[1/13, 8:22 PM] Bintu: 94&95 Yini cur! mu kayi a d'aki sallah ce kawai take fitar dashi, amma na samu kula sosai da garinsa, sai dai na kasance cikin fargaba da damuwa! domin damuna ya dinga yi ta'ba nan, ta'ba can, duk jikina ciwo yake min mussaman kirjina zafi yake min sosai irin na rashin sabo, ban san me yasa ba, gabad'aya hankalinsa ya fi karkata a gurin, haka ya yini yana lugudar min jiki, ni sam bana wani jin dadi saboda tsoro, shi kuwa jikinsa har karkawa yake, duk yanda ya so na yarda yayi irin na jiya na'ki yarda da shi, domin ba zan amince ya dawo min da ciwo sabo ba, wannan dalilin ne yasa ya damu kirjina kamar zai raba ni da su, sai zafi suke mussaman nipples d'in. Bayan fitarsa sallar magariba, na daddafa na shiga bandaki nayi wanka tare da shiga ruwan d'umi, na d'auro alwala na fito, akwatin kayana na bud'e na dauko doguwar riga milk mai adon duwatsu da hula, sosai rigar tayi min kyau! kuma da ka gani tana da tsada, na sa a jikina a take ta zauna ta kuma fitar min da surori, kamar na cire na sanja domin ina gudun abinda duk zai gani a tare dani da zai ya tayar masa da hankali. haka dai na hakura na zauna da rigar a jikina, bayan na gabatar da sallar isha'i yunwa ta addabi cikina gashi an sauka da tarkacen kwanukan abincin rana, babu komai a dakin. Firjin dake gefan gado na bud'e nan naga lemuka kala-kala da fresh milk da yogurt sunyi sanyi sosai. na dauko fresh milk din guda daya na mayar da firjin na rufe. Ina kokarin bud'e robar madarar ya shigo d'akin. da sallama a bakinsa. na amsa hankalina na kan madarar dake hannuna. Gefe na ya zauna tare da zagaye 'kugu na da hannunsa. cikin kunnena ya ce." Na san dole ki bukaci abinci ban san wane irin hali gare ki ba. Murmushi kawai nayi ina d'an janye jikina daga nasa, domin ganin kamar yana so ya zarme! bai damu da abinda nayi ba ya fito da wayarsa ya kira Shukura tare da bata umarnin kawo abinci. Minti biyar a tsakani ta buga 'kofar dakin. ya tashi ya bud'e mata amma bai yarda ta shiga d'akin ba, ya kar'bi kayan abincin itama ba tace komai ba ta juya ta tafi jikinta duk a sanyaye! wai yau ita ce ta zama tamkar 'yar aiki a gidan ubanta, ita takewa wata 'kask'antanciyya bauta! kuka mai 'karfi ya kwace mata da gudu! ta shige Hajiya dake zaune a falo ta bude dakinta ta zube a gado tana kukan b'akin ciki! yanda dadyn nata ke rawar jiki a kan musakar yarinyar shine abinda ya fi tsaya mata a rai! ko a mafarki bata ta'ba tsammanin hakan zata faru ba, 'Yar talakawa kuma muskiniya ita ce take juya kowa a gidan, gaskiya dole suyi wa tufkar hanci. Wayarta ta d'auka ta kira Mommynta duk ta sheda mata abinda yake faruwa. Hajiya Fatima Hankalinta ya tashi ainun! nan ta ajiye a ranta cewa; yarinyar shiga tayi ta fita har ta sami nasarar mallake zuciyarsa, a yanda ta san halinsa a can baya mutum ne shi mai tsare gira, wanda baya son raini, amma yau 'kan'kanuwar yarinya mara galihu ita ke juya shi a gidansa. lallai da sake dole ta shiryawa al'amarin. Tare muka ci abincin yana ta tsokanata, ni dai umm kawai nake iya cewa, saboda gabad'aya! jikina a mace yake ga bacci da gajiya sun dabaibaye ni. Wanka ya shiga ya fito ina kwance ina kallonsa, ya shirya cikin suit wanda sukayi masa kyau ainun, kasa dauke idona nayi daga kansa har ya k'araso kusa dani yana gyara gilashin dake sakaye da idonsa, yayi murmushi tare da fad'in" Nayi kyau ne?" Ajiyar zuciya kawai na sauke na tashi zaune tare da ri'ke hannunsa a marairaice na ce" Zaka tafi kano ka barni." Ya sassauta fuska da fad'in" Ki kwantar da hankalinki don Allah kada kiyi min asarar hawayen nan, kar ki bari su zuba kinji ko nayi miki alkawari in sha Allahu za kije Kano a kurkusa domin ni kaina tafiyar dole ce, amma komai dare a gida zan kwana." Jin abinda yace yasa na sassauta fuskata tare da k'ok'arin mayar da hawayen dake 'kokarin zuba, na ce" Shikkenan Allah ya kiyaye hanya." Ya amsa da "ameen fuska a sake ya ce." Ba ki da sa'ko gurin Baban-baba?" Dariya ya bani na ce" Ga ka nan a zaune a gabana, zan dai sake jadadda maka cewa; ka kula da kanka, kuma banda kallon mata." Dariya yasa tare da jan karan hancina, ya ce." Ni mata basa damuna tunda ina dake bana ganin kowa." Tsira masa ido nayi ina nazarin maganarsa, mafi akasarin mazan nan basu da al'kawari, bana so na saba da dad'in bakinsa na saki jikina dashi ya aikata min halinsu. Ganin kamar ina masa kallon zargi ne yasa ya dubi agogon dake d'aure a hannunsa 9:30 na safe da sauri ya mi'ke tare da ri'ke hannuna muka sauka 'kasa. Hajiya na zaune ita kad'ai tana kallon sunnah tv. zuwanmu gurin yasa ta fad'ad'a fuskarta da fara'a. Na tsuguna har 'kasa na gaisheta, ta amsa cike da farin ciki. kafin ta kalle shi da cewa" Na ganka a shirye da fatan dai ba wani guri za kaje ba?" Ya ce." Kano na nufa In sha Allahu. amma ba kwana zanyi ba, zan dawo yau idan Allah ya nufa". Ta ce. " To ko da naji ai ya kamata ka d'auki hutu, domin ka samu nutsuwar gabatar da komai! domin so nake na samu jiki da wuri" Tsakani da Allah ta fadi maganar. Maganarta ta bashi dariya ya ce" Hajiya ai haihuwa ta Allah ce, zamana a gida ba shi zai kawo haihuwa da wuri ba komai lokaci ne, amma muna ta addu'a in sha Allahu rabon a kusa yake. Cikin damuwa ta ce" Alhaji Habu halinka na sani da son kud'in tsiya kai kenan yawo a sama kaje nan kaje can, ai gwara kuma ka zauna a gida ka samu 'ya'yan da zaka tarawa dukiyar. Ya dinga kyalkyala dariya yana kallonta. nima na shagala gurin kallonsa da mamakin yanda yake dariya, nan na gasgata maganar da suke bata shafe ni ba, domin da na ga damuwa a fuskar Hajiyan sai jikina yayi sanyi, duk da ban ji abinda suke tattaunawa ba, na tsargu shiyasa na kasa sakin jikina a gurin, amma yanzu ganin yana dariya yasa na samu kwanciyar hankali tabbas maganar da suke bata shafeni ba. Ya kalle ta tare da fad'in" Ina Shukura ne? ban ji motsinta ba. Ta ce." Au! kaga na manta wallahi ta bani sallahu ganin baka fito ba ta ce na fad'a maka cewa ta je filin jirgi d'auko mamanta wai ta dawo " Ya 'bata fuska da fad'in"Shukura bata jin magana Hajiya na rabata da Fatima amma ta raina maganata" Murmushi tayi ta ce" Ai hakan ba zai yuwu ba, domin dai babu wanda ya isa ya raba uwa da d'a, addua kawai zaka cigaba da yi mata Allah ya shirya mana ita, amma yana da kyau ka zauna da ita lallai ta fitar da miji daga cikin masu neman auranta" Ya ce." Kwanaki na zauna da ita akan hakan, amma in sha Allahu a karo na biyu zan sake zama da ita domin na ji a wace matsaya ta tsaya domin ba zata mayar dani 'karamin mutum ba. Ta ce." Hakan yayi, Allah ya za'ba abinda ya fi alheri. Ya amsa da ''ameen tare da kallona ya ce" Sai na dawo ko." Cikin nutsuwa nayi masa fatan alheri tare da dawowa lafiya ya kama hanyar fita sai duk muka bi shi da kallo har ya bude 'kofa ya fita. Ganin fitowarsa yasa escorts d'insa gaishe shi ya amsa da kulawa d'aya ya kar'bi 'yar jakar dake hannunsa ya wuce sai suka rufa masa baya, kafin ya shiga mota sai duk ya gaisa da ma'aikatan dake harabar gidan, Sule da shi za a yi tafiyar domin amintaccen yaronsa ne kuma direbansa, shi ya bude masa motar ya shiga, escorts din suka zauna kusa dashi. sannan Sule ya zauna a mazauninsa ya ja motar. masu tsaron 'kofar su kayi masa fatan alheri tare da dawowa gida lafiya. Kusan zaman kurame! mu kayi ni da Hajiya domin biye min tayi ganin duk maganar da tayi min bana iya tanka mata sai da umm ko a'a domin gabadaya nauyi da kunyarta sun hana ni sakat! a gurin, har gwara zama a saman na d'an fi sakewa! ganin haka yasa tayi min shiru ta cigaba da kallon tv amma da murmushi a fuskarta. Shigowarsu falon yasa gabad'aya muka kalli Bakin k'ofa, hamsha'kiyar maca ce tana sanye da suttura ta alfarma, kallo daya nayi mata gabana ya fad'i! ganin Shukura rike da akwatin kayanta yasa na gazgata cewa Mamanta ce, gabadaya falon ya cika da masifaffan 'kamshin turaranta. Ta 'karaso ta zauna kan kujera tana ya tsine fuska. ta kasan ido nake kallon duk motsinta, magana suke da Hajiya wacce ban fahimci komai ba tunda a hankali suke kawai dai naga bakinsu yana motsi. Kallonta nayi a karo na biyu tun bayan zamanta a gurin, wayayya ce daga gani, ga ha'koran maka nan 'kasa da sama, wuya da hannuwanta uban gold ne masu nauyi, mayafi da d'ankwalin kanta ta cire ta ajiye, nan naga uban gashin doki a kanta anyi mata kitso dashi, duk sai na raina wayonta, domin ni a rayuwata na tsani 'karin gashi, da alama kuma tana shafe-shafe, domin farin gaskiya ya fita daban, gajera ce don na fita tsayi, amma a cike take ta ko'ina, hakan bai dameni ba saboda na san babu abinda za ta nuna min na daga suffah. Hajiya ce ta katse tunanin da nake ta hanyar fad'in " Shukura Fatima tana magana. Sai nayi saurin kallonta tare da aro jarumta na ce" Sannu da zuwa." Ta amsa tana min wani banzan kallo kafin ta d'auke kanta ta ce" Hajiya don girman Allah meye abin so a tare da wannan muskiniyar"? Kalmar k'arshe kawai na iya tsinta a cikin maganarta, raina ya 'baci mutuka amma ban ce komai ba, kawai nayi shiru ne domin naga matakin da Hajiyan zata dauka. Babu walwala a fuskarta ta ce" Fatima bana son neman fitina don Allah ki kama girmanki, babu ruwanki da yarinyar nan zaman aure take. Ta she'ka da dariya tana kallonta ta ce"Ai fa zaman aure manya ayi ma gani." Na sake tsintar karshen maganarta, domin ban ji abinda Hajiyan tace mata ba har ta fad'i wannan maganar, na dai fuskanci damuwa da a tare da ita. Yun'kurin tashi nayi domin na bar gurin, saboda bana so na zauna matar ta fusata ni mu zo muyi abinda bai dace ba. da sauri ta ce"Shukura ina zakije kuma ki zauna mana. Tafad'a tana 'boye damuwarta. Na ce" Hajiya zan hau sama ne na kwanta bacci ne a idona." Ta ce"To shikkenan idan kina bu'katar wani abu kiyi magana kada kiyi shiru." Na ce"In sha Allahu Hajiya." da sauri nayi nufin barin gurin, sai kawai na ji shewarsu Shukura da Mamanta, nayi saurin juyawa domin naga abinda sukewa dariya, kawai Shukura sai tayi min maganar bebaye da hannunta, wai tambaye ta take menene tana kwaikwayon irin maganata. Wasu zafafan! hawaye suka ciko idona, da sauri na mayar dasu cikin sassarfa na hau saman na bude daki na shiga na zube! kan gado. lokacin kukan ba'kin cikin da nake dannewa ya 'kwace! min, tun ina yarinya nake da kishin kaina, na tsani wani ya kushe hallitata ko ya kwaikwayi maganata hakan yana min ciwo sosai! kuma duk dauriyata bana iya jurewa sai na zubar da hawaye, haka na kwanta ina ta sharar hawayen takaici. [1/15, 10:20 AM] Bintu: 96&97 KANO Cikin manyan kaya ya fito daga d'akinsa yana ta zabga 'kamshin turare mai tsadar gaske. Ya tsikara hula gaban goshi da alama dai wani muhimmin guri za shi duba da irin adon da yayi, ko da yake dama can tuntuni shi d'an fafah ne! bai yarda da tu'ammali da 'kananun sutturu ba, har yanzu yana nan da halinsa zai yi kwalliya ya fita shar-shar sai ka rantse da Allah cewa; wani mugun attajiri ne saboda yanda yake kashewa kansa kud'i, amma gidansa kuma ko za a kwana da yunwa wannan bai dame shi ba, domin dai a 'koshe yake dawowa gida, Hujaj yana nan da mugwayen d'abi'unsa sai abinda ma ya yi gaba. Talatu na gurfane! gaban murhu tana fifita wuta da mafici! duk tayi wujiga-wujiga! ta jigata! zani daban riga daban, daka gani tana fuskantar rayuwa! idonta sai tsiyayar da ruwa yake sakamakon haya'kin wutar da ya turnuke! gidan. Kallonsa tayi a lokacin da ya tsaya a gabanta fuskarsa babu fara'a domin mugun haushinta yake ji ganin yanda ta mayar da kanta jakar mata, duk ta mokad'e! ta ko'ina babu wata mamora, shiyasa ya daina kwamciya da ita ko ta nemashi a shimfid'a sai ya wulakanta ta sannan zai bata hakkinta na aure, wannan shine dalilin da yasa ya fara neman wata 'yar duma-duma aure zai 'kara domin ya huce takaici! Tasa gefen zaninta ta goge hawayen fuskarta kafin ta ce" Ka san Allah yau ba zaka fita ba sai ka biya bashin dake kanka." Tsaki ya ja ya kalleta a wulakance kafin ya ce." Idan kuma na'ki fa?" da hanzari ta ce" Sai na d'auki mataki a kanka, domin na gaji da wannan wulakancin da kake mana ni da yarana. Wallahi Jamilu baka da imani ko kad'an, kuma na fada maka cewa; tun shekaran jiya rabon Hadiza da gidan nan, na bincika gidajen 'yan uwa nawa da naka bata nan amma Jamilu kayi biris da maganata, wallah ka kiyayi had'uwarka da Ubangiji domin tilas ya tuhumeka akan amanar da ya baka." Babu wata damuwa a tare dashi ya ce."Wannan kuma matsalarki ce, ai ke ki ka lalata yarinyar, don haka sai kiyi hakuri da sakamakon da zaki gani, ni dai ba zan lamunci cikin shege a gidana ba." Rushewa tayi da kuka! da fad'in " Yanzu fatan da kake wa 'yar cikin ka kenan? cikin shege fa kake magana Allah ya kiyaye." Yayi tsaki da cewa; Ai ni Shahida ta fi yaranki sau dubu a guri na, tana can tana zaman aure, duk da mijinta talaka ne mai rangwamin gata, amma tsayin wata hud'u wata matsala bata faru ba, abinda ki ke nufi a kanta na sharri, sai gashi ya afku a kan 'yarki" Zubewa tayi a gurin tana kukan bakin ciki da takaici, ya d'auko dari biyar daga aljihunsa ya jefe mata a jiki kafin yasa kafa ya fita daga gidan babu abinda ya dame shi. Ganin fitowar Hujaj daga gidansa yasa Sule dake cikin mota yayi saurin fitowa ya riske shi. hannu ya bashi suka gaisa kafin ya ce." Kai ne Jamilu Hujaj ko?" Ya ce." Eh 'kwarai kuwa ni ne Allah dai yasa lafia." Sule ya ce."Lafiya lou ina fatan kasan Attajirin dan kasuwar nan Alhaji Habu Dangaske." Da sauri ya ce." Eh na san shi a hoto da kuma kafafan watsa labarai amma ban ta'ba ganinsa a zahiri ba,ina fatan dai lafiya?" ya 'karasa maganar cikin fargaba." Sule yayi murmushi tare da cewa" Alhamdulillhi dama shine ya turo ni gurinka domin yana bukatar magana da kai yanzu za mu je ofis d'insa tare " Hujaj hantar cikinsa ta kad'a! baki na rawa ya ce." Me ya faru kuma? ni wata alaka bata ta'ba had'ani dashi ba wallahi." Sule ya dafa kafad'arsa ya ce'' Ka kwantar da hankalinka ba wani abu bane sai alheri in sha Allahu." A sanyaye ya ce."To shikkenan tunda kace haka mu je babu komai." Hujaj tsuru-tsuru yayi a mota gabadaya jikinsa ya mutu jin cewar ga wanda yake nemansa sosai ya zurfafa tunani domin gano dalilin neman. amma bai hasaso komai ba, haka dai ya hakura sai dai zuciyarsa ta kasa nutsuwa har suka isa zooroad in da babban ofis dinsa yake. Ofis ne babban wanda aka 'kawata shi da kujeru na alfarma! tare da komai na bu'kata akwai hotonan Sarki shugaban 'kasa tare dana gwamna da kuma hoton mamalakin ofis din, wanda yake sanye da manyan kaya yayi kyau sosai. Cike da fargaba Hujaj yayi sallama ya shiga jikinsa in banda rawa babu abinda yake. Wayar dake hannunsa ya ajiye fuska a sake ya amsa sallamar tare da nuna masa gurin zama. Hujaj kasa zaman kujerar yayi ya tsuguna gabansa tare da mi'ka hannunsa da fadin"Barka da yamma yallabai." Ya ri'ke hannunsa a lokacin da yake amsawa da "Barka kadai Babana." Jamilu ya kama ya'ke jin sunan da ya kira shi da shi "Babana." yayi ta nazarin sunan a cikin ransa. Ya ce."Ba zan yi wata magana da kai ba sai ka zauna kan kujera domin girmanka ya wuce a ce ka tsuguna a gabana, ni ya dace nayi hakan amma ban yi ba. Hujaj ya tsira masa ido jin irin maganar da yake wai shin me yake shirin faruwa ne. Ofis din yayi shuru na minti biyu, kafin ya sake nuna masa gurin zama a karo na biyu ya ce."Ka zauna ka samu nutsuwa sai mu tattauna maganar da ta had'a mu. Ya tashi ya zauna kan kujerar kamar yanda ya umarce shi, amma fa gabadaya jikinsa ya mutu! tunaninsa ya tsaya cak. Sai da ya tabbatar da cewa; ya samu 'yar nutsuwa sannan ya mi'ka masa wayarsa da fad'in" Ko zaka sheda waye a jikin wannan hoton." Hannu na rawa ya kar'bi wayar yana dubawa. hoton mijin 'yarsa ne Shahida wanda ya tafi da ita abuja. Da sauri ya ce." Wannan ai Baban-Baba ne mijin yarinyata Shahida ina fatan ba wani abu su kayi maka ba domin dai mutumin yana da 'yar matsalar 'kwa'kwalwa." Ya ce." Me yasa ka san yana da ta'bin hankali ka dauki 'yarka ka bashi har ya tafi uwa duniya da ita kuma baka taba bibiyarsu ba. A sanyaye ya ce" Wallahi dole ce tasa hakan, a lokacin babu yanda zanyi ne domin ina cikin masifa, to sai ya zo da maganar yana sonta zai aureta, ni kuma nayi al'kawarin bashi auranta mutukar yayi sanadiyar fita ta daga cikin masifar da nake ciki." Shuru yayi na minti biyu kafin ya ce."Ba kowa bane wannan mutumin face ni da nake zaune a gabanka, ni ne Alhaji Saddiku Dangaske, kuma ni ne Baban-Baba mahaukacin nan dake rayuwa a 'kasan mota." Hujaj fitsari ya kusa kwace masa a gurin, bakinsa ya shiga rawa da k'yar ya iya furta "Alhaji ya akayi hakan ta faru innalillahi wa'ina ilahi raji'un! ya k'arasa maganar da kiran sunan Allah. Murmushi yayi kafin ya tashi a nutse ya je ya bud'e wata dirowa wata leda ya dauk'o mai d'an girma ya zo ya zauna k'asan kafet! Hujaj tsuru! yayi kawai ya zuba masa ido a lokacin da yake sanjawa kansa hallita. Abinda ya faru shine: Wato tunda ya kudiri aniyar neman matar aure ta wannan sigar, sai ya shirya ya nufi india dama kuma a garin shi ba 'bako bane, yana da jama'a sosai a garin wanda harkokin kasuwanci ya had'a su, akwai wani abokinsa mazaunin 'kasar babban likita ne, tare da had'in gwiwarsa komai ya tafi dai-dai, fuska akayi masa wacce tayi kamanceceniya da tasa, amma sabuwar fuskar tasa tayi tsufa sannan da kuma gemu mai tafe da furfura, akwai wasu sinadarai da yake shafawa a jikinsa gabadaya sai fatarsa ta bushe! ta yamushe ta kuma sauya kala, hatta da fartansa da tafukan hannu da kafafunsa suma sanjawa suke, amma yana zuba ruwa a jikinsa komai zai wanke ya dawo daidai! wannan shine abinda ya faru. Hujaj yana zaune yana kallonsa har ya gama sanjawa kansa hallita ya dauki yagaggiyar rigar da yake amfani da ita a lokacin yasa a jikinsa, lokaci guda ya rikid'e ya zama Baban-baba. Ya nemi guri ya zauna suna fuskantar juna ya ce."Nayi hakan ne saboda manufofi da yawa, alhamdulillhi na ci nasara domin na samu biyan b'ukata na had'uwa da macen da ta dace da rayuwata, a can baya nasha wuya sosai a hannun mata amma yanzu dole na godewa Allah na kuma gode maka da ka kasance mahaifi ga wannan yarinyar, na kuma yi alkawarin ri'ke ta da kyau dalili nasha wahala kafin na sameta, wannan shine dalilin da yasa na ce kazo domin na sanar da kai abinda baka sani ba. Asalin Sunana Abubakar Saddiku wanda jama'a da yawa suke kirana da 'Dangaske, ni mutumin jahar katsina ne cikin karamar hukumar Jibia kamar yanda nayi maka bayani a farko lokacin da nazo neman auran 'yarka da sunan Baban-Baba. sannan kuma ina so na tabbatar maka da cewa; Shahida tana nan cikin koshin lafiya ta kuma bani sa'kon gaisuwa a gare ka." [1/15, 4:14 PM] Bintu: 98&99 Hujaj dai kasa daurewa yayi cikin rawar murya ya ce." Wallahi Yallabai na rasa wace irin godiya zanyi a gare ka. gabadaya kaina ya d'aure! ashe har na kai matsayin da zaka iya had'a jininka da nawa? Alhaji yanzu ace ka tsallake duk matan dake wannan duniyar ka zo ka auri yarinyar nan da bata cikakkiyar lafiya wallahi ni duk a tunanina wanda zai aureta irinta ne ko kuma dai mai ramgwamin gata saboda wai lalurarta ashe ba haka bane yarinyar tana tare da baiwar da ba kowa yake da irinta ba." Cikin rashin jin dad'in lafazinsa ya ce."Amma ban ji dad'in jin wannan kalaman daga bakinka ba, ni waye dana wuce na auri yarinyar, na fad'a maka cancanta na duba har naji sha'awar auranta, kyawun sura ko tsantsar kyau na fuska bashi nake da bukata ba, kwanciyar hankali nake bukata, babu ruwana wai don yarinyar na da matsalar kunne! wannan sam bai dameni ba, kuma sonta nake da gasken gaske, duk duniya babu wata mace da take gabana kamar ita , saboda haka ina so kasa a ranka cewa; ni Shahida tayi wa alfarma tunda ta aure ni a matsayin mahaukaci! talaka! ta toshe kunnanta tace taji ta gani saboda k'aunar da take min babu halin da bata shiga ba, don haka wallahi ina kara jadadda maka cewa; Alfarma tayi mini, ba ni nayi mata ba, kuma tafi k'arfn komai a gurina." Hujaj jikinsa yayi sanyi jin kalaminsa, sai bakinsa ya mutu, cikin zuciyarsa yake kad'aita Allah! lallai idan Ubangiji yana saukar da ikonsa dole kowa ya zuba ido, shi a haukansa saboda yarinyar kurma ce! to ba zata auri cikakken namiji ba dole shima zai kasance muskini sai gashi Allah ya d'aukaka darajarta ya aura mata miji mafi k'ololowa. Shiru ofis din ya d'auka na 'yan mintina kowa da tunanin da yake. Shi ya katse shirun ta hanyar fadin." Sannan ina neman wata alfarma a gurinka. Da sauri ya ce."Ranka shi dade wace alfarma ce wannan?" Yayi shiru yana nazarin maganar dake ransa, da akwai nauyi amma ya zama dole ya nuna masa kuskuran abinda yake aikatawa tunda yana matsayin surikinsa ba zai so a ce mahaifin matarsa na aikata shirme ba. Ya ce."Ina da labarin irin abubuwan da kake a gari na rashin kyautawa da zubda mutunci. ina rokonk'a da Allah da Annabi ka daina, saboda abinda ka iya zuwa ya dawo a nan gaba." Jamilu kunya ta rufeshi ya sunkuyar da kansa yana wuri-wuri! tare da 'kokarin kare kansa. Sai ya katse shi da cewa; Wannan duk ba hujja bace, Ubangiji da kansa ya ce" Ka tashi ka nema ni kuma sai na taimaka maka, ba zai yuwu garin son zuciya ka jefa kanka cikin sabon Allah ba, cah-cah! sam ba sana'a bace, akwai wulakanci da tozarci a ciki, sannan kuma dole ranar lahira Ubangiji ya tuhumeka, saboda haka ina neman wannan alfarmar a gurinka ka ajiye wannan harkar ka fuskanci alkibula mai kyau, ni kuma nayi maka alkawarin taimaka maka." Cikin mashahuriyar kunya da nadama ya sunkuyar da kansa 'kasa a sanyaye ya ce." In sha Allahu na bari har abada Alhaji na daina da ikon Allah. Cike da jin dadi ya ce."Na gode sosai da wannan alfarmar da kayi min. Yana murmushi irin na ya'ke ya ce."Yallabai kafi karfin komai a gurina saboda haka babu godiya a tsakaninmu. "Hakane" ya fad'a tare da tashi ya nufi wata dirowa kudi ya d'auko d'auri biyu dubu dari biyu ya isa har kusa dashi ya mika masa tare da cewa" Ga wannan ayi cefane, kafin na kammala shirye-shiryen da nake a kanka, sannan kuma ina so zaka bar wannan gidan da kake ciki a zaune akwai wani gidana dake rijiyar zaki zaka koma can da zama domin tuntuni an kammala komai ko gobe kake da ra'ayi zaka iya tarewa a gidan, tunda akwai komai na bukata. Da sauri ya ce."Haba Alhaji ai babu wata jayayya a tsakaninmu, kayi min kyauta irin wannan nace sai nayi tunani wannan bai taso ba gobe in sha Allahu zan tare a sabon gidana, ina kara jadadda godiyata a gare ka, rabbi ya rufa maka asiri duniya da lahira ya jikan magabatanka." Cikin jin dadin adduarsa ya amsa "Allahumma ameen na gode sosai Babana Allah ya 'kara girma " Jamilu farin ciki ya cika masa zuciya, hakika yana alfahari da mutumin, kuma yana jin dadi a duk lokacin da zai kira shi da uba a gare shi, wannan kad'ai ya isa ya godewa Allah. Mukkulin gidan ya bashi tare da fadin" In sha Allahu gobe kafin na tafi Sule zai kai ka gidan. Allah ya sanya alheri yasa an shiga asa'a." Ya 'kare maganar da yi masa fatan alheri. Hujaj ya dinga amsawa yana washe baki! ga damin kudi na dubu dari biyu, ga kuma sabon gida! lallai haihuwa tayi masa rana. Godiya ya dinga zabgawa har sai da ya dakatar da shi, ya nuna masa cewa; babu godiya a tsakaninsu, sannan ya hakura yayi shiru amma kana kallonsa zaka fahimci cewa; yana cikin farin ciki. Kafin su yi sallama sai da ya sake neman wata alfarmar a gurinsa saboda ya lura cewa; kamar yana zumud'in zuwa ya kwazawa duniya halin da ake ciki, ya ce masa yayi shiru da bakinsa a hankali koma meye duniya zata sani. Wannan ya sanyayyar masa da jiki! domin da sauri kawai yake ya fita ya je ya shedawa abokansa abinda yake faruwa domin ya nuna musu cewa; bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane. sai kuma aka katse masa hanzari, a sanyaye ya ce."Yallabai ai komai yana 'bukatar sirri in sha Allahu nayi alk'awarin babu wanda zan fad'awa halin da ake ciki, sai dai kowa ya gani a aikace." Ya ce" To na gode sosai Babana, wayarsa ya d'auka ya kira Sule ya bashi umarnin ya d'aukeshi ya mayar dashi gida. Jamilu ya tashi da kwarin gwiwa da karsashi! Aljihunsa cike da kud'i! su kayi sallama cikin mutunci da mutunta juna. Yayi niyyar komawa gida a ranar, amma hakan bai samu ba saboda cinye lokacin da yayi gurin tattaunawa da mahaifin matar tasa, bayan haka kuma yana so ya je gurin Baba Asabe domin itama yayi mata cikakken bayani don fita daga cikin duhu! ya kamata ace kowa ya san waye shi a cikin dangin matar tasa. Shukura ya kira a waya ya bata umarnin cewa; ta shedawa Shahida ba zai samu dawowa yau ba sai gobe." Ta ce" To shikkenan Daddy zan fada mata in sha Allahu." kashe wayarta tayi ranta a 'bace! cike da kishi da jin haushi ta kalli Mamanta ta ce." Daddy ne fa ya kira yana cewa; na je na fad'awa kurma ba zai dawo yau ba sai gobe, sai kace ita kad'ai ya ajiye a gidan, ai mu ma muna da hakki a kansa. Hajiya ta ce" To menene don yace ki fad'a mata matarsa ce fa, sannan kuma bata saba da wannan tafiye-tafiyen ba, mu kam! ai mun saba don haka ni banga abin damuwa b.....Hajiya Fatima ta katseta. rai a 'bace ta ce"Hajiya na lura fa bakya son abinda zai 'batawa yarinyar nan rai! duk maganar da za ayi a kanta sai ki kare! kada fa ki manta mune naki ita kuma kawota akayi daga baya kuma idan ta samu dama wallahi ba zata tuna dake ba, gwara ma kiyi karatun ta nutsu kuma kisa baki ya mayar dani dakina" Ta ce" Ba zan yi masa dole ba wallahi! yarinya kuma ba za a had'a baki dani a zalince ta ba, me yasa ki kayi wasa da damarki a can baya wane irin rashin mutunci ne ba kiyi masa ba, yanzu ai na fahimci dalilin da yasa ki ke so ki koma d'akinki saboda kinga yayi arziki shiyasa ki ke binbini! to ni ba zan tilasta shi ba domin mai d'aki shi ya san inda yake masa yoyo." Hajiya Fatima ta fashe da kukan takaici! "Yanzu Hajiya har wata banza ta fi ni a gurinki? kece fa ki ka haifi ubana amma 'kiri-'kiri ki ke nuna min 'kiyayya! meye a ciki don kin bashi umarni ya mayar dani, ai d'an adam ajizi ne, kuma kowa yana lefi, nayi nadama na bashi hakuri ko don darajar zuriar dake tsakaninmu ai ya kyautu ya tausaya min." Hajiya ta ta'be baki da cewa" Yanzu ki ka san da haka, kina maganar zuria sau nawa kina zubar masa da ciki? itama Shukuran Ubangiji ne yasa zata zo duniya shiyasa ya nuna miki ishara! saboda haka yanzu ni na dawo daga rakiyarki Fatima ki nemi miji kawai kiyi aure don ni ba zan sa Alhaji Habu ya dawo dake ba alhalin baya ra'ayi." Hajiya Fatima bakin ciki kamar ya kasheta ya zama dole ta shirya zuwa jibia domin ta samu Baba Audu da maganar tana ganin idan ta biyo ta kansa bu'katarta zata biya. Ni dai na sauko na gansu jigum-jigum! muka had'a ido da ita sai kawai naga ta galla min harara! idonta yayi fululu! da alama kuka tayi, abin ma sai ya bani dariya amma banyi ba, nayi saurin dauke kaina daga kanta. Hajiya ta kalle ni da kulawa take tambayata Na ce" Zan shiga kicin ne domin samun abinda zan ci yunwa nake ji." Fad'in Wannan maganar nayi sai naga Shukura tana motsi da bakinta tana min wani irin kallon banza! na san dani take, amma ban tanka mata ba kawai nayi hanyar kicin din, Hajiya ta ce." Da kin bari ma yanzu Marka zata fito ta shirya mana gurin cin abinci domin tana ciki tana aiki." Sai na tsinkayi maganarta tana cewa" Jakar mata kawai dama ai irinsu ci gare su mussaman an samu shinkafa 'yar gwamnati da jar miya ai sai abinda muka gani." Tayi maganar ne da sauti mai k'arfi don na ji, kuma sa'konta ya iske ni domin duk na karanci inda ta nufa, wato neman masifa take dani daga zuwanta. Hajiya ta bude baki kenan za tayi magana na ce"Hajiya rabu da ita don Allah! domin duk na fahimci abinda take nufi da ni, to ni dai ba karya bace ballananta nayi ta haushi! sai an kula kashi yake d'oyi! Aikuwa! da fad'in wannan maganata tawa sai suka fusata! Shukura kaina tayo tana d'ura min ashar da fad'in" Sai dai idan ni ce karya amma ba Mommynta." Na kalle ta da cewa" Kin ga da wacce zanyi domin ita ce daidai da ni, ke baki isa nayi hayaniya dake ba sai da wannan." Na fad'a ina nuna uwarta dake zaune tana mamakina! domin bakinta mutuwa yayi, yanda na fuskanta tana mamakin yanda akai nake mayar mata da martani. Darajar Hajiya kawai tasa na saurara musu na haye sama zuciyata sai tafasa take, dole ne idan ya dawo ya yi wa tufkar hanci domin ba zan lamunci cin mutunci ba. [1/19, 10:35 AM] Bintu: 100&101 Jama'a da yawa sun yi mamakin ganin daya daga cikin motacin 'Dangaske na kutsa kai cikin layin dake tattare da kwazazzabai tare da kwatoci da tsibiri-tsibirin bola dake jibge a bakin kwatar. manya da yara suka dinga bin motar da kallon mamaki da tunanin dalilin da yasa motar shigowa layin, To duk da cewa; ya shirya shiga unguwar da daddare hakan bai hana mutane fahimtarsa ba. abinda baya b'ukata kenan k'allo da surutun jama'a, hakan ne ya faru domin dai yara da manya cika su kayi suna bin motar da kallo har Sule ya damu guri ya tsaya daf da kofar gidan Baba Asabe. Aikuwa kafi ki ce kwabo wani yaro ya shiga gidan da gudu yana fad'in"Baba motar 'yan sanda ta tsaya kofar gidanki." Domin shi duk a tunaninsa motar 'yan sanda ce ganinta zungureriya baka wuluk! domin tintac ce ba a ganin wanda yake cikin sai dai na ciki ya ga na waje. abinda yasa jama'a suka fahimce shi saboda sunansa dake bayan motar 'Dangaske14 duk motacinsa na sufiri (zirga-zirga) sunan dake jiki kenan, shiyasa duk inda ya shiga baya 'buya jama'a sai sun sheda shi. Baba dake lissafin kudi ta kalli yaron da faduwar gaba ta ce."Laminu 'yan sanda kuma? wane dalili ne ya kawo su gurina?" Ya ce."Wallahi nima ban sani ba." yana fadin haka ya ruga a guje ya fita daga gidan Gaza samun nutsuwa tayi ta suri mayafi ta d'ora a kanta don fargaba ta hana ta tsaya ta yafa mayafin a jikinta, da sauri ta kama hanyar fita tana salati, Saliha itama ta fito daga cikin d:aki gabanta sai dukan uku-uku! yake amma tsoro ya hana ta fi bayan kakar. Hayaniyar jama'a ta cika gurin, yana so ya fito daga motar abin ya gagara domin dai yara da manya ne su kayi dafifi! a jikin motar, sai kace wani d'an siyasa! jama'a sai kambaba darajarsa suke tare da yi masa fatan alheri akan abubuwan da yake na alheri, sam bai ta'ba tsammanin cewa; zai samu wannan karamcin daga gurin jama'a ba. Sule da Escorts d'insa suka dinga fama da mutane, cewa; suyi hakuri su bashi hanya ya fito domin gabatar da uzurinsa. Baba Asabe ta kutsa gurin tana tambayar abinda yake faruwa.Sule yake mata bayanin wanda yake cikin motar kuma gurinta yazo. Kallon mamaki take masa bakinta yayi nauyi ta rasa abinda za ta fad'a, shin me ya kawo wannan Attajirin gurinta? Allah yasa dai ba wani sharrin aka 'kulla mata ba, domin dai tunda Shahida tayi mata gargadi ta daina sakin baki tana aibata shi a gaban jama'a. A sanyaye ta koma cikin gidan tana shedawa Saliha abinda yake faruwa, Ita kuma shashashar sai ta raya a ranta cewa; ko ita yake so, tana farin ciki ta ce" Watakila ko ni ya gani yake so. Baba tayi mata wani irin kallo kafin ta ce" A gidan uwar wa zai gan ki har ya ce yana sonki, bana son rashin hankali da shashanci! maza ki kira min babanki a waya! domin dai gabad'aya na tsorata da al'amarin wallahi." Saliha da sauri ta shiga d'aki hannu na rawa ta kira Kawu a waya ta sheda masa cewa; Maza ya zo Babarsa tana nemansa. Ta fito ta samu Baban a tsaye tana tunani ta ce" Na kira shi ya ce yana kan hanya. Baba talfe ha'ba da hannunta jikinta yayi masifar sanyi duk ta tsure! sai tunane-tunane take. ita kuwa Saliha sai murna take cikin zuciyarta tana addua Allah yasa saboda ita mutumin ya zo gidan. Yana zaune a cikin motar yana ganin yanda yaran nasa suke fama da jama'a, amma ko gezau! sun ja tunga sun'ki barin gurin, kamar ma jama'a k'aruwa suke a gurin, domin duk wanda ya zo wuce wa ya ji wanda yake cikin motar sai ya tsaya domin dai (Bangon sukari) ne a gurin kowa ya jingina dashi sai ya lasa. A hankali ya sauke gilashin motar ya fito da kud'i masu yawan gaske ya bawa Sule da saurin gaske ya zuge gilashin yana murmushi ganin yanda hayaniya ta 'kara tashi a gurin sakamakon hango shi da sukayi. Kud'i kenan masu raba gardama! kamar dama abinda suke jira kenan, sai suka yuya yuuuu! suka bi bayan Sule dake rike da damin kudin a hannunsa. Wannan ya bashi damar bude motar wuf! ya shiga soron gidan, yana godewa Allah a zucci da fili na yanda ya azurta shi da dukiyar da yake taimako da ita "Allah ya kara rufa mana asiri." Ya fadi wannan kalma a fili. Gyaran murya yayi kafin yayi sallama cikin gidan. Baba ta amsa cikin sanyin jiki ta shimfida tabarma mai tsafta sannan ta ce"Alhaji shigo daga ciki." Ya shiga da wata sallamar a bakinsa, 'kamshin turaransa ya cika gidan. takalmansa ya cire kafin ya zauna kan tabarmar ya saki fuska sosai yana gaisheta amma da muryar Baban- baba yayi hakan ne domin ya samu saukin fahimtar da ita abinda yake tafe dashi. Itama gabanta ne ya fadi jin muryar mahaukacin nan mijin jikarta da kullum take mafarkinta sai kawai ta zuba masa ido gabanta na dukan uku-uku! Abin mamaki! sai ga Saliha ta fito cikin kwalliya tana 'kamshin turare ta tsuguna tana gaishe shi, ya amsa yana murmushi tare da cewa; Ke ce Saliha ko?" da sauri ta daga kanta tana wasa da yatsun hannunta, ya sake wani murmushin kafin ya ce." Shahida tana gaisheki." Gabad'aya sai suka kalleshi da mamakin jin furucinsa. Baba Asabe za tayi magana kenan. Kawu ya shigo a fujajan! yana fadin" Wai me yake faruwa ne a waje! jama'a sun cika sai hayaniya suk.....maganar ce ta ma'kale a bakinsa ganin wanda yake zaune, duk da babu wadataccen haske a tsakar gidan sai da ya sheda wanene a gurin, haba ashe shiyasa ya ga dan'kareriyar mota a fake a kofar gidan. Takalmansa ya cire da sauri ya mi'ka masa hannu da fadin"Yallabai barka da dare ?" Ya rike hannunsa da kyau! kafin ya ce."Barka dai Kawu kayi mamakin magani na ko?" Kawu ya ce."Kwarai kuwa Yallabai Allah dai yasa ba wani gagarimin lefi mu kayi ba." Murmushi yayi wanda yake kara masa haiba da kwarjini ya ce." Ni nayi muku lefi Kawu, amma yanzu na zo gareku ne domin ku gafarce ni." Kawu ya nemi guri ya zauna da al'ajabin abun a tare dashi ya ce."Ranka ya dade lefi kuma? wane iri kenan?" Ita kuwa Baba Asabe kasa magana tayi kawai dai tana zaune ta zubawa sarautar Allah ido tana dai jinsa har ya fara basu labarin abinda yake faruwa, kamar yanda yayi musu bayanin asalinsa da farko yanzu ma sai da ya sake jadadda musu, sannan ya fahimtar dasu dalilin da yasa ya sauya kammani domin neman matar aure, tabbas hakan na iya faruwa mussaman idan anyi duba da irin gwagwarmayar da ya sha a baya, ba lefi bane don ya nemi matar aure ta wannan sigar, ya sake yi musu cikkaken bayanin kansa cewa; Shine Alhaji Habu, wanda jama'a suka fi saninsa da 'Dangaske, kuma shine Baban-baba wannan mahaukacin da yazo ya auri 'yarsu cikin talauci da rangwamin gata. Baba Asabe ta dinga tasbihi ga Ubangiji tana kad'aita shi! wannan al'amari ya bata tsoro mutu'ka wato dai shi Ubangiji ba a yi masa wayo kuma ba a yi masa dubara, tayi kuka sosai a lokacin da ta rabu da yarinyar, kuma duk sanda ta tuna cewa; wanda ta aura bashi da cikakken galihu tana shiga tashin hankali mai tsanani! ba komai take tunawa ba sai mahaifiyar yarinyar da kuma lalurar da take tare dashi, amma sai ta fawwalawa Allah ta bar abin cikin ranta, sai dai duk daran duniya tana tashi tayi wa yarinyar adduar samu kwanciyar hankali da rayuwa mai kyau! sai gashi adduarta ta kar'bu! ashe wanda yarinyar ta aura nagartaccen mutum ne irin wanda yake wahalar samu, hakika ha'kuri da tawakkali yayi wa Shahida rana wannan shine matakin nasara, babu wani abu da ake samunsa kai tsaye ba tare da an fuskanci kalubale ba, Yarinyar tasha gwagwarmaya ta rayuwa, amma da tayi hakuri ta fawwalawa Allah sai gashi yayi mata alheri mafifici. Gabad'aya suka kasance cikin walwala da farin ciki idan ka cire Saliha daga cikinsu,kasancewa tayi cikin k'unci da bakin ciki, ido cike taf da hawaye ta tashi ta shiga daki ta kwanta sai kawai ta rushe! da kukan takaici! yanzu ace wai kamar Shahida kurma ita ce ta mallaki hamsha'kin mutum mai daraja wanda duniya tasan dashi ta sanya masa rigar arziki shine mijinta to ita kuma wa zata aura ? bayan ta san tafi Shahidan kyau nesa ba kusa ba, kuma duk samarin dake zuwa gurinta talakawa ne, domin saurayinta na farko da a ka sanya musu ranar aure, saboda bashi da gidan kansa tace ba zata aureshi ba, babu yanda ba a yi da ita ba ta bijire sai mayar masa da kudinsa akai, a halin yanzu kuma babu wanda yake zuwa gurinta da maganar aure! dole hankalinta ya tashi da jin wannan al'amari! a ce yarinyar da takewa dariya muskiniya wai ita ce ta auri d'aya daga cikin attajiran da ake ji dasu a duniya. kuka sosai ta dinga yi tana shar'ben majina. Yayin da su Baba suke kwasar garar alheri daga gurin dattijo mai halin dattako mutumin da ya dauki kansa dai-dai da kowa duk kuwa da cewa; Ubangiji yayi masa baiwar ilimi dukiya nutsuwa wadatar zuci hankali da kuma hangen nesa da sanin ya kamata, hakan bai sanya ya ajiye kansa a wani bigire na daban ba, ko da yaushe mu'amula yake dai-dai da mutane, ya ajiye hakan a ransa cewa shima ba kowa bane a wannan duniyar, tunda tun kafin zuwansa anyi ire-irensa da yawa, akwai wad'anda suka wanye lafiya kafin mutuwarsu, akwai kuma wad'anda su kayi mutuwar wulakanci bayan Allah ya 'kwace damar da ya basu saboda sun d'auki kansu wata tsiya har suna jin kai isa da izzah! uwa uba girman kai! duk mutumin da Ubangiji ya azurta da dukiya ba wai ya azurta shi ne saboda ya fi sonsa a cikin bayi ba, a'a jarrabawa ce daga gareshi, daga lokacin da ya ga kana ta'kama da izzah! tare da nuna kamar kai kayi wa kanka da wulakanta mutane sai yayi maka kwaf d'aya! zai iya saukar da ibtila'i akan dukiyar taka sai ka wayi gari baka da ko kwabo. karshe wanda ka ke wulakantawa ya zama shi yake taimakonka. to wannan dalilan yasa D'angaske baya d'aukar kansa wata tsiya, kuma bai ta'ba sanyawa a ransa cewa; zai dawwama da dukiyarsa ba, watakila kafin mutuwarsa Ubangiji ya kar'ba ya bawa waninsa. Kyautar kudi masu kauri yayi musu, sannan ya roki alfarmar Baba Asabe ta daina sayar da abinci, duk abinda take bukata na rayuwa yayi al'kawarin d'auke mata! kana yayi wa Kawu Al'kawarin bashi jari mai kauri domin ha'baka kasuwancinsa. Wannan gida kuma da Baba ke ciki za a rushe a gina na zamani gobe za a fara aikin. Baba Asabe kasa daurewa tayi ta dinga kuka tana godiya tare da yi masa fatan alheri da gamawa da duniya lafiya. Cikin jin dadi da farin ciki yake amsawa domin ya ji dadin yanda suka fahimce shi, sai suka 'kara martaba a idonsa yayi musu godiya mai yawa ya kuma ce su zauna a shirye cikin 'yan uwa ga duk wanda yake da bukatar zuwa gidanshi zai turo da motaci a d'aukesu, hakan ya 'karawa Baba Asabe kwarin gwiwa, In sha Allah gobe da wuri za ta fita domin ta shedawa 'yan uwa da abokanan arziki abinda yake faruwa. Cikin mutunci da karrama juna su kayi sallama. Kawu ya take masa baya abin mamaki! suna fitowa waje sukayi arba da cincirindon mutane har sun fi na da yawa. ganin Fitowarsa gurin ya hautsine, ya dinga d'aga musu hannu yana godiya yayin da Kawu ke kokarin kare shi da hannuwansa ganin yanda wasu daga cikin mutanan ke ja masa babbar rigar jikinsa wai ya taimaka musu. suna da yawa sosai! babu halin ya tsaya ya saurari Uzurinsu, sai da ya samu nasarar shiga mota tukkuna ya ce da Sule ya bawa mutanan hak'uri amma duk mai bukatar ganinsa ya je gidansa dake giginyu ya same shi amma sai 'karshen wata domin gobe da wuri yake so ya tashi. Sule ya sheda musu abinda mai-gidansa ya ce sannan fa aka samu sau'ki suka fara watsewa daga gurin, wannan ya bawa Sule da escorts dinsa damar shiga motar. Sule ya tashi motar Kawu ya daga masa hannu da fadin" A sauka kafiya Yallabai mungode sosai Allah ya 'kara girma." Shima hannun ya daga masa yana godiya kafin ya sauke gilashin. lokacin motar ta fara 'kokarin fita daga layin. hakan ya bawa jama'ar da su kayi saura a gurin damar bin bayan motar suna ta bambad'anci mussaman matasan da basu da aikin yi duk a 'kokarinsu na ya za a yi su samu wani taimako daga gurinsa. [1/20, 11:32 AM] Bintu: 102&103 Ganin tunda ta hau sama bata sauko ba yasa Hajiya yanke shawarar bin bayanta, hakika itama ta ji takaicin abinda akayi mata na rashin kyautawa, zahirin gaskiya zaman Hajiya Fatima a gidan ba zai haifar da alheri ba domin duk ta fahimci abinda take nufi wato tana so ta dawo gidan su had'a kai da 'yarta su cizgunawa yarinyar mutane to gaskiya ba zata yarda da wannan al'amarin ba. Ina kwance kan kujera abin duniya ya yi min yawa Hajiya ta turo kofar dakin ta shigo da sallama a bakinta. Zaune na tashi tare da kokarin daidaita yanayin fuskata. Gefe na ta zauna fuskarta babu yabo babu fallasa! Nima nayi 'kokarin kawar da damuwata. na sake gaisheta a karo na biyu ta amsa cikin kulawa kafin ta d'ora da fad'in abinda ya shigo da ita. Murmushin takaici kawai nayi zuciyata na wani irin turiri! domin a lokacin idan nayi magana zan iya fashewa da kuka saboda b'acin rai! Ta ce" Don Allah kiyi hakuri kin ji ko, in sha Allahu za a yi wa tufkar hanci! idan mijinki ya dawo duk zan sheda masa abubuwan da suka faru domin ita kanta Fatiman idan bakya bukatar ta a gidanki to dole ta daina zuwa tunda ba alheri ne yake kawo ta ba. Da mamakin maganarta na kalleta na ce"Hajiya ya za ayi na raba zumuncin dake tsakaninsu? 'yar uwarsa ce fa, kuma uwar 'yarsa tilo d'a yake da ita a duniya, ni kuma wacece da zan hana ta shigowa gidan nan." Tayi murmushi da cewa" Duk dan a samu zaman lafiya yasa nayi wannan maganar, Fatima jika ta ce, domin ni na haifi Ubanta to amma bana 'kaunar halayenta saboda bata da kirki! wannan dalilin yasa na yanke shawara cewa; idan mijinki ya dawo ya tsawatar mata! sannan itama Shukura dole ta fuskanci hukunci akan abinda tayi miki, ai duk 'kan'kantar ki a matsayin uwa ki ke a gurinta tunda kina auran ubanta." Girgiza kaina nayi tare da cewa; A'a Hajiya kada kiyi haka don Allah! domin ba naso daga zuwa na gidan nan wata matsala ta faru mara dad'i! wallahi gabad'aya idan sun fahimce ni to zamu zauna lafiya da juna, domin bana son tashin hankali! kawai ki bar maganar kada ki fada masa da kaina idan ya dawo zan masa bayani sai yayi wa tufkar hanci." Ta ce"To shikkenan tunda kin ce haka, amma don Allah ki 'kara hakuri kuma ki saki jikinki gidanki ne babu wanda zai nuna iko domin ni ba zan yarda a had'a baki da ni a cutar da ke ba." Cikin jin dadin furucinta na ce"In sha Allahu Hajiya Na gode sosai da kulawa kuma nayi miki alk'awarin cewa zan yi iyakar bakin k'okarina a gidan nan, Allah ya kawar da sa'bani a tsakaninmu.' Ta amsa da ''Ameen suma ameen sannan ta ce" Ai tuntuni mijin naki ya kira wayar Shukura ya ce" Ta fada miki cewa ba zai samu damar dawowa yau ba saboda wani dalili sai dai gobe idan Allah ya nufa. Duk da ban ji dadin hakan a raina ba. amma ban nuna a fuskata ba na ce"To shikkenan Allah ya dawo dashi lafiya ai da yau da goben duk d'aya ne." Tare muka sauka 'kasa nan muka same su a zaune sun yi baja-baja da kaya da alama ta kwance jaka ne Shukura sai duba dogwayen riguna take. Da saurin gaske na d'auke kaina kai tsaye gurin cin abinci na nufa, ita kuma Hajiyan ta je ta zauna kan kujera tana kallonsu. Abincin na zuba daidai cikina na ci na k'oshi ban sake bi takansu ba har na kammala. na ta shi a nutse na isa gurin da Hajiya take zaune nayi mata sallama. Kai tsaye sama na nufa kawai na ji muryarta a bayana tana kiran sunana. "Anti Shahida." Na tsaya ina kallonta da mamaki! sosai a tare dani kamar ba ita ce ta gama d'ura min ashar d'azu ba. Ta miko min wata leda da fadin "Wai gashi in ji Mommy tsarabarki ce." Na bi ledar da kallo ina nazari. Ta ce"Ki kar'ba don Allah kuma kiyi hakuri akan abinda ya faru d'azu tsautsayi ne ba zan sake ba." Na sa hannu na 'karba da cewa"Kada ki damu ni dama ban ajiye abin raina ba ballanatana ya dame ni, Na gode sosai Allah ya bamu hakurin zama da juna." Da farin ciki a fuskarta ta amsa da "Ameen Anti." Da ledar a hannuna na isa gurin da hamsha'kiyar ke zaune tana waya, sai da ta kammala tukkuna ta kalle ni, babu yabo babu fallasa na ce"Shukura ta kawo min tsaraba duk da ban duba ba ina godiya kwarai Allah ya kara arziki." Ta amsa da murmushi a fuskarta kafin ta kai hannu ta dauki d'aya wayar dake gefenta wacce take ta kuwwa! ganin tana amsa waya yasa na sake yi wa Hajiya sallama a karo na biyu na hau sama da tunanin abubuwa da yawa a raina. Sai da ta gama wayar tukkuna Hajiya ta kalle ta da fadin"Yanzu hakan ai ya fi alheri da mutunci. wannan yarinyar dai a haife kin haifeta domin duka bata fi Shukura a shekaru ba, amma tana da hankali da nutsuwa irin na masu yawan shekaru, don Allah ki zauna lafiya a gidan nan har ki gama kwanakin da za ki yi ki tafi tunda dai kin 'ki aure kin fi bukatar zamanki a haka" Shiru kawai tayi mata ba tace komai ba sai wani irin murmushi dake fuskarta shi ba na farin ciki ba, shi ba na bakin ciki ba. *** Kwata-kwata ban yi tsammanin dawowarsa da wuri ba, shiyasa dana yi sallar asubahi na koma na kwanta bacci mai nauyi ya d'auke ni. Mafarki nake ko a gaske ne? yanda dai al'amarin yake ratsa min jiki da k'okarin tayar min da hankali yasa na tsorata! na zabura! da sauri na bud'e idona jin nauyi a kaina tare da jin ana tatta'ba wasu guraran na jikina uwa uba k'amshin turaransa da ya cika min hanci, wannan ya tabbatar min da cewa; ba mafarki bane. idona na bud'e da saurin gaske! fuskarsa daf da tawa yana kokarin had'a bakina dana shi. a tsorace! na ture shi ya fad'i saman gadon yana bina da wani gigitaccen kallo. Ni kuwa gabad'aya hankalina a tashe yake kallonsa kawai nake sai kace majanunin! (mahaukacin!) gaske. da suffar Baban-baba ya dawo gare ni. Ya tashi zaune yana murmushi har ila yau da muryar Baban-baba ya ce."Meye abin firgita! ni ne fa mijinki majanuni! na dawo da bege da kwad'ayi tare da ishirwarki! ki taimaka min a cikin wannan yanayi." Kukan takaici ne yake kokarin 'kwace min. na ce"Wallahi ka d'auki alhakina! ka bani tsoro me yasa zaka shigo min da wannan suffar! ka cire wannan yagaggiyar rigar ta jikinka, da kuma wannan fuska da kasa domin ba kayi kyau ba." Tsakani da Allah nake maganar hawaye na kwaranya daga idona. Hankalinsa a kwance ya ce."Kefa ki ka ce kin fi bu'katata a haka. ashe dan na zo miki da wannan suffar da ki ke so ba wani abu bane a gurinki, tunda dama a haka ki ka aure ni." Rintse idona nayi na ce"To yanzu na ce bana bu'kata! zahirinka nake so da 'kauna." Ya 'kara nutsuwa a cikin kogin kaunarta, yarinyar ta riga ta gama kamashi dumu-dumu! tunda bata jin nauyin fad'a masa abinda ke cikin zuciyarta. "To na ji bu'de fuskarki ki ga wani abu." Jin haka yasa na bud'e fuskata ina kallonsa yasa hannuna ya tattago fuskar dake cike da gashi mai furfura! duzaza! babu kyawun gani ya cire ya ajiye asalin fuskarta ta bayyana! ajiyar zuciya ya sauke ya sauko daga gadon, nan na dinga bin ilahirin jikinsa da kallo, fatarsa a bushe duk tayi duhu tayi wani irin kamar dai lokacin da ya shud'e! ya kama hannuna muka shiga bandaki a tare ina tsaye ina kallonsa ya had'a ruwan d'umi! ya cire yagaggiyar rigar jikinsa ya rataye kafin ya fara kokarin cire gajeran wandon jikinsa, da sauri na kama kofar band'akin zan fita, ya sha gabana da cewe; babu inda za ki sai kin tsaya kin kalli zahirin mijinki domin a yau ina so ki san waye Abubakar Saddiku". Gabana na fad'uwa na ce"Wane irin sani kuma bayan wanda nayi maka" "Ina so ki fita daga cikin zargi ne, ki san cewa; na sauya hallitata ne saboda ke, domin takanas ta kano na je india nayi tsayin sati hud'u domin shirya yanda al'amarin zai kasance." Na ce"Wallahi na amince da hojjojinka domin babu wani sauran zargi a tare dani tunda dai yanzu na ga zahiri don haka ka rabu dani kawai na fita sai kayi wankan." Ya girgiza kansa yana lumshe ido ya ce."So nake na wanke jikina da ruwa a gabanki domin ki sake gazagata waye ni? dan har yanzu akwai sauran abinda baki sani ba. Kokarin magana nake kawai naga zura sakata kuma tsawo na ba zai kai ba ballanatana na bud'e, ina kallo ya fara cire wandon jikinsa na juya bayana gabana sai fad'uwa yake lallai mutumin nan bashi da ta ido. Motsin ruwa na fara ji hakan ya tabbatar min da cewa; ya fara wankan, na sauke ajiyar zuciya ko kusa ban yi gangancin juyawa na kalle shi ba har sanda na daina jin motsin ruwan. Ba zato na ji ya kinkime ni kuma babu komai a jikinsa, gabad'aya ya manne ni a kirjinsa ruwan daya kwanta kan gashin kirjinsa ya ji'ka ni! tsigar jikina ta tashi. ture shi nake ina kokarin sauka yana sake talfe ni har sai da ya tsunduma ni cikin kwamin wankan dake cike da ruwan d'umi! sannan hankalinsa ya kwanta. na rufe idona tsabar tashin hankalin dana gani girmansa a zahiri ya tashi tsaye! jikina jagab! da ruwa ina yoyo na fara kokarin fitowa daga kwamin wankan, sai yayi saurin shigowa ciki ya mayar dani na fad'i cikin ruwan! yayi fallatsi! har cikin idona! kuka mai k'arfi nasa! tare da rufe fuskata da tafukan hannayena cikin takaici na ce"Wai meye haka? don Allah ka suturta jikinka." be ce min komai ba ya zauna kusa dani kawai ya sani a jikinsa yana kokarin cire min tufafin da suka jik'e. Ban san lokacin dana bud'e idona ba da tsoro ! na kallonsa nan na hango tsantsar fitina cikin idonsa don gabad'aya sun sauya kala duk girmansu sun 'kankance! kuma jikinsa sai wani irin karkarwa yake kamar wanda zazzabi yayi masa mugun kamu. Wata irin runguma ya yi min a cikin ruwan ya turmushe ni bayan ya samu nasarar cire min tufafin jikina, gabadaya ya gigice! ya fice daga hayyacinsa ya dinga bin ilaharin jikina da zafafan! kesses har sai da ya samu nasarar janye hankalina domin ya riga ya gama fahimta abinda na fi bukata shiyasa ya mayar da hankalinsa gurin, a cikin ruwan dai mai afkuwa ta afku! hankalinmu bai kwanta ba sai da muka samu gamsuwa sannan muka dawo nutsuwarmu. Kunyarsa nake ji sosai! hakan yasa na kasa kallonsa a lokacin da yake wankan tsarki! cike da farin ciki da annashuwa! sai da ya fita daga bandakin sannan na samu sararin yin nawa wankan na fito na same shi zaune a gefan gado har ya shirya yana waya da abokinsa A gurguje na kimtsa jikina na samu guri na zauna amma ban iya kallonsa ba saboda har yanzu na kasa manta abinda ya faru a tsakanimu. Hannuna ya ri'ke sai na kalle shi naga yana 'yar dariya, duk sai na tsargu! nayi saurin sunkuyar da kaina. Ya ce."Ina fatan wannan had'uwar tamu ta haifar da alheri a jikina nake jin cewa; nayi ajiya mai muhimmanci." Cikin nazari nake kallonsa domin ban fahimci maganar tasa ba. ya zura hannunsa kasan rigata ya ce."Ina da burin samun zuria masu yawa dake." Ajiyar zuciya na sauke ina kallonsa yana cikin wani irin yanayi zahirinsa ya nuna abinda yake d'ankare a cikin zuciyarsa, tabbas haihuwa rahama ce, sosai na tausaya masa na ce"Allah Ubangiji ya bamu masu albarka." Ya amsa da "ameen" ya kanne min ido da fadin"Ya ki ka ji had'uwarmu ta yau?" Tsira masa ido nayi da nazarin maganarsa. Yasa hannu kan bakina ya ce."Akwai dad'i a cikin ruwan ko? don naga ba ki yi kuka ba, sai ma taimako da ki ka bani." Kunya ta rufe ni, ashe abinda yake nufi kenan? da farko ban fahimci maganarsa ba. Shiru nayi masa na kasa magana sai dai tsabar mamakinsa da yake kashe ni. Ajiyar zuciya mai k'arfi ya sauke! yana ta murza tafin hannuna dake cikin nasa, na kalle shi. nan naga yanda idonsa ya sauya! da sauri na cire hannuna na matsa daga kusa dashi, na fahimci idan na biye masa sai mu yini muna abu daya, ni har mamaki yake bani yanda yake da kuzari da muzakkaranci tamkar bai kwana biyu a duniya ba. "Tashi mu sauka kasa mu samu abinda za mu ci." Ya fad'a yana k'okarin tashi. Na kalle shi yana gyara doguwar jallabiyar dake jikinsa. Sunkuyar da kaina nayi Na ce"A haka zaka sauka dubi jikinka fa?" Ya ce."Ya za a yi to?" ya fad'a tare da yi min wani irin kallo yana lumshe idonsa . A nan na fahimci abinda yake nufi. wanda ni kuma nake ganin ba zan iya ba gaskiya. Na girgiza kaina tare da sake kallonsa a karo na biyu har yanzu girmansa yana nan a bayyane da yake rigar dake jikinsa irin mai kwanciya a jiki ce na ce"Ka dai kira waya a kawo abincin ina ganin hakan ya fi akan ka sauka a haka." sai ya zauna kusa da ni. ya fito da wayarsa ya kira Shukura tare da bata umarni. 'Kokarin tashi nayi daga kusa da shi. saboda ina jin kunyar ta shigo ta same mu a manne da juna, amma sai ya hana ni tashi ya sake matsowa jiki na, a haka ta turo kofar dakin ta shigo dama a bude ya bar kofar lokacin da ya shigo. ni dai da 'kyar na iya amsa gaisuwarta don ban iya hada ido da ita ba saboda kunya sai bayan ta fita daga dakin sannan na iya d'ago kaina. [1/21, 12:08 PM] Bintu: 104&105 A tare muka ci abincin. Cikin nutsuwa yake bani labarin zuwansa Kano da kuma sa'kkonin gaisuwa da a ka bashi zuwa gare ni, amma kuma ko da wasa bai sanar da ni irin alherin da yayi wa iyaye na ba, ya ce min dai ya je ya gaishe su kuma suna nan lafiya kalau. Sosai nayi farin cikin jin hakan daga gare shi, dama kullum tunani na yana kansu. Na kalle shi tare da cewa" Ni yaushe zan je na gaishe su?" yana goge bakinsa da tissue ya ce."Sai an kwana biyu tukkuna." Na ce"Ban gane sai an kwana biyu ba?" Babu kunya ya ce."Sai kin samu ciki sannan." Shiru kawai nayi ina kallonsa da auna maganarsa, shin meye manufar hakan to? ganin ina kallonsa yasa ya ce" 'Karshe watan nan dai in sha Allahu zan tura da mota ga duk mai bukatar ya zo ya ga d'akinki hakan ya yi miki ko?" Ajiyar zuciya na sauke na ce"Eh ya yi mun gode sosai da karamci." Murmushi kawai yayi bece komai ba ya dauki wayarsa yana dubawa. sai na tashi na je na d'auko tsarabar da Hajiya Fatima ta ba ni, dama ban duba ba, na zauna kusa dashi ina kwance ledar. Ya ajiye wayar hannunsa yana kallona har na fito da doguwar riga mai kyau da tsada da kuma mayafi shima da ka gani mai tsada ne irin na manyan mata. Ya ce."Wannan fa?" "Hajiya Fatima ce ta bani tsaraba jiya ta dawo." na fad'a ina dudduba rigar. gaskiya tana da kyau sosai! Ba tare da ya ce komai ba ya d'auki wayarsa ya cigaba da dubawa. Na kalle shi babu yabo babu fallasa na ce"Ka taya ni godiya a gurinta." Nan ma uffan be ba min ba hankalinsa ma yana kan wayarsa. Na d'an 'bata rai da fad'in "Wai ko dai kana hira ne da budurwarka?" Kallona ya yi. sai na sake shan kunnu! na ce"To idan ba haka ba mai zai sanya muna tare kawai ka d'auki waya kana kallo. bayan na nuna maka abin alheri har ina ro'kon ka taya ni godiya a gurinta amma ka share ni." Ya ce"To ya ki ke so ayi ? ko kiranta zanyi a waya ne?" Yanda ya fadi maganar a harzuk'e yasa na fahimci cewa; bashi da bukatar maganar. Na ce"Ai tana cikin gidan nan ma." Da mamaki a tare dashi ya ce"Tana cikin gidan nan tun yaushe kenan?" Na ce"Tun shekaran jiya da ta dawo nan ta sauka." Fuskarsa ta sauya da b'acin rai! na ce"Wai don Allah me yasa ka tsane ta ne? 'Yar uwarka ce fa, sannan kuma uwar 'yarka tilo." Hannu ya d'aga min da fadin" Yanzu zamu 'bata idan ki ka sake yi min irin wannan maganar. Na dinga kallonsa da mamaki sosai a tare da ni na ce" Kayi hakuri don Allah idan nayi kuskure amma ni a gani na kamar abinda ka ke bai dace ba, kai babba ne dole kai za kayi hakuri a matsayinka name hankali bai kamata kuna irin wannan zaman ba." Ya ce"Idan na fahimta kina so ki ce min na dawo da ita dakinta ko me?" Gabana ya fad'i! da sauri na ce"A'a ni ba nufi na kenan ba, so nake na daidaita tsakaninku." Wani irin kallo yayi min. Cikin takaici ya ce."Duk lokacin da ki ka sake yi min maganar Fatima a gidan nan to zaki sha mamaki." Yana gama maganarsa ya je ya kwanta kan gado tare da rufe jikinsa da bargo, tsayin zaman da nayi da shi ban ta'ba ganin 'bacin ransa ba sai yau. Ganin haka yasa na sauka 'kasa domin na d'ebe kewa da mutan gidan. Duk suna zaune falo suna hira, sai dai kuma uwar kwalliyar da Fatima ta yi ta ba ni tsoro sai kace wacce zata fita gasar sarauniyar kyau! wani ubansun material ne mai mugun tsada da akayi mata doguwar riga fitted gwon dinkin ya fitar mata da suffar jikinta ta ko'ina dama tubarkallah cikakkiyar maca ce ta ko'ina, tayi wani irin d'aurin dankwali. bayan uban gold din da ta yi ado da shi, ga kwalliyar fuska har da su gashin ido, gaskiya tayi kyau sosai tamkar amarya falon gabad'aya k'amshin turaranta yake. Jiki babu 'kwari na isa kafin na zauna kan kujera sai da na fara gaishe da Hajiya ta amsa fuska a sake take fad'in"Maigidan bai tashi bane?" Na ce"Eh ai bai jima da kwanciya ba. Ta ce"Ayyo ko da na ji." Na kalle ta da k'okarin danne damuwata na ce"Hajjaju mun tashi lafiya?" Ashe fasa mata kai na yi dana kira ta da wannan suna. ta wani amsa kamar bata so tana taunar cingum! Na d'auke kaina gabana na fad'uwa kad'an-kad'an! gabad'aya hankalina ya tashi domin bana bu'katar mijina ya sauko ya ganta da wannan uwar kwalliyar wanda nake da tabbacin cewa; Saboda shi ta yi. Shiru ne ya biyo bayan zama na a gurin. kafin su cigaba da hirarrakinsu wanda ba sosai nake ji ba saboda lalurata! sai gabad'aya duk na tsargu! don gani nake kamar za su iya gulmata, duk da Hajiya tana zaune a gurin hakan bai sanya na saki jikina ba. Marka mai aiki ta fito daga kicin, gani na a zaune a gurin yasa ta tsuguna har kasa tana gaishe ni, na kalli girma da shekarun matar, a shekaru ta kusa kai wa Baba Asabe. Na ce"Marka idan zamu gaisa ki daina tsuguna min don Allah." Murmushi kawai tayi ta kalli Hajiya da fadin." Yau me za a girka?" Hajiya ta kalle ni kafin ta bata amsa da cewa; Ga matar gidan nan ita zaki taimabaya." Hajiya tayi hakane duk a kokarinta na bani ha'kkina. na kuma ji dadin hakan. Na ce"Marka ayi abinci mai dad'i! amma zan shigo kicin din da kaina zanyi na mai-gidan." Ta ce."To Hajiya." Tashi tayi ta bar gurin da sauri. Minti biyar a tsak'ani na tashi na bi bayanta, na san kallo suka bini dashi saboda yanda na dinga gargada gurin tafiya. Irin abincin mu na gargajiya na shirya masa towon dawa da miyar kuka wacce ta ji daddawa! da wake. gefe guda kuma na soya miyar dage-dage! da zallan tsokar naman sa! nasa Marka ta soya man shannu da albasa mai yawa, zobo na had'a masa irin hadin gargajiya! da yake na fito daga hannun tsohuwa wacce ta gwanance gurin iya sarrafa girki kala-kala abin bai bani wahala ba, nan da nan na kammala komai ganin da sauran lokaci yasa nayi masa farfesun dankwalin turawa da hanta tare da kayan lambu. 'karfe biyu shaura na fito daga kicin din, sai dai abinda na gani a falon ya yi masifar tayar min da hankali! duk da ba wani abin ashsha na ga suna aikatawa ba, amma kusancin dake tsakaninsu zai iya janyo faruwan wani abu. babu kowa a falon sai su biyu ashe tuntuni ya sauko ni ina can ina yi masa bauta yana cin amanata, abinda na ayyana kenan a cikin raina. wasu zafafan hawaye! suka ciko idona, da saurin gaske na d:auke kaina daga kansu na fara hawa matattakalar bene amma kafin na isa d'akin kukan da nake dannewa ya 'kwace! kwanciya nayi tare da tsirawa rufin dakin ido hawaye na gudana a saman fuskata, gaskiya ban san ina sonsa sosai ba sai yau! bana tsammanin zan iya jure wannan cin fuskar ashe dama duk 'karyar banza ce! a duk lokacin da za ayi masa maganar matar sai ya fututtuke! har ya dinga ikirarin kada a tayar masa da ciwo! gashi kuma saboda munafurci! ya zauna kusa da ita har yana yi mata murmushi. "Ba zan lamunta ba!" na fadi hakan a fili wanda yayi daidai da shigowarsa dakin, nayi saurin goge hawayen fuskata na tashi zaune ina kallonsa har ya 'karaso kusa dani ya zauna, yasa hannu zai janyo ni jikinsa na matsa tare da d'aga masa hannu! Irin kallon da nake masa ne yasa ya ma'kale maganar dake bakinsa, kawai dai ya zuba min ido yana kallo. Mun jima a haka tsakanin ni dashi muna kallon juna babu wanda ya iya wata magana. sosai na danne 'bacin raina gudun kada cikin fushi! na zage shi ko na fad'a masa wata maganar mai zafi! hakan yasa nayi ta kiran innalillahi cikin zuciyata kafin na samu sassauci! amma duk da hakan sai da naja masa tsaki! kafin na tashi na shiga band'aki domin watsa ruwa a jikina. Sai da cire kayana da niyyar yin wanka kawai ya shigo band'akin, hankalina ya tashi! na dinga zabga masa harara! mugun haushinsa nake ji. ko a jikinsa bai damu da hararar da nake masa ba, kawai ya hau cire kayan jikinsa bayan tsaf yake da sabuwar sutturarsa alamu sun nuna ma bai jima da yin wankan ba. Ganin haka yasa da sauri na d:auki towel na d'aura a jikina da sauri na kama hanyar fita, ya kamo ni tare da manne ni jikin bango! idonsa ya tsira min wanda gabad'aya yasa gwiwata yin sanyi. Yasa hannu ya talfo fuskata yana kallon bakina tare da so ya kusance ni. Kawar da kaina na yi, ya sake juyo da ni wani mayen kallo yake min yana lumshe idanuwansa da suka soma sauya kala. Hawaye ne suka fara zuba! gaskiya ba zan iya jurar wannan fitinar ba, cikin zuciyata nake raya hakan. Na shi 'bangaran kuma lafiya lau ya tashi daga bacci ya yi wanka ya shirya ya sauka 'kasa, sai dai tunda yayi tozali da Fatima notikan kansa suka kwance, ko da can dama yana masifar son wasu abubuwan na jikinta, sai gashi ya riske ta cikin kwalliyar data kid'ima shi, tana kuma fitar da sihirtaccen kamshin da ba kowace mace ke irinsa ba. wannan dalilin ne yasa jikinsa mutuwa! amma kima ya yi k'okarin kama kansa, domin ba tare da cikakkiyar kulawa ba ya amsa gaisuwarta, sai dai lokacin da Hajiya da Shukura suka bar gurin, ita kuma ta samu nasarar janye hankalinsa, domin kusa da shi ta zauna tana marairaice fuska tare da wasu maganganu wanda ya kasa fahimtarta sakamakon zamanta a kusa da shi ya haifar masa da gagarimar matsala, domin gabadaya sha'awarsa ce ta shi, ganin tudun nonowanta a waje ga uban kamshin dake fita a jikinta, ko da can da irin wannan salon take janye hankalinsa har ya manta da lefukan da tayi masa. Kusa da shi ta zauna tana share hawaye ta rik'e hannunsa tana ro'konsa Allah da Annabi ya dubi zumuncin dake tsakaninsu ya mayar da ita dakinta tayi alkawarin gyara halayenta kuma zata zauna matarsa lafiya. To cikin wannan yanayin Ta zo ta riske su, wanda ya hango tsantsar kishi a tare da ita! shima hakan bai masa dad'i ba, shiyasa bayan shigewarta bai 'kara minti daya a gurin ba ya bi bayanta domin ya rarrasheta, duk da ya san da wuya ta amince da hujjarsa. K'okarin janye jikina nake yana sake matseni yana hargitsa min jiki, towel din har ya fad'i 'kasan band'akin, ya zama babu komai a jikina, duk ya damu 'kirjinta da ta'bi! takaicin abinda yake min yasa na bud'e murya da karfin gaske na kurma ihu! Da sauri ya sake ni, nayi gaggawar d'aukar towel din na d'aura a jikina ina ta hararasa! wanda shi a lokacin ma ya gama susucewa! domin kamar wani bugagge! ya zama sai kai kawo yake a band'akin! Ban bi ta kansa ba na bude kofar da sauri na fita na fasa wankan ma. Hijabi na zura a jikina na zauna kan kujera tare da tattake hijabin da k'afafuna! nayi hakan ne saboda na san halinsa zai iya zuwa ya matsananta min. ya fito daga band'akin! ya zo ya tsaya kaina. Wato shi abu kad'an shi ke tayar masa da hankali! sai ka ce wani ayu domin dai shine a cikin hallitu yake jima'i duk bayan minti biyar a rana, to shima dai ina kyautata zaton hallitarsa ta bambanta da ta sauran maza, domin dai abin nasa na nema ya fi k'arfi na, duk da cewa; Ya fad'a min yana da k'arfin sha'awa, amma ban yi tsammanim cewa; Abin ya yi yawa irin haka ba. [1/22, 9:36 AM] Bintu: 106&107 Motsa baki ya yi da 'kyar ya iya furta "Ta shi ki je kiyi wankan na fito tunda ni ne bakya bu'kata." Kallonsa nayi domin dai ban ji abinda yake fad'a ba na dai ga bakinsa yana motsi na san magana yake min duba da yanda ya tsira min jajayen idanuwansa dake cike da fitina. Da hannu ya nuna min hanyar band'akin tare da maimaita maganarsa, amma wannan karon da sauti mai k'arfi ya yi domin na ji." Girgiza kaina nayi alamun na fasa wankan. Ya ce."Saboda me?" Shiru nayi tare da d'auke kaina daga kansa domin har yanzu da sauran haushinsa a raina. Ya fara 'kokarin zama kusa da ni, da azama! na tashi zan gudu! domin gabad'aya na riga na gama tsorata da shi, sai ya yi gaggawar ri'ke min hannu ya riga ni zama kan kujerar sai ya d'ora ni kan cinyarsa ya fara kici-kicin cire min hijabin jikina. Kuka nasa da cewa; Ni ka rabu da ni don Allah ba zan iya wannan abun ba." Ya girgiza min kai! a marairaice ya yi magana cikin kunne na "Ki taimaka min kin ji my love." Yafad'a yana d'ora hannuna a mararsa, da sauri na cire tsigar jikina na tashi jin yanda gurin ke tsaye 'kerere! bud'e baki nayi zan kurma ihu! yasa hannu ya rufe min baki yana bina da wani masifaffan kallo, lokacin jijiyar kansa duk ta tashi ga wani irin rawa da jikinsa yake. Yanda jikinsa yake kyarma! nima haka nawa jikin yake domin na gama tsorata da irin abubuwan da yake min duk ya hargitsa ni. ban san lokacin da na rushe! da wani irin kuka ba! na dinga ture shi daga jikina na ce"Tun sanyin safiya ka ke abu d'aya don zatin Allah ka rabu dani na huta ni kad'ai na san irin zafin da gurin yake min." Fuskarsa tsakankanin wuya na ya ce."Yin hakan shi zai sanya gurin ya saba, na fad'a miki ni mabu'kaci ne! a ko da yaushe ina da buk'atar mata ta a kusa dani muddin ina gida, shiyasa nake so ki saba da hakan. Na share hawaye da cewa" Ni kam ba zan iya ba gaskiya kuma matsalarka idan kayi sau d'aya baka ha'kuri sai kayi sau biyu ko uku duk ka galabaitar da ni." Ya ce."Ke d'in ce daban da sauran mata, na rantse miki idan zan kwana akanki ba zan gaji ba saboda ni kad'ai na san halin da nake shiga." Na ce "Bayan na ganka da tsohowar matarka daf da juna kuna murmushi! ni duk maganganunka ba zan yarda da su ba kawai kana min dadin baki ne. A rikice! ya ce." Wace ce Fatima idan dake a guri wallahi babu wani abu dake tsakani na da ita, kawai dai ta tsare ni da wasu zantuka marasa ma'ana." "Kallonsa na yi, sai ya gyad'a min kai domin so ya tabbatar min da gaskiyar maganarsa cikin rarrashi da kalamai masu taushi ya shawo kaina har na amince masa amma da sharad'in sau d'aya zai kawo kuma ban amince mun hau gado ba saboda a gani na idan ya ji shi a gado zai wuce gona da iri, nan kan kujerar komai ya faru. sharad'i na ya tashi a banza domin dai tunda na shiga hannunsa bai sake ni ba sai da hud'u shaura na la'asar! ya sauka cikin nishadi da walwala ni kuwa ya bar ni cikin kuka da jin zafi! da ciwon jiki cinyoyina duk sunyi tsami! da k'yar na tashi zaune na d'auki towel na d'aura a jikina nayi zaune ina share hawaye. Ko da ya fito ban yarda na kalle shi ba, na tashi da kyar na nufi band'akin kamar mai koyon tafiya, sai da nayi ruwan d'umi sannan na samu sa'ida na yi wankan tsarki tare da alwala na fito na same shi har ya kintsa jikinsa da sabuwar jallabiya ruwan madara yasa farar hula mai raga-raga sai ya nad'e kansa da farin rawani! yayi kyau sosai! kamar balarabe abin ya bani 'yar dariya ganin yanda ya zama ustaz har da carbi a hannunsa ya yi shirin shiga massalaci bayan ya gama wasu Abubuwa! yanda ya shirya tsaf! babu wanda zai ce shi ne a d'an ta'kin lokacin da ya gabata wanda gabad'aya suffarsa ta sauya kamar wanda ya samu matsalar k'wak'walwa haka yake surutai marasa kan gado mutu'kar yana wannan abu bakinsa baya rufuwa numfarfashi! da zantuka! wani sa'in har kunne na yake ciza ban sani ba ko yana sane yake hakan oho! Zumbura baki na yi da sauri na nufi bakin madubi na da'uki mai ina shafawa a jikina. Haka ya bud'e dakin ya fita yana murmushi wanda na kasa tantance ko na meye. Mudubi na tsirawa ido ina kallon kaina, sosai kwarmin idona ya zurma! na san ba komai ne ya janyo hakan ba sai wannan al'amari, cikina sai 'kugi! yake kamar anyi min yasa, wata masifaffiyar yunwa nake ji. A gurguje na shirya jikina cikin doguwar rigar atamfa 'yar ingila wanda d'inkin ya zauna cif a jikina, gaskiya telan da ya yi min d'inkuna ya gwanance sosai! duk wanda nasa a jikina sai ya yi min kyau! turare na fesa, sai na yafa dankwalin atamfar na sauka 'kasa domin cin abinci, yanda nake jin yunwa bana tsammanin zan iya gabatar da komai tunda da sauran lokaci idan na ci abincin sai na gabatar da sallar la'asar d'in. Babu kowa a falon da alama sun shiga yin sallah, wannan ya ba ni damar zama gurin abincin a nutse na dauki towo daya nasa miya daidai misali na fara ci da bisimillah! kauuu! bakina ya d'auka na gishiri da sauri na furzar da abincin na dauki ruwa na kuskure baki na, cike da d'umbun mamaki nake bin kayan abincin da kallo. ni dai na san lafiya lau na kammala girki na saboda sauri yasa na bawa Marka Umarnin shirya gurin cin abincin, to amma ya akayi hakan ta faru? shin waye ya lalata min miya bayan ba haka nayi ta ba" Ta shi nayi na nufi kicin din na same ta tana goge-goge na ce"Marka tun yaushe ki ka shirya gurin cin abinci?" Ta ce."Bayan fitarki da kad'an, wani abu ne ya faru? Na ce." Mu je ki ga ni " Ta bude miyar tasa cokali tasa a bakinta, ya mutse fuska tayi tana kallona da mamaki! a tare da ita, ta bude jar miyar itama ta dand'ana! tana girgiza kanta ta ce."Hajiya duk yanda a kayi bayan na gama shirya gurin nan wani ya zo ya lalata komai, amma wallahi ba ni da hannu a cikin faruwar hakan." Na ce"Na yarda da ba zaki aikata hakan ba Marka kawai na kafa hujja dake ne, amma lokacin da kina shirya gurin wa ki ka samu a falon?" Ta ce"Hajiya Fatima ce kad'ai a zaune har take tambayata menene? na ce "Towo ne wanda ki ka shiryawa mai-gidan. daga haka ba ta sake magana ba, har na 'kare abinda nake na fita. Na ce" Bana raba d'ayan biyu ita ce ta lalata min abincin" Ta ce"Kash! amma dai wallahi bata kyauta ba gaskiya, amma kiyi hakuri Hajiya bari nayi sauri na had'a wata miyar." Na ce''Ni kam yunwa nake ji sosai wallahi. bana tsammanin zan jira har ki kad'a wata miyar, kawai ki bani abinda ki ka girka musu." Ta ce."To shikkenan bari na kawo miki." Hanyar kicin din ta nufa da sauri. ni kuma na tsirawa kasan gurin ido tare da tunanin yanda zan magance matsalata. Har ya shigo ban sani ba sai sautin muryarsa na ji yana kiran suna na, na amsa tare da kallonsa. Ya ce." Tunanin me ki ke yi ne?" Ajiyar zuciya na sauke kafin na ce."Babu komai?" Ya ce."Ban amince ba, tun shigowata na hangi damuwa a tare da ke, shin wani abun a kayi miki?" Gurin cin abincin na kalla na girgiza kai takaici kamar ya kashe ni, na ce" 'Bata lokaci na yi gurin shirya maka abinci amma an lalata shi." Ya ce."Ban fahimta ba." Murmushin 'bacin rai nayi kafin na ce."Ba zaka fahimta ba dama kawai mu bar maganar. bai sake cewa komai ba ya nemi kujera ya zauna wanda ya yi dai-dai da kiran wayarsa. Tunda na ji ya ambaci Sadiya na gane da 'kanwarsa ya ke waya. ya kalle ni da fadin"Sadiya tana kan hanya tare da yaranta." Na ce"Ubangiji Allah ya kawo su lafiya." Ya amsa da "ameen" kafin ya d'ora da fadin" Yunwa nake ji mutu'ka! ki bani abinci idan zan samu." Na ce"Zaka samu gayan towo." "Wane irin gayan towo kuma? kwad'o za ki yi min bayan kin gama tatse ni" Na kalleshi takaici fal! a raina. wai na tatse shi maganar mamaki ta ba ni, na ce" Idan ta kama sai ka ci kwad'on tunda nayi duk 'kokarin da zan yi, gurin ganin ka samu abinci mai kyau amma hakan bai samu ba, sai dai yanzu Marka zata kad'a maka wata miyar." Ido ya zuba min yana kallona, na mayar da hankalina gurin Marka dake k'o'karin zuwa gurin, na 'karbi abincin hannunta kai tsaye sama na nufa da abincin a hannuna jiri na kwasa ta tsabar yunwa da takaicin abinda ya faru. Fatima tana nema ta zame min kadangaran bakin tulu. Saman ya biyo ni muka ci abincin a tare, duk ya cinye ya bar ni da sud'e hannu gashi ina jin kunyar Marka dashi kansa kada su kira ni da jaka, tunda azahirin abincin da ta zuba min yana da yawa, kuma idan ni kad'ai zan ci ya ishe ni watakila ma har na rage wani. Ganin ya sauka k'asa yasa da sauri na bud'e firji na d'auko robar yoght na bud'e na fara sha ko na cike wani gurbin. [1/23, 11:57 AM] Bintu: 108&109 Yanda ya shigo dakin da annushuwa yasa na tashi zaune ina kallonsa ko bai fad'a min ba, na san Sadiya ce ta sauke. Zauna kusa da ni tare da rik'e hannuna Ya ce "Sadiya ta iso ta na 'kasa tare da yaranta suna nan gwanin sha'awa." Yanda ya fad'i maganar da zumud'i yasa na karanci abinda yake cikin zuciyarsa, yana da son yara sosai! a lokacin kawai sai na kwad'aita da haihuwar nima, domin samun farin cikinsa sai na saki fuska sosai na ce"Gaskiya sun sha hanya bari to na je mu gaisa?" Ya ce."Hakan yana da kyau! hannuna ya rike muka sauka k'asan a tare! Rungume ni tayi kamar ta shekara da sani na, sai farin ciki take muka zauna kujera d'aya nima na saki fuskata sosai na marabance ta fiye da yanda tayi nuna murnar gani na. Ashe hakan yayi masifar k'unanta zuciyar Fatima da take hakimce a kan kujera; ita kuwa Hajiya murmushi kawai take tana kallonmu, ballantana kuma uban gayyar da ya rasa ina zai tsoma ransa ya ji d'adi, a duniya yana k'aunar wanda zai nuna kulawarsa ga tilon 'kanwarsa da ta rage masa, yarinyar da suka sha gwagwarmayar rayuwa! shiyasa ya ke kula da ita sosai! duk lokacin da ya je jibia makotanta sai sun san ya zo, ballanatana Kishiyarta duk abinda ya yi wa 'yar uwarsa na alheri haka zai mata ya dauke su duk a daya a gurinsa duk ya kai su aikin hajji har mijinsu, wanda sai ya fi shekara bai sayi abinci a gidansa ba, domin dai duk zuwan da zai yi garin mota guda ta kayan masarufi a ke sauke musu mutukar Alhaji Habu ya kai ziyara mahaifarsa sai jama'a da yawa sunyi kwanan farin ciki. 'Ya yaranta mata uku duk sun zama 'yan mata mazan biyu ne suma sun girma gasu da nutsuwa d'aya bayan d'aya suka gaishe ni, na dinga sanya musu albarka ina jin k'aunarsu a cikin raina Fatima ta cika ta batse! kamar ta fashe! a lokacin duk wanda ya kalleta zai gane tana cikin 'kunci! sai na rasa gane dalilinta na yin hakan. bana tsammanin ma sun gaisa a tsakaninsu, Shukura ce kawai naga ta gaisheta itama daga gaisuwar ba ta sake wata magana ba sai zum'bura baki take Hira muke yi jefi-jefi yana zaune a kusa da ni ya d'an sa mana baki mussaman idan ta fadi wata maganar ya lura ban ji ba sai ya maimaita min abinda ta ce. haka hirar ta kasance tsakaninmu Hajiya ma nasa baki sa'i da lokaci. Sai bayan ya ta shi daga gurin ne Hajiya ta kalleta babu walwala a fuskarta ta ce" Hajiya Fatima wannan wane irin zubar da mutunci ne? yanzu a matsayinki na babba shin wannan abinda ki kayi daidai ne?" Ta kalleta tana ta'be baki ta ce"Hajiya me nayi kuma? ni sarkin 'yan lefi." Ta ce" Sadiya ta zo amma kin gagara kallonta ballanatana ku gaisa kece fa babba me yasa za ki bari wata 'baraka ta shiga tsakaninku." Ta ce"Hajiya gashi da bakinki kin kira ni babbah to ni zan gaisheta ko ita ?" Hajiyan ta ce"To meye a ciki don kin mata magana ai ba'kuwa ce kya tambayata 'yan uwa da abokanan arziki. Girgiza kanta tayi da cewa"Ba ta kai wannan matsayin ba wallahi " Gabad'aya muka kalleta da mamakin furucinta. Sadiya ta ce"Allah ya baki hakuri Hajjaju a ko da yaushe dama ni ba ba'kuwar zafi ba ce, ina wuni ai durkusawa wada ba gajiyawa bane." ta fad'i maganar cikin zolaya. "Kin ga Sadiya bana son munafurci da kitifi! da kuma neman suna ya isa haka bana bukatar gaisuwarki." Ta ce.''Aikuwa ni ba zanyi gaba dake ba." Sai ta fusata! ta fara sakin maganganu muryarta na rawa! "Dama mana komai zaku iya yi min na wulakanci dake da d'an uwanki, itama Hajiyan tana take muku baya saboda kuna da kud'i! shiyasa har wata banza ta fi ni daraja a gurinku ai shikkenan." Hajiya ta ce"Duk mai ya janyo wannan maganar? wato ke ba damar a gyara miki kuskuranki sai ki fara sakin maganganun da basu da ce ba, dake dasu duk daya kuke a gurina, ki daina kuma kiran yarinyar da munanan kalmomi domin itama daidai take daku bayan haka nan gidan mijinta ne, ki bar ganin cewa; tana da matsalar kunne, dole ta tsinci wasu abubuwan hakan kuma bai daidai bane Sadiya ta ce" 'Kwarai kuwa don Allah Anti Fatima ki daina haka babu dad'i, kuma ki bar komai ya wuce yanda muka manta kema ki manta da komai, mu yi zumunci irin yanda Allah ya umarta." "Munafuka ba zan bari ba d'in." Ta fad'a a hasale! idonta ya yi jawur! tsabar kishi ne yake damunta yanda muskiniyar yarinyar ta samu kar'buwa a gidan, kowa sonta yake. Kalmar dana tsinta ke kenan, don na yi ta kallon bakinsu domin na hasaso maganar da suke tunda a hankali suke, nan fahimci cewa rikici ne a tsakaninsu ko ga yanayin fuskokinsu. sai kawai na ta shi na bar gurin ina mamakin abinda matar take, na lura kishi take da ni sosai! kuma ta ga wani sa'bani bai faru a tsakanina mijina ba sakamakon abinda ta yi na janye hankalinsa shiyasa b'akin ciki yake nema ya kashe ta. Suna ta mayar da maganar a tsakaninsu ya shigo! sai kawai ta fashe da kuka! saboda tsabar sharri itama Shukura! ta fashe da kuka suka rungume juna kamar wanda akayi musu gagarimin abu! Jikinsa a sanyaye ya zauna kan kujera. Yayin da Hajiya da Sadiya abin ya dinga ba su mamaki! Kallonsu ya yi sai kukan suke rungume da juna!sosai ya ji rashin dad'i a cikin ransa, wani sa'in ya kan tausaya mata duba da yanda take wahala a kansa, bayan haka kuma yana duba zumuncin Allah shiyasa baya duba abubuwan da tayi masa na rashin kyautawa, ta wani gefen kuma tana cin albarkacin 'yarsa, shiyasa yake d'an sassauta mata, Ya kalli Hajiya da fad'in"Wani abu ne ya faru?" Hajiya duk ta warware masa komai. Sai ya kalli Sadiya da fad'in" Ke me yasa baki gaisheta ba ai ta girme ki bana son rashin kirki Sadiya zamu 'bata dake muddin haka zaki dinga yi." Ta ce."Kayi hakuri Yaya ba zan sake ba, amma itama kayi mata fad'a ta daina kira na da munafuka don ban ga dalili ba, matarka dai 'yar uwata ce, kuma ba zan wulakantata a kan son zuciyar wani ba, don na lura 'bacin ran hakan yasa suke kuka, har tana fad'in wasu maganganu da basu da ce ba." Ya daga mata hannu da cewa; Ya isa haka wannan dai ya zama na farko, ya kuma zama na k'arshe! kada ki sake." Ta ce."In sha Allahu." Sunanta ya kira "Fatima." ta kalleshi da hawaye sha'be-sha'be! a fuskarta ya dan sassauta muryarsa da fad'in"Meye abin kuka kamar 'kan'kanuwar yarinya, gashi itama kin sanya ta kuka! dake da Sadiya duk daya kuke a gurina baku da bambanci, saboda haka ki tsayar da zuciyarki ki daina wasu tunane-tunane marasa kyau! sannan kuma ba zan lamunci wani ya tozartaki ba. Jin haka yasa ta kalle shi a sanyaye! ta ce"Abunda ya 'bata min rai yanda Hajiya da ita kanta Sadiyar suka bada goyan baya har matarka ta samu asararin cin mutuncina, wallahi wannan abun shi ya 'bata min raina." Ya ce"Mata ta kuma me tayi miki?" Ta ji wani kuttun! takaici jin ya kira yarinyar da matarsa! wasu hawayen suka 'kwace! mata wannan kukan na sharri ne domin tana sane take yi. Su Hajiya dai al'amarin ne yake ta basu mamaki! wato ta nan kuma ta b'illo zata had'a miji da matarsa. A maimakon ta bashi amsar tambayarsa, sai kawai ta tashi da sauri tana share hawaye ta nufi masaukinta Shukuran ta bi bayanta itama sai kuka take! minti uku suka fito a tare. Shukura hannunta rike da akwatin kayan mamanta hanyar fita suka nufa. Ya buga musu tsawa! da fad'in" Wallahi idan ku ka fita a haka sai ranku ya 'baci! Tsayawa! su kayi a gurin! Ya kalli Hajiya da cewa"Wai me yake damun Fatima ne?" Ta ce"Bakin kishi mana, so take ta dawo dakinta kuma sai ta biyo ta wannan hanyar! masharanciya kawai." Kansa ne ya fara ciwo sakamakon wannan hatsaniyar ciwonsa na nema ya ta shi. Ya d'aga murya tare da bawa Shukura umarnin mayar da akwatin. ita kuma Sadiya ta je ta dinga rarrashinta har ta shawo kanta suka shiga d'aki a tare! Tsaki mai tsayi ya ja! ya tashi ya hau sama da tunanin abin a cikin ransa, dama can Fatima ce matsalarsa, yanzu ya yi aure domin ya huta ta zo zata hargitsa masa tunani! akwai abinda yake dubawa shiyasa baya so ya kore ta daga gidan, amma duk abinda za tayi ya bar zama da ita har abada. Cikin rashin kwarin jiki ya shigo dakin, na bi shi da kallo a lokacin da yake kokarin shiga band'akin, girgiza kaina nayi cikin zuciyata nake tunanin ko wani abun ne ya faru tunda dama lokacin dana bar falon rigima suke a tsakaninsu, nima a raina bana 'kaunar zaman Fatima a gidan, don dai babu yanda zan yi ne, amma akwai damuwa abubuwan da take . Wanka ya yi ya fito d'aure da babban towel a jikinsa, ya nufi madubi ya dauki man shafawa kafin ya zauna gefen gado, ido muka hada, domin tunda ya fito nake kallonsa, ganinsa cikin damuwa nima duk sai na ji bana jin dad'i." Magana ya yi min, amma ban ji sosai ba, na dai bi bakinsa ne, wani lokacin hakane yake faruwa idan ban ji magana ba ina kallon bakin mutum a lokacin da yake maganar nan nake fahimtar abinda ya nufi. 'Kasa na sauka lokacin babu kowa duk suna d'aki sai dai amma ina jin hayaniyarsu kamar masu rigima, nayi saurin harhad'a duk abinda nake bu'kata na bar falon, domin bana so wani ya fito ya gan ni saboda gudun zargi. Kad'an ya iya cin abincin, na kalleshi lokacin yana goge bakinsa na ce" Har ka 'koshi? na ga duk kayi wani iri Allah yasa lafiya?" Kai tsaye ya ce "Fatima ce matsalata me ya had'a ki da ita har ki ka zage ta?" Gabana ya buga jin wannan maganar. Fuska na had'e sosai! na ce."Wani abu ta ce nayi mata to Allah yasa da mutane dai a gurin, kuma duk sharrinta zai koma kanta da izinin Allah! sannan kuma mijina ya yi mata nisa wallahi." Cikin tsantsar kishi da fargaba na kai karshen maganar. Ta'be bakinsa ya yi, ya d'an murmusa, ba kuma tare da ya ce min komai ba ya haye gado ya kwanta ya ja bargo ya rufe jikinsa. Hakan ya kara 'bata min rai kishi ya dinga taso min domin na kasa fahimtar inda ya nufa akan tsohuwar matar tasa, hakuri na dinga bawa kaina tare da tausar zuciyata ban bari kishin ya yi tasiri a tare dani ba, na daure na tuttura abincin ina nazarin al'amarin a cikin raina Babu kuzari nayi wanka nasa kayan bacci sannan na kwanta kusa da shi, lokacin bacci har ya d'auke shi! Fuskarsa na tsirawa ido a lokacin da yake sauke numfashi cikin nutsuwa yake bacci babu munshari bare buge-buge! ina tausaya masa sosai a raina ban san meye dalili ba, amma can 'kasan zuciyata nake jin wani irin abu wanda ba zan iya fasaltashi ba, kawai dai na bar abin a cikin raina ne, ina adduar Allah yasa na rayu ni kadai a tare da shi. *** KANO Talatu taga tujara iri-iri da 'kan'kanci gurin Hujaj! kuka kuwa tayi har ta gaji, duk ta figale ta lalace sakamakon jin labarin auran da zai yi, kuma tun lokacin da surukinsa ya ba shi kyautar gida, ya kwashe kayansa kaf daga gidan Talatu! shi kadai ya tare a sabon gidansa dake rijiyar zaki, a cewarsa amarya ce zata fara shiga domin Talatu zata iya lalata masa gida. Babban abinda yake sa ta zubar da hawaye a kullum. rashin Hadiza domin dai ta famtsama duniya kusan wata guda kenan rabonta da gida, tana cikin wannan masifar mijin nata ya zo yana sheda mata irin alherin da ya samu yarinyar da ta d'auki karan tsana ta d'ora mata! wai ace kamar Shahida mummuna b'aka kurma(muskiniya) ita ce take auran daya daga cikin attajiran da sukayi suna a duniya, wannan al'amari ya sanya ta zautuwa duk ta sayar da abunda ya rage mata tana yawan asiri akan malamai su raba auran, sannan shi mijin nata a dora masa ciwo ko amaryarsa ta zo ya gagara tsinana wani abu. Malamai da bokaye duk sun tsiyata ta! ta rasa komai a gidanta, hatta da kwanuka da farantai na cin abinci ta kwashe ta sayar, bata da komai sai tsummokaran da take d'aurawa a jikinta, sai ta fara bin hanya duk gurin da ta ga anyi shanya sai ta kwashe tasa a buhu ta je ta sayar, ta kar'bi kudin ta nufi gurin malami yayi mata aiki akan Shahida da kuma ubanta. har yanzu ta gaza gane annabi ya faku bahaushe yace wanda yayi nisa baya jin kira. ** To haka rayuwar ta dinga tafiya da dadi babu dadi haka nake ta hakuri, domin kwanan Sadiya biyu da zuwa mai-gidan yayi tafiya zuwa chana domin bud'e sabon kamfanin sarrafa zannuwa! na samu sauki ta b'angaransa! domin idan yana gidan matsanta min yake kullum bani da hutu, a 'kalla sai ya kwanta da ni sau uku ko sau biyu a raina, kuma idan ya fara baya ji baya a ga ni, to tafiyarsa sai na samu sassauci! Sai dai bana iya sauka kasa na zauna a cikinsu domin ina ganin zamana a cikinsu kamar akwai matsala, tunda har yanzu dai Fatima bata ajiye makamanta ba, duk lokacin da zamu had'u kallon banza ne yake raba tsakaninmu, wannan dalilin yasa nake yin nesa da duk gurin da take, kuma cikin zuciyata nake neman hirji da ita, kuma in sha Allahu mijina yayi mata nisa. Amma tsakanina da Hajiya da Sadiya babu matsala, cikin girmamawa da mutunta juna muke gaisawa, yaranta kuwa duk mun saba, suna bani girma sosai anti sama anti 'kasa. Muna gaisawa da juna kullum da mai-gidan, dalilin sabuwar wayar da ya saya min a lokacin da zai tafi, kullum da safe zan yi masa text na gaisuwa tare da fatan alheri. shi kuwa kullum maganarsa, na shiryawa zuwansa domin dai duk abinda yake daurewa kawai yake, amma yana daf da dawowa. saboda haka na shirya idan ya dawo sai na biya bashin dana d'auka! Dariya abin yake bani duk lokacin da yayi wannan maganar. amma kuma na himmatu da gyaran jikina, kullum sai na hada kankana da madara na sha, sannan na jika kaninfari da yawa, shi ya zama ruwan sha na. a jikina na dinga jin sauyi kuma sa'i da lokaci idan sha'awa ta taso min sai dai na kwanta nayi ta rungume fillo ina tunanin abubuwan da yake min na soyayya a lokacin da muka kad'aice! 'kwarai ya iya sarrafa mace a wannan fage, kuma cikin nutsuwa yake yin komai matsalarsa kawai dogon zango! yana jimawa bai kawo ba, kuma idan ya samu gamsuwa ta farko maimakon ya risina a'a kamar an 'kara masa 'karfi da himma! zai d'ora a inda ya tsaya. wani lokacin har mamakinsa nake idan na dubi shekarunsa na ga irin muzakkaracinsa, sai na godewa Allah da ya azurta ni da lafiyayyan namiji wanda bani da kaico sai dai kuma na kasa sanya abun a raina, kullum idan wata mu'amula zata faru a tsakanina da shi rimi-rimi za a fara dan wani lokacin ma har taimaka masa nake, amma tafiya kad'an zan fara kuka ina ro'konsa ya yi sauri ya gama don na gaji, mussaman idan na samu gamsuwa da wuri gabad'aya sai komai ya fice min a rai, a lokacin da nake wannan rokon shi kuma kamar 'kara masa kuzari ake. [1/24, 5:39 PM] Bintu: 110&111 Bacci ne ya 'kauracewa idona sakamakon masifar dake damuna, yini nayi a kwance a gado marata sai ciwo take, gaskiya da wuya na 'kara shan wani abu da zai tayar min da hankali duba da cewa; wanda zai d'ebe min kewar baya kusa, kwana biyar da tafiyarsa na ji su Hajiya na fadin zai iya yin sati biyu ko fiye da haka bai dai dawo ba, a lokacin na shiga tunani da nazarin maganarta domin dai sati d'aya ya ce min zai yi, yau ina lissafi kwanansa biyar kenan da tafiya, shiyasa na mayar da hankali gurin gyara jikina dalili na riga nasan yanayinsa. amma kuma abin yana nema ya zame min d'an zani. ga kuma maganar da Hajiya tayi cewa; bai zama lallai ya dawo a lokacin da ya fad'a ba saboda ya saba yin hakan a wasu lokatan zai yi tafiya da zummar yin kwana biyu ko uku amma sai ya shud'e wasu kwanakin bai dawo ba. Gabadaya nayi saranda na fara tausayawa kaina halin da zan shiga, domin jikina ya riga ya saba da jangwale-jangwale, sai dai ni da kaina na fahimci cewa; ba ni da juriya, domin da tafiya tai nisa nake gajiya, amma kuma da alama inda da sha'awa a kusa. Waya ta na daura tare da tura masa text Yaushe zai dawo?" sai ya bani amsa da cewa; sai wani satin saboda wasu dalilai." Ban ji dadin amsar da ya bani ba. Na sake tura masa da wani sa'kon cewa; _"Amma dai kai ka ce sati d'aya za kayi don Allah ka dawo nayi kewarka."_ Sai bayan na tura masa text din kuma nazo ina jin nauyi domin ina tsoron kada ya fassara ni. Ina ta tsumayin amsarsa shiru. a sanyaye na ajiye wayar na sauka daga gadon, band'aki na shiga na sake watsawa jikina ruwa a karo na biyu tun bayan wayewar gari wai a tunani na ko zan samu sassaucin wani abun. Na shirya jikina tsaf na sauka 'kasa ba tare dana yi kwalliyar fuska ba. Babu kowa a falon, dama tun safe Sadiya ta sheda min cewa za su zaga gari ita da yara domin mai-gidan yana dawowa za su tafi tasan kuma idan ya dawo ba zai bar su fita ba. ganin babu Hajiya a falon na raya a raina cewa da ita akayi tafiyar. murmushi nayi cikin zuciyata dana tuna cewa; jiya da daddare naji tana kuka da k'afafunta suna ciwo, tabbas da mai-gidan yana nan ba zai bari ba. Kai tsaye kicin na nufa! Baba Marka tana ta aikace-aikace! muka gaisa cikin mutunci da karamci. na ce"Wallahi awara nake sha'awa ko zaki aikata min, kinga bana jin dadin jikina, amma da ba haka ba da kaina zan yi." Za tayi magana kenan sai gata ta shigo kicin din jikinta sanye da riga da wando masu kama dana sanyi, amma kuma dasu gwara babu domin duk hallitun jikinta a waje suka, babu hula ko dankwali a kanta sai tarin kitson attachment da ta daure da ribbon kamar ba cikakkiyar musulma ba, domin dai ni da ta tsaya a kusa dani ma 'karni na ji tana yi wallahi, ba komai ne ya janyo hakan ba sai bleaching din da take. Baba Marka ta gaisheta ta amsa kamar ba ta so. Dama ni tuntuni mun daina magana, domin ko na gaisheta bata amsawa sai dai kallon banza. Bakinta nake kallo a lokacin da take magana, nan na fahimci abinda take nufi. "Marka zanyi 'baki saboda haka ki ajiye duk wani aiki da ki ke yi ki fara hidimar shirya musu abinci. kada ki 'bata min lokaci" Yanda take wa matar magana a tsatstsaye! daga gadara! sai abin ya bani haushi, na kalle ta da cewa; Baba Marka akwai waken suya ko?" da sauri ta ce"Eh Hajiya." Na ce"To ki fara aikin dana sanya ki.'' Sai ta fusata! ta kalle ni da fad'in" Ba ki isa ba kuwa! dole sai ta kammala uzuri na kafin naki". Na ce"Saboda me?" "Saboda na isa!" Tafada kamar zata cinye ni. Dariya ta ba ni, na murmusa kafin na ce"Nan gidan aurena ne, ni nake da umarnin komai koda mai-gidan yana nan, to ballananta kuma baya gari, komai yana hannuna, don haka ban ce kada kiyi abinda ki ke bukata ba, amma ki bari ta kammala uzurina tukkuna ." "Ke shashasha! rufe min baki anan gurin." Tafad'a tana girgiza. Na jingina jikin bango ina kallonta tana magana kamar ta tsokane min ido sai kumfar baki take Na ce"Wai don Allah mai na tsare miki ne? kin d'auki karan tsana kin d'ora min kin san ke baki isa ki kashe min aure ba, amma na fahimci abinda ke damunki idan mijina ya dawo zan rarrashe shi ya mayar dake dakinki shikkenan hankali ki sai ya kwanta ko". Hannu ta daga zata zabga min mari! na kauce! da sauri ina kallonta idonta yayi jajawur! sai rawar murya take da alama maganata ta 'bata mata rai. Baba Marka sai hakuri take ba mu, na ce"Baba don Allah ki cigaba da aikinki ki kyaleta idan ta gaji zata bari." " 'Yar iska muskiniya kawai ke har kin isa ayi abu don ke? to wallahi ki rubuta ki ajiye idan mijina ya dawo hannuna sai kin kwashi kashinki a hannunki da k'afafunki zaki gudu." Na ce" Ahaf! ai sai da amincewata tsohon mijin naki zai mayar dake, ki lallabani kawai na je na rarrashe shi.'' Cikin dariya nayi maganar domin na sake 'kuntata mata rai! Aikuwa sai ta rarumi! kofin gilashi zata kwad'a min, nayi gaggawar shigewa kicin d'in ina mamakin al'amarin.lallai wannan bata da hankali. Hanci ta sha'ka kwalla cike da idonta ta nuna ni da yatsa kafin ta ce" Zaki gane kuranki ne 'yar shegiya 'yar gidan d'an cah-cah! Na ji kamar ta zuba min tafashashshen ruwa a jikina! ta cigaba da zumdumawa ubana ashar tana ambatar sunansa! da kiransa d'an bariki! al'amarin ya d'aure min kai mutu'ka! nayi mamakin! yanda a kayi ta san sirrina irin haka, shin waye ya fad'a mata asalin mahaifina! Ban zubar da hawayen ba sai bayan data fita tukkuna, na tsuguna kicin din na rushe da wani irin kukan b'akin ciki! Baba Marka ta dinga bani hakuri tana bani shawara cewa; ko don gaba da na sake biye mata mu zubar da mutumci, ta ce kuma aikina zata fara sai ta kammala tukkuna ko meye sai ya biyo baya. Babu 'kwari na fita daga kicin. falo na ganta a zaune tana waya sai kuka take kallo d'aya nayi mata nayi saurin d'auke kaina, sai dai na tsinci wasu maganganun da take kuma da alama da mai-gidan take waya. Raina ya sake 'baci na hau saman da tunanin matakin da zan d'auka dole idan ya dawo ya zaba ko-ni-ko-ita don wallahi ba zata zauna min a gida ba a rasa gane tsakanina da ita wacece matar gidan. Kwanciya nayi ina nazarin da tunani akan lamarin. abinda yake bani mamaki shine; cikin labarinsa wanda ya ba ni ya nuna min cewa babu wacce ya tsana sama da ita, kuma a zahiri yana nuna 'kiyayyarta 'karara! to a ya akayi cikin lokaci k'ank'ani! ta janye hankalinsa har yake sauraranta su yi doguwar magana a waya da kuma zahiri? ni wallahi kukan da take yi ma shine yake ba ni mamaki! girgiza kaina nayi da tunanin abinda zai faru idan ya dawo don wallahi ba zan lamunta ba don na ga abin nata babu arziki. Jin cikina na k'ugi yasa na sauka 'kasan domin duba Baba Marka ko ta kammala. Suna zaune falo tare da 'kawayenta suna shewa wasu manya mata ne biyu 'yan duniya irinta, gabansu babban tire ne cike da kayan marmari. Ganin yanda suka tsira min ido ne yasa na soma neman tsari a zuciyata. Cikin dauriya da jarumta na isa gurin da suke a nutse na ce"Sannunku da zuwa." Sai naga sun kalli junansu zuwa can kuma suka fashe da dariya suna kallona, raina ya sosu! na san maganata sukewa dariya abinda na tsana a rayuwata kenan!. " 'Kawata wannan abar fa?" wacce take kusa da ita ke yi mata wannan tambayar. Ta kalle ni a wulakance kafin ta ce"Ita ce matar tasa." Suka dinga dariya suna kallona kafin d'ayar ta ce"Allah shi kyautawa Alhaji watakila dai kyawun sura ya duba, amma in ba haka ba meye abin so a tattare da wannan abar, na farko ga ta 'baka mummuna! uwa uba bebiya, wallahi wani cewa zai yi bata da hankali idan ya ga yanda take magana ai sai mutum ya tsorata.'' Bakinta kawai nake kallo a lokacin da take maganar. bayan haka kuma kunnuwana duk sun ji abinda take fad'i a kaina. sosai nayi mamakin furucinta. Ta ce" Wai nan sai da aka gigita! tunanin mutane sannan aka same ta, domin shi fa a ganinsa daban take da sauran mata! bari ma ku ji wani abu mahaifinta d'an bariki ne mugun dan iska ne duk ina da labarin komai." Al'amarin da ya fusata ni! nayi tsalle! na dira gabansu! da hannusu na ce" Ku shiga hankalinku wallahi 'yan iska jahilan banza da wofi!" na juya kanta tana zaune tana min kallon mamaki! ina ga ba tayi tsammanin zan iya mayar da martani ba, ido jawur! na ce" Ke kuma wallahi idan ki ka kuskura ki ka sake fadin mummunar kalma a kan mahaifina sai na fasa miki baki! idan kuma kina shakka! ki kara cewa tak! a gurin nan kiga abinda zanyi miki." Cike da mamaki! take kallona kafin ta ce" Ai ba 'karya akayi muku ba, ko zaki rantse da cewa; mahaifinki ba mutumin banz......bata 'karasa ba na kaiwa bakinta bugu! ban sameta ba dalilin saurin kaucewa da tayi! Tsaye! ta mi'ke da dumbun mamaki! ni kuma jikina sai tsuma! yake na sake nuna ta da yatsa a karo na biyu na ce" Abu d'aya nake dubawa yasa nake saurara miki, amma zan cire rigar mutumci muddin zaki ci zarafin mahaifina wallahi sai na cire miki iskar dake kanki! ki ji da wai! 'Yar Kano ce ni, kuma haihuwar Jakara! zan iya jure komai amma ba zan lamunci ki ci mutumin mahaifina ba, kuma mijina sai dai gani daga nesa." Naushi ta kawo min 'kawarta ta ri'ke ta tana bata hakuri! tana fincikewa wai lallai sai ta doke ni, sai zunduma min ashar! take tana yi min cin mutumci, cikin wannan halin su Hajiya suka shigo. Hajiya ta fashe! da kuka da fad'in "Me zan gani ni Saude! dama wallahi tun a mota gabana yake fad'uwa! wai shin Fatima me yake damunki ne?" Cikin kuka take maganar tana mamakin al'amarin. Sadiya ta janye ni daga tsakanin kujerun tana tambayata ba'asi, duk na warware mata komai. Ta ce"Gaskiya dole ayi wa tufkar hanci domin zamanta a gidan zai haifar miki da matsala, ai iyaye sun fi gaban wasa." Ashe ta ji lokacin da Sadiyar take wannan maganar. sai ta koma kanta da zagi! da fad'in" Sai ta ga wanda zai fitar da ita daga gidan. Itama Shukura ta goyi da bayan uwarta suka dinga yi wa Hajiya rashin kunya! wai sune bata k'auna! komai su kayi lefi ne. Hajiya dai barin gurin tayi. Yayin da 'yan iskan 'kawayenta suka d'auki jakukkunansu suka tafi babu wata damuwa a tare dasu duk da fitinar da suka haddasa! Duk sona da awarar da 'kyar! na iya cin uku! na gabatar da sallar magariba na kwanta kan dadduma ina tunane-tunane. Sadiya ta shigo dakin da sallama a bakinta Zaune na tashi ina kallonta har ta zauna a kusa da ni. "Hakuri na zo na baki Antina." ta fada tare da rike hannuna. Na ce"Wane irin hakuri kuma 'kanwata?" Ta ce"Kan abubuwan da Hajiya Fatima keyi min don Allah kiyi hakuri kuma kada kisa damuwar komai a ranki, akwai dalilin da yasa take hakan, ni kuma na san duk abinda za ta yi yayana ba zai sake zaman aure da ita ba." Na ce"Meye hujjarki na fad'in hakan?" "Saboda babu wacce ya tsana kamar ta." Murmushin takaici nayi na ce" Da kenan! a yanzu dai ta janye hankalinsa akwai yuwuwar ya dawo da ita dakinta, tunda yana iya sauraranta a waya ko a zahiri, ni ganau! ce." Ta ce"Kada ki manta 'yar uwarsa ce! kuma uwar 'yarsa, ina ganin wannan ala'kar ce ke sanya ya shiga huruminta, amma bana tsammanin zai cigaba da zaman aure da ita." Dariya ta bani ganin yanda take kare shi, na ce"To shikkenan tunda kin ce haka, amma ni idan ya dawo zan zauna da shi, tilas ya fada min dalilin Fatima na zama a gidansa, idan kuwa babu k'wa'kwkwaran hujja! to zai za'ba ko-ni-ko- ita don mutane su bambance! wacece matar gidan a tsakaninmu. Ta ce."Kema kina da hujjah antina, amma don Allah a sassautawa dattijo kinga shekaru sun fara hawa kansa, bayan haka ga zirga-zirga da hatsaniyar neman halal! a gurinki kawai zai samu sassauci! kada ki tsawwala masa da yawa. 'Yar dariya nayi na ce"Nayi miki al'kwarin ri'ke miki dan uwa bisa amana. ki taya ni addua." Ta ce."In sha Allahu. zan taya ku adduar zaman lafiya tare da samun zuria masu albarka domin babban burin Yayana kenan." Murmushi kawai nayi ina kallonta. cikin zuciyata na amsa da "Ameen" domin har ga Allah ina so na haihu domin tabbatuwar farin cikinsa tare da cikar burinsa. [1/25, 10:08 PM] Bintu: 112&113 Sadiya ta jima a tare da ni duk a 'ko'karinta na ganin ta kwantar min da hankali dangane da irin abubuwan da suke faruwa a gidan, ganin yanda ta damu da al'amarin ne yasa na nuna mata cewa; komai ya wuce a gurina, hakan yasa ta kwantar da hankalinta, muka jima muna hirar duniya, yanda take fahimtar maganata da yanda take mu'amula da ni sai ka rantse da Allah cewa; mun jima a tare, sosai take gane maganata fiye da tunani na, hakan ya kara mata matsayi a cikin zuciyata, domin ni a rayuwata ina so naga wanda ya iya mu'amula mai kyau! kuma yake fahimtata a koda yaushe idan nayi furuci! bai kyare ni ba, bai kuma nuna gazawarsa ba. Da kanta ta kawo min abinci da duk abinda zan bu'kata, tana ta yi min hidima tare da tsokanata da fad'in" Yau ta fanshi d'an uwanta! Dariya kawai nayi na girzgiza kai. gaskiya na yabawa k'o'karinta, kuma ta yi nasarar gusar da kashi hamsin na 'bacin ran dake damuna, haka da muka kasance cikin tsokanar junanmu irin na wasan kanin miji. Sai wajan goma da rabi na dare tayi min sallama ta sauka 'kasa Ni kuma na shiga band'aki domin watsa ruwa a jikina. Tsaf na shirya cikin kayan bacci masu taushi na gyara gashin kaina wanda yake ta wani irin kumburi dalilin mayukan da nake shafawa, gashin ya cika ya yi laushi da ba'ki sosai gwanin sha'awa, manya ribbon nasa na daure sannan nasa hula, na nemi guri na kwanta da tunanin abubuwa da yawa a cikin raina Wayata na d'auka ina dubawa nan naga text d'insa yana tabbatar min da dawowarsa gobe. Dubawa nayi amma ban bashi amsa ba, kawai na ajiye wayar ina tunani a akan dawowarsa, tun dai kafin faruwar hakan, da bakinsa ya ce sai wani satin saboda wasu dalilai to amma na fi zargin ya samu labarin hatsaniyar da ta faru shine dalilin dawowar tasa bagatatan! na san kuma ba kowa ne zai sheda masa ba sai ita fitinanniyar. Addu'a nayi sosai kafin bacci ya d'auke. cikin ikon Allah ban farka ba sai asubahi, nayi baccin dana jima ban yi irinsa ba. Bayan na idar da sallar asubahi. sai na sauka 'kasa domin gaisawa da mutanan gidan kamar koda yaushe. Ina shiga d'akin Hajiyan na same su gabad'aya har da shi a zaune da alama bai jima da sauka ba, kuma a dakin ya yar da zango. Na ji wani iri a cikin raina kuma na tsargu! mussaman ganin irin kallon da suke min. yanayinsu ya nuna suna tattauna muhimmiyar magana ne, ita Hakimar ma tana zaune a kusa da shi, kuma babu wata sutturar arziki a jikinta, kayan bacci ne, duk ga nononta nan a waje da shattin cinyoyinta. 'Bacin raina ya sake nunnukuwa! amma ban nuna a fuskata ba, nayi k'okarin danne damuwa na gaishe da Hajiya kamar koda yaushe ta amsa cikin kulawa. na kalleshi lokacin ya tsira min ido kamar wanda yaga sabuwar hallita, na daure zuciya da fadin" Yallabai sannu da hanya ka dawo lafiya?" Da sauri ya amsa min yana 'kokarin tashi tsaye da jakarsa a hannu. "Antina ina kwana." Sadiya ce take gaishe ni. na amsa fuskata a sake kafin na yi ya'ki da zuciyata gurin kallonta da Cewa; Anti Fatima mun tashi lafiya?" Ta amsa ba tare da ta kalle ni ba sai wani cin magani take. Tsaye na mi'ke da niyyar fita, sai kawai ya biyo bayana muka fita daga dakin a tare, al'amarin da ya basu mamaki! kenan, mussaman wacce ta assasa zaman! ranta ya 'baci ainun! ganin yanda ya dauki jakarsa ya bi bayan matarsa daga shigowarta duk ya rikice! ana magana da shi rimi-rimi! amma ya tashi ya fita. wasu hawaye masu ciwo suka ciko idonta, tana ganin dole sai ta tashi a tsaye gurin ganin ta farra'ka tsakaninsu! yarinya 'kan'kanuwa ta rikita babban mutum irin wannan! ba zata iya jure wannan takaicin ba. Tun da muka fito daga dakin yake ta kallon fuskata! ni kuma naki yarda na kalleshi, na dai yi namijin kokarin kar'bar jakar hannunsa nayi sauri nayi gaba ba tare da nace masa komai ba. Yana shigowa d'akin ya zo ya zauna kusa da ni. idanuwansa kawai na kalla na gane abinda yake da akwai, abu biyu suka dame shi, sha'awa da kuma damuwa! gabad'aya ba a nutse yake ba sakamakon tayar masa da hankali da Fatima tayi, wannan dalilin yasa ya d'auko hanya babu shiri, duk da cewa bai kammala uzurinsa ba, sai da ya bar komai gurin amintattun abokansa da yaransa. "Me ya faru bayan tafiyata?" Ya fad'a tare da rike hannuna. "Me ta fad'a maka ya faru?" Nima nayi masa tambaya irin wacce ya yi min. Ya d'an 'bata ransa da cewa; Ya ina tambayarki kina maimata min irinta." Na ce"Ai dole na tambayaka nima." Tsira min ido ya yi na 'yan mintina kafin ya ce." Me ya had'a ki da Fatima har kina kiranta da karuwa! kuma kina 'ko'karin sheganta Shukura." Gabana ya fad'i! kallonsa nayi da mamakin furucinsa! fuskarsa babu walwala yake kallo na. Sai kawai na fashe da kuka! na ce"Sai Allah ya saka min wannan sharrin wallahi. kuma akan wannan matar zan iya barin gidanka muddin ba kayi wa tufkar hanci ba." Ya ce."Ni ba wannan na tambayeki ba, dalilin da yasa ki ka fad'i wannan maganar. saboda na baki labarin rayuwata, shi yasa ki ka samu makami! gurin tozartani a idon duniya, idan kin kira Fatima Karuwa, kin sheganta Shukura mijinki ki ka zubarwa da mutumci! me yasa za ki yi min haka." Hawaye na kwaranya na ce" Ka ga kawai kayi shiru tunda dai baka iya yanke hukunci ba, ya za a yi kawai daga zuwa ka fara tuhumata akan abinda ban aikata ba, sosai nake ganin girma da mutuncinka kada wannan ya janyo maka zubewar mutunci a idona." Ya ce."Mutunci wane iri kuma bayan wanda ki ka zubar min! Shahida ina miki kallon mai hankali me yasa zaki 'bata rawarki da tsalle?" Hawaye na goge na kalle shi ina ayyana abubuwa da yawa a raina , wato ina ganin idan ban fito masa a mutum ba, zai cigaba da raina min hankali ne, na lura hawayen da nake zubarwa sam! bai dameshi ba, ya zauna yana so ya tarwartsa min zuciya! Na ce"Ai dama ka saba yaudara! to akan wane dalili zan yarda da kai? duk maganganunka k'anzon kurege ne! ka saba sanja suffofinka tare da kalamanka a duk lokacin da ka so hakan." Ya zuba min ido da mamakin furucina a tare da shi. Na ce "Kana ta wani abu! ko ka d'auka kidahuma ce ni? to idan kana da burin dawo da ita gidanka ban damu ba abinda dai na sani shine ranar da ka dawo da ita ni kuma a ranar zan bar gidanka don ba zan zauna ana min yawo da hankali ba." Cike da d'umbun mamaki! ya ce."Ke kina da hankali kuwa?" Na ce"Sosai kuwa! kayi magana ne na baka amsa daidai da wacce kayi. Ita kuma wacce tsohuwar guzumar mai kama da arna sai ta gane kuranta wallahi. zata san ni take shiryawa wannan sharrin." Ya dinga kallona kamar babu gobe, ni kuma ina zaune turmin danya, ko gezau! kuma ban yi nadamar magana ta ba. yanda ya tsira min idonsa nima haka na tsira masa nawa, da kansa ya janye nasa ya tashi ya shiga band'aki babu wani karsashi a tare da shi, kwata-kwata bai ba ni tausayi ba saboda tsabar haushin da ya ba ni. Ina zaune ya fito daga band'akin da towel a jikinsa, fuskarsa na kalla sai naga kamar bai ta'ba dariya ba, jijiyoyin kansa sun fito, jikina ne kuma ya yi sanyi dana tuna cewa bashi da cikakkiyar lafiya, kada wannan damuwar tasa ciwonsa ya ta shi. Ina zaune ina kallonsa ya shirya cikin sabulwar jallabiya fara tas! ya fesa turare kamar koda yaushe, ya zauna kan Sofa da wayoyinsa a hannu. a lokacin duk ya kunnasu kira ya dinga shigowa tare da sa'kkoni! Kallona ya yi, a lokacin da nake kallonsa, sai nayi saurin d'auke kaina ya bud'e murya da bani umarnin kai masa kwamfiyutarsa (loptop) dake kan dirowar gado. Babu 'kwari a jikina na d'auka na kai masa kafin na shiga band'aki domin yin wanka. d'aure da towel mai girma na fito daga band'akin, wai ni a dubura ta kada ya hangi wani abu na jikana, ashe nayi a banza, domin tunda na fito yake bina da kallo, gabad'aya yanayinsa ya sauya ya ture loptop din dake gabansa, ganin ya nufo gurin da nake tsaye duk sai na diririce! ni nake da muradin kasancewa da shi, amma 'bacin ran dana kwana dashi ya haddasa ficewar komai daga raina, sha'awar ma ta d'auke! sai 'ko'karin ganin na samu hanyar warware matsala. Hannu nasa na sake d'aure! towel din dake jikina na zuba masa ido har ya iso ya tsaya daf da ni hucin numfashinsa na dukan fuskata. Ido na lumshe sakamakon yanda na ji wani irin 'kamshi ya bugi hancina, hucin bakinsa ma abin kwantace ne. mutum ne mai tsabta da kula da komai na jikinsa. Hannuwansa biyu yasa ya rike k'ugu na da kyau! ya manne kirjinsa da nawa, ya cire hannu daya tare da kokarin kwance towel din dake daure a jikina. Jin haka yasa na d'an ture shi tare da kokarin kaucewa abinda yake shirin yi. Da sauri na matsa daga kusa da shi tsigar jikina duk ta tashi. Ya jima yana kallona kafin ya sauke zazzafar a jiyar zuciya ya koma ya zauna kan Sofa, amma ya gagara aikata komai sai aukin kallo da yake min, duk motsina akan idonsa har na shirya jikina na iske gurin da yake ba janye idonsa ba. Rashin abin cewa yasa na ce."Ko zaka ci abinci?" Kai ya girgiza a nutse ya ce."Zauna ina son magana dake." Ganin babu alamun wasa a tare dashi yasa na zauna a gabansa, amma na kasa kallonsa. Ya yi magana da sautin da zan ji "Shahida ni ki kayiwa rashin kunya ko?" A sanyaye na ce"Kayi hakuri raina ne ya 'baci wallahi. Ya ce." Ki yi min bayanin abinda ya faru bayan bana gari. Na ce" Ni kam ba za ka ji komai daga bakina ba, amma ka ajiye a ranka cewa; ba zan ta'ba tozartaka ba, sannan kuma nayi al'kawarin ri'ke amanarka a gabanka da bayan idonka, amma kuma ina neman alfarma guda daya a gurinka, don Allah kada ka boye min gaskiya ka fada min, meye amfanin zaman Hajiya Fatima a gidanka?" Na kai karshen maganar idona a tsaye a kansa. Murmushi ya yi kafin ya ce." Fatima 'yar uwata ce kamar yanda ki ka sani, ban da wannan ala'kar babu wata, a can baya dai nayi zaman aure da ita, amma yanzu babu wannan a tsakaninmu, kuma bani da ra'ayin sake zama da ita, hujja ta biyu kuma Fatima na sauka a gidana ne a duk lokacin da tayi tafiya ta dawo to a nan zata sauka idan baki manta ba ita din 'yar kasuwa ce, tana da gidan kanta wanda ta gina, sai dai zamanta a gidan ita kad'ai akwai had'ari! wannan dalilin yasa na amince da ta dinga sauka a nan, bayan haka babu wata alak'a ta soyayya a tsakaninmu. Na ce" To yanda na fahimta ita ta d'auke ni kamar kishiyarta, kuma idan baka sani ba a yanzu babban burinta ka mayar da ita d'akinta, tunda duk ta nuna alamu, bayan haka kuma bana tsammanin zan yarda da hujjarka domin dai na gani da idona har sau biyu tana waya da kai a duk lokacin da ta bukaci hakan, bayan haka kuma zata zauna kusa da kai cikin shigar banza, shin wannan daidai ne a gurinku?" Shiru ya yi yana nazarin maganata kafin ya kalle ni da cewa; Kina zargin wani abu na shiga tsakani na da ita kenan?" Girgiza kaina nayi na ce" Ba na zarginku amma ai akwai shaid'an zai iya shiga tsakaninku, mutukar zaku ke'bance! kana kallon suffofin jikinta a waje! mai yasa ba za ka tsawatar mata ba, ko da yake na gane abinda kake bukata kenan." Dariya maganar ta ba shi, ya ce." In banda abinki ni mai zai burge ni a tare da Fatima! ke kad'ai kin ishe ni domin kin tara duk abinda nake bu'kata matsalar kawai kin kasa sabawa da ni, kullum cikin tsorana ki ke, wannan kad'ai shi yake damuna dake, amma ni babu ruwana da Fatima." Yanda yake maganar yana dariya sai ya ba ni haushi, na tamke fuskata da cewa; "Bana ra'ayin kasantuwarta a cikin gidan nan, muddin ina da hakki a kanka, kuma idan duk jikina kunne ne to ba zan amince da maganarka ba, ina so Fatima ta koma gidanta da zama idan ba haka ba to ni zan bar mata gidan sai ta maye gurbi na tunda dama haka take muradi" Ya gyara fuskarsa da fadin" Yanzu ya ki ke so ayi kenan?" "Fatima ta fita da sabgata, sannan kuma ina so ka ja mata kunne ta daina cin mutumcin iyayena domin ban san a ina ta samu labari ba, bayan haka kuma ta yi gaggawar yin nesa da ni, idan ba haka ba to kai zaka kasance cikin damuwa da tashin hankali." Ya jima yana kallonta tare da ayyana abubuwa da yawa a ransa, ya lura yarinyar nada zafin kishi! kuma sai da so ake kishi! amma damuwarsa yanda zai hana Fatima zaman gidansa, ko babu komai akwai zumunci, bayan haka akwai zuria a tsakaninsu, wannan sune manyan dalilan da ya sanya yake jin nauyin yi mata wani abu na tozarci, idan ta lalace! dole a zage shi a duniya, dama kuma ya lafiyar kura! da yawa jama'a suna yi mata wani bahagon kallo. zamanta a gidansa a duk lokacin da take gari, shine rufin asirinsu bakid'aya. to amma ya san ta inda zai 'billo mata. Ya ce."Shikkenan ranki ya dad'e abinda ki ke so za a yi, amma kema kada ki sake biye mata kuyi abinda bai dace ba kin jiko, sannan maganar cin mutuncin iyaye zan dauki mataki a kai in sha Allahu. Ajiyar zuciya na sauke tare da jin sassauci a zuciyata, ina ganin hakan shine samun salama a gare mu bakid'aya domin ni sam ban yi tunanin abinda zai je ya dawo ba. [1/26, 10:37 PM] Bintu: 114&115 Ina da bu'katar abinda zan ci." ya fad'a yana d'aukar babbar wayarsa dake ajiye a gefensa. Tashi nayi na sauka k'asan da zummar cika umarnin mai-gidan, abun mamaki! Hajiya Fatima da Shukura suna zaune a falon su kad'ai, Hakimar ta she'ka ado wanda ya ba ni mamaki! sai ka rantse da Allah cewa ita ce matar gidan, abinda ya sake d'aure min kai shine yanda gabad'aya hankalinsu yake kaina a lokacin da nake kokarin saukowa, sai muka shiga kallon-kallo a tsakaninmu, wani bahagon kallo suke min, yayin da ni kuma nake masu kallon mamaki! yanda na fahimta gabad'aya babu alheri a zuciyoyinsu. shiyasa na gyara fuskata, ban kuma yarda na bi ta kansu ba ballanatana wata magana ta had'amu kai tsaye kicin na nufa, a jikina kuma na ji cewar ba su janye idonsu daka kaina ba. Wainar shinkafa da miyar tantakwashi! tare da kunun gyada Marka tayi na karin kummalo. lokacin dana shiga kicin din ta kammalla komai sai k'amshi ne yake tashi. Marka tana da tsabta da kula, kuma ta iya sarrafa abinci nau'i-nau'i! ba yanda za a yi ka shiga kicin din ka ga 'kazanta daga zarar ta kammala girke-girke take gyarawa ta goge ko'ina tasa turaran wuta, idan kuwa tayi abinci kamar kunne zai tsinkr?e saboda dad'i! shi kansa mai-gidan yana yaba k'okarinta! kuma baya shakkar cin abincinta, sa'i da lokaci kuma yana yi mata alheri sosai, domin har aikin hajji taje ta dalilinsa. Cikin mutunta juna muka gaisa da juna. A nan ta samu damar yi min nasiha akan abunda yake faruwa, ta kuma bani shawarwari masu kyau! mutukar na daure zuciyata nayi amfani da shawarwarinta zan ci riba, sai dai hakurin shi yake da wuya. Godiya nayi sosai! kafin na had'a duk abinda nake bu'kata na d'auki kwandon abincin na fita. Wuce ta nayi tana waya amma babu Shukura a gurin ita kad'ai ce a zaune. Cikin zuciyata na ce"Allah shine zai yi min maganinku. Ina shiga d'akin ita kuma tana k'okarin fitowa! kallonta nayi, sai tayi saurin cewa;Anti ina kwana?" na amsa da nazarin abinda ya shigo da ita dakin, da sauri ta bude kofa ta fita, na sauke ajiyar zuciya tare da nufar gurin da yake zaune. Na ajiye kwandon abincin dake hannuna a gabansa, na zauna tare da tsira masa ido. har yanzu fuskarsa tana nan a yanda take kadaran-kadahan! sai kawai na tsinci kaina da tambayarsa dalilin shigowar 'yar tasa d'akin. Hankalinsa na kan wayar dake hannunsa ya ce." Wai mamanta ke kira na." Wani irin kallo nayi masa mai kama da harara! Ya ajiye wayar yana 'yar dariya da satar kallona. kawai sai idona ya ciko da ruwan hawaye! wato ya mayar dani abin dariya kenan. Murya na rawa na ce"Gaskiya ba zan lamunta ba, kada yarinyar nan ta sake shigo mana d'aki domin hakan bai dace ba, sannan kuma ba tarbiya ba ce" Ya ce"Zan yi mata magana in sha Allah." Tashi nayi na bashi guri na je na kwanta duk yanda na so daurewa na kasa, hawaye suka shiga zuba a kumatuna. Ni ban san yanda zan yi da wannan masifar ba, gabadaya matar ta hana ni kwanciyar hankali. masifar kishinta nake a raina. A nasa 'bangaran kuwa dad'i yake ji ganin yanda take nuna kishinsa, hakan na 'kara masa sonta a cikin ransa, shi duk abinda take kawai kallonta yake idan ba wani kad'aru na Ubangiji ba babu yanda za a yi ya sake zaman aure da Fatima. Abinci ya ci sosai! ya gama ya wanko bakinsa duk ina kallonsa. Ganin yana nufo gurina yasa nayi saurin juya masa baya. ya hayo gadon yana d'ora hannunsa a jikina. na tashi zaune ido jawur na ce" Ka je kiran da take maka mana." Girgiza kansa ya yi ya ce."Ba zan je ba domin shirme za ta zo min da shi a halin yanzu ke kad'ai nake da muradi." Shiru nayi masa, ya kalle ni da cewa" Kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki kinji ko, in sha Allahu komai zai daidaita, kuma zan yi miki hallaci fiye da yanda ki kayi min a baya. Zuciyata ta tsinke! hawaye suka zubo! na ce"Sanin zuciyar mutum sai Allah! amma a jikina nake jin kamar akwai abinda zai faru mara dad'i, domin naga Fatima ta bud'e wuta! a kanka, ga kuma 'yarta tana taimaka mata da campaign. " 'Yar dariya yai ya ce." Da zan cigaba da zama da Fatima da sai dai ki zo ki sameta a matsayin matata, haukan banza take kuma zan kawo k:arshen matsalar in sha Allahu." Ajiyar zuciya na sauke ina d'an jin sassauci a raina. Hannu yasa ya goge hawayen da ya rage a fuskata. ido ya lumshe yana min wani irin kallo. Ya ce." Zaki biya ni bashin dana ke bin ki ko?" A shagwabe na ce"Bani fa da lafiya ina ganin ma kamar na samu ciki." A take fuskarsa ta sauya da wani irin annuri! ya rungumeni tsam-tsam! a jikinsa, sai godiya ga Allah yake, gabadaya sai jikina ya mutu! na dinga nadamar 'karyar da nayi masa lafiyata lau. kuma bana jin wani sauyi a jikina irin na masu ciki. Cikin kunnansa na ce"Da wasa nake maka fa." Sake matseni ya yi kafin ya ce." Hakan zai tabbata in sha Allahu rabbi, yau zan bada himma! sai nayi cikin 'yan biyu a wannan rana." Murmushi nayi tare d'ora hannuna kansa a hankali nake shafa gashin kansa had'e da wuyansa, na tsinci kaina da sumbatar gefan fuskarsa cikin tsantsar tausayi da k'auna na ce"Allahu ya amshi adduarka mijina." Ya amsa da "ameen ya Allah." lokacin ya fara rikicewa sakamakon abubuwan da nake masa, wanda ni kaina nake mamakin hakan, sosai na tarairayeshi a ranar, ya mayar da kansa 'karamin yaro, ya dinga biye min ina zuba sangarta da shagwaba iri-iri! da wani irin salo ya tafiyar da ni, wanda muka jima a cikin yanayin cikin jin dadin juna, na kasance cikin farin ciki, domin ban ta'ba jin dadin al'amarin ba sai a ranar, salon ya tafi da ni mutuka! dan har sai da na fi shi za'kal'kalewa! hakan kuwa ya faranta masa rai! ya dinga sanya min albarka har iyayena sai da suka samu nasu rabon. Bayan komai ya kammala sai kuma kunyarsa duk ta dabaibaye ni, na gaza kallonsa, shi kuwa babu abinda ya dame shi sai tsokanta yake da cewa; muddin zan dinga bashi irin wannan kulawar to ya rufe 'kofa! kuma sai yanda nayi da shi. murmushin kunya kawai nake amma a zuciyata wani irin farin ciki nake ji, ganin yanda na faranta masa, lallai kuwa zan zage damtse domin gaskiya bana kaunar kishiya, shiyasa na tashi hankalina akan tsohowar matarsa dake nema ta zama min ciwon ido. A gurguje nayi wanka na fito yunwa na sasakar cikina, dama ban ci abinci ba, al'amarin ya wanzu! shiyasa har jiri-jiri nake. ko da na fito daga bandakin, baya nan, a zuciyata na raya cewa; ko ya tafi amsa kiran da akayi masa, ina shirya jikina ina wannan tunani, yayin da wani sashi na zuciyata ke nuna min ba hakan bane. "Fatima." Ya ambaci sunanta idonsa a tsaye a kanta. Ta amsa tana kallonsa tare da marairaice fuskarta! Ya ce" Wai tun yaushe muke maimaita magana guda a tsakaninmu?" "Bangane ba?" ta fada gabanta na fad'uwa! "Ki nemi miji kiyi aure! wannan kalmar har na gaji da fad'a miki ita, idan domin ni Abubakar ki ke zaune a haka ba zan ta'ba mayar dake ba." Ya cire shakku da jin nauyi ya fada mata gaskiyar abinda ke zuciyarsa. Sai ta rushe da kuka! da fadin" Me yasa? yanzu ashe ba zaka tausaya min ba, wallahi nayi nadama! a yanzu babu wani namiji da yake burgeni sai kai." Ya ce." Bayan na zama wani abu a duniya ko?" Shiru tayi tana kallonsa hawaye na zuba. Ya girgiza kansa yana tuna kuttun! takaicin daya k'unsa! a can baya. ya ce" Abu biyu nake dubawa nake sassauta miki Shukura da zumuncin Allah. idan ba haka ba, da tuni na san yanda nayi dake wallahi, kin zame mini masifa a rayuwata, kin hana ni nutsuwa, nayi aure domin na samu kwanciyar hankali kin zo kin zaune min a gida kina neman fitina da matata, wannan shine maganata ta k'arshe dake, ki fitar da miji kiyi aure ko kuma ki fice min daga gidana, kada ki sake tafiya yawo ki ce zaki sauka a nan, sai na ci mutuncinki." Kuka! take sosai tana kallonsa, shi kuma ya sha kunu! kamar bai ta'ba dariya ba ta ce" Abinda ta kitsa maka kenan? tun safe kana daki manne da ita tana shirya maka mugun abu har kake i'kirarin tozarta ni da cin mutuncin barin gida, ai idan Sadiya ce ba za ka yi mata wannan cin mutuncinba tunda ciki daya kuka fito, shikkenan babu komai rayuwa ce." Tana mashahurin kuka take maganar. Ya ce." Ke kin fi kowa sanin halina, babu wata mace da ita isa ta juya ni ko ta tsara min magana na hau kai na zauna, dama can kawaici nake miki, amma naga kina nema ki wuce gona da iri! don haka na fad'a miki ni ba zan mayar dake ba, ki fitar da miji kiyi aure, idan kuma ba hakaba ki tattara kayanki ki fice min daga gida. Hannu ta d'ora a kanta ta kurma ihu! tana kiran sunan babanta wato Baba Auta. ni da nake sama sai dana ji ihun! ballantana su Hajiya dake daki, Sadiya na shirye-shiryen tafiya Gabad'aya muka had'e a falon muka riski abinda yake faruwa. Tana kuka ta je ta rungume Hajiya tana sheda mata irin hukunci daya yanke, Hajiya a sanyaye ta ce" Alhaji Habu kana cikin nutsuwarka kuwa? Fatima fa 'yar uwarka ce kada giyar kudi tasa ka ci mutuncin zumunci! Ya ce." Hajiya na gaji da abubuwan da suke faruwa a gidan nan, ke da kanki kin san yarinyar nan itace matsalata, to mai zai sanya ta zo ta hana ni nutsuwa da matata? darajarki da zumuncin dake tsakaninmu yasa har na amince take zaune a gidana, amma bayan haka banga dalilin da zai sanya tazo tana tayar min da hankali ba, ga yarinyar nan Shahida kullum cikin kuka take da 'bacin rai iri-iri, saboda haka hukunci na riga na yanke ta fita min a gida mutukar ba zata fito da miji tayi aure ba." Kafin Hajiya tayi wata magana Shukura ta yanke jiki ta fadi a gurin, hankali kowa ya tashi, yarinyar wani irin abu take kamar mai farfad'iya! ko wacce manyan aljanu suka buge! gidan ya hargitse da koke-koke! ni kaina kukan nake ina nadamar tunzura zuciyarsa da nayi gurin yanke wannan hukunci! Da 'kyar da tasirin addua Shukura ta dawo daidai! amma sai kuka take tana rokon mahaifin nata, ba tare da ya yi wata magana ba, ya haye sama ya bar mu cikin alhini da tashin hankali. Fatima a ranar ta tattara kayanta ta wuce Jibia cikin halin damuwa tare da nemo hanyar warware matsalarta, tafiyar uwar ya 'kara tayar da hankalin 'yar a ranar dai sai da ta fad'i sau uku! har sai da uban ya kira wani malami ya raba dare a kanta yana addua sannan aka samu sassauci! Babu wanda ya rintsa a tsakaninmu, domin nima kuka nasa masa na ce hukuncin da ya yanke ya yi tsauri da yawa! kada jama'a su zarge ni, tunda ina jin lokacin da Hajiya ke fad'in" Shekara da shakaru! Shukura bata ta'ba abu makamancin wannan ba, lafiyarta lau kuma bata da iskokai! Washe gari! Sadiya ta had'a kan yaranta suka tafi cikin kuka da damuwa domin ita kanta ba ta ji dadin faruwar al'amarin ba, saboda ganin yanda Hajiya ta sauya gabad'aya tunda abun ya faru take kuka! al'amarin dai yana nema ya zama tashin hankali da rabuwar kai. Ashe tashin hankali na gaba, domin mai-gidan ne ya kwanta magashiyan ciwo ya ta shi, muka sake shiga damuwa matsananciya! kuka! nake ina nadama domin gani nake kamar ni na haddasa rikicin! yayin da a 'bangaransa yake jaddada min cewa; kada na dami kaina, dama can da wannan kudirin a cikin ransa. Da taimakon Allah dana likitansa jikinsa ya warware! amma sai da ya yi sati biyu bai fita ba a cikin halin jiyyar Baba Audu ya kira shi a waya wai yana nemansa, wannan dalilin yasa bai tunkari garin ba sai da warware sosai! sannan ya shirya zuwa, nima ya ce na shirya domin gabadaya zamu tafi har da Hajiya, wacce gabad'aya ta sauya min, ta daina sakar min fuska, sai dai duk lokacin dana gaisheta zata amsa amma babu kulawa kamar yanda ta saba. [1/27, 8:13 PM] Bintu: 116&117 Jikina gabad'aya ya yi sanyi sakamakon faruwar al'amarin, yanda Hajiya ta d'auke min wuta shine ya fi damuna, dalilin da yasa nake tsoron zuwa garin nasu domin ban san abinda zai faru ba, abinda na fahimta shine Hajiya tana ganin kamar da sanya hannuna gurin hukuncin da mai-gidan ya yanke. shiyasa nake shakkar shiga cikinsu don ban san irin kallon da za su yi min ba. Jiki babu k'wari nayi wanka na fito na same shi har ya kammala shiryawa yana sanye da manya kaya dakakkiyar shadda (wagambari) da aikin irin na sarauta a jikin babbar rigar, kasancewar shaddar sky blue ce sai ya yi amfani da farar dara ya nad'a farin rawani a kansa, kamar dai koda yaushe ya sakaye idanuwasa da farin gilashi. gefen gado ya zauna yana sanya safa a k'afarsa gefe takalminsa sahu ciki ne a ajiye. Babu kuzari nake shiryawa lokacin na ji yana waya da alama babban abokinsa ne don na ji lokacin da ya ambaci sunansa Alhaji Faruk! Ina k'o'karin daura dankwali a kaina ya ce." Ki maza ki sauko ku gaisa da abokina yana 'kasa, saukarsa kenan ya shigo domin duba ni, gashi kuma mun shirya barin garin. A sanyaye na amsa da "To." daga haka bai yi wata magana ba ya fita daga dakin. Mayafi na d'auko wanda ya dace da less din dake jikina, Sannan na fito da set din takalmi da jaka masu kyau! wanda suka dace da shigar da nayi. Duk da ban yi wata kwalliya a fuskata ba, nayi kyau sosai! ni kaina na sheda hakan, komai na jikina na mussaman ne, mussaman gold din dake wuya da hannuwana. Ban fesa turare ba saboda na san hakan haramun ne a matsayina na matar aure sai dai idan ina tare da mijina A nutse na sauka k'asan na same su gabad'aya har da Hajiya suna gaisawa. Wani irin kallo Hajiyan tayi min kafin ta amsa gaisuwata, ban ji dad'in hakan ba, shima na lura bai ji dadin abinda tayi min ba. Gudun kada ba'kon dake zaune a gurin ya fuskanci wani abu yasa na saki fuskata sosai! na gaishe shi da yanayin da Allah ya hallice ni, shi ma wani irin kallo naga yana yi min, sai na sunkuyar da kaina ina jin wani irin rashin dad'i, a duk lokacin da zanyi magana da yawa mutane sai su dinga yi min wani irin kallo wanda bana jin dadin hakan, shiyasa sau tari idan na shiga cikin mutane nake shiru da bakinta idan ba da wani dalili mai k'arfi ba bana magana har na bar gurin, to a halin yanzu mijina ne kawai yake fahimtata kuma baya kyarata! baya nuna gazawarsa akan komai nawa, shine yake magana da ni kai tsaye kamar yana magana da mai lafiya irinsa, ya riga ya gama gane yarena, wanda a cikin kurame ni ina daya daga cikin masu saukin fahimta. Yana murmushi ya ce."Amarya tuntuni nake son zuwa mu gaisa Allah bai nufa ba sai yau! kwana biyu bana zama shiyasa, sai kuma na samu labarin rashin lafiyar abokina wannan dalilin yasa ina sauka a garin na shigo domin na dubashi sai gashi kuma kun shirya barin gari zaku je jibia ko?" Bakinsa na bi nan na gane abinda yake nufi tunda bai yi maganar da karfi yanda zan ji ba. Na ce"Eh wallahi. Ai ya ji sauki da taimakon Allah da na likitansa, amma duk da haka mun gode sosai da ziyara." Ya ce."Babu komai ai an zama d'aya Allah ya sanya alheri." na amsa da "Ameen" Ina wasa da yatsun hannuna. Kud'i masu yawa ya ajiye min a gabana, da cewa; Ga wannan babu yawa ko." Na ce" Kai da kazo dubiya kuma har da wahala." Dariya yayi, ya kalli abokin nasa dake tsaye ya zuba hannuwansa cikin aljuhu, kallo daya za kayi masa ka fahimci cewa yana da damuwa! Ya ajiyewa Hajiya kudi masu yawa irin wanda ya bani, sallama ya yi mana suka fita tare da abokin nasa suna tattaunawa. Ya ce" Abokina amma abun ya bani mamaki fa." Murmushi yayi da cewa" Dole ne amma hakan shine alheri a tare da ni. Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce." Sosai yarinyar ta bani tausayi wallahi. Babu yanda Allah baya zartar da ikonsa. amma Allah yasa hakan shine alheri da samun kwanciyar hankalinka." Ya amsa da "Ameen ya rabbi amma ina da damuwar Fatima har yanzu." Kallonsa yayi da bukatar k'arin bayani. Nan ya warware masa dukkanin abinda yake faruwa da kuma dalilin zuwansa jibia. A matsayinsa na abokinsa da suke taimakon junansu ta kowane fanni, sai ya bashi shawarwari masu kyau! ya kuma ce dashi ya daina sanya damuwar komai a ransa yin hakan zai janyo masa samun matsala tunda dama lafiya bata wadace shi ba. Cikin karamci da girmama juna su kayi sallama. Alhaji Faruk ya shiga mota direbansa yaja suka fita daga gidan. Cikin nutsuwa ya juya ya koma gidan, da tunanin abubuwa da yawa a cikin ransa. KANO Hujaj dai ya ga ranar haihuwa, domin gabad'aya rayuwarsa ta sauya ta dalilin yarinyar da ya hofintar a can baya yake ganin kamar wahala ce a gare shi, sai gashi itace sanadin samun rufin asirinsa, domin a yanzu mijinta shi ya rufa masa asiri ya bashi muhalli tare da bude masa babban shagon sayar da takalma a kasuwar kwari! sannan ya bashi kudi masu yawa ya biya mutanan dake binsa bashi, a yanzu bashi da wata matsala sai ta Talatu domin ta riga ta zame masa matar jaraba! amma ba zai rabu da ita ba zata cigaba da zaman 'ya'yanta. gefe guda kuma shirye-shiryen auransa ya kammala saura sati biyu a d'aura aure! hankalinsa kwance yake gudanar da harkokinsa, sai dai wasu daga cikin abokansa sun takura masa maula mussaman wanda suka she'ka suka ga ba k'waya, da yawa daga cikinsu sun tsiyace! sun fatarce! dalilin abinda suke aikatawa na sabon Allah. wadanda Allah yaso daga cikinsu sun shiryu, shiyasa suke lallabowa gurin abokin nasu domin ganin yanda Allah ya rufa masa asiri! Sunyi-sunyi da shi, ya yi musu jagora gurin surukin nasa, amma ya'ki a cewarsa ba za su je su zubar masa da mutunci ba, bayan duk kanwar ja ce, su kuwa sun riga sun san cewa Alhaji Habu (Dangaske) Bangon sukari ne kowa ya jingina sai ya lasa. To dama ai duk wanda ya ketare umarnin ubangiji yana 'kare rayuwarsa ne a tsiyace! shiyasa duk rintsi bawa yayi k'o'karin ganin ya ci halilinsa. Kasancewar akwai abun. ginin gidan Baba Asabe bai ja dogon lokaci ba, bayan tafiyarsa da kwanaki biyu ma'aikata suka rushe gidan, aka fitar da tsari mai kyau. cikin kwana goma gida ya kammala, ya fita zakkah a cikin unguwar! zuwa yanzu jama'a da yawa sun samu labarin abinda yake faruwa. da yawa 'yan uwa suna alfahari da kasantuwar mutumin a cikin zuriarsu, hakan abin farin ciki ne, a ce babban mutum irin wannan ka had'a nasaba dashi, shi kansa Kawu Musa rayuwarsa ta sauya data iyalinsa, itama Baba Asabe sai dai ta wanke goma ta tsoma biyar, bata cas bare as! dalili surikin nata ya wadata ta da duk abubuwan bukata kamar yanda yayi alkwari. sai suka kasance cikin farin ciki idan ka cire Saliha data kwarzabi kanta kullum cikin kuka da damuwa! Har Baba Asabe ta ranfo abinda ke damunta wato hassada takewa 'yar uwata bisa alherin da ya same ta, al'amarin ya bata mamaki mutu'ka! ta zaunar da ita domin tayi mata nasiha sai ta rushe da kuka! a guje! taje ta rungume! rijiya wai gwara ta fad'a ciki ta mutu! Hankalin Baba Asabe ya tashi ta kira ubanta ta sheda masa duk abinda ke faruwa! Kawu Musa ya fusata! ya zazzabga mata mari! a fuska ya rufe ta da fad'a da cewa; tayi hattara da rayuwa, kuma ta ajiye a ranta cewa; hassada babu inda zata kaita sai tashar nadama, kuma idan Ubangiji yace خن في خن akan bawansa babu wanda ya isa ya ce dan me." Ta tashi ta shiga d'aki tana rusa! kuka tare da nadamar rayuwa, wato dai ta tabbata cewa; Shahida tayi mata nisa kenan, itama dole tayi mubaya, tunda iko ne na Ubangiji ya sauka kamar yanda mahaifinta ya tabbatar mata, sai ta kwanta kan gado tayi lamo! tana hasaso fuskar Shahidan, tana can cikin daula da kwanciyar hankali, ganinta sai an cike form watakila ma duk gurin da zata je akwai masu tsaronta. Abinda Saliha bata sani ba shine Ubangiji yana iya jarrabawar bawansa ta hanyoyi da dama, da yawa jama'a suna ganin Allah yayi wa yarinyar gyadar dogo gurin auran attajirin mutum irin Dangaske! tabbas akwai jin dadi da dukiya wacce bata da iyaka! sai dai har yanzu bata samu irin nutsuwa da kwanciyar hankalin da take bukata ba, duba da cewa; tunda akayi auran take cin karo da matsala daban-daban, kuma har yanzu a cikinta take, wannan shine cikar mumini a gurin Ubangji, kuma duk wanda Allah yake jarabtarsa sa'i da lokaci yasa a ransa cewa shi d'an gatane, wanda aka bari sa-sakai yake sabgoginsa ba tare da ibtila'i ba, babu shakka shine abin tausayi. Talatu ita ma dai ta kasa tawakkali! duk ta zauce! tasa masifa a cikin ranta kullum tana tafe! a hanya kuma duk inda ta ga shanyar mutane sai ta kwashe ta tura a buhu ta je ta sayar, abinda Allah ya jarrabeta kenan. Hujaj duk yana da labarin abinda take aikatawa a gari, ga Hadiza ta famtsama har yanzu ba a san ina take ba, idan Talatu ta fita tun safe sai dare take dawowa gida. kuma babu yunwa bare kishirwa a gidan, tunda ya samu abinyi yana basu abinci su ci su k'oshi! amma ta gaza hakuri babban burinta ta samu nasarar hana shi aure sannan kuma ta haukata yarinyar da tayi mata fintinkau! Sutturun mutane cike da buhu! ta d'auka ta kai gurin dilallai ta sayar ta hada kud'in ta nufi gurin malamin dake mata aiki. Ta bashi kudin kamar yanda ya bukata. ya d'auki kayan asirin ya bata cikin wata k'warya da aka rufe da jan yadi! yayi mata bayani duk yanda zata aiwatar da aikin, cikin mota k'waryar asirin ke ciki ta fad'i! a take wasu tsintse sukayi firr! suka fito, lokacin ta kurma! uban ihu! direban ya tsayar da motar yana tambayar ba'asi! cikin fitar yayyaci! ta bude kofar motar ta fita tana ihu! tare da kokarin kamo tsuntsaye dake shawagi a kanta, sai ta cire dankwalinta tayi d'amara! dashi kawai ta dauki hanya yayin da tsuntsayen ke mata wani irin kuka a tsakiyar kanta. sune suka saita mata hanya ta dinga tafiya tana wasu irin surutai! Direban kuwa yana addua ya watsa sauran kayan shirkan, yaja motarsa ya bar gurin yana neman tsari da sake d'aukar fasinja irinta. **** Duk da kasancewar wannan shine karo na farko shiga jirgi a gareni ban nuna k:auyanci ba, na dai ji tsoro a cikin raina amma na daure ban nuna ba, kusa da shi na zauna Hajiya da Shukura suna tare. Hira suke a tsakaninsu wanda duk na tsargu sai nake ganin kamar da ni suke duba da yanayin fuskokinsu babu walwala. Shi kansa tunda muka shiga jirgin be ce komai ba, kuma har yanzu da damuwa a tare da shi, kuma ya lura da duk abinda su Hajiyan suke min, hakan ma ya 'kara masa 'bacin rai! kawai sai ya mayar da hankalinsa gurin jan madaidaicin carbin dake hannunsa. Ganin haka yasa nima na kama kaina amma cikin zuciyata na tsananta da addua. A haka muka sauka garin. Direbansa ne yazo ya d'auke mu bayan mun sauka a filin jirgin kai tsaye gidansa dake garin muka nufa domin shine umarnin da ya bayar. [1/28, 10:40 PM] Bintu: 118&119 Babban gida ne mai d'auke da 'bangare hud'u! ma'ana zaman mace hud'u! ginin gidan irin na zamani ne, kuma ya k'ayatu! da ababen more rayuwa, masu gadi da masu aiki cike da gidan kai kace a nan mai-gidan yake zaune dindindin! To jin cewa ya shigo garin yasa jama'a suka fara turereniya, kafin kice kwabo harabar gidan ta cika da mutane mata da maza. Akwai bu'katar ya samu hutu, idan san samu ne ma ya kwanta yayi bacci domin abinda na lura yana damunsa kenan bacci da gajiya da kuma damuwa! ga jama'a sunyi dafifi sun ja dogon layi suna jiransa a waje. Sama ya hau domin ya watsa ruwa a jikinsa ko ya warware. ganin haka yasa na bi bayansa domin ba zan iya zaunawa a tsakanin Hajiya da Shukura ba duba da irin kallon zargin da suke min. A sanyaye na bud'e dakin na shiga k'amshin sanyayan turaransa ya ba'kunci hancina, d'akin ya tsaru sosai! komai na mussaman ne a dakin, na samu gefen katafaran gadonsa na zauna ina kallon wani hotonsa dake kafe a bangon dakin, lokacin yana samartaka yayi kyau sosai! D'aya bangon kuma hotonsa ne a yanzu wanda yake cikin manya kaya farar shadda babbar riga da 'yar ciki da d'inkin sarakai! kamar koda yaushe da nad'in farin rawani a saman hular dake kansa, idonsa sakaye da farin gilashi. sosai na shaga gurin kallon hoton har ya fito daga band'akin ban sani ba, gilmawarsa na gani d'aure da babban towel a jikinsa da wani k'arami a hannunsa yana goge kansa . Ajiyar zuciya na sauke na kalleshi, shima ni yake kallo har ya zo ya zauna kusa dani da vasilin a hannunsa. Sai kawai na tsinci kaina da yi masa sannu. Ya yi murmushi da cewa; Ke za ayi wa sannu." "Saboda me?" na fada ina kokarin kar'bar vasiiln din dake hannunsa. Shiru ya yi bai bani amsa ba. kawai sai na fara shafa masa man a bayansa da hannayensa. Ya lumshe a ido tare da sauke ajiyar zuciya. cikin nutsuwa nake shafa masa man a sassan jikina ba tare da na kawo komai a raina ba na ce" Jiki ya yi sauki alhamdulillhi, ya kamata ka kwanta ka huta sai dai hakan ba zai samu ba duba da irin tarin jama'ar dake jiranka a waje, gashi kuma ka ce yau zamu koma gida. Duk maganar da nake bai ce min komai ba sai aukin kallona da yake. Lokacin gabana ya fad'i ganin yanda yanayinsa ya sauya, da sauri na cire hannuna daga kirjinsa tsoro nake kada ya ce zai min wani abu, dama tunda ya kwanta jinyya tsayin kwanaki takwas kenan babu wata mu'amula da ta shiga tsakaninmu. Aikam kafin ma nayi wani yun'kuri ya kamo ni zai kwantar a gadon. Ture shi nayi na matse a tsorace tare da gyara wuyan rigata. Ya kalleni a galabaice ya ce." Meye haka kuma?" Kai na sunkuyar k'asa na ce." Kayi sauri ka kintsa jikinka jama'a suna jiranka a waje. Ya ce." Bayan kin tayar min da hankalina, ba zan sauka ba sai nayi wani abu." Na ce."Ni kam babu ruwana me nayi maka?" Ya nuna kirjinsa da fadin." Nan kika sosa min." Kunya ta rufe ni ganin yana nuna min nipple dinshi, wai nufinsa lokacin da nake shafa masa mai na sosa masa gurin. Ya sake kamo ni a karo na biyu yana kici-kicin cire min riga. kuka nasa da cewa; daga zuwa sai wani abu don Allah ka bari ka fuskanci abinda ya kawo ka garin". Kai ya girgiza da cewa; Idan ban manta ba yau kwanaki takwas kenan rabona dake! kokari kawai nake, amma bana tsammani zan iya hakuri a yanzu kiyi hakuri ki sakar min jikinki, kuma ki taimaka min tunda babu kwari a jikina har yanzu. Na ce" To ka bari mana sai ka warware gabad'aya, nima jikina babu kuzari! ba zan iya komai ba." Shiru yayi na minti biyu kafin ya ce" Duk da haka dai idan kina so nayi sauri na kammala, sai kinyi wani abu akai, tunda kin fi kowa sanin yanda nake." Bude baki nayi zan yi magana yasa hannu ya rufe min baki tare da lumshe idonsa da duk suka sauya kala! Hakanan nayi ha'kuri! al'amarin ya kasance! wai mutumin da yake fadin bashi da 'kwari! amma sai da ya shud'e mintina arba'in yana abu daya kuma kamar koda yaushe sai da yayi sau biyu tukkuna ya sauka! A galabaice na tashi zaune ina gyara jikina, shimfidar gadon duk ta lalace! sai dana gyara tukkuna yana fitowa daga bandakin na shiga domin tsarkake jikina. Bashi da matsalar suttura a ko'ina, wardrobe dinsa dake dakin cike take da kaya nau'i daban-daban, ya zabi wanda yake so ya shirya ya sauka kasan, lokacin har iyayen nasa sun hallara suna zaune a falon gabadaya har da ita wacce ta assasa zaman wato Fatima. A mutunce ya gaishe da 'yan uwan mahaifin nasa, ya nemi uzurin zuwa ya sallami jama'ar dake jiransa a waje, kafin ya zauna domin gabatar da abinda ya tara su. Kimanin awanni biyu ya dauka da talakawansa ya yi musu alheri kamar yanda ya saba, sai dai matsalar har yanzu sun ki 'karewa dalili wasu na shiga wasu na fita, domin dai garin ya riga ya san da zuwansa. Ba don ya gaza ba, ba kuma don babu kudin ba a'a saboda uzurin dake gabansa ya dakatar da jama'a da cewa; suyi hakuri sai wani lokacin idan Allah ya nufa. sannan ya sanya daya daga cikin ma'aikatan gidan ya yi list din sunayen wanda suka rage, ya yi musu alkawari cewa; duk ranar da ya sake zuwa garin da su zai fara. Wannan ne ya kawo sanadin watsewar jama'ar da sukayi cikar kwari ciki da wajan gidan domin samun tallafi na abinci ko na kudi da makamantansu. Sai da suka gabatar da sallar azuhur tukkuna suka zauna Baba Audu ya bud'e taro da addu'a kafin ya d'ora da fad'in abinda ya tara su. Sai bayan da Baba Audu daya kammala maganarsa tukkuna ya kalli Sadiya dake zaune a kusa dashi ya ce." Hau sama ki kira min Shahida domin yana da kyau a zauna da ita." Hajiya da sauri ta ce" Alhaji Habu anya yarinyar ba ita ke sauya maka tunani ba? nifa yanzu na daina tausaya mata, bayan haka kuma meye amfanin zamanta a cikinmu, ita da ba kunne ba, me zata fahimta? ai na dauka itace ta assasa tashin hankalin.'' Ranshi ya sosu! da irin zargin da Hajiyar keyi wa yarinyar, ya gyara fuska da cewa; Shahida bata da hannu cikin faruwar wannan al'amarin, saboda haka don Allah Hajiya ku kyautata zatonku a kanta, sannan kuma ni dai wannan yarinyar bata isa tasa ni ba, bare ta hana ni." Kwafa! tayi da cewa" Mutum mugun icce ne wallahi, ni tausayinta nake da farko, amma ganin yanda lokaci guda ta birkita maka tunani yasa na fara zarginta, wani sa'in talaka abin tsoro ne." Baba Audu ya ce." Hajiya kiyi shiru wannan maganganun duk basu taso ba, idan fa an bi ta barawo to abi ta mabi sawu! itama Fatima bata da gaskiya, mai zai sanya ta je tana neman fitina da matarsa" Baba Auta ya kalleshi yana girgiza kai, wato ba tun yau ba, ya lura da cewa; D'an uwan nasa yafi goyuwa da bayan daya b'angaran duba da cewa akwai k'umbar susa! a duk lokacin da zama zai had'asu irin wannan kullum Saddiku ne mai gaskiya a gurinsa saboda yana da kud'i! yana ganin idan yaso zai iya umartar yaron ya mayar da Fatima dakinta amma yayi shiru saboda ba 'yarsa ba ce, ya san irin zaman da zai yi da shi. Ina kwance ina sa'kawa da kwancewa! Sadiya ta shigo na tashi zaune ina kallonta da tambayar yaushe ta zo? A sanyaye ta ce" Ban jima da zuwa ba, ki zo kasa ana nemanki." Gabana ya fad'i na ce" Ni kuma? Sadiya meye amfanin zuwana? ko nayi muku wani lefin ne?" Ta girgiza kanta da cewa" Ya kamata ki zo dai ki gaisa da iyayanmu suka ganki sannan kuma ki wanke zargin da suke miki, Hajiya ma yau ta furta da bakinta cewa; da sanya hannunki al'amarin ya faru." Hawaye suka cika idona na ce"Sadiya wallahi dana san abinda zai faru kenan da nayi shiru da bakina, domin na tsani abinda za a ce ni ce sanadi, kuma bana so zumunci ya lalace! sanadiyata. Amma wallahi ni ban sanya shi yin abinda ya yi ba." Ta ce." Kina da hujja mai karfi ba, ni kaina banga amfanin zamanta a gidan ba, tunda babu aure a tsakaninsu, kuma komai yana iya faruwa! baki da laifi domin kin nuna rashin amincewarki akan hakan, matsalar dai shi da ya yanke hukunci cikin fushi, shine dalilin da yasa Hajiya take zargin da sanya hannunki tunda bai ta'ba irin wannan furjewar ba. Jiki a sanyaye na ce" Ai shikkenan. ni fa idan abin zai zama rikici wallahi na hakura ya mayar da ita mutukar zamu zauna lafiya." Ta ce." Lallai Antina baki da wayo! kuma har yanzu baki san wacece Fatima ba, ko da yake zama bai had'aku ba shiyasa ki ke tunanin zaku zauna lafiya, wallahi bana sha'awar ta dawo gidan d'an uwana domin gabadaya sai kun rasa kwanciyar hankali. saboda haka duk rintsi kada kiyi wannan furucin. Shiru kawai nayi ina kallonta da tunanin abubuwa da yawa a raina. Tare muka sauka kasan, suka zuba mana ido har muka samu gurin zama. cikin girmamawa na gaishe su, suka amsa babu yabo babu fallasa, cikinsu babu wanda ya nuna min wani abu a fuskarsa, sai dai sanin zuciyar mutum sai Allah. Shiru na minti uku bayan zuwanmu gurin, Ya ce." Baba Audu duk na ji bayaninka, kuma ina so ku ajiye a ranku cewa! ni Abubakar abin ikon ku ne, komai na zama a duniya ban isa na sauyawa towo suna ba, ku ne iyayena kuma ina alfahari da hakan, koda yaushe kuna da damar yanke hukunci a kaina a matsayinku na 'kashin bayan samar da ni, sosai nake jin ku a raina dalili bani da wasu bayanku, amma ina so ku san da cewa; shi aure na mutum biyu ne, kuma ana yin sa ne domin samun nutsuwa da kwanciyar hankali, idan baku manta ba a can baya dole ku kayi min na auri Fatima ba don raina yana sonta ba, hakan yasa na sha wuya a hannunta, bayan ina iyakar bakin kokarina a kanta, babu irin masifar da ban shiga ba ta dalilinta, karshe ta zama sanadiyar mutuwar mahaifiyata, tabbas mutum baya kashe mutum face kwanansa bai kare ba, to amma wani yana iya zama sanadin wani, ni daku duk mun sheda cewa itace sanadin uwata dalilin zubar min da ciki da tayi ta dauka a leda taje ta dire a gabanta hakan yasa zuciyarta ta buga. babu imani bare tsoron Allah Ta tsallake tayi tafiyarta, a lokacin Ubangiji ya nuna mata ishara! tazo min da yarinya a matsayin tawa, wanda idan naso a lokacin zan bijire na nuna rashin amincewata, tunda bani da tabbas a kanta, amma ganin yanda yarinyar take kama da ni ya sanya na cire kokwanto bayan munje asibiti an gwada jini an tabbatar min da gaskiya lamari, wannan yasa na kwantar da hankalina na kar'bi yarinyar. Bayan haka abubuwa da yawa sun faru marasa da dadi da Fatima lokacin da take kasuwanci 'kasa-'kasa take zuwa, ta tara kudi masu nauyi ta sayi gida ta zauna ita kadai a ciki, wannan ya janyo ce-ce ku-ce na jama'a a kanta da yawa wasu na zarginta da harkokin banza, hankalina ya tashi da labari ya sameni, Hajiya tayi min maganar domin itama tana tsoron 'bacin suna a duniya, da kaina na sameta da maganar cewa; ta rufe gidan nan, amma ban hana ta kasuwancin taba, sai dai a duk lokacin da ta dawo yawonta ta sauka a gidana domin hakan shine rufin asirinta tunda taki aure, nayi hakan ne domin zumunci da kare mutuncinmu bakid'aya, sai kuma ta samu hanyar lalata min zamantakewar gida, ta d'auki karan tsana ta d'ora a kan matata, tashin hankalin yau na gobe daban, wannan yasa na ce lallai ta fitar da miji tai aure idan ba haka ba ta fice min daga gida. wannan shine abinda na san ya faru tsakanina da ita, sannan ina kara jaddada muku cewa; ba zan iya zama da Fatima ba saboda wasu dalilai! kuyi hakuri! ba wai na'ki bin umarninku bane, bana son abinda zai biyo baya na bacin rai, Fatima ta samu miji tayi aure ni zan shige mata gaba." Baba Audu ya ce." Hakane kana da gaskiya lamarin aure babu tursasawa! a ciki mussaman idan anyi ba a ji dad'i ba, saboda haka ni daga 'bangarena ina muku fatan alheri dukkaninku." Fatima na kuka Shukara na kuka yayin da Baba Auta ke marairaicewa! gabad'aya ya koma kalar tausayi! ya rasa wane kalar rarrashi zai yi a mayar da 'Yarsa. Itama Hajiya yanda na fahimta jikinta duk ya yi sanyi, ita kanta ta san idan Fatima ta sake shiga rayuwarsa a karo na biyu komai zai dagule! tunda dai har yanzu bata sauya hali ba. Jikina ya mutu murus! don wallahi a lokacin na tausaya mata sosai ganin yanda take zubar da hawaye! ba shakka tayi nadama! kuma yana da kyau! idan mutum ya tuba a kar'bi tubansa. Na kalleshi yana zaune fuskarsa kadaran kadahan! na ce"Duk da cewa; maganar bata shafe ni ba amma ina neman alfarma a gurinka." Gabad'aya duk sai suka zuba min ido har ita Fatiman ni take kallo idanuwanta ya yi fululu! saboda tsabar kuka da takaici. [1/29, 10:49 PM] Bintu: 120&201 Idona a tsaye a kansa na ce." Idan da yuwuwar Fatima ta dawo dakinta don Allah kayi hakuri komai ya wuce a tsakaninku, babu d'an adam d'in da baya kuskure! kuma tayi nadama ta nemi afuwa yana da kyau ka yafe mata, domin Annabi SAW yana son masu hakuri, wallahi nayi alkawarin zama da ita lafiya mutu'kar zata zauna da ni tsakani da Allah to ba ni da matsala." Falon ya yi shiru bayan gama maganata, duka suka zuba min ido, mussaman shi da gabad'aya bakinsa ya mutu, Sadiya kuwa wani irin kallo take min na rashin wayo da dubara. Sunkuyar da kaina nayi tare da k'o'karin daidaita yanayina domin dai nima k'arfin hali nayi gurin yin wannan maganar domin na tabbatar da cewa; ba shine gaskiyar abinda yake zuciyata ba, nayi hakan ne domin na goge zargin da suke min, to ya zanyi? ina bukatar zama dasu lafiya tunda ina son mijina, dole na nemi hanyoyin da zan samu nutsuwa da zaman lafiya da 'yan uwansa, amma har ga Allah ina jin tsoron ya amince da maganata ban san iya adadin tashin hankalin da zan shiga ba. A nasa 'bangaran kuwa gabad'aya yarinyar ta gama kashe masa jiki da kalamanta, a yanzu dai ba shi da wani furuci da zai yi wanda zai gamsar da su, tunda ta riga ta watsa masa tsakuwa a ido! sai kawai ya sauke ajiyar zuciya da fad'in" Shikkenan zan yi shawara a kan hakan, duk hukuncin dana yanke in sha Allahu zamu sake zama makamancin wannan." Jin abinda ya ce sai farin ciki ya baibayesu mussaman Hajiya da bakinta ya kasa rufuwa albarka kawai take sanya min. Dukkaninsu Suka kasance cikin walwala da farin ciki, Sadiya ma ta ara ta yafa ta shiga murna amma in zaka tona zuciyarta tafi kowa 'kin al'amarin, dalili ta san da cewa ba za a wanye lafiya ba. Ni kam damuwa mai tsanani! na shiga a lokacin da na ji yayi furucin, sai na fara hasaso irin zaman da za mu yi, wasu hawaye masu zafi suka ciko idona, babu yanda zanyi shiyasa na yanke wannan hukuncin domin samun maslaha a tsakaninsu tunda naga hakan na nema ya lalata zumuncinsu, wanda ni kuma ba zan so hakan ba, kuma ina so na cigaba da zaman lafiya da Hajiyar kamar yanda muka dauko. Bayan la'asar muka shirya tafiya bayan mun ci abinci kowa ya samu nutsuwa a tsakaninsu idan ka cire ni da shi da muke cikin damuwa, domin tun bayan da nayi masa wannan maganar ban sake ganin dariyarsa ba, kuma bai min wata magana ba, har muka shiga jirgi babu abinda ya ce min, sai dai jefi jefi idan su Hajiya suna hira na kan sanya musu baki. Amma yanda ya watsar da ni abin ya mini ciwo sosai daurewa kawai nake har muka sauka. Ina shiga d'akin na kwanta kan gado, kukan dake cin raina ya kufce! na rufe fuskata da tafukan hannuwana ina ta risgar kuka! zuciyata na wani irin zafi! Maganarsa na ji a kunnena na bud'e ido ina kallonsa har yanzu fuskarsa babu sassauci! ya ce." Kukan me ki keyi kuma?" Shiru nai ban ce komai ba. Ya ce." Kin 'bata min rai sosai wallahi, kin fi kowa sanin cewa; bani da wannan ra'ayin mai zai sanya kiyi wannan furucin a gabansu, idan ke kad'ai ce ba kya bukatar zamanki a haka sai na auri wata amma babu Fatima a cikin tsarin rayuwata a halin yanzu." Hawaye na goge wasu na sake zuba na ce" Ya kake so nayi? dukansu fa suna min wani irin kallo tare da zargin kamar da sanya hannuna cikin faruwar al'amarin, ni kuma wallahi babu mugun nufi a zuciyata, hakika ina sonka mutuka, kuma ina da burin na zauna ni kadai babu kishiya sai dai na san hakan ba zai yuwu ba saboda tsakanin ni da kai babu wanda ya isa ya tsarawa kansa rayuwa face wacce Allah ya tsara masa, duk 'kin ka da Fatima idan akwai shauran zama a tsakaninku dole sai ta dawo gidanka, ni ban isa na hana ba, amma nayi hakan ne domin na wanke kaina a gurin iyayenka da Hajiya wacce lokaci guda ta sauya min, ta daina sakar min fuska ko na gaisheta da 'kyar take amsawa, ni kuma ina sonka tare da k'aunar zama da kai, dole kuma na nemi zaman lafiya da 'yan uwanka." Wani irin tausayi da k'aunarta ya sake nunkuwa a zuciyarsa, tabbas yanda yarinyar ke k'aunarsa tare da sadaukar da farin cikinta a kansa, ya zama dole ya nuna mata cewa shima d'an halak ne. Ya ce." Kiyi hakuri ki share hawayenki kuma ki cigaba da addua Allah ya za'ba min abinda yafi alheri a rayuwata, in sha Allahu kuma zan yi miki hallaci fiye da yanda ki kayi min, zaki zauna ke kad'ai kamar yanda ki ke bukata. Hannunsa na rike da cewa" Maganar Fatiman fa?" "Zan yi istahara a kai kada ki damu ke dai kiyi mana addua." A sanyaye na ce" Allah yayi mana za'bi na alheri." Ya amsa da "Ameen ya Allahu." KANO To an nemi Talatu an rasa a garin Kano, anyi cigiya gidajen tv da redio har yanzu ba a samu labarinta ba, 'Yan uwanta sun shiga damuwa sosai tare da 'ya'yanta, abu biyu ya damesu, dawowar Hadiza gida da cikin shege wanda ya janyo Hujaj d'in ya yi mata dukan mutuwa! har sai da ya yi mata targad'e a hannu saboda ta'ki fad'ar wanda yayi mata cikin, sai da aka tsananta mata da tijira da duka sannan ta ce ita ba zata tantance wanda ya yi mata ciki ba tunda mazan da suke nemanta suna da yawa cikinsu babu wanda zata nuna tace shine ya yi mata. Hujaj ya kasa daure zuciyarsa kuka wurjajan! ya dinga ti'ka! domin da shi a ganinsa yarinyar ta gama keta masa rigar mutunci, duk da yana jin irin surutan da jama'a sukeyi cewa; abinda ya aikata ne ya waiwayo! amma ai shi duk yawon bariki da ya yi, bai ta'ba yin zina ba, ya san dai yana kashewa mata kudi a can baya yana d'an tattaba jikinsu, amma bai ta'ba yi wa yar wani ciki ba. Takaicinsa shine a yanzu da duniya ta sheda tuban sa ta sanya masa rigar mutunci, tare da azurtashi da suruki nagari, wannan matsalar ta kunno masa a rayuwarsa dole da yawa mutane suyi masa wani irin kallo. bayan haka kuma duniya ta tabbatar da cewa; Talatu 'bauraniya ce! domin har gida aka zo nemanta da zummar binkice a kanta a lokacin da wani yaro ya ga lokacin da take satar tufafin mamansa da mai wanki ya shanya a baranda, wannan shine mummunan aikin da ta aikata na 'karshe ! wanda kuma yanzu bata cikin hayyancinta sakamakon abinda ta shuka ta ke girba. Hakanan Hujaj ya yi ha'kuri da k'addara! ya kar'bi Hadiza da cikin dake jikinta wanda aka rasa waye ubansa, sai dai ya zubar da hawaye sosai! na bakin ciki tare da nadamar hada zuria da Talatu, amma yanzu ya yi sa'a matar da ya aura mutuniyar kirki ce, kuma tana da ilimin addini, itace take tausar zuciyarsa da kalamai masu sanyi, kuma ta bashi shawarar dawo da yaran gabansa, sannan kuma tayi alkawarin rike su da amana, domin dai d'a duka na kowa ne. To wannan shine dalilin da yasa su Hadizan suka dawo gaban mahaifinsu da zama, kuma Murja matar Hujaj din dai-dai gwargwado tana iyakar bakin 'ko'karinta a kan su mussaman Hadiza dake d'auke da juna biyu. Ba a tashi ganin Talatu ba sai a Damaturu, cikin wani k'auye lokacin duk ta fice daga hayyacinta, don an samu wasu 'bata garin ma sun kwanta da ita ba'a adadi! gabanta sai ciwo yake mata yana zubar da wani irin ruwa mai wari! domin ko lokacin daka d'aukota haukata take tu'kuru! tana soshe-soshe! jiddin hannunta a gabanta tana karta! cikin surutan da take na hauka ta dinga tonawa kanta asiri kan abubuwan da ta aikata tun daga kan Mariya har zuwa kan 'yarta data tafi ta bari. Kai tsaye gidan mahaukata aka nufa da ita domin bata taimakon gaggawa! **** ABUJA Sati biyu da faruwar al'amarin, zamantakewar gidan tayi kyau! dalili Hajiya da Shukura duk sun kwantar da hankalinsu sakamakon furucin da nayi akan dawowar Fatima gidan, sun saki jikinsu sosai! muna mu'amular arziki, Sosai Shukura take bani girma, wanda hakan yake faranta min rai mutuka. Bangaran mijina ma sai godiyar Allah zama muke na mutunci da girmama juna, idan soyayya ta zo muyi kamar zamu cinye junanmu, yawan shekarunsa bai sanya ya tauye kansa ba, abubuwan da yake min na soyayya har mamaki nake! lallai na yarda da cewa; dattijai sun fi iya kula da mace da tarairaya ba kamar matasa irin na yanzu ba, sosai muka samu fahimtar juna, kuma muna kokarin kyautata kanmu ta hanyoyi da yawa, mussaman ni da na riga na fahimci abinda yake so, sai na rike hakan hannu biyu, na kuma sanya juria a cikin raina, amma duk da haka ban zauna ba, ina 'ko'karin gyara jikina da sha da kuma cin abubuwan da zasu saukar min da ni'ima duk domin ya samu yanda yake so idan bu'katarsa ta tashi. Hankali ya kwanta sosai! wata irin ki'ba nake narkawa ta 'kasa, nono na ya ciko sosai ya 'kara girma! kwankwasona ya bud'e! da yawa duk kayan da nake sanyawa sunyi min kad'an, sai wasu aka din'ka, ga wani irin haske da nayi fatata tayi kyau! ainun! lokacin sai ka rantse da Allah cewa; Yaron ciki ne da ni duba da yanda suffofina suka sauya ta ko'ina. Shi kansa mai-gidan tsokanata yake wai na zama 'yar lukuta! ko dai na samu ciki ne nake 'boye masa! dariya kawai na kan yi a duk lokacin da ya yi irin wannan maganar sai na ce" Sai na fi kowa farin cikin samun ciki a yanzu kuma in sha Allah da 'yan tagwaye zan fara." Kalamai na suna faranta masa rai mutu'ka! addua yake tare da burin tabbatuwar furucin bakina. Watana biyar a gidan 'yan uwana suka zo kaf! Baba Asabe da tawagarta Babana ma tare da 'yan uwansa maza da mata. sosai na yi farin cikin ganinsu, kuma sun samu tar'ba mai kyau daga gurin mai-gidan, don lokaci guda ya ware ya zauna tare dasu suka gaisa cikin girmamawa, hakan ya faranta min rai sosai yanda ya karrama dangina itama Hajiya bata nuna wani abu ba yabo na ta dinga yi a gabansu tana fad'in alheri na. Baba Asabe ta dinga jin dad'i tana kallona na san mamaki take ganin yanda gabad'aya na sauya bakinta ya'ki rufuwa duk inda na gifta sai ta bini da kallo. shi kansa Babanmu na lura da yanda yake kallona sa'i da lokaci sai dai yayi murmushi ya girgiza kansa. Saliha kuwa har sai da na gaji na tambayata kallon me take min, domin tamkar tv na zama a gurinta, ajiyar zuciya kawai ta sauke ba tace min komai ba ta d'auke kanta, sai kawai nayi murmushi cikin zuciyata na ce Saliha kenan har yanzu hali yana nan, dama can haka take min ko yaya na samu cigaba a rayuwata sai naga wani canji a tare da ita, ban san abinda yake damunta ba. Na ce." Baba ban ga Talatu da Hadiza ba me yasa basu zo ba?" Jamila ce ta kalle ni sai naga idonta ya ciko da ruwan hawaye! Jikina ya yi sanyi na dafa kafadarta da fadin." Menene?" Sai kawai ta fashe da kuka tare da rungume ni! Nima nan take na ji hawaye ya ciko idona! Na kalleshi da cewa; Allah yasa lafiya?" Shiru ya yi yana girgiza kansa. "Anti Murja matarsa ta ce" Sai hakuri da rayuwa! kaddara kuma bata wuce kan kowa ba." A sanyaye na ce"Anti Murja me ya faru? ko mutuwa su kayi ?" Ta ce" Duk suna raye sai dai suna cikin wani hali wanda addua ita kad'ai ce magani." Hawaye suka zubo min. na ce"Rayuwa kenan! Ubangiji Allah yasa muyi kyakykyawan karshe yanda yanayin ku ya nuna tabbas al'amarin babu dad'i, amma duk rashin dad'insa ina da bukatar na sani ko da taimakon da zanyi a kan hakan." Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya warware min duk abinda ya faru! gabad'aya kasa daurewa nayi hawaye masu tsananin zafi suka shiga sauka a fuskata, na gagara! cewa komai tsabar yanda nake jin wani irin takaici a cikin raina Hannu nasa na share hawayen fuska da cewa; Allah ya bata lafiya, ita kuma Hadiza Allah ya sauketa lafiya, amma hakika na tausaya mu su sosai! Allah yasa mu fi karfin zuciyoyinmu." Gabad'aya suka amsa da "Ameen ameen. Duk cikin alhini da damuwa! Kwanansu biyu suka shirya tafiya, shatara ta arziki mai-gidan ya yi musu, sannan ya yi musu kyautar kujerar Hajji su Uku Babana Baba Asabe da Anti Murja! To basu ba ni kaina sai da na taya su godiya, sai ya nuna babu wannan a tsakaninmu, duk abinda ya yi min riba ce a gurinsa ba fad'uwa ba. Da zasu tafi nayi Wa Saliha da su Jamila kyautar zannuwa da mayafai tare da kayan kwalliya da turaruka masu tsada! duk abinda na san zai faranta musu rai! sai da na d'auka na ba su, muka rabu cike da kewar juna! sai da suka shiga mota sannan kuma zuciyata tayi rauni! kuka ne yake so ya 'kwace min ina hana shi, amma ban samu nasara ba, motar tana fita daga gidan, nasa hannu na rufe fuskata da sauri na juya domin komawa cikin gidan, ya rungumo ni jikinsa yana rarrashina sai kawai na fashe da kuka! tare da kwanciya a jikinsa a haka muka shiga falon, duk ya rasa yanda zai yi da ni, Allah yasa babu kowa a falon, hakan yasa duk nauyi na ya d'auke ni muka hau sama yana ta yi min kalamai! ni kuwa ina sane nake kuka da sangarta lallai sai na bi su tamkar k'aramar yarinyar haka na zama, ya zaunar da ni kan gado duk ya rikice! fad'i yake " Yanzu ki ke so ayi?" Shiru nayi kuma ban fasa kukan ba don hawaye ne jaga-jaga a fuskata! wani sa'in ina jin dad'in yanda yake biye min idan ina irin haka duk sai ya shiga damuwa! komai nasa sai ya tsaya, baya samun nutsuwa har sai ya ga na warware ina dariya sannan zai kwantar da hankalinsa. Yanzu ma kwantar da ni ya yi a gadon yana ta shanye hawayen fuskata yana jijjigani tamkar 'yar goye! ganin yanayinsa ya fara sauyawa yana wasu abubuwa yasa da sauri na tashi daga jikinsa, aikuwa yace bai san wannan ba! sauka zanyi daga gadon, ya kamo ni ya kwantar! danne ni ya yi ya d'ora min nauyinsa, lokacin na shiga nutsuwata! na fara dana sanin abinda na aikata, aikuwa dai bai sake ni ba sai da nayi kuka mai dalili da ro'ko da bada hakuri sannan ya sauka na tashi jikina duk ya yi tsami. [1/30, 9:20 PM] Bintu: 122&123 Rayuwa tana tafiya sannu a hankali, da dad'i babu dad'i haka ake hak'uri, dama ba dole d'an adam ya samu abinda yake so d'ari bisa d'ari ba, sosai na samu kwanciyar hankali fiye da lokacin baya ba, amma wani lokacin na kan 'buya a d'aki na zubar da hawaye a duk lokacin dana tuna cewa ko 'batan wata ban ta'ba yi ba wanda ya yanzu watanni goma kenan da auranmu, kuma iyakar bakin k'okari yana yi idan yana gari babu d'aga kafa kullum maganarsa na samu ciki na haihu amma babu labari, na shiga damuwa sosai, lokacin da watarana na farka daga bacci na ganshi gurfane! gaban Ubangiji yana addua kamar zai fashe da kuka! wasu hawaye masu rad'ad'i suka ciko idona da sauri nasa hannu na rufe bakina gudun kada sautin kukan da nake ya fito fili, rufe fuskata nayi da bargo hawaye na ta kwaranya watakila ba zan haihu ba, abinda nake rayawa kenan a cikin zuciyata, idan Allah ya kaddara mini hakan dole na bashi goyon bayan auran wacce zata haihu, ko kuma tilas ko baya so ya dawo da uwargidansa domin samun zuria tunda Allah ya bashi dukiyar dashi kansa bai san adadinta ba. Tunanin da nakeyi kenan wanda ya haddasa min karyewar zuciya kukan dai da nake boye wa sai da ya fito fili, na rungume! filo a jikina tare da kiran innalillhi-wa'ina ilaihi raji'un! Cikin tashin hankali ya zauna kusa dani yana birkitoni ina sake kudindine jikina! kuka mai sauti ne yake fita kuma ban fasa kiran sunan Allah ba. Damuwa mai tsanani! ya shiga ya rungume ni tsam! a jikinsa yana rarrashina domin na fad'a masa damuwata. Murya a dashe! na ce" Wata'kila bani da rabon haihuwa a duniya." Gabansa ya fad'i jin abinda ta ce. da sauri ya ce." Saboda me zaki fadi wannan maganar? ko kina da masaniyar abinda Allah ya rufe?" Hannunsa na ri'ke da kyau na ce" Wata goma kenan ina lissafi ban ta'ba 'batan wata ba, duk da cewa kana iyakar bakin 'ko'karinka, amma babu wani alamu da ya nuna zan samu ciki, ina jin tsoron halin da zamu shiga idan Allah ya kaddaro ni a matsayin juya mara haihuwa." Ya ce." Wace irin magana ce wannan?" yafad'a cikin 'kunar zuciya. Girgiza kaina kawai nayi ban ce masa komai ba. sai ya cigaba da cewa" Ashe kin manta Allah shi yake bayarwa kuma shi yake hanawa, me zai sanya kiyi wannan furucin bayan kina cikakkiyar musulma, idan kin kasance d'aya daga cikin mata marasa haihuwa menene? ko kina tunanin zan rabu dake saboda wannan matsalar? wannan ba hujja ba ce domin banga abinda damuwa da tashin hankali ba, wata goma kacal ba shi zai tabbatar da abinda ki ke zargi ba, akwai ma'auranta da suka fi shekara goma da aure basu haihu ba, amma basu cire tsammani ba, domin wani rabonsa yana nesa mutukar an barwa Allah lamarin sai ya kawo d'auki a lokacin da ba ayi tunani ba, don haka kada ki sake damuwa da wannan komai lokaci ne. A sanyaye na ce" Ba zan iya jurewa ba, domin a yanzu babban burina na haihu mussaman dana fahimci abinda kafi bukata kenan! yana da kyau a duba ni ko ni ce nake da matsalar mahaifa" Cikin rauni da sarewa nayi maganar. Shiru yayi na minti biyu kafin ya ce." Za a yi hakan in sha Allahu. amma abinda nake so dake shine; ki samu nutsuwa kada ki sake kuka akan wannan dalilin komai na Allah ne, kuma in sha Allahu zaki haifa min yara da yawa." Ajiyar zuciya na sauke a sanyaye na ce" Amin ya Allah. Rabbi ya bamu masu albarka. Ya amsa da "Ameen tare da rungumeni tsam! a jikinsa. To koda likita ya dubani bai ci karo da wata matsala ba, kyakykawan sakamako ya fito cewa; cikin kowane lokaci zan iya d'aukar ciki, kawai lokacin ne beyi ba, amma likitan ya ba shi shawara cewa; ya d'an dinga d'aga k'afa saboda wani sa'in! cikin yana iya shiga amma yawan wannan abu na sanya maniyin ya tsinke cikin ya fita ba tare da an lura ba. Wannan dokar tasa shi a damuwa mai tsanani domin da ya riga ya saba mutukar yana gida yana manne dani, nima har na saba da lamarin, haka dai ya yi hakuri tare da 'kokarin bin dokar amma wani lokacin idan lamarin ya bijiro masa haka zai zo ya yi kwance a gado! yana nishi! hanyoyin dana san yana so nake yi masa duk don ya samu gamsuwa, hakan baya samuwa domin baya iya samun satisfied a haka sai ya shiga wannan guri, don haka baya ma neman shawarar kowa a lokacin yake mantawa da dokar likita ya haye kaina kuma baya sauka sai ya zubar da duk abinda ke damunsa. Haka muka cigaba da tafiya dokar likita ta tashi a banza domin babu abinda ya fasa, a cewarsa idan Allah yaso zartar da hukuncinsa babu wanda ya isa ya hana, duk yanda naso na fahimtar da shi, ya'ki saurara ta, wani lokaci idan na furje! na ce ban yarda ba, sai mu kwana mu yini bai kulani ba, idan ya fita tun safe baya dawowa sai dare! ganin haka yasa na ha'kura na kyaleshi yana yin yanda yake so. A cikin tsukin muka je umara gabad'ayan mu har da Shukura! sati biyu mukayi muka dawo gida. kamar wacce ta dawo da ciwo a ranar haka na kwana da wani irin ciwon ciki mai tsanani! na galabaita sosai! sai gefin asubahi! jinin yazo! nayi mamaki sosai! ganin cewa duka ban fi kwana goma da yin wanka ba, amma jinin ya dawo mini, wanda ban ta'ba haka ba tunda nake lafiya lau yake zuwa ya tafi bana ciwon mara bare na 'kafa! kuma jinin ya sha bam-bam! da irin na haila, wannan mai kauri ne! Likita yasa aka turo daga babban asibiti, tazo har gida ta dubani! to itama dai shawarwari ta bani, sannan tace watakila na samu ciki ne ya lalace! sai ta bani magunguna wanda zasu taimaka min. Bayan likitan ta tafi na kalleshi da cewa; Itama kaji abinda ta fada ko? ka bar mutum da aikinsa da kuma abinda ya sa ni, don Allah kayi hakuri kana d'aga kafa kada mu dinga asarar 'kwai'kwayanmu a banza. Maganata ma dariya ta ba shi sai da ya dara tukkuna ya ce." Tom zan yi kokarin yin hakan." Cike da jin dadi na ce "Yawwa to ko kai fa." Kallona ya yi tare da murmushi ya tashi ya nufi band'aki sai na bi shi da kallo ina tunanin abubuwa da yawa a tare dashi. Mutum ne shi mai kawaici da kawar dakai! na karanci halayensa! sosai yana da sauki kai da fahimta, amma duk abinda yake akan lamarin na lura cewa dauriya ce, abin yana damu sa, kawai yana dannewa ne gudun kada na shiga damuwa. Matsalar da ta kunno kai a gidan ita ce ta rushe duk wani farin cikina, sai ya kasance! kullum ina sama sai kace tsuntsuwa! bani da damar na sauko k'asa nayi walwala da mutan gidan, sai 'bakar magana daga Hajiya. gabad'aya ta sauya mini kullum maganarta d'aya ban haihu ba, amma na kankane! gida na hana a dawo da mai haihuwa! da sauti mai k'arfi take maganar a duk lokacin dana gifta ta kusa da ita sai ta san irin munanan maganganun data fad'a mini har cewa take na zama bijima! na samu duniya sai narka uwar 'kiba nake ina kasayarwa, amma na gagara! daukar ciki! kuka nake sosai a duk lokacin da bakin ciki ya ishe ni, gashi mai-gidan baya gari ya je ghana duba wasu ma'aikatu da zai saya! shi da kansa yake fad'a min cewa" Allah ya had'a arzikimu domin tunda ya aure ni yake ganin bud'i da d'aukaka! domin dai har sarauta a ka ba shi wato maji dad'in Katsina saboda irin gudumawar da yake bayarwa yasa sarki ya bashi wannan sarautar, bayan haka kuma dukiyarsa sai kara yawaita take dalilin samun nutsuwa da ni matsalar dai itace wannan dake 'kokarin kassara farin cikinmu. Na san ina da hakuri sosai! amma idan nazo iya wuya ina da wuyar sarrafuwa! domin idona rufewa yake duk sai na amayar da abinda yake damuna. Abinda ya faru kenan tsakanina da Hajiya na sauko da zummar shiga kicin, ta fara farfad'a min magangunu kamar yanda ta saba sai na gaza hakuri na dawo da baya na tsaya, lokacin Shukura tana zaune kan kujera da wayarta a hannu uffan ba tace ba, domin itama tun bayan tafiyar mahaifinta take min wani gani-gani. Na ce" Wai shin Hajiya haihuwar waye yake bada ita ne?" Kallona tayi kafin ta ce.'' Rashin kunya za ki yi min ne fitsararriya ai ba banza ba Allah ya hallice ki haka." Wasu hawaye masu zafi suka ciko idona, ban bari sun zuba ba na ce" Har da kushe hallitar Ubangiji kuma? ke ma dai baki wuya komai a gurin Allah ba, domin ba a gamawa dan adam hallita har sai ranar da ya mutu. Hajiya a she dama duk kulawar da ki ke min ta ganin ido ce? me nayi miki da zaki tsawwalawa rayuwata, ke kanki kin san cewa'' Allah shine mai bayarwa kuma shine mai hanawa." "Kin ga yi min shiru munafukar banza da wofi." Tafada tana zazzare min ido! raina ya sake 'baci! na ce"Hajiya munafurcin me nayi miki?" Tsaki tayi kafin ta ce " Duk abinki sai Fatima ta dawo d'akinta, idan kuma bata dawo ba to babu shakka sai an kawo mai haihuwa tunda ke ba zaki haihu ba." Hawayen da nake dannewa suka subce suka fara gudana a saman fuskata! na ce" Maganar dawowar Fatima d'akinta Allah ya gani nayi iyakar bakin k'ok'arina hakan bai yuwu ba, aure kuma ko baki fad'a ba da kaina zan sanya shi ya yi, domin samun zuria kamar yanda kuke buk'ata, idan yaso duk lokacin da Allah ya bani sai ki kashe shi." Shukura ta ce" Lallai wannan baki da mutunci Hajiyar ki ke fad'awa wannan maganar?" Ko kallonta ban yi ba naja tsaki! na bar gurin zuciyata a masifar k'untacce! Ashe bayan na bar gurin kiransa sukayi a waya Hajiyan tana kuka take sheda masa cewa; na yi mata rashin kunya harda zagi! Bai ji dadin faruwar al'amarin ba, shiyasa ba kasafai yake so yayi tafiya mai nisa ba saboda gudun faruwar matsala irin wannan, amma ba zai yanke hukunci ba tukkuna sai ya koma gidan. Sai da ya dawo na lura da sauyi a tare da shi, tunda dai lami lafiya mukayi sallama da juna ya tafi, amma kuma ya dawo babu walwala. Duk abinda yake bukata na gabatarsa masa, ya yi wanka ya shirya cikin k'ananun kaya kafin ya zauna gurin hutarsa na kai masa abinci, na had'a masa komai har ya kammala cin abincin bai ce min uffan ba, nima banyi masa magana ba kawai na zuba masa ido ne nasan lallai ruwa baya tsami banza. "Me ya had'a ki da Hajiya har kina kiranta da munafuka yaushe ki ka lalace kema?" Ya yi maganar ne a lokacin da ya kammala cin abincin yana goge bakinsa da tissue. Shiru nayi ina kallonsa da jin takaicinsa a raina, har kullum idan matsala zata faru baya binkice akai zai zo ya turke ni. Ganin nayi shiru ina kallonsa yasa ya ce." Ko ba kya ji ne ki bani amsar dana tambayeki." Ajiyar zuciya na sauke da cewa; Ni bani da wata amsa da zan baka." Ya 'bata rai da cewa" Kin raina ni ko? shiyasa ki ka samu sararin cin zarafin Hajiya saboda kina ganin hakan shine daidai a gurinki ashe kema mutuniyar banza ce." Kuka ne ya kufce min na ce" Wallahi na gaji da wannan masifa! na gaji! kawai ka sake ni! idan yaso sai ka auri mai haihuwa ai Allah shi yake bada haihuwa ba wani mahalu'ki ba." Zuba min idonsa ya yi a lokacin da nake maganar ina rusa kuka! tabbacin abin yana mugun damuna! na tashi naje na kwanta kan gado hawaye na zuba kamar an kwance famfo! Ya zo ya zauna kusa da ni yana kokarin ri'ke min hannu na fizge da fadin." Ko da yaushe idan matsala ta faru baka binkice zaka d'auki lefi ka d'ora mini, to na gaji da wannan abu, a k'yale ni na samu nutsuwar zuciya haka. Ya ce." Ni ki kewa tsawa?" d'auke kaina nayi daga kallonsa naja bargo na rufe fuskata! kukan dai na cigaba da yi tare da nemo hanyar warware matsalata. Gadon ya hau ya tayar dani zaune, da alamar sassauci a fuskarsa ya ce." Na yi kuskure! kuma na kar'ba, amma mai yasa zaki biyewa Hajiya har ki fad'a mata maganar da bata dace ba, kin san da cewa dole raina ya 'baci idan na ji hakan. Hannu nasa na share fuskata na ce" Yanda ka kira ni da mutuniyar banza shine ya 'bata min rai! amma wallahi ban zagi hajiya ba ballanatana na fada mata mummunar kalma, nasan dai tun bayan tafiyarka ta hura min wuta a gidan nan, cin mutuncin yau daban na gobe daban....duk na kwashe abinda yake faruwa na fad'a masa! Ya ce." Ki yi hakuri watarana sai labari, abinda yake damun Hajiya shine yake damuna yake kuma damunki, amma dukkaninmu bamu isa mu bawa kanmu farin ciki ba face sai Allah ya bamu. babu shakka haihuwa rabo ce ga wanda rabbi ya so, muna sanya rai muna daga cikin wad'anda ilahi zai azurtamu da zuria masu yawa da albarka. tuntuni na barwa Allah ikonsa domin duk yanda naso idan lokaci beyi ba dole nayi hakuri, amma idan abinda ya dame ni nakan zubar da hawaye tare da tsananta roko a gurin Ubangiji." Cikin tsantsar damuwa ya kai karshen maganar. Na ce" Ga shawara idan zaka d'auka zata amfane mu duka." Kallona ya yi kafin ya ce." Ina sauraranki. "Don darajar Allah da Annabi ka dawo da Fatima idan kuma hakan ba zai yuwu ba to kayi aure, dalili shekaru sun fara hawa kanka ya kamata a ce yanzu kana da yara masu yawa. ni ba zan tauye ka ba, duk da cewa; shekarar mu guda da aure amma ba zan damu ba don ka auro wata wata'kila nima na samu rabona ta dalilin hakan." Fuskarsa ya had'e ya ce." Zanyi shawara a kan haka." Bai sake magana ba ya sauka daga gadon. lamarin da ya janyo mini 'bacin rai! domin dai daina shiga hurumina ya yi duk 'kwa'kwarsa da sha'awarsa ajiyesu ya yi a gefe ya shiga sabgar gabansa, sai ya zama gaisuwa ce kawai take had'amu da kuma sannu da zuwa a duk lokacin da ya dawo. Ni na neme shi da maslaha domin na tsani irin wannan zaman a rayuwata! shi kuma b'acin ransa akan me zan ce ya yi aure! a lokacin ya sake jaddada min cewa; zai ha'kuri da yanda Allah ya tsara masa rayuwarsa, zai kuma zauna tare da ni a yanda Allah ya halliceni. sosai na yabawa k'o'karinsa da sadaukarsa kuma ya cika d'an halak! kamar yanda yake fad'a mini a koda yaushe cewa zai yi mini hallaci fiye da yanda nayi masa to naga zahiri gashinan, Allah ya riga ya gama yi masa komai na daga jin dadin duniya yana da ikon ajiye mata hudu a gidansa ba tare da wata matsala ba, rabbi ya wadata shi da lafiyar da ba kowane namiji ba, uwa uba kuma zahiri ya nuna matsalar rashin haihuwa daga gareni ne, tunda shi dai ga sheda nan budurwar 'yarsa Shukura! amma hakan bai sanya ya yi yun'kurin kawo wacce zata tara masa iyali ba kamar yanda yake da buri, sai ya sadaukar da farin cikinsa saboda ni, ban san wane irin so yake mini ba. [2/1, 10:08 PM] Bintu: 124&125 Haka rayuwar ta cigaba da tafiya yau fari gobe b'aki, jin dad'in duniyar gashi nan, amma babu kwanciyar hankali, rashin nutsuwar kuma bai sanya na lalace ba abin mamaki! ma wata irin ki'ba na ke yi mussaman ta k'asa, kwankwasona ya bud'e sosai! haka ma k'irjina ya bun'kusa, ga wani irin kyau da na yi fatar jikina ta yi taushi da kyau! tamkar ta jarirai! wannan shi yake d'aga hankalin Hajiya da duk wanda zai ga yanda na zama babbar mace! tabbacin cewa; ina hutawa da jin dad'i, ko ga yanayin sutturun da nake tu'ammali da su, domin duk lokacin da ya yi tafiya 'kasashe! tsarabata ta mussaman ce, idan ya je india akwati guda yake kawo min ta kayan ado irin na su, fakistan da sar'k'oki da abun hannu har da sar'kar k'afa, a cewarsa yanda na zama yar duma-duma shigarsu za ta yi min kyau! ganin yana so sai na mayar da hankalina gurin yi masa ado iri daban-daban. Zuwa na ganin gida na farko! 'karara na ga bacin a fuskarta Saliha, sai dai ta yi 'kokarin 'boyewa amma hakan bai yuwu ba, tunda dama can haka take nuna min sam bata k'aunar wani cigaba na. Baba Asabe kuwa ta din ga ina asa ka ina a aje da ni, duk ta rasa yanda za ta yi, kula ta mussaman take ba ni, har abin ya so ya yi yawa, sai da na ga ji nayi mata magana tukkuna ta rage, to hakan ma ya 'bata ran Saliha, ni kuwa duk da na fahimci hakan daga gare ta ban fasa yi mata alheri ba, zannuwa masu kyau na yi mata kyauta da su tare da sar'koki irin wanda na cire. Gidan Babana ma haka sun tar'be ni hannu biyu, wannan karon Baba ya yi sa'ar matar aure tun bayan rabuwarsa da mahafiyata, ko da yake shima ba halin kirki gare shi ba, yanzu ne dai ya kintsu! Lokacin da naga Hadiza turus! da ciki wasu hawayen takaici ne suka ciko idona! wanda duk da na yi 'ko'karin dakatar dasu sai da suka zuba. na kalleta a lokacin duk hallitunta sun sauya, da alama daf take da haihuwa, lebanta ya yi jajawur! haka nan, jikinta duk ya kumbura! kawai na zauna ina kuka! ina kallonta Itama sai ta fashe! da kuka ta rike min hannu tana kukan ta ce." Kin ga halin da Talatu ta je fa ni ko? watakila ma cikin nan shine ajalina." Na yi saurin rufe bakinta da cewa; Hadiza k'addara ba ta wuce kan kowa ba, amma wani lokacin mutum na biye wa son zuciyarsa gurin aikata mummuman aiki, lokacin da na samu labarin abinda ya faru da ku hankalina ya ta shi, sai dai ba ni da yanda zanyi, bahaushe ya ce." Tun ran gini ran zane, ki yi hakuri ki kar'bi wannan jarabawar kuma idan kin haihu lafiya kada ki nemi wata hanya domin kashe abinda ki ka haifa, ki nemi gafarar Allah, in sha Allahu zai gafarta miki, abu na 'karshe da za ki yi shine; aure. domin shine cikar mutumcin duk wata 'ya mace! Ta share hawaye da cewa; Yanzu wa ki ke tunanin zai aure ni da abinda na haifa, wallahi ni na fi bukatar na mutu! domin ba zan iya da abin kunya ba." Rushewa ta yi da kuka tare da dafe kanta! Jamila ta kalleni ina goge mata hawaye ta ce" Anti Shahida ki 'kyaleta don Allah kullum haka take tayar mana da hankali, ai dama duk wanda ya sayi rariya ya san zata zubar da ruwa, lokacin da take kan sharafi babu irin nasihar da ban yi mata ba, amma wani sa'in sai su had'a kai da Talatu suyi ta zagina to yau ga ranar da nake gudu ta zo, kin yo cikin shege, ita kuma Talatu garin yawon malamai 'kai'kayi ya koma kan mashe'kiya." Cike da 'kunar zuciya take maganar muryarta na rawa, da alama itama daf take da ta rushe da kuka! Na ce"Jamila kada ki sake taso da abinda ya ri ga ya wuce, ina so gabad'ayamu, mu dauki wannan a matsayin 'kaddara wacce ta riga fata, sannan mu yi wa Hadiza adduar haihuwa lafiya, ita kuma Talatu Ubangiji Allah ya bata lafiya." Ta amsa da ''Amen anti Shahida in sha Allahu ba zan sake ba.'' Duk muna zaune jigum!-jigum! domin halin da Hadiza take ciki na ciwon mara mai tsanani! tana kwance sai rike ciki take! tana kuka Anti Murja ta shigo dakin, na kalleta da cewa" Anya kuwa ba za mu je asibiti ba watakila haihuwa za ta yi fa." Ta ce'' Ai Babanku ya hana ban san meye dalilinsa ba, amma a duk lokacin da ta shiga irin wannan halin akwai wata likita dake zuwa ta dubata to yanzu ma gidanta na nufa na duba ko ta dawo daga aiki. Na ce" Yawwa Don Allah ki je wallahi hankalina ya ta shi." Ba ta ce komai ba ta shiga d:aki domin d'auko mayafi. Na ce" Jamila kira wayar Babanmu ki fada masa halin da ake ciki. Ta ce" Fad'a zai yi wallahi, domin fa har yanzu bai sauko ba, da k'yar ma yake amsa gaisuwarta a cewarsa ta gama ci masa mutunci a duniya shiyasa ya 'kullace ta! Girgiza kai na yi da cewa; Ban san abinda yake damunsa ba wallahi. ita fa rayuwar duniyar nan hakuri ake da ko wane yanayi, kuma fad'in Annabi ne cewa; duk abinda ka yi shi za a yi maka, lokacin da yake kan ganiyarsa meye be yi ba? babu irin kukan da ba mu yi ba, a yanzu sakamako ya ke ga ni." Shiru ta yi na minti biyu kafin ta girgiza kai da cewa; Ai kullum cikin tsinewa Talatu ya ke, ita kanta Hadiza a cikin tsiniwarsa take, ya 'ki ya yafe mata, ni da Walida ne kawai muke mu'amular arziki da shi. Na bud'e baki kenan zan yi magana su anti Murja suka shigo. Da sauri likitan ta sanya safa a hannunta, muka fita daga dakin ta fara dubata domin itama ta yi tunanin haihuwar ce ganin yanda take murkususu! da kiran sunan Allah. Tabbas Haihuwa ce amma cikin ikon Allah babyn yana zaune daram ma'ana bai juya ba. Ta kira Anti Murja tana sheda mata halin da ake ciki cewa lallai a tafi asibiti akwai matsala don abin ya fi 'karfinta! Waya ta na dauko na ce Jamila ta kira Sule ta sheda masa cewa ya zo yanzu-yanzu da mota dama kuma shine ya kawo ni garin. Minti goma sha biyar a tsakani, sai ga shi ya zo, da kyar muka fita da Hadiza daga gidan, lokacin ta kai ma'kura gurin galabaita, kai tsaye babban asibiti muka nufa. Na ce Jamila ta kira Babanmu anti Murja ta kar'bi wayar ta yi masa bayanin halin da ake ciki, sai ya fara fad'a da cewa; da izinin wa suka fita shi ya fi so Hadizan ta mutu! ya huta da abin kunya! sai da ta fada masa cewa; ai ni ce na zo garin na riski abinda yake faruwa kuma ni ce nace aje asibitin, sannan ya saurara da fad'an ya kashe wayarsa. Babban likita ne ya dubata, kuma shi ya tabbatar mana da cewa; ba za ta iya haihuwa da kanta ba, ana bukatar ayi mata aiki da wuri! dukkaninmu mun shiga damuwa matsananciya! nan ma na ce a kira shi a fad'a masa ya zo ya sanya hannu. Dole ba don ransa ya so ba ya zo asibitin, ya kalleni da fadin" Shahida don dai kin shiga cikin al'amarin nan ne, amma wallahi na fi bukatar mutuwar Hadiza da rayuwarta, domin dai ta gama tozartani a duniya." Na ce" Baba don Allah ka daina wannan maganar, jahili kad'ai shi zai yi jayayya da abinda Allah ya hukunta, kaddara ta riga fata babu yanda za mu yi da ikon Allah, ka yi hakuri ka ya fe wa Hadiza kuma kayi mata adduar sauka lafiya." Ya sauke zazzafar ajiyar zuciya, ba tare da ya sake wata magana ba ya kar'bi takardar ya sanya hannu kamar yanda likitocin suka bu'kata, cikin gaggawa aka shirya Hadiza aka shiga da ita tiyata. Cikin ikon Allah a kayi aiki lafiya aka fito da baby girl k'atuwar gaske! kyakykyawa! jawur sumar kanta 'baka sunkuf! babyn ta fi kama da 'ya'yan k'warori ko larabawa, sam ba ta yi kama da Hadiza ba, na jima ina tasbihi ga Ubangiji ganin yarinyar cikin koshin lafiya an shiryata cikin kayan sanyi sai tsotsar hannunta take, wasu hawaye masu zafi suka ciko idona, lokaci guda yarinyar ta shiga raina ina jin dama ni na haife ta, rungumeta nayi a kirjina ina jijjigata a lokacin da take tsanyara kuka! ga uwar a kwance bata farfad'o ba. Babanmu kuwa tafiyarsa ya yi, tun bayan da ya sanya hannu, sai Jamila ce ta kira shi ta sheda masa abinda yake da akwai. hakan ma bai sanya ya dawo asibitin ba, ya kuma umarci anti Murja da cewa; lallai ta koma gida. Ni da Jamila muka zauna asibitin, da yake na kudi ne ba mu samu matsalar komai ba, kuma duk abinda suke bu'kata na ha'kkinsu na tura musu, shiyasa suke ba mu kulawa ta mussaman. hankalina bai kwanta ba sai da Hadiza ta farfad:o na kira sunanta ta amsa tare da kiran sunana, nan na tabbatar da cewa; ta dawo hayyacinta. Na ce" Kin samu baby girl ga ta nan kyakykyawa." na fad'a ina murmushi tare da nuna mata babyn dake kwance a wani gado tana bacci. Dauke kanta ta yi ba ta kalli gurin ba, sai wasu hawaye da na ga suna gangarowa ta gefen idonta. Na ce" Ka da ki sanya damuwa a ranki don Allah kin ga baki da koshin lafiya." A hankali ta juyo ta kalleni ta yamutse fuskarta da 'kyar ta ce." Gabad'aya na tsani duniyar nan wallahi. yanzu wa zan nuna a matsayin uban yarinyar nan? ba zan tantance iya adadin mazan da nayi mu'amula da su ba." Wani kuttun! bakin ciki ya tokare min a wuya. na ce" Dama illar kenan Hadiza. ba ki ji bahaushe yana fadin." Duk abinda namiji ya yi ado ne, ita fa 'ya mace rayuwarta ta'kaitacciya ce, kamar yanda ki ka fad'a! babu wanda zai kar'bi yarinyar nan da sunan shine ubanta ko da kuwa kammani sun nuna! kin ga sun bar ki da wahala. babban tashin hankali anan shine; yarinyar ta girma ta bukaci sanin ubanta anan damuwar take." Hanci ta sha'ka! wasu hawayen na sake zuba ta ce" Ki d'auke ta na bar miki don zatin Allah ki yi min wannan alfarmar." Kallonta na yi , tausayinta ya cika min zuciya na ce" Ba zan 'ki ba Hadiza na kar'ba kuma zan ri'ke ta tsakani da Allah kamar ni na haife ta, amma mu bari ta yi 'kwari, ina nufin sai bayan kin cire ta daga bakin nono, tunda kinga ni ban ta'ba haihuwa ba, ban san ya ake ba." Ta ce." To shikkenan haka za a yi." Shiru ta yi tana yamutse fuska! na ce" Ko wani abu yana damunki?" "Jiri da ciwon kai nake ji." Na ce"Sannu bari a kira likita ya duba ki." Tare muka shigo d'akin da likita lokacin babyn na wutsil-wutsil da kuka. na je na dau'kota. ya kalle ni da cewa" Yarinyar nan na bukatar abinci! saboda haka ko ya ya ne, mamanta ta bata nono. idan ya so sai a d'ora ta akan madarar da ta dace." Na ce."To shikkenan.'' Ya kama hanyar fita da cewa; nurse za ta shigo yanzu sai ta taimaka miki gurin shayar da babyn." Cikin dubara muka jingina babyn jikin Uwarta nurse din ta fito da nonon tasa mata a baki, cikin ikon Allah ta janyo ruwa ta dinga sha kamar babu gobe, ita kuma Hadizan sai hawaye take tana kawar da kanta. ita kanta nurse din sai da abin ya bata mamaki! ta gama aikinta ta fita. ni kuma na kwantar da babyn a gadonta. Na dawo na zauna da fadin." Hadiza ki daina wannan kukan dan Allah. Da 'kyar ta ce" Yanzu na tabbatar da uban yarinyar nan." Da sauri na ce" Waye shi? kuma a ina yake?" Girgiza kai ta yi ta ce" Wani k'wara ne! ba mu jima da had'uwa ba, kuma ban san a wace 'kasa yake ba, lokacin dai da muka had'u ya sheda min cewa; gwamnatin ce ta d'aukesu wani aiki. shine na tare a gidansa. kuma yake mu'amula da ni kamar matarsa ta aure, amma ya kashe min kud'i sosai, kuma fa duk lokacin da za mu yi wata mu'amula sai ya ba ni 'kwaya ya kuma sanya condom gudun samun wata matsala, dama ba a yi wa Allah wayo." Ta karasa maganar da fashewa da kuka! Da sauri na ce" Ki yi shiru don Allah ai kin san abinda yake da akwai, kada ki dawo da aiki baya" Hannu nasa na goge mata hawayen fuskarta Ta ce." Ina Babanmu ya zo asibitin?" Na ce" Eh ya zo ya duba ki har ya yi miki addua.'' Na fadi hakan ne domin ta samu kwanciyar hankali. Murmushi kawai ta yi tana kallona, yanda na fahimta kamar bata gamsu da maganata ba . Ta ce." Ki nema min gafara a gurinsa tare da Talatu da duk wanda na 'batawa a wannan duniyar." A sanyaye na ce" Mai ya kawo wannan maganar kuma?" Shiru ta yi ba ta ce komai ba. Na ce." In sha Allah za ki samu lafiya. A hankali ta amsa da "ameen Allah ya sa haka.'' Sai da na ga ta samu bacci tukkuna na fito daga d'akin da take, na samu Jamila tana bacci. na tasheta tare da fadin" Lokacin sallar la'asar ya yi. na shiga band'aki na d'auro alwala na fito. Tare mu ka ci abinci muna tattauna abinda ya shafe mu. lokacin na samu 'yar nutsuwa na samu sararin duba waya ta. nan na ga tarin messages d'insa. duk rabi na soyyaya ne tare da sake jaddada mini cewa; yana nan yana kewata amma na tsammaci dawowarsa cikin satin da za mu shiga, karshe ya bada sa'kon gaisuwarsa gurin iyaye da 'yan uwa. Nan nima nake sheda masa halin da ake ciki. ya tausaya sosai! ya ce kuma na yi 'kokarin ganin nayi duk abinda ya da ce kafin na bar garin. Godiya na yi tare da ba shi amsa wacce ta yi dai-dai da umarnin da ya yi min. na kuma yi 'kokarin tura masa kalaman soyayya irin wanda na saba a duk lokacin da baya gari. [2/3, 7:47 PM] Bintu: 126&127 Kwanan da mu ka yi babu bacci yasa na 'bingire kan dadduma bacci mai nauyi ya d'auke ni, tabbas Annabi ya yi gaskia da ya yi hani da baccin la'asar domin akwai firgici da razani a ciki, idan ba a yi sa'a ba ma mutum na iya tashi da ciwo mai tsanani! abinda ya faru kenan, domin mummunan mafarki nayi wanda ya sanya na farka a razane! na tashi zaune jikina duk ya jike da gumi! babu kowa a dakin sai ni kadai, da alama Jamila ta jima da fita. shiru nayi ina nazarin mafarkin wanda ya danganci Hadiza! gabana ya dinga dukan uku-uku! ina kiran sunan Allah a zuciyata, tabbas mafarkin d'anyan nama ba a bu ne mai kyau ba, domin da yawa ana dangata shi da mutuwa ko wani 'bacin rai mai tsanani! Mafarkin da na yi kenan, bayan wanda na ga Hadiza cikin da fararan kaya tana d'aga min hannu da murmushi a fuskata, ta ajiye min 'yarta a kan cinyata, kafin ma nayi wata magana na nema ta na rasa a gurin, sai 'yarta dake tsanyara ihu! Jikina ya mutu gabad'aya na gaza ta'buka komai wasu irin tunane-tunane nake marasa kan gado. Jamila ta shigo dakin da sauri tana fadin" Anti Shahida likita na magana na shigo ya kai sau uku kina bacci shine ban tasheki ba." Gabana na bugawa na ce" Amma dai lafiya ko?" hawaye ne suka zubo a fuskarta, ta ce" Jikin Hadiza ne ya rikice! tun d'azu take suma, yanzu dai naga likitoci uku sun shiga dakin. "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! wannan adduar na yi kafin na yun'kura na tashi saboda tsabar fargaba da razani 'kafafuna duk sunyi sanyi kamar an bubbuga min ta'barya haka nake jan k'afa muka fita daga dakin. Babu halin mu shiga d'akin da Hadizan take tunda likitoci suna ciki sai muka samu guri muka zauna tare da tsirawa dakin ido! Jamila dai hawaye kawai take sharewa! ni kuwa addua kawai nake a zuciyata akan kada Allah ya tabbatar min da mafarkina, wanda na san hauka kawai nake domin ba zan dakatar da abinda Ubangiji ya hukunta ba. Har akayi sallar magariba ba su fito, a daddafe muka gabatar da sallar muka zauna jigum-jigum! da jiran tsammani! 'Daya daga cikinsu ya fito. kallon fuskarsa kad'ai ya sanya gabana fad'uwa! bahaushe ya ce." Labarin zuciya a tambayi fuska." Tsaye na mike baki na rawa na ce" Likita ya jikin nata? wallahi lafiya lau na fita na barta a dakin tana bacci. Kallona ya yi da fadin." Ina mahaifinku yake?" Na ce" Ya zo ya tafi." na fadi hakan ne domin kada ya fahimci wani abu. Katsaham! ya ce." Allah ya yi mata rasuwa yanzu sakamakon jijjiga bayan jinin da ya b'alle, mun yi duk iyakar bakin k'o'karinmu abinda muke so bai samu ba, Hadiza kwananta ya 'kare." Hannu na d'ora aka da fadin"Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! na zube kasan gurin wasu hawaye masu mugun zafi suka shiga gararanba a farfajiyar fuskata! Jamila kuka take tana fadin." Shikkenan Hadiza ta mutu! shikkenan ta mutu ta bar maka duniyar Baba! ba ka yi mana adalci ba." Kamar zautacciya haka take sakin maganganu! nayi saurin toshe bakinta ina girgiza mata kai. Shiru tayi amma fa hawaye sai shatata suke. Sosai nayi ta nanata addua a fili da zucci har na samu k'warin gwiwa na d'auko waya ta, lambar babanmu na kira. yana d'agawa na mi'kawa Jamila wayar. hannu na rawa ta 'karba cikin kuka ta sheda masa abinda yake faruwa, ta kashe wayar ta mi'ko min. Na nemi lambar wayar Saliha nan ma Jamila ta kar'bi wayar ta sheda musu abinda yake faruwa. da karshe na kira maigidana shima na fad'a masa. Na kalleta sai kuka take tana girgiza kanta, na ce" Jamila ki kira dangin mamanku suma ki sheda musu, sannan ki dai na yi wa Hadiza kuka tayi shahada Allah yasa ta mu ta yi kyau." Ta ce."Anti Shahida wane irin Shahada kuma? ki dubi akan tafarkin da mutu, haihuwar shege fa, me zata fad'awa mahallicinta. Raina ya 'baci ainun! na ce" Wai ke yaushe za ki yi hankali ne Jamila? ko so ki ke ki tona masa asiri a cikin asibitin nan, ina ruwanki da tsakaninta da Ubangijinta? to mutu'kar kina so mu shirya kada ki sake tayar da magana irin wannan. mu dai fatanmu anan shine Allah ya kar'bi shahadarta ya kuma raya abinda ta bari.'' A sanyaye ta amsa da " Ameen." Tana ta jan majina kuka duk ta rasa yanda za ta yi. To kafin gari ya waye jama'a da yawa sun sami labarin mutuwar Hadiza, kowa dai da abinda yake fad'a akan lamarin. domin shi kansa Babanmu da yake jin haushinta sai da mutuwar ta doke shi! kuka sosai ya yi a gaban gawarta yana nema mata rahama, Jamila kuwa faduwa ta yi a gurin tana iskokai! wanda tunda muke da ita ba mu ta'ba sanin tana dasu ba. Haka aka yi jana'izar Hadiza Talatu na can gidan mahaukata sai dai a nema mata sauki daga Allah. amma kuma 'yan uwanta cika su ka yi a gidan a kayi duk abinda ya cancanta da su. Har yamma muna tare da Baba Asabe domin har da ita a cikin masu wanke Hadiza da shiryata zuwa gidanta na gaskiya. A nan nake sheda mata kyautar jaririyar da marigayiyar ta yi min Ta ce" Shahida kina ganin hakan ba zai janyo miki matsala ba kuwa?" Girgiza kaina na yi murya na rawa na ce" Babu wata matsala Baba, dama nema muke ni da mijina ni kuma yanzu ga shi mun samu, in sha Allahu za mu rike yarinyar kamar mu muka haife ta. Ta ce." Shikkenan Allah ya taya riko, kema Ubangiji ya baki naki rabon masu albarka. Na amsa da amin suma amin. To ganin yanda jama'a suke ta turareniyar zuwa gaisuwa ya sanya na sha jinin jikina, domin dai da yawa idan sun zo gaisuwar ba sa tafiya sai sun ce aba su baby su ga ni, ashe gari ya d'auka cewa; Jaririya tana nan kyakykyawa kamar 'yar larabawa, to wannan shine dalilin da yasa mutane basa tafiya sai sun gazgata abinda suke ji a gari. Hakan ya sanya ranar da a kayi adduar uku. na shirya tafiya gida domin bana jin dadin irin kallon da jama'ar gari sukewa jaririyar da bata san komai ba. Tsaf na kammala shiryawa, dama kuma tun safe nayi sallama da Baba Asabe domin da ita a ka gabatar da adduar uku kafin ta tafi. Muna zaune tare da Jamila a d'aki ina tsammanin zuwa Sule a lokacin, tunda nasa an kira shi a waya ya ce gashinan a kan hanya. na kalleta a nutse na ce"Wai Jamila ina saurayinki ne wanda a kayi muku baiko?" Shiru ta yi na minti biyu kafin ta ce." Bayan dawowar Hadiza da abin kunya, da kuma aika-aikan da Talatu ta dinga tabkawa ya sanya ya janye aurena, dama kuma can iyayensa basa so a cewarsa Babanmu bashi da kirki dan bariki ne, Shine ya ma'kale dole sai ya aureni, ganin haka yasa iyayen nasa suka ha'kura, amma sakamakon faruwar wannan al'amarin sai ya daina zuwa kona kiransa a waya baya d'auka, daga karshe ma wakilansa suka zo suka kar'bi kudin da suka kawo na zance." Sosai na tausaya mata domin yanda take maganar na fahimci cewa; ta ji ciwon abin. na ce." Kiyi hakuri in sha Allahu. Ubangiji zai baki wanda ya fi shi. Ta ce" Allah ya yarda." Rufe bakinta ke da wuya Walida ta shigo tana cewa" Anti Shahida ga wata mata tazo gaisuwa anti Murja ta ce na fada muku. Tare muka fita tsakar gidan, matar babbar macace daka ga ni kuma ta ga jiya da yau! ha'koran makka sama da 'kasa! ga wani ubansu less da yake jikinta da wani dan'kareran mayafi, sai k'amshi turare! take. Cikin rashin fahimta muka gaisa ta ce" Na san baki gane ni ba ko?" Na ce"Eh gaskiya kuwa.". Ta ce" Sunana Hajiya Zaliha 'kawar Hajiya Fatima tsohuwar matar 'Dangaske ina nufin mijinki, tare muka zauna da ita a saudia." Na ce" Ayyo! Allah sarki ya a kayi ki ka san gidanmu." Murmushi ta yi da cewa." 'Kawata ce ta yi min kwatance sai na ga ashe ma muna kusa da juna, shine na ce bari na shigo na yi miki gaisuwa kafin ki tafi, duk da yake nima cikin satin nan nake koma saudiya. Jin haka yasa na gazgata abinda nake zargi, wato a gurinta Hajiya Fatima ta samu labarin komai, wanda ta samu damar cin zarafin mahaifinta. Shiru na yi mata ban ce komai ba, amma na lura fakaice take yi min wani irin kallo. Wanda ya sanya gabad'aya na tsargu! 'bata fuskata na yi nayi bala'in shan kunu! don gabadaya matar bata kwanta min a rai ba. Sai ta yi 'yar dariya da cewa; Allah sarki Hadiza Allah ya gafarta mata ya raya abinda ta bari." Na amsa da ameen'' kamar na gaura mata mari saboda takaicin abinda take. Ta mik'e tare da d'aukar jakarta da cewa; to Allah ya kara hakuri." Anti Murja ta ce" Ameen ya rabbi Allah ya bada lada." Tana 'kokarin sanya takalminta take amsawa. Tana fita na ja tsaki da fadin." Anti na lura da yawa mutane gulma ce take kawo su wallahi. wannan shine dalilin da ya sanya yau-yau din nan zan bar garin nan wallahi". Ta ce" To ya za a yi da sha'anin mutane! kin san yanzu jama'a sun fi zuzuta! sharri! a kan alheri Allah dai ya rufa asiri." Na amsa da "Amen dai Allah ya sa mu dace." **** Cikin gajiya na fito daga cikin motar, lokacin ana ta kiran sallar magariba. Walida ta fito goye da babyn a bayanta wacce muka mayar mata da sunan mamanta sai muka yanke shawarar kiranta da Nanah! lokacin da na shirya tafiya ne na nemi alfarma gurin Babanmu ya ba ni Walida. ba don komai ba sai dan ta d'ebe min kewa ta kuma taimaka mini da rainon yarinyar. haka nan ba don ransa ya so ba ya amince ne kawai saboda baya son 'bacin rai na, amma maganar kyautar da Hadiza ta yi mini ta tafasa bai ce ba balle ki sauke, kawai ya ja bakinsa ya yi shiru, yanda na fahimta ma kamar hakan ya yi masa dad'i yarinyar tayi nesa da shi. Da sallama muka shiga falon, Shukura ce kawai a zaune da waya a hannunta Wani irin kallo take mana na san tana mamakin ganin Walida ne da kuma yarinyar dake goye a bayanta tana tsala ihu! Na daure na yi mata magana da cewa" Shukura ya gida? ina Hajiya?" Da k'yar ta bani amsa da cewa" Ta shiga sallah. Ban sake wata magana ba na fara hawa saman domin babu abinda na fi bu'kata a yanzu kamar na watsawa jikina ruwa. Walida ta biyo bayana tana jijjiga yarinyar dake wani irin kuka da alama dai akwai abinda ke damunta . Hajiya ta fito d'aga daki tana fadin" Kukan jarirai na ke ji a cikin gidan nan". Shukara ta bata amsa da cewa" Eh mana matar gidan ce ta dawo ina jin ta je gidan marayu ta dauk'o mana jangwam! Ta zauna kan kujera da fadin" A'a to ba a gidan nan ba, domin mafi akasari duk yaran da suke gidan marayu shegu ne an rasa yanda za a yi da su aka kai su can aka aje." Shukura dai ta'be bakinta ta yi ta cigaba da danna wayarta ita dai babban burinta mamanta ta dawo gidan. Ina 'ko'karin shiga wanka kawai na ga mace ta shigo dakin. fuskarta kawai na kalla na gane cewa; ba alheri ne ya shigo da ita ba. Na ce" Hajiya sannu da gida, na dawo ai Shukura ta ce mini kina sallah. Ta shiga bin Walida da kallo wacce take kokarin cirewa babyn pampas. "Wannan jaririyar fa?" ta fada idonta a tsaye a kaina. Na ce." 'Yar gidan Hadiza ce, na san kuna da labarin mutuwarta ko?" Ta ce" A'a mu ba mu da labari. to yanzu da ki ka dau'ko ta kina da nonon da za ki bata ne?" Na ce" Hajiya wannan ai duk mai sauki ne akwai madara da likita ya dora ta akai. Wani irin kallo ta yi mini kafin ta ce." Kin d'auko nauyi kin kawo mana cikin gida ita kuma wannan fa?" ta fad'a tana nuna Walida dake zaune. Na danne 'bacin raina na ce" 'Kanwata ce ita ce 'karama a cikinmu." Tsaki! mai tsayi ta ja kafin ta ce" Allah ya kyauta! ai na d'auka gidan marayu ki ka je ki ka d'auko mana jaraba! domin dai duk shege ne a gidan." Gabana ya fad'i da jin abinda ta ce. ina jin tsoron ta san asalin yarinyar ban san wane irin tashin hankali ne zai faru ba. Na yi namijin 'kokarin fadin." A'a Hajiya ba duka suke shegu ba, don Allah ka da kiyi wa al'amarin mummunar fahimta, domin wasu kaddara ce take kai su gidan, kuma shegen da ki ke magana a kai ai yana da uba, domin dai mace ita kadai bata iya haihuwa, kuma dukkansu Allah ya kaddara hallitarsu ta wannan hanyar. Uffan ba ta ce mini ba, sai mummunan tsaki da ta ja min ta kama hanya ta fita. Ajiyar zuciya na sauke tare da shiga band'akin da tunanin abinda zai je ya dawo. A gurguje na yi wankan na fito, dalilin kukan da yarinyar take tsalawa, dama kwana biyu abinda ke damunta kenan koke-koke! rashin kwanciyar hankali ya sa ba mu kaita asibiti an dubata ba. Walida na tsaye da ita a kafadarta tana jijjigata ta ce." Anti anya ba wani abun ne yake damun yarinyar nan ba, ina kokarin sanya rigata na ce." Na fi tunanin cikinta ne ya kumbura tunda kinga tunda aka haifeta ba ta yi kashi ba, tun bayan wanda suke a ranar da aka haife su'' Cike da alhini ta ce."To anti yanzu ya za a yi?" Hannu nasa na kar'be ta da cewa; Kada ki damu in sha Allah likita zai zo har gida ya duba ta, ke dai je ki yi wanka ki d'auro alwala ki fito. Ta amsa da ''To" ta ta shi ta nufi band'akin! Iskar bakina na dinga hura mata a kunne har Allah ya sa tayi shiru jikinta ya saki alamun baccin ya dau'keta, a hankali na kwantar da ita. na hau kan dadduma na gabatar da sallah. Sai da ta idar da sallah tukkuna na kalleta da fadin."Kina jin yunwa ko Walida?" Murmushi ta yi da cewa" Ba sosai ba, amma Anti ina da tambaya idan babu matsala." Ido na tsira mata ina sauraranta. Ta ce" Da alama ba kya jin dadin zama da mutanan gidan nan, duba da irin kallon banza da su kai mana, maganganun da matar nan ta yi, sun tsaya min a rai." Murmushi na yi na ce" Walida al'amarin sai dai addua kawai, amma na ajiye abinda yake faruwa a matsayin ibada, kin san shi aure hakuri ya fi rinjaye, ke ma ina so ki kawar da kanki a kan dukkanin abinda za ki ga yana faruwa a gidan nan." A sanyaye ta ce" Shikkenan Anti Allah ya ba ki hakurin da juria." na amsa da "ameen" kafin mu sauka kasan domin nu na mata masaukinta Akwatin kayanta na can a jiye a bakin kofa! na ce." Ki dauko kayan ki biyo ni." Dakin dake kusa da Shukura na nufa. da mukkuli a jikin kofar ina murzawa ya bude, muka shiga tare, komai a akwai a dakin, sai dai ya yi datti! yana bukatar gyara, na ce'' Ki gyara abinda ya sawwaka idan ya so da safe sai ki 'karasa. amma ki fito min da kayan Nanah dake cikin akwatinki." Ta ce"To shikkenan Anti." fita na yi daga d'akin cike da tunani a cikin raina. To a daran na tura masa text na bayanin duk abinda yake faruwa, na ba shi tabbacin cewa mun dawo gida amma yarinyar tana bukatar ganin likita. Washe gari da sassafe sai ga likita mace ta zo. na sauk'a kasa da yarinyar a hannuna na shiryata tsaf! muka gaisa da juna, ta kar'be ta na dubata, nan na yi mata duk bayanin da ya dace. Ta ce." Watakila madarar da ake bata ce bata kar'be ta ba, amma za a sauya mata wata in sha Allahu. sannan akwai magunguna da za a dinga bata za su taimaka mata." Na ce" Na gode sosai 'yar uwa. yanzu za ku je da Sule sai ki hada masa duk abinda ya dace." Ta ce"To shikkenan hakan ya yi Allah ya bata lafiya." Cike da kulawa na amsa da "Amen." To cikin ikon Allah yarinyar ta samu lafiya sakamakon madarar da aka sauya mata da kuma magungunan da nake bata a kan ka'ida, ta dai na kuka yini take tana bacci, sai dare ya yi ta hana ni yin nawa, k'arshe k'asa na sauko na tare a masaukin Walida muna renon tare. Wani lokacin kuma Baba Marka ta kan taimaka mana domin idan ta kammala ayyukanta, yini yarinyar take a bayanta, a lokacin muke samun dama rama bashin baccin da muka tara. Hajiya kuwa kallonmu kawai take duk d'auki ba dad'in dake faruwa ci kanku ba ta ce ba. Cikin wannan halin Hajiya Fatima ta dira a gidan, tun bayan abubuwan da suka faru ba ta sake zuwa gidan ba sai wannan lokacin. sama-sama muka gaisa, sai dai gani na, ina hidima da jaririya ya sanya ta dinga yi min wani irin kallo wanda sai da na sha jinin jikina, kuma na tabbatar da cewa; sai wani abu ya faru na tashin hankali. [2/4, 8:41 PM] Bintu: 128&129 Aikuwa dai ina fitowa daga kicin na riske su suna mayar da yanda akayi gani na ya sanya Hajiya cewa" Shahida ashe wannan yarinyar ta hannunki shegiya ce shine ki ka d'auko najasa ki ka kawo mana gida?" Na ce" Lallai duk wanda ya fad'a miki wannan magana ya cika ma'karyaci." Na fad'i hakan ne saboda Fatima domin ina da tabbacin ita ta zo da maganar, tunda ta tura k'awarta ne domin ta d'auko mata rahoto! Kallona ta yi da cewa'' Ke kada ki mayar da mutane shashashai mana, ko kin d'auka ba mu da labarin abinda ke faruwa? idan Hajiya ba ta san komai ba, to ni a tafin hannuna ki ke?'' Na ce." Oh! shiyasa ki ka tura 'kawarki mai suffar karuwai." Kallona ta yi kafin ta yi murmushi da cewa" Hajiya Zaliha dai ba ta ta'ba ajiye d'an shege ba ballanatana ki goranta mata, tsiya da fasadi ya tattara a zuriarku masu mugun abun fad'a." Karaf a kunnan Walida Fatima ta kai karshen maganarta, dama can Walida ba kanwar lasa ba ce, jin irin cin mutuncin da Fatima ke yi ya sanya ta dakatar da ita ta hanyar fad'in" Ga ki nan karuwa! mai bilitin da suffar 'yan wuta!" Shukura ta zabura! ta mike tsaye tana d'urawa Walida ashar da fadin"Lallai yau sai ta bar gidan." Na ce" Walida kada ki sake wata magana ki k'yalesu koma meye dai ba zan mayar da yarinya ba tunda gidan mijina ne da kuma amincewarsa komai ya ke faruwa." Hajiya ta ce" Aikuwa ni zan bar miki gidan. domin kuwa ba zan zauna da najasa a gida d'aya ba." Shiru na yi mata ban ce uffan ba, na ja hannun Walida muka shiga daki. Na ce" Walida wallahi akan wannan yarinyar zan iya barin gidan nan, bari maigidan ya dawo na ga ji da wannan masifar." Cike da alhini ta ce" Anti gaskiya mutanan nan sun matsanta miki da yawa, ke da gidanki sun zo suna takura miki mussaman waccer tsohuwar wallahi na tsaneta. Na ce" Walida ki bari kawai! ni kadai na san irin takaicin da nake k:unsa a gidan nan, amma Allah zai yi min maganinsu.'' Ta ce" Shiyasa fa wasu basa son auran masu kud'i saboda gudun matsala irin wannan, ga dai jin dadin amma babu kwanciyar hankali." "Ni ba ni da matsala da mijina domin yana sona mutu'ka, matsalar kakarsa ne da tsohuwar matarsa sune suka addabi rayuwata.' Ta ce" Anti ki yi hakuri amma ki tsananta da addua in sha Allahu. komai zan wuce." To a can falo kuwa Hajiya ta sa a kira mata maigidan a waya. ta rushe da kuka da cewa" Babu shakka Alhaji Habu ka kalalace, yanzu a ce da goyon bayanka matarka ta d'auko najasa ta kawo mana gida, to wallahi zan tattara kayana na bar maka gidanka muddin ba za ka d'auki mataki ba. Sai ya kasa gane inda maganarta ta dosa ya ce." Hajiya wace irin najasa kuma? don Allah ki yi hakuri kina sasautawa yarinyar nan, abinda ke faruwa a tsakaninku baya yi min dadi." Ta ce" Dama ai da gadara take fad'in gidanta ne kuma miji na ta ne, sai yanda ta yi, to ai babu lefi tunda kai ka bada goyon baya kuma baka hango kuskure hakan ba, zan tattara kaya na bar maka gidanka tunda dai haka ku ke so. Ajiyar zuciya ya sauke ya ce." Ki yi hakuri in sha Allahi gobe i war haka ina gida sai mu tattauna maganar." Ta ce." To shikkenan Allah ya kawo ka lafiya." Wayarsa ya kashe yana girgiza kansa, ya rasa abinda yake damun Hajiya, dama bahaushe ya ce." Idan ka shekara ba ka ga mutum ba, to duk lokacin da ku ka had'u ka tambaye shi halinsa, a lokacin zamansa da Zinaru har tausaya Hajiyan yake, amma da yake 'yar adam ce ta samu yarinyar kirki tana wahalar da ita, maganar dai guda daya ce ta rashin haihuwa har yanzu sun kasa gane cewa; Ubangiji shike bayarwa kuma shike hanawa. Hajiya Fatima kuwa jin cewar zai dawo gobe ya sanya tattara komatsanta da sassafe ta nufi jibia, domin tana jin tsoron ya dawo ya risketa a gidan, ya kuma samu labarin cewa da sa hannunta a cikin faruwar al'amarin, tabbas ta san cin mutunci ne zai biyo baya, shiyasa ta ware! To dama tun dare ya yi mini text cewa zai dawo gobe, dalilin da ya sanya kenan na yi 'yan shirye-shirye irin wanda ba a rasa ba, na san dai yana sauka da abin zai fara, shiyasa na shirya jikina. Sai dai kuma matsalar da a ka samu. baby ta wayi gari da rikici! kuka take na ba gaira ba dalili, tunda babu yunwa a tattare da ita, Walida ta yi ta ga ji ta ba ni ita, na kar'be ta ina ta aikin jijjigata, lokacin kuma Baba Marka tana kicin tana aiki ballanatana ta taimaka mana, cikin wannan halin ya dawo gidan. Hankalina ya rabu gida biyu, duk na rasa yanda zanyi domin dai kukan da yarinyar take ya fara ba ni tsoro sai nake zargin ko dai ba ta da lafiya! tausayinta ya cika mini zuciya. Hakan ya janyo na kasa ba shi kulawar da yake bukata, gashi ya dawo da matsananciyar bu'kata! don ko abinci bai ci ba, yake ta 'ko'karin kwanciya da ni, ni kuma na ce lallai sai ya huta gajiya tukkuna ya barwa dare koma meye sai ya faru. Hakan sai ya janyo min b'acin rai mai tsanani! domin dai fad'a ya rufe ni da shi wanda nima na gaza ha'kuri! na mayar masa da martani ina kuka dama kuma a kusa nake sakamakon irin tujarar da Hajiya take min a gidan ta ishe ni ta gallabeni kuma ya kasa d'aukar mataki, kullum maganar dai guda daya ce na yi ha'kuri, gaskiya na ga ji ba zan iya jurewa ba." Abinda na fad'a masa kenan ina kuka! irin wanda na jima ban yi irinsa ba, domin na riga na tara abubuwa da yawa kukan ne kawai zai sanya na samu sasauci! Ganin na 'ki na daina kukan ne ya sanya ya ce na tashi na fitar masa a da'ki! yanda ya yi maganar zai tabbatar maka da cewa; a kufule ya ke, ban nemi sulhu ba kawai na ta shi na fita. idona jajawur! Hajiya da Shukara suna zaune a falo na sauko, gani na cikin rashin nutsuwa ya sanya suka bi ni da kallo. har na shige masaukin Walida ba su janye idonsu daka kaina ba, tabbas na san hakan ba 'karamin dadi ya yi musu ba. Ko da na shiga d'akin kasa daurewa na yi na kwanta kawai hawaye! na ambaliya a fuskata! Walida goye da baby a bayanta ta tsuguna gabana murya na rawa ta ce."Anti menene? wani abu su ka yi miki ko?" Shiru kawai na yi mata domin duk bayanin da zan yi mata ba za ta fahimta ba. Tasa hannunta tana goge min hawaye! yanda lura itama saura kiris ta fashe da kukan, domin kwalla ta kwarmin idanuwanta. Ganin haka ya sanya na daure zuciyata na tashi zaune na goge hawayen da suka kasa daina zuba na ce" Kada ki yi kuka Walida, na daina nima ka da ki zubar da hawayenki." Muryarta na rawa ta ce."Anti mutane da yawa suna sha'awarki cewa kina auran attajiri! ashe ke kad'ai ki ka san matsalar dake damunki, wallahi ba na jin dadin ganinki cikin damuwa Anti zan ta ya ki da addua in sha Allahu. Na ce" Na gode sosai Walida amma ni babban abinda yake damuna cin zarafin mahaifina da akeyi wallahi idan ni kad'ai abin ya shafa zan iya jurewa, amma duk lokacin da a ka fadi mummunar kalma akan Babanmu hankalina yana ta shi." Ta ce" Anti duk wannan masifa da 'kask'ancin da muke ciki shine sila. domin shi ya zubar mana da mutunci a duniya a can baya yana ganin duk abinda yake aikatawa daidai ne, wannan shine fa dalilin da ya sanya aka fasa auran Jamila, ga shi har yanzu da ni da ita ba mu da tsayyayen wanda zai aure mu. "Komai yana da lokaci Walida kada hakan ya dame ki, in sha Allahu za ku yi aure idan lokacin ya yi, addua za ku tsananta." Na fad'a cikin kwantar mata da hankali. Ta ce" Kin ga dai yarinyar nan ta yi bacci. wallahi Anti wani sa'in kawai rigima ce, amma na ga ke sai ki dinga ganin ko ba ta da lafiya ne. Na ce" Walida kukan yaro ai babu dadi. wallahi duk lokacin da yarinyar nan take kuka sai na tuna Mamanta, hakan sai ya tayar min da hankalina na ga kamar na gaza ta wani fannin shiyasa ki ka ga ina shiga damuwa " Za ta yi magana kenan Shukura ta shigo babu sallama. Babu walwala a fuskata na kalleta. Ta ce" Ki zo Daddy yana magana." Daga haka ta kama hanya ta fita. Ta shi nayi na bi bayanta fuskata a murtuke! bana tsammanin zan d'auki wani raini. Ya zaune kan kujera cikin farar jallabiya mai karamin hannu. kamar ko da yaushe idonsa sakaye da farin gilashi. amma kallo daya nayi masa ban sake marmarin sake kallonsa ba, saboda yanda fuskarsa take a had'e! da alama har yanzu da sauran 'bacin ran d'azu. Ba tare da na saki fuskata ba na zauna kan kujera amma ban ce komai ba, sai dai na tsirawa bakinsa ido domin na fi fahimtar maganganunsa. "Duk lokacin da a ka kawo min 'korafi a kanki na kan 'karyata saboda ina miki kallon mutuniyar kirki, sai ga shi yau nima kin gwada min halinki." Ya ja numfashi kafin ya cigaba da cewa; Ni na baki umarnin d'auko yarinyar nan ki zo da ita domin ki samu sasaauci na daga irin jarrabawar da Allah ya yi miki. watakila ri'konta Allah yasa kema ki samu na ki, sai ga shi tun ba'a je ko'ina ba abubuwa marasa dad'i suna faruwa, wanda har da ni suka shafa, saboda haka ina ganin ki mayar musu da 'yarsu, idan kuma ba haka ba, zan d'auki wacce za ta yi rainonta har ta yi wayo idan ya so sai ki 'karba." Kallonsa na yi na ce" Ba mu yi haka da uwarta ba, yarinyar nan amana ce a gurina, kuma na kar'ba tsakanina da Allah ba na duba ta hanyar da aka sameta, kuma kafin hakan ta faru sai da na nemi shawararka ka amince, amma me yasa yanzu za ka sanja magana. to gaskiya in dai ka ce dole na mayar da ita za mu tafi tare domin nima na ga ji da wannan zaman wahalar, idan ya so sai ka auro mai haihuwa. Idonsa ya tsira mini da zallar 'bacin rai a cikinsu! Ni kuwa ban ji nauyi da shakkar furta masa maganar ba, domin na ranste da girman Allah ba zan mayar da yarinyar ba, mutukar kuwa ya ce sai na mayar da ita to zan bar masa gidansa Karaf! sai ta ce."To Alhaji Habu tunda matar gidan ta yanke hukunci ai shikkenan. sai mu ta shi mu yi gaba domin dai nima nayi rantsuwa da Allah ba zan zauna da najasa a gida d'aya ba.' Raina ya dungunzuma! na tsani na ji tana danganta yarinyar nan da najasa ina jin haushi mutuk'a! A fusace! na ce" A'a Hajiya ki daina kira na da matar gida, nan gaba kad'an za ki kawo masa mace mai haihuwa, kamar yanda ki ka ci alwashin raba tsakanina da shi, to bukatarki za ta biya amma fa ki sani za ki je ki tarar da sakamako a lahira! Fashewa ta yi da kuka! ni kuma ban yi aune ba kawai na ji saukar lafiyyan mari a kumatuna, abinda bai ta'ba faruwa ba tsakanina da shi! Ido na tsira masa wanda suka bushe! da zallan b'acin rai da takaici! na nuna ta da yatsa da fadin" Ka ga wannan tsohuwar ba za ta ta'ba barin ka ka zauna da mace ba. ni kuma nayi imani cewa; a zamantakewa ta daku ban zalince ku ba, amma cikinku duk wanda ya zalince ni dai-dai da second d'aya na bar shi da Allah. Gabadaya na gama kashe musu jiki. Ban jira komai ba na hau sama na harhad'a kayana cikin akwati, ikon Allah har lokacin ban ji alamun kuka ba, zuciyata ta gama bushewa! Na sauko cikin shirin barin gidan hannuna janye da akwatin kayana, suna zaune a falon har yanzu suna mayar da magana, ko kallonsu ban yi ba, na shiga na kira Walida muka fito a tare. Zuwa ya yi ya 'kwace akwatin dake hannuna, be ce min komai ba sai dai na hango tsantsar damuwa cikin k'wayoyin idonsa! jijiyar kansa duk ta ta shi. Ido ya tsira mini kawai yana kallo. na fashe! da kuka da k'arfi na ce" Yau babu wanda ya isa ya hana ni barin gidan nan, na gaji da wannan bala'i." Na kai hannu ina jan akwatin hannunsa yana ja ina ja!! su kuma duk sunyi cirko-cirko! Hajiya tayi kalar tausayi kamar mutuniyar kirki! ita kuwa Walida kukan take ta ya ni. yayin da Shukura take ji kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha saboda farin ciki. Ganin ya ki ba ni akwatin yasa nayi gaba da cewa" Walida shige mu ta fi ko a kafa za mu kai kan mu gida." Bai ji kunyar kowa ba ya rungumeni tare da yi mini wani irin ri'ko! wanda na rasa yanda zanyi na k'waci kaina, dole haka na ha'kura na kwanta a jikinsa, a lokaci wasu azababbun hawaye masu tsananin zafi suka fara gararanba! a farfajiyar fuskata. [2/7, 1:31 PM] Bintu: 130 'Kokarin zarmewa yake domin gabad'aya hannuwansa sun kasa tsayawa guri guda, sai yawo suke a sannan jikina, jin haka ya sanya da sauri na cire jikina na matsa gefe ina bin falon da kallo. babu kowa sai ni da shi, ina tsammanin ganin abinda yake faruwa ne ya sanya suka gudu. lallai an tafka abin kunya. Kallonsa na yi yana tsaye kamar wanda aka dasa a gurin, ya yi mini 'kuri da idanuwansa da su ka k'ank'ace! babu abinda ke damunsa sai fitina, domin duk lokacin da ya shiga irin wannan yanayin ina fahimta, kuma idan na shiga hannunsa sai abinda Allah ya yi. Hannu nasa zan d'auki akwatin ya janye. ya matsar da ita gefe tare da kusantata, yana ta wani lumshe idonsa, wasu lokutan idan yana wasu abubuwan har mamaki yake bani, ni na tabbatar da cewa; yaro d'an shekara ashirin ba zai nu na masa iya soyayyah ba. 'Kugu na ya kamo ya sake matsani a jikinsa da fad'in." Kina so na rasa rayuwata ko ?" Kuka na fashe! da shi tare da sake yunk'urin ture shi! ya ri'ke gam! yana ta cusa fuskarsa a jikina. Na ce" Na ga ji wallahi. don Allah ka yi aure ko kuma ka sake ni, don gaskiya ba zan iya ba, Hajiya ta takurawa rayuwata, kuma ka san hakan, amma ka kasa daukar mataki! har sai da aka 'kure ha'kuri na, mutukar cin zarafi zai wuce kaina ya je kan iyayana ba zan lamunta ba." Fuskata ya rik'e da hannuwansa. sai da ya daidaita yanayinsa tukkuna ya ce." Ba zan sake ki ba, kuma ba zan yi aure ba. wannan maganar na sha nanata miki! saboda haka kada ki sake min irin wannan maganar. Yanda yake maganar babu wasa yasa na tsira masa ido da cewa" Ni kuma ba zan iya mayar da wannan yarinya ba, haihuwa kuma Allah shi yake bayarwa ba wani mahaluki ba. Ya kai minti biyu yana kallona kafin ya ce." Za ki koma daya d'aga cikin sashen dake cikin gidan nan, wanda dama tun farko hakan na so, ki ka ce ke kin fi bukatar zamanki anan, abinda ya sa na yanke wannan hukuncin saboda a samu maslaha a tsakaninki da Hajiya, itama ina so na cika mata rantsuwarta, wannan yarinyar kuma na 'karba bisa amana, Allah yasa sanadin hakan mu samu namu rabon." Ajiyar zuciya na sauke ina jin sasauci a cikin raina. lallai hakan shine mafita a gare mu bakid'aya. Na ce" Shikkenan hakan ya yi Allah ya ta ya mu ri'ko." A kasalance ya amsa da "Ameen" ya ja hannuna muka hau saman. abinda ya faru a lokacin yana da wuya da tsayawa a rai! wata irin zazzafar soyayya mai tsayawa a rai ce ta gudana a tsakaninmu. domin ban ta'ba sanin haka ya mutu! a kan k'aunata ba sai a ranar! ya dinga zubar da hawaye wanda na rasa ko na menene! ko da ya ke ni kaina na san na gwane gurin iya sarrafashi a shimfida, shiyasa yake rasa control d'in kansa, ya haukace! da sambatu! da shiririta, abin ya yi ta ba ni dariya da tausayi, hakika kamar yanda ya sha fada min cewa; ko ya yi wani auran ba zai iya adalci ba, na yarda saboda kwata-kwata baya gajiya da ni, kullum kira na yake da sabuwar amaryarsa. *** Hankalina ya kwanta sosai na koma b'angarena na mussaman, wanda aka sake shirya shi da ababen jin dadi da more rayuwa, domin har ya fi wancan sashin da na bari kyau da tsaruwa, ni da Walida muka sake muna rayuwa cikin kwanciyar hankali. ga Baby Nanah dake samun kulawa, ta yi gwab'i tubarkalah! yarinya kyakykyawa suma sunkuf a kanta ba'ka mai kyau da 'kyalli, shi kansa Maigidan baya nuna k'yama a kan yarinyar, duk lokacin da yake gidan ya kan sanya na d'auko masa ita ya yi mata wasa. tare da yi mata addua irin ta iyaye. Wannan abu da ya faru ya tsayawa Hajiya a rai! mutu'ka! sai da suka tabbatar da cewa; baya gari ya yi tafiya, sannan suka tattara kayansu suka tafi jibia. Ni dai na je da safe domin gaisheta kamar ko yaushe tun bayan bari na sashen, sai na samu Baba Marka ita kad'ai a falo tana goge-goge, muka gaisa cikin mutunci da karamci. na tambayeta ina Hajiya. nan take sheda mini cewa; ai sunyi tafiya. ban kawo komai a raina ba, nayi mata sallama na ta fi. Sai bayan ya dawo da kwana biyu sannan ya ya nufi jibia domin jin abinda ke faruwa, ni dai ko da wasa ban yi gangancin ce masa komai ba, ko da ya tambayeni sai na ce'' Wallahi nima ban sani ba, na san dai watarana na je gaisheta Baba Marka take sheda min cewa sunyi tafiya. shiru ya yi be ce komai ba, amma yanayinsa gabad'aya ya nuna 'bacin rai, wanda ni hakan bai mini dad'i ba, dalili na riga na san da cewa; ba shi da 'koshin lafiya 'bacin rai na iya tayar masa da ciwonsa, shiyasa na dinga lallabashi, tare da kokarin yi masa duk abinda na san zai faranta masa ransa. Ko da ya sauka a garin bai je da sassauci ba, domin dai yana so a yau din a yi ta ta k'are, ya lura idan bai yi wa tufkar hanci ba Hajiya na iya dagula masa lissafi, ta dauki karan tsana ta dorawa a kan yarinya da ba ita ta hallici kanta da lalura ba, ba zai taba manta irin wahala da gwagwarmar da mahaifiyarsa ta sha a hannun Hajiya ba, to yana ganin tarihi ne zai maimaita kansa akan matarsa wanda yake ganin shi ba zai iya jurewa ba, domin kuwa shi kadai ya san irin wuyar da ya sha kafin ya sameta. Wannan karon ma a gidansa a ka zauna. Baba Audu da Auta cikinsu dai babu wanda ya yi wata magana, Hajiya ce take ta sababi kan cewa; lallai ya mayar da Fatima domin samun zuria, idan kuma yana ganin ba zai mayar da ita ba, to dole fa ya yi aure muddin yana bukatar ta cigaba da zaman gidansa. Sai da ya gama sauratanta tsaf! sannan ya ce." Wai shin Hajiya ba sai da lafiya ake aure ba?" Kallonsa su ka yi da mamakin furucinsa. Sai ya cigaba da cewa" Na farko dai ni tuntuni na riga nayi rauni, matar da nake zaune da ita a yanzu hakuri kawai take da ni, domin sai nayi wata biyu zuwa uku ban bata hakkinta ba, dalili ba ni da wadataciyar lafiya, bayan haka kuma bana zama a gari. wannan shine dalilin da ya hana samun cikin da ki ke bukata, kuma ita Fatiman da ko da yaushe ki ke magana a kanta sau nawa tana zubar mini da ciki? watakila wannan adadin da ta zubar shine rabona a duniya." Fatima ta kalleshi tana jin wani kuttun takaici a ranta, ta san duk wannan maganar da yake fadi karya ne, kawai ya yi hakan ne domin ya kare kansa, ta san halinsa ba tun yau ba, yana da k'arfin sha'awa da kuma kuzari, kuma shekarunsa basu kai har ya tashi daga aiki ba, kawai bashi da ra'ayin mayar da ita kamar yanda ya sha fad'a, ita kanta ta zauna tayi karatun ta nutsu ta lura cewa; ko da Allah ya kaddara ya mayar da ita din wahala za ta sha, domin ta lura wannan kurmar yarinyar ta gama dashi, baya kallon ko wace mace da mutunci kamarta. Ta ce" Idan duk jikina kunne ne wallahi ba zan yarda ba, kawai ka fadi hakan ne domin ka kare kanka, ai shikkenan ni dama tuntuni na ha'kura! har na fara duba wanda ya cancanta a cikin masu k'auna! saboda haka mutukar a kaina a kayi wannan zaman to na janye." Shukura ta rushe da kuka da cewa; Mommy ya haka kuma? don Allah kada ki janye ki dawo auran Daddy domin ni ke ce uwata babu wata banza da girmama." Dama tana zaune a kusa da shi, aikuwa ba ta yi aune ba ta ji saukar mari a fuskarta! a fusace! ya ce." Nima daga yau na bar zama dake ki bi uwar taki idan yaso sai ta sauya miki uba." Ta 'Kara rurucewa da kuka tana wani irin abu.itama Fatima ido cike da 'kwalla ta ce" Wace irin magana ce wannan kuma? Hajiya kuna jin abinda yake fadi ko? wai na sauya mata uba bayan shi ya haife ta." Cikin reshin kuka ta kai karshen maganar. Baba Audu ya ce." Alhaji Habu kasan irin maganar da zaka dinga furtawa wannan maganar ba ta cancanta ba. Shiru ya yi bai ce komai ba amma gabadaya yanayinsa ya sauya da bacin rai mai tsanani! Ita kuwa Hajiya tunaninta gabadaya ya ta'allaka gurin ganin ta nemo masa magani, domin dai ita har ta yarda da maganarsa, kuma tana so kafin ta mutu ta sake ganin wasu daga cikin 'ya'yansa, halin da su Fatima suke ciki sam bai dame ta ba. Shiru falon ya dauka kowa zuciyarsa babu dadi mussaman Baba Auta da tunda aka zauna be ce komai ba, ransa in banda zafi babu abinda yake, watakila yana ganin bacin rai da takaicin yaron shi zai zama ajalinsa, tunda duk 'yan kadarorinsa ya daga ya sayar, duk a kokarinsa na ganin malamai da bokaye sun shawo kansa ya mayar da 'yarsa gidansa, anan yake ganin zai fanshe! abinda ya lalatar, to sai dai abin mamaki! aikin ake ana zubar da jini amma a banza domin dai kullum yaron gaba yake arzikinsa yana ha'baka, duniya tana cigaba da suturtasa da rigar arziki. wannan tunane-tunane sune suka zautar da shi, ya yi tsiru a kan kujera sai zare ido yake. Lokacin Shukura ta tashi ta buga wani uban tsale a tsakiyarsu, ta yi zaman 'yan bori! wasu abubuwa ta shiga yi tana furzar da yawu, tasa hannu ta cire d:ankwalin kanta tana walagigi a falon. Gaba'daya hankalinsu ya ta shi. Baba Audu ya dinga yi mata tofi! amma kamar k'ara zugata! yake ta dinga yin iskanci samfur-samfur, don har na wannan lokacin ya fi na baya, duk ta hargitsa musu tunani, Hajiya Fatima sai kuka suke sunyi cirko-cirko a tsaye! Duk yana zaune a kan kujera yana kallon abinda ke faruwa, cikin ransa ya ce yau ko sarkin aljanu ne akan yarinyar zai sauke mata shi. Sama ya hau ya dauko wata murtukekiyar bulala! ya nado ta a hannunsa! yana zuwa ya fara zabga mata a jiki da dukkanin k'arfinsa! Ihu! ta tsala! a guje! ta tayi yunk'urin ta shi ya mayar da ita ya cigaba da zabga mata yana fadin." Za ka yi magana ko ba za ka yi ba." Ya fada lokacin da ya lafta mata duka a gadon baya!.. Ta zabura! jiki na makyarkyata! ta ce" Daddy kayi hakuri don Allah wayyo Allah na shiga uku " Ya k'ara zabga mata da cewa" Shukura ce ko ba ita ba?" Tana wani irin kuka kamar za ta shid'e ta ce" Ni ce wallahi Daddy ni ce kayi hakuri." Bai san lokacin da ya kifa mata wani lafiyayyan mari ba, wanda gabadaya ji da ganinta suka dauke, jini ya billo ta hancinta, sai kawai ta bingire! a gurin ta fadi ta suma. Ba tare da ya ce komai ba ya jefar da blet din ya zauna kan kujera yana wani irin numfashi. Hajiya Fatima jikinta duk ya yi la'asar, alamun rashin gaskiya ya bayyana a tare da ita. Hajiya tare da su Baba Audu hankalinsu bai kwanta ba sai da Shukura ta dawo hankalinta sannan. falon ya yi tsit! sai sautin kukan Shukura dake fita a hankali a hankali. Ya kallesu da fadin." Wannan shine abinda nake fad'a muku, na tabbatar da cewa; abinda yarinyar nan tayi da sanya hannun uwarta a ciki. ni na san wacece Fatima da halayenta" Cikin tsantsar bacin rai ya kai karshen maganar yana sake jin tsanar Fatima a cikin ransa. 'Bangaranta kuwa tun ba a je ko'ina ba yanayinta a nu na cewa bata da gaskiya ta yi tsamo-tsamo! Baba Audu ya ce " Shukura don Uwanki aljanu ki ke sha'awa! da har za ki dinga burgima kina tumami! da iface-iface! ashe baki da hankli dama ?" Hajiya ta ce" Ga babbar mara hankali nan a zaune ai tunda duk abinda yake faruwa da sanya hannunta wallahi ni kaina nayi mamakin ganin Shukura tana iskokai, tunda a gaba ta girma bata ta'ba nuna wata alama ba sai da lamarin nan ya bijiro. amma Fatima kin bani kunya wallahi. wato ashe tuban muzuru! ki kayi? ni ina ta balo'ko'ko! a mayar dake ke kuma kin shirya mugun abu " Shukura na kuka ta ce." Wallahi duk Mommy ce ta tsara mini komai. wai saboda ta lura Daddy yana sona ta ce mu gwada wannan hanyar ko za a dace ya mayar da ita nima na san watarana dole asirin mu zai tonu." Sai ta fara borin kunya da fad'in" Kausasan! maganganu! Baba Auta ya fitar da hannu ya tsinka mata mari! zuciyarsa na tafarfasa! ya ce." Yi mini shiru munafukar banza da hofi." Kallonsa ta yi tana mamakin furucinsa! yau ita yake kira da munafuka bayan duk abubuwan da suke faruwa da sanya hannunsa a ciki, yanzu da ya ga ta kwa'be shine zai cire kansa, wallahi don dai ubanta ne kawai amma da sai ta tona masa asiri. Tana share hawaye ta dauki jakarta ta bar gidan tare da yanke shawara cewa; ko maza sun kare a duniya ta bar Dangaske har abadah. Ko da ta fita babu wanda ya bi ta kanta illah shi da suke ta bawa hakuri, ita kanta Hajiyar nadama duk ta dabaibayeta ta ce." Ni damuwa ta wannan rashin lafiyar da ka ke fama da ita, kuma watakila son kudi ya sanya ka watsar da al'amarin baka neman magani." Tsakaninta da Allah take maganar tare da mayar da hankalinta kansa. Sai ya bagarar da maganar ta hanyar fad'in" Babu Audu ina so ku zama sheda a wannan lokacin. na yankewa yarinyar nan hukuncin fito da mijin aure a cikin sati hudu kacal. idan ba ta tsayar ba, to wallahi nayi rantsuwa da Allah zan d'aura mata aure da duk wanda na yi ra'ayi. Baba Auta ya ce." Wannan daidai ne abinda ka yi saboda haka ke Shukura kin ji abinda mahaifinki ya fada, kiyi kokarin fito da miji kafin cikar lokacin da ya gindaya miki. Kukanta ya 'kara tsananta! gabadaya tunanin ya ta'allaka gurin hanyar da za ta bi domin warware matsalarta. a shekarun baya tayi samari kala-kala, kuma 'ya'yan manyan mutane, amma da yake babu auran a cikin ranta ta dinga wulakantasu har suka watse, yanzu dai shawarar da ta yanke za ta dinga binsu daya bayan daya tana kiransu a waya, idan anyi da ce sun dawo sai ta tantance wanda za ta aura. *** Sai wajen tara da rabi na dare suka dawo gidan gabadaya har da Hajiya da duk ta shiga damuwa sakamakon lalurar dake damunsa domin dai ita duk a tunaninta da gaske ya ke, ba ta san da cewa; a daran ranar ma bai d'aga 'kafa ba, sai da ya sha shagali da bired'ensa hankalinsa kwance, lafiya ce da shi sosai, kuma cikin ikon Allah sam baya shaye-shayen magungunan k'arfi irin wanda mazan yanzu suke tu'ammali. Abun mamaki da safe da na shiga gaishe da Hajiya ta amsa a sanyaye tana sunkuyar da kanta, yanda na lura kamar ba ta so mu had'a ido. har da tambayata baby Nanah. mamaki na ya sake k'aruwa ganin Shukura ta zube a gabana tana gaisheni muryata na rawa take fadin." Antina don Allah ki yi hakuri da abubuwan da suka faru wallahi sharrin shaid'an ne." Murmushi kawai na yi na ce" Ai babu komai Shukura dama can ni ban ri'ke ku a raina ba, wallahi na yafe Allah yafe mana bakid'aya." Ita da Hajiyan suka amsa da "Ameen ameen. kafin na yi musu sallama na fita da tunanin al'amarin a cikin raina. Ashe shine ya ce." Mutukar ta na so ya shirya da ita to lallai sai ta girmamani, kuma ta daukeni a matsayin uwarta, bayan haka kuma ta nemi afuwata. dole ta bi umarninsa domin samun nutsuwa da kwanciyar hankalinta. **** Tun bayan faruwar al'amarin wata hatsaniya ba ta sake faruwa ba, muna zaune lafiya da juna duk da cewa; gurin kowa daban, amma duk lokacin da za mu had'u cikin girma da mutunci muke rabuwa. lokacin ita Shukuran ta tsayar da miji daga cikin masu sonta har an sanya rana wata uku, uban yana ta murna dalilin yaron da za ta auran d'an babban malami. shima kuma nasaba ya duba da nagarta ubanta ya sanya ya dawo har ya saurareta suka daidaita kansu. Kafin zuwan lokacin Hajiya Fatima ta daure aure da wani balarabe a can saudia amma ba tare ba, wai sai bayan bikin 'yar za ta tare a can saudia din. Hankalina ya kwanta ganin uwar da 'yar za su yi nesa da ni, dama sune matsalata kuma sune matsalar mijina. **** Wattanin Nanah goma. tayi 'kafa gudu ko'ina, ga yarinyar tubarkallah. tana burge mutane da yawa saboda kyawunta, tayi gwibibi abin sha'awa, sai dai wasu lokotan idan na kalli yarinyar na kan ji zuciyata ta karye idan na tuna hanyar da aka samar da ita, ina jin tsoro kada a samu wani mara tsoron Allah ya fayyace mata komai, bayan mu muna iyakar bakin kokarinmu gurin nuna mata cewa; mu ne iyayanta. *** Ubangiji yana tafiyar da al'amuransa cikin nutsuwa da hikima. abu uku suna tafiya akan ma'auni guda, Aure-Mutuwa- Haihuwa. dukkaninsu suna tafiya ne da hukuncin rabbil-izzati. abinda ya faru kenan ga rayuwata. lokacin da na cire tsammanin haihuwa na rungumi kaddara, domin dai tuntuni na sanya kaina a cikin jerin wadanda Allah ya jarabta sai kuma ya azurta ni a lokacin da ban yi zato ba, ciki har ya yi wata shida ba mu san da zamansa ba, dalili dama can tun ina budurwa na kan yi tsallaken wata ban yi al'ada ba, bayan haka kuma na yi ki'ba sosai shiyasa cikin ya bi jikina, sai dai 'kasan mara ta da ya d'an kumbura, amma ban kawo komai a raina ba, domin na fi tunanin cewa ko kibar da nayi ne, amma sa'i da lokacin na kan ji kasala da kwad'ayi! da motsi jefi-jefi a cikina. nan ma sai da al'amarin ya yi tsanani tukkuna na fad'a masa halin da ake ciki. Ya kira likitansa domin ya turo likita mace ta dubani. Wallahi lokacin da ta gama aune-aunenta result ya fito, gabadaya ni da shi rasa bakin magana mu ka yi, kawai naga idonsa ya ciko da ruwan hawaye! kamar zai fashe da kuka yake ta zabgawa likitar godiya. ta dinga dariya tana yi mana fatan alheri, anan gurin ya yi mata kyautar sabuwar mota tare da kujerar hajji, ta fita daga gidan da kwarin gwiwa tana godewa Allah. ashe tana da rabon sauke farali kafin ta mutu. *** Na ga gata da kulawa ta kowanne fanni, domin Hajia kusan a sashena take wuni. hidima take mini ba kadan ba, cikin zuciyata na ce" Lallai babu wanda yake iyawa da d'an adam sai wanda ya halliceshi. kuma bahaushe ya ce." Mutum tara yake bai cika goma ba. Har gida ake zuwa a duba ni tare da yi mini duk abinda ya kamata. scanning ya nuna tagwaye ne duk maza. 'Bangaransa kuwa godiya yake ga Allah da fadin." Ko d'aya ya samu ya yi godiya. domin bai sanya a ransa cewa biyun ne ba, saboda ya san babu wanda ya san gaibu sai Allah. Haihuwa ta zo mini cikin sauk'i! a gida na haife yara maza biyu tare da taimakon Hajiya. wacce ta rasa ina zata tsoma kanta ta ji dad'i, ganin zaratan samari a gabanta suna ta tsala ihu! alamun suna cikin k'oshin lafiya. Yanda suke farin ciki ita da maigidan abun sai da ya so ya bani tausayi, Allah kenan mai kyautar ban mamaki! shi yake bayar da abinda kud'i ba za su iya saya ba. Bikin suna aka shirya gagarimi. daga can 'bangarena babu wanda bai samu damar halarta ba. domin motoci maigidan ya tura aka dinga jigilar dauko mutane wanda suke da sha'awar zuwa. Komai ya gabata cikin walwala da karamci. jama'a duk suka koma gidajensu da abubuwan arziki tare da turmin atamfa. To sai dai rainon 'yan biyu akwai k'alubale! wannan dalilin yasa duk na susuce! na rasa yanda zan yi ciwon kai na rashin bacci ya taru yana nema ya haifar mini da matsala ga garima, gefe guda kuma matsalar maigidan ta rashin ha'kuri ta nan, sai abinda ya yi gaba, domin tunda ya lura da cewa; na fara sallah. ya ma'kale mini sam bai bari ma nayi gyare-gyare ba, haka nan yake zuwa ya sauke bu'katarsa ba tare da ya nuna wata damuwa ba, a kullum maganarsa daya ba zai ta'ba gajiya da ni ba. Sai da yaran su ka yi k'wari tukkuna na d'auki masu raino! sannan ne fa na fara gyara kaina wai ni nan zan cigaba da gayu! aikuwa tafiyar ba ta yi wani nisa ba, wani cikin ya samu! na shiga tashin hankali mai tsanani! ganin duka-duka Hassan da Hussani watansu bakwai a duniya ya za a yi na sake wata haihuwar. kuka na dinga yi sosai! da tunanin yanda zanyi da cikin, domin ina gudun kada yaran su samu matsala. gashi maigidan baya nan ya yi tafiya. Haka dai na yi hakuri har ya dawo ya sameni na kod'e! ido duk ya zurma! saboda fargaba da tashin hankalin hankali, babu kwalliya babu kulawar da yake samu. Ko da ya tambayeni abinda ke faruwa? rushewa nayi da kuka! na ce" Ciki ne da ni, kuma wallahi yanda nake jin motsi sosai ya yi 'kwari! yanzu ni ban san ya zanyi ba. Ya zuba mini ido da yanayi na damuwa a tare da shi ya ce " Shine me ? don kina da ciki." Na ce." Ban gane ba, ai ka san dole na damu tunda yaran nan ba su yi kwari ba watansu fa bakwai." Ya daga mini hannu da cewa" Za ki butulcewa Allah kenan?" shiru nai ina kallonsa. ya cigaba da cewa; ban za ci haka daga gurinki ba wallahi. idan duk shekara za ki dinga haihuwa abin alfahari ne a gurina, domin ita muke nema ido rufe kuma ya ba mu mai ya kamata mu yi masa?" Jikina ya yi sanyi na ce" Ni fa bana nufin wani abu kawai ina tunanin halin da yaran nan za su shiga" Ya ce."Allah shi yake rayawa, da ikon Allah ba za su samu wata matsala ba." A sanyaye na ce" To shikkenn amma dai idan na haihu sai mu yi tsarin iyali saboda yaran su yi 'kwari." Ya murtuke fuskarsa yana kallona! bacin rai na hango mai tsanani a fuskarsa! Sai na sunkuyar da kaina gabana yana fad'uwa. Ya ja tsaki! mai tsayi ya ta shi ya fita ya bar ni a zaune da tunanin mafita. Da 'kyar na shanyo kansa ya ha'kura! amma ya yi mini gargadi cewa kada na sake yi masa maganar tsarin iyali, idan ba haka ba, to zai auri wacce take son had'a jini da shi. jin haka yasa na daina masa maganar saboda har ga Allah bana bukatar had'a miji da wata wani mugun so nake masa mussaman yanzu da muka zama abu d'aya zuria tana yawa a tsakaninmu. **** Da jegon yarinyata Hamida wacce taci sunnan mamansa na je kano bikin Saliha da Jamila wanda ya kasance tsiran sati daya a tsakani, shiyasa na ji dadin hakan, domin dai na riga na san da cewa idan bikin ya rabe, bai zama lallai ya bar ni na je duka ba. Sai dai yanda na ga unguwar ta sauya ya sanya na yi mamaki sosai. gabad'aya hanyoyin da suka lalace a tsakanin bakin titin da cikin lokon gidan Baba Asabe kwalta ce a shimfid'e, wanda ni dai tunda na ta so nake ganin gurin a haka da tudu da kwari kwatoci ko'ina da bola babu kyawun gani, amma tun daga bakin titi komai ya canza gwanin ban sha'awa. Baba Asabe ce take sheda mini cewa; duk wani cigaba da unguwar ta samu daga mijina ne, kuma duk wanda yake makotaka da ita yana cin arziki, nan take fada mini jerin mutanan da ya bawa kyautar kujerar hajji daga cikin 'yan uwata, ashe duk lokacin da ya zo garin sai ya shiga unguwar ya gaisheta. Cikin zuciyata na ce" Zai aikata fiye da haka, domin kyauta a jinin jikinsa take, babban burinsa ya samu ya bayar ga mabu'kata. Dubu dari-dari na bawa Saliha da Jamila gudummawa, sosai na yi musu fatan alheri tare da tabbatuwar zaman lafiya a gidajen auransu, sai da yanda na ga Talatu ta lalace! al'amarin ya ta'ba mini zuciya, wallahi 'buya na yi na ti'ki kuka na k'oshi! wato dai shi dan adam ba a gama masa hallita har sai ya mutu, lafiyayyar macace, ta koma Zautacciya, yau da lafiya gobe babu, kullum tana rufe a daki tana zage-zage! duk gashin kanta ya gwaigwaye! saboda yanda take cizgarsa, idan abin ya yi tsamari! sai a mayar da ita asibiti a cigaba da bata magani. kai jama'a mu shuka alheri don girman Allah. za mu gama da duniya lafiya. Haka na bar garin kano cike da alhini da tunanin yanayi na rayuwa. ***** Kallonsa na yi a lokacin da yake 'ko'karin zama a kusa da ni, wanda fitowarsa kenan daga wanka daure da towel a jikinsa. Yanayin kallon da yake mini ya sanya jikina yin la'asar! na ce" Na shirya maka abinci yana kan tevur na san kana jin yunwa ko?" Girgiza kansa ya yi da cewa; ba wannan yunwar na ke ji ba" ya fada tare da riko hannuna. na zura masa ido domin sake nazartarsa duk da na riga na fahimci abinda yake da akwai. na ce" dawowarka kenan fa, na san akwai gajiya da yunwa a tare da kai. ya kamata ka ci abinci ka huta sannan komai sai ya biyo baya. Ya girgiza kansa tare da matsowa jikina ya d'auki hannuna ya d'ora gabansa da cewa; damuwar wannan ta kori komai. bana jin wata yunwa domin na ci abinci a jirgi, ya kamata ki bani kulawa ta mussaman, idan kinyi la'akari da shud'ewar lokacin da mu ka yi ba mu had'u ba, wata uku fa, wallahi ni kadai na san irin wuyar dana sha, bayan haka kuma Hamida ta yi wayo, ina so yau na samar mata da mabiyi mace ko namiji, ke yau ma dai yanda nake jina din nan, biyu zan zuba" Dariya ta su'bce mini na ce" Allah sarki! amma ka ba ni tausayi wallahi domin abin nan dai ba zai samu ba, saboda ba ni da tsarki.' Lokaci guda yanayinsa ya sauya, ya ce." Ban yarda ba wallahi sai na duba." Ya fada yana kokarin kamo ni. na goce tare da kokarin guduwa! ri'ke ni ya yi da kyau! ya kwantar da ni kan gadon da cewa; idan na duba na ga 'karya ki ke to mai k'watarki a hannunsa sai Allah." Kukan shagwaba na fara ina tureshi tare da san bugun 'kirjinsa. a kasalance ya kalleni! yana lumshe idonsa, turje-turjen da nake na lura kamar yana kara masa kuzari! da za'kuwa! Aikam na samu abinda na ke so, domin dai ni babban burina naga yana yi mini rawar jiki, ina jin d'adin hakan. Ya dinga bin fuskata da zafafan kesses masu hargitsa lissafi, yana yi yana shanye hawayen da ke fita na iya shege! jikinsa sai kyarma yake, ya fara yi mini wasu abubuwa wanda na gaza jurewa! da yake nima a bu'kace nake! ban san lokacin dana matseshi a jikina ba, tare da bashi taimako. ban san wanda ya bi buk'atuwa ba a tsakaninmu, ban ta'ba kuka ba a ranar sai da nayi saboda irin abubuwan da yake mini wad'and'a suka susutar da ni, na dinga buga sambatu! gashi na ri'ke wuta ya zama ni nake sarrafa komai. Tabbas a ranar munyi abubuwa masu wuyar mantuwa da tsayawa a rai! kuma babu shakka Allah ya yi ikonsa ya rantsar da rabo a tsakaninmu. Haihuwa nake duk shekara, yayin da arzikin mijina ya cigaba da yalwata, na samu nutsuwa da shi, ya samu nutsuwa da ni, bani da matsalar komai domin mijina ya tsaya mini yana kula da ni da yara na biyar maza uku mata biyu, sai cikin da nake d'auke dashi a yanzu haihuwa ko yau ko gobe. Ina rokon Allah ya sauke ni lafiya tare da masu lalura irin tawa. 'KARSHE *ALHAMDULILLAHI.* Abinda na rubuta daidai Allah ya ba mu ladan tare, kuskuran kuma ina rokon Ubangiji Allah ya yafe mini. *BINTA UMAR ABBALE*