na tuna na fishi kyau zai dinga mun dadi" Dariya kawai Fodio yakeyi, surutan Hamza ko da gaskiya tattare suke da zafin kishi, idan hakan zai sama mishi sauki Fodio din zai biye mishi, a ranshi dai addu'ar zabin alkhairi yake ma su Hamzan, duk yanda suka so suga zaman Hamza da Hindu ya gyaru sun hada da addu'ar alkhairi, har sadaka yayi, sosai suke musu addu'a shi da su AbdulHafiz. Yana kuma da yakinin yanda zaman nasu ya kare shine alkhairi. Tunda suna numfashi, yanzun kaddara ta fara bude musu shafuka mabanbanta...! * *Littafina na siyarwa ne. Akan #250 kacal* Account details: 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number 08074545149 9/20/20, 1:04 PM - mmn khalid: Prologue "Wai baku gama ba har yanzun?" Hamza ya fadi yana daurama Amna takalminta. Fitowa Sadiya tayi daga cikin dakin da Suhana da ta turo bakinta tana gab da fashewa da kuka, ko zip din rigar jikinta ba'a zage ba "Ban gane me take cewa ba, nayi maganar duniya tayi shiru ta kyaleni" Sadiya ta furta cike da neman taimakon Hamzan, wani lokaci har tunani takeyi anya Suhana bata wuce shekara shidda ba, saboda attitude din yarinyar ya wuce shekarunta, tana sane da bakomai Sadiya take ganewa da fulatanci ba, shekara daya kenan da yaran suka dawo hannunta, shekara ta uku kuma da auren su da Hamza, tasan ba shi kadai ba, harta Annar shi sun barta ne su gwada hankalinta kafin su yarda ta rike su Suhana. Yanzun ma rabin rayuwar da kwata a wajen Anna sukeyi. Yau weekend din karshen wata, sabon shine ya sauke su wajen Hindu duk karshen wata, acan suke mata hutun karshen mako "Kina so in zane jikin ki ko Suhana? Me kike so kuma?" Bakin da ake cewa irin nashi ne, sai dai shikam yasan baya turo shi haka kullum "Ni farar riga nake so...kalar na Amna" Kai ya girgiza, su kadai yake da har yanzun, Sadiya tun barin da tayi har yanzun shiru, Allah bai kawo musu wani rabon ba. Amman baya hana shi zane su, akwai kananun rashin kirkin da ba zai dauka ba, ko Sadiya yana mata fadan yanda take sangartasu, yasan yanzun ma fadan shi take tsoro shisa bata sake ma Suhana rigar ba, zama dasu yasa tana jin fulatanci sosai sosai, kawai mayarwa ne bata iyawa har yanzun. "Ki dauko takalman ki. Idan na sake magana babu inda zaku je" Yana kallon hawayen da takeyi sanda ta wuce tana komawa sama. Numfashi Sadiya ta sauke "Ke ma baki shirya ba ko? So kuke sai kaina yayi ciwo" Dariya tayi tana bin bayan Suhana, Amna ce kawai bata saka shi surutu, ita maganarta ma sai kayi da gaske zakaji, sunfi fada akan ya mata magana tana ji tayi shiru ta kyale shi, fiye da tayi laifi. Karya yake idan yace rayuwa ta kawo shi wannan matakin cikin sauki, ya wahala, yayi jinyar rashin Hindu kamar ba zaiyi rai ba. Sai da ya dauki shekaru biyu ko mace baya daga idanuwa ya kalla, a sujjada Anna ta dinga mishi addu'a kafin ya fara sauraren maganar auren da take yi mishi Ranar da tace yaje wajen Sadiya, yar kawarta bai musa ba. Yayi mamaki bayan yaje kofar gidan yaga ita ce ta fito "Saad..." Ya kira da sunanta da yasanta da shi, sun hadu a manhajar BBM tun lokacin blackberry, ita ce mace ta farko daya sani data ke da group a farkon WhatsApp cike taf da mutane duk Ire-iren Hamza, ita kadai admin a cikin su. Ya taya Saad tun a lokacin, saiya kula da duk badalarta a screen ta tsaya, sosai ya karanci tsoronta da yai mata tayin haduwa da shi. Shi kan shi ya girgiza daya ga hotonta, yarinya ce karama a lokacin, daya matsa mata da tambaya ta fada mishi WAEC tayi a lokacin. Fada yayi mata kamar kanwar shi, basa bin kananun yara, basa bin yaran da basuyi hankalin sanin abinda zabukan su zasuyi musu ba tuntuni. Tayi blocking din shine, bai kuma kara bi ta kanta ba, dariya ya kwashe da ita bayan ta fito ba dan yana cikin nishadi ba. Yasan karya yakeyi yai wa Ayar Allah wayau. Dan rana daya ya wayi gari cewar ya tuba ya daina bin yaran mutane baya nufin kuskuren shi ba zai biyo shi ba. Yasan duk sujjadar shi yana kare sauran addu'ar shi da nemar ma yaran shi kariya, da neman canjin kaddarar laifukan shi su tsaya iya shi Idan hakan na nufin auren macen da take da tarihi irin nashi zai hakura, sosai yaga kokarin Fodio na auren Mansy da yayi. Ashe shima bai wuce wannan din ba, kan gwiwoyinta Sadiya ta tsugunna tana rokon daya rufa mata asiri, yace batai mishi ba amman karya fadi dalili "Ki tashi kawai, mu duka ba zamu guje ma laifukan mu ba, ni zan aureki, idan ma ban aureki ba wata dai zan aura..." Yai maganar a gajiye, kuma a yau inda yake zai godewa Allah da zabin da yayi, a duk rana Sadiya na kokarin ganin ta faranta mishi, tana kokarin cike gurbin abinda bata bashi a darenta na farko tare da shi ba wajen gujema bacin ran shi. Daya daina bin mata, ya daina shan wani abu, sauran halayen shi suna nan, ya kula babu inda zuciyar shi da saurin fushi ya tafi, kawai Sadiya ta iya hakuri da shi, tana kokarin tausasa nata harshen idan shi nashi yana tashi. Da yawan lokutta yasan inda ta biye mishi daya daga mata hannu, daya daketa duk bayan alkawarin da yayiwa kan shi, amman bata biye mishi, tana da hakurin da Hindu bata da shi ta wannan fannin, zai karya idan yace yana jinta a ranshi har kasan zuciyar shi kamar yanda yaji Hindu bayan ya rasata. Amman Sadiya ce abokiyar rayuwar shi yanzun, baya dana sanin aurenta ko na minti daya, a aljanna ma yana so ya fara ganinta a jerin matan da zai samu, shisa yake kokarin rike hannunta su nufi hanyar a duniyar su ta wajen kokarin kyautata zaman su da ibadar su "Mun gama..." Ta furta tana rike da hannun Suhana da sai lokacin ya kula da sun fito, tare suka fita suna nufar mota, har kofar gidan Hindu da yake nan Hayin Rigasa ya karasa yana tsayawa a bakin kofa, Sadiya ta fita da kanta tana bude ma su Suhana bayan motar, itama tsaye tayi sai da taga sun kwankwasa an bude musu gidan, ko da wasa bai juya kan shi da nufin kallon kofar gidan ko zaiga Hindu ba. Ta riga ta zama wani bangare daya bari can wani waje mai nisa, ba kowa bace ita yanzun a wajen shi sai Umman su Suhana. Sai da Sadiya ta dawo motar ta rufe tukunna yaja su. Gidan AbdulHafiz zasuje da matar shi tayi haihuwa ta biyu, zai sauke Sadiya wajen sunan. * Tunda ta tashi da safe take duba agogo dan aiki ya rincabe mata yau. Ga Bello ba shayi yake sha da safe ba, dole sai ta dafa mishi wani abu, cefane ne ta markada tasa a fridge, wutar unguwar ta lalace. Karamin generator ne da ita, shikuma ba daukar fridge din yakeyi ba. Dakyar ta lallaba shi yaci indomie da kwai yana mata mita ba zai rike mishi ciki ba "Kai da abincin nan yana nuna wa a jikin ka da yanzun kofofin gidan nan sun maka kadan" Dariya yayi "Ni har wani cin abinci nake" Kai ta girgiza mishi tana fadin "Baka ci kam" Ya dai fita, tare suka wuce da Yusuf, yaronta daya da ta haifa tare da Bello. Da yake yana da gidan ruwa bayan aikin da yake, kuma zata ce suna samun rufin asiri ba kadan ba da gidan ruwan na shi. Da Bello irin mazan da suka dogara da albashin sune da sun sha wahala. Amman suna zaune cikin rufin asiri, a shekaru hudu da auren su yanzun har yar mota yana da ita, duk da bata kai ta Hindu tsada ba. Ko da tata ta fara bata matsala sosai yan kudinta data tara ta cika ta dauki wata tana lallaba kayanta. Tunda Bello ba shida sa ido, bai damu da albashin da take samu ba, da yake ta samu aikin lakcarin a poly tana daukar yan aji daya. Tana jin dadin aikin matuka tunda babu takura sosai. Ba zatace tana da matsala da kishiyarta ba, sai tayi wata shidda bata sakata a ido ba inba da wani dalili ba, gidansu daban, unguwannin da suke ma haka, dan ita tana Kabala, Hindun kuwa tana Rigasa. Yusuf ne ma yakan yi har sati biyu a can gidan, hakan yake kara tabbatar mata da cewar matar Bello wato Amina bata da matsala ko kadan, da tana nuna ma Yusuf din wani abu ko a fuska ba zai dinga nacin zuwa gidan ba sam. Alkhairi ta roka, sai Allah ya jeho mata Bello a cikin rayuwarta, karya take idan tace bashi da tashi matsalar, amman wannan abune da yake a cikin kowacce rayuwar aure, itama tasan ko rashin hakurinta da saurin daga harshe aka barta bakowanne namiji bane zai iya dauka. Amman da yake akwai kyakkyawar fahimta a tsakanin su da Bello, kuma auren sukayi dan su zauna, auren sukayi dan zallar ibadar da take ciki hankalin su a kwance yake. Har abincin rana ta samu ta kammala, duk da ba girkinta bane, tasan dai zai dawo ya dubata kamar yanda yakan yi ko da ba girkin wata a cikin su bane ba. Amman saboda ta samu wadataccen lokacin zama da su Suhana ne, tasan Hamza ma ya mata halacci da yake kawo mata su duk karshen watan duniya inba sunyi tafiya ba. Ko Anna takan kirata wani lokacin su gaisa, ana zumunci sama-sama da take da tabbacin saboda yara ne. Tanajin an kwankwasa tasan sune, taje ta bude, ba wani Babban gida bane ba, dan flat ne mai dakuna uku, kitchen sai dan karamin store, ita a gidan haya ma ta fara zama da Bello, kafin a hankali ya gina wannan din da suke ciki yanzun, ko shekara basu hada ba. Sosai take zaune da yaran a falo suna hira da Suhana, Amna na kwance a jikinta tunda surutu ba damunta yayi ba, dariya takeyi cike da nishadi, a haka Bello ya shigo ya same su "Ai tunda nake jin dariyar ki nasan ke da su Suhana ne" Da gudu Suhana ta karasa inda Bellon yake "Abban Yusuf" Ta kira kamar yanda take ce mishi, gara Amna tana cewa Abban kawai, Hindu tayi tayi da Suhana, amman Abban Yusuf yaki barin bakinta, harta kyaleta tunda taga Bellon bai damu ba. Yarinya kamar tana taya Babanta kishin Bellon "Suhana...ya kike?" Amsa shi tayi da yaren fulatanci, tana dorawa da "Ina Yusuf?" Tana kallon fuskar shi "Yana dayan gidan su" Bello ya fadi yana karasawa inda Hindu take ya zauna a gefen ta "Gaskiya yau akwai rana... Kinji dana tunkarota" Dariya tayi "Sai da nace ka dauki motata da zaka fita ai" Rausayar da kai yayi "Na dauka zai gyaramun tawa kafin inje ne wallahi, da naga inata kiran shi bai daga ba" Kai kawai ta girgiza, gaddamar shi bata sallah, ko da ba'a gyara din ba in bai niyyar dauka ba tasan ba zai dauka ba, shisa ba akan komai bakinta yake surutu ba, mikewa yayi "Zan duba kine daman, bari in wuce nikam... Kije ki dauko Yusuf daga islamiyya anjima zan kawo shi, kinsan ba zai zauna ba in yaji su Suhana sunzo" Kai ta jinjina mishi tana zame Amra daga jikinta ta mike, har bakin kofa ta raka shi "Gidan har ya fara mun shiru" Ta fadi, murmushi yayi "Kaji neman magana ko? Ke da ga yaranki kina magana kamar zakiyi kewata" Dariya tayi kawai, tana mishi sallama ya fice ta mayar da gidan ta rufe. Kalma daya take da ita idan aka tambayeta me ta samu a gidan Bello banda Yusuf, idan mutane suna tunanin tayi kuskuren kin komawa auren Hamza saboda a komai yafi Bello, shine "Kwanciyar hankali" Abinda bata sani ba a zaman aure sai da ta auri Bello, hankalinta a kwance yake, suna cikin rufin asiri, ci da sha, suttura ta mutunci batafi karfin su ba, wauta tayi da take tunanin samun MIJIN NOVEL, soyayyar mazajen ciki da wadda take tafiya a rayuwar yau da kullum suna da banbanci mai nisan gaske. Tana ganin soyayyarta a tare da kalar kulawar da Bello yake bata, a lokuttan da zata bude baki tace wani abu na mata ciwo, ko da farcen yatsanta ne, saboda hankalin shi baya kwanciya sai yaji ta samu sauki, soyayyar shi na cikin yanda yake zuwa gidansu duk juma'ar duniya ya gaishe da iyayenta har yai musu alkhairi duk da bashi da wadatar tsohon mijinta da mutane suke tunani. Tana ganin yanda yake sonta a aikace batare daya furta ba, tana kuma ganin banbanci kulawar da taso samu da wadda ta samu yanzun. Ko kadan bata tsoron sauran shafukan da kaddara zata bude mata, me kyau ko akasin hakan, tare da Bello rike da hannunta tana da yakinin wuce komai, mijinta zai tayata raba ranakunta marassa dadi, kamar yanda yake raba na farin cikinta da ita. Bata da bakin furta komai sai "Alhamdulillah" Kalmar karshe da ta furta, kalmar kuma da zan amfani da ita wajen rufe wannan tafiyar da Allah ya kawo karshenta. * Nagode da karamcin ku, Nagode da kaunar ku, Nagode da uzurrrukan da kukayi mun a cikin tafiyar nan. Ina muku fatan alkhairi a duk inda rayuwa zata kai ku gabaki daya. #SonSo saboda ALLAH.