[8:06AM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO-1 PG-1 Kanal Aliyu Gwarzon jarumin soja kenan, Alhaji Yahuza shi ne mahaifinsa, matansa biyu da 'ya'ya biya. Hajiya Habiba ita ce uwargida, da 'ya'yanta uku. Aliyu shi ne babba, sai Sani da Sa'adiya. Sai Hajiya Talatu me 'ya'ya biyu, Ni'ima da Hamza. Dukkaninsu kansu a hade ya ke, da ya ke sun sami tarbiya sam babu yan ubancin nan bare nuna banbanci a junansu. Alhaji Safiyanu kanin Alhaji Yahuza ne, uwarsu daya ubansu daya, matarsa daya Hajiya Saude, da 'ya'yansu uku, maza biyu Faruq da Sadiq, sai karamar su mace mai suna zainab. Babban gida ne kowanne da bangarensa, gaba dayansu akwai kyakkyawar dangantaka da son juna a tsakaninsu. Mahaifiyarsu Hajiya Babba, ita ma a gidan ta ke bangarenta daban. Dattijuwar arziki ce me addini da ibada, ga ta da kokarin zumanci, du inda ta ji dan'uwanta wanda ko kaka dangantaka ta hada su, sai ta jawo shi jikinta ya ci arzikinta da na 'ya'yanta. Hajiya kyaftin kenan dattijuwar arziki, ko yaushe jikokinta suna tare da ita tana hada kawunansu, tana yi musu nasihohi da tattausar murya, ta rinka yi musu tarihin Annabawa da abubuwan da ta san za su karu dasu, su kara samun fahimta ko da a makaranta ne. [1:15PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**2 Yace, kai hajiya, kin matsanta min da maganan auren nan, wai ke bakya kishina ne? Tace ni ai indai akan wannan ne banayi, ka samo min abokiyar zama, idan kuma kai bazaka iya ba ni na samo maka." hajjaju kenan, za'a nemo in Allah ya yarda. Tace dakai wani ne saika samo a hadaka da 'yar uwarka sadiya, tunda kaga ansa rana data yi candy za'ayi aure insha Allahu." yace kai hajiya, kedai kina son hada sabgata da yaran nan so kike su rainani ne? Tace, "ai kaji sha'anin naka, sai son girma kamar gyambo, yo meyesa baka nemo tuni kayi ba? To bari kaji na fada maka, ko ka nemo yarinyar da kake so ayi auren kafin bikin sadiya, ko kuma ayi auren lokaci daya da sadiya." ya mike yana dariya, "hajaju kenan, kin taba ji anyiwa namiji auren dole? Tace za a fara shi kuwa daga kanka." hajiya dai da gaske take lamarinta, don ta matsu taga Aliyun yayi aure, tana so ya kara samun daraja da mutunci a gun iyayenshi, saboda Aliyu yaro ne nutsatse mai hankali da nutsuwa, yana da biyayya. Du abunda iyayensa suke so shi za yayi. Du da karancin shekarunsa yanada halin ya kamata, shiyasa ya zama abokin shawarar iyayensa. Karfe shidda na yamma direba ya kwaso 'yan makaranta tun safe. Da yake zainab a firamare take, karfe daya ake tashinsu, to saita shiga lesson na awa daya, karfe biyu take fitowa sannan antashi su sadiya da ni'ima da suke 'yan sakandare. To sai suyi sallah direba ya kawo musu abinci suci, sai kuma shiga islamiya data ke duk a cikin makarantar. Karfe hudu zasu fito sallar la'asar, suyi dan ciye-ciyensu su kuma komawa aji, sai karfe shidda za'a tashesu suyo gida. Yau direba yana tsayawa zainab ta bude ta fito tayi bangarensu, kicin ta nufa don tasan mamanta tana kicin ita da 'yan aikinsu don gudanar da girkin dare. Hajiya saude ta tari 'yarta da murna tana cewa, "sannu da zuwa auta." ta rungumeta suna dariya ta cika uwar tata ta nufi firiji tana cewa, wallahi mama yunwa nake ji." ta bude firij tace kai mama ina vanilla ice-cream dina? Mama tace a'a zeey bana son rigima, ba tun jiya kika gama shanye naki ba? Tace "to mama bana sa ragowar dayan a firij ba." tace to ai kuwa dashi sadik ya tafi makaranta da safe. Zainab tanajin haka ta yarda jaka ta hau tsalle da ihu tana kuka, "wallahi saiya biyata ice-cream. Faruk da sadik suka shigo duk da goyon jakunan su, suma nasu direban ya dauko su, don makarantar matan daban ta mazan daban aka sakasau. Tace "wai ice-cream dinta tasa a firij waye ya daukar mata a cikinku. Faruk yace "mama ai sadik ne ya tafi dashi makaranta." sadik yace ai banaki bane ragowa ne na dauka da zaki kama yiwa mutane kuka." tace "to bani nasa shi a firij ba kaje ka dauka min ba, wallahi sai biyani abuna." taci gaba da kukanta tana tsalle. Aliyu yana dakinsa ya ringa jiyo ihunta, ya shigo da sauri yana cewa lafiya? Me akayi mata mama? Tace rigimar data saba ne kawai, ice-cream ne du sunsha roba dai-dai, ragowar daya ne wai ta dauka tasa a firij shikuma dan uwan dayan abokin yin nata ya dauke ya tafi makaranta dashi ya shanye, shiya kawo wannan rikici nata." ya daka mata tsawa, "tashi zaune." ta mike a razane tayi daki da gudu. Dai-dai lokacin ni'ima take shigowa take cewa "wallahi yaya ko abinci bata ci a makaranta ba sai youghot me sanyi ta rinka siya tana sha wuni guda, yaya sadiya tai ta mata fada ta kwace youghot din ta siyo mata meat pie da yambos, saida taga zata daketa sannan taci. Aliyu yace a'a ba akai muku abinci bane? Tace, "ankai mana mana, bata cin abinci sai kayan zaki dana sanyi take sha." ya kwada mata kira da karfi, "zainab kina ina? Ta fito daga falon da sauri ta rabe a waje daya. Yace maza ni'ima shiga kicin ki zubo mata abinci ina zaune ta cinye shi. Ni'ima ta zubo mata abinci ta dire a gabanta, Aliyu ya daka mata tsawa dauki ki cinyeshi. Taja filet din ta fara cin abincin, tsoronsa take ji sosai, don tasan baya wasa. Yace ki cinye shi du idan kika rage ko kaka nida kene. Ya juya ya fita, ya sami direba a waje ya bashi dubu biyar, yace yaje bakori ya siyo masa ice-cream da youghot masu sanyi, da gashashiyar kaza guda biyu." ya wuce dakinsa. Zainab kuwa tana zaune tana kuka tana tura abincin, saida ta cinye tas sannan ta tashi tayi daki ta kuka, me aikinsu ta bita tana rarrashinta, ta hada ruwa a baho, ta cuda ta sannan ta kyaleata ta karasa wankan da kanta ta dauro alwalar sallar magariba, tana cikin shiryawa taji sallamar direba da yake kaisu makaranta. Mama ta amsa masa, ya shigo ya durkusa yace, "gashi mama inji yaya Aliyu, na zainab ne. Maman ta karba tana budawa, tace "Aliyu kenan, ai shine ma ja gaban sangartar da zainab, don daman can shiya koya mata irin wannan cimar bata damu da abinci ba, gashi ta fara girma abu yana nema ya zame mata jiki. ta kwala mata kira, ta fito da sauri tana cewa "mama me yayan ya kawomin. Ta tura ma kayan, gashinan 'yar lelen yaya. ta fito ta kama dubawa, robar yght guda shida, ice-cream guda shida, gasassun kaji guda biyu, ta dauki robar ice-cream da nono dai-dai ta saka a firij, tace wlh mama kada ki bari sukuma daukar min. surayya [1:16PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**3 MAMAN ta bata kaza daya da youghot guda uku, ice-cream guda uku, gashi nan saii tafi gidan hajiya ki hadu keda 'yan uwanki mata da mazan tunda suna can kuci, wannan kuma in na nashiga wajen su hajiya cin abinci maci acan." zainab ta dauki ledar tayi bangaren wajen hajiya, ta shiga da sallamarta, ni'ima ta tarota tana dariya tare da cewa, "sai 'yar gidan daddy, me kika samo mana. Tace, "ai bazaki ciba tunda kika sa aka sani cinye abinci." tace haba yi hakuri 'yar kanwata, kinsan tsakaninmu bata baci." sadiya ta karbo kayan tace, bawanin kunyi fada da ita dani take shiri." gaba daya suka hadu suna cin kazar da youghot din da ice-cream din. Ahaka Aliyu ya shigo ya sami kujera can nesa dasu yana duba jarida. Zainab tasa jummai mai aikinsu ta dauko mata jakarta ta islamiya tana son yin hadda, don gobe malaminsu yace su zo masa da haddan Arrahaman izu bakwai. Ta bude Qur'ani ta bawa hajiya, tace hajiya rikemin nayi hadda, gobe malam yace muzo masa da hadda, du wanda bai iya ba zai sha bulala. Hajiya ta rike mata Qur'ani ta fara karanto Arrraman cikin kwararen larabci irin wanda ake koya musu a islamiyasu, da yake tana da zakin murya, gashi ta iya fitar da kowane harafi, ta iya rera karatun da kome kake yi in kaji saika tsaya ka saurareta. Aliyu ya lumshe ido yana mai jin dadin karatun nata, a ransa kuwa fassara suran yake yi yana fasalta mata 'yan aljannan da Allah ya yiwa rahama. Tana kaiwa karshen suran tace Alhamdulillah, na haddace a kaina." hajiya tace "barakallahu fik, kin wuce dukan malam." hajiya tace shiyasa nake sara miki mutuniyata shagwabarki bata damuna tunda akwai ki da kwakwalwa mai kyau, du abunda aka gaya miki kya dauke shi a kanki. Sadik yace "iyayi dai da neman suna wai ita ace mata mai ilimi." zainab tace toh ilimi karyane? Ai ilimi shine kan gaba a rayuwar dan Adam. Ilimi lallai ne mace ya kasance tana kula dashi, ilimin addinin ta da kuma ilimin rayuwa. Misali, bari na baka misali da kowanne. Ilimin addini don tasan yadda hukunce-hukunce sallah, tsarki, jinin al'ada, jinin biki da dai sauransu. Ilimin rayuwa kuwa, don kanta ya waye ya kasance tasan abunda yake faruwa a duniya, koda ta sauraron ko radiyo, kada ace mace bata san sunan gwamnan garinsu ba, ko shugaban kasa. Kinga akwai karancin wayewa a wajenki kenan. Ilimi wani abune da yake karawa mutum daraja, Allah mai girma da daukaka yace "Allah ya shaida lallai babu abun bautawa da gaskiya sai shi." kuma mala'iku ma'abota ilimi sun shaida yana tsayar da adalci mabuwayi mai hikima. Kaga saboda muhimmacin ilimi a wannan aya, sai Allah ya ga hada shaidarsa data mala'iku da kuma ta masu ilimi. Ashe du wanda ba malami ba, ba kuma mai neman ilimi ba, toh bai cika cikakken mutum ba. Haka kuma annabi ya fada acikin wani hadisi, "duk wanda Allah yaso shi da Alkhairi, saiya fahimtar dashi Addini." haka kuma yana cewa, "neman ilimi farilla ne akan kowane musulmi namiji ko mace. Kuma Darajar farko idan ance ilimi shine ilimin addinin musulunci,sai kuma ilimi na rayuwa, kamar su ilimin likita, injiniya, siyasa, mu'amala da dai sauransu. Daraja da kimar 'ya mace tana karuwa gwargwadon yadda ta kula da iliminta, kamar kuma yanda darajar da kimarta take lalacewa a wulakance sakamakon yanda taki yin ilimi." mace ta gar itace wadda kunya bata hanata neman ilimi, ilimi na addini kona rayuwa. Ka duba ka gani, nana Aisha matar manzon Allah (S.A.W) du da yarinya ce karama, domin har annabi ya bar duniya shekarunta sha takwas ne, amma tayi gwagwarmaya da maza wajen haddace hadisan Annabi (S.A.W), domin itace ta hudu a cikin mutane bakwai da suka fi kowa haddace hadisai annabi acikin sahabbai. Kaga wannan yana nuna kulawar mata da ilimi kenan. To kada kuma yi min zargin son gwaninta ne yake sani yin karatu, a'a inason yin koyi da nana Aisha ne, don nima inaso na zama mace ma wadatatcen ilimi. Hajiya tace Allahu akbar, Allah ya baki ikon yi. 'yan'uwan suka sa mata dariya, tare da cewa sai auta. Aliyu yarinyar yaji ta burgeshi, ta kara shiga ransa sosai, yanda take da kyakyawar kwakwalwa ya kamata abarta tayi ilimi mai zurfi don ta zama wani abu gaba. Iliminta ya amfani sauran al'umma. Washe gari yaya Aliyu sammako yayi ya koma kaduna bakin aikinsa. Cikin hukuncin ubangiji sai ga mama da ciki, don ita harta fitar da ran sake haihuwa, to ta ga zainab shekara bakwai harda wata uku. Sannu a hankali hajiya tana matsawa aliyu da maganar aure, shifa ya gaya mata bashi da lokacin da zai tsaya duba matar da zai aura, ita tace "to ta nemo masa, don ita tanada lokaci. Du da akwai gidan makocinsu Alh haruna, 'yar gidan mansura ita take mutuwar son Aliyu, du sanda yazo tai ta shige da fice kenan a gidan, ayi masa soye-soye na kayan dadi akawo masa, amma baya kulawa saidai kannensa su cinye, hajiya ta zuba tukuici. Duk yanda mansura taso taja ra'ayinsa don ya sota, ya rinka sauraranta bata isa ba, ko kallonta ba yayi saboda miskili ne. Ita kuwa hajiya taga tayi tayi dashi ya samo matar da zai aura ya kasa, suka nema masa auren mansura. Surayya Abubakar [1:16PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**4 SUKA nema masa auren mansura. Alh haruna mahaifinta yaji dadi, inda yace a hade sa ranar data yaya sadiya ayi biki gaba daya." da mansura taji wannan labarin kamar ta zuba ruwa a kasa tasha don zumudi da murna. Shikuwa yaya Aliyu ya hakura ne ya yarda don bashi da yanda zaiyi, tunda iyayensa da kakansa sunfi karfinsa. Yaya sadiya sunyi candy a ranar suka yi fatin candy, kawayenta da 'yan makarantar sun shayin hotuna harda bidiyo caset don dai tarihi. Sun kakkarbi adireshin junansu da lambobin waya, don dai su rinka tunawa da juna suna sada zumunci a junansu. Satinsu biyu da candy yaya sadiya ta fara rabon katin bikinta. Inda itama mansura ta ke raba nata katin bikin ga kawayenta da 'yan uwa. Haka yaya Aliyu anbawa sani ya kai masa katunan can kaduna, yanata rabawa abokan aikinsa da abokan arziki. Ranar alhamis akayi kamun mansura, ranar jumma'a akayi kamun yaya sadiya. A ranar yaya Aliyu ya dira daga kaduna, da wasu tawagar abokanan nasa da yayi musu masauki a daya daga cikin gidajen iyayensu. Washe gari ranar asabar akayi daurin aure, gaba daya ankon galila shadda suka matsa, da hadadden dinki yi mata na aikin saa. Du ita suka sa, saida akaje gidan su mansura aka dauro auren yaya Aliyu, sannan aka daura auren yaya sadiya, daga nan maroka suka shiga busa da kade-kade, su Alh suka shiga rabon kudi ana watsawa maroka kudi. Haka abokanan yaya safiyanu mijin sadiya, sukai ta watsawa maroka kudi. Karfe hudu dai-dai aka shirya walima, kawayen yaya sadiya da kawayen mansura, abokanan yaya Aliyu da abokanan yaya safiyanu, du sun ci kwalliya ta kece raini, hadaddun 'yan mata gogaggu, wannan ta wace wannan, wannan tana wace waccan, sun sha ado da kwalliya. A harabar gidansu akayi da yake farfajiyar katuwa ce, an kafa rumfuna aciki an zuzzuba kujeru farare acikin rumfar. An ware gunda Aliyu da mansura, safiyanu da sadiya zasu zauna. Anyiwa wajen ado da fulawoyi da roba balan-balan, an wadata wajen da amare da angwaye, sunyi kyau kamar fulawa aka dasa dan kyau. Ni'ima 'yar shekara sha hudu ta fara zama budurwa, domin makerin budurci har ya fara kerata. Tayi kyau ta ratso cikin tsakiyar filin gurin da lasfika take, ta dauki lasfikar tace, "ansuturillah." ta fada sau uku, jama'ar sai kowa sukayi shiru suka zuba ido. Ni'ima ta kalli inda iyayenta suke taga daddyn zainab da Abbansu, shigarsu iri daya. Haka iyayen su mata duka su ukun shiga iri daya suka yi. Ta kalli jama'a taga kowa yayi shiru ya nutsu ya zuba mata ido. Saita ce "muyi salati ga annabi." gaba daya suka ce (s.a.w)." bayan an gama karantawa tace, "ya shafi sha biyu, Allah ya shafe du wata fitina da zata kunnowa ma'auratan nan." gaba daya akace ameen." bayan angama tace Ayatul kursiyu kafa uku, Allah ka karemu ga mugun ji, mugun gani, sharrin mutum dana Aljan, da sharrin duk wani abunki. Allah ya basu zaman lafiya, Allah ya basu zuri'a dayyiba saliha, Allah yasa anyi wannan aure a sa'a. Ta cika da fatiha, ta daga hannunta tana addu'a ana amsawa da Amin. "waman yattikillah yaja'allahu makraja, wa yarzurku min haisu lah ya tasiri, waman tawakal alallahi fa huwa hasbun, innallaha baligul amri kadija'Allahu li kulli shai'in kadira. Amin. Yayinda kowa ya shafa. Tace to Alhmdllh, jama'a muna yi muku barka da zuwa, mungode da hallartat taronmu da kuka yi don ku taya mu murnar auren 'yan uwan mu. Bari na kira muku autarmu dan tazo tayi mana 'yar fadakarwa kadan kafin malaman namu da zasu yi wa'azizzikan su gama karasowa, tace "zainab zeey daddy bismillah." zainab 'yar shekara takwas ta taso cikin nutsuwa tana murmushi daya karawa fuskarta kyau, tana sanye da dan dan datsetsen yelow les da yake ta walwali, dambara-damran dutsuna ajiki kamar madubi, tasa gwagwaro yelow, ta yafa dankwalin les din. Tasa fashion azurfa mai yalayen dutsuna wuya da kunne, da zobensu, tasa warwaraye suma yaleye. Yarinyar tayi kyau sosai, tsarin kwaliyarta kamar wata babba. Shiga iri daya sukayi da ni'ima komai da komai. Ni'ima ta mika mata lasfikar suna yiwa juna murmushi, yayinda masu hotuna suke basu flasha, masu filet din dvd da cd suke ta dauka, ni'ima ta koma wajen zamanta, zainab cikin zakin muryarta tace "Aslm 'yan uwa musulmi." gaba daya kuwa suka amsa mata da "wslm. "hakika ina taya 'yan uwana murna da wannan rana ta aurensu, Allah ya basu zaman lafiya dauwamamme, yaya sadiya da aunty mansura, yanzu Allah ya kaiku wani matsayi da rayuwarku zata canja ba kamar sanda kuna gida ba. 1- abu na farko da ake so 'ya mace ta gane ta fahimceshi shine, hakkin mijinta akanta, ta gane cewar miji shine shugabanta, ta rinka jin hakan a ranta. Saboda Allah ubangiji yace, maza masu tsayuwa ne da shugabanci a kan mata, kuma maza suna suke da fifiko wajen girma da daraja akan mata." wadanan dalilai su zasu mace ta dinga jin cewa, namij fa shugabane, kuma ta dinga jin haka a jikinta, kuma tasan yana da hakki akanta, domin tasan bazata fita ba saida izninsa, kuma duk inda zata je saita san ransa bazai baci ba. Manzon Allah (s.a.w) ya fada a cikin hadisi ingantacce [1:17PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**5 YA fada acikin hadisi ingantacce, saboda girman hakkin miji akan matarsa, "da za'a umurci wani yayi sujjada ga wani, dana umurci mace tayiwa mijinta sujjda. Koda miji zai bukaci amfani da matarsa, ita kuma tana kan sirdin rakumi, to kada ta hanashi. A wata ruwayar ta bukhari, manzo Allah (s.a.w) yace, "idan mij ya kirawo matarsa zuwa ga shimfidarsa ita kuma taki har ya kwana yana fushi da ita, to mala'iku zasuyi ta tsine mata har sai an wayi gari, bukhari ne ya ruwaito. Idan mace ta gane hakkin miji akanta, kuma tayi masa da'a akan abinda ba sabon Allah bane, to hakan zai taimaka kwarai wajen gyara zuciyarta. 2- abu na biyu shine amana, anaso mace ta zamo mai amana bata cikin abunda ya shafi dukiyarsa, kuma bata ha'ince shiba akan karan kanta. Ha'intar miji wajen dukiyarsa daukan wani abunsa batare da iznin sa ba. Ha'intar miji aka karan kanta kuwa, shine ta bada kanta ga wani namiji. Ko kuma tayi kawance da mijin da banata ba. Du matar kirki bazata yi haka ba. Toh macen kirki itace wadda bata ha'intar mijinta daga dukiyarsa ko kuma akanta. Salihan mata masu da'a ne ga mazajensu, masu tsare mutuncinsu ne da dukiyoyin mazajensu, basa ha'intar mazajensu alokacin da basa nan. Manzon Allah (s.a.w) ya fada cewa babu yanda za ayi mace ta dauki wani abu a dakin mijinta ba tare da izninsa ba, to bai halatta ba, sai sahabbai suka tambayi annabi cewa "ko abinci ne? Sai annabi yace "wannan shine mafi daraja acikin dukiyoyin mu, ba a yarda mace ta dauki abincin mijinta tayi kyauta dashi ba. Kuyi hakuri plz yau bazan samu daman pstn ba, wannan wanda nadan soma rubutawa jiyane, amma gobe insha Allahu zanyi muku 3 times pr day, kuyi hkr [1:17PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**6 BA AYARDA mace ta dauki abincin mijinta tayi kyauta dashiba saidai in dafaffe ne in tayi, gudun kada ya lalace, to sai a sadaukar dan gudun kada ya zamo almubazaranci. Shima idan miji ya dawo saiki sanar masa, ko gidanku zaki aika da abinci saiki sanar masa, bare ki bawa wani can daban. Wannan yana cikin cin amanar miji. Manya mutane suka rinka mikewa suna yiwa zainab kyautar kudi, saboda yanda yarinya karama ta burgesu, Abba da daddy sai washe baki suke yi don jin kokarin 'yar tasu da kwazonta. Mamanta kuwa tayi hamdala acikin ranta, tana mai jin dadin baiwar da Allah yayi wa 'yarta tun tana karama, kowane tebir mutum hudu ne a zagaye dashi, akayi umurni da masu sabis su fara rabon abinci, shinkafa ce fara da taliya itama haka, sai soyayyun kaji da gasashen nama, sai mitfy, samosa, sopringros, haka kowa za a tsira katon filet a dire a gabansa, mata masu wa'azi sun zo, wajen yayi shiru an nutsu ana cin abinci, yayinda aketa kwararo wa'azi akan zaman aure ga ma'aurata. Washe gari akayi yini, ranar litinin akayi fati, a ranar kuma aka kai amare dakunansu. Burin mansura ya cika, yau ta auri gwarzon namiji cikakke, wato Aliyu. Tasan sarai Aliyu miskili ne bai fiya wasa da dariya ba, shi hasalima magana wahala take masa yi masa, don inzaka daka ta tashi sai dai kuyi ta zaman kurame dashi. Aliyu mutum ne mai tsafta, dan gayu ne mai son kamshi, baya damuwa du tsadan turare zai saya indai kamshin shi yana da dadi. Aliyu yana ji da kansa, akwai iya jan aji, yana da tsananin iyayi da gwalli kamar mace, ya fiya kasaita da son girma kamar wani basarake. Washe gari ranar talata gajiyar biki bata bar ni'ima da zainab zuwa makaranta ba. Tun asuba da aka tashe su suka yi sallah, suka sake komawa gado suka nade cikin bargo suna bacci. Karfe bakwai masu aikinsu sukayi ta tashinsu don su shiry su tafi makaranta, amma du sunki tashi. Dole sai rabuwa suka yi dasu. Karfe goma dai-dai Aliyu ya shigo gidan don gaishe da iyayensa. A farfajiyar gidansu mai gadi da direbobi suna ta risinnawa suna gaisheshi. Aliyu ya cewa malam idi direba, "ina 'yan makaranta , i ce kodai basu makara bako? Malam idi yace ai basu fito ba, yau ban kaisu makaranta ba." a zuciye Aliyu ya shiga gidan, kafa kawai yasa ya daki kofar ta bude garam. Ni'ima da zainab suka tashi a firgice, suna mitsike ido. Suna dago kai suka ganshi. Kafarshi daya akan gadon, dayar tana kasa, fuskar nan tayi kirtif da ita kamar bai taba dariya ba. Zumbur suka mike suka diro kasa daga gadon, suka durkusa can nesa dashi, suka kama cewa "yaya ina kwana? Bai amsa musu gaisuwar ba, sai tambaya daya jefo musu cewar "meya hanaku zuwa makaranta? Gaba daya jikinsu ya hau bari suna in'ina da kame-kame abunda zasu ce, ya daka musu tsawa "ku tashi ku saka uniform dinku, ina jiranku a falo." suka mike da sauri kowacce ta nufi kwaba. Shikuma yayo falonsu yana tsaye. Mintuna kadan suka fito sanye da kayan makaranta da jakunkunansu a rataye, ya sasu a gaba har farfajiyar gidansu, ya kwalawa malam idi direba kira, ya taho jikinsa na rawa. Yace "daga yau du ranar daka kara kin kaisu makaranta abakacin aikinka." malam idi ya rikice jikinsa yana bari, yace "kayi hakuri yallabai, wallahi ba laifi na bane sune basu fito ba." yace "daga yau idan kaga basu fito ba kayi min waya kawai ka gaya min. Yace "to yallbai." suka shiga motar direban ya jasu. Shikuma Aliyu yayi cikin gida. Zainab tace, "inbanda abun yaya, daga yin aure saika fito da sassafe. "ni'ima tace, "ai gwandake bangarenku ma na 'yan firamare ne, ni 'yar sakandare nasan wallahi sai an dake ni, daya kyalemu gobe basa muzo ba." gidan Aliyu yana nan daga bayan gidansu ba nisa. Amma tunda aka kai mansura basu je gidan ba, saboda basu da wani lokaci sai dare, sukuma ba fita suka yi da dare ba. Yau alhamis ana tashi daga boko gida suka yo, dan ba islamiya. Ni'ima da zainab tuni sun gama shiri, anko sukayi na wani dandatsesen material baki, ni'ima tana rike da hannun zainab suka tafi. Suna zuwa gidan suka shiga, 'yan aikin gidan sai sannu da zuwa suke yi musu. Suka karasa babban falo inda matar gidan take, sukayi sallama, saida akayi musu izni sannan suka shiga. Mansura ta taresu da murna, a'a sai yau zaku zo, nayi fushi." suka rike hannunta suna cewa, "tuba muke aunty, kinsan kullum da makaranta. Tace, "to amma gaskiya yau anan zaku kwana." suka ce wai kwana aunty? Ai baza a barmu ba a gida." tace haba don Allah, ya ya zasu hanaku kwana a gidan babban yaya." yayinda take kwalawa mai aikinta kira talatuwa, "na'am ranki ya dade, ta amsa da saurinta, ta durkusa a gabanta, mansura tace "bakya ga munyi bai ne baki kawo musu komai ba, nifa bana son shashanci, kirinka kula da aikinki fa." talatuwa tace kiyi hakuri aunty. Ta fita da sauri ta shiga kicin ta hado musu lemuka da snacks taje ta durkusa a gbansu ta ajiye. Zata mike zainab ta bude jakarta ta dauko dari biyar ta mika mata. Talatuwa tasa hannu biyu ta karba tana godiya. Inna laraba tashigo ta durkusa a gaban mansura tana tambayarta hajiya me za'a girka? Surayya Abubakar [1:19PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**7 TA YAMUTSA fuska tana tsara mata abunda zata girka. Harta mike ta fara tafiya zainab tabita tasa mata dari biyar a hannunta, tsohuwa laraba tace, "auta me za a sayo miki? Tace a'a ki rike baki nayi. Laraba ta washe baki tana murna tana godewa zainab. Yaya Aliyu ya shigo, da sauri zainab da ni'ima suka yi masa sannu da zuwa tare da gaishe shi. Ya wuce bangarensa. Mansura ta kwalawa talatuwa kira, tazo da saurinta. Mansura tace, "ki hadawa Aliyu abinci kikai bangarensa." zainab kanta data ke yarinya tayi mamakin abun, bare ni'ima data fara zama budura. Sun san haka bai kamata ba, don ba haka ake yi a gidan su ba. Wata mata ce da goyon 'yarta ta fita da hayyacinta kamar almajira, ta durkusa tana gaida mansura. Mansura ta hade rai tana ya musta, da kyar ta amsa gaisuwan matar. Ni'ima da zainab suka gaishe da matar, zainab tace kwanto yarinyar, bata da lafiya ne? Matar tace "wallahi zazzabi ne da amai da kashi na hakori." yayinda take kokarin sakkota. Zainab ta mika hannu zata karbeta, mansura tayi karaf tace "ke zeey auta yarinyar ba lafiya kokarin daukarta kike? Saita yo miki amai ajiki." zeey tace to kije ki sai mata magani ta sha mana. Matar ta girgiza kai cikin yanayi na tausayawa, tace, "aiba kudin ne, magani har dari tara da hamsin, banida kudin dazan sai mata, kudin yayi yawa, ko dari da hamsin bani da'ita bare har dari tara da hamsin." zainab ta bude jakarsu ta zaro gudan dubu daya ta mikawa matar, "ungo kije kisai mata maganin." matar ta karba bakinta yana rawa. Mansura tace, "ke zeey kudin wa kika samu kiketa rabarwa haka? Zainab tace daddy ne ya bamu da zamu zo ko zamu sai wani abun. Mansura tace to shine kike rabar da kudi baku sai komai ba." zainab tace aunty ai muna da komai me zamu saya? Ba gwanda mu bayarba." matar nan dai tanata sawa zeey albarka harta fice ta tafi. Ni'ima ta fuzge jakar daga hannun zainab, ta bude ta leke bakomai aciki, ta harareta to kin rabar mana da kudin, to yanzu dame zamu sai ice-cream din? Ni shiyasa wallahi bana so nabar kudin mu a hannunki, du saiki rabarwa da mutane mu ki barmu haka. Nidai kawai kirinka bayar da iya naki, kada ki kuma bayarmin da nawa kudin." zainab tayi murmushi, tace "haba yaya ni'ima, abunki ai nawa ne, zan iya iko da komai naki, Allah ya bamu rai da lafiya, muna da kudi a gida, ko an bamu ma tarawa muke yi idan bamuda abun siya. To ga masu bukata saimu hanasu." ni'ima tace, "to amma ai bakya bayar du ba, ai kinsan zamu sai ice-cream." zainab tace bakomai yaya ni'ima, zaki ga Allah ya bamu wasu, don ranan malaminmu yace, "anaso mutum ya rinka ya waita sadaka, saboda tana juyar da bala'i. A zamanin annabi sulaiman (a.s) akwai wani mutum a gidansa akwai wata katuwar bishiya, tsutsuwa tayi 'ya'ya akai. Sai wata rana matar ta gaya wa mijinta cewar, ya hau kan bishiyar nan ya debo musu 'ya'yan wannan tsutsunwar zasu ci suda 'ya'yansu. Mutumin nan ya kwaso 'ya'yan, suka gashe shi, shida matarsa da 'ya'yansa suka cinye. Sai tsunsuwar nan takai karar wannan mutumin gurin annabi sulaiman (a.s), shikuma yasa aka kirawo mutumin yayi musu tsakani da wannan tsuntsuwar, mutumin yayi alkawari bazai sake ba. Ana haka sai wata rana matar nan ya kuma gayawa mijinta ya hau bishiya ya kuma debo musu 'ya'yan tsunsuwa, mutumin yaki, yace "annabi sulaiman ya hana shi ya sake dibar mata 'ya'ya." sai matar tace kana ganin annabi sulaiman zaiyi maka wani abu danka kwashe 'ya'yan tsunsuwa, alhalin shima me shagaltuwane da mulkinsa? Matar dai tai ta rudarsa har ya hau ya debo. Sai tsuntsuwar nan tasake kai kararsa wajen annabi sulaiman, annabi sulaiman yayi fushi, ya kirawo shaidanu guda biyu, daya daga gabas daya daga yamma. Yace sutafi kan bishiyar nan su zauna, idan mutumin nan ya sake zuwa wajen 'ya'yan tsunsuwar nan su rike kafafuwansa su watsoshi kasa. Shaidanu suka je kan bishiya suka zauna. Shikuma mutumin ganin ya debo wa'yancan ba ayi masa komai ba, don haka sa wannan karon ma ya sake komawa domin ya debo 'ya'yan. Har ya taka kafarsa zai hau, sai yaji almajiri yana bara a kofar gida, saiya umurci matar nan data bawa almajirin nan wani abu. Sai matar nan tace bakomai awajenta. Sai mutumin nan ya dawo ya samu lomar abinci ya bawa almajirin nan, sannan ya koma bishiya ya debo 'ya'yan tsuntsuwar nan, saita sake dwowa ta gayawa annabi sulaiman, sai yayi fushi mai tsanani, ya kirawo shadanun guda biyu daya tura kan bishiyar. Sai suka ce bamu saba maka ba, muna kan bishiyar koda yaushe, lokacin da mutumin zai hau kan bishiyar sai wani almajiri yayi bara ya koma ya bashi lomar abinci, sannan ya dawo ya hau. Zamu kama shi kenan sai ubangiji ya aiko da mala'iku guda biyu, daya ya kamani ta wuya ya jefar dani inda rana take bullowa, daya yakama abokina ya jefar dashi inda rana take faduwa. To kinga dalilin sadakar da yayi ya kubuta daga sharrin shaidanu. Aliyu yana daga dakinshi yana jinsu, ya sake jinjina hankalin autarsu, yasan hakika akwai bawar da Allah yayiwa autarsu na musamman. Ya fito daga dakinshi. Surayya abubakar [1:19PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**8 YA FITO daga dakinshi, yayi gyaran murya, ya ciro dubu biyar a Aljihunsa ya mikawa zainab, yace "zeey auta ga kudin ice-cream." ta rissana ta karba tana godiya. Yaya Aliyu ya wuce ya sake fita. Zainab tace yaya ni'ima kinga abunda nake fadamiki ba, inka bayar da kadan sai Allah ya baka mai yawa." ni'ima tace nagani, amma bani su nan kada ki sake bayar mana." ita kuwa mansura a zuciyarta cewa takeyi, "wannan yarinyar da shegen iyayi take. Wajen mangariba suka isa gida. Bangaren hajiya suka nufa sukayi sallar mangariba, zainab ta mike tayi bangarensu, saita tarar da mamanta kwance tana juyi. Ta tafi da sauri ta rikota, tana cewa menene mamana, meya sameki? Maman tace banida lafiya zaina, marata da bayana ciwo suke yi. Nan da nan sai zainab tasa kuka tana cewa, "mama tashi muje asibiti kinji? Mama don Allah tashi mu tafi asibiti ko kya samu lafiya. Maman tace da kyar, saboda ta fara galabaita "zainab asibiti babu abunda zasu iya yi min, Allah ne kadai zai bani lafiya. Ki kirawomin hajiya da umma da ummi, tayi cikin gida da sauri, du ta gaya musu gaba daya suka taho, a lokacin Aliyu yana gidan. Maman ta galabaita sosai, ko hannunta bata dagawa. Umma tana ta hado kayan haihuwar a dakin. Umma tana rike da maman, hajiya tana mata tofi a ruwa a kofi, zainab din taje ta rike maman tana jijjigata tana kuka, tana cewa mama! Mama!! Ki bude idonki kiga hajiyan fa na kirawo miki ita. Ki bude idonki kifa tofi take miki, don Allah mama ki bude idonki kiga umma da ummi., kefa kika ce nakira miki su, don Allah ki tashi." ta kama jijjigata tana gwale mata ido, tana cewa mama! Mama!!. Aliyu yace "umma ku kamata mu tafi asibiti." a lokacin Aliyu yaiwa abba da daddy waya, suka ce to suma sun wuce asibitin." a can suka tarar dasu Abban har sun riga zuwa, aka shigar da mama dakin haihuwa, zainab sai kuka take yi, ta tafi ta rungume daddynta tana kuka tana cewa daddy kana ganin mama bata da lafiya sun shigar da ita can, daddy kazo mu bita. Ya rungumota yana rarrashinta, "kiyi hakuri zainab, ki kwantar da hankalinki, mamanki haihuwa zatayi. Ko bakya so tasamar miki kanwa? Tace ina somana daddy." to kiy shiru ki daina kuka, mamanki haihuwa zatayi kinji ko? Kita yi mata addu'a kinji? Tace "to daddy zanyi mata. Abba yace, hajiya su koma da zainab gida a ar umma da ummi a gurinta. Abba ya taho da hajiya da zainab gida, zainab sai kuka take yi, suna zuwa gida suna ni'ima da sadik su ni'ima suka tare su da cewa ta haihu? Hajiya tace musu a'a ta dai kusa. Du rarrashin da hajiya take yiwa zainab ta kasa yin shiru, sai kuka take yi. Su kuwa can asibiti sun kasa samun nutsuwa, saboda jikin mama da yayi tsanani. Wajen karfe uku na dare ta haifi 'yarta mace, su umma da ummi suka ta hamdala suna yiwa Allah godiya. Karfe bakwai na safe gaba daya 'yan gidan sun hallara, ganin yanda jini ya tsinkewa mama, hankalin kowa ya tashi. Daddy mijinta yana rike da ita yana salati, yayinda likitoci suketa iya bakin kokarinsu. Sunyi mata allura jinin ya tsaya, du 'yan uwa sun zagaye ta, harda sadiya amarya da mansura, su sadik da ni'ima du suna wajen. Zainab kuwa hajiya ta janye ta suna falon dakin da aka kwantar da maman nata. Saboda kuka da zainab din take yi. Ita kuma mama jikin nata yayi tsanani, sai wasiya take bayarwa, sai cewa take cikin dakushashshiyar murya, "ina zainab autata, ki kirawo min zainab dina. Sadik ya fita da gudu yana kuka ya kira zainab, ta taho da gudu ta rike hannun maman nata ta jijjigawa, tana cewa "gani mama, tashi gaya min abunda zaki gaya min, kinji mamana? Ta kwantar da kanta akan ruwan cikin maman nata tana kuka, maman data ke fitar da nishi da kyar ta dora hannunta kan zainab din tana shafawa, a hankali ta rinka motsa bakinta tana karanto kalmar shahada 'yan uwa sunata amsa mata, tana ta shakewa. Su sadiya da ni'ima kuwa gaba daya sun rikice da kuka. Can mama tayi shiru, hamza cikin firgita yace, "ta mutu! Iyayen suka dauki salati ga daya da hawaye, yayinda yaran suka cika daki gaba daya da kururuwar kuka. Zainab kuwa tana yin baya ba'a ankara ba ta sulale ta fadi kasa ba numfashi. Aliyu ya sunkuce ta aguje ya shiga office din likitan da ita. Likitan ya karbe ta da sauri ya dorata kan gado yana kokarin ceto rayuwrta. Aka tafi da mama gida akayi mata sutura aka binneta, kowa yaji ciwon mutuwar mama. Mama mutuniyar kirki me kawaici da hakuri, daddyn zainab karfin hali kawai yake yi, domin yasan yayi rashin da da wuya ya mayar da'ita. Don rashin hajiya saude ba karamin gibi rayuwarsa tayi ba. Anata amsar gaisuwa shikuwa sai yayi jigudin yana tunani, ga 'ya'yanshi 'yan mazan faruk da sadik suna manne da jikinsa, yaran sun kasa manta mutuwar, sai dai kawai kada suna sharar hawaye. Faruk shine sa'a ni'ima mai shekara goma sha hudu, sadik kuma shekararsa sha daya. Kwana daya da rasuwar mama aka sallamo zainab suka taho, da yake ummi ce a wajenta. Yarinyar tayi wata irin rama sai kace wacce ta dade da ciwo. [1:22PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**10 ABBAN yace "toh shikenan Aliyu, Allah ya tayaka riko." Aliyu yace amin Abba, nagode, Abban yace to ka gayawa daddyn naku? Yace "eh, saida na fara zuwa nayi shawara dashi tukunna." yace, "to ai shikenan komai yayi dai-dai, Allah ya tayaka riko." ya amsa da Amin. Ya yiwa mahaifinsa godiya ya tashi ya nufi gidansu, ya gayawa kakarsu. Hajiya murna tayi takara karfafa masa gwiwa daya rike 'yar uwarsa dakyau, ta hakane zumunci zai kara karfi a tsakaninsu." don ita hajiya mace ce mai zumunci, tana so taga kan zuri'ar ta a hade, yayiwa hajiyar alheri, hajiya tanata godiya dasa masa albarka, ya fice ya nufi bangarensu. Ya tarar da umma da ummi a babban falo suna hira. Yace musu, "ku hadamin kayan zainab da daddare zan zo na tafi da ita." gaba daya suka hada baki cikin razana suka ce, "zaka tafi da ita ina? Gidana zata koma zan cigaba da rikonta. Umma ta mike ta kama yi masa fada, " wato mu ka raina irin rikon da muke yi mata, shine zaka ce zaka dauketa saboda kafi mu sanin darajarta, ko iko zaka nuna mana akanta? Yayi murmushi yace "kuyi hakuri, umma ba haka bane." iyakacin maganar kenan yayi musu shiru. Sun riga sun san bai fiya yawan magana ba, sai dai yayi atakaice. Inkin ji shi yana hira mai tsawo, to da iyayensa ne maza. Ya mike yana ce musu, "umma bari na karasa gida." umma tace "saboda maganar tamu bata da amsa ko? Yayi murmushi ya dire musu kudi a gabansu, yace ummi kwasai goro." tace "to, mungode, Allah yayi albarka." yana fita umma ta kama baki, tace, "ki gane min yaro, wai shi babba har ya fimu sanin abunda ya dace. Ummi tayi dariya tace "Aliyu kenan gadanga kusan yaki. Shifa zuwan da yayi yaga dazu bata je makaranta ba, gani yake kamar zamu kara sangartar da ita mu rika biyewa shagwabarta." Aliyu yana isa gidansa yayi fakin ya shiga, a falo ya zauna yana karkade kafa. Mansura ta fito daga daki, tace "sannu da zuwa Aliyu, ga break dinka can, koda yake rana ma tayi kaine kayi fitar safe." yace "nayi break a office din daddy bana tare da yunwa." yace kisa a share wancan dakin, zan dawo da zainab gidan nan zata zauna acikin dakin can. Ta dafe kirji tace "haba Aliyu, ya zaka ce zaka dawo da zainab? Ai zaka takurawa rayuwarta. Don Allah ka kyaleta a gidanku, wannan shagwababiyar yarinyar in zamu iya da ita anan? Ya doka mata harara yace ba shawararki nazo nema ba, idan zainab tazo kada ki barta ta zauna ki koreta." tace, "haba Aliyu kai ka fiya zafin zuciya, daga 'yar wannan maganan saika hau tari, ba nufi na haka ba, ita da gidan wanta "ai ban isa na koreta ba." yamata shiru bai sake ce mata komai ba daman tasan ba zai sake magana ba, don ya fiya miskilanci, baya son yawan magana. *** **** karfe shidda 'yan makaranta sun dawo, suna cin abinci ba dadewa akayi mangariba, suna idar da sallah hajiya ta rungumo zainab jikinta tana shafa kanta, tace "zainab yanzu fa yayanki zai zo zai tafi dake gidansa, zaki ci gaba da zama acan." zainab tasa kuka tace, nidai hajiya bazan jeba nace, yai tamin fada koma ya dokeni, hajiya tace bazai dokeki ba, kuma fada ma ya daina yi miki. Kije ki zauna kinji zainab? Ta make kafada, um-um, ni ba zanje ba." suna haka taji yo sallamarsa, da sauri ta tashi da gudu tai cikin dakin hajiya. Aliyu ya shigo ya sake gaida hajiya, hajiya tace masa "zainab dai tace baza taje ba, ka ganta can harda kuka." ya kwala mata kira ta fito a tsorace, tazo ta durkusa a gabansa yace "shine kika ce bazaki gidana ba? Ta girgiza kai alamar cewa, a'a yace to meye nayin kukan? Yi min shiru. Tasa hannunta ta toshe bakinta ta hadiye kukan. Yace ki goge hawayenki kije, kiyi wa Abba da daddy sallama." tace to, ta goge fuskarta. Ta shiga bangaren su umma ta tarar da Abba da umma da ummi suna falo, Abba yace yaki 'yata tazo ta zauna a jikinsa." yace menene naga idonki alamar kinyi kuka? Tace bakomai, Abba sallama nazo inyi muku zan koma gidan yaya." Abban yace "zainab bana son abunda zai takuraki, in bakya son zuwa ni zansa ya kyaleki kiyi zamanki." tace a'a Abba zanje." yace to shikenan zainab, Allah yayi miki Albarka, kici gaba da maida kai da kokari a makaranta, tanan ne zaku fi shiri da yayan naki kinji 'yata? Tace "to Abba nagode." ta mike ta shiga wajen daddynta, ta daura kanta akan cinyarsa tana kuka. Yasa hannunsa yana shafa kanta yace "kiyi hakuri zainab, nasan bakya son tafiya. Zainab ko yaushe kina raina, dana ganki saikin tunamin da mamanki. Zainab du ina tausaya mana ni dake na rashin mamanki. Kiyi hakuri zainab kiyi zamanki, nasan zai rikeki da amana kamar ni. Kiyi masa biyayya shida matarsa, banda rashin kunya kinji? Tace "to daddy zan kiyaye." ya bude firij ya dauko rubutu a roba ya bata, ungo shanye rubutunki maganin tsari da kariya daga shaidanu." ta karba tayi bisimilla ta shanye, ya karba yasa ruwa ya dauraye mata, ta karba tasha, ragowar ya zuba a hannunsa ya shafa mata a kanta da fuskarta. Yaita mata nasiha mai shiga jiki, yace ta daina kuka ta tashi taje su tafi." hajiya dasu ni'ima su sadik har gindin mota suka rakota suna hawaye tana hawaye. Surayya [1:23PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**11 HAJIYA tana rungume da ita tana rarrashinta suka bude mata gaban mota ta shiga, ta dunkufar da kanta akan gwiwoyinta tana ci gaba da kukanta kasa-kasa, Aliyu ya sallame su du yaraba musu kudi, yace su koma gida, suna tunanin 'yar uwarsu wai anrabata da gidansu kenan. Ya kalleta au baki daina kukan ba? Tayi saurin hadiye kukan nata, ta goge idanuwanta. Tafiya kadan suka isa gidansa, suka fito har daki ya kaita, "nan shine dakinki, talatuwa zata rinka taya ki kwana." dakin yayi kyau, a yau dinan ya sayo mata gadon silba da madubi, sai kwaba ta jikin bango, sai labuye da jan kafet, shikenan ba wani shirgi, sai toilet aciki dake gefe, tace "to yaya." ya fita ya nufi sashinsa, zainab itama ta shiga dakin aunty mansura. Zainab ta kwantar da hankalinta tana zaune a gidan yayanta, tsakaninta da abinci saita ga damar ci, ko yaushe yayan nata yana cikin siyo musu ice-cream, youghot su biskit da cakulet, da yake abinci bai dami zainab ba, ita hakan saya fiye mata dadi. Ita kuwa mansura ta fiya lalaci da sangarta, bata wani iya girki ba, shikuwa Aliyu dan gaye ne mai aji, gashi da kyankyami, don haka bazai iya cin abincin mai aiki ba. Don haka inya zo garin ma saidai yaje gida yaci abinci, don a gidansa inna laraba ita take yin girki. Babbar mace ce amma da kwarinta, don bata wuce yin aure ba, sai 'yar budurwa wato talatuwa, ita take yi mata shara dasu goge-goge da gyaran gado, inta yi baki ta kula dasu. Don wata wauta ta mansura dai-dai da mijin ma inya nason wani abu sai dai ta kira talatuwa. Don haka ma ko meye ya gwammace yayi da kansa, abinci kuwa saiya je gidansu sannan yaci. A gidansu su umma har fada suke yi masa, don me zai rinka baro girkin matarsa baya son ci. Sai dai yayi murmushi kawai yace musu bakomai. Bama yanzu da mansura take fama da laulayi. Da safe yana zaune a falo da wando iya gwiwa da farar shirt, yana lumshe idanuwarsa kamar mai jin barci. Mansura tana zaune kusa dashi tana cin wainar kwai da dankalin turawa, ta zuba shayi a kofi yana ta turiri, gashi yayi kauri da hadin madara da naskofi da dai sauransu. Zainab ta fito sanye cikin shirin makaranta, ta durkusa ta gaishe da yayan nata da mansura. Ta mike a gurguje take, dan takusa makara. Ta dauki shanyin gaban auntyn nata tadan kurba, tace "wai aunty wannan kaurin ai yayi yawa, bakya tsoron ya kulle miki ciki? Mansura tayi dariya tace, laifin babynku ne ba ruwana. Zainab tayi dariya tace ai, "ai gwanda ki dinga ci sosai don ki haifa mana katon baby in rinka daukarsa da kyar." ta nufi firij ta dauko ice-cream da youghot da cake, tazo ta wuce su da sauri saboda yayan nata, tace aunty natafi makaranta." kafin tayi magana Aliyu ya kirata "zainab." tayi saurin juyowa tare da amsawa, a sanyaye tace na'am yaya." zo nan. Ta dawo ta durkusa a gabansa. Yace haka zaki tafi makaranta baki karya ba? Tace yaya zanci cake da ice-cream da youghot a mota." yace wato har yanzu kina nan dakin cin abincin ki ko sai kayan kwadayi? Ke wace iri ce ne? Da safe ma sai kin sha sanyi bazaki ci abinda zai dumama miki ciki ba? Mansura tace wallahi haka nake fama da ita, bata son cin abinci, daga shan kayan zaki sai shan kayan sanyi." yace ina break din nata? Mansura ta kwalawa talatuwa kira, tace mata ina break din zainab? Talatuwa ta shiga dakin zainab da sauri ta dauko break din data kai mata, yanda ta ajiyeshi haka yake, ko budawa bata yiba. Ta ajiye a gaban zainab din. Aliyu ya kalleta yace to maza ki cinye shi yanzun nan." idonta yayi rau-rau alamar sonyin kuka. Shikuwa sai ya jingina da kujera ma ya lumshe shanyayyun idanuwansa kamar zaiyi barci. Ba yanda zata yi, haka ta rinka tura dankalin nan da kwai tana shan ruwan shayin. Cikinta ya cika taji kokarin yin amai take yi, tace a hankalin cikin sanyin muryanta, "yaya ya dago kai yayi mata wani kallo, bata iya fada masa komai ba, ta sake sunkuyar da kanta, ya sake lumshe idonsa. Haka taci gaba da ci tana hawaye, saida ta cinye du. Dakyar ta iya tashi tsaye, tace yaya na cinye, na tafi? Ya bude ido daya yayi mata alama da hannu wai ta tafi. Ta fice inda direba yake jiranta ta shiga ta tafi. Mansura tace gaskiya Aliyu kana matsawa yarinyar nan, da nice saika bata min rai kace ina takurawa kanwarka." ya bude ido daya yace karki manta shekaranta goma sha daya, yanzu ta shiga sakandari aji daya, har yanzu ita yarinya ce, idan bana matsamata taci abinci sai yunwa ta kamata." ta tabe baki tana gunguni, "in rashin cin abinci ne ai a wurinka ta gado, tunda kaima baka cin na gidanka." ya kwanto akan cinyarta yace, kiyi min da kanki mana, du rashin dadinsa ai zanci. Amma zaki rinka sa tsohuwar mutane wahalar girki, sannan kisa wata yarinya daban itace mai bani abinci, kallon yarinyar nan kadai tayar min da zuciya yake." ta zumburi baki bata ce komai ba, ya shafa cikinta yana cewa, "i luv u baby, yaushe zaka iso kaga daddynka? Tace ai kuwa zai jima baiga daddyn ba, sai nan da wata biyar." ya gyada kanshi, Allah kawo minshi lafiya." tadan rankwafo kanshi tace, "Aliyu dan Allah zaka danyi min tausa? Surayya [1:23PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**12 ALIYU dan Allah zaka danyi min tausa? Yace nikuma me zakiyi min? Tace bakomai." yace to kyaleni bacci nake ji." ta ture masa kansa akan kujera, tace to dagani naje na kwanta." yau alhamis karfe biyu direba ya dauko zainab daga makaranta, saboda yau basuda islamiya, shiyasa basu kai shidda ba. Ta shigo tana jan jakartata, ta zube a falo tace "wash! Aunty sannu da gida, ya bybynmu? Mansura tace gashi nan dai yana ta min zillo. Aunty ki bashi abinci yaci yunwa yake ji, inya ci zai daina yi miki zillo." ai naci abinci zeey, kin zata ni irinki ce sai anyi min dura ina kuka? Zainab tayi saurin mikewa, bari na tashi kada ya shigo ya ganni anan ya kuma sani cinye abincin daya fi karfin cikina." tayi dakinta suna dariya. Da mangariba ni'ima tazo gidan, sukayi tsalle suka rungume juna suna masu jin dadin ganin juna, kamar ba dazu suka rabu a makaranta ba. Suka zauna a falo suna dariya. Ni'ima tace auntyn mu ina wuni, ya babyn namu? Lafiyarsa kalau gashi nan yana jinki." ni'ima tace zainab kinsan gobe ne fatin zara'u yusuf shidda na yamma, ya zamuyi wajen tafiya, don yanda muke da zara'u dole ne mu fasa fatin nan? Zainab tace, wallah yaya ni'ima ina so in rakaki, to amma ya zamuyi da yaya, dama ya tafine da sauki, to shi sai ranar littinin da safe zaiyi sammakon tafiya kaduna kan bakin aikinsa." ni'ima tace, "ai dolene ma kije zainab, tare fa nayi mana ankon fatin, har gwagwaron, har takalimin da not din iri daya ne. Kuma yanda zara'u take sonki, ke wallahi kin fiya tsoro, ba sai kice masa zaki zo gida ba sai muyi tafiyar mu ta gida." mansura tace amma ni'ima anyi saurin yiwa zara'u kawarki aure da wuri, shekararki sha bakwai fa? Koda yake daga ganini zara'un nan ta girmeki, Allah ne dai ya hada kaunarku." ni'ima tace shekara biyu fa ta bani, yanzu da ita fa zamuyi candy, wai mijin zai barta ta karasa a gidansa." to saurin na meye? Inji mansura, saura wata shidda fa kuyi candyn, da ya kyaleta ta karasa ba shikenan ba." ni'ima tayi dariya tace tsoro yake yi kada ayi masa kwace, tafiya samari daya wa." talatuwa ta shigo tana jera musu abinci, ni'ima ta bude jalof din taliya ce da farfesun kifi. Ni'ima tace zubamin jalof din kadan da farfesun." talatuwa ta zuba mata. Zainab kuwa farfesun kawai ta diba, ta debo musu fantar gwangwani a firij. Ni'ima tace, zainab wai ke wace iri ce? Ban taba ganin makiyin abinci ba sama dake, yanzu kuma inkinci wannan shikenan saida safe ko? Tace "a haba yaya zai taho mana da cake da icream. Ni'ima tayi tsaki tace, shikenan abincin naki." tace don Allah aunty ki rinka yi mata fada, shiyasa kullum gata nan kamar a busheta ta fadi. Mansura tace ai tasan karonsu da yayanku, saina shiga gaya masa tukunna." talatuwa ta dawo da tangaram a rufe, da gasasshiyar kaaza aciki da mansura tasa agasa mata. Ni'ima tace kai aunty ni aida nasan da wannan ai bazan ci farfesun ba, ba ruwanki aunty, abinda kike so kici shi zaki ci. Muma dai Allah ya aurar damu, ina daga kwance aita yimin komai." mansura tayi dariya tace, ke kuma abunda yake baki sha'awa kenan. Suka fara cin kazar suna hirarsu, zainab ta fara cire hannunta waita koshi, ni'ima da mansura kuwa har kashi saida suka taune. Ni'ima ta kwalawa talatuwa kira tazo, "gani. Kije ki gayawa direban gidan nan gani nan fitowa zai kaini gida." talatuwa ta fita da sauri. Ni'ima ta mike tana yafa mayafinta da jaka, zainab ta rike hannunta tace, "don Allah yaya ni'ima ki bari sai anjima kya tafi kinji? Tace a'a zainab gwanda na tafi, kinsan yanzu yaya yana kan hanyar dawowa gida, kada ya gane ni nazo najaki ya hanaki zuwa goben." tace to shikenan saina zo goben. Ta rakata har mota ta tafi. Sannan ta dawo ciki ta wuce dakinta, alwala tayi ta tayar da sallar ishsha. Aliyu ya shigo ya wuce dakinsa, sai da ya watsa ruwa ya dan shafa lotion a jikinsa, yasa kananan kaya, ya fito falo yana kallon tashar zee-aflam, suna wani tsohon film mai kyau. Mansura tana gefensa tana cin tufa, zainab ta fito daga daki ta durkusa a gabans, tace, yaya sannu da zuwa." ya amsa a hankali. Taci gaba da tsugunnawa tana so ta tambayeshi zuwa gida gobe ta rasa ta ina zata fara. Ya kula da ita yasan akwai abunda take so ta tambaye shi, don haka sai yaci gaba da kallonsa ya dauke kansa daga bangaren tana zaune tana zaune tana wasa da yatsun hannunta, tace "yaya. Yace "uhm! Ba tare da ya kallo taba. Saita yi shiru ta kasa cewa komai. Shikuwa yana jingine da kujera ya lumshe ido yana kallo kamar ma baisan da zamanta a wurin ba, ta sake cewa, yaya don Allah gobe zanje gida. Yace me ake yi a gidan? Tace bakomai. Yace to bazaki jeba." ta sunkuyar da kanta sai hawaye kawai itada bata da wahalar yin kuka. Mansura tace don Allah ka kyaleta taje." yayi mata shiru kamar baiji abinda tace ba. Mansura tace, ni tsiyata dakai kenan, sai ayi ta ma magana kayi shiru kana jin mutane kamar wani kurma. Ko motsi bayyi ba balle yasan dashi take. Zainab ta mike a hankali zata wuce daki, ya kirata "zainab." ta juyo da sauri tare da amsawa na'am yace "don nace bazaki jeba shine kike kuka? [1:23PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**13 TA juyo da sauri tare da amsawa na'am. Yace "don nace ba zaki gidan ba kike kuka? Tayi saurin girgiza kai. Yace bakida baki? Tace a'a ta koma ta durkusa a gabansa tace, "yaya dama bikin kawar yaya ni'ima za'ayi, shine zan rakata." yace "to me ya hanaki ki gaya min gaskiya? Tace, "don Allah yaya kayi hakuri ba zan sake ba." ya jinjina kai. Tace yaya naje goben? Ya daga kai. Amma kada kiyi dare." tayi murmushi, "yaya nagode, Allah ya saka da Alheri." tamike ta shige dakinta tana murna. Da safe a makaranta zainab take gaya wa ni'ima yaya ya barta zata zo. Ni'ima tayi murna, tace "to ki taho da wuri dai. Bayan sun tashi daga makaranta, karfe biyar na yamma ni'ima ta bugo wayar mansura tana neman zainab. Zainab din tana karba ni'ima tace, "haba zeey, ki sauri kizo man biyar fa tayi. Zainab tace, "nayi wanka na gama kwalliya, yaya nake jira ya fita nasa kayana na taho. Tace baya barki ba ki fito ki taho kawai mu tafi. Tace mata, cewa fa yayi kada na dade, to kinga gwanda yasan ban taho da wuri ba. Tace eh to gaskiya hakane. Yauwa kingan shi can ma ya fitarsa, yanzu direba zai kawoni. Wajen fatin ya hadu, ango da amarya sunyi kyau kamar fure, sai walwali suke suna sheki. Ni'ima sai kaiwa da komowa take a matsayinta na babbar kawa, du inda tayi kuwa zaki ga idanuwan samari a kanta, saboda ni'ima ta zama budurwa kyanta ya kara fitowa, ga gwalli ga iyayi. Su masu sabis da aka dauka sunata kaiwa mutane abinci dasu swan, lemon kwali dana gwangwani. Jama'a suna cin abinci Ali jita ya saki kida, tuni zakin kidansa yasa jama'a suka fara kada kai. Amarya da ango suka shiga filin rawa, nan fa kawaye da abokan ango 'yan uwan amarya da 'yan uwan ango, aka shiga filin rawa aka rinka watsi da naira kamar ba a san zafin nema ba. Hankalin zainab ya tashi ganin har takwas na dare tayi, ta rinka damun ni'ima ta taho su tafi gida. Ni'ima tayi tsaki, waike meye hakane? Ki bari agama basa mu tafi ba. Zainab tace um-um yaya ni'ima, kinsan halin yaya, kizo mu tafi, ni'ima tace ke wallahi kin fiya matsala, saika ce wata matar aure, kita faman jin wannan tsoron, bafa abunda zaiyi miki. Tace um- um, nidai kizo mu tafi bana son bacin ran yaya, wallahi du saina ji na damu." dai- dai lokacin da Ali jita ya saki cashiyar karshe ni'ima ta riko hannun zainab suka fice suka shiga motarsu, direba ya kawo su gida. Saida aka sauke zainab sannan ya wuce da ni'ima gida. Yana zaune a falo yayi zaman nasa na kasaita kamar wani basarake, ya lumshe ido daga gani tunani yake yi, mansura tana kwance da littafi tana karatu, zainab tayi sallama ta shigo, mansura ta amsa sallamar tare da cewar "kun dawo? Tace mun dawo aunty." tace yaya sannu da gida." ya bude ido daya yace sai yanzu kuka ga damar dawowa? Bance ku dawo da wuri ba? Ta marairaice, "don Allah yaya kayi hakuri bazan sake ba." ya daga kai "shikenan tashi kije. Ta mike tana hamdala a ranta da abin yazo da sauki. Ranar littini da asuba Aliyu ya nufi kaduna bakin aikinsa, sai kuma ranar jumma'a da yamma zai dawo. Kwanci tashi asarar mai rai, cikin mansura ya shiga wata tara harda kwanaki, tana zama dakyar tashi da bisimillah. Ranar jumma'a da mangariba Aliyu ya iso, bai samu wata tarba ba, sai dai mansura ta langwabe masa bata da lafiya, sai kuka take yi masa. Shikoma du ya wani rikice, don shi kukan yaro ma baya so bare na babba. Ya kwasheta suka nufi asibiti, raki take yi da ihu tana murkususu acikin motar. Zainab kuwa sai hawaye take yi, tana cewa aunty kidaina ihu salati zakiyi. Tun a motar Aliyu yayi waya gidan su mansura da gidansu. Suna isa asibiti aka shigar da mansura dakin haihuwa, Aliyu yayi tagumi yana sauraron ikon Allah, yayinda zainab ta dukufar da kanta acikin gwiwarta tana kuka kasa-kasa. Tana tuna lokacin da suka kawo mamanta acikin irin wannan halin, wanda haihuwarce sanadiyar mutuwarta, 'yan gidan su mansura sun zo. Yart da kishiyar babarta. Can saiga ummi tazo, zainab ta tafi ta kankame ummi tana kuka, ummi ta rinka shafa kanta tana rarrashinta. Wani ihu da suka ji mansura tayi shine dai-dai da dan ya fado. Nurse din ta garzayo da gudu tazo ta kwantsama musu labarin haihuwa, tuni kowa ya washe baki ya daga hannu sama yana yiwa Allah godiya. Sun shiga dakin anata yiwa juna barka da yaba kyan yaron. Aliyu ya rungumeshi a jikinsa yana maiyi masa addu'a da fatan Allah ya raya shi. Washe gari da safe ka sallamesu kasancewar mai jego kalau da ita da babyn. Gidan ya cika da 'yan barka 'yan uwan Aliyu dana mansura. [1:24PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**14 GIDAN ya cika da 'yan barka 'yan uwan Aliyu da 'yan uwan mansura. Sadiya ta taho tinkis-tinkis dana ta tsohon cikin, ni'ima da zainab suka rungumota suna murnar ganinta. Dakin mai jego sai kamshi yake. Kowa yazo barka zainab ce zata karbeshi da farin cikinta, ta dakko masa jaririn. Ko yaushe yaro yana rungume ajikinta, kamar kada ta bawa kowa." ranar kwana hudu aka kawo kayan barka a katuwar akwati, kayan jariri ne tsala tsala masu kyau, da dan jeans da shet na yara, takalma, safofi, fidoji, saitin shawul da tawul, barguna masu laushi. Kaya ne masu kyau da tsari duk 'yan waje. Sai karamin akwati kayan mai jego ne, turmin super holllan biyu, leshi biyu, shadda galila mai tsadar guda daya, kowanne da mayafinsa, sai takalma da jaka kala bibbiyu. Ya bawa ni'ima da zainab da sadiya super holland biyu su uku, ya karawa zainab da galila anyi mata haddaden dinki aikin sama mai tsalelen kyau. Da mangariba Aliyu yana dakinsa, mansura ta shiga da jaririn, Aliyu ya karbeshi yana murmushi, sai shafashi yake yana murmushi. A zuciyarsa kuwa godiya yakewa ubangiji daya bashi kyautar da duk duniya babu wanda ya isa ya baka kyautar da sai Allah. Mansura tace Aliyu nazone akan maganan shirye-shiryen suna. Yace uhm! Me da me zaku yiyyi? "inaso da yamma ayi walima, da daddare mu fita fati a daula hotel, sai bokitai da manyan robobi da kalanda, du za'a rarraba a wajen. Yace za'ayi komai amma banda fati." ta wani harzuko, haba don Allah don Annabi, wallahi ka fiya yawa, ya zaka ce ba za'ayi fati ba, alhali ni inaso na burge saboda kawayena zamu kakko makadi don kawata fatin, kuma zaka kawo min matsala. Yace albarka nake nemarwa 'ya'yan, bana so su taso akan harkar shaidanci. Ta mike ta kama masifa, kai dai kawai kana so ka wulakantani a gaban kawaye na, haka wai haihuwar fari dan kwaya daya amma bazaka saki kudi ayi bushasha ba, don kasan bakai kasha wahalar haihuwan ba. Ya daga mata hannu yace, ya isheni haka fita ki bani waje." ta fito tana kunkuni tare da bakaken maganganu. Ya dafe kai don jin kansa yana sarawa, mansura zata haddasa masa ciwon kai, shi baya son hayaniya. Ta dawo daki tana kunkuni da fadar maganganunta. Saratu yayarta tace, meye kuma? Mansura tace kinji wai baza ayi fati da kida ba. Saratu tace, ai wannan wulakanci ne, ya mayar damu kananan mutane bayan ni har na buga kati na fara rabawa? Lawisa kawar mansura tace, kawai inba zai bari mu tafi ta nan ba, ba saiki ce masa zaki je kiyi sunan a can ba, inyaso da daddare muyi tafiyarmu fatin, ai mun riga munyi dai ai shikenan." saratu tace ita wallahi jeki ce masa zaki tafi gida zamuyi sunan acan. Mansura tace wallahi yace na fice na bashi waje, idan na koma nasan halin zuciyarsa, sai ya iya marina. Saratu tace tabdi ya mareki? Ai kuwa wallahi daya mari aurensa. Lawisa tace, tunda kuwa kika nuna kina jin tsoronsa kinsha wulakanci iri iri. Nan suka hadu sukaita aibata shi, suna fadar maganganu son ransu. Zainab kuwa ranta ya baci, kawai saita sa kuka. Saratu da lawisa suka hau yi mata masifa. Kinji yarinya da munafunci, dan uwanki yayi ba dai-dai ba zaki hanamu fadane munafuka? Kiyi kukan jini bana hawaye ba." zainab ta mike tayi dakinta tana kuka. Lawisa ta rike baki, tace ahaka kike zaune da wannan yarinya mai miskilancin tsiya, har wani kuka take don anfadi laifinsa. Mansura tace kuma wallahi baki ga yanda yake takura mata ba, ni har tausayi ma take ban, don inyana gari bata da sakewa" saratu tace "ai wani irin mutum ne, shiko fuska baya saki don kada akawo masa raini." ranar suna dole mansura ta hakura da maganar fati, akayi taron suna da yamma akayi walima ta burgewa da bajinta, mai jego sai shiga take tana fita tasa wannan ta cire tasa wancan ta cire. Yaro yaci suna Ahmad, sadiya da ni'ima da zainab, les din da Alh ya dinka musu suka saka, da yamma a wajen walima suka sa super ta wajen Aliyu. Can jimawa zainab ta canjo da shaddar da Aliyun ya dinka ma, sadiya tayi mata daurin gwagwaro akanta, tayi kyau, kamar ka saceta ka gudu. Sadiya da ni'ima sun cancanja shiga, suma dai shadda ce amma kalar ta kowa daban. Sadiya ta rinka raba kalanda mai hoton zainab tana dariya rungume da jariri, kaandar tayi kyau kowa ya karbi kalandar ya kalla saiya yaba da ita. Haka su saratu da lawisa su kaita raba robobi da 'yan kananan bokitai. Da haka taro ya tashi lfy, kowa yana san barka. Kayan barka da atamfofi data samu, da rigunan jarirai kamar wadda zata bude shago. Ba ruwanta kibarta kawai take yi, taci mai kyau tasha mai kyau, ta hau gado ta mimmike ba ruwanta da harkar Ahmed, yana wajen masu rainonshi su zasu hada masa madara su bashi yasha, su bashi ruwa, idan ya koshi su goya shi. Shan nononsa sai lokaci lokaci, saidai idan ta jiyo kukansa ta kirawo 'yan aikin nata ta balbalesu da masifa, mai suke yi masa yake kuka? Suyi ta faman rantse rantse cewar, wallahi basu yi masa komaiba, sannan zata karbeshi ta bashi nono, tasa su goya shi suyi ta faman jijjiga har sai yayi barci. [1:25PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**15 TASA su goya shi suyi ta faman jijjiga shi har sai yayi barci. Sai dai fa du sanda zainab ta dawo daga makaranta, tana yin sallah zata karbo ahmad daga wajen masu rainonsa, taita yi masa wasa tana tarairayarsa, tai tayiwa mansura naci da magiya dole saita karbe shi ta bashi nono ya sha ya koshi. Ahmad yayi wayo sosai, yayi mugun sabo da zainab, don har yafi ganeta akan mamanshi don zainab har ta iya yi masa wanka, ta shirya shi cikin kaya masu kyau, tasa mishi turare yaita kamshi. Har mansura taita sha'awarshi, abinda ita lalacinta da son jikinta bazai barta ta iya ba. Du da zainab din ba wani lokacine da ita ba, inta fita tun takwas na safe sai shidda na yamma take dawowa, idan sun taso data dawo gida inta ci abinci tayi sallah, tayi wanka tasa kayanta, saita dakko yaronta ahmad taita yi masa wasa tana lallabashi, har lokacin bacci ta kaiwa mansura shi ta bashi nono yasha ya koshi ta taho dashi dakinta ta kwantar dashi a gado, ta canja kayan barci tayi musu addu'a taja bargo ta rufe su, ta rungume ahmad a jikinta suyi barcinsu. Talatuwa data ke tayaa kwana idan ya farka cikin dare, ita zata dakko shi ta bashi madara da ruwa, tasa shi shi akafada ta jijjiga shi yayi gyatsa ya koma baccin shi, saita shimfida shi a gaban zainab ta rufe su. Itama ta koma baccinta du sanda Aliyu yazo weekend, yana kula da abinda yake faruwa da yaronshi da yake kokarin zama marayan karfi da yaji. Sun sha fada da mansura akan sakarwa masu aikin dansa data keyi. Yasha korota intaje kwana dakinshi, yace saita dakko mishi dansa. Saita rabu dashi ta tafi dakinta tayi kwanciyarta. A hankali ya fuskanci tsananin son da zainab take yiwa ahmad, ya gano zainab ce take kwana da ahmad ba yan aiki ba, sai ya samu nutsuwa a ransa, yayi wa Allah godiya, don yasan zainab tafi mansura tarbiya da sanin ya kamata, yasan danshi zai taso da tarbiya matukar yana tare da zeey autarsu. Yau asabar, Aliyu yana gida, zainab babu makarantar boko, wajen tara na safe tayi wa ahmad wanka a bahon shi, Aliyu yana kallonta yana yaba baiwar da Allah yayi wa yarinyar, 'yar da har yanzu bata cika shekara goma sha uku ba, amma tana da nisan hankali da tunani wanda 'yar shekara ashirin da biyar bata dashi, wato mansura. Ta gama yi masa wanka, ta nade shi a tawul tana yimi shi wakar data ke yi masa inyana rigima. Wayar falonce tayi kara, zainab ta daga tace "hello yaya ni'ima." daga can ni'ima tace yau ne fa yinin kawata murja sule, kizo da wuri muje." zainab tace don Allah yaya ni'ima kiyi hakuri, ba zan samu damar zuwaba." ni'iman tace saboda me? Zainab tace, yaya ni'ima wallahi ban tambayi yaya ba, kuma kinga yau nadan samu hutu ba boko, ina so na wuni da ahmadina, ba zan iya fita waje na barshi ba. Ni'ima tace kinfiya shirme zainab, ina uwarsa ko zaki zama mai rainonta ne? Ita ba unguwa take ficewa ta barshi ba, sai ke zaki zauna ki rinka yi mata wahala dashi? Tace "haba yaya ni'ima kada ki manta ahmad dana ne gudan jinina ne, don wallahi basu da maraba da abunda zan haifa, tunda dan yaya nane. Ina ruwana da halin uwarsa, tsarina daban nata daban. Kiyi hakuri wata rana na rakaki, kinji yaya ni'ima? Tace to shikenan auta, ba komai ki shafamin kan ahmad ki sumbace shi, kice masa inji momynshi." zainab tayi dariya tace, "to bar kiji ma nayi masa kafin ki kashe wayar." ta suabcin kumatun ahmad tace yarona momynka tace nayi maka, tana kuma gaisheka, inta dawo daga gidan biki zata zo ganinka." ta ajiye wayar tana dariya. Ta zauna ta gama gogewa Ahmad danshin jikinsa, ta shafa masa manshi, ta shafa mashi farar hoda, sannan ta daga wuyarsa da hammatarsa ta zazzaga masa, ta shafa masa kasan wuyansa da hammatarsa, tasa masa kwalli, tasa mai pampas, tasa masa farar ves, tasa masa safa da dan takalminsa, ta shafa masa turarensa. Shirin yaron yayi kyau, gashi yana ta kamshi. Ta dama mishi madararsa a fida daidai cikinsa, tasa masa abaki ya kama zuka, ya shanye tas, ta bashi dayan fidar mai ruwa a ciki ya sha, ta dora shi a kafadarta tana shafa bayanshi, yaron har yayi gaytsa. Ta dago shi tana yi masa wasa yana dariya, daga bayanta taji ance " bani yaron naki na taya ki raino." ta juyo da sauri tace "lah! Yaya yanzu ka shigo? Don ita kwakwata dazu bata ganshi ba, don ita inta na tar da Ahmad bata tunanin komai sai yanda zata kula da yaronta. Ta durkusa ta mikawa Aliyu shi, ta gaisar da Aliyun ta mike tayi dakinta itama ta shiga wanka. Tana fitowa ta goge jikinta da tawul, ta zauna gaban madubi tana kalkale jiki. Zainab tun tana karamarta 'yar iyayi ce da son kwalliya, gata da son kamshi, da kudinta ma sayan turaruka take yi bare yaya Aliyu yana sai mata, hakama Abbansu ko daddynsu suna bata. Ta tsara kwalliyarta cikin wani fine les mai fulawoyi, bashida nauyi, riga da siket ne filet, ta kafa daurin dan kwalinta daya kara fitowa da kyanta, ta fesa turaruka sai kamshi take zubawa. Ta fito falo har yanzu Aliyu yana zaune yana lallaba Ahmad da yayi barci, tace yaya yayi barci kawo shi naje na shimfede shi. Ta dan marairaice masa cikin shagwabarta tace.... Next episode by 6pm via #Justice_hamxat [1:26PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**16 TA DAN marairaice masa cikin shagwabarta, tace don Allah yaya kabarni naje gida. Yace meyasa kike so ki koyi karya ne, ba inaji ni'ima tayo miki waya zakuje gidan biki bane? Tayi kasa da murya cikin shagwaba tace, wallahi yaya ba gidan biki zanje ba, aina gaya mata bazan jeba, tunda ban gaya maka ba. Daman su hajiya zan kaiwa Amadina su ganshi." ya gyada kanshi, "kuje direba yana waje sai ya kai ku." tayi murmushi, yauwa yaya nagode." ya gyada kanshi ya jingina da kujera yana ta kallonta, tana ta hada fidar Ahmad ta ruwa data madara, da dan fulas dinshi na ruwan zafi, ta debo masa kaya kala biyu da pampas guda biyu ta zuba acikin jakar goyonshi. Wannan page ya dan samu matsala yayi baki kwanci tashi ba wuya, zainab ta zama budurwa, tana da shekara goma sha bakwai, yanzu tana aji shidda a sakandare. Zainab kyanta ya kara fitowa, tana da iyayi da kwainane, akwaita da tsabta dason gayu, don du wata saita je salon, bata gajiya da kunshin tafin kafanta ko zanen fulawa ta lalle. Ta fiya sanyi magana da marairaita; saiki zata sangarta ce da shagwaba tayi mata yawa. Idan tana magana mace ma burgeta take yi bare namiji, akwaita da iyayi da yauki da yanga. Abinda yafi fisgar maza da hura wutan sonta a ransu, inhar zata shiga waje saita samu maza masu sonta. Amma bata iya tsayawa ta sauraresu, domin tana tsoron yayanta, tana gudun abunda zai bata masa rai, bata so tayi masa laifi. Don waya ma ya hanata rikewa, sai wata rana data je gida Abba ya bata wata mai kyau, amma ta rinka dari-dari da tsoron gaya masa. Sai Ahmad ne ya dauka da gudu ya kai masa yana gaya masa Abbanshi ya bawa aunty maminshi waya. Saida ya mata gargadi sosai akan in ta sake yaji ta bawa wani saurayi numbar wayarta sai ranta yayi mummunan baci, don haka take kiyaye wa. Ni'ima anzama babbar budurwa sosai, tana karatun diploma har ansa mata ranar aure har ma ankusa bikin. Aunty sadiya tanada 'ya'ya biyu, hafiz da sajida. Mansura kuwa tun daga Ahmad bata sake haihuwa ba, tace dama saiya shekara biyar, toh gashi yanzu ya shekara biyar din. Zainab yarinya mai hakuri, ga hankali da nutsuwa, tana da kwazo, don tayi saukar qur'ani yanzu ta juya hadda. Yau asabar tana tasowa a daga islamiya ta ware kitson kanta tana son zuwa salon, harta fara tunanin ta yanda zata tambayi yayan nata fita, bata son yayi mata fada. Zainab tayi murmushi tace don Allah aunty gayawa yaya zanje salon. Tace "bazan je inda yake ba munyi fada." tace haba aunty, don Allah kije ki lallabashi ki bashi hakuri, ki tambayo min nidai na tafi. Ta tabe baki tace hakuri? Hakuri fa kika ce? Don ya kara wulakantani." zainab ta kalleta cikin mamaki, Ahmad ya fito da gudunshi da hijabin nata a hannunshi yana cewa "aunty mami gashi mu tafi kinji. Tace jeka gayawa Abbanka cewar zanje salon. Dai-dai lokacin Aliyu ya shigo, Ahmad yaje ya rike hannunshi yana gaya mishi "Abba inji aunty mami wai zamuje salon. Ya dago kai ya kalleta, "saida kika dauki mayafin tafiya sannan zakice a gayamin." ta durkusa cikin marairaice warta, tace don Allah yaya kayi hakuri, tun dazu nake jiran fitowarka, ba mayafin tafiya nadauka ba." ya gyada kanshi kuje Allah kiyaye. Tace yaya na gode. Ya bawa Ahmad kudin salon din, suka tafi direba yakaisu. Suna yin fakin a gaban shagon salon din, suna fitowa daga kanta da zata yi karaf idanuwanta suka hade dana wani dan kyakyawan saurayi daya zuba mata ido, tayi saurin kawar da kanta, taja hannun Ahmad suka shiga ciki, a gurin suka wanke mata kai suka gyara mata shi, suka yanke mata farce, suka goge mata kafa, du da karfa tata sumul take kamar ta jarirai. Ta fito da youghot da biski ta bawa Ahmad don kada yaji yunwa. akayi mata kunshi kunshi sarka a hannu da kafa, nan da nan ta canja ta kara yin kyau kamar tauraruwa. Tana fitowa daga wajen idanunsu suka sake haduwa, yayi mata murmushi ta dauke kanta da sauri, ya taso ya tari gabanta. Yace "don Allah ki taimakamin ki saurareni ki gaya min inda gidanku yake nazo na sameki a gida." ta mika masa katin yayanta, tayi saurin shigewa motar direba yaja suka tafi. Saurayin nan ya sumbaci katin data bashi yana mai jin dadi da farin ciki haduwarsa da wannan beb din. Suna tafe tana tunanin saurayin data gani, gaskiya ya hadu, itace da tsayawa yau harda bawa saurayi katin yayanta, wyarta ce tes ya shigo, tayi mamakin waya turo mata tes. To kodai ni'ima ce? Ta bude tes din, bakuwar lambace bata san mai lambar ba, ta fara karanta sakon kamar haka. "i 've been lucking 4 a chance to tell u my message, i luv u." mamaki ya kamata bata ankara ba ta kuma jin shigowar wani sakon, ta bude ta fara karantawa. This secret has been in my heart enough now i want to make it. Ta bude dayar da suka shigo tare, i told you that i want u to be my wife" a'a wannan wane irin kalamomi ne masu rikitar da zuciya, waye wannan? Ta sake dubawa ta maimaita karantasu gaba daya. Ba suna to waye wannan? Ita dai tasan ba wanda suka hadu dazu bane, donshi bata bashi lambar wayarta ba. Kuma tasan ba wani namiji data bawa lambar wayarta, to ko waye? Next episode by 9pm via #Justice_hamzat [1:26PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**17 Har suka karaso gida zuciyarta tana cike da tunane-tunane, waye wannan? Meyasa ya boye mata kanshi bai fadi sunanshi ba? Ahmad yayi barci, ta saboshi akafada ta kwantar dashi kan kujera. Mansura ta kalleta tace ammafa kinyi kyau, saide kin dade." ta zauna tace "hum! Kedai ki bari aunty, saurayi fa nayi a wajen, kuma harna bashi katin gidan nan, ina tsoro kuma kada yazo yaya yayi min fada. Mansura tace a haba wane irin fada kuma? Ai yanzu kin wuce wannan ajin. Don ma keba wayayyi bace kanki a duhu yake, amma yanda kike kyakyawar nan gaki danyar budurwa shine dai-dai fara wankar samari, toke sai rashin waye wa, kullum kina like a gida, idan zaki fita ki zurma hijabi saika ce gyatuma. Don Allah ki waye. Tace, to aunty wai ya kike so nayi ne, wace iri ne ce wayewar? Haka dai ta ringa ce mata tanasa matsatsun dinki ita kuma zainab tace ba haka Allah yace ba, ka waye akan addininka shine wayewa, aunty sadiya ce ta shigo da sallama da kanwar mijinta yasira, a'a auntyn mu barka da zuwa. Zainab taje ta rungumeta, tace yasira rabon goron harda aunty kuke yi ne? Tayi dariya tace to ya zanyi tace da ita za'a kawowa zeey autarsu na fati. Zainab tace fati yasira, anya zan dai zo miki yini, yaya bazai barni naje miki fati ba. Sadiya tace haba don Allah, ke bari zakiyi yasan zakije? Kice masa gidana zaki zo, ni'ima ma nan zata zo saimu tafi tare, nayi muku ankon fati da gwagwaronsa, harda takalmi set din kayan." zainab tasa ihu, "sai auntyn mu, kedai kina son fito da 'yan kannenki. A to inbanyi muku ba wa zanyi wa, ku kenan fa kannen nawa mata, ai dole na gyaraku. Mansura tace, "ai wannan autar taku saikin dage mata don taki wayewa, kullum kanta a duhu yake. Sadiya tana dariya tace ai laifin mijinki ne, bakina kallo yke takura mana auta ba, ki rinka hanashi kin barin ta da yake ta sake. Mansura ta kama baki tace rufamin asiri da yayanku, idan nayi magana tawa ce take yin zafi, ranar jumma'a wato ranar fatin, mansura ta shigo dakin zainab tace, "bazaki je ki fada masa maganar fatin ba saiya fito? Tace don Allah aunty gaya masa." tace kinsan in ni na gaya masa cewa zaiyi inason koya miki yawo. Ta mike bari naje, aunty kiyi min addu'a Allah yasa ya barni." tace "to Amin." yana shirin fita mansura ta kawo masa jakarsa, zainab ta fito ta durkusa tace "yayana. Bai kulata ba yace "uhm! Ya akayi? Yaya dan Allah zanje gidan aunty sadiya? Me akeyi a gidan? Bikin kanwar mijinta ake yasira, shine nake neman alfarma dan Allah yaya kabarni naje. Ya daga kai kada ki dade. Tace to yaya nagode." yana fita ta tafi gidan sadiya, direba ya kaita. A can ta tarar da ni'ima suka rugume juna suna murna. Kinyi sa'a 'yar uwa ya barki." kinganni dai, yayan namu ne sai a hankali. Amma yau ba laifi fuskar tasa a sake take. Hu! Aunty wannan material din fa? Tana daga su tana yaba kyansu. Tace Abban yasir ne ya kawomin su tsaraba, amma naga sun zo akaya zan sai muku. Yauwa auntyn mu kina burgemu fa. Suka gama tsra shirinsu na zuwa fati, wani hadadden material ne da aka sake fito da kyansa da wani dinki mai kyau. Gaba daya su ukun sunyi kyau amma ba kamar zeey da kamar don ita aka yoshi. Suna bayan motar sadiya da mijinta suna gaba. A gidan fatin suka bi bayan amarya da ango suka rakata har mazauninta. Yaron sa'adu bori yanata kida da waka 'yan mata sunata rawa daga baya aka tsaya da kidan, babban kawar amarya tazo ta yi addu'a tareda yiwa bakin da suka zo barka da zuwa. Daga nan ango da marya suka tashi suka ja zugar kawaye da abokai suna biye da bayansu har wajen masu sabis. Kowa shiyake sabis din kansa. Zainab duk inda tyi idon mutane ne akanta, ita kallon ya isheta, don bata saba da irin wannan shiga ba, ta saba kullum tana hijabi, to ita abunda yafi damunta ma sha daya har tayi, tana jin soron yaya fa. Amma yaya sadiya da mijinta sunce har dakinta zasu rakata su bawa yaya hakuri.. Wata kawarta tazo taja hannunta, dole saita yi rawa. A hankali take juyawa, kusan maza hudu ne suka rufa kanta suna mata liki. Kamar daga sama yaya Aliyu ya diro wajen, saiji tayi an damki hannunta. Ta juyo a tsorace dan ta razana, ganin yayanta ya hade rai kamar wanda bai taba dariya, saita firgice ta tsorata. Ya funciki hannunta yayi waje da ita, ya bude mota ya turata ciki shima ya shiga. Ta takure a tsorace take, saboda tasan halin yayanta sarai, akwai zafin zuciya. Aliyu ransa ya baci sosai ganin maza suna yiwa zainab liki, ba dai sonta suke yi ba? Wani abu ya soki kirjinsa, ya rinka ganin bibbiyu a idonsa, yayin da motar ta fara tangal-tangal kamar zata kifa. Zainab ta fara salati ta baro kujerarta ta rungume Aliyu tana ihu tana salati. Tirkashi! Mu hadu a littafi na biyu, waishin menene ya soki zuciyar Aliyu? via #Justice_Hamzat [9:14AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**1 & 2**2 A hankali ya dawo hayyacinsa, yaci gaba da maimaita salatin daya ji zainab tanayi. Saida taji ya samu nutsuwa sannan itama tafita daga tsoron data shiga, tayi saurin komawa wajenta. Yaci gaba da tukin a hankali cikin nutsuwa, zainab ta fashe da kuka tace, "don Allah yaya kayi hakuri bazan kuma ba. Don Allah ka yafe min." da kyar ya iya bude bakinsa yace, zainab meya hadaki da wa 'yannan maza da suka rufu suna yi miki liki? Tace "wallahi yaya ban san su ba, ban taba ganinsu ba sai yau. Kuma ko magana bata hadamu dasu ba, wallahi ina zaune wata kawata tajani gurin rawar, kawai sai gani nayi anamin liki. Kayi hakuri kaji yaya bazan kuma ba. Ya daga kai, yace shikenan ya wuce." da sassafe aunty sadiya tayo mata waya tana tambayarta, "ince kodai yaya bai dake kiba? Tace baiyi min komaiba." ta bata labarin abunda ya faru, suka yi dariya gaba daya. Bayan sun gama hirarsu, ni'ima ta bugo ta tambayi abunda yaya yayi mata. Itama ta bata labarn yanda suka yi. Ni'ima tace, "dadina da yaya akwai zafin zuciya, amma inka bashi hakuri shikenan komai ya wuce. ** ** ** ** *** ni'ima ce ta shigo, suka rungume juna, suka zauna talatuwa ta shigo musu da abinci, ni'ima tace, aunty sadiya fa tace muje goben ta sai mana material din, kala uku ta dibar mana. Zainab tace sai auntynmu, gaskiya mun gode, kawai daga can sai mu wuce gurin dinki. Ni'ima tace daman mama ma zata karba mana kudin dinki awajen Abba." ta mike, tafiya zanyi." haba yaya ni'ima tun yanzu? Wallahi inkin zo bana so ki tafi." ta dafa kafadarta, kiyi hakuri zainab, na baro yaya a gida, kinsan yanzu zai taho, idan ya sameni anan, gobe inkin tambaye shi zuwa gidan aunty sadiya cewa zaiy ni nake zuwa nake saki yawo. To shikenan yaya ni'ima sai goben." sha biyun dare ta tashi tayi na filla, tai ta addu'o'inta tayiwa mahaifiyarta addu'a tare da mahaifinta, da fatan Allah ya bashi zaman lafiya da matar da ya sake aura. Ta gama shirinta, ta gama tofa addu'o'inta ta kwanta, taja bargonta zata rufa. Yayinda ta jawo wayarta zata kashe, dai-dai lokacin da zata kashe, sakkonni suka shigo. Mamaki ya sake kamata, ta fara budewa ga abunda yake ciki. "wah! Zeeytah tsananin sonki da kaunarki kullum yakan hanani bacci. Zeeytah yaushe zaki ban dama na bayyana gareki, na matsu na aureki. Na jini manne a kirjinki ina bacci kona ji sauki da radadin sonki. Wayyo zeey kece rayuwata." subhanallahi, waye wannan? Na shiga uku! Allah yasa dai ba aljani bane. Ta sake bude sakon ga yanda yake. "zeeytah kaunarki takai makura a zuciyata, dab nake da rasa rayuwa saboda zugin sonki. Wai yaushe mafarkina zai zamo gaskiyane? Na jiki kan kirjina ina lallaminki ina riritaki, na dameki da soyayyata mai hanani bacci. Ta cillar da wayan tana cewa na shiga uku! Waye wannan? Waya ke son rikitamin zuciya? Mutumne ko aljan? Allah gani gareka, Allah ka kawomin sauki. Dakyar tunani ya barta tayi barci. Ranar alhamis da yamma bakonta yazo, saurayin da suka hadu a kofar wajen salon. Ahmad ne ya shigo da gudunsa yana cewa, "aunty mami kizo inji wani dan gayu a mota mai kyau. Tace "dan gayu a mota mai kyau? Yace ka kirawo ni? Eh, aunty mami, yace nace wai mutumin da muka hadu dashi ranan." mansura tace mutumin da kikace kin bawa katine. Saiga talatuwa ta shigo tana dariya, tace "don Allah aunty mami. Yanda Ahmad yake gaya mata, tace don Allah yau dai kije kada ki kori wannan, ki taimaka kije. Mansura tace kai mata kujera farare guda biyu harabar gida, yanzu zata zo. Mansura tace kije ki shirya, ba kyau fa wulakanci." ta mike ta shiga dakinta ta sako hijabinta ta fito. Mansura ta kalleta tayi tsaki, meye haka? Yanzu zance ma saida hijabi zakije? Wallahi kedai gidahuma ce kije ki yafo karamin mayafi." tace don Allah aunty ki kyaleni, yaushe zanje gaban wani kato da dan karamin mayafi ya karewa halitta na kallo ya cuce ni? Mansura tace saiki tayi 'yar kauye kawai." tayi murmushi ta wuce ta tafi harabar gidan. Yana zaune akan kujera, ya rinka sakin murmushi dan yaga ta taho gareshi. Ta zauna tace barka da zuwa." ya amsa "yauwa zainab ya gida, kun dawo? Ta amsa da "lafiya lau. Yace "to dama gaskiyar abunda yake tafe dani, na ganki kuma gaskiya naji ina sonki, ina kaunarki, ina matukar son na aureki. Shiyasa nake neman amincewarki, daki amince ki aureni dan mu zamo abokanan rayuwan juna nan gaba." tace mishi, bakomai Allah ya zaba mana mafi Alkahiri. Yace Amin. Kin amince naci gaba da zuwa kenan? Ta daga masa kai. Yace naji dadi, ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkahairi." talatuwa ta kawo mishi ruwa da lemo, zainab ta zuba masa ruwa da lemon a kofuna, tace masa bisimillah mana, kasha." ya dauka yana sha suna ci gaba da hirarsu, yayi mata bayanin kansa. "nidan garin nan ne, muna zaune a unguwar gandu. Mahaifina Alh sani yana da mata biyu da 'ya'ya tara, nine na uku a gidanmu sunana nura. Nayi karatu na firame da sakandare a garin nan, inda nayi jami'a a dubai. Ina kan harkokin mahaifina na bangaren kamfanin motoci." ta jinjina kai, tace naji labarinka, Allah yayi mana jagoranci na Alheri. ALLAH yayi mana jagoranci na Alheri, sukayi sallama zai tafi ya bata rafar kudi taki karba. Yaita mata magiya data karba, tace don Allah yayi. Hakuri bazata karba ba. Ta wuce gida. Tes ne ya kuma shigowa wayarta, ta bude ta karanta kamar haka. " i luv u zeey, luv is like d music of the nature the note 're heard by the loving heart that is tender nd pure, i care 4 u, i miss u, na i luv u." ina sonki, ina sonki, na dade cikin sonki. Ki soni zeey shine samun kwanciyar hankalina. Zeey yaushe zaki amince dani na bayyana gareki." ranta ya kuma dagulewa, wai waye wannan ne yake damunta da kalamai? Maye nufinsa? Ta mayar masa da amsa kamar haka. "dan Allah waye kai? Me kake nufi da rayuwata? Don me zaka boyemin kanka? Nifa marainiyace dan Allah ka rabu dani kada ka cuci rayuwata. Tana tura tes din mintuna biyu da tafiya waya ta shigo ta kama ringin, tana dubawa lambar da ake yo mata tes da itace. Tsoro da fargaba suka kamata, ta kasa daga wayar harta katse. Aka sake bugowa ta sake katsewa, sai akaro na uku sannan ta iya dagawa, muryanta can kasan makogoro tace hello! Wake magana? Cikin taushin murya da kyakyawan lafazi yace, "salamu alaiki ya hasken ruhina. Sanin muhimmacin sallama shiyasa ta amsa, amma a zuciyarta tana cike da tsoro da fargaba. Ya ce, "haba zeey, kada ki taba mugun tunani akaina, zainab ni masoyinki ne na usuli mai burin gina miki ingantacciyar rayuwa. Zeey ta na dade cikin tafarkin kaunarki, tun kina kankanuwa zainab Allah ya jarabceni da azababbiyar sonki. Zainab ki amince da soyayyana kona samu dadadden burina ya tabbata, wato ya zamo na aureki." to waye kai? Aina kake? Ya sunanka? "to ni sunana haidar, kuma ni haifaffen garin nan ne, sai dai aikina daya sa bana zaune anan din dindindin." to taya akai ka sanni, kuma waya baka lambar waya ta? to nasanki ne idan nazo garin ina ganin sanda ake wucewa dake a mota zuwa makaranta da safe, ina ganin sanda direbaku yake daukoki shidda na yamma. Lambar wayarki kuma wata rana na tsaya zan sai kati a wajen wani me dan kes din katuna waya da wayoyi, saina ga wata mata, ina ganin mai aikinku ce tazo da wayarki wajen. Saina ji tace bari taje ta dawo kafin yasa mata katin. To tanan na samu dama na dauki lambarki. Shikenan bayanin da kike sonji? Tace a'a meyasa ba zaka fito na gankaba kake yomin tes? Yace haba zeey ina yo miki tes ne danki san dani kada nazo miki gaba gadi ba tare da saninki ba, shiyasa nake yo miki tes dan nasamu amincewarki tukunna kafin nazo. Da fatan kin gane? tace na gane. Sannu a hankali soyayya da shakuwa ta shiga tsakaninsu, don yanzu zainab ta saba da soyayyarsa, sai sukai sha biyu na dare suna hirar soyayya, amma har yau basu ga junansu ba, daga waya sai tes ke hadasu. Saidai har yau ta kasa gayawa yayanta Aliyu maganan saurayinta haidar da yake neman amincewarsa daya fara zuwa zance wajenta, sai dai har yanzu suna tare da saurayinta nura, du sati ranar Alhamis yake zuwa wajenta, basu taba haduwa da yayanta Aliyu ba. Yau ma nura ne yazo, ta fita harabar gidan, yana zaune kan farar kujera da tebur fari zagaye a gabanshi, dayar kujerar tana kallonshi. Zainab tayi masa sallama ya amsa da fara'arsa, taja kujera ta zauna suka gaisa fara tambayar ya bayan rabuwa. Talatuwa ta kawo masa lemo da cin-cin da meatfay yana ci yana yi mata hira, har yanzu bata wani sakewa dashi ba, amsarta daga um sai a'a sai dai kuma tayi murmurshi. Wayarta tayi kara tana dubawa tayi ta amsa da hello! Mazaje ya akayi ne? Zeey ta inakan hanya yau na taho gida, na gaji da tunaninki, inaso zan zo muga juna." kai amma fa naji dadi mazan jiya." yauwa zeeytah, nagode, shigowar safe zan miki dan ki ganni sosai." bakwai da rabi zanzo gidanku, nizan kaiki makaranta muna tafe muna hirarmu mai dadi, na jira tunda jumma'a ce ba dadewa ba zakuyi a tasoku, mu sake tahowa tare muzo gida mu wuni muna hirar soyayya." Allah mazan jiya? Allah zeeyta, saina iso. Ok mazaje, bey." nura ya kalleta yace dama kina hira haka? Ko donni bakya sona ne, naji har sunaye kika rada masa mazaje dan mazan jiya. Tayi murmushi tace ba haka bane, bazan iya fadar sunan sa bane saboda sunasu daya da yayana, shiyasa nake ce masa mazaje. Inace masa mazan jiya ne saboda yanayin aikinsa. Ta tsiyayo lemo ta miko masa ungo yi hakuri karbi kasha. Yace saidai ki bani abaki in kina so nasha. Tace "a gaskiya baza iyaba, ka karba kasha da hannunka kawai." ta miko mishi. Shikuma ya kawo baki yana so ya kurbi lemon. Dai-dai lokacin Aliyu ya shigo get din gidan idonsa ya gano mashi. Yayi wani irin kogi da motar. Tsoro yasa zainab ta saki kofin lemo ya fadi. Aliyu ya bude motar ya fito kamar namijin zaki, ransa abace fuskarshi a daure kamar bai taba dariya ba, da kakinsa ajikinsa na soja ajikinsa. Yana taku cikin kasaita ya nufo inda suke, tuni zainab ta hankade tebir din gabanta tayi cikin gida a guje. Cikin kakkausar murya ya nunawa nura dan yatsa yace "waya baka iznin kula kanwata? Zoka fice kada na sake ganinka da ita. Zoka fice. Nura yana so yayi masa bayani ya daka masa tsawa tareda [9:14AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**3 & 2**4 NURA yaba so yayi masa bayani ya daka masa tswa tare da nuna masa kofa, da sauri nura ya fice ya shiga motarsa yaja. A fusace ya shiga gidan, zainab duta gigice ta rukunkume mansura tana cewa "aunty ki ceceni, ki ceceni aunty. Mansura tana ta tambayarta meye? Ta kasa gaya mata saboda rudewa da gigita da take ciki. Cikin takunsa ya shigo, ta saki mansura tai daki da gudu ta turo kofar, da kafa ya daki kofar dakin ta bude, ya zari wayar radio, ta rude, tana bashi hakuri yace "uban waye ya baki iznin zance da wani? Harda bashi lemo a baki. Dama abunda kikeyi kenan in ba na nan? Ya tsula mata wayar, ta gigice ta rukukume mansura. Mansura ta tareshi tana masa magiya yayi hakuri. Ya hankade ta, yace ina nan zuwa kanki, zaki san kinsata zance. Mansura tayi saurin barin gurin danta san halinsa. Ya sake tsulawa zainab, ta rukunkumeshi tana ihu, "don Allah yaya kayi hakuri, wallahi bazan sake ba kaji yaya, kayi hakuri yayana, wallahi dukan da zafi. Allah zankiyaye bazan sake ba." ya cillar da wayan, tayi saurin cikashi, yayi dakinsa. Zainab ta zauna tana kuka. Mansura ta dagota tayi dakinta da'ita tana rarrashinta. Wallahi bansan zai dawo yau ba, shida baya dawowa sai jumma'a da mangariba, to me ya kawoshi gida yau Alhamis? Ya kwalawa mansura kira, ta fito da saurinta. Ya rinka gaya mata maganganu, yaci mata mutunci. Yace wallahi wannan shine na karshe, du sanda ta sake barinta ta fita zance wajen wani sai ranta yayi mummunan baci. Ya fice ya bar gidan, mansura tace, masifaffe, kada ka barta tayi zance ta samu mijin aure, saika kwadantata kaci." zainab tana daki tana sheshekar kukanta taji wayanta na ringing. Ta duba, saita daga tace hello! Mazaje. Yace a'a zeeyta yana ji haka? Du yanda akayi akwai damuwa, gaya min zeeyta meyake faruwa? Cikin sanyinta tace lafiya lau mazan jiya ba komai. A'a daga jin muryar nan ba kalau ba, bazan iya hakurin zuwa gobenba, bari yanzu nazo naji ko meye." tayi saurin cewa a'a mazaje kada kazo ka bari tukunna saina gayawa yayana. Haba zeeyta ki bari nazo mana muga juna, yanzu du donki da nake bazaki bari nazo ba? Tace, "kabari sai wani lokacin. Yace don bakya sona baki damu dani bako? Ya kashe wayar tasa. Ta dafe kanta, "ya Allah sharrin soyayyar kenan, da da bata kula kowa tayi zamanta lafiya, yanzu kuwa daka fara soyayyar tata gashi ta fara cin karo da matsaloli." ita dai gaskiya tana son haidar, don bata taba ganinshi ba amma yanda take jin muryarsa da lafazinsa tasan cikakken mutum ne me mutunci da kamala baza taso ace ta rabu dashi ba dan bata san wa zata hadu dashi agaba ba. Ta dauki wayarta ta buga masa, ringin daya ya dauka, yayi shiru. Cikin sanyinta da marairaita tace "mazaje fushi kake yi? Yayi mata shiru cikin shagwaba tace, "mazan jiya, kada kayi fushi dani, baka sani bane wallahi ina cikin matsala shiyasa." cikin sanyi rai yayi ajiyar zuciya, yace wacce irin matsalace? Ki gaya min mana." dazu yayana yazo ya sameni ina zance, baka ga yanda ransa ya baci ba. Yaita mana fada nida aunty na. To idan kazo ya ganka kaga bansan abunda zai kuma faruwa ba. Wallahi bana so naga ran yaya abace, ballantana kuma ace nina bata masa, wallahi raina yaki dadi duk nadamu da fushin da ya keyi, don ni yaya shine uwata. Haidar yace gaskiyane na gane, tunda ina sonki dole na tayaki biyayya ga iyayenki da 'yan uwanki, zan nemi yayan naki na gaya masa ina sonki, ina so ya amincemin na fara zuwa zance gurinki kina ganin hakan yayi? Tace, yauwa mazaje nagode. Yace kada ki damu na gaya miki, i care 4 u, i miss u, i luv u." tace, "nima haka" tayi saurin kashe wayar tana dariya. Shima daga can dariyar yayi yana mai farin ciki yanda ya samu karbu awajen yarinyar. Sai goma na dare sannan Aliyu ya koma gida, yana zaune a falo, Ahmad yazo ya zauna a jikinsa yana dan lallbashi har yayi bacci. Mansura tana jin shi bata fito ba, ita a dole fushi takeyi akan fadan da yayi mata akan zainab. Zainab tana sanye da kayan bacci kwance akan gado ta kasa bacci, tunaninta yana kan yayanta da yake fushi da ita. Ta mike ta daura zani tasa hijabinta akanta, ta rufe jikinta. Ta bude dakinta ta fita falon, tayi sallama cikin sanyinta da yanayi na tausayi aciki, ya amsa sallamar, ta zauna akasa kusa da kafarshi, tace yaya don Allah kayi hakuri, Allah ya huci zuciyarka, don Allah yaya ka yafe min bata maka danayi. Yace, zainab kin batamin rai, daman inba na nan zance kikeyi? Meyasa kike kula samari? Don Allah kayi hakuri yaya bazan kuma ba. Yace, "gaya min da mutum nawa kike yin zance. Wallahi yaya shikadai ne yake zuwa." to kuma suwa kike waya dasu? Wallahi yaya shima shikadai ne." gaya min sunansa? Tayi murmushi sunkuyar da kai. Yace kina sonshi? Ta rufe idonta bata ce komaiba. Yace "nida burina naga kinyi digiri, ashe hakan bazata samu ba, samari bazasu barki kiyi karatu ba, ko auren za ayi ne? Yace ga maganin na dauki kisha kada jikinki yayi ciwo. Tace to yaya nagode. Ta dauka tayi dakinta. Ya bita da kallo yana kissima abu a zuciyarshi, yayi murmushi ya lumshe ido yana tunani abunda yake tabo ranshi. A daure ayi like da comments don hakan ke kara mana kwarin gwiwa ZAINAB sunyi candy, ita dai bata samu hutu ba ta fada kacaniyar bikin ni'ima. Ranar Alhamis akayi kamu, kuma dije ya cashe musu da kida, ranar zainab ta ajiye ustazancinta tasha rawa. Da daddare yunwa ta isheta, gata ba gwanar cin abinci, daman ga abun ya hade ma da hidimar biki. Tana cikin kawayen ni'ima da zasuyi kwanan biki anata hira da ita, kowa sonta yake yi, suna son hira da ita, don sha'awa take basu. Gata fara kal kyakyawa, gata da fara'a ga ladabi, don kowacce aunty take ce mata. Tace yaya ni'ima nifa yunwa nake ji." tace baga tuwon shinkafa ba da zafinsa? Tace tuwo yaya ni'ima, ai ba zan iya ci ba." ta dauki wayarta ta buga, "hello, yayana yunwa nakeji." ya hauta da fada, "don me zaki zauna da yunwa? Cikin shagwaba tace, "to yaya su basuda komai sai tuwo." mintuna kadan sai gashi a gidan da youghot da ice-cream, da kaji uku manya ya kawo mata. Ta bude tana ci, ni'ima tace 'yar gatan yaya kenan." sakina cikin kawayen ni'ima tace, yarinyar nan kinaji da gata, irin wannan cima da kikeyi dole kiyi ta faman kyalli, baki da matsala." zainab tayi dariyarta mai ban sha'awa tace, yayana ai shine babata, baya barina cikin damuwa, suna cin nama da youghot da ice-cream tana basu labarin yayanta da yanda take tsoron shi da gudun bacin ransa. Da safe ta shiga gurin babanta ya bata rubutun tsari da magani a dame da kindirmo, da tsumi da zuma. Tun tana 'yar shekara sha uku babanta yake tsumata da magani, shi tausayinta yake ji, yana ganin tunda ta rasa uwa ba mai kula da ita ta wannan bangaren. Kullum addu'arsa Alah ya bata miji na gari wanda zai kula da ita, ya tallafi maraicinta. Washe gari suka tafi gyaran amare, akayi musu dilka da halwa, jikinsu ya rinka tsantsi da sheki. Suna gidan kunshi haidar yayo mata waya, "hello mazaje ya akayi ne? Nifa na matsu zeeytah so nake kawai na aureki, zainab kaunarki tayi min yawa, zainab yaushe zamu hadune? Yaushe zamu ga juna? Karka damu mazan jiya gobe kazo daurin auren yayata saimu ga juna." yauwa zeeytah zan zo miki cikin farar shadda da bakar dara, da farin takalmi. Zansa babbar riga, zansa farin agogo na azurfa da farin gilas. Tara da rabi zanzo, sannan saura rabin awa a daura auren kenan, tunda goma za a daura. To naji dadi wallahi sai goben. Ranar daurin aure zainab tagama tsara kwalliyarta cikin wata dakakkiyar shadda mai tsadar gaske da yayanta yayi mata biki, ta nada dan kwalin kamar nadin gwaggwaro, tayi kyau sosai. Haidar yayo mata waya cewar ya iso yana dakin saukar baki na gidansu, ta kara feshe jikinta da turare ta fice tayi dakin baki. Tayi sallama cikin sanyinta, ta hango bayanshi cikakken mutum mai zati dakyan kira, irin mazan nan masu wahalar samu. Kamar yanda ya gaya mata zaiyi shigarsa haka ta gani. Tayi sallama tare da cewa hello, haidar barka da zuwa. Yana juyowa hanjin cikinta ya hautsina, nan da nan ta dabarbarce ta nemi nutsuwarta ta rasa, bakinta ya dabarbarce. Dakyar ta iya hada sunansa ta fada, tace, yaya Aliyu!" ta juya cikin gida aguje ta fada daki tasa kuka tana jimamin meyake shirin faruwa da ita? Karfe goma dai-dai taji an daura auren ni'ima da hamza saurayinta. Dai-dai lokacin da aka sake daura auren Aliyu da zainab. Zainab bata karasa jiba ta yanke jiki ta fadi, inda mansura ta sheko da gudu dakin data ga zainab ta shiga tana cewa, "ni zaku yaudara ku ciwa Amana? Yau zainab koni ko ke, saina kasheki nayi maganin maciya amana." inda ta shaki zainab. Zainab ta rinka kakari. Sadiya da ni'ima suka yo dakin da gudu, suka cakumi mansura suka cillar da ita gefe suna cewa, ke kada kiyi mana hauka, 'yar uwar tamu zaki shaka kina kokarin kashewa? Umma ta shigo a guje ta dago zainab ta rungumeta tayi dakin da ita. Mansura ta rinka zage-zage, "ni za ayiwa rashin mutunci da tozarta na rike yarinya tun tana 'yar shekara takwas, sirrina babu wanda bata saniba, na riketa kamar 'yar cikina, amma cin amanar da zai biyo baya kenan ku aurawa mijina ita? Ta rinka deban kayan wajen tana watsi dasu. Sadiya tace mudai kiyi mana shiru kada ki bata mana taro." ta kawowa sadiya duka, mutane suka tare suna bata hakuri, amma tijara take tana zuba ruwan rashin mutunci. Saida ummi tayi waya gidansu babarta da yayarta suka shigo suna tambayar meya faru? Mansura ta fada jikin babarta tana kuka, tana cewa hajiya kinga abunda suka yi min, kina kallon irin sakayyar da sukayi min, du kyakyawan rikon dana ma zainab yau sunga ta mike ta zama mutum, shine suka aurawa Aliyu ita." ta karasa tana kuka. Hajiya da saratu suka saka salati tare da cewar, amma Aliyu da zainab sunci amanarki sun tozarta ki, sun wulakantaki, amma kansu sukayi wa, yanda sukayi miki Allah ya tozartasu, taho mu tafi, aure ne bakya yi su rike dansu. Bayan zainab su kara aura masa mata uku su zama hudu. Daman munafunci daya sa aka kai miki zainab din don ta gama ganin sirrin gidan, ta riketa Amana tamkar uwarta, amma sakayyar da zakuyi mata kenan. Don kanku ku rike Aliyu, Allah ya bata wanda ya fishi, suka jata suka nufi nasu gidan sunata sababi. Tofa Littafi ya canja salo [9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**5 & 2**6 SUKUWA maza 'yan daurin aure, ana gama daurin aure suka nufu daula hotel, don cin abincin daurin aure, wato walima ta zama kadai 'yan daurin aure. Aliyu ba abunda ya dame shi sai washe baki yake, yana ta gaisawa da mutane. Da yawa mutane sunata mamaki, don sun san miskilanci da rashin yawan dariya irin na Aliyu, amma yanzu ya kasa rufe bakinsa saboda fara'a da amsa gaisuwar jama'a da masu sanyawa auren nasu albarka. Cikin gida kuw, masu gidan yaransu da manyansu cikin farin ciki suke da wannan aure na Aliyu da zainab, saboda kawunan su a hade yake. Su sadiya dasu ni'ima kuwa sai murna suke suna zuba shewa da tafi. Zainab kuwa tana dakin umma kudundune cikin bacin rai, duniyar tayi mata zafi, ta rasa mai yake mata dadi. Ita bata ga laifin auntyn ta ba, dole tace taci amanarta. Mai auntyn ta rage ta dashi? Ta dauketa kamar 'yar cikinta, amma yau sakayyar da zata yi mata kenan ta aure mata miji? Ta sake fashewa da kuka. Meyasa haka? Meyasa yaya Aliyu mata haka? Tana ganin yaya Aliyu mai rikon gaskiya da amana, ashe shima zai iyabin son zuciyarsa. Ya aureta yaci amanar matarsa? Wayyo ni Allah! Kaico da wannan rayuwar, ranta ya rinka kuna, makogwaronta ya rinka daci, ta rinka jin wani yuuu a kanta. Ta dafe kan tana jin wani sara mata da yake yi, wasu duhu suka gifta ta idonta, idanuwanta suka rufe tayi baya ta fadi numfashinta ya dauke. Umma da ummi suka shigo dakin a lokaci daya, suka ganta a wannan halin. Gaba daya sukayo kanta suka dagota suna salati, umma ta rungumeta tana salati tare da nanata kalmar innalillahi wa'inna ilaihi raji'un." yayin da ummi tayi falo da sauri tana salati, mutane suka yo caa akanta suna tambayarta lafiya? Ta rude sai fadi take ku kirawo mana direba, zainab ce ta suma." sadiya da ni'ima suka saka ihu suka yi cikin dakin. Dakyar aka samu direban aunty sadiya a waya, don duka direbobin sun kwashi mutane suna can daula hotel. Aka dauki zainab bata san inda kanta yake ba, suka tafi asibiti. Sunata neman wayar Aliyu gaba daya wayoyinsa a kulle suke saboda jama'a. Haka ta Abba da daddy ma du ba'a samu. A asibiti kuwa gaba daya matan sun cika daki sunata koke koke, su umma da ummi kuwa da mama matar baban su zainab, sunyi jugum- jugum sai salati suke suna hailala a zuciyarsu, tare da nemawa zainab lafiya cikin zukatansu. 'yan nurse din duk suka korasu falon asibitin, sannan likita ya fara yiwa zainab taimakon gaggawa. Cikin ikon Allah ta farfado, sai likitan yayi mata allurar bacci donta samu nutsuwa. Sai sha biyu aka tashi daga walima, sannan aka samu lambar wayar Abba da daddy. Suna jin zainab a asibiti suka ce subhanallhi, meya faru kuma haka? Umma tace, "shidewa tayi ta zube a sume." to Allah sauwake gamu nan zuwa." Abba ya binciko Aliyu cikin abokansa yace kaifa muke jira ka gama sallamar abokanka kazo muje wata 'yar anguwa. Aliyu ya amsa musu cikin girmamawa, bai tsaya tambayarsu ina zasuje ba. Aliyu yana gaba kusa da direba, Abba da daddy suna baya. Direba ya kaisu asibiti, tunda suka shiga gaban Aliyu yake faduwa, yake tunanin me kuma ya faru? Direba ya tsaya suka fito, suka nufi falon asibitin jikin Aliyu a sanyaye, yana hango su umma da ummi, ni'ima da sadiya da hajiya ya fara karanto kalmar "innalillahi wa'ina ilaihi raji'un. Daga nan ya rinka tsintar bayanin da ummi take musu, na abunda ya samu zainab, ran Aliyu ya baci hankalinsa ya tashi. Bai tsaya sauraron ummi datake gaya masa likita yace kada a shiga inda take ba, da saurinsa ya nufi dakin da aka kwantar da zainab din. A hankali ya murda kofar ya shiga da sallamarsa aciki. Nurse din data ke gadinta tana zaune gefe daya tana sauraron farkwanta, tana ganin Aliyu tasan shi sarai, don haka ta mike ta fito. Aliyu ya tasaya gaban zainab yana kallonta, yarinyarshi zainab mai kyau da nutsuwa, lallai ta shiga tashin hankali, yau daya kawai ta rame haka. Yasa hannu ya shafi fuskarta, tayi fiyau da ita. Saiya ga takara fari, dan bakinta lebenta jajaye, siririn dogon hancinta mai tsawo, ga zara- zaran gashin idonta, baki lafiyayyen gashin girarta daya kwanta das kan girar. Ya zame dan kwallin kanta, bakin gashinta mai tsawo da sheki wanda kullum yake kasancewa cikin gyara, yaita walwali yana sheki, shiyasa bai taba hanata zuwa salon ba, yanzu du sati biyu take zuwa salon, dan ya fuskanci bata damu da kitsoba saide kalba. A hankali ya rankwafa kanta ya hada fuskarsa da tata, cikin kyakyawan lafazi muryansa can cikin makogwaronsa yace "zeeyta ki soni don Allah ki kaunaceni, bani da buri kullum saina yanda zan mallakeki. Zainab kece rayuwata, tun ranar da kika fado duniya ina ganinki Allah ya dasa min kaunarki a zuciyata, kullum kwanan duniya karamin kaunarki akeyi. Zeeyta ba kya ceto rayuwar yayanki ba, ki tsamoni daga cikin damuwa ba? Haba zeeyta, ke kadaice farin cikin rayuwata." aka taba kauren kofar ya dan ja baya. Likita ne zai shigo, yayi saurin gyara mata dan kwalinta ya rufa mata maya fi, wai don kada yaga jikinta. Likitan yayi sallama, yace, ta farka ne? Yace mishi a'a ya mika masa hannu suna gaisawa.. YACE kada ka damu idan ta farka normal zaka ganta. Sai dai don Allah adinga kiyaye wa abunda zai bata mata rai."Aliyu ya gyada kai, yace "insha Allahu za'a kula. Abba da daddy suka shigo suka tsaya akanta suna yi mata addu'a da fatan Allah ya bata lafiya. **** *** **** saratu da lawisa sun saka mansura a gaba sunayi mata fanfo zuga iri-iri, lawisa tace, "don haka nake gaya miki, ki kula da yarinyar nan, mutum mai shiru-shiru abun tsorone, kinga yanzu ta kaiki ta baro. Ta gama sanin sirrinki kaf gashi yanzu ya aureta ta zamo kishiyarki, wallahi ko kadan kada ki saurara mata, kada ki barta ta zauna don ba gidan zama tazo ba. Kuma wallahi ki fito da kudi mu shiga malamai ki samo kansa, ki mallake shi tsab. Dai-dai da uwarsa da ubansa ki rabasu dashi, ya zamo babu wanda yake gabansa saike da yaronki. Mansura tace, "um! Wannan uban 'yan taurin kan zai mallaku ne, tun kwanakin baya fa na kashe kudi akansa, amma inda kika san dutse haka yake, kwata-kwata baya lankwasuwa. Kuma halinsa ne bawai ni kadai yake yiwa hakan ba, ita kanta yarinyar baki ga yanda yake takura mata ba. Inta jin tausayinta. Ashe shidai akwai abunda yake kullawa ransa. Kiga mutum kullum kicin-kicin dashi ba fara'a shi ba zai zauna ayi wata hira mai dadi dashi ba ballantana kiga dariyarsa. Wallahi na gaya miki sai muyi kwana biyu dashi bama magana, don haka ma tsani naga yazo garin gwanda yana can. In nayi magana yace wai dan Allah na rabu dashi ban iya soyayya ba. Du wayewata yana cewa ban iya soyayya ba, yanzu daya auri wannan gidahumar kifin rijiyar aina ga ta yanda zasuyi soyayyar. Saratu yayarta tace, to inbanda ke da abunki wannan ai du shi zai koya mata." mansura tace, tabdijam wannan, wannan dinne zai zauna yana koya wa mace wani abu, ai shi inbanda isa da iko da gadara babu abunda ya iya. Shifa ason ransa komai saide kayi masa yana daga kwance, tunda naga sangartar tasa tayi yawa kai tsaye inya ce inyi masa abu nake cewa bazan iya ba. Lawisa tace wallahi na gaya miki namiji ba dan goyo bane, ko uwarka ka yanka ka bashi inya tashi mantawa zaiyi ya zuba ma rashin mutunci." saratu tace to ba gashi ya mata ta gani, ta rike 'yar tamkar cikinsu don yankan kauna ya tashi ya aureta. Mansura tace shekara takwas ina rikon 'yar nan, ko shekara banyi gidan miji ba ya tattaro min rikon 'ya, karshe abunda ya sakamin dashi kenan? Ai duk zasu ci buhun ubansu, mun saka kafar wando daya dasu. Wallahi saina rushe zamansu, basu bajin dadin rayuwar, mu zuba su gani. **** *** **** kwanan zainab biyu a asibiti, tayi bacci ta huta sosai, don data farka take komawa baccin zuciyarta ta huta ta samu nutsuwa, ta manta da abunda ya faru. Dakin cike yake, da mutanen gidan, zainab ta farka ta yunkura zata mike, umma ta dagota a hankali tana yi mata sannu. Zainab tayi salati tace, "umma meye na ganni a asibiti? Tace ishiru bakida lafiya ne, zo muje ki wanke bakinki." ta kamata takaita toilet ta wanke mata bakinta da fuskarta. Ta dawo da ita ta zauna a bakin gado 'yan uwanta da iyayenta suna mata sannu. Ummi ta hada mata shayi mai kauri tana bata da kofin, mama ta zubo mata farfesun kaza ana bata tanaci, taci dayawa. Aliyu ne ya turo kofa ya shigo da sallamarsa, tayi kur ta zubo masa ido tana so ta tuno wani abu, shikuwa murmushi yake yi, ya daga hannunsa sama yana yiwa Allah godiya. Ta kura masa ido tana kallonshi ko kiftawa batayi, a hankali abun ya fara taro mata cikin kwakwalwarta, tabbas abunda taji ba mafarki bane gaskiya ne, yanzu ita matar yayanta Aliyu ne da gaske? Hawaye ya fara zubowa a idonta, ta mike a hankali tana takawa sannu a hankali ta nufi inda Aliyu yake a tsaye, ta durkusa a gabansa cikin kuka, ta rike kafafuwansa tasa kanta ajiki tana kuka, da sheshsheka tana cewa, yaya, haba yayana yaza kayi min haka? Haba yaya kaine fa uwata? Yaya yaza ka rikide ka zama mijina? Yaya du abunda uwa take yiwa 'yarta tunda na rasa mamana kai ka fansheta, ka juye ta a wajena, ka hanani maraicin rashin uwa, ka zama kaine uwar tawa. Ya zakayi min haka yayana? Kaifa mijin auntyna ce, matar da na dauketa kamar 'yar uwata da muke ciki daya, ta rikeni da gaskiya da rikon amana, zumunci ne mai karfi tsakanina da ita. Yaya ya zakayi sanadiyyar rugujewar wannan zumuncin? yaya don Allah, yaya don girman zatin Allah ka taimake rayuwata ka sauwakemin aurenka ka bani ko waye kaga dama." dakin shiru yayi bakajin motsin komai sai kukanta, mahaifinta ya taso yazo ya dagata, yace "haba zainab ina ganinki da hankali da ilimi, ashe sun zamo na banza tunda zaki iya cewa mijinki ya sakeki." tace kayi hakuri daddyna bazan iya zama da auren nan ba, naci amanar auntyna, da wani ido zan kalli auntyna? Na yaudareta naci amanarta, naso kaina daddy, bazan iyaci amanar auntyna ba." daddyn yace yau, "zainab yau zan gaya miki abunda baki saniba, tun kafin Aliyu ya san zai san mansura mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke." ta juyo a razane ta kalli mahaifinta. Ya daga mata kai yace kwarai hakane. Bazan taba mantawa bayan mamanki ta haifi sadik da banda lpia ina fatan zky hkri [9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**7 Bazan taba mantawa ba bayan mamanki ta haifi sadik da faruk, tana so ta haifi 'ya mace, ita da Aliyu har nafilan dare sun sha yi da rokon Allah ya bata 'ya mace mai hankali da nutsuwa da hakuri da baiwar ilimi. Saboda tunda na auri mamanku Allah ya hada jininsu da Aliyu, komai nasa a gurinta yake. Shawararsu daya bakinsu daya. Lokacin da mamanki ta samu ciki kusan tare sukayi laulayin cikin nan, idan tayi amai shi zai kwashe ya gyara wajen, du abunda take son ci shine dan aiken sayowa. Ranar da aka haifeki kuwa kiri-kiri Aliyu ya hana daukanki wai kada asa miki datti da ciwon jiki, du sanda akace Aliyu ya samu hutu bashida wajen tarewa sai wajen mamanki yana rainonki. Kina da shekara daya ya shirya miki birthday. Kina kan kafadarsa yana yawo dake. Lokacin da ya yanka cake din yasa miki abaki aka dau tafi, yace Allah yasa na miki na aurenmu watarana." mamanki tace, "haba Aliyu, yaushe zakayi jiran karamar yarinya haka? Yace wallahi mama tun ranar da aka haifi zainab Allah ya dasa min kaunarta araina, ni dai dan Allah mama inaso kimin Alkawari zaki auramin zainab inta girma." mamanki tace na dau alkawari, in dai har Allah yayi kai mijinta ne, to ba mai aurenta sai kai, na baka zainab tundaga yanzu ta zama taka. To kinji yanda mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke, tun kina 'yar shekara daya. Abunda ya tashi aurenku kuwa yanzu, yazo mana ne ransa a bace yace "shidai dan Allah a taso da alkawarin mamanki a aura masa ke, don yana tsoron samarin da suke yi miki tururuwa, yaga har kin fara zance. Shiyasa ya nemi alfarma a hade aurenku data ni'ima. To yanzu mahaifiyarki tana karkashin kasa ta rasu, baza kiyi kokari ki cika mata alkawarin data dauka ba, kinfi so kita barinta da nauyi akanta? Ta dago kanta tana kuka tace, daddy ko wane irin alkawari mamana ta dauka akaina zan iya cika mata shi, na hakura daddy. Kayi hakuri ka yafe min bata maka da nayi." yace bakomai zainab, tsakanina dake kullum sai albarka." ***** ****** **** kwananta uku a asibiti aka sallameta, don taji sauki. Amma du shigowar da Aliyu zaiyi tana asibiti nan bata iya dago kanta ta kalle shi bare tace zatayi masa magana kota gaisheshi, kunyarsa take ji sosai. Bama inta tuna haidar shine Aliyu, du tes din kalamomin soyayyar da ya rinka turo mata da wayar da suka rinka yi ashe du yayanta ne Aliyu, ita ya zata yi da wannan abun kunya? Ita kuwa mansura data ji zainab tana asibiti, addu'a ta rinka yi Allah isa kada taji sauki a fasa aurenta da Aliyu. Da Aliyu yaje dadadare gidansu mansura zai dauketa su tafi gida, sai tace ai ita ta gama zaman gidansa, mayaudari maci amana, Allah ya isa tsakanina dakai! Tunda kaci amanata." abun ya konawa Aliyu rai, yace ni kike gayawa wannan maganar? Tace ana gaya maka din azzalumi! Yace to ya isheki, kada ki sake bakinki ya kuskure ki zageni, zaman gidanku kuwa kiyi tayi, randa kika gaji kya dawo." yaja motarsa ya tafi ya barta nan tsaye. Saboda kwanciyar zainab a asibiti, an fasa bikin da kaisu acikin wannan satin sai asabar mai zuwa za'ayi wuni akaisu dakin mazajensu. Zainab ta zamo bata da sakewa ko yawan magana, ko yaushe ka ganta tayi shiru tana tunane-tunane. Aliyu daya fuskanci kunyarsa take ji sosai, saiya daina shigowa inda take. Sai dai da safe d daddare yayo mata tes yace kici abinci fa, kinsan bana son zama da yunwa. Ya karashe mata tes din da kalaman soyayya masu sanyaya zuciya. Takan girgiza kai tace, "kai namiji, ba ruwanshi da kunyar abunda yake so. Wai yayanta Aliyu shine yake mata irin wannan kalaman soyayyan, baya jin nauyinta bare kunyarta. Yaita aiko mata da cimarta ko yaushe, abubawa da yasan tafi so, suna zaune a falo ita da ni'ima, wayarta tayi kara, ta duba ta gani saita kyaleta taita burarinta harta gaji ta tsinke don kanta, amma sai aka sake bugowa. Ni'ima ta dago kai ta kalleta, tace ki dauka mana dan Allah, nasan bazai wuce yaya ba." ta girgiza kai tace bashi bane." ni'ima tace to ki dauka mana." ai ban san mezan ce masa bane. Ni'ima tace ki gaya masa abunda ya faru kawai kada yaga kin yaudareshi." tana daf da katsewa ta dauka, a sanyaye tace "hello! Daga can nura yace ai dole kiki daga wayata, kunya ma ai ta isheki. Wato zainab ina ganinki simi-simi kamar ma hankali, ashe azzaluma ce ke, kin yaudareni. Kinsan saurayinki ne aurenki zaiyi kika binneni a cewar yayanki ne a hannunsa kike, ashe masoyinki ne. Zainab idonta ya fara zubar da hawaye, tace ba haka bane, don Allah nura ka saurareni kaji. Karaf a kunnen Aliyu daya shigo dakin a yanzu, tuni hanjin cikin zainab ya hautsina, tuni ta rikice ta kasa cewa komai, wayar tana manne a kunnenta tanaji nura yana gaya mata maganganu. Aliyu ransa ya baci, ya rinka wani huci ya karaso inda hankalinra ya tashi, ta rintse idonta tana jiran saukar mari. Yasa hannunsa akan nata hannun da yake kange a kunnenta, ya zare wayar , ya daka masa tsawa kai wawa shasha! Kana sane da matar aure kake waya? Wallahi kayi na farko kayi na karshe... Bakwa comments ko likes don haka zanyi daina wahalar da kaina may be littafin bai muku bane shiyasa nayi typing kadan ma. [9:16AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**8, 2**9 & 2**10 DU sanda ka sake yiwa matata waya saina daureka bbu beli. Kuma yanzu ma ka saurari zuwan kana nan sojoji, zasu zo su koya maka hankali." ya cire wayar da kunnansa yayi cilli da ita ta daki bango ta tarwatse, ya karasa gurin ya ciro sim card din ciki ya kakkarya shi gutsi-gutsi ya watsar a wajen. Ya dago kansa yana mata wani irin kallo, yace wannan ya zamo na karshe, idan na kuma gani kina waya ko kina magana da wani sai ranki ya baci." ya juya ya fita. Ta dafe kanta tana kukanta. Ni'ima ta dawo dakin da tun shigowar yaya Aliyu data ga sababin da yake yi ta zame jikinta ta gudu, don kada ya huce akanta." ni'ima ta zauna kusa da ita ta dafa ta, tace meye na kuka, ke matsalarki kenan saurin kuka." tace, haba yaya ni'ima, kin san sarai yaya Aliyu ya fiya saurin fushi da zafin zuciya, ni kuma bana so naga bacin ransa balle kuma ace ni na bata masa, taya za ayi zaman aure a haka? Ni'ima tace haba zainab kefa mai hakuri ce zaki iya zama da yaya Aliyu, don kinfi kowa iya gudun bacin ransa. Ni sai yanzu ma na fahimta ashe du tsanani da yaya yake yi miki soyayya ce da kishinki da yake yi, ni wallahi ban taba ganin amarya da ango da suka dace da juna ba irin ke da yaya." idonta yayi narai-narai hawaye ya sake zubowa tace, "ke yaya ni'ima haka zaki rinka yi min? Ta fashe da kukanta. Ni'ima ta rungumota tana rarrashinta, "to shikenan kiyi hakuri na daina, ba zan kuma ba." du wayanci kawayen zainab ta gayyace su bikin ni'ima, to da abun ya zamo haka ya hade da nata, sai babbar kawarta hauwa Rabi'u ta rinka yiwa kawayensu waya tana sanar musu tare da basu hakuri na rashin ganin kati. Du da haka saida Aliyu ya sanar a gidajen radio, saboda na nesa kawayenta da basu sani ba. Ranar jumma'a akayi mata kamu, kamun da ya bada mamaki saboda cikar kawayenta da 'yan uwanta suka yi, sai da aka fara saukar Qur'ani sannan aka kamata." daga nan wata malama ta bude filin da dan wa'azinta (kusan hakkin miji akan matarsa ne wa'azin kuma inaga munyi a baya basai na maimaita ba). Malamar nan tai ta wa'azi da fadakarwa akan aure, wanda tunda aka fara zainab take kuka, dan jikinta har rawa yake yi. Du da tasan hakkokin miji akan matarsa babu abunda malamansu na islamiya basu koya musu ba, amma wa'azin malamar nan ya shigeta. Yanzu taya zata hada jiki da yayanta Aliyu harta kwanta gado daya dashi? Ya salam! Allah kaika san abunda kake nufi da auren nan, Allah ka bani ikon biyayya ga mijina. Ranar asabar tun asuba akayi wa zainab da ni'ima gyaran jiki, inda jikinsu ya fara laushi da tsantsi, fuskarsu kuwa kamar kwan lantarki dan kyau. A wajen walima shiga iri daya akayi musu, wani dankareren abu me kyalli da walwali pink, da gwagwaro pink, dutsen da suka sa a hannu da wuya duk pink, takalmi da jaka duk pink, sunyi kyau sosai. Walimar ta tara kyawawan 'yan mata gogaggu masu takama da ayar Allah. Domin ayau ma wani wa'azin aka kuma yi mai shigarwa, daga nan wani babban malami yayi lakca wadda ya ladftar da zuciyar mai saurare, ya dasa tsoron Allah a zukatan wanda suka saurara. Daga karshe aka rufe da addu'a, aka yiwa angwaye da amare addu'ar Allah basu zaman lafiya. Amaren suka rinka zagaye tebir-tebir suna gaisawa da kawayensu, suna yi musu godiya da damar da suka samu ta hallartar bikinsu. Aunty sadiya tana ta raba manyan bokitai da farantai, da kofunan shayi na tangaram. Sun so yin kalanda, Aliyu ya hana wai baza aje a lika masa hoton matarsa a wani waje ba, wani gardin ya kalleta yayi sha'awarta ba. Da mangariba daddyn zainab ya kira Aliyu ya tambayeshi ya maganar mansura? Aliyu ya gaya masa yanda sukayi, yace randa ta gaji da zaman gidan nasu saita dawo. Daddy yace, "ashsha haba Aliyu yaushe zaka daka shirme na mata, ai hakuri zakayi ka rarrasheta tunda kai ka tabota, kayi mata laifi babba, don su mata wannan shine babban laifi da zakayi wa matarka." don haka ni yanzu zanje wajen babanta mu tattauna na bashi hakuri kai kuma da daddare saika je ka tafi da matarka." Aliyu ya rissina ya amsa masa tare da yi masa godiya. Daddy yayi sallama gidan Alh haruna, alh ya fito da fara'arsa, ya bude dakin saukar bakinsa suka shiga, bayan su gaisa daddy yake cewa, "nazo bikon mansura ne, na tambaya dazu aka cemin ai har yanzu tana gida bata koma dakinta ba." Alh haruna mutumin arziki, yace kasan halin mata sai hakuri, hauka tayi masa yace tayi zamanta a gidansu. To in banda rashin hankali ma ya za'ayi da hukuncin ubangiji. Allah ya kaddara hakan tun fil azal, towa ya isa yaja da hukuncin ubangiji? Daddy yace"hakane fa don wallahi naso na sa shi ya hakura da auren zainab ya rinka yi min magiya dana hakura na kyaleshi, to ya za ayi da hukuncin ubangiji. Don Allah kuyi hakuri Alh, in ajima Aliyu zai zo ya duketa su tafi gida." Alh ya washe baki yace, wallahi bakomai saiya zo din." da Aliyu yazo Alh ya hadasu da mansura yayi musu fada. Ya dauko mansura suka taho gida. Tunda suka taho take yi masa kuka, yace "haba mansura, kin san bana son kuka, laifi ne kince nayi kuma na baki hakuri ba sai ki yafe minba." LAIFI ne kince nayi kuma na baki hakuri basai ki yafeni ba." niba wani wallhi, ai kasan ka zalinceni, haka kawai saikoyo aure bakamin kayan fadar kishiya ba, kuma baka canjamin kayan daki ba." yace kiyi hakuri, idan nagama ginina wanda zan hadeku waje daya saina canja miki, kayan fadar kishiya kuwa ga akwatuna biyu can da kudi dubu dari suna dakinki na ajiye miki." sannan tayi shiru tana Allah-Allah suje gida taga irin kayan da yake cikin akwatunan. Suna zuwa gida shiya bubbude mata akwatunan ta gani, kaya masu kyau da daraja da tsada, kala goma, super, holland,leshi, shadda,ingila, diamond, takalma uku, mayamayai da turaruka da sauransu. Ta zumburi baki tace ita kala nawa kayi mata? Yace, "ba abinda ya shafeki bane wannan, tace dama mana kace haka, kaci amanata na rike yarinya ta gama sanin sirrina ka aureta." ya daga mata hannu yace, "ki rinka yiwa bakinki linzami, tun kafin nasan zan hadu dake nake son zainab, tanada shekara daya aduniya mamanta ta bani ita. Shiyasa lokacin da mamanta ta rasu na dawo da ita gidana gabana don nasa ido sosai akanta kada wani ya hure mata kunne. Yayi ficewarsa ya barta ta dora hannunta aka tana zunduma ihu. Ranar lahadi akayi wuni ni'ima taci kwalliyarta, tna cikin kawayenta sunata hotuna da bidiyo. Zainab kuwa tana cikin dakin hajiya tana kudundune tanata aikin kukanta, sadiya ta shiga ta dagota, "haba zainab wai miye hakane, yanzu du kaunarku da yaya don an aura miki shi kike kuka irin haka? Tace, yaya sadiya aunty mansura fa marikiyata ce, kuma saina juye na zama kishiyarta." to meye ba haka Allah ya shirya ba. Ta lallabata tayi wanka, ita ta shiryata ta dandasa kwalliya cikin wata dakakkiyar galila da akayi mata dinkin bubu, ta aikatu da surfani ta nada mata dan kwalin shaddar kamar nadin gwaggwaro. Tasha gwal tanata sheki, ta fito da ita zuwa babban falo, mutane sai guda suke suna binta, maroka kuwa sai wasata sukeyi. Sadiya ta fito da kudi tana watsa musu, ta zaunar da ita. Ni'ima tazo ta rungumota tana cewa, "haba my sister ko kefe. Kawayenta du sunzo sun zagayeta ana yi mata shekiyanci, bata iya cewa komai sai hawaye. Jikinta kuwa ya dumame da zazzabi, aunty sadiya ta bugawa Aliyu waya, yana dauka tace, "hello yaya, dama cewa nayi zainab ce ba lafiya take fama da zazzabi, shine nace ko zaka bari a barta a gida inta samu sauki akwota? Yace dan Allah gafara can, inkun ajiyeta a gidan me zakuyi mata inbanda ku dameta da sannu-sannu. Kunga ku kawo min matata na bata kyakyawan kulawa." tace "a yaya haka za'ayi? Yace ku bata waje ta kwanta ta huta kada kusa mata ciwon kai, bana so kudameta da hayaniya." 'yan wajen suka sa ihu da dariya. Zainab kuwa ta dafe kai data ji yana sara mata. Da daddare akayi jerin gwanon motoci, sai aka raba jama'ar biyu, rabi zasu kai zainab da kawayenta rabi kuma zasu kai ni'ima da kawayenta. Ankai ni'ima janbulo kabuga, gidanta babba mai kyau ita kadai abunta, zainab an kaita nasarawa G.R.A gidanta mai kyau zaman mutum daya, fadan kyaun gidan bata lokacine. 'yan kawo amarya sun zagaye ko ina kowa sai santin gidan yake. Da yanda aka tsara komai, gashi ba wani babba bane tsarin turai ne komai, 'yan kawo amarya zasu tafi zainab ta kankame aunty sadiya tana kuka. Sadiya ta rasa yanda zatayi mata saboda yanda taga jikinta yana karkarwa, yayi zafi zau, zazzabi ne mai zafi. Sadiya tayi mata dabara tace "zauna anan na samo miki magani da ruwa a kicin. Ta zaunar da ita a bakin gado ta fice da sauri tana kuka, bata ankara ba taji gidan shiru alamar kowa ya fashe kenan. Ta dora kanta kan filo taci gaba da zubar da hawaye, kanta yanata sara mata, ta dora hannunta akanta ta dafe shi. Aliyu yayi sallama cikin sanyi muryarshi, du da tasan muhimmacin sallama amma saita kasa amsawa, saboda wani irin rudani data shiga, itace yau da yaya Aliyu a daki daya, daga ita saishi a matsayin matarsa ta aure. Ko ina auntyn nata? Yanda dai taji anata zugugun gidan tasan ba gidan da auntyn take ya kaita ba. Yazo ya zauna a bakin gadon, ta zame kasa tace, yaya ina wuni? Ya dagota "lafiya lau zainab ya taro? Tayi shiru tana sheshshekar kukanta. Yace zainab kiyi hakuri nasan bakya sona, kada kiga na takuraki. Zainab tsananin kaunar da nake miki bazan iya bawa wani aurenki ba, saina ga kaman zai cutar min dake. Kiyi hakuri zainab kidaina yawan kuka, bana so ki jawowa kanki matsala, a sannu a hankali wata rana zaki soni, kinki zeeyta? Ni jininki ne dan'uwanki ne, ki daina damuwa akaina kinji babyna." yana dan bubbuga bayanta na rarrashi, ya shafa cikinta, "kinga cikinki kwalam kina zama da yunwa, bana son zamanki da yunwa kada olsa ta kama minke. Ya jaeo ledar kusa dashi yana zaro katon nadin takarda, gasassun kaji ne guda uku, sai robobin youghot da ice-cream, ya yago naman zaisa mata abaki ta kauda kai, cikin sigar rarrashi yace kinga, "kinsan bana son gaddama, ki karba kici." ya rinka bata tana ci, a zuciyarta kuwa tunani take yi, wai dama yaya Aliyu zai iya rarrashin mutum da lallabashi haka? Yau babu wannan fadan da hargagi na yaya,.. YAu babu fada da hargagi irin na yaya, sai wani ji yake da ita. Lallai namiji kenan. Ta kifa kanta a jikin gadon saboda yanda taji yana sara mata kamar zai rabe biyu, yace zeeyta mene ne? Ya dagota yaji jikinta zafi zau, yace, ya ilahi. Yanzu zeeyta bazaki daina sama kanki damuwa akaina bako? Ta rinka lumshe idonta yana kokarin rufewa, saboda azabar ciwon da kanta yake yi, Aliyu hankalinshi ya tashi, ya kwantar da ita ya mike ya shiga kicin ya debo ruwa awata a silba, ya taho da hankicif. Ya kwantar da ita a cinyarsa ya cire mata rigar, sai farar shimi mai kyau a jikinta, ya rinka tsoma hankicin a ruwa yana goga mata jikinta. Sannu a hankalin zafin jikin nata ya fara raguwa, ya bata magani tasha, ya barta daga ita sai bes da siket, ya shimfideta a gado ya mike ya koma kicin don ya mayar da kayayyakin ciki, ya jere ice-cream din da youghot din a firij, ya shiga dakinsa ya fada toilet yayi brush, ya saka kayan bacci ya koma dakin bayan ya rufe ko ina, ya tofe ko ina da addu'o'i ya hawo gadon. Tuni ta dade da fara bacci, ya dagota ya dorata akan kirjinsa ya rungumeta, a zuciyarsa ya ringa jin wata irin nishadi, wai yau shine rungume da zainab dinshi, ashe zaiga wannan rana? Ashe wannan lokaci yana nan zuwa gareshi? Yaso suyi sallah raka'a goma sha biyu don nuna godiyarsu ga Allah, to matsalar rashin lafiyar zeey dinshi hankalinshi ba akwance yake ba. Zainab ta dan motsa, ya rinka jijjiga ta yana lallabta kamar yarinyar goye, da yake zazzabi ya sauka baccinta take yi sosai. Sai wajen asuba ta farka, tana jinta rungume ajikin yayanta Aliyu du kunya ta dame ta, tana kokarin zame jikinta daka nasa sai ji tayi ya sake kankameta, dole ta hakura amma du kunya ta isheta, ta kasa wani kwakkwaran numfashi. Saida akayi assalatu sannan ya shimfideta a gadon, ya rada mata akunnanta, "ki tashi kiyi sallah ni zan tafi masallaci. Ita kunyarsa take ji sosai, bata iya amsa masa ba, ya fita ya nufi dakinsa ya shiga toilet ya daura alwala, ya fita masallaci. Ta mike tana mamakin yaya Aliyu, daman haka yake? Tayi alwala tayi raka'atul fijir, ta tashi tayi sallar asuba, ta gama laziminta ta daga hannu sama tana addu'a, Allah ya basu zaman lafiya, Allah ya hada kanta da kishiyarta yaya Aliyu Allah ya kara buda masa, Allah ya bashi ikon yin adalci a tsakaninsu. Ita kuma Allah ya bata ikon yin biyayya ga mijinta. Tana cikin yin addu'a yaya Aliyu ya shigo, sai ya huce dakinsa. Tayi sauri ta shafa addu'ar ta koma dakinta saita rufe kure kofofi, don ita a tunaninta da wani ido zata kalli yayanta. Daya taba kofar tata yaji ta rufe, sai yayi murmushi kawai ya koma dayan dakin ya kwanta, sai sannan ya samu bacci mai karfi ya daukeshi. Karfe takwas ta tashi ta shiga wanka, ta shirya cikin riga da siket na shadda ruwan goro dinkin stayil ne, anyi mishi hawa-hawa kamar asabari, an zuba dutsuna aciki yana ta walwali. Farar fatarta tayi das aciki, ta hade kananan kalabar kanta tasa ribon ruwan goro ta daure, ta feshe jikinta da turare tana ta zuba kamshi. Ta rinka jin ana kwankwasa kofar falon, taje ta bude. 'yan gidansu ne hamza da sadik suka kawo musu abun karyawa. Ta basu hanya suka shige. Hamza ya kama tsokanarta, "amarya kinsha kamshi, don Allah du kukan da kika sha jiya harda su zazzabi amma kalleki yanzu shar dake kinsha kwalliya. Yace kin hakura kenan? Tace "ban hakura ba, yanzu zan biku mu tafi tunda ku kuka fara zuwa." sadik yace kibi su wa? Na biku mana." hamza yace rabu da ita fade take, ina zata iya zuwa, data sha bulalan Yaya. Sadik yayi dariya, yace irin wacce tasha data yi zance ba. Gaba daya suka sa mata dariya. Tace to ya isa, tunda kun kawo aiken da akayi muku kuzo ku tafi. Sadik yace zamu tafi bamu gaisa da yaya ba? Tace to bacci yakeyi. To ki taso mana shi mana. Ya zan taso shi yana bacci aiba haka akeyi ba. Hamza yace, "wati har kin fara rowarsa ko? Tace, "kai ka sani. Suka fice suna mata dariya. Ta bude taga shiryayyun break din da akayo musu ta girgiza kai tasan iyayensu mata ne zasu yi ba 'yan aiki ba. Ta shirya komai a tebir, tuni ta gyara falon tasa turaren wuta mai dadin kamshi. Daga bayanta taji motsi, tasan Aliyu ne, saita kasa juyawa, a haka ta durkusa tace, yaya ina kwana? Sai shima ya durkusa ya dora kansa a bayanta yace, "haka akeyin gaisuwa a juyawa miji baya? Yace "zeeyta ya jikin, meyasa kika rufe min kofa da asuba? Du ya saukar mata kasala ta kasa wani katabus, wai shi yaya baisan kunyarsa take ba, meyasa yake yi mata hakane? Ya kama shafa wuyantayana cewa "zeeyta zazzabi ya sauka ko? Ta rasa yanda zatayi, du ya kanainayeta, kunyarsa da nauyinsa ya isheta, gashi ta gaji da tsugunan. Ta zame zata zauna ya tallafota jikinsa a hankali yana shakar ni'imtaccen kamshin jikinta, muryanta can kasa cikin marairaita tace "don Allah yaya ka bari, kunyarka nake ji. Cikin kunnanta ya rada mata, kidaina jin kunya ta nifa mijinki ne, kin taba jin inda mata take jin kunyar mijinta? Kefa malama ce kinsan hakkin miji akanki, kada kunyata tasa ki sabi dokokin ubangiji, ki saki ranki ki saki jikinki. [9:16AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**11, 2**12 & 2**13 ALLAH NE ya shirya aurenmu, kodai akwai haramci aciki? Ta girgiza kai alamar a'a ya dagota, taso muje muyi break, dura zan ringa yi miki bana son zamanki da yunwa." ya riko hannunta zuwa kan tebir din, yana bude abincin yana shirin zuba musu, ta rike hannunsa, ka bari yaya na zuba mana. Yace, yauwa ko kefa, ai gwanda ki fara aikin lada." ta zuba masa farfesun da soyayyen dankali da kwai, ta hada masa tea mai kauri, ta tura masa gabanshi. Yace to sannu, muci." ta girgiza kai tace, bana jin yunwa." yace, "kinfi so na miki dura kenan? Ta hada tea kadan tana sha a hankali. Ya zuba mata ido, shi yarinyar sha'awa take bashi, komai nata a nutse cikin hankali da nutsuwa. Suna gamawa ta kwashe kayan ta kai kicin. Shikuma ya zauna akan doguwar kujera. Tazo zata huce ta shiga daki, ya jawota ta fada jikinshi, yace mata a kunnenta in zaki je kibar mijinki? Zo muyi hirar soyayya, nine fa haidar dinki kin manta da hirarmu da mukeyi mai dadi? Ta boye fuskarta. Yayi murmushi wayarshi tayi kara, ya dauka da sauri ya kara a kunnensa, ya rissina tare da cewa hello, umma ina kwana? Lafiya lau, ya jikin zainab din? Yace, dasauki umma gata nan ma ya nana mata wayar a kunnenta, ga umma zata yi miki ya jiki. Ta noke um-um, nidai kunyarta nake ji. Yace au yau kunyar umman taki kike ji, bazaki amsa mata wayarta ba? Cikin sanyinta tace, hello, umma ina kwana? Lafiya lau zainab ya jikin naki? Da sauki umma. "kiyi hakuri zainab kinji, yanda nasanki da hakuri da biyayya ki kara akan da, kada kisa kunya a harkar aure, saita jawo miki halaka kinji zainab? Cikin sanyita tace to umma, nagode, don Allah umma ku daina wahalar da kanku wajen girki don Allah umma kada asake kawowa zan girka da kaina. Anya zainab, ki bari ki kara hutawa mana ba zaki iyaba akwai wahala. Tace bakomai umma zan iya. To shikenan zainab Allah yayi miki albarka." amin umma. Ta kashe sannan Aliyu ya cire mata wayar daga kunnenta, yace, "nifa kada kije ki kone ko ki yanke, zaki ce zaki iya girki da kanki. Tace yaya niba mace bace, ai dole nayi girki, zan bar iyayenmu suna wahala ne? Ai saidai mu muyi musu don su huta mu kuma samu lada ko? Ya daga mata kai kawai saboda shi yana yabawa da hankalin zeey din tashi. Tace, yaya kaje ka gano aunty da Ahmad kaga yasuka kwana? Au har korata kikeyi? Tace ba haka bane yaya, gwanda kaje kaga yanda suka kwana. Ya gyada kanshi zanje, daganan zan wuce office din daddy da Abba na gaishesu. Sha biyu dai-dai ya fita ya nufi gidansa, yayi sallama falon mansura tana zaune bata amsa ba. Ya shiga ya zauna bata juyo ta kalleshi ba. Yace yau bakisa su talatuwa sunyi shara da wanke wanke ko ina kaca kaca haka? Tace, tunda kazo ai saikai kasa suyi. Ina Ahmad kinsa ankaishi makaranta daiko? Tace nidai kada ka dameni, ka damu da rayuwarsa meyasa baka tafi dashi can gidan naka ba? Wai don Allah ko kunya baka ji ka riki yarinya ka aureta yau ka kwana gado daya da ita har wani abu ya faru a tsakaninku? Wannan abun kunya da yawa yake, wallahi idona idon yarinyar nan saina raunanata. Ya daka mata wata irin tsawa data firgitata, yace, wallahi ki kiyaye, du ranar da kika sake kika dora hannunki akan matata saikin gane kurenki wallahi sainayi maganinki. Bissimillah kije ki tabata. Abunda yasa kenan nakasa bawa kowa auren zainab, don kada wani ya cuceta, shiyasa na aureta don nabata kulawa, sannan ke kuma kice zaki daketa. Wallahi da sai kin raina kanki." ya mike ya fice ya bar mata gidan, yayi office din iyayensa. Zainab kicin ta shiga, inda duk aka jere mata kayan amfanin kicin kamar a turai, du wata na'ura da zata dafa abu kota gasa abu cikin sauki an sa mata aciki.(nan yanda za ayi abincine nasan basai na rubuta ba) Ta gama abinci ta shiga wanka ta dauro alwala, tayi sallah tashafa mai, ta shafa farar hoda du da ba wata kwalliya tayi ba saida ta kara kyau tasa atamfa holan baka, dinkin karamine yayi das ajikinta, ta fesa turaruka tanata kamshi. Ta jona abun turaren wuta, mintuna kadan gidan nata ya dumame da kamshi. Tana so taji mutuniyar tata yayarta ni'ima, to bata tunda yaya ya fasa mata wayarta batayi wata ba. Koda yake bawa zai ba tunda shine me sayen? Yaya Aliyu yayi parking motarsa ya fito a harabar gidan, daddan kamshi daya ji yana tashi shiya shaka ya ratsa masa zuciyarsa, saiya ji ya sanyaya masa rai. Yayi murmushi ya shige ciki, ya tura kofar falon ya shiga da sallama. Tana zaune akan kujera ta amsa sallamar kanta a sunkuye. Yazo ya zauna kusa da ita, saita zame kasa ta durkusa, "yaya sannu da zuwa." ya dagota ya karata ajikinsa yace, "zeeyta meyasa baki taso kin tareni ba kina oyoyo sannu da zuwa yaya? Tace, "a da girmaba? Wane girma kike dashi? Kefa babyna ce. Ta rufe idonta, yaya kana sani jin kunya. Zanyi kokari na cire miki kunyar nan dai ta daina takura mana." don Allah yaya ka bari, ga abincinka can a tebir." a lallai yau zanci girkin amaryata, to taho muje ki bani. Ya riko hannunta suka jere harkan tebir din, ta jawo masa kujera ya zauna, tana bude abincin kamshi ya bugesa ya lumshe ido..... TA loda masa abincin ta rinka tura masagabansa, tasa masa cokali, ta zuba masa hadinlemo data yi masa. Tace yaya kaci mana." yazaunar da ita kusa dashi, ya debo a cokalin yanufo bakinta, tace dn Allah yaya kaci, nasan fabaka ci komai ba tunda safe. Nikuwa nasha ice- cream."inbanda ke wa yake maida ice-cream abinci. Yabata ta karba cikin kunya taci, shima yaci yceum-um carkwai, waya koya miki girki haka?Tayi murmushi ta sunkuyar dakai, ya rinka cinabinci yana santi, saigashi yaci dayawa. Ta rinkamamaki ashe yaya yana cin abinci? Ita saita gaidan aunty ta ajiye masa, idan yazo kokarinsayayi cokali biyu ya ajiye.Intayi magana yace yakoshi. Saidai suyi ta ciye-ciye, da yamma kuwa ya tafi gida yaci acan.Kodai daman rashin dadi ne yake hanashi ci?Yana tafiya sallar isha ta rufe dakinta ta kwanta,daya dawo ya taba kyauren yaji shi a rufe, saiyakoma dayan dakin yayi kwanciyarsa.Da asuba daya fito sallah ya buga mata, saidayaji motsin tashinta sannan ya tafi masallaci.Yana dawowa dakinsa ya shige ya koma bacci.Itama baccin ta koma, sai karfe takwas ta miketa shiga kicin, tana gamawa ta kwashe komai tajera a tebir, ta gyara kicin din ta share ko ina, taturare shi da turaren wuta.Ta koma dakinta ta shiga wanka, tana fitowa tashirya cikin wani jan les riga da siket, dinkinkaramine yayi das ajikinta, sai kamshi take.Tana jera kayan kwalliyarta akan madubi yashigo, ta durkusa da sauri tace yaya ina kwana?Yace bazan amsa." ta marairaice, haba yayasaboda me bazaka amsa min gaisuwata ba?Kinyi min laifi jiya kin rufe min kofa." kayi hakuriyaya kunyarka nakeji.To zeeyta me zanyi miki, na sani ke yarinya ce,nima ina tausayinki, ki saki jikinki ba abundazanyi miki, rainonki zan tayi har sai kinyi wayo,kada ki kuma rufe min kofa ina tsoro kada waniabu ya sameki a daki ke kadai, gwanda munatare a waje daya.Saiki yi kwanciyarki a gado, ni saina kwantaakasa. Kinji zeeyta? Ta daga kai, kayi hakuriyaya bazan kuma ba.To shikenan na hakura.Yaya ga break can.Zeeyta harkin gyara waje haka kinyi wanka?Zainab aiki yayi miki yawa, kodai asa umma tasamo miki mai aiki? Haba yaya zan iya komai, wallahi malaminmu yagaya mana du abunda kayi a gidan mijinka ladane, idan ka bawa wani yayi maka, to shi yake daladan ba kai ba. Nikuwa yaushe zan yardalahirata mu rinka rabawa da wasu?Ya gyada kai, haka akeso zeeyta, mutum ya rinkaamfani da abunda yake karanta.Akan tebir inda ta shirya masa break ya rinka ciyana santi yana sa mata albarka. Saida yacidayawa ya koshi yayi hamdala, yace zeeyta zokigaya min waya koya miki girki ne? Naga a gidanauntyn naki bata fiya yi ba bare nace gani kika yitana yi kka koya.Yaya a makaranta mana ai har fanni koyon girkiakwai, shiyasa in mun tafi tun safe sai shidda nayamma za a tashi. Yaya Aliyu yace ai makarantartana da kyau, daddy baya wasa a harkar ilimi."wayar tasa tayi kara, ya dauka yace, ke ina kikabar mijin naki kika bugowa mutane waya dasassafe? Kayi hakuri yaya, wallahi inaso injizainab shine na bugo a taka.Ta gaisheshi. Ya mikawa zainab wayar, ni'imatana jinta tace mutuniyar ya akai? Ina taso najiyo ki saina tuna kefa kurmace yanzu tundabakida waya. Wai ya yayan ne, komai ya faru ko?Zainab tace oho! Ke kika sani. Yaya ni'ima inakika barshine?Yana kicin yana soya mana break.A'uzubillahi, kiji tsoron Allah kina zaune mijinkiyana kicin."ni'ima tace, ai shiya jawo, bashi ya dora mingajiya ba, a wahale nake ba abinda zan iyayi. Aiya kuma shiga kicin."ke yaya ni'ima wace irin gajiya ce da zata hanakishiga kicin?Ni'ima tace 'a daga jin bayaninki bakisankomaiba. Wai yaya kallonki ya tsaya ne haryanzu baiyi miki komai ba?Tace "don Allah yaya ni'ima ki bari ni bana sonirin wannan maganan.Zainab da wahala fa, nima nasha wahala bare keda kike yarinya.Zainab tace don Allah kidaina min irin wannanmagana, Allah zan ryfe wayar.Ni'ima tace wai yaya na wajen ne koya tashi?Tace mata, oho ke kika sani, ni dai ki bari banaso."to shikenan naji matsoraciya, wata rana da kankizaki zomin da zancen bazan saurareki ba.Tace, eh naji na yarda. Ta rufe wayar tana dariya.Yaya Aliyu yace, me take gaya miki kike cewabakya son ji? Gaya min ni."tace kai yaya nidai ba ruwana. Ta tashi zatagudu daki ya rikota, zeeyta ba zaki gaya minba,ni inason ji gaya min kinji.Ta boye fuskarta, don Allah ka bari ni bazan iyaba. Wata wayar ce ta sake shigowa, da yayi birisda ita saida yaga numbar mai bugowan sannanya daga.Hello mansura ya akayi? Hello! Mansura ya akayi? Jin yaambaci mansura tasan auntynta ce,kawai saita mike zata bar wajen, yazuba mata ido yana kallon yanayinyanda take tafiyarta kamar bata sontaka kasa, yarinyar ta shige ransadayawa, yanda yake jin kaunarta tarinka azalzalar zuciyarsa, dole sai yaganta koya ji muryanta, inba hakaba baya iya rintsawa. Son gaskiyakenan, ko yaushe yana ranka. Yaugashi zeey dinshi a matsayinmatarshi ta aure, ko yaushe mafarkinnasa zai tabbata ya ganshi manneajikinta suna faranta ran juna? Tace baka jinane? Yace inajinkimansura ya akayi? Dama yar lawisakawata ce ta haihu, shine zamujesuna.Yace a'a bazaki ba.Saboda me? Kana ganin irinamintakar da take tsakaninmu dalawisa, amma kace bazan je sunanyarta ba.Eh nace bazaki ba, kada kuma ki sakekiyi min maganar.Ta kama maganganu, "haka kawai adakeka a hanaka kuka, ka gama cinamanata ka auri 'yar dana rika kumani ka rinka takurawa rayuwata kanagallaza min. Haka kawai kai ba'agidan kake ba kuma ka hanani fita,zanta zama ne ni kadai kamarmayya?To ya isheki haka, ina gaya miki kirinka iya bakinki, ki rinka saninkalmar da zaki gaya min.Ya kashe wayar.Lawisa ta kalleta, tace, to ya ya, yabarki? Ta tabe baki, ya hananizuwa." lawisa tace mugu, dayakyaleki muka je wurin malamin nandu taurin kansa sai yayi laushi, donsaiya lankwasa mik shi, saikin juyashi a tafin hannunki. Amma yanzuma ba zama za ayiba, ki bani kudi ninaje miki." tace to. Ta mike ta shigedaki, ta fito da kudi ta bawa lawisa.Yauwa kin gani ba, ai Aliyu dazainan sun shiga uku, sai sun sansunci amarki."yauwa aminiyata, don Allah kikokarta, kada kiji komai kawata.***** **** *****da daddare ta bar yayan nata a faloyana kallo, tayi shiri kwanciya bacci,saita rasa ya zatayi saboda yayanyace kada ta sake rufe kofa takwanta bacci ita kadai a daki. To yazatayi?Ta dauko bargo da filo takudunduna a kasa kan kafet, tayiaddu'o'inta ta shafa, ba jimawa bacciya dauketa.Du da har yau 'yar uwar tashi takisakin jikinta dashi, saboda tsaninkunyarsa data keji, shidai yana so yakasance tare da ita, don inya kalletasaiya ji farin ciki.Intayi magana kalamominta sai sunsanyaya masa zuciyarsa, yana sonyanayin maganarta cikin shagwabada sanyi, bata son yawan hayaniyaamma baza a kirata miskila ba,saboda akwaita da fara'a da kumafaram-faram da jama'a.Tunda ta mike yaji du zaman kadaiciya isheshi, shi kadai awajen. Donhaka ya kashe komai ya rufe ko ina.Ya tofe ko ina da addu'o'i, sannan yashiga dakin ya rufe kofar, ya ganta akudundune akasa cikin bargo tatakure waje daya.Yayi murmushi ya tsugunna kasanya janye bargon a hankali, bacci takesosai. Yasa hannu ya shafikumatunta. Yasan shidai maikyaune, du inda ya shiga ana yabashi. 'yan uwa suna zuzuta kamaninsada zainab. Amma ina, shidai yasanzeey dinshi tafi dhi kyau, yarinyamai hakuri da nutsuwa, shidai Allahya barshi da zeey dinshi.Ya dauketa cak ya daurata akangado, ya tofeta da addu'o'i, sannanshi ya sakko kasa ya kwanta. Shidahakan yafi mashikwanciyar hankali, da ace zeey dinshitana wani daki shi yana wani dakidaban.Cikin dare ya manta bai kashewayarsa ba, tai ta damunshi da karahar zainab ta farka, tayi mamakinganin yayanta akasa ita kuma akangado, alhalin ba anan ta kwanta ba.Yayi tsaki cikin yanayin bacci yadaga wayar, daga can dayanbangaren amininsa, abokin aikinsadaga kaduna, kanal faruk yayi yomasa wayar, cikin magagin bacciyace waye ne?Faruk yace, magagin amarci kakeyine shiyasa baka gane lambarba?Aliyu yace "shegen gari maye nayomin waya cikin dare haka?Ai tun dazu naso nayo maka, sainace dai kada na katse maka hanzaribari na bari ka gama samun untsuwatukunna."Aliyu yace, dan ganganci, autar tamudanake ji da ita a rayuwata, aiyarinya ce karama saita wahala.Faruk ya kwashe da dariya, yacekaidai ko gudunka take yi, yandanasanka da kaunar zainab anya zakasaurara mata?Ba dole ba tunda ina tausayinta, waimeyene ka tasheni cikin dare haka?Yanzu da idon zeey biyu ai da kafirgitamin ita.Faruk yace, ai ya zama dole nanemeka, aiki aka turamu kasarbayelsa tafiyar gaggawa jibi-jibnnan.Aliyu yace haba dan Allah, kumadole saidani basu san inada sabuwaramarya ba? Ina zan tafi na barta?Faruk yace ai anan zaka tafi ka barta,ai tasan cigabane yazo ai bazata kicigabanka ba.Aliyu yace, wai daga ina tafiyar tataso haka?Daga can sama takardar ta iso manaa dazun nan office, kamata yayigobe ka taho nan kaduna, jibi dasafe jirginmu zai daga."Aliyu yace innalilahi wa'inna ilaihiraji'un, banso tafiyar nan ta sameni awannan lokacin ba, ya zanyi dazeeyta?Faruk yace, kaji ka, saika ce wanimace, kai ba namiji bane. Kakarfafawa iyalanka gwiwa har mujemu dawo. Bari na barka sai gobeninka iso."da safe tun wuri ya tashi, zainab tanakicin tana hada break, tana fitowataga yayi zugum alamar tunani. Takawo break din ta jere, tazo tadurkusa agabansa tace, yayamenene?Ya rike hannunta zainab tafiyace tasamemu ba shiri." A daure ayi likes da comments [9:19AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**14, 2**15 YA rike hannunta, zainab tafiya ne ta samemu bashiri.Toh don Allah yaya meye abun damuwa? Bakasaba tafiye- tafiyen nan ba, zaka sawa kankadamuwa. Don Allah ka cire komai daga ranka zomuyi break din.Ya biyota kan tebir, ta rinka jan ra'ayinsa yanatura abincin aciknsa, har yaci mai yawa. Yacemata zaije wajen mansura yanzu zai dawo."yana fita zainab murna ta rinka yi sosai, zatakoma gidansu kafin yaya ya dawo.Aliyu yana shiga falon mansura yaji shiru, yashiga cikin dakin tana kudundune cikin bargo, yazauna gefen gadon ya zanye bargon, ta budeidonta, tana ganinsa tayi zumbur ta tashi tace,lafiya yanzu da sassafen nan?Yace lafiya lau ke baki san ma garin ya waye bako?Karfe goma kina kwance. Kaduna zan tafi yanzu.Tace au har amaryar ta ginsheka ka fasa yi matakwana bakwai, yau fa kwananku hudu.Yayi tsaki ya harareta, ki rinka sanin kalmar dazaki gayamin.Yau zan koma kaduna zamuyi asubancin tafiyabayelsa aikin gaggawa.Tayi dariya da shewa, Alhamdulillah, Allah nagode maka, ai gwanda ka tafi. Ya bude baki yanamamaki, au har so kike ma na tafi bakya sonzamana kusa daku."tace wallahi bana so, aini tafiyarka tafi komaikwanciyar hankali awajena. Ya daga mata hannuto naji, ya kuma isheni haka kafin ki fara fatannabar duniyar. Kiyi min lis din abunda kukebukata keda Ahmad. Sito dai cike yake da kayanabinci.Tace "zaku dade ne?Ya mutsa fuska, eh to zamu iya yin sati hudu kozuwa sama.Ta hau lissafe- lissafemai dalili da mara dalili. Yabata damin kudi kamar yanda tace ya kara matawasu ma akai.Ya mike zai fita yace mansura kiyi min addu'a,anason addu'ar mace zuwa ga mijinta, Allah yanaamsawa zan biya makarantar su Ahmad yanzumuyi sallama, don Allah ki kula da komai, kijagirmanki da mutuncinki, don Allah kada kuyiabunda zai daga min hankali.Kinga yaki zamu tafi, ko mudawo da rai koakawo gawarwakinmu, laifin da kike ganin nayimiki kiyi hakuri ki yafemin.Jikinta yayi sanyi tace, amma kasani baka kyautamin bako?Na riki yarinya ka aureta.Yace haba mansura, ba zaki yarda da kaddara bakinsan bana son mita. Kiyi hakuri don Allah kibarmaganan nan.Tace to shikenan naji, Allah ya kiyaye hanya."yace Amin, nagode.Ya shiga motarsa ya nufi makarantar su Ahmad,har sun fito break, yana ganinsa ya rungumesayace Abbana har yau aunty mami bata dawoba.kuma naje gidan Abbanka ban gantaba, in natambayi mama ina aunty mami saita doke bakinatace kada na kuma zancenta.Abba zaka kaini wajen aunty mami? Ya shafakanshi, zan kaikaamma kayi hakuri kaga yanzu tafiya zanyi wajenaikina, sainayi kwanaki dayawa zan dawo, karinka kula kana maida kai akan karatunka kaji.Ya rike hannunsa zuwa wani dan kes na cikinmakarantar, ya saya masa mitfy da kek da lemonkwalba, ya zaunar dashi ya cinye indomi da kwaidin, ya shanye lemon kwalbar yace ya koshi.To sai ya saka masa mitfy din da kek a jaka,yace ya koma aji.Shikuma ya tafi gida.Zainab tun bayan fitarsa ta gama share- sharentada goge-gogenta, ko ina yayi tas yana kyalli, tayiwanka ta gyara kanta cikin wani material bakimai gwaldin da gashi-gashi ajiki. Dinkin yayimata das dai-dai jikinta, farar fatarta ta karamata kyanta da kwarjini acikin kayan, ta feshejikinta da turararuka.Haka kawai take jin nishadi, yau zata komagidansu du da dai tasan dole ta rinka jin kunyarsu umma da ummi, ai saitai ta zama abangarensu wajen babanta.Yaya Aliyu ne yayi sallama, ya katse matatunaninta, ta mike tsaye tana yi masa sannu dazuwa, ya nufo wajenta ya zaunar da ita, ya zaunakusa da ita yana amsa mata da yauwa. Ya shafikuncinta kinyi kyau zeeyta."ta mike ta nufi firij ta dauko mishi lemo da ruwa,ta shiga kicin ta dakko masa gasashen nama takawo masa. Yace yauwa zeeyta nagode.Yana ci yace, yanzu zeeyta yanda kika farasangartani da wannan girki naki masu dadi badole nayi maraicinki ba, wa zai rinka kula daniidan na koma can?Gashi da yamma zan tafi.Tace yaya inka tafi da yamma nikuma saida darezan tafi? Yayi saurin cewa ina? Har yana kokarinkwarewa. Cikin sanyin murya tace, "yaya gidamana.Kije gida kiyo me?Yaya ba a gida zan zauna saika dawo ba?Ya girgiza kai, a ina kika taba ganin anyi haka?Zamanki zakiyi a gidan mijinki har saina dawo.Nan da nan hawaye ya wanke mata fuska, tadurkusa kasa agabanshi takama kuka, "don Allahyaya ka mayar dani gida. Idan ka dawo na dawo.Wallahi yaya tsoro nakeji bazan iya zama ni kadaiba, kaji yaya.Ya dafa kanta yana rarrashinta, kiyi hakuri za akawo miki wa'yanda zasu tayaki zama ko mutumnawa ne a 'yan uwanmu, amma bazan iya mayardake gida ba, gwanda kina inda na ajiyeki.Nidai nafi son ka mayar dani gida.Ta kifa kanta a jikin kujera, kuka take yi masasosai.Ransa du ya baci shi kwata-kwata baya sonkuka.Bare kukan mace, ballantana kuma zeey dinshiwanda tun tana yarinya baya kaunar ganinkukanta....... Wadda tun tana yarinya baya kaunar ganinkukanta, yanzu yaji hankalinshi ya tashi, sai yanemo mata komai take so sannan yake samunnutsuwa, bare yanzu data zama mallakinsa.Ya sanyaya murya can kasa kamar zaiyi kuka,yace "zainab so kike ki daga min hankali ko?Bakya son kwanciyar hankalina zeeyta? Ya kikeso nayi da rayuwata? Zainab tafiyarki gidaawajena ba karamin tashin hankali bane. Habazeeyta kiyi hakuri ki zauna agidan ki rikeminamanar kanki da dukiyata da gidana. Yanzu inkika tafi bakya nan gidan ai kango zai zama.Ya zauna dirshen a kasa ya jawota jikinsa yanararrashi, kiyi hakuri zainab ki kwantar dahankalinki ko na samu nutsuwar zuciyata.Zainab yaki fa zamu tafi, ko muyi nasara ko akashemu . Tayi firgigit ya dago kanta daga jikinsacikin razana. Tace yaya mutuwa? Ya maida kantaya kwantar jikinsa. Yace kada ki damu, ai hakamuke, nasara tana wajen ubangiji mun dogaradashi zai karemu, cikin hukuncin ubangiji, Allahzai bamu nasara akan abunda muka jeyi.kita yimin addu'a kinji kada ki kuma damuwa.Ta dago kanta tace "yaya kayi hakuri in na batamaka ka yafe min kaji.Bakomai zainab na hakura na yafe miki ki dainadamuwa ki taimaka min da addu'a.To yaya na dau alkawari zan tayi maka nafilfili daaddu'o'in neman nasara. Yauwa kanwata,nagode. Bari naje gida nawa su Abba da daddymaganar tafiyan, wa kike so akwo miki ta tayakizama?Hajiya."yace, hajiya babba?Ta daga kai. Yace babbar magana, bari na gayamusu, ai 'yar gatan hajiya ce ke zata zo.Yana fita ta mike ta shiga kicin zata tanadarmasa abunda zaiyi guziri dashi.Tana gamawa ta shiga tayi wanka, tayi alwalatayi sallar la'asar, ta tsala kwalliyarta da orangedin shadda, ta kafa daurinta tayi kyau tanatasheki kamar ba ita bace tasha kuka dazu ba. Tajeta bude jakar tafiyar ta zuba mishi kunshin ledamai kyalli guda hudu, daya hadadden kek ne datayi masa mai kwakwa, dayar kuma mitfy, dayarkuma kwallon kaza, sai soyayyen cincin maisugar data ke dashi, ta dibar masa. Daya kena'uroro sun zo mana masu saukaka mana aiki,shiyasa nan da nan ta gama.Aliyu kuwa daya jewa iyayensa maganar tafiya,nasihohi suka yi masa kamar yanda suka saba,suka yi masa addu'ar samun nasara da fatanalkhairi.Daya zo wajen hajiya yake fada mata sakonmuniyarta, hajiya tace "Allah sarki, ai zainab cesaina zo na tayata zama, yarinya mai hankali danutsuwa, ka gaya mata ta kwantar da hankalintakana tafiya direba zai kawoni."Aliyu yace yauwa hajiyarmu, kakarmu ta kanmu,ya bata kudi mai yawa taita masa godiya, yabawa su umma suma sukaita masa godiya da saalbarka.Ya amsa da Amin, ya shige motarsa ya tafigidanshi, yana ganin gimbiyar sai yaji hankalinshiya tashi daya tua tafiya zaiyi ya barta har nawani lokaci.Ta tare shi tana murmushi tare dayi masa sannuda zuwa, ya zuba mata ido da irin kallon nan maibirkita kwanyar masoyi, ya nufi wajenta, ya warehannunshi ya rungumeta yana sumbatarta ahankali kamar zai hadiyeta.Du kunya da nauyinshi ya isheta, kokarin zamewatake daga jikinsa amma yaki ya bata damarhakan saima ya kara matseta ajikinshi.Sannan ya zauna akan kujera yana shafa kanta,du ta noke ajikinsa kunyarsa take ji sosai.Ya rada mata a kunnenta yaushe zaki daina minkunyar nan ne Amma zanyi kokari na rabaki dakunyar nan.ta rufe fuskarta ta zame daga jikinsa tana maitsananin jin nauyin abunda ya fada mata.Yace baki bani abinci bafa taso muje ki baniabinci yunwa nake ji.Da kyar ta mike tayi gaba yana biye da ita harzuwa tebir din, ta bude abincin kamshinsa yabugeshi. Malmala biyu ta cire daga ledar sunataturiri ta zuba kan filet din tangaram, ta zubamiyan cikan tagaran din ta zuba masa kunun aya,ta rinka tura masa gabansa. A hankali tace kacimana.Ya jawota ya zaunar da ita acinyarsa, yace waihar yanzu kunyarce ne? Don Allah ki cire kunyarnan ki bani abaki. Tace um-um, nidai bazan iyabadon Allah ka kyaleni.Ta mike da gudu tai cikin daki, yabi ta da kalloyana murmushi, saida ta shige ciki ya girgiza kaiya kama cin abincin yana mai jin dadinsa sosai.Ya rinka shan kunun ayar nan da yaji madararruwa yana santi.Saida ya gama ci, ya shiga dakinsa ya fadatoilet, yaga ta tara masa ruwan wanka a baho, yashiga yayi wanka ya fito.Ya shirya cikin kakinsa, ya fito ya shiga dakinta.Tana zaune abakin gado tayi tagumi, ya zaunakusa da ita ya cire hannun tagumin yace babukyau ki daina, ya ciro sabuwar waya akwalinta yamika mata. Ga waya zainab kullum zamu kasancetare awaya kinji.Ta daga kai tace nagode.Ya fito da kudi masu yawa ya mika mata, ungowannan kirike a hannunki ki rinka 'yan bukatunki.Ta bude baki cike da mamaki, tace ai yaya kudinsunyi yawa, me zan siya? Komai fa da akwai asito.Ta karba ta raba kudin biyu, tasa masa rabi aaljihunsa, don Allah yaya ka barsu wa'yannan masun isa nagode Allah kara budi.Yace Amin nagode nji dadin addu'arki. Ya mikezainab zan tafi? Ta dago kanta a sanyaye yayatafiyar zakayi? Sai kuma hawaye. Ya dawo yazauna, ya jawota jikinsa, sai kuma ta sakar masakuka......kawaisai tausayinta ya kamani na tsaya da rubutun ina kallonsu Bakwa komai [9:20AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**16 & 2**17 Ya dawo ya zauna, ya jawota jikinsa, sai kuma tasakar masa kuka.Ya rinka rarrashinta yana lallaminta kamaryarinyar goye dake jikin mamanta, kiyi shiruzeeyta kiyi hakuri bazan dade ba zan dawo, mekike so na siyo miki? Ta girgiza kai bakomai." yadago kanta yana share mata hawayen, to kiyishiru bana son kukan nan, yana daga minhankali.Ta hadiye kukan tana ajiyar zuciya, ya rinkararrashinta yana lallaminta tare da dan bubbugabayanta, sanyin iskar data rinka ji ta cikinkunnenta shiya saukar mata da kasala jikinta yasaki kawai sai bacci ya dauketa.Ya lallaba a hankali ya shimfideta, sadaf-sadaf yafita ya shiga dakinsa, ya dauki jakar kayansa yafice ya fada motarsa, ya sallami mai gadi yayiwaje da gudu ya dauki hanyar kaduna.A zuciyarshi yana tunani zeey dinshi saita tashitaga ya tafi.Kai zeey da rigima take, du ta daga masa hankali,inba dole ba yaushe zai tafi wani waje ya barta.Ya zari wayarsa ya bugawa hajiya,yace dan Allah hajiya direba ya kaiki yanzu fanabar zeey ita kadai a gidan.Hajiya tace ai kayana ma ake sawa a mota yanzuzamu tafi.Yauwa hajiyata nagode. Ya kashe wayar. Lokacindaya isa kaduna ya tarar da abokinsa faruk yanajiransa, suka rungume juna, ya dakkowa Aliyutakardar, Aliyu ya bude ya karanta yaji bayananda suke ciki.Aliyu ya ninke yace to Allah ya taimaka mana.Faruk yace, bari na karasa gida na barka kadanhuta kayi shirye-shiryenka. Tafiyar asuba zamuyigwanda ka kwanta da wuri. Aliyu yace badamuwa. Ya rakoshi wajen motarsa ya tafi.Aliyu ya shigo cikin gida ya wuce dakinsa, yafada toilet yayi wanka yayo alwala yayi sallah,yayi addu'o'insa ya shafa.Ya shafa cikinsa daya ji yunwa ta fara matsamasa, yasan yayi maraicin zainab ko don yandatake kula dashi wajen abinci, yanzu dole saide yahada shayi yasha, don ya gaji bazai iya fita gidanwani abinci ba.Gashi yaronsa maiyi masa girki shima yaje ganingida bai dawo ba. Ya bude wayarsa ya dannalambar zeey dinshi, ringin daya tayi ana biyu akadauka, "hello yaya." saita sa masa kukanshagwaba. Ya kama rarrashi, yi shiru yi hakurizeeyta, daina kukan gaya min meye? Mene nezeeyta? Gaya min kinji babyna.Yaya shine kayi min wayo kasani bacci ka guduko? Yaya kuma kudin dana raba biyu na dau rabinace maka sun isheni na baka rabin shine kaajiye min ko?Oh! Sorry zeeyta, bazan kuma ba nadaina kinji,daina kukan kina tsiyayar min da hawayenki maitsada a kasa, gashi bana kusa bare na tsotse.Tace, ka gani zaka fara ko?To na daina, hajiya tazo ko?Hajiya tazo tuntuni, suna falo ita da hamza dasadik suna hira.Yace, yauwa ai nasan bazasu barmin ke cikindamuwa ba zasu rinka zuwa suna tayaki hira. Keko dai kinci abinci? Bana so ki rinka zama dayunwa fa, ki rinka cin abinci sosai kinji?Tace, to yaya ai kaima baka ci ba.To ni wa zai bani zeeyta? Yanzu ma zan jonahita na tafasa ruwan shayi nasha, don yunwanakeji.Ya marairaice masa tace, haba yaya da kanka?Yace to ya zanyi zeeyta, wa zaiyi min? Tace yayaka duba cikin kayanka da akwai sako.Sakon me?Um-um nidai bazan gaya maka ba, ka budeyanzu inka kashe wayar."yace to.Ya kashe wayar ya jawo jakar kayan nasa yanabudewa, yaga nadi-nadi na leda har kashi hudu.Ya rinka warewa ganin abubuwan da suke cikiyasa shi tsananin mamaki da al'ajabi, a yaushezeey tayi wannan aikin? Kai wannan yarinyaubangiji Allah yayi mata albarka. Hakika yaji dadita faranta masa sosai, ya daga hannunsa yanayiwa Allah godiya. Allah na gode maka da wannanbaiwa dakayi min nasamun nutsasiyar mace maihakuri da sanin ya kamata.Ya ware komai ya rinka ci cikin nutsuwa danishadi, saida yaci ya koshi yasha lemo yayigyatsa yayi hamda ga ubangiji, yaita shiwazainab albarka a zuciyarsa.Yayi waya gida ya sanarwa mahaifansa ya isolafiya, ya bugawa mansura itama ya gaya mataya iso lafiya, taba shi Ahmad sukayi hirarsu yanagaya masa abunda zai sissiyo masa.Mansura ma ta karba ta gaya masa abubuwandatake bukata, sukayi sallama. Yana kashe wayarzeey dinshi ya sake bugawa.Tana dauka tace, hello! Yayana ka koshi?Nakoshi zeeyta Allah yayi miki albarka.Amin yaya nagode.Yace, wai zainab ba zaki rinka gayamin sunayendana ji kin radamin ba, mazan jiya da mazaje?Tace "kai yaya nidai ban zan iyaba, da dinma danbansan kai bane ba.To yanzu me zaki rinka gayamin? Honey ko myluv?Tace, kai yaya dan Allah ka bari.Yace, au bazaki gayamin kalmar da zata sanibacci cikin nishadi ba? Sai ya kashe wayar.Ta dafe kai tace kai yaya da saurin fushi yake,toni yanzu ya zanyi masa? Ta dake ta bugamasa wayar, ya dauka yace uhm! Ina jinki. Cikinsanyita tace yaya fushi kayi? Don Allah kayihakuri kada ka kwana kana fushi dani kaji.Yace to naji na hakura, amma saikin cemin I luvu.Tace, kai yaya don Allah....Au bazaki fada ba?Saika ce mai koyon magana ta fada da dai-dai, iluv u, tayi saurin kashe wayar. Yayi dariya yanamaijin dadin hankalin zeey din tashi dakuruciyarta.Da asuba yayi sallama da iyayensa da iyalansa,jirginsu ya daga zuwa bayelsa.... Da asuba yayi sallama da iyayensada iyalansa, jirginsu ya daga zuwabayelsa.Zainab suna tare da hajiya bata dawata matsala, hajita macece maibarkwanci da sanin ya kamata. Tai tanusar da ita yanda zata zauna damijinta, da yanda zata rinka yi masabiyayya.Ga 'yan gidansu su sadik, faruk, dahamza, sun riga sun saba hirarsu awajen hajiya, to dole wajen hajiyansuke tahowa nan gidan zainab dindon haka zainab take cikin nishadi,kullum tana ganin kamar a gidatake.Aunty sadiya ta sai musu littafankaratu, tunda ta karanta matar so,saita ji lallai itama tana so tayi huldada aunty hadizan nan, ko don tabata shawara ma kan nata auren,gaskiya zata nemeta dan ta samushawar wari da zasu tallafa mata garayuwar auren su.Ta jawo wayarta ta buga mata,ringin daya biyu ana uku ta dauka,"hello wake magana?Aunty hadiza bakuwace ina wuni?Lafiya lau."ya gida ya harkoki?Alhamdulillah.Aunty ina karanta wani littafi matarso, sai naji matsalar khadija, wallahinima ina cikin matsala.Matsala kamar ya ya? Mijin ne bayasonki? A'a yana sona, auren namu nenake ganin kamar na cin amana.Daga nan ta bata labarin komai dayanda akayi auren.Aunty hadiza tayi dariya tace, zainabkika ce sunanki ko?Tace, eh.Aunty hadiza tace Allah sarki gaki dasunan 'yata zeey auta, haba zainabkada ki bada mata mana akan watasaiki ki farantawa mijinki alhali bawaje daya kuke da ita ba.To ki saki jikinki ki farantawamijinki rai, du abunda kika san zaisashi farin ciki kiyi masa, ki kyautatamasa, abokiyar zamanki ki riketa dadaraja da mutunci, kada ki bari wataharkar raini ta shiga tsakaninku.Kada ki sake kiyi mata rashin kunyako ki wulakantata, yanda kike ganinmutuncinta da darajar a da, to kikara ninkawa akan na da din.Amma zainab na fuskanci ke yarinyace baki san komai ba, don haka zangyaraki, zan koya miki yanda akegyara jiki, na koya miki yanda akehada turare na ruwa dana wuta, fararhumra da baka da kulacca, hadinman gashi da zaiyi tsantsi da tsawo,ya rinka sheki da yana daukan ido.Sannan na koya miki yanda akehadin lallen kunshi wanda aketurarawa jiki yana kamshi, sai yayiwata biyu a kafarki bai fita ba.Tayi caraf tace, don Allah auntyyaushe zaki koya min? Wallahi inason kunshi da gyaran jiki, kumawallahi inason turarunkan nan masukama jiki da kama daki.To shikenan zainab, zan rubuto mikisu na turo miki.Yauwa aunty nagode, Allah ya sakada alkhairi. Don Allah aunty sainajiki.Uhm! Karki damu."to aunty, ki huta lafiya.To nagode.*** *** *******lawisa bayan kwana uku tazo,mansura ta tareta da murna, ya akayimutuniyar, kinje?Ai naje, ga abubuwa ya bayar ta fitoda kulle- kullentq,wannan gashi aruwan wanka zaki zuba masa,wannan ki barbada a shimfidar dazai kwanta, wannan kuma kiyi kokarikisa musu acikin abunda zasu ci.Gaba dayansu ita dashi zasu tsanijunansu, baza taba jituwa ba har saian raba auren."yauwa aminiyata nagode, gaskiyikinyi min kokari, amma kuma wanihanzari ba gudu ba kinsan Aliyubaya gari kuwa? Ta dafe kirji, ina yatafi?Yau kwanansa biyu da tafiyakaduna, jiya kuma sun tafi bayelsa,zasu yi sati hudu.Lawisa tace ba yanzu maganin zaifara aiki bama kenan, to da ita yatafi?Mansura tace, haba ina zashi da ita,tana can inda ya ajiyeta.To mu shirya muje gidan muci matamutunci, mu tsorata ta mu fakiidonta mu zuba mata maganin aabincinta ta tsane shi kafin ya dawo.Daya dawo ta burkice ta zuba masarashin mutunci, ke kuma saikiyi masaamfani dana wajenki, shima yatsaneta ya burkice ya saketa, kingashikenan mun samu aiki a saukake.Mansura tace, ai dole sai dai mu barisai ya dawo, don bata yanda zanyinaje gidanta.Saboda me? Lawisa ta tarinumfashinta.Ai hajiya kakarsu tana gidan.Lawisa tace ai kaji, munafukai kawai,wato har gadinta akeyi, ki nemi wajeki boye, kawai idan ya dawo din saiayi amfani dashi.To shikenan lawisa nagode**** *** ******da safe suna yin break sadik ya shigoda sallama, ya gaida hajiya sannanzainab ta gaisheshi, sadik yace hajiyakin gama mutafi? Don nayiwa likitawaya yana asibitin."hajiya tace, nagama mana, nida nakeshiri tun asuba. Zainab tace, donAllah hajiya zan biku asibitin, hajiyatace, waya gaya miki mace tana fitaba tare da iznin mijinta ba? To donAllah hajiya na buga masa wayar kigaya masa?Sadik yace a'a wallahi bazata gayamasa ba, ba mijinki bane ki gayamasa da kanki mana.Zainab tace, kai don Allah, yayasadik wai ina ruwanka ne? Don Allahhajiya kinji, kinga ni kadai zaku baria gidan shiru bazan ji dadi ba.Hajiya tace saika ce wanda zamushekara a can, naga dana gamaganin likitan nan zan taho ba indazan biya.Ta zumbura baki cikin shagwaba,nidai hajiya bazaki tafi ki barni nikadai ba, inma bazaku je asibitindani ba, to ku ajiyeni gidan yayani'ima, inku dawo saiku biyo ni mutafi.Hajiya tace banki taki ba amma farabugawa mijinki waya, abunda yaceshikenan.Sadik yace hajiya kema kin wanidaka ta tata, sai wani lallabata kikeyi, ki kyaleta ki taho mu tafi, hajiyatace ai dole.... [9:22AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**18 Hajiya tace, ai dole na lallabata, mijinta amana fa ya barmin ita. Sadik haushi ya cika shi, don shi yana da wajen zuwa su kuma gashi suna bata masa lokaci. Sadik ya fito da wayarsa ya buga, can Aliyu ya dauka, hello sadik kun isa asibitin ne? Yace, wallahi zainab tana ta bata mana lokaci. Yaya Aliyu yace bani zainab din. Ya mika mata wayar. Tace hello, yaya, yace zeeyta ya akayi su hajiya basu tafi bane? Tace, don Allah don Annabi, yaya mu tafi tare na rakasu, tsoro nakeji ni kadai a gidan." haba zeeyta, ko zaki fita ai saina dawo mu fita tare, yaushe zan bari ki fita ni ina nan wani gaular ya kallar min ke. Yanzu ma munyi yanda zamu bullowa mutanen, damun gama zanyo miki waya muyi hirar mu har su dawo, yanzu ki bawa sadik wayarsa, kiyi wa hajiya bye-bye kice sai sun dawo, Allah ya kiyaye hanya, kinji zeeyta? Amma fa kada ki damu, kiyi hakuri kinji? Tace, to yaya na hakura. Yauwa zeeyta Allah yayi miki Albarka. Amin yaya." ta mikawa sadik wayar ya kashe yasa a aljihu yace hajiya mu tafi. Zainab ta rakosu har kofar falo da dariyarta, tana musu Allah kiyaye hanya. Hajiya taji dadi a ranta ta yaba hakurin zainab da biyayyarta. Suna fita tasa mukulli a kofar falon ta rufe, ta shige daki ta fada gadonta, ta jawo wayarta ta buga. Ringin biyu aka dauka, hello, aunty hadiza kiyi hakuri kada kiga na dameki. Lah haba bakomai wallahi, ai irinku muke so masu son gyara aurensu. To aunty dan Allah ki fara gaya min sirrikan turarukan. Kin shirya na fara gaya miki. Eh na shirya aunty (so wajen yanda ake hada turarukan na tsallake bt inkuna son yanda akeyi zan rubuta muku bayan mun gama). Zainab ta shiga tunanin irin nasihar da malamansu suke yi musu game da zaman rayuwar aure, ta tuna irin burin da suka rinka ci na yanda zasu kyautatawa mazajensu, to ita gashi yanda nata auren ya kasance mata, dole ta share komai ta rufe idonta ta nunawa mijinta kulawa ta musamman. Tun daga lokacin ta kasance bata bacci da dare, ta kara kusanta kanta ga ubangiji tana yawan yin nafilfili, tai ta kirari ga ubangiji tana rokonshi daya bata ikon yin biyayya ga mijinta, Allah ya tsaresu ya kuma karesu dukkan wani sharri da bala'i da zai tunkaresu. Allah ya hade kansu da abokiyar zamanta. Mijinta kuma, Allah ya karesu, aikin da suke yi Allah ya basu nasara, ya kuma dawo dasu lafiya. Kullum saita yi tashin dare tayi nafila da wa'yanan addu'o'in, hajiya ta rinka jin dadi tana kara karfafa mata gwiwa data ci gaba dayin hakan, hanya ce ta tsira, alamomi ne kuma daga mace tagari. Ta sake bugawa auntynta waya cewar, don Allah duk turaruka data lissafa ta hado mata, harda man gashi da turaren tsuguno na jiki dana dakuna. Aunty tace kada ki damu zan kawo miki harda hadin kayan itatuwa da zakiyi amfani dashi na karin ni'ima. Tayi 'yar dariya, tace kai aunty har kin bani kunya." kwana hudu a tsakani auntynta ta hado komai ta kawo mata. Cikin lokaci kankani zainab ta canja tayi wani irin kyau, fatarta ta goge sosai saboda turaren jiki data keyi, kamshi ya kama jikinta ko yaushe tana cikin kamshi mai dadi. Dakunanta kuwa duk wanda ya shiga baya so ya fito saboda fitinan kamshi da mutum yake shaka, gaba daya gidan nata kamshi yake mai dadin shaka, du saida ta dibarwa 'yan uwanta aunty sadiya da yaya ni'ima. Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah, yau Aliyu satinsu biyar kenan a bayelsa, sunyi kokari su dawo a sati biyu da suka ce zasuyi to abun ya ci tura, gashi har sunyi sati biyar, yau da mangariba hajiya tana daki tana lazimi, don intayi sallar magariba bata tashi daga wurin sai tayi sallar isha. Zainab tana falo tana shan romon kaza da aka dafa mata da magangunan karin ni'ima, irin cikin kayan da auntyn nata ta hada mata. Wayarta tayi kara ta dauka, tace hello, yayana, kaki ka dawo yaya sai yaushene? Yace, au zeeyta kina so na dawo ne? Ina so mana, yaya nafi so ka dawo gida." to gaya min me kika tanadar min? Me zaki bani? Zaki shayar dani madarar soyayya? Kai dan Allah yaya ni bana son irin wannan maganar. To gaya min wani iri kike so? Tace nidai kawai so nake ka dawo to kin yarda in na dawo zamu rinka kwana gado daya tare na jiki manne a jikina, ina ririta ki inayi miki lallamin kauna? Tace don Allah yaya kabari. To shikenan tunda bakya so na dawo. Yaya inaso mana, yaushe zaka dawo? Yace insha Allahu yau saura kwana shidda na dawo, amma ki sani dana dawo zan yaye miki wannan hijabin kunyar, don ni take cuta." tace, yaya nidai don Allah saida safe." yace, au abin ma hakane, shikenan mu kwana lafiya. Da safe zainab take gayawa hajiya maganar dawowar yaya Aliyu saura kwana biyar, hajiya ta rangada guda tace, ina baiwar Allah nan data miki turarrukan nan tazo ta gyara minke, bani lambar wayarta na kirawota da kaina. Washe gari auntyn suka zo da aka fara gyaran amarya zainab, kwana uku ana gyaran jikin zainab, ranar kwana na hudu akazo akayi mata kunshi, akayi mata sarkar kafa data hannu. Ana gamawa aka wuce da ita salon, aka gyara mata gashi suka dawo gida, zanso kuga yanda wannan tauraruwar mata take. Saimun hadu a littafi na uku Sai night kuma😜😜😜 [9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**1 To yanzu mai kika shirya na tarar angon naki? Cikin jin kunya tace "aunty me kike ganin za ayi masa? Ina ganin ayi masa girkin zamani. Karfe nawa yace miki zasu iso? Tace, karfe hudu zasu iso gida. To gobe saiki tashi da wuri sai kiyi masa satisfishal din girke-girke, dakko littafi da biro na koya miki wasu girke-girken. Ta dakko da sauri ta rurrubuta mata wasu, tayi mata sallama ta tafi. Da safe tasa aka turo mata mata guda biyu 'yan aikin gidansu don su tayata aiki. (zan wuce wajen grike-girken nan). Ta gyara tebir din ta shimfida leda me cin bakin les da adon fulawoyi, akan tebir din ta jera saitin filas din akai guda uku, daya farar shinkafa, daya jalof din makaroni, daya miyar kaji. Sannan ta jere saitin tangarayen nan guda biyar, daya soyayyan kwai cikin nama, daya kuma samosa, daya spring rolls, daya kuma gasasshen nama me romo ta dasa fulawa a tsakiyar tebir din. Su jimmale suka gyara mata gidan suka share ko ina, suka goge yana ta zuba kyalli. Hajiya data ga yanda aka gyara tebir din aka cikashi da kayan abinci, ta rinka gyada kai tana murmushi, tana cewa ma me cikin zani yanda zaiyi da wannan kayan abincin. Ko giwa ne shi ai ba zasu ciyu ba awajensa. Hajiya tace, jimmale tunda kun gama kunci abinci, ku zo mu tafi tare daku. Zainab ta rike hajiya ta marairaice mata, don Allah hajiya kiyi zamanki kada ki tafi." hajiya tace, ke baki da kai ne, yanzu sadik suka gama waya dashi jirginsu ya sauka ya za ayi na zauna har ya sameni? Haba hajiya ki zauna mana mu duk ba jikokin ki bane? Hajiya tace, uhm kyayi kya gama jummale ku shige muje. Zainab tace, hajiya ai baki cinye abinciccikan naki ba. To taya zan iya cinye wannan girke- girken haka? Jimmale kwashi ki saka min a mota, in munje gida naci." zainab ta rike hajiya tana kuka, hajiya tace, to ai ke kinga halinki, bakya so kenan inya kuma tafiya inzo in zauna miki ko? Tace a'a hajiya inaso, don Allah ki dawo, tace to zan dawo, amma sai kinyi shiru, kije ki shiga wankan. Tace to, ta tafi dakinta ta shiga toilet ta fara wanka, hajiya dasu jimmale suka yi saurin tafiya kafin ta fito. Yaya Aliyu kuwa karfe uku suka sauka da abokansa su bakwai da faruk, usman, hafiz, Anas, Amir da bashir sai Aliyu na bakwai. Gaba daya suka ce, sai sun biyo Aliyu sun gano amarya tunda yayi aure su suna nesa, bai gayyacesu ba. Yace, to kuma ba sai ku bari sai wata rana kwazo ba, sai yau mun dade bamu ga juna ba, ina dokin ganin 'yar kanwata kuma saiku bini ku katsemin hanzari? Usman yace, kaji zancen banza, yana wani kanwarsa wa ya sani ma ko tuni ya gama aiki? Faruk yace tun yaushe kai ma kasan rawar kan nan da yake yi kasan ba haka kawai bane, ya dandani zumar amarci. Aliyu yace, don Allah ku bari ita fa karamar yarinya ce, wallahi yanda nake son zainab nake tausayinta, bazan iya yin abin da zata wahala ba, aini rainonta zanta yi sai nan da wasu shekaru. Gaba daya suka sa masa dariya suna tafa hannu, tare da cewar, maji magani, faruk kaine na kusa dashi ka bamu labari. Ita kuma mansura tana ta shiri ita da Ahmad suka shiga mota, suka shiga mota sukayi filin jirgi tarar Aliyu, suna isa filin jirgi suka hangoshi cikin abokansa, Ahmad ya tafi da gudu yana kiran daddy! Daddy." Aliyu ya juyo da sauri ya daukeshi ya rungumeshi suna dariya su duka biyu. Mansura ta karaso inda suke tana dariya tace, barka da sauka, Aliyu yayi dariya ya riko hannunta ya sumbata, barka dai uwar gida sarautar mata, mun sameku lafiya. Lafiya lau." ya nuna mata abokansa du da dai tasan wasu daga ciki, ta gaishesu suka amsa cikin fara'a, suka rinka tsokananta mun biyo ango zamu ga amarya. Tayi dariyar yake tace, so ni ba zaku je nawa gidan ba, sai gidan amarya? Suka ce a'a mu mun isa? Ai sai mun fara zuwa gidan uwar gida tukun. Tayi dariya tace, to kun fitar da kanku." gaba daya suka shiga motoci suka yi gidanta. Zainab tana fitowa wanka tayi sallar la'asar, gaba daya gidan ta turareshi, sihirtaccen kamshin jikinta kuwa sai tashin fitinanun turarukanta yake yi. Dai-dai da gashin kanta saida tayi masa nashi turaren. Ta saka sabuwar super acikin kayan lefenta. Tayi kyau sosai, fatarta tayi wani sulbi da santsi, sai wani shnin take, tana wani daukan ido, ta lika kati ajikin kofar shigowa falonsu, dole du wanda zai shiga falon sai ya gani. Katin me kyau ne, yanata kamshi fari me fulawa, anyi rubutu da hausa da ruwan gwal, ga abinda yake jiki. BARKA DA DAWOWA YAYANA INA TAYAKA MURNA DA SAMUN NASARA AKAN ABUNDA KUKA JE. tana lika wani katin akan tebir din data jera kayan abinci taji tsayuwar motoci, taji gabanta ya fadi, ta runtse idonta ta karanto addu'o'i na yiwa Allah godiya, da isowar yayanta lafiya. Ga abunda yake jikin katin tebir din kamar haka. GODIYA ME YAWA TA TABBATA GA ALLAH DAYA DAWO DA YAYANA CIKIN IYALANSA LAFIYA. tayi saurin shigewa daki, yaya Aliyu daya taho da tawagar abokansa akafar falo yaci karo da katinnan, ya kalli abokansa sukayi dariya tare da jinjina masa. Suna bude falon fitinan kamshinan ya dakesu, gashi ya hade da sanyin A.C sai ya rinka feso musu kamshi mai dadi. [9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**2 & 3**3 Kowa ya shaka sai ya lumshe ido. Abun bai kara rikitar dasu ba, saida suka shiga falon suka rinka taka canis cafet, kafarsu tana nitsewa cikin taushi babu wani datti ko ina a gyare kal-kal yanata sheki. Ga falon ya tsaru, dole ko kai ka gani ya baka sha'awa, gaba dayansu suka zube a kujeru suna ware gajiya, kusan du a galabaice suke saboda yunwa. Faruk ya hangame baki yana ina matar gidan ne, baza tazo taryar mai gida ba? Aliyu yace, bari mana kada ka tsoratata da wannan muryar taka." ta sako hijabi ruwan atamfar dake jikinta, a hankali ta turo kofar tana murmushi, tayi musu sallama, tace don Allah kuyi hakuri. Gaba daya zuba mata ido sukayi, suna kissima kyawun zainab da hankalinta, Aliyu kuwa wasi-wasi yake a ransa, anya zeey dinshi ce takoma haka? Tabbas du yanda zeey dinshi takoma, bazai taba mantata ba. Ta durkusa a gabanshi, tace "yaya ina wuni, kun dawo lafiya? Yayi firgigit kamar wanda ya tashi daga bacci, yace zeeyta mun sameku lafiya, ya kike? Ya na dawo na sameki zeeyta? Tayi murmushi kawai, ba tare da tace komai ba, ta gayar da abokan nasa, suna ta zolayarta da tsokanarta ita kuwa kunyarsu take ji da nauyinsu. Tace yaya kuzo kuci abinci a tebir mana kona kawo muku nan? Yace zeeyta har yanzu baki daina shiga kicin yin girkin nan ba? Ni dai ina tsoron kada ki kone ko ki yanke, nasa a nemo miki mai aikin girki. Ta dan marairaice, tace haba yaya meye amfanina, in banyi ma girki ba? Allah yaya bana iya cin abincin 'yan aiki, saina tajin kyankyami, koma tashin zuciya. Usman yace gaskiya kin burgeni, inason mutum mai iya tattalin lafiyarsa. Faruk ya mike yace nidai kuzo muje ga tebir din nan don yunwa nakeji. Nasir yace badai koshi zakayi ba, abunda aka shiryawa mutum daya mun debo jiki har mu bakwai kowa yadan taba mu bar mishi abincinsa. Zainab tace, haba don Allah ku cinye, ni wallahi saina shiga kicin na girka muku wani, ai ba wahala. Aliyu ya riko hannunta, kyalesu zeeyta, sa karata a hotel ba zasu wahalar min dake ba. Usman yace, ai aci har dakai a hotal din. Zainab ta musu ja gaba har inda tebir din yake, suka jawo kujerun duk suka zauna. Tana fara bude abincin cikar kamshi ya rinka bugunsu, suka rinka hadiyar yawu. Tana bude musu abincikan suka ga uwar dinar kamar awajen walima zata fara sabis dinsu Aliyu ya kirata, zainab jeki daki ki huta, tace to. Cikin sanyinta. Shikuwa Aliyu kishintane yasa yace tabar wajen, saboda lafiyayyen kunshi daya hango a hannunta, sun shagala suna cin dinar sunata santi, Aliyu ya silale yayi daki wajen amaryarsa. Ya tabata yana sansanar kamshin jikinta, cikin sarkewar murya tace yaya bazaka ci abinci ba, ka taho nan? Yace, zeeyta kin rikitani dayawa, wai kece kuwa zeeyta, me kike ci kika canja haka, bana kusa bare nace abune ya karbeki, gaya min zeeyta meye sirrin wannan kyau da kika kara? Ba ruwanki kinyi kyau kin kara fari abunki bakya tunanina, ko zeeyta? A hankali, tace haba yaya wa ya gaya maka? Gashinan kuwa na gani kin kara kyau da murjewa, ni kuwa ina can tunaninki ya hanani sukuni, kullum saina yi mafarkinki. Ya kamo hannunta ya rinka sha'awar kunshi ya rinka sa zara-zaran yatsunta abakinsa ya tsotsa, yana lumshe ido. Ya rinka shafa tafin kafarta yana yaba kyan kunshin, ga laushin fatarta da wani tsantsi da yaji tana yi, dadadan kamshi daya yake shaka a jikinta du yasa shi ya birkice. Ya taba nan ya taba can, ita kuma du ta rasa yanda zatayi da kunyarsa du ya wani birkice mata kaman ba yayanta ba. Taji yana kokarin wuce gona da iri, ta rike hannunsa tace don Allah yaya kabari, yayi kasa da muryarsa yana cewa me zan bari zeeyta, wa yayi miki wannan kunshin? Ya zame dankwalin nata, ya rinka yamutsa gashin nata yana tura kansa cikin gashin nata, ya ilahi, wannan wane irin kamshine me dadi da saka ka shiga wani hali na yanayin sha'awa da shaukin bege? Wai shin yaya zaiyi da zeey dinshi ne, anya zai iya hakuri da yarinyar nan har zuwa wasu shekaru daya ambata? La a ina! Irin wanan jiki haka mai tsantsi da laushi, kamar tufa. Ta rike hannunshi cikin shagwabarta tace, yaya kabari, banaso. Idonsa yana lumshe ya marairaice mata, yana cewa, ni mijinki nefa zeeyta kike gaya min haka, bakya son aljanna? Cikin sanyita tace kayi hakuri yaya. Wayarsa tayi kara, yana dagawa yasa dariya, yana cewa aini na manta daku ma, gani nan fitowa. Yana fita suka haushi da tsiya, usman ya kwala mata kira amarya zamu tafi. Ta sako hijabinta ta fito tana dan murmushi, suka ce amarya fa mun gode, kin cika mana ciki da girki masu dadi, kin hada mana walima tunda bamu samu zuwa ta aure ba ko, amma ma hadu ata suna, nan da wata tara ko? Taji kunya sosai ta sunkuyar da kai, Aliyu kuwa ya zuba mata ido, don yaga yanayin da zata nuna. Suka dire mata dubu goma-goma, cikin sanyita tace don Allah ku barshi ku debi kudinku. A'a amarya kar muyi haka dake sai gani na biyu inmun kawo iyalanmu. Tayi musu godiya suka tafi, ta shiga toilet ta hada masa ruwan wanka, ta zuba turaren wanka, nan da nan ruwan ya dauki kamshi. Yana shigowa ya fada toilet, yaji dadi daya samu ta hada.. Fitinannan kamshin danaji shiyasa ni tsayawa da rubutu batare dana shirya ba, amma dai bari naci gaba Yana shigowa ya fada toilet, yajidadi da yaga ta hada masa ruwayana ta tashin kamshi, ya rinkatunanin irin wannan kamshi iri-iri dayake jin a wajen zeey din tashi, yanawankan cikin nishadi kamar kadaruwan ya kare.Ya fito ya shirya ya fito kan tebirdin, ya kwala mata kira ta fito ahankali cikin nutsuwa salon yangartatana tafiya das-das kamar bata sontaka kasa.Ya zuba mata ido yana kare wakwalliyarta kallo, amma tunaninyanda akayi ta kara samunsihirtaccen kyau na ban mamaki.Tace, yaya gani, yace zauna. Yayindaya gyara mata kujera, ta zauna tasunkuyar da kanta tana wasa dayatsun hannunta.Yace, bisimillah muci abincin, taceyaya na koshi.Yace, a'a zeeyta kada muyi hakadake, 'yar kanwata nasan wannanhidimar da kikayi mana bata barkikinci abinci ba, kisa hannu mucikona yi miki dura...um-hum.Ya karasa taji kunyarsa tasan tanajin yunwa, amma yaushe ammayaushe zata iya cin abinci a gabanshiyanda ya tsareta da kallo haka, batayi aune ba taji abinci a bakinta tace,don Allah yaya kayi hakuri zaci dakaina.Yace, to ci.Ta fara ci a yangace.Ya rinka ci yana yi mata santi, waidama zainab makarantar koyon girkikika yi ne?Tayi murmushi yana ta cika bakiyana yi mata santi, har ya koshi.Ya mike akan doguwar kujera yana,wash nafa gaji, kamata yayi karnakuma fita saida safe."wayarsa ta dameshi da burari, yadaga "hello mansura.Tuni zainab ta bace daga wajen,haba Aliyu wulakanci zakayi minkadawo daga tafiya ko zaman rabinawa baka yi damu ba, ka fice kayitafiyarka, kayi zamanka?To naji gani nan zuwa, ya kirazainab a waya ta fito, ya mika matahannu saita noke ta zauna akasa kankafet.Yace bari naje wajen auntynki yanzuzan dawo." tace adawo lafiya, Allahya kiyaye.A gidanshi mansura ta taho masa dalemo daya sha magani maimakonkaji kamshi sai baurin maganin.Tasan sarai Aliyu yana da kyankyamikamar likita yake, wajen tattalinlafiyarsa.Ahmad ya taho da gudu ya fadacinyar babansa yana murna, kafarsata zunguri jug din lemon ta bare,mansura ta zuba masa uban dukandaya gigita shi. Ahmad ya kwalawata irin karan kuka ya rukunkumeAliyu. Shikuma Aliyu ya rinkararrashinsayana shafa masa wajen ransa yayimasifar baci, ya zuba wa mansurawata irin harara data sata nutsuwa,ya doka tsaki yayi bal da jug din yatarwatse, ya dauki dansa yayi wajedashi.Mansura tayi tsaki, uban 'yan bakarzuciyar tsiya. Yaro ya jawo min asarakace bazan hukuntashi ba.Zainab tana zaune a falo tajisallamar Aliyu, ta dago kai tanaamsa sallamar, karaf suka hada idoda Ahmad, da gudu Ahmad din yataho ya rugumeta yana dariya, auntymamita ina kika tafi na dade banaganinki?Ta rungumeshi tana shafa kansa,Ahmad dina ka kara girma, yakaratu, kana zuwa islamiya ko? Inazuwa mana, jiya ma saida malam yadakeni, wai ban iya komai ba, yacena gaya masa sharrudan sallah, dafarilla sallah da watanni musulunci,du ban sansuba shine ya dakeni.Ranta ya baci data ji zancen duka,tace to malamin bai rubuta muku, yakoya muku ba?Yayi mana, ni kuma na manta, danazo gida na dakkowa mamana, naceta biya min, tace, na kyalleta baccizatayi. Aunty mami dama kece mekoya min bakya nan to ya zanyi?Shiyasa malam yake dukana.Tayi tsaki, kayi hakuri yarona,zamuyi zaman mu tare dakai anannai ta koya maka kaji.Yauwa aunty mamena, nafi sonzama wajenki, mamana fadane daita ga duka.Du Aliyu yana kwance kan duguwarkujera yana jinsu, ta fara koya mishiyana nanatawa, saida taji ya rike yaiya tukunna ta shiga kicin ta hadamasa abinci da lemu, ya rinka ciyana santi, aunty mami kin iya girkimai dadi, anan zanyi zamana, naitacin girki mai dadi.Tayi dariya Allah Ahmad dina? Kacedaddynka ya kawo ma kayanka kadawo nan kaji.Aliyu yana kallon yanda take tatattalinsa, koda daddare ma dayakoma gidan mansura yi matasallama ta tambayeshi ina ahmad,banza yayi mata, bai kulata ba, to bafuskar da zatayi masa fitsara, donhaka taja bakinta tayi shiru.Lokacin da ya dawo tuni sunyi bacci,suna gado daya ya kallesu cike dasha'awa yayi murmushi, sai ya yayebargon ya shiga tsakiyarsu.Daya fita sallar asuba ya wucedakinsa, da safe yana jinkwaramniyar Ahmad da zainab akicin ta gama komai ta jera akantebir, tayiwa Ahmad wanka, ta shafamasa hoda tasa mai kwalli, tasamishi dan pant, tunda ba kayansa, tatura shi tace yaje gaida daddynshi,ita kuma ta shiga wanka. Aliyu yabude cikin kayan tsarabarsu ya fitomasa da t.shit masu kyau, Ahmad yasaka yana ta murna.Suna kan tebir suna break, wayarAliyu tayi kara, Ahmad yayi saurindauka.Mansura tace, Ahmad kana ina?Ina wajen aunty mami, tana banidadi dadi.Tana ina zainab din?Gata nan.To bata wayar."Ahmad yasa mata wayar a kunnantaaunty ga mamana.Zainab ta rikice ta tsorata, cikinrawar murya tace aunty ina wuni?Ta wani daka mata tsawa dalla canyi mun shiru munafuka.Aliyu yayi saurin karbar wayan yasaa kunnansa, ba tare da yayi maganaba.Mansura taci gaba munufaka...... [9:16PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**4 & 3**5 Aliyu yayi saurin karban wayar yasaa kunnensa, ba tare da yayi maganaba.Mansura taci gaba, munafuka,annamimiya, ki dawomin da dana,ko shima za ayi min iko dashi ne?Ki karba kun hada munafuncinku kinauri Aliyu dama ashe duk abundamukeyi idonki yana kaikina sha'awar Aliyu, to kin aureshimatsiyaciya, kuma ki sani kedasamun kwanciyar hankali har abadaa gidan Aliyu.Shiya katseta da cewar, to naji nakuma gode, ba zainab kika zaga bani kika zaga, tunda iyayenmu daya.Kuma ki sani, wannan shine na farkokuma na karshe, du sanda kika sakeyin kwatankwacin haka, sai kin rainakanki, tace to naji amma a kawomindana, don ba ita ta haifa min shi ba.Rawar kan da kake yi da zirgillo kadaasa ma da yanzu saiku jira ta haifatukunna."ya wani daka mata tsawa acikinwayar, daya sa tayi saurin kashewayar, ba shiri.Ya kira direba yace, ya kai Ahmadislamiya, ya biya ta gidansa yadaukar masa jakarsa.Zainab da tunda Aliyu ya karbawayar a hannunta ta shige daki.Ya bita dakin, tana zaune a bakingado tayi tagumi, ya janye taguminyace, meye haka, bana gaya miki kidaina babu kyau ba?Tace, to yaya nadaina."ya riko hannunta, meye zeeyta fushikike yi? Gaya min menene, me akayimiki?Tayi murmushi bakomai yaya bafushi nakeyi ba.Taso muje na baki tsarabarki, ya rikohannunta har dakinsa ya jawojakunkunan daya zo dasu, ya zugejakar ya ringa fito da kananan kayamatsatsu yana buda mata, tana ganiyana yaba kayan, har kala 20 yace,kinga irin kayanan su zaki ringasamin dagani saike. Tace yaya yazansa wadanan kayan kanana nefa.Toni ba mijinki bane? Na fita dagasahun yaya na koma mijinki, kikwasa kije ki saka daya ajikinkiyanzu, kizo muyi hira yau ba indazanje, jeki canja kayan. Tace yaya...Ya daka mata tsawa, bana songardama. Da gudu ta kwashi kayantayi waje.Ta tsaya gaban madubita, ta sakawata damammiyar riga iya cinya,tana da hannun breziya, adon les nea gaban kirjin rigar, rigar ta lafeajikinta, tayi mata kyau, ta juya tasake juyawa agaban madubi tayitsaki, ya ya za'ayi na saka wannanrigar na tsaya a gaban yaya?Karar wayarsa ce ta katse masatunani wai ta sameshi a sama.Ta dauko after dress ta daura akankayan, ta yane janta da siririnmayafin ta karawa jikinta humra tafice ta haura sama.Ta shiga falon baya ciki, ta budefilin shakatawarsu, yana gurin kuwakan katifar ruwa, gabanta ya fadiyanda ta ganshi daga shi sai shimifara kal da ita, ta dame masa jiki dagajeren wando iya cinyarsa, tatsorata da yanda da yanda ta ganshidon ita bata taba ganin babba haka,saidai yaro kamar su Amadi.Ya mika mata hannun yauwa zeeytazoki bani labarin abunda ya faru daina bayelsa.Ta marairaice fuska kamar mai shirinyin kuka, ya tashi ya tako a hankaliyazo har inda take, ya cire after dressdin ya ga yanda rigar tayi mata kyaukamar 'yar budurwar baturiya, yashafa kanta, ta saki kuka mara sauti,ya rinka rarrashinta yana bubbugabayanta, na rarrashi.Haba zeeyta nine fa mazajenki, ninefa mazan jiyanki, duk kin mantaalkawrinka da kika yi min.Kinki sakin jiki dani, ko hira bakyasonyi dani. Zeeyta mena miki bakyasona?Ta daga kanta, yaya ina sonka manakunyarka da nauyinka nake ji, yayakaine fa yayana dana daukekatamkar uwar data haifeni." nasan dahaka zeeyta, shiyasa nake tattalinkinaga bazan iya bawa wani ke ba.Don kada ya cutar min dake, ki sakijikinki zeeyta bazan cutar dake ba,kuma ni ba wani abu zanyi miki ba,ko wani abu zai shiga tsakanina dakesainan da shekara uku, sannan kinshekara 20 nasan kin danyi kwari,yanzu kuwa makaranta zan mayardake.Tayi dariya tace yauwa yaya nagode,kullum makarantar itace araina.Nasani zeeyta na dade da saninburinki." ya zaunar da ita a cinyarsayana shakan ni'imtaccen kamshinjikinta, yana bata tufa abaki.Zainab ta saki jiki da yayanta,saboda abunda take gudu yace,bazai kusanceta ba sai nan dashekara uku sannab tayi kwari, lallaiyayanta mai kaunarta ne datausayinta.Yanzu ta riga ta saki jiki dashi sosai,ya riga ya koyar da ita salonsoyayyarshi mai tsaya ma ta araibasu da abun sawa sai kananan kaya,to daga ita saishi, ba wani wandayake shigo musu har bata so taji zaifita, don bata so taji zaiyi nesa daita, ko yaushe tana makale ajikinsatana zuba masa shagwaba, shikumadu ya wani sukurkurce akanta, donshi yana tunani anya zai cika wnnanalkawari daya dauka nan da shekarauku? Yarinyar tana birkita masakwanya, da lallausan jikinta dashamararren kamshinta.Du sanda suka kwanta gaba dayakarfin hali yake yi.Sai ya manneta gam yake samunsauki, to yau gashi kwanansa uku dadawowa, da kafin ya tafi ya matakwana hudu, yanzu ya cika kwanauku in an hada kwana bakwai kenan,a bisa ka'ida yauce ranar da zai komagidan uwargida. Du ya damu ya rasaya zayyi da zeey dinshi, shidaigaskiya ba zai iya barinta a gidan itakadai ba.Yayi nisa cikin tunani, yayinta yajikamshinta, ya dago kai yanakallonta, tana sanye da dogonwando na jeans da farar bes ta tsukeda bel, ta lumshe idanuwan nannata,... TA lumshe idanuwan nan nata, mekamar jin barci, ya miko mata hannutazo ta shige jikinsa ta kwantaacinyarsa, lallausar fatarta dakamshin jikinta shi yake karadimautar dashi, ya kara hura wutarkaunarta, da sha'awarta a ransa. Yashafa lafiyayen bakin gashinta metsawo da sheki da yake ta kamshi medadi.Mansura ce tayo waya, zainab zatatashi ya kara matseta a jikinsa, yaamsa wayar, hello, tace Aliyu najikashiru ko harda nawa kwanakin zakahada mata? Gashi har biyar tayi,kasan na shiga aiki ita kuma ta fita."yace, ai ina sane, yanzu, zan taho, yakashe wayar.Yace, zainab talatu zata zo taci gabada zama dake, kin gani yau a gidanauntynki zan kwana.Ta makale kafada, um-um ni bazankwanta ni kadai ba ka kaini gida.Ya dafe kanshi yana jin rigimar zeeydin tashi, yace zeey rigimarki yawane da ita, ina kika taba jin aurehaka? Ta zumburo baki, to yaya nikadai zan kwana adakin. ya sumbacikuncinnta, ya lallabata, taso mujemuyi ball.Tana sanye da karamar riga singileti,da gajeren wando iya cinya, suka fitaharabar gidan suna ball, sunatakokawa ya hanata bugawa, data zozata buga, sai ya gara ball din dakafarsa, tayi wani wajen, ta bita dagudu, ya kuma sa kafa ya janye balldin ta rikeshi tana tsalle tanayunkurin gara ball din.Motar mansura ce ta shigo gidan,tana ganinsu ranta yayi mummunanbaci, tace dama wannan dan raininhankalin wannan yarinyar yake kwa-kwar so? Shiyasa ni kullum yakedaure min fuska, ko hirar arzikibama zama muyi dashi?Yanzu kuwa dubi irin shigar da sukayi, suke ta wasa cikin nishadi. Tuni tasaki kan motar tayi kansu a guje.Zainab bata kula da motar datashigo ba saboda ball din ta daukemata hankali, tabi ball din da dangudunta, tana so ta kamota indaAliyu ya sake garawa.Aliyu yayi wani tsalle don ya daukezainab, ganin mansura tayi kanta damota. Amma ina kafin ya karasoharta bugeta da motar.Ya kwalla kara, tare da kiran zainab.Zainab ta fada kan gaban motar tagangaro ta fadi kasa. Aliyu yadurkusa gabanta ya dagota, yarugumeta a jikinsa, ransa yayimasifar baci, ya dago kai yayi wamansura wani mummunan kallo.Sai ya shimfide zainab gefe daya,yayi wani irin tashi kamar namijinzaki, yayi kan mansura.Du yanda taso ta dake ta kasa,domin bata taba ganin bacin ransakamar haka ba.Tana ganin ya tinkarota, tayi saurinmurza siterinta tayi baya, tuni ta ficedaga get din gidan, ya kaiwa bayamotar wata irin dukagun saida ya dan loba, ya busar dawani hucin zafi abakinsa, ya komabaya ya dauki zainab tana yi mishikuka, yaya cikina zafi yake yi min,wayyo yayana cikina zafi.Ransa ya kara baci, baya so abundazai taba masa yarinyar nan. Ammatazo ta buge masa ita harta gogemata fatar ciki. Gashi gurin yayi jini,dole ya dauki tsattsauran matakiakan mansuradon bazai dauki wulakanci ba. Bazaiiya sa ido a cutar masa da zainab ba.Ga zainab din tana kara daga mishihankali da kukanta, wanda yakekamar a ransa.Wayyo yayana cikina zafi, ya kamararrashinta, yi shiru zeeyta yanzu zankaiki asibiti, asa miki magani, kinjizainab kiyi hakuriyi shiru.Yaya karka kaini ayimin allura, banaso yaya da zafi, yace yi shiru bazanbari ayi miki allura ba.Magani za a sa miki a wajen yadaina yi miki zafi.Tace, to, ya canja kayansa da shaddame tsada, yasa ma zainab after dresstare da hijabinta, ya daukota kamarjaririya, a hankali ya jingineta kankujerar, wai du dan kada ta famaciwon, ya shiga motar ya rinka tuki ahankali, har ya isa da ita wanitsaddaden asibiti na kudi.Wani baturen likita shi yake yi matadiresin din wajen. Aliyu yana zaunea gefen gadon kan zainab yanajinyarta, tana ta raki, wayyo yaya kahanashi tabamin, zafi yaya, kace yadaina yayana zafi.Ransa ya kara baci tunanin irinhukuncin da zai ma mansura yakeya kama shafa kanta yanararrashinta, sannu zeeyta kiyi shiru,yanzu zai gama miki, ki bari yakarasa miki zeeyta, yi shiru kinji, yihakuri zeeyta sannu, yana shafakanta yana rarrashinta, har likitan yakarasa yi mata diresin din. Ya daukoallura zaiyi mata,ta kankame Aliyu tana kuka, yayabana so, kada yayi min.Ya rinka rarrashinta, yana shafabayanta, likitan yayi mata alluran takankame Aliyu tana kuka, ya rinkalailaya mata gun yana hura matakunanta, yana rarrashinta, sannu ahankali bacci ya dauketa, sannanAliyu yayi ajiyar zuciya.Ya ciro wayarsa ya bugawaummansa, tana dauka suna gaisawa,tace ina zainab? Yace umma munaasibiti.Lafiya meya kaiku asibiti?Wallahi umma yarinyar nan ce tashigo da mota har gida ta bugezainab.Umma ta dafe kai tana salati. Tajiciwo daya wa?Eh, umma ta kwale a ciki, saida likitaya rede fatar wajen.Zainab tanata kuka saboda zafi,Allah umma saina dauki tsattsauranmataki akan mansuratace a'a kayi hakuri ni zan daukimataki da kaina, idan kaine nasanabun baci zaiyi, kayi hakuri zanyimaganin abun.Yace to shikenan umma na kyaleta.Umman ta fito ta shiga dakin ummi,ta zauna take labarta mata abundaya faru.Ummi ta kama salati, tana cewakinga yarinya da rashin mutunci.. [9:17PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**6 & 3**7 UMMI ta kama salati, tana cewa,kinga yarinya da rashin mutunci,lallai har yanzu bata san Aliyu akanzainab ba, yarinyar da tun kafin yaaureta baya kaunar bacin ranta ko yaganta a cikin damuwa, amma shineyanzu zata nemi nakasta masa ita?Wallahi in bata yi wasa ba indai dangidanane ya sallameta, ya koretadaga gidan nasa.Umma tace ai shiyasa nace yayihakuri ya bar maganar a hannuna,don inna kyaleshi nasan abun bazaizo da sauki ba.Ummi tace ai gara da kika yi hakabari na gayawa Alhj naje gidan sumansuran da kaina.Umma tace to gara kije din, suyiwa'yarsu fada sosai, inba haka ba watarana zata dauko musu abunda yafikarfinsu."(nayi missng wannan page din).Saratu ta shigo tace, a'a 'yar uwasaukar yaushe?Ta kara hade rai, tace, yanzu nazolafiya meye na ganki rai abace? Taceum raina min hankali zasuyi, nikumanaje gidan na gansu cikin nishadi,har sun manta da kuncin da sukasakani.Don wani rainin hankali, sunyi shigarkananan kaya, sunata ball a harabargidan, ni kuwa na saki motar nayikanta, na bigeta, na fito nayitahowata, shine yayo min tes waikada yazo ya sameni a gidan, nataho saiya nemeni.Saratu tace, to saime, don yace kitaho? Allah yasa kinada gidan zuwaba kwararo zakije ba, indai akanwannan yarinyar ne, wallahi sai yaraina kansa, saiya zo har inda kikeyana baki hakuri.Mansura ta kwashe da dariya Allahyayata? Tace Allah ai mu bana wasabane.**** **** ****A asibiti kuwa gaba daya 'yangidansu sun hadu harda sadiya daamarya ni'ima, sai tattaunawa sukeyiakan abunda ya faru suna cewazasuyiwa mansura rashin mutunci, suumma suna tausar kan cewa ai sumazasu dau mataki.Gaba daya suna falon asibitin, suumma da su mama da ummi dasusadik. Sadiya da ni'ima ne kawai adakin, sai Aliyu daya ke gefe dayakan darduma, yana sallar mangariba,zainab ta farka tana cewa washyayana. Sadiya da ni'ima suka tasosuna yi mata sannu, ta bude ido takallesu, tace aunty sadiya yayani'ima ina yaya? Suka ce sallah yakeyi, sannu zainab ya jikin? Tace dasauki aunty sadiya, sau daya kikataba zuwar min, yaya ni'ima ke kumabaki taba zuwa ba, sai yau zaki zomin asibiti.Tace ke Abba ya hanashi ya barni nafito, ko gida fa ban taba zuwa ba.Sadiya tace ba kunjejje unguwadashi ba.Munje bikin kanwarshi, na kuma jegidansu sau biyu, mun kuma jegidan yarshi, fitata fa hudu kwata-kwata.Ya taso ya zo bakin gadon yacezeeyta kin tashi? Ta shagwabe fuskatace yayana.Ya dagota zaune ya zauna a bakingadon ya jinginata da jikinsa, yacesannu zeeyta, ya kike jin ciwon nakihar yanzu da zafi? Ta girgiza kai yadaina yaya, ba zafi yanzu.Yace yauwa Alhmdllh, yace sadiyahado min shayi, ni'ima zubo minfarfesun can.Ta rissina ta miko masa shayin datafirfita sosai, ya karba ya rinka batashayin a hankali tana sha, har saidata shanye.Ni'ima ta miko masa farfesun yakarba ya miko mata, ta kauda kaitare da cewa na koshi.Yace a'a ban yarda ba, karbi kici,tace don Allah yaya, wallahi nakoshi.Yace kinfi so nayi miki dura ko, bazaki karba kici ba, saina dura miki?Tana langabe a jikinsa, yana bataabaki harta ci dayawa.Cikin sanyita tace, yaya na koshi.Ya gyda kansa kawai, yasa tisue yagoge mata bakinta, likita ya shigo yababbata magunguna tasha, ya fesamata magani akan ciwon na busarda ciwo ne,likitan ya fita, Aliyu yace zaki yifitsari ko? Kin dade a kwance, kadaya kullar miki da mara."ya sako mata kafafuwanta kasa dagagadon ya mikar da ita tsaye yanarike da ita, suna tafiya a hankali, yarakata har toilet ta gama abundazatayi, sai ya daukota kamar watajaririya, ya dire ta a gadon nata.Ya daga mata gira tare da cewa "reu okey? Tace "yes sir"yace bari na gaya ma su ummakintashi.Ta daga mashi kai, ya fita falonasibitin.Ni'ima tace 'yar uwa kin ware yanzuba tsoron yaya dajin kunyarshi, kinsaki jiki kunata soyayyarku.Sadiya tace aini nasan wallahi komaidaren- dadewa sai yaya ya aurizainab, saboda kaffa-kaffa da yake yimata, da kulawa kasan kauna ce dasoyayya zalla.Ai hauka mansura take yi, idan tacehaka zatayi wallahi ba karamarwahalar da kanta zatayi ba, ta kumazubar wa da kanta mutunci a idonkowa, ni'ima tace aita ma zubarmutunci da ake ganinta dashi da,yanzu wa yake ganinta dashi?Zainab tace, don Allah kuyi hakuri,kada ku tsaneta, wallahi bana sonabunda zai jawo mana kiyayyardangin miji.Kishi nefa ai ita tayi da sauki,shekararsu tara da mijinta, wayataba jinsu, ta riki yarinya shekaratakwas a hannunta, lokaci dayamijinta ya aura mata ita, ta zamakishiryata.Ai tyi tawakkali ma, in wata ce aisaitayi hauka, yanzu ni yanzu ba fatanake yi ba, yanda nake jin yayaaraina yace zai yo min kishiya, auntysadiya ai saikun mike kaina daaddu'a, don saina zare.Gaba daya suka sa dariya, su ummasuka shigo gaba dayansu, ta rinkagaishesu tana murnar ganinsu, sukuma du tausayinta suke ji, sunatajajanta mata, tare da addu'ar Allahya bata sauki.Zainab tace ina hajiya bata zoba?Umma tace ai hajiya bata sani ba,Alh ne ya hana a gaya mata,... Alh ne ya hana a fada mata dan kada hankalintaya tashi.Cikin shagwaba tace ummi dake da mama daumma duk kunki zuwar min. Suka ce kiyi hakurizainab daga ke har ni'ima du bamu je muku ba.Alh ne ya hanamu zuwa yace kadamuzo mu daga muku hankali.Tace, nidai don Allah umma kuzo, umma ta dafata, kada ki damu 'yata, zamu zo ai munji dadi damuka ga kinyi kyau dake, munsan kin kwantar dahankalinki kenan, kinga ai mafi jin dadin zuwa.Abba da daddyn zainab suka shigo. Abba yacesannu 'yata ya akayi haka ta faru?Tace wallahi Abba banji shigowarta ba, da bazantsaya ba Abba, saina gudu daki.Abba yace "hukumullahi ta'ala, yace kiyi hakurikinji 'yata kada kice zaki dau fansa ko ki rainatakici gaba da bata girmanta kamar yanda kikasaba, wata rana sai labari kinji.Tace to Abba nagode.Kwanan zainab uku a asibiti, kullum ni'ima dasadiya sai sun zo sun wuni a asibitin, haka ummada mama da ummi, har hajiya data samu labaridaga baya.Har yau samarin gidan du anan suke wuni, Aliyukam dama tarewa yayi, danshi yake jinyarta,komai shi yake mata.Ya kara wani sangartata da shagwabata.Zainab ta samu lafiya, ciwon du ya kame yawarke sai dan abunda ba a rasa ba, Alhmdllh tasamu saukia ranar aka sallamesu gaba daya, gidanta sukadunguma suka yi mata rakiya, har gidanta.Gidan fes dashi, ba wani datti ko kura, dakunankuwa suna manne da daddan kamshinta data kebadawa.Bayan sallar mangariba, kowa yayi musu sallamasuka tafi suna me addu'ar Allah ya kara matasauki.Ta kwanta lamo akan kujera Aliyu ya shigo dagarakiyar su hajiyaya tabota, ya akayi ne babyna? Ta lumshe idoyaya bacci nake ji.Yace daure kiyi wanka zaki fi jin karfin jikinki,taho muje nayi miki.Ta makale kafada, um- um yaya da kaina zanyi.To taso muje kiyi, saida ya rakata har toilet, yace,inkin gama kizo dakina mu kwanta.Ta daga kai sannan shima ya nufi dakinsa yafada toilet. Tana gama wanka tayi alwala, tayisallar isha'i tare da shafa'i da wutri, ta tsayagaban madubi goge nan, shafa nan, ta shafejikinta da manta me sihirtaccen kamshi.Farar hoda kawai ta shafa a fuskarta, sai manlebe data sakata shafa farar kulaccarta ta shafa humrarta, tasaka wata riga mara nauyi iya cinyarta ta doraafter dress da mayafin akanta, ta tafi dakin yayannata.Yana sanye da rigar baccinshi yana tsaye yanadaure madaurin rigar kamshinta ne ya fara mishisallama, ya shaka cikin annashuwa ya lumshe idoyana mai cike da farin ciki, don shi babu abundayafi sashi nushadi a duniyar nan irin turare, donhaka ko nawane zai iya kashewa turare, shiyasadu turarukansa 'yan dubai ne, masu tsadar gaske,da dadin kamshi.Don haka yake mamaki wane irin sihirtaccenturare me ni'imtaccen kamshi take amfani dashi,tunda dai shi yasan iya kashe kudi yana kashewaturare, amma sai yaji nata kamshin da bambanci.Cikin sanyin muryanta tayi sallama, ta shigo yaamsa mata sallamar yana murmushi, ya dagomata hannu ta taho, sannu a hankali ta shigejikinsa, kamshin jikinsu ya gwauraya ya badawani nau'in kamshi mai dadi, da sanyaya zuciya.Ya cire mata after dress din, yaga surarta cikinshedaniyar rigar data sa ya kara, a zuciyarsakuwa hamdala yake yiwa ubangijisa da yayiwazeey dinshi tattausan jiki da laushi.Ta langabe a jikinsa tana lumshe ido ya radamata a kunanta baccin ne? Ta daga kanta, zomuje na baki nama da fresh milk kici saikikwanta.Tace yaya kasan fa naci abinci tun su hajiyasuna nan, a koshe nake. Yace kadan zaki ci, banason ko kaka ki zauna da yunwa ne, kinji zeeyta,ta daga kai kawai.Tana manne ajikinshi yake bata naman da freshmilk, saida ya tabbatar da lallai ta koshi, sannanya rabu da ita.Ta kara wanke bakinta a toilet ta matsa mouthfreshna a bakin nata.A hankali tana jin dadin tausar tana lumshe ido.Ya jawo filo ya kwanta ya mannata ajikinshi,yana shafa bayanta yana wani lallabata kamarwata jaririya, da haka bacci mai dadi ya daukesu.Ranar littinin da safe Aliyu ya tura direba gidansumansura yace, ya dauko masa dansa, ya kaishimakaranta, in an tashi ya kaishi gidansu wajenumma.Mansura tun tana daukan lamarin abun wasaabun har ya fara damunta, domin ta shafetsawon sati biyu a gidansu, amma Aliyu baiwaiwaiyeta ba.Kawarta lawisa da yayarta saratu sai kudi sukekarba suna zarya suwa mata wajen malamai dona karkato hankalinsa, ya nemi ta koma ita kumataja masa aji.Amma lamarin shiru kamar an shuka dusa.A wannan lokacin ne kuma aka karawa Aliyugirma tare da wani kereren gida mai suna aljannarduniya a Abuja. Lokacin da takardar ta samuAliyu zainab tafi kowa nuna farin cikinta.Ta kankame Aliyu tana murna, ta cewa yayana"cngrtl yayana na tayaka murna naji dadi sosai,Allah ya sanya Alkhairi Allah ya kara daukakaka.Ya shafa kanta Amin zeeyta.Ita tai buga wa 'yan uwansu wayacikin murnarta da dokinta, tana gaya musuankarawa yayanta girma, 'yan uwansu suna tazuwa tayasu murna.Haka abokansa wasu na zuwa wasu nayo masawaya, suna taya shi farin ciki. [9:17PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**8, 3**9 & 3**10 SUNA waya da Abbansa yake gayamasa gobe zaije abuja fadarshugaban kasa zaiyi godiya ya ganokuma gidan, amma kwana biyu zaiyiya dawo.Ta taso ta haye cinyarsa tana shafafuskarsa tace, yayana kaida wa zakutafi?Ya shafa kanta ni kadai zan tafizeeyta. Tace um nidai gaskiya banyarda ka tafi kai kadai ba, sabodame? Nidai gaskiya yaya inka tafi kakadai 'yan mata zasu zata baka daaure wata tace tana sonka.Yana dariya, zeeyta wannan fa kishine, kin iya kishi zainab.Tayi murmushi ta boye fuskartaajikinshi tace, yaya ba haka bane.Yace to yaya ne? Tace nifa yayabazan iya barin mijina, ya tafi waniwaje har ya kwana shi kadai ba nafiso ko ina na kasance tare da mijina."yayi dan jim a zuciyarsa yana tunaniirin baiwar hankali da Allah yayi wazainab shi.Yarinya karama tasan darajarmijinta, abunda mansura bata iya bakenan, don ita har Allah-Allah matake kada ya zauna a garin, don itagani take zamansa kusa da ita takurane don baya barinta ta sake dayawan fice-ficen unguwa.Yace, zeeyta na tafi dake? Ta dagakai yaya inaso in bika.To idan na tafi dake wacce irinkulawa zaki bani?Tace yaya zan ringa yi maka girkime dadi, yace ita kenan kulawar dazaki bani?To yaya me kake so inyi makawanda yafi hakan?Yace zeeyta nasan ke me ilimi ce, kinsan hakkin miji akan matarsa, ni danuwanki ne, nasan zaki guje minfadawa gararin rayuwa tunda harkina kishina, kina so ki kasance tareda ni, don ki rika bani kulawa.Zainab nakai kololuwa wajenkaunarki, sonki yana neman illatamin zuciyata, zainab ki bani damarda zan nuna miki cikakkiyar kaunarda nake miki. Tace kamar ya yakenan yaya?Yace, zainab inaso ki bani hakkina.Cikin razana da tsoro ta dafe kirjitace "yaya nifa yarinya ce, kaminalkawari sai nan da shekara uku zakakusanceni, amma yaya daga yinwannan magana, wata shidda zakanemi karya alkawarin?Yace, bazan iya barinki har shekarauku ba zainab, wata shiddan nan maa daddafe nayi su,ki bani hakkina zeeyta. Ta mike dagajikinsa tana hawaye, tana ja da baya,tace bazan iya ba yaya.Ya mike a fusace ya wani daka matatsawa, tayi saurin durkushewa kasajikinta yana rawa, yace don na gayamiki ina bukatar hakkina, shine zakice min baza ki iya ba?To kije ki rike abinki. Ya tashi yanufi dakinsa, ta koma ta zauna sosai,ta dafe kanta, ya ilahi, ta kama rantainnalillahi wa inna ilahi raji'un yaya!yaya!! Yaya meyasa yaya zaiyi minhaka?Yaya ya manta abunda ke tsakaninadashi, shine babban yayanmu, shi yadauki kulawa ta musamman yakemin, nake ganinsa tamkar uwata.Yaya fa shine uban rikona, yanzu yazamo mijina, ta ya ya zan iyawannan al'amari dashi?Ai da kunya, bazan iyaba."lawisa tayi sallama dakin da mansuratake, dakin da yayarta saratu takezawarci, shiru taji ba a amsa ba,alhali ance mata mansura tana ciki,don haka lawisa ta danna kai cikindakin.Ta samu mansura tana zaune tahada uban tagumi. Lawisa ta dafatatace lafiya? Mansura tayi firgigit tadawo hayyacinta, tace, lawisaabubuwa ne suka taru suka yi minyawa, tace abubuwa wane iri?Tace "kina kallo kashe kudin da nakeyi wai don Aliyu yazo da kansagidannan bikona, amma shiru balabarinsa, wai ya ma manta danikwata-kwata.To jiyan nan labari ya sameni, ankarawa Aliyu girma tare datanfatsetsen gida a Abuja dadankareriyar mota.Lawisa ta hau salati tace kada famuna zaune anan yarinyar nan tamallake shi, yazo yana mikiwulakanci daya fi wannan.Mansura tace, nifa yanzu yarinyarnan bata gabana, burina kawai nagaAliyu yazo ya maidani, domin niwallahi nasan halin Aliyu sarai, bakaramin miskili bane.Wannan yarinyar bata da wayewanda zata iya jan hankalin Aliyu, waiharta mallakeshi domin gidahumacena karshe.Kuma tana da sanin da bata so tacuci wani kota danne hakkin wani,bare nace zata bi malami don cutardani, kota mallaki Aliyu.Idan har zatayi hakan, to waye zaiyimata, ita ba fita zai barta ta rinka yiba.Ita ba ya ba, ba kanwa ba, ita bawata 'yace da ita kanwa ce da itada suke uwa daya uba daya ba.Ita ba dagin uwarta ne akusa da itaba, bare suyi mata.Don nasha jinsu idan muna tare,idan kanwar Aliyu, yayarta ni'imatazo, idan tana ta dokin aurenta,tana gaya mata ita harta kagu akaita gidan mij, saboda kawayentasuna bata labarin ana kaza da kaza,saiki ji zainab din tana mata magiya,da ta daina mata irin wannanzancen, wai ita wallahi tsoratar da itatakeyi, don ita cewa tayi, ko karaminyaro ta gani tsirara tsoro yake bata.Lawisa tace anya kuwa ba aljanineya aureta ba? Mansura tace Allahyasa shi dinne ma, inga ta karyar so.Nifa lawisa abunda yafi damuna,rashin kudi, kinsan ni ba wani abunake sayarwa ba, karyata ta Aliyu ce,bani da wata takama saita Aliyu, kinsan shi akwai sakin kudi, ga cima maikyau, wallahi yanzu duna raina cimargidanmu,... Wallah yanzu duna raina cimar gidanmu, shinkafa da miya dayankan nama biyu, da daddare tuwoda miya, da safe shayi da biredi dadan dankali.Kya hada da gidan Aliyu da akewatandar kaji, kwai, farfesu, saina gadama fa nake girki, na gwammace ahadomin take away a hadaddenresturant.Gashi Aliyu baya jin kudi ko nawakikace ya baki bazai rage ba, saidaiya kara miki ma. Shifa abun duniyabai dameshi ba, burinsa kawai yawadata iyalinsa da komai.Bare yanzu da aka kara masamukami nasan wasu ninkakunkudine zasu sake shigo masa.Ga harkar kasuwancisa, kullum Allahkara buda masa yake, nifa gaskiya sonake kota karfi kota tsiya na komagidan mijina, don kinga iyayenafushi suke yi dani.Da zasu yiwa Aliyu magana wallahida zai maidani, don Aliyu yana damutunci baya ketare maganar nagaba dashi, indai yasan maganarbata banza ce.Ki kawo kudi na koma miki wajenmalam, to ai kinjiki, ina naga wanikudi, du ba kun karbe ba, kun kaiwabokaye sun cinye a banza ba? Lawisata kwantar da murya tace mata, "menema fa baya gajiya, acikinyarirrikanki ki bada wannan karaminyarin gwal dinnan naki a siyar a jemiki gidan malam da kin koma zakimayar da mafiyinsa, mansura tacehaba dai, du kudin dana fito dasu,sun kare ace har na fara fitar dakaddarata.Lawisa tace to zauna son duniya,kwazama ku biyu zawrawa a gidan,ai gaki ga yayarki saratu ni kingatafiyata.Ta mike zata tafi mansura ta riko ta,tsaya lawisa bari na dauko mikita dauko mata yarinta, bata kiyasinkudinsa zaiyi dubu tara.Lawisa ta karba tace, zan aiko mikida yanda mukayi da bokan abundaya bani na kawo mikizan bawa kanwata ta kawo mikidon kada hajiyarku taga zuwannawa yayi yawa ta zargi wani abu.Inyaso sai nayo miki waya, nayi mikibayanin komai, tace to shikenannagode.Lawisa tana fita tasa yarin a kunantatana cewa, matsiyaciya tare mukataso dake, Allah ya rufa miki asirinki,kina gidan mijinki kina cin daulararziki, ni kuwa ina rabe har yanzumiji yaki samuwa tsakanin kyautarda zakimin basa wuce dari biyar, saikuma kwacen sutura, yanzu tundaAllah ya kawo hanya mafi sauki aidole naci ba wani wajen malamin dazanje.Don suma malaman ci suke yikwanciyarsu. Sai daf da mangaribasannan lawisa tayiwa mansura waya,take gaya mata yanzunan ta dawodaga wajen malamin ta tsara matakaryayyaki akan tace malamin yacezaiyi aiki akansa ya bata hakuri yanemi ta koma dakinta. Mansura taringa murna tayiwa kawarta godiya.**********kwana daya kawai da 'yarhatsaniyarsu amma zainab ta kasasamun sukuni.Don tuntuni bata son bacin ranyayanta bare kuma ace akanta yakefushi, du saita shiga tashin hankali.Bare yanzu da ya sangartar da ita, yasabar mata da dumin jikinsa, lallaiyayi mata sabo mai wuyar bari, jiyadai du da agado daya suka kwanaamma da kyar ta iya bacci, sabodabe jawota jikinsa ya dorata a kirjinsaba.Amma a jiya akai da kafa ma sukakwana.Shikuwa Aliyu du abunda yayi mata,yayi mata ne don ta gane kurenta,domin har yafi shiga damuwa darashin jin dumin jikinta.To ya riga yakai kololuwa tasha'awar zeey din domin yarinyarkullum kara cika take yi da wanifresh.Da safe ma da suka zo yin break bawani lallbata din nan da yake yi nataci sai takura mata dayayi ta cinye,kamar yanda yake yi mata sandatake gida.Gashi wuni gida yaki zama a gidan,yana can wajen iyayensu ya barta itakadai a gidan.Ita abunda yafi damunta ma kadagobe tayi, yayi tafiyarsa ya barta.Ta mike daga tunanen data keyi, tafada toilet ta tsalo wanka dahadadden sabulunta, ta rinkamitsitsike jikinta da turaruka.Ta gama tsara kwalliyarta, tasa watairin karamar shimi ta dame matajikinta, amma fa bata rufe matacibiya ba, tasa wani dan mini siketiya cinya, ta karawa jikinta turare,tayi kyau tanata ambaliyar kamshi.Ta jiyo motsinsa a falo, ya gama cinabinci yau ko nemanta baiyi ba.Ta dafe kanta tana cewa, yaya yayifushi da ita, da yawa, ta dauki afterdress zata saka, sai kuma ta fasasawa, saboda shi yafi so ya ganta ahaka kawai, ya ringa kiranta dabebynshi.Ta gyara gashin kanta, ta dan sakoda kadan gaba tayi turaren gashi, tahada ta daureshi a baya da ribom.A hankali ta tako zuwa falon, yanajiyo kamshinta ya kishingida akankujera, ya lumshe ido yana shakarkamshinta, tana karasowa ta ganshiya lumshe ido, a zuciyarta tace, Allahka taimakeni na samu na gyarakomai.Tana zuwa ta kwanta a cinyarsa, baisan sanda yasaki ajiyar zuciya ba,don ya gasu jiya kawai da be jidumin zeey din tashi ba.Ya bude idonsa ya kalleta, sai kacewata 'yar tsana, shigar data yi tayimasa kyau sosai, yasa hannu yanashafar wajen.Ya dagota ya dora a kirjinsa, yanashakar ni'imtaccen kamshinta, taceyaya don Allah kayi hakurikaji yaya naga ranka ya baci, yayanakayi hakuri.Ya taba cikinta, zeeyta baki ci abinciba, kina son zama da yunwa ko?Cikin shagwaba tace, to yaya bakaikaci abincinka baka nemeni ba?Ya dagota zo muje na baki abaki,sakwara ce da miyar agushi, ya rinkabata abaki,.... YA rinka bata abaki tana ci ayangace, shikuwa yangartatabirgeshi take, don haka suka daukilokaci kafin ta gama cin abincin.Harta gama, cikin shagwaba taceyaya baka ce fa ka yafe minba.Yace, zeeyta ai bazanso Allah yakamaki da hakkina ba, na yafe miki,tace yaya nagode.Allah ya saka maka da alkhairiyayana.Ta marairaice fuska tace, yaya zuwaabujan fa?Yace a'a bazanje dake ba, kiyizamanki a gidan nan har na dawo."ta kuma marairaita da magiya, donAllah yayana kaje dani.Ya mike tsaye yana tafiya, yace um-um ba inda zanje dake.Yayi shigewarsa dakinsa, yayi shirinkwanciya ya haye gadonsa, yayiaddu'a ya shafe jikinsa, ya rufeidonsa yana so yayi bacci, don yasaninya tashi sallar asuba bazaiyi baccinsafe ba.Ta shigo cikin wata shedaniyar rigarbacci, 'yar karama, me siririn hannushimi daya, komai na jikinta abayyane yake, ta fada kansa tana yimasa kukan shagwaba. Ya ilahi!Yarinyar nan so take ta zautar dashida kaunarta yaushe zai iya fushi dazeey?Ai bazai yiwu ba, yarinyar 'yarkarama da ita ta san yadda zatafaranta ran mijinta, lallai samunmace ta gari shine mafi alkhairi jindadin duniya.Shi yasan yanzu bazai iya tafiyanwuni guda ba tare da zeey dinshi ba,bare wajen da zai je ya kwana.Ai dole ne yaje da ita, don inbatakusa dashima bazai iya bacci ba.Ta dameshi da kukan shagwabarta,kukan da ba hawaye, ya bude idonsadaya, yasa hannu daya yana shafakanta daya kuma yana dan bubbugabayanta alamar rarrashi.Yace zeeyta kinsan bana son kuka,kiyi shiru ki kyaleni nayi bacci, kadakisa na makara gobe wajen tafiya.Ta marairaice masa don Allah yayakayi hakuri ka tafi dani tsoro nakeji,bazan iya zama a gidan nan ni kadaiba, kaji yayana? Ya daga kai najizeeyta, zan tafi dake shikenan? Tashiga jikinsa ta kankameshi sosaitana murna.Ba jimawa bacci ya dauketa, saimunsharinta take yi a hankali, tanabaccinta cikin kwanciyar hankali baruwanta, ba abunda ya dameta.Shikuwa ya kasa baccin, ya rasa inazai cusa zeey din tashi, ko zaijisa'idar zogin sonta, ya addabeshi azuciya.Suna yin break suka daga zuwaabuja, tafkeken gidan da aka bawaAliyu katon gaskene, fadan tsaringidan bata lokacine, sun gamazagaye gidan Aliyu ya jawohannunta, ta fada jikinshi sosai sunamasu farin ciki, tace dashi yaya najidadi na tayaka murna sosai, Allah yakara daukaka.Amin zeeyta."yace "zeeyta zaki zauna dani anangidan? Tace yaya aunty fa? Yaceita zata cigaba da zamanta a kano,tace "to yaya ai zata ci ga anyi matarashin adalci.Yace bazata ce ba, tun ina kadunana taba cewa zan tafi da ita can, tanuna bata so, tafi son zama a kusada iyayenta da 'yan uwanta, kingakuwa ai ke bazaki ki zama dani ananba, tunda ni dan uwanki ne ko? Taceyaya ko aina ne zan zauna dakai,koda cikin tandun mai ne. Karkadamu yayana zan zauna dakai.Dakyau zeeyta nagode,**** ****** ****daga cewa kwana biyu, shiru balabari, ita kanta lawisa bata kumazuwa gidan su mansura ba, gashi satibiyu kenan, ba wata magana dagagidansu Aliyu, gashi Aliyu ya daukezainab sunyi tafiyarsu sunyi zamansushiru.Ga iyayenta sun watsar da ita, bawanda yake mata maganar komawagidan Aliyu, ita yanzu abun tsoroyake bata, tana gudun kada watarana Aliyu ya aiko mata da takardarsaki.Lallai data yi muguwar asara, donina zata samu gwarzon namijikaman Aliyunta? Wai ya zatayine tadawo da Aliyu gareta?Ita yanzu abunda ya dameta kusankullum sai sunyi fada da yayartasaratu.Ita fa ta gaji da zaman gidan nan, sotake kawai ta koma gidan mijinta.Saratu ce ta shigo ta doka tsaki, tace,wai dan Allah malama uban waye zaiwanke miki wadancan wanke- wankeda kika bari guda yana bi?Dubi yanda kikayi kaca- kaca da daki,kinsha shayi kudaje sai bin kofi dawaje sukeyi.Mansura tace haba saratu ki rinkatausaya min halinda nake ciki mana,a gidan mijina tsinke bansan yandazan kawar dashi a wajen ba, ammayanzu kuta hadani da shara dawanke-wanke, inayi kinayi minmasifar ban iyaba.Haba kefa 'yar uwata ce, yanzubazaki taimakamin na koma dakinaba?Saratu, tace me zanyi miki, rashinhakurinki, tunda mijinki yayi niyyaraure ko ba zainab, sai ya aura mikikilaliyar mata gogaggiya, wacce zataiya fitar dake lokaci daya, amma donya auri wannan karamar yarinyar,doluwa, mara wayo, du kinbi kindaga hankalinki har kina nemankashe musu 'ya, to kadan ma kikagani, donma ba aurenki ne, ya mutuba da bakin cikin da zaki gani, saiyafi haka.To yanzu yaya saratu ya zanyi?Nifa nayi nadama.Ki kawo kudi naje miki wajen wanishararren malami, aikinsa kamaryankan wuka.Haba yaya saratu, ni na gaji da binwasu malamai, kudina du sun kare,na fara fitar da kaddarata ama dubabu wani ci gaba, nina gaji.Saratu tace, saiki ta zama, zamangidan ne baki gaji dashi ba.Tace, to me zan bayar ki siyar? Tace,kayan da ya baki na fadar kishiyabana ga baki dinki supern kiba, kibayar asiyar, biyan bukata ai yafidogon buri.Mansura ta bude akwati ta daukosuper ta mika mata.Saratu tace, to kinga inada kudidubu koma sha biyar, [9:18PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**11 Saratu tace, to kinga inada kudi dubu goma sha biyar, zan sai super nan taki dasu, tunda ta zama ta hannu, saina je miki gidan malam da kudin. Mansura tace, to shikenan. Saratu ta fita da super ta kaita dinki, tana cewa a ranta. Me shegiyar rowar tsiya, inba da hakaba bazaka ci komai nata ba. Tace, na fara jin tausayinki, yanzu zanje nayi miki taimako daya, don ta hanyar ne kawai Aliyu zai saurareta, wannan uban zuciyar. Daga nan saita wuce ofis din daddyn zainab, yace lafiya saratu kika zo nan? Cikin ladabi tace, wallahi daddy daman akan abunda mansura tayiwa zainab ne nazo kara baka hakuri, wallahi mansura tayi nadama sosai, don Allah daddy kayi hakuri, kasa Aliyu ya mayar da ita dakinta. Daddy yace banganeba, kina nufin wai mansura bata gidan Aliyu? Tace wallahi daddy tun sanda tayiwa zainab abun nan ya korata gida. Har yanzu tana nan. Iyayenmu kuma sunce ba ruwansu, donsu kunyarku suke ji. Ba zasu tunkareku da maganar ba. Daddy ya rinka salati yana cewa, wallahi daga shi har iyayensa basu san haka ba. Abu wajen wata uku, ace tana zaune a gida, Aliyu yayi kuruciya, yace kije saratu yanzun nan zan nemi Aliyu a waya, a satin nan mansura zata koma dakinta. Saratu ta taso tanata godiya. Tana zuwa gida ta cewa mansura ai malamin yace, ta kwantar da hankalinta, acikin satin nan ALiyu zai zo da kansa bikonta, tace, yace amma daya zo kibishi, idan kika ce zaki tsaya jan aji, to kuwa ajin zai tsinke miki, ke kika jiyo wannan kuma ba ruwana. Mansura tace, um ni abun mafa ya fara bani tsoro, Allah yasa dai yazo din. Can kuma Saratu na fita daddy ya kira Aliyu, ringin daya tayi Aliyu ya dauka, da saurinsa ya rissina yana gaishe shi, saika ce agabanshi yake. Yace haba Aliyu kai danake ganin hankalinka, zakayi wannan danyen aikin? Ka ajiye mace a gidansu tsawon wata uku, baka waiwaiyeta ba? Kuma dagani har yayana bamu sani ba, ai sai a rinka zarginmu ace don mun aura maka tamune muka sa ka wulakanta 'yar mutane. Banji dadin abunda kayi ba Aliyu kwata-kwata. Aliyu yace kayi hakuri daddy, Allah ya huci zuciyarka. Yace na hakura Aliyu, amma kazo da kanka, kaje kayo bikon matarka, yace to Abba zanzo. Kazo fa acikin satinnan, bana so a kuma daukan lokaci. Yace "to daddy insha Allahu jibi karshen sati zanzo. To Allah kaimu. Sukayi sallama yana yi masa godiya suka kashe wayar. Kanta yana kan cinyarsa tana so tayi bacci, ta bude idonta tace, yaya me kayiwa daddy, du yanda kuke shiri dashi yake cewa yau baka kyauta ba? Yace akan maganar auntynki ne yake min fada, naje na dawo da ita gidana. Yaya wai ina ta tafine? Gidansu na turata, take ta zama, tace kai yaya auntyn tawa? Ni wallahi dana san tana gidansu da tuni naje da kaina nayo bikonta. Meyasa yaya kayi mata haka. To ya zanyi mata zeeyta? Ta tabamin tauraruwar matana, ai dole in nuna mata kurenta. Amma kuma yaya saika barta a gidansu kowa yasan tana gida? To zeeyta ai bani da abinda zan mata daya fi hakan, don in nace dukanta zanyi bansan wani irin mugun duka zanyi mata ba. Kuma in na daketa mutane saisu manta abunda tayi min, ace na daketa akan kanwata, yanzu kuwa kinga ba duka ba zagi, nasan ta horu. Tayi dan murmushinta mai kashe zuciya tace "yaya jibin da wuri zamu tafi ko? Yace ina? Keda fita ai sai ranar da kika zama mace. Yaya yanzu ni ba mace bace? Yanzu ke muna mace ce, baki zama cikakkiyar mace ba tukunna. Yaya to yaushe zan zamo macen? Du ranar da kika so zaki zama. Tayi shiru tana tunani me kalmar tasa ke nufi, sai kawai ta share maganar, bata kuma zancen zata bishin ba. Sai da safe bayan sun gama break, yake ce mata, sadik tuntuni sun taho, suna kan hanya, zai kawo miki talatu nan zata ci gaba da zama dake, kwana uku zanyi na dawo. Ta zumbura baki ta mike tsaye tana bubbuga kafa, ta tafi wajen labule zata bude ta fita. Ya kirata, zeeyta meye haka? To yaya kai kadai zaka tafi, ni bazaka tafi dani ba, naga su Abba da dady ba? Don Allah yaya ka tafi dani kaji? Ya girgiza kai, kiyi zamanki a gida, kwana uku kawai zanyi. Ta juya ta hada kanta da bango ta kama kuka, ya taso ya jawota jikinsa, yana rarrashinta, yi hakuri zeeyta keda kike 'yar gatana, ga sadik nan shida talatu zasu zauna dake, har na dawo, tunda sadik yana cikin hutu zai zauna idan nadawo, sai ya tafi, talatu kuwa anan zata zauna ta ringa taimaka miki. Ko bakya son zuwan sadik din? Tace inaso. To yi shiru share hawayenki, bazan dade ba kinji zeeyta. Ta daga masa kai, to yi dariya. Tasa dariya, yauwa zeeyta. Dai-dai lokacin da ake kwankwasa kofa ta bude da sauri, wadanda take zato su dinne, ta kankame sadik tana murna, ta riko hannun talatu tana yi musu sannu da zuwa. Lokaci kankani ta cika musu gabansu da kayan ciye-ciye, sannan ta zauna suna gaisawa, ta tambayi wannan ta tambayi wancan. Sukuma sunata cin abubuwa data kawo musu, suna gamawa suka mika suna zaga gidan. Sadik ya rinka santin gidan, gskya yaya ka gama hutawa wannn tanfatsetsen gidan, gashi yaji kayan kawata gida kaman a turai? Aliyu yayi murmushi yace Allah sarki sadik, to idan ka tashi aure irinsa zan gina maka. [9:19PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**11, 3**12 & 3**13 Saratu tace, to kinga inada kudi dubu goma shabiyar, zan sai super nan taki dasu, tunda ta zamata hannu, saina je miki gidan malam da kudin.Mansura tace, to shikenan.Saratu ta fita da super ta kaita dinki, tana cewa aranta.Me shegiyar rowar tsiya, inba da hakaba bazakaci komai nata ba.Tace, na fara jin tausayinki, yanzu zanje nayi mikitaimako daya, don ta hanyar ne kawai Aliyu zaisaurareta, wannan uban zuciyar.Daga nan saita wuce ofis din daddyn zainab, yacelafiya saratu kika zo nan?Cikin ladabi tace, wallahi daddy daman akanabunda mansura tayiwa zainab ne nazo karabaka hakuri, wallahi mansura tayi nadama sosai,don Allah daddy kayi hakuri, kasa Aliyu ya mayarda ita dakinta.Daddy yace banganeba, kina nufin wai mansurabata gidan Aliyu?Tace wallahi daddy tun sanda tayiwa zainab abunnan ya korata gida. Har yanzu tana nan.Iyayenmu kuma sunce ba ruwansu, donsukunyarku suke ji.Ba zasu tunkareku da maganar ba.Daddy ya rinka salati yana cewa, wallahi daga shihar iyayensa basu san haka ba.Abu wajen wata uku, ace tana zaune a gida, Aliyuyayi kuruciya, yace kije saratu yanzun nan zannemi Aliyu a waya, a satin nan mansura zatakoma dakinta.Saratu ta taso tanata godiya.Tana zuwa gida ta cewa mansura ai malaminyace, ta kwantar da hankalinta, acikin satin nanALiyu zai zo da kansa bikonta, tace, yace ammadaya zo kibishi, idan kika ce zaki tsaya jan aji, tokuwa ajin zai tsinke miki, ke kika jiyo wannankuma ba ruwana.Mansura tace, um ni abun mafa ya fara banitsoro, Allah yasa dai yazo din.Can kuma Saratu na fita daddy ya kira Aliyu,ringin daya tayi Aliyu ya dauka, da saurinsa yarissina yana gaishe shi, saika ce agabanshi yake.Yace haba Aliyu kai danake ganin hankalinka,zakayi wannan danyen aikin? Ka ajiye mace agidansu tsawon wata uku, baka waiwaiyeta ba?Kuma dagani har yayana bamu sani ba, ai sai arinka zarginmu ace don mun aura maka tamunemuka sa ka wulakanta 'yar mutane.Banji dadin abunda kayi ba Aliyu kwata-kwata.Aliyu yace kayi hakuri daddy, Allah ya hucizuciyarka.Yace na hakura Aliyu, amma kazo da kanka, kajekayo bikon matarka, yace to Abba zanzo.Kazo fa acikin satinnan, bana so a kuma daukanlokaci.Yace "to daddy insha Allahu jibi karshen satizanzo.To Allah kaimu.Sukayi sallama yana yi masa godiya suka kashewayar.Kanta yana kan cinyarsa tana so tayi bacci, tabude idonta tace, yaya me kayiwa daddy, duyanda kuke shiri dashi yake cewa yau bakakyauta ba? Yace akan maganar auntynki ne yake min fada,naje na dawo da ita gidana.Yaya wai ina ta tafine?Gidansu na turata, take ta zama, tace kai yayaauntyn tawa? Ni wallahi dana san tana gidansuda tuni naje da kaina nayo bikonta.Meyasa yaya kayi mata haka.To ya zanyi mata zeeyta? Ta tabamin tauraruwarmatana, ai dole in nuna mata kurenta.Amma kuma yaya saika barta a gidansu kowayasan tana gida?To zeeyta ai bani da abinda zan mata daya fihakan, don in nace dukanta zanyi bansan waniirin mugun duka zanyi mata ba.Kuma in na daketa mutane saisu manta abundatayi min, ace na daketa akan kanwata, yanzukuwa kinga ba duka ba zagi, nasan ta horu.Tayi dan murmushinta mai kashe zuciya tace"yaya jibin da wuri zamu tafi ko?Yace ina? Keda fita ai sai ranar da kika zamamace.Yaya yanzu ni ba mace bace?Yanzu ke muna mace ce, baki zama cikakkiyarmace ba tukunna.Yaya to yaushe zan zamo macen?Du ranar da kika so zaki zama.Tayi shiru tana tunani me kalmar tasa ke nufi, saikawai ta share maganar, bata kuma zancen zatabishin ba.Sai da safe bayan sun gama break, yake ce mata,sadik tuntuni sun taho, suna kan hanya, zai kawomiki talatu nan zata ci gaba da zama dake,kwana uku zanyi na dawo.Ta zumbura baki ta mike tsaye tana bubbugakafa, ta tafi wajen labule zata bude ta fita.Ya kirata, zeeyta meye haka?To yaya kai kadai zaka tafi, ni bazaka tafi daniba, naga su Abba da dady ba?Don Allah yaya ka tafi dani kaji?Ya girgiza kai, kiyi zamanki a gida, kwana ukukawai zanyi. Ta juya ta hada kanta da bango takama kuka, ya taso ya jawota jikinsa, yanararrashinta, yi hakuri zeeyta keda kike 'yargatana, ga sadik nan shida talatu zasu zaunadake, har na dawo, tunda sadik yana cikin hutuzai zauna idan nadawo, sai ya tafi, talatu kuwaanan zata zauna ta ringa taimaka miki.Ko bakya son zuwan sadik din? Tace inaso.To yi shiru share hawayenki, bazan dade ba kinjizeeyta.Ta daga masa kai, to yi dariya.Tasa dariya, yauwa zeeyta. Dai-dai lokacin daake kwankwasa kofa ta bude da sauri, wadandatake zato su dinne, ta kankame sadik tana murna,ta riko hannun talatu tana yi musu sannu dazuwa.Lokaci kankani ta cika musu gabansu da kayanciye-ciye, sannan ta zauna suna gaisawa, tatambayi wannan ta tambayi wancan.Sukuma sunata cin abubuwa data kawo musu,suna gamawa suka mika suna zaga gidan.Sadik ya rinka santin gidan, gskya yaya ka gamahutawa wannn tanfatsetsen gidan, gashi yajikayan kawata gida kaman a turai? Aliyu yayimurmushi yace Allah sarki sadik, to idan ka tashiaure irinsa zan gina maka. Sadik yayi dariya yace, yaya nan dashekara sha biyar fa."au kace saika kusa zama tuzuru,sannan zakayi auren?Dai-dai lokacin da suka shigo boyskwatas yace to ga inda zaka zauna.Aliyu ya gama shirinsa, zainab taratayo jakarsa ta taho zata yi masarakiya, har zuwa wajen mota.Ya shiga motar ya zauna, ta sakomasa jakar idonta yayi rau-rau tanakokarin zubo da hawayen nata.Ya jawota kan cinyarsa, haba zeeytabazaki yi min addu'a ba, sai kuka,kina so ki daga min hankalina, nakasa tukin? Tace yi hakuri yaya,Allah ya kiyaye hanya ya dawo dakailafiya.Yace yauwa zeeytah, maza tafi gidadon bazan iya tafiya na barki aharabar gidan nan ke kadai ba.Ta juya tana dan gudunta da tsalle-tsallenta, tana dariya tana daga masahannu, alamar bye-bye, ya dauko yawayarsa ya ringa daukarta a bidiyo,tana ganin yana daukarta, tasadariya ta juya tayi cikin gida tanacewa yaya saika dawo.Yayi dariya ya kashe wayar yasata aaljihu.Yaja motar ya tafi.A hanya ya tsaya yayi musu uwartsaraba. Yana isa gida, ya samu suAbba da daddy dasu mama, sunatahiransu cikin nishadi.Yayi sallama cikin falon, suka amsamama da ummi suna ga Aliyu gaAliyu.Ya rissina ya gaishesu, daddy yaceAliyu jeka, ka nutsu ka dan huta inanijima kaje ka dawo da matarka.To daddy nagode, ya mike ya fitayasa me gadinsu dame wanki sukashishigar da kayan.Ya shiga motarsa yaja sai gidansu dazeey.Yana shiga gidan, wannan dadadankamshi yana nan, ya rasa wannansirrin kamshi na zeey dinshi.Ya fada toilet yayi wanka yayi sallah,yana fitowa ya tarar hamzaya kawo masa abinci daga gida.Yaci ya kwanta a gado don ya danhuta, yana so yayi bacci, amma sai yakasa rintsawa tunanin yaji zeeydinshi a manne a kirjinsa yadameshi.Ya jawo wayarsa ya buga mata,ringin daya ta dauka, hello yayanakaje lafiya?Nazo lafiya, gashi har naci abinci,nayi wanka, nayi sallah na kwantawai don na dan huta, tunaninki yahanani bacci.Cikin shgwaba tace, um ba kainekayi tafiyarka ka barni ba?Yaya ka jawo min sai nayi awasaba'in da biyu ban ganka ba, yacezeeyta ke rashin ganina ne kawai, nikuwa rashin jin dumin jikinki yafikomai daga min hankali.Zeeyta wai yaushe zaki bani dama nakusanceki? Tace yaya me kake so nayi maka, mekake so na baka yayana? Komai kakeso yaya zanyi mka.Matsayinka da darajarka a wajenakafi karfin komai yayana.Yace zeeyta ina matukar so ki banihakkina na jikinki, amma fa sai kinara'ayi, don wallahi in zamu shekaragoma a haka bazan taba takura mikiba, ko nayi miki dole.Kuma kada kiyi tunanin kina dahakki a wajen ubangiji, a'a tsananinkaunar danake yi miki bazata bari nakullace ki ba.Kona yi fushi dake ba, na yafe mikizeeyta.Kayi hakuri yayana, na amince maka,na baka dama du sanda kaso kayira'ayi yayana, ka karbi hakkinka,yace dagaske zeeyta? Kada kisa nayitsuntsu na taho yanzu.Tace a'a yayana kada ka dawo yanzu,ka zauna ka kula da auntyna ka batahakkinta, ka rarrasheta, ka batahakuri kan abunda kayi mata.Ina jiranka yayana nanda kwanauku, kamar yanda kace, Allah yadawo min da kai lafiya. Ka kulaminda auntyna ka bata hakuri, kararrasheta ka lallbata harta huce, kashafamin kan Amadina. Kayi hakuriyaya, don Allah kada ka damu, zankashe kada na cinyewa auntynalokaci, don nasan yau sabon amarezaku zama, kayi mata kalamai masusanyi da tausasa zuciya, ka nunamata tattalin so yayana saida safe.Dif ta kashe wayar, ya rinka juyawayar a hannunsa yana murmushi,yarinya karama ta iya kalamai maisanyaya zuciya.Ya kunna bidiyo wayar ya rinkakallonta sanda tayi masa rakiya, dangudun data keyi tanata tsalle-tsallenta, tana dariya, du dai dontasa shi nishadi ta kuwa shashi, donkifa wayar yayi a fuskarsa, yana jinzuciyarsa wasai, cike da nishadi bacciya rinka fusgarshi ya kashe wayar yakwanta.**** ***** ***mansura taga shiru har mangaribaba Aliyu, tace yaya saratu anya kuwaAliyu zai zo, kinji shiru har yanzu?Saratu tace ke kinfiya wutar ciki, dukudin da kike kashewa wanne kikasamu nasara kamar wannan?Kina gani kanin babanshi yazo yaitabawa Alh hakuri, yana cewa basu sanhakaba.To ko Aliyu baizoba idan daddynzainab ya sake zuwa basai ki komadakinki ba, inya ji ya dawo dake aidole yazo inda kike.Bayan sunyi sallar isha'i suna cinabinci, hajiya ta shigo take gayamata, taje falon baki inji babanta.Mansura ta tashi da saurinta tawanke hannunta, ta yafa mayafinta,ta nufi falon babanta.Wani mayataccen kamshine taji yadaki hanncinta, a hankali tayisallama, ta zauna ta cewa babantagani. Ya mike tsaye yace, game songaninki nan sai a sannan ta dagakanta ta ga bakon da yake zaune.Aliyunta ne cikin shiga na alfarma,ya kara murjewa da kyau, ya karahaske da kwarjini, fatarsa har wanidaukan ido yake yi.Yana ta zuba kamshi mai dadi,idonsa yana sanye da farin glass.Du saita raina kanta taga ta muzantaa gabanshi, me Aliyu yake ci dayakara wannan kyan, da kwarjini?Lallai Aliyunta ya kara samun canjinrayuwa, ma'ana kudi sun sake zamamishi.A hankali tace masa ina wuni? . A hankali tace masa ina wuni?Ya dago kai ya kalleta, du tayi baki ta rame, takusan fita daga hayyacinta.Yace lafiya lau ya zaman jin dadi? Tayi shiru,yace so ya kika gani, zaki tafine yanzu ko bakigama hutawa ba?Tace zan tafi, yace to sai kiyi sauri ina jiranki amota, ya bata dubu dari yace, ta bawa hajiya daAlh su sai goro.Alh ya mata fada, ta durkusa a gabansu tayimusu sallama, ta tafi, ganin mota ta bawamansura mamaki, tasan tabbas motar manya ce,a ranta, tace daula tazo, tana neman tayiwakanta.Tukinsa kawai yake yi baice mata komai ba,itama bata ce masa komaiba, sai satar kallonsadata keyi, suna isa gidan tayi mamakin yanda taganshi gyare, ya zube mata ledoji a gabanta, yawuce dakinsa, wanka ya sakeyi yasa kayan bacciya fita falo, ya tarar itama tayi wanka, tasakayan baccinta, yace baki bude ledojin bane?Tace a'a na bude kai nake jira.Ya zauna ta dauko plate ta juye gasassun kaji, tazuzzuba musu fresh milk a kofuna.Sunaci har ya koshi.Ta nufi toilet yin brush shikuma ya nufi dakinsa,yayi brush ya rinka feshe dakin da turaruka kusankala biyar amma sai yaji baiyi masa irin kamshindakunan zainab ba, yana kwance yana karantaaddu'o'in tsarin jiki, yana shafawa ta shigo dasallamarta ta rufe kofar ta jingina a jiki, ya mikamata hannu ta tashi ta miko masa nata hannun,ya jawota ta fado jikinshi,yayi saurin cikata ya dagota yana tambayarta,mansura meya sameki naji kin rame, rashin lafiyakika yi?Ta girgiza kai saita fashe da kuka, ya kwantar daita a jikinsa yana dan bubbuga bayanta, yi shiruya isa haka, kinsan bana son yawan kuka,fadamin meye?Ta kama fada masa irin wahalan data sha nashara da wanke- wanke.Aliyu yace "O sorry mansura, na godewa suhajiya da suka tayani horonki, kinga gobe idankika sake kwatan-kwan abunda kika yi, idan nayimiki horon da yafi wannan, suma wanda zasu yimiki sai ya fi wannan da suka yi miki.Tace Aliyu ai bazan kuma ba, na gane kurena,yace a to dakin samawa kanki lafiya.Don kinsan halina bana daukar raini, bare kumayanzu da girma ya sake hawa kaina.**** *****bayan tafiyan Aliyu sadik ya shigo suna hira dakanwarsa, tanata tambayanshi daddy da faruk,yace mata du lafiyarsu lau.Yace gashima abunda daddy yace na kawo miki,ya bata jakar hadadden tsumi da jakarhadaddiyar zuma ta mata, harda su cukudi,gumbar matam haddaden dakar gari na karinni'ima.Hadadden kayan karin ni'ima dai mai kyau nasakkwato, don da kanshi daddynta yaje har canya hado mata su, don yana ganin tunda ta rasauwa bame gyarata tanan bangaren, shiyasa yakeiya bakin kokarinsa yana so ya maye matamaraicin rashin uwa.Tace Allah sarki daddyna me sona.Sadik yace wai magangunan meye wannan ne?Tace, kaidai ina ruwanka? Cikin farin ciki danishadi sukaita hira da yayanta sadik, sai da yajiya fara hamma sannan yayi musu sallama ita datalatu.Zainab ma tayiwa talatu sallama ta fada dakintadon ta kwanta, sai taji kwanciyar ta gagareta saijuyi take a gado.Taita faman tsaki du dundumiyar katifar dake kangadon, da lallausar bargo da zanin gadon da yakekai, sai take ji kamar akan kaya take, saboda yauba kirjin gwarzon mijinta.Data ga ta kasa baccin saita mike ta shiga toiletta dauro alwala tai ta nafula tana musu addu'a.Tana kwanciya taji karar wayarta, tayi saurindauka tace yayana, cikin sanyita yace zeeyta,meyasa bakiyi bacci ba, har yanzu sha biyu darabi?Ta danyi karamin tsaki tace Allah yaya ban sandalili ba, tun dazu na kasa bacci.Sai yaji dadi a ransa, yasan lallai zeey dinshi tadamu dashi, kiyi bacci bana so ki samu matsalarciwon kai. Tace to yaya zanyi, ina auntynagatanan tana bacci kona tasheta na bata wayarku gaisa?A'a yaya kyaleta tayi baccinta ta huta. To kemakiyi baccin kada kizo kina ciwon kai.To yaya saida safe.Tun a ranar bayan tafiyan yayantata hada kwastan da madara da kwanduwar kwaida manja ta dama, ta shafe jikinta gaba dayata jika jar dilka da ruwan dumi ta rinka mitsesikejikinta iya karfinta.Har kwana uku a ran na ukun ne da safe ta hadalallenta da ma'ul kal da lalle da tacecciya humra,lipton, kar-kar, mahalbiya, turaren S.S mai maiko,garin sanda madaran turare, ta hada tayi kwabinlallen sannan ta dura a kwararon yin kunshi.Ta zauna ta zana sitayel a kafarta da biro tabawa talatu lallen tayi mata kunshin, ta kuma yimata zanen fulawa hannu da kafa.Tayi mata a saman 'yan yatsun hannunta.Daddy yayo waya da safe yace sadik ya taho gidazasu je gaisuwa dashi da sauran 'yan gidankanwar kakarsu ce ta wajen uwa ta rasu donhaka ya tafi bai jira zuwan yayan ba.Sha biyu zainab ta wanke kunshindu inda tayi talatu na binta da kallo.Aliyu ya yo mata waya, yace sun taho tuni tamike ta shiga kicin.Talatu ta bita ta sata yanka wannan gogawancan. Jajjaga wancan shikenan abubuwandata ke sata amma dai-dai da juya miya batayarda tayi mata ba, tace girkin yayanta bata soasa mata hannu talatu tana tsaye tana kallontamasa jalof din makaroni dasu dankali, da pepechiken, tayi miyar nikaken kaza da koren wake. [9:20PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**14, 3**15 & 3**16 Tayi masa miyar nikakkiyar kaza, ta dafa masahinkafa da zaici dashi, tayi masa hadin kos nakabeji, tayi masa lemon kwa-kwa da madara, tayimasa lemon abarba, du tasaka a firij yayi sanyi.Tasa talatu ta fito mata da wasu hadaddun fulassabbi kar a sito, aka wankesu kal, komai tazuzzuba taje ta jeresu a tebir yasha ado dafulawoyi masu kamshi, tace talatu ta gyara makicin din, ita kuma ta sake sharo dakunanta danaAliyu, ta sake goge ko ina yayi tas tasa turarenwuta nan da nan gidan ya canja, ta bawa talatuabincinta dana mai gadi, tace ta mika masa.Zainab ta fita ta kulle ko ina ta fada toilet, tashiga wanka, tana fitowa tayi alwala ta tayar dasallar la'asar.Goge nan, goge can, sai uban kamshi data kezubawa.Ta bude kwabarta ta zubawa suturunta ido, tadauko wani les a ciki na lefenta da yake bata tabasashi ba.Riga da zani ne, ta daura dankwali daya kara fitomata da kyaunta, tasa fashion yari da sarka, daabun hannu du kalar kayan nata.Yayo mata waya, ya karaso cikin murna dazumudi take yiwa Allah godiya.Suna kashe wayar taji bude get.Tana jin tsayuwar ta bude kofar a hankali tarinka wani irin taku kamar hawainya.Ta cikin gilashin motar ya ringa hangota.Yarinyar ta rikide masa, kamar aljana, anya kuwazeey dinshi ce? Kamshinta daya jiyo shiyatabbatar masa da zey dinshi ce tafe gareshi.Yana zaune cikin motar ya kafa mata ido ya kasahasala komai.Ta rinka yi masa dariyarta mai ban sha'awa takama murfin motar ta bude, ta zura jikinta cikinmotar ta zauna a cinyarshi, ta kwantar da kantaa kirjinshi.Yasa hannu biyu ya tura kansa cikin jikinta yanashakar ni'imtaccen kamshinta.Tace yaya nagodewa Allah daya dawo dakailafiya.Yace zeeyta hakika Allah shine abin godiya, dayasake canja minke, zeeyta Allah ya bani kyakyawardiya mace me kama da ke sak.Ta boye fuskarta a jikinshi, tace yayana zaka sanijin kunya.Yace haba zeeyta ai kunya ta kare, ko kin mantakalaman da kika gaya min ta waya?Ta kara cusa kanta cikin kirjinshi.Daukota yayi cak yayi falonsu da ita, yasa kafaya tura kofar falon nasu.Ta mike daga jikinsa tana murmushi, ta ballemasa madaurin takalmansa, ta cire masa, tazame masa safar kafarsa, ta cire masa kwat dinjikinshi, ta jawo hannunsa zuwa dakinsa.Ta shiga toilet ta hada masa ruwan wanka,yanata kamshin turaren wanka, ta ajiye masahadin sabulunta data ke amfani dashi.Ya shiga wanka kafin ya fita ta ninke kayan dayacire, ta adanasu a ma'ajiyarsu. Ta fito masa danashan iska du ta feshe su da turare ta fita dagadakin.Ya gama shirinsa ya fito falon, ta tashi ta taryoshi, tayi masa rakiya har kan tebir.Tsarin data yiwa wajen ma ba karamin birgeshitayi ba.Ta zauna tana zuba mishi abinci, kallonta kawaiyake yi yana kallon tsarin ado da kwalliya.Ta rinka tura mishi gabanshi, tace yaya kacimana? Yace zeeyta ki karasa ladanki ki baniabaki mana.Tayi murmushi bazan iyaba yayakunya nakeji, ya kashe mata ido daya, yace inamijinki kike kunyan bani abinci abaki?To ni zona baki. Ta marairaice don Allah yayakaci, ni ta taka nake kaida ka dawo daga tafiya.Ya dauki cokalin ya fara ci, yana cin abincin yanagyada kai, yana santi yaci abincin nan da yawa,komai saida yaci, saida ya gama ya jawotacinyarsa, ya rinka bata abaki tana ci.Yaya don Allah ka kyaleni haka na koshi, ya shafacikin nata, kullum cikin ki a dame saboda bakyason cin abinci ko dagowa ba ya yi, ko saimunsamu baby ne zai taso?Ta mike da gudu tayi dakinta, ya bita da kallonsha'awa yayi murmushi.Sai da ya shigo daga masallaci, bayan sallarisha'i sannan suka gaisa da talatu da yarangidansayana shiga falon yaga bai ganta ba, a cikindakinta ya sameta, ta kanannade a gado hardarufa da bargo, ya dafa kanta lafiya zeeyta meyafaru kika kwanta? Tace yaya bacci zanyi, yace yanzu zeeyta zakiiya bacci ba tare da kin jini a jikinki ba?Tayi shiru bata ce masa komai ba, don yau atsorace take dashi, tunda taga alamunsa, yakamo hannunta taso muje muyi nafila.Ta biyoshi zuwa toilet, sunyi nafila raka'a biyu,ya dafa kanta ya dade yana musu addu'a, sannansuka shafa.Ya wani kunshin gashin hanta da koda ya rinkabata tare da fresh milk me sanyi, du ta marairaicemasa, tace ta koshi, bazata iyaci ba. Lallabata yarinka yi tana ci, yana fito mata da ice cream saitaware ta karba tana sha katuwar roba saida tashanyeta.Ta mike tayi dakinta yaya saida safe. Ya bita dakallo kawai, ya tashi ya rurrufe ko ina ya tofe daaddu'a, yana shiga dakinta wani kamshi ya dokihancinsa, ya hangota a tsakiyar gado takanannade. Ya hau tsakiyar gadon ya janyebargon. Tsoro ya sake kamata.Zeey dinshi ta rikitar masa da zuciya a yau daibazai iya mata hakuri ba.Lebenta jajir mai taushi, yasa hannu yana zagayeleben nata da dan yatsan shi daya, tana jinsasaita juyar da fuskarta dayan gefen ya kwantoakan bayanta yana shafa fuskarta sai yaji hawayeya mirgino da ita gabansa yasa harshensa yanalashe hawayen da haka yayi dabarar.A yanda yake azabtuwa da kaunarta zai iyahakura da zeey dinshi kuwa? A yanda yake azabtuwa da kaunar zeey anya zaiiya hakura da ita kuwa?Zainab ita kadai ce macen da ya mace akanta, yazube tarin kaunar da yake yi mata, tun tanajaririya bazai iya barin zeey dinshi ba, domin tatafi da zuciyarsa kamar a mafarkinsa daya sabayi. Ko da yaushe.Yasha shgawabar zeey tana yi masa kukansangarta, da marairaita, wanda ya rinka karamasa kaimin abunda yake yi.Ya kara sanyashi cikin yanayin kaunarta, da wanidumbin farin ciki da annashuwa, daya tsincikansa, ta rinka yi masa kuka tare da magiyar yakyaleta, yaya kaine fa yayana, mai sona, maitausayina, yayana ka daina bani wahala. Yanajinta, amma ya kasa kyaleta, sai dai yabi da ita ahankali, don kada tasha wahala sosai amma tawahalar,sanda ya tashi yayi wanka, yayi alwala, kasa fitamasallaci yayi, yayi sallarsa a daki, ya dade yanayi musu addu'a, yanata nuna godiyarsa ga Allahtare da sawa zeey din tashi albarka.Kujera yaja ya zauna, a gaban gadon ya zubamata ido yana mai jin tsantsar farin ciki dakaunarta data ke kara ratsa shi.Yayi murmushi komai na daren jiya yana tunashi,yana son wannan daren yana sashi nishadi.Ya ware masa fili guda acikin zuciyarshi bazaitaba manta shi ba.Yana can tunaninsa na daren jiya yaji motsinta ahankali yana dubawa yaga ta farka.Du ta marairaice tana son yin kuka. Ya kamohannunta zeeyta tashi kiyi wanka kiyi sallah, nabaki break kinga rana tayi.Ta kasa hada ido dashi, don tana tsananin jinkunyarsa, tace ni ka kyaleni bazan iya tashi bajikina ciwo yake yi.Taja bargonta ta dada lulluba.Zeeyta, ya janye bargon, wayyo yaya ni ka kyalenitasa masa kuka.Oh! Zeeyta sorry auta, yau na taboki ko? Yadagota yana matsa mata jikinta a hankali, yanawani lallabata ta langwabe ajikinsa, tana zubarda hawaye, yafi kowa sanin laifinsa dan yasanshagwabar zeey bata kaunar abunda zai tabajikin nan nata, ko yaya ciwo yake taita kukakenan.Kiyi shiru mana zeey.Yayana jikina ciwo yake yi.Kiyi hakuri zeeyta zaki koma dai-dai, bana sonkukan zai haddasa miki ciwon kai.Tayi shiru tana langwabe a jikinshi tamkar tayibacci, ya dauketa yayi toilet da ita, ya hada mataruwa mai dumi, ya rinka gasa mata jikinta, saidayaga tadan ware sannan ya ba waje, tayi wankantsarki tayi alwala.Ta lallba tayi sallah ya fito da break din, ya rinkabata kadan taci ta kauda kai, ya bata maganitasha, da yake lallabata yake yi bai kuma matsamata saita kara ba.Ta langwabe masa yaya bacci zanyi, ya kwantarda ita yana mammatsa mata jikinta, tanata yimasa raki da shagwaba, da haka bacci yadauketa.Yayi ajiyar zuciya ya rungumeta suka ci gaba dabacci, bacci mai dadi ya rinka yi, sai karfe dayaya farka a hankali ya zare jikinsa daga na zainab,wai gudun kada ta farka.Yayi wanka ya shirya cikin shadda da akayi matadinkin boda, yayi kyau sosai aciki yayi aurinficewa, ya nufi gidan wani abinci don yayi wazeey take away tunda shi bai iya girki ba bare yagirka mata.Lokacin data farka taga baya nan, saita mike tashiga toilet ta sake yin wanka, ta dauro alwalatayi sallah. Ta tsaya gaban madubi ta tsarakwalliayarta ta saka wani jan material mai kyalliriga da siket dinkin du sun matseta.Ta saka yari da sarka da abin hannu, du jajayetayi daurin dan kwali daya kara fito mata dakyaun fuskarta.Ta kara turare dakunansu da falon da gidan takunna a.c.Yayi sallama ya shiga tana kishingide akandoguwar kujera tana kallon tashar zeey arabiya, aciki ta amsa sallamar, yazo ya zauna kusa da ita,ya ajiye ledojin hannunsa.Ya kamo hannunta yace "zeeyta abun ma kotarya babu, ya jikin naki?Ta sunkuyar da kanta kasa tace ni lafiyatakalau."yace haba zeeyta kefa kika ce min jikinki na ciwokinata kiran daddy da Abba.Ta durkusa kasa tana boye fuskarta, tace kaiyaya don Allah nidai ka bari.To naji na bari, ai yanzu du abinda bakya so nadaina gimbiyar zuciyata.To taso kici abinci, yana fitowa dashi, tace yayameyasa baka tasheni nayi girki ba, ka siyo abinci.Zeeyta ai yau ranata ce, bazan bari girki yawahalar min dake ba.Sai kinyi sati kina hutawa daga kwanciya saibacci, sai sallah, sai cin abinci sai kula dani.Cikin shagwaba tace a'a nidai yaya zan rinka girkina, bana so ka rinka fita sanyan abinci, dadarajarka, yayana zan iya maka komai, don nafaranta maka, ina kwadayin samun ladan aure.Yace zeeyta ai kin gama samun ladan aure, tundanake ban tabajin farin ciki da nutsuwa irin na jiyaba.Allah yayi miki Albarka zainab, Allah ya barmutare har karshen rayuwarmu.Allah yasa na sama mana baby, ko kuma inanjima mu samu. Tace um-um nidai yaya baza akuma ba bana so.Yace kash zeeyta kada ki kuma fadan hakabakyau, ta kwantar da kanta cikin raunin murya,tace yaya nadaina bazan kuma ba, ka yafe min.Yasa hannu ya shafa kanta, na yafe miki zeeyta,kowane irin laifine da wanda na sani da wandaban sani ba, du na hada na yafe miki kinji zeeyta.Ta daga kai nagode yayana, bani ice cream dinda kec din naci. ta daga kai na gode yayana, bani ice cream dinda kec din naci.A'a zeeyta ki fara cin abinci, ga mutuniyarki kazagashin inji.Ga youghot da fresh milk a frij gasu tufa kiciabinci kadan du saiki ci abunda kike so.To yaya du zanci, dan bani ice-cream din na farasha, ya bude mata yasa dan cokalin yana batatana sha, zeeyta kin farantamin sosai bazangajiya dasa miki albarka ba.Allah yayi miki albarka ubangiji ya miki tukuici dagidan Aljanna, kinsamin nutsuwar da ban tabasamu ba.Zeeyta ki gaya min me kike so nayi miki? Komekike so ki zanyi miki, gaya min me kike so.Yaya ni bana bukatar komai, don komai kayi minyaya, inada komai bani dawani abu dayagagareni.Nidai yaya karatuna shi nake so naci gaba. Yarinka shafa kanta, kada ki damu zeeyta karatu kintayi kenan, har sai kince kin gaji dashi, gobe nanzan sayo miki form ki cike, kwanan nan zaki farazuwa makaranta.Yauwa yayana nagode.Aliyu da zainab sun kara shakuwa da mannewajunansu kamar tif da taya.Da safe ita take shirya musu break dinsu mai raida lafiya, idan da lokaci suci tare, idan sunmakara ta zuzzuba masa a fulas ya tafi ofisdashi.Yana ofis bini-bini yayo waya shidai yaji ya take,yaji muryanta yasan kalau take, kafin yamma yadawo ta sake shirya musu wata dinar.Ta gyara gidan ta baje kamshin nata, cikin gidada falon da jikinta gaba daya ko ina da nau'inkamshin da yake daban ne.Du da talatu tanayi musu girki da ita da sojojinbiyu da suke gadin gidan, da yaron gidan maishayar da fulawowi da share-shareamma du abunda zainab tayi sai zuba musutabawa talatu ta raba musu, saboda sanin hakkindan adam.Ta tsara kwalliyarta ta gani ta fada, tayi shigarkece raini.Ta zauna zaman jiran yayan nata.Da taji karar motarsa zata fito cikin yauki dayanga ta taroshi ya makaleta yana mai jin farinciki da ganinta.Yaita yaba kwalliyar data yi masa.Shiyasa ko kadan baya son yayi nesa da ita, dusanda sai tafikano weekend da kyar suke rabuwa,tana kuka yana aikin rarrashi.Dakyar yake iya tafiya ya barta, amma ko yausheyana manne da waya, suna hira cikin shaukin soda tsantsar kaunar juna.Tuni ya siyo mata form ta cike, harta fara zuwamakaranta.Tare suke fita, ya sauketa a makaranta, intagama laccarta direbanta yazo ya mayar da itagida.Watanta shida a abuja bata taba lekawa kano ba,kuma tana son zuwa don dai yaki kaitane, intayimagana yace karatunta.Zainab ta kara canjawa tayi wani irin kyau naban mamaki tayi fresh da ita, sai wani shekitakeyitayi dumi-dumi da ita, jikinta a murje ta karahaske.Haka Aliyunta da yake yanzu shima da hadinsabulunta yake wanka, da turarukanta shima dasuyake amfani, don haka komai nasu iri daya, duinda akaji kamshinsu ansan sune.Mansura tasan Aliyunta farine, me kyau yanakuma da son kamshiamma tana mamakinsa yanzu, yanda ya wanicanja ya kara kyau da haske, fatarsa take wanitsantsi da shainin wanda ita data ke mace manata baya tsantsi haka.Tana mamaki yanda yanzu yake dan sakin fuska,kamar zafin zuciyar tasa ya ragu, amma ita kumarashin sabo da hakan bata wani sakin jikinta.Bata yi masa maganar zainab, ko tace masa yatake, shima kuwa baya yi mata zancenta.Ba kamar zainab dinba da bata da zance sainaauntynta da Amadinta.Yau litinin yayi sammako daga kano zuwa abuja,a jirgi yana zuwa ofis ya wuce, don bashi dalokacin da zai fara biya wa ta gidalokaci ya kure.Yana tayiwa zeey dinshi waya yana lallbata,tunda yaje ofis din bai samu zama ba, ayyuka neagabansa, sai shidda ya samu kansa, ya isa gida.Yana shiga gidan yaji zuciyarsa ta cika da farinciki, ya dawo zai kasance da zeey dinshi.Yana tsaida motar ya hangota ta taho tana yaukida yanga, kamar hawainiya, yarinyar kullumkamar canjata ake yi, kyanta kara karuwa yake,to ta samu kulawar gwarzon namiji, ya kasadaurewa ya fito da sauri ya tareta, cak! Yadauketa, suna farin cikin ganin junansu.Ya shiga falon da ita, ya zauna akan kujera tanakwance ajikinsa, ta dago kai tana shafa fuskarshi,tace yayana daganin ka yau kasha wahala, yace"wallahi fa zeeyta, tunda naje ofis yau ban hutaba, jikina sai ciwo yake yi.Ta marairaice fuska cikin tausayawa tace, Oh!Sorry yayana, sannu don Allah ka rinka hutawa.Ta mike ta cire mishi kwat din jikinshi da fararrigar ciki ta barshi da bes.Ta cire masa takalmi da safa, du da e.c datawadata falon da sanyi, saida ta rinka yi masafirfita, ta dauko masa sanyaya kunun aya dayasha madara da kwa-kwa da filebo, yayi dadisosai, ta rinka bashi abaki, ta marairaice fuskaalamar tausayi karara a fuskarta, sai wanilallabashi take yi, shi kuma du ya wani langwabemata, ya kwanta mata ajiki, tana dan mammatsamasa jikinsa. Da kyar ya barta taje ta hada masaruwan wanka, me zafi, ya sha turaren wanka.Yana shiga ya mimmike a ciki, sannu a hankaligajiyar ta rinka rabuwa dashi, yaji jikinsa ya ynrmlYana fitowa ya sameta a tsaye a kofar toilet dinda karamin tawul a hannunta, ta rinka goge masaruwan jikinsa, ta zaunar dashi akan abin zama,hadin manta ta dauko tana shafa masa. [9:20PM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 3**17, 3**18 & 4**1 Hadin manta ta dauko tana shafa masa a hankali,shikuma yana wani lumshe ido don ji yake kamartafiyan tsutsa take yi masa.Ta gama shirya shi cikin kananan kaya, ta shafamishi turaruka kamshinsu ya gauraye, suna fitarda kamshi mai dadi.Ta leka fuskarsa tana murmushitace yayana kayi kyau.Ya jawota jikinshi yana jin wata nutsuwa da farinciki du sanda ya rungumi zeey dinshi, don hakako yaushe yake so yajita manne dashi. Du sandayaje kano abunda yake wahalar dashi kenan.Babu irin wannan tarairaya daga wajen mansura,babu irin wannan tattalin son, da daddan kamshi,babu irin girke-girken da zeey dinshi take shiryamasa.Yace zeeyta Allah yayi miki albarka, zeeyta mekike so nayi miki yanda kike faranta min nimazanso inta faranta miki.Gaya min me kike so?Yaya so nake naje gida, naga iyayenmu da 'yanuwanmu.Ki kwantar da hankalinki zeeyta zaki je kano dandazu da safe da zan taho, umma suka tafi kaini'ima asibiti, dazu ina ofis suka yo min waya tahaihu.Ta wani doka tsallen murna ta rukunkumeshi,yaya ni'ima ta haihu? Yayana meta haifa?Ta haifi danta namiji yana nan kato akace.Wayyo yayana gobe zamu tafiyadan bugi bayanta kin fiya zumudi zeeyta.Aikin nawa fa wa zaiyi min.Sai karshen sati zamu tafi muje ki bani abinci.Ta gama zuzzuba masa komai ta tura masagabansa du da sanyi a.c saida tadau mahuccitana dan fifita masa abinci wai don kada yakonashi.Ta dauki wayarsa ta lalubo sunan ni'ima tadanna, ringin biyu ni'ima ta dauka, tace helloyaya.Ihun zainab taji tanata murna, yaya ni'ima kinsama mana baby.Ni'ima ta kyalkyale da dariya, ni kada ki kashemin dodon kunne, yaushe zaki zo autamu?Sai karshen satihaba zeey har sai kin kwana hudusanan zaki zo, kiga babyn naki? I, wallahi to ya zanyi. Kinsan bazan iya tahowana bar yayana ba shi kadai anan, dole saikarshen satin mu taho tare.To shikenan zeey kin san kawai ni na matsu dana ganki ne, tun safe gidan nan cike yake damutane.Kowa yazo sai yace ai yanzu zeey kam zata zotunda na haihu.Auta mun matsu fa da muganki.Tace wallahi nima yaya ni'ima kuna raina.Tun sanda yaya zai taho inaso ya taho dani donna ganku sai yakisaboda makaranta, bakomai autarmu sai kunzo.Kafin tace wani abu, Aliyu ya karbi wayan yakashe.Ya jawota cinyarsa taho kici abinci.Ya fara bata ya taba cikinta "yaushe zaki baninawa babyn ne?Ta langwabe a jikinsa nidai ba yanzu ba yayana.Nikuma yanzu nake so zeeyta.Yaya da wahala fa, kana kallo wajen haihuwamamana ta mutu.Ta saka kuka, yana rarrashinta ya rinka radamata a kunanta, kada ki kuma yiwa mama kuka,addu'a zaki rinka yi mata. Ki taya mama farin cikitana aljanna ta manta da kacaniyar duniya.*** *** ****Ranar jumma'a tun asuba zainab ta gama musushirinsu, tana ta murna da doki, yana dawowadaga ofis kuwa, suka bi jirgin shidda na yamma,harda talatu suka tafi, a filin jirgi direbansu yazoya daukesu, taga an nufi hanyar gidanta.Ta kalleshi tace yaya ba gida zamuje ba, tundayaya ni'ima tana can? Yace a'a saimun je gidakin huta. Tayi shiru kawai bata ce mishi komaiba.Suna zuwa gidan taga komanta fes, yana ajiyeinda ta barshi, yaushe rabonta da gidanta tsawonwatanni, amma babu wani kura ko datti a gidanga kamshinta na nan ciki. Ko du sanda yaya yazoyana zaman gidan?Sallah suka yi ya hau kan kujera ya mike, yanalumshe ido son yayi bacci. Tazo ta zaunaajikinshi ta dan marairaice masa, yaya don Allahka tashi muje gidan yanzuya bude ido daya yana kallontazeeyta bazaki barni na danyi bacci ba? Kayihakuri yaya yanzu aunty sadiya tayo min wayanace mata mun sauka yaya gaba dayansu fasuna gida sun hallara, don Allah yaya mu tafi.Ya mike tsaye tashi mu tafi.Tace yaya kayi hakuri idan ranka ne ya baci,haba zeeyta ba raina bane ya baci,watanni da kikayi ba kiga 'yan uwa ba ai nasandole kiyi zumudi,ya kamo hannunta ya dagota, taso mu tafi.Suna shiga gidan wani ihun da suka sa suka zosuka rungume zainab kowa murna yake yi, dafarin cikin ganinta.Hajiya ta rinka taba jikinta tana cewa, "Aliyuwankan inji kayi mata? Suka sa dariya, zainabtace hajiya me kika gani?Kin canja kinyi kyau, kin kara fari, gashinki yakara tsawo da baki.Kinyi bul-bul dake.Aunty sadiya tace in a hanya muka hadu, ai bazamuyi saurin ganeki ba.Yaya ni'ima tace autarmu, hutu ya kara samuwada jin dadi.Zeey anya kina cin abinci kuwa?Du yanda akayi daga madara sai youghot sai icecream dasu cakulet, cimar hutu dai da jin dadikina kwance komai sai anyi mikizeey auta canjawar taki tayi yawameye sirrin, ko yayanmu yayi ajiyane?Tace ke kika sani, ina babyn namu? Du nafidokinshi da murnar son ganinsa.Ta dauki baby fari tas, kato dashi, ta rungumeshitana jin kaunar yaron.Ta rungumeshi tayi dakin Abba, umma ta tashi dasauri ta rungumota tana cewa 'yata zainab najidadin ganinki, kin kwantar da hankalinki kinyikalau dake.Abba yace "yaki zonan 'yata.Umma ta tafi da ita gaban Abba, ummi tacemasha Allah dana ya iya kulawa ta musamman,Wai zainab saita samu kanta da jin kunyarsu. Wai Zainab sai ta samu kanta da jin kunyarsu, tarinka sun kuyar da kanta, ta kasa dago kaitakallesu.A hankali ta bude bakinta ta gaisheshi, yarinyarta kra birgeshi da shiga ransa.Ta gaishe da umma da ummi, Aliyu yana kasagefen kafar Abba yana mamakin irin kunyar dazainab take ji, du yanda ta matsu tazo ta gaiyayensu, amma ta kasa sakewa yanzu.'yata zainab ya zaman abuja, ince dai ko bawatamatsala?Tace bakomai Abba.Yauwa zainab haka nake sonji, Allah yayi mikialbarka.Amin Abba.Ta ajiye masa turaruka manyan kwalabe masutsada yaita juyasu yana sa mata albarka.Ta ajiye umma da ummi nasu harda humra dakulacca, suma sukai godiya suna sa mataalbarka.Da kyar ta iya mikewa rungume da jariri tayibangarensu.Ta tafi gaban babanta ta zauna, yana lazimi, yayisaurin sallamewa, yana murmushi.Zainab haka kika koma.Tayi murmushi, babana naji dadi da nazo naganka lafiyanka kalau.Kullum kana raina Babana, ina wuni?Lafiya lau zainab kin kyautamin da kika kwantarda hankalinki.Gashi kinyi kalau dake.Mama ta fito da fara'arta tana yi mata sannu dazuwa, ta gaisheta ta bata tsaraban turarukan, babawa mahaifinta kamar yanda ta bawa Abba.Sukai godiya suna sa mata albarka.Ta mike baba bari na koma wajen su yayani'ima.Yace to zainab.Ni'ima tana kwance a gado, aunty sadiya tanaamsa wayar mijinta, tana gaya masa zuwanautarsu, yace ai yana kan hanyar zuwa daukanta,ya ga yanda zeey dinta suka koma.Ni'ima tace gaskiya zainab kin canja da yawa,lallai ruwan aure ya karbeki.Zainab tace, me kuma ruwan aure?Sadiya tace, ai kinsan ita bata sanshiba, yaya maitausayinta ne, saita cika shekara ashirin, sannanzata fara sani ko?Zainab tayi murmushi tace ku kuka sani. Suka samata dariya, ta zauna suka fara hiran yaushegamo.Aliyu ya shigo dakin ni'ima da sadiya suka gaisheshi.Yazo ya zauna kusa da zainab, ya dauki babyn dayake jikinta, ya rinka sumbatarsa yana yabayaronya kalleta, zeey tashi mu tafi gida, tayi kasa damurya tace don Allah yaya ka bari na kwanaanan.Yace ya za ayi na barki, ki kwana anan nakigidan fa?Yaya bafa a gidan zaka kwana ba, kafi so kabarni ni kadai na kwana.Kafin yayi magana tes ya shigo wayarsa, wayartana hannun zainab saita bude tes din, tunda tagaba lambar mansura bace, ta karanta tes dinkamar haka.barka da zuwa yallabai, naji labarin saukarka,kaida madam,ka iso lafiya?Kirjinta yayi wani irin mummunan bugawa,gabanta yana fadi ta dafe kirjinta tana haki.Yayi saurin cewa lafiya zeeytah?Meya faru?Ta sunkuyar da kanta, ta dafe kanta da hannunta,ya ciro hannun ya daga kanta, yace, zeeyta meyafaru?Ta marairaice hawaye nason zubo mata, taceyaya wacece tayo ma tes yanzu?Yace tes me akace acikin tes din?Ta mika masa ya karanta, ya ajiye wayar, yacegaskiya ban san ko wacece ba, don ni banma sanlambar ba, bare nasan wacece tayo tes din.(page nan ya balle).Ranar suna sai da yamma aka fita hotel da zaayi fatin sunan.Jama'ar suna yi musu murna samun karuwa jaririda aka samu yasa masa sunan babansa anakiransa da hanif.Suka zauna a kwataccen wajen da aka tanadarmusu, gaba daya wajen anyi shiru sabodaaddu'ar da ake yi. Sannan wani hadadden motarAliyu ya sawo kai.Hankalin mutane gaba daya yayi kan motar, zubaido kawai suke yi suga isasun da zasu fito dagacikin motar, du da dai wasu sun san motar waye,suna isa wani soja ya fito daga wajen tukin, yabude dayan bangaren na baya, sannan ya budedayan bangaren.A tare suka fito Aliyu da zainab kamar taurari,gaba daya kamshinsu ya cika wurin, suka jerosuna tafe suna hirarsu da dan murmushi, dukawajen saida suka birgesu, tare da basu sha'awa.Banda mansura data diririce ta dabarbarce, itatambaya ma take wacece wannan take manne damijinta? Saida yayarta saratu ta rikota ta mayarda ita kujerarta ta zaunar da ita, tace ki kula kisaisaita hankalinki, kada kiyi wata gigiwa anan,don kada ki manta abunda Aliyu ya miki akanzainab, kinsan ya gaya miki zai iya yin komaiakanta.Sannan mansura ta kawo ajiyar zuciya, yanzuwannan zainab ce, 'yar da nake kiranta dagidahuma itace ta koma haka, ta waye?Aliyu ya cuceni daya barni a kano, saidai ko nimaya mayar dani abuja, ko kuma ayi du wacce zaayi.Saratu ta tabe baki, tace sai kiyi kin manta sandaya koraki gida, yanzu kuma naga alamar kina soki yanke igiyar aurenki, me wannan cikakkiyarmata 'yar kwalisa 'yar gayu, don rabu dake mezai dameshi. Zainab ta dan mika bakinta dai-dai kunnen Aliyutace, don Allah yaya ka amince min naje na gaidaaunty?Yace okey bakomai kije.A hankali ta rinka keta jama'a suna gaisawa.Kamshin data keji a jikin Aliyu mai dadi shi taji tadago kai.Tana dago kai zainab tana mata murmushi, saitaji gabanta yayi mummunar faduwa.Zainab ta rissina sannu aunty ina wuni?Da kyar ta iya amsawa, ta kuma rissina ta gaidayaya saratu.Ta dan doki kafadar hauwa, mutuniyar ba aganinku ko?Hauwa tayi dariya tana rike da hannunta, taceAllah zainab kin canja, sam ban ganeki ba, saikace bakuwar baturiya.Tayi murmushi hauwa bana son sharri fa.Zainab tace aunty yaya yace kizo mu koma can.Ta kalleta ta doka mata harara, tace dan Allahcan matsa ki bani waje, banza munafuka, bazanjeba din.Zainab tace kiyi hakuri aunty, don Allah kizomuje.Bazan jeba munafuka Aliyu dai kin aureshi kinjiabunda yake min mun zama matsayi daya dake.Hankalinki ya kwanta ko?Zainab tace da ita subhanallah aunty me yayi zafihaka? Allah ya zuci zuciyarki.Tayi murmushin karfin hali tace hauwa yayasaratu sai anjima.Suka ce to zainab yaya saratu ta riko hannunta,don Allah zainab kiyi hakuri da abunda ta miki.Tace, lah wallahi bakomai yaya. Ta juya ta tafi.Dai-dai lokacin sabis suke raba abinci, Aliyu yarikota yace mata a kunnenta, kika yi zamanki kikabarni ni kadai ko?Tace kayi hakuri yayana, bazan kuma ba.To shikenan na hakura.Ni'ima da sadiya suka zo wajensu, anata hotuna.Sadiya tace, sadiya tace dan Allah yaya kadanara mana zainab mintuna kadan kagakawayenmu ne ke son yin hoto da ita.Yace, to bakomai, amma kada a wahalar da ita.Tasa dariya, yaya daga yin hoto sai mutum yawahala? Suka tafi da ita, sunata hotuna da kawayensu.Yana shan lemo hankalinsa yana kan zeey dinsa,tana tsakiyarsu anayi musu hotuna, dukkansubabu wanda ya kama kafar zeey dinshi wajenkyau.Yaji anayi masa sallama, ya dago kai ya kalleta,zulaiha ce, kanwar abokinsa yarinyar data keneman takurawa rayuwarsa, a dole sonsa take,du da hade mata ran da yake yi.Ya dan hade fuska yace ya lafiya?Tayi masa murmushi ta zauna, tace yallabaikenan, kwana uku kenan ina yo maka tes baamsa, ko sau daya nayi call dinka kaki dagawa,haba yallabai ina laifin mai sonka?Zainab ana shirin daukansu a hoto, kamar walkiyata hango mace kusa da Aliyu tana yi masamurmushi.A hankali ta rinka yo takunta, tazo ta zauna kantebir din da yake gabansu.Bata ce komai ba, tadai juya musu keya, yacezeeyta, tayi masa shiru kawai.Yace lafiya zeeyta me yake faruwa?Taki waiwayowa bare tace masa wani abu.Ya taso ya rankwafo gabanta, yayi kasa damuryarsa, gaya min meye zeeyta? Kawai saihawaye ya gani ya kokarin zubowa dagaidanuwanta.Yace, "O shit zeeyta.Ya kamo hannunta, taso mu tafi.Sojan yayi saurin bude musu bayan motar, sukashiga ya rufe, zai shigo ya jasu Aliyu ya dagamasa hannu, tare da cewar ba tafiya zamuyi ba.Yace ok sir, ya tafi can wajen shuke-shuke yayizamansa.Ya dubeta, yace zeeyra menene?Meya daga miki hankali kike hawaye?Ta marairaice masa, tace yaya daman 'yan matane dakai? Yace zeeyta wace irin magana ce wannan? Ainakika taba ganina da 'yan mata?Yaya gani nayi ranar da muka zo, wata tayomaka tes, tana yi maka barka da sauka, yanzukuma gashi kuna ta hira da wata, tana tayi makamurmushi.Oh! Sorry zeeyta, ya rungumota yana rarrashinta,yayi murmushi wai zeey dinshi ta iya kishi.Ya rada mata kunanta zeey kinsan bani dara'ayin tara mata, da ina da ra'ayi shekarun damukayi da mansura a baya danayi aure.To da yake bani da wani buri sai naki shiyasawata 'ya mace bata taba burgeni ba, bare ta banisha'awa. Shiyasa na zauna zaman jiranki HarAllah ya kawomu na aureki, yanda kike auta agidanmu, to a wajena ma kene autar mata, dominkece gimbiyar zuciyata ba wata bayanke. Tasadariya Allah yayana?Allah zeeyta.Ta rungumeshi tana dariya.Satinsu biyu a kano suka koma abuja, kuma batasake haduwa da mansura ba, tun a wajen fatinnan, bata kuma gayawa Aliyu cewar, ga abundatayi mata ba.Tana kicin tana girki, ta rinka jin kanta yanajuyawa, jiri yana dibanta, ta kasa hassala komaita zauna a kicin din dirshan, ta matsa kararrawarkiran talatu ta shigo da saurinta, tana fadin ganiaunty mami,halin data ganta ciki ya bata tsorolafiya aunty mami.Ta rinka nuna mata kanta tana lumshe idosaboda jiri.Talatu ta gigice ta daukota ta shimfide a falo, kandoguwar kujera.Ta dauki wayan zainab din ta laluba numbarAliyu, ta danna, tana ringin daya ya dauka, hellozeeyta.Cikin dabir-dabir tace, ba ita bace talatu ce, yacecikin rikicewa, talatu lafiya, ina zeey din tawa ne? Tace bata jin dadi ne gata a kwance.Yayi zumbur ya mike da wayan a hannunsa yafito, ya hau motarsa, bai tsaya kiran direba bayayo gida cikin mintuna kadan.Talatu tayi mamakin saurin zuwansa.Ya dagota zeeyta lafiya meya sameki haka?Ta rinka nuna masa kanta, ya rike kan yana yimata addu'a, ta rinka jin tashin zuciya, tanakokarin amai, ta yunkura, tana so tabar jikinsa, [7:59AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**2 Tana kokarin amai ta yunkura, tana so tabar jikinsa, don kada ta bata shi, amma sai ya sake rungumeta, ta rinka yunkurin aman kasancewar bata ci komaiba sai ruwan shayi kawai data sha ta amayar. Ya rinka shafa kanta yana yi mata sannu, idonsa shima yayi ja kamar yayi kuka don tausayin zeey dinshi. Saida ta gama aman ta kwanta luu a jikinsa saboda rashin kuzari. Ya dauketa ya kaita toilet ya wanke mata jikinta, ya cire mata kayan jikinta, ya sake yi mata wanka ya nadeta a tawul. Ya cire kayansa yayi wanka ya canja kaya, yasa mata wasu kayan, ya dauketa ya nufi mota, ya sata ya figi motar da gudu. Don du ta galabaita aman data yi ya rafkar da ita. Abunka da asibiti na kudi, na manya mutane, nan da nan aka karbi zeey, likita ya fara yi mata aune-aune da taimakon gaggawa. Aka debi fitsarinta da jininta. Suka jona mata karin ruwa da allura, tana ta baccinta, Aliyu yana zaune gefenta, du ya damu ganin yanda ta rame lokaci daya. Bayan lokaci kadan likita ya dawo da gwaje- gwajen tes din da yayi mata. Ya mikawa Aliyu hannu cngrtln soja mata tana dauke da cikin wata biyu. Wani irin nishadi da farin ciki ne ya kwarara a zuciyar Aliyu, ya washe baki yana murna ya daga hannu sama yana godiya ga ubangiji. Yace nagode likita, ka duba min madam sosai, inaso ka kure tunaninka, ka rubuta mana maganguna masu kyau, wanda zasu kara mata lafiya da kuzari ita da baby. Likita yayi murmushi yace, kada ka damu, du maganin da nasan zai taimaka musu zan rubuta muku, amma laulayi dole sai kunyi a hankali, da cikin yayi kwari zata samu yanda kake so. Ka rubuta min abubuwan da zata rinka ci da sha da zai kara mata lafiya da babyn. Ok zan rubuta muku, Allah ya kara sauki, amin. Likitan ya fita Aliyu yayi waya ofis dinsa yake gayawa sakatariyarsa du wanda yazo nemansa yana asibiti, madam dinshi ba lafiya. Ta jajanta masa tare da fatan Allah bata lafiya. A hankali ta bude idonta tana kallon karin ruwan da akayi mata. Ya kashe wayar tare cewa sannu zeeyta. Tace, yaya kasa akayi min allura, a cire min wannan bana so. Ya rinka shafa kanta yi hakuri barinsa su cire miki, ya dagota zaune, tana rungume a jikinsa, likitan ya shigo Aliyu yace, yauwa cire mata karin ruwan naga ya kare. Tana noke hannun, tana wash-wash, tana langwabe ajikin yayan nata, da haka likitan ya zare mata allura yana tsokanarta raguwa me raki. Aliyu ya rinka rarrashinta yana bata youghot da kaza. Kwananta uku a asibiti ta samu sauki, ta ware, abokan Aliyu da matansu kullum suna turuwar zuwa dubata, taji sauki an sallameta ta koma gida. Aliyu kullum yana manne da zainab har hutu ya dauka, yake zaune a gida, don dai kawai kulawa da ita, bashi da magana sai cikin dake jikinta kamar bai taba haihuwa ba. Tana kwance akan kujera tayi matashin da cinyarsa yana karanta mata jarida. Talatuwa ta kwankwasa kofar akayi mata iznin shigowa. Tace aunty mami, me za a girka miki? Tace kiyi min pepper chicken, sai kiyi min hadin salad. Shikenan tace, to yaya fa? Tace a'a haba talatu girkin yayan nawa zan baki kiyi? Ki bari kawai na samu sauki zan mishi da kaina, na hotel dinma an daina siye. Talatu tayi murmushi, tace to uwar dakina, ta fita Aliyu yace nifa bana son abunda zaki wahala ki bari naci gaba da siyo a hotel din. Tace, haba yayana kamarka ka rinka shiga hotel siyan abinci. Ni dai bana so, ka bari zan rinka yi maka nafa samu sauki. Ya shafa cikin nata, to ai ni babyn nawa kada yazo yana kara saki amai, wahala kike yi zeeyta. Bari dai nayiwa su Abba waya na gaya musu albishir tunda kin samu sauki na gaya musu mun samu ciki. Tayi saurin damke wayar cikin shagwaba, nidai yaya gaskiya kada ka gaya musu, so kake su san abunda muke yi, da wane ido zamu kallesu? Nidai kunya nake ji. Haba zainab haka zamuyi ta zama bazamu gaya musu abun farin ciki da ya samemu ba? Um nidai yaya kada ka fada kunya nakeji. To shikenan bazan fada ba. Cikinta yana wata hudu aka karawa Aliyu girman babban matsayi a soja, a lokacin ne kuma ya gama musu tamfatsetsen gida da yake musu gina a kano, ginin da aka farashi tun kafin ya auri zainab. Kowa da bangarensa fadin tsarin gidan bata lokacine, lokacin suka taho kano don zasu tare a sabon gida. Sannan zainab ta ciko tayi fresh, yaron cikin dan wata hudu yayi mata kyau, yadan tasa kadan, amma ba kowa ne zai iya ganewa da cikin ba, sai me kula. Lokacin da suka sauka 'yan gidansu sun zagayeta kamarsa cinyeta, kowa dada sonta yake, Abba da daddy sunfi kowa jin dadi da alfaharin auren 'ya'yan nasu. Umma kuwa kamar ta lashe zainab saboda tsananin jin dadi, bama data hango dan matashin cikin da yake jikinta, tana ganin kuma ta samun jika daga wajen yaron kirki. Ni'ima da sadiya suna zuwa suka rungumeta, suka yi saurin cikata suna taba cikin, zeey ciki? Ta kwalalo ido "bani da komai, suka yi dariya, "um mun gani dai. Ranar akayi walimar tarewansu a sabon gida, kowa ya yaba da tsarin gidan da kyansa makeken gida unguwa guda, ga wajen wasan buga ball, wajen basket ball, lilina na yara, ga lambu da swiming ful a ciki. Da dai abubuwan kawata gida. TATTALIN SO 4**3 . Yarinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya, harta koma bacci, sannan ya mike ya tafi. Be dade da jan motarsa ya tafi ta farka da wani gigitaccen ciwon baya da mara, ta farka tana salati, ta matsa kararrawar kiran talatu shiru bata shigo ba ta tuna fa ashe tun dazu ta tafi gidan yarta. Ta taso a hankali tana dafe da kugu, tana salati ta fito babban falo. Mansura tana zaune tana kallo, ta jiyo salatinta da nishinta, ta juyo tana kallonta, ta tabe baki ta juya taci gaba da kallonta. Zainab ta durkusa a gabanta ta daura kanta akan cinyarta, tana salati. Aunty dan girman zatin Allah ki taimaka min ki tallafawa maraicina, ki dubi girman Allah aunty kinsan abunda nakeji. Saita ji jikinta yayi sanyi, taji tausayin yarinyar ta tuna irin gigicewar dayi sanda tana nakudar Ahmad, da yanda yarinyar tai ta kuka. Ta juyo ta kalleta, ta murkususu a jikinta, ta dauki waya ta bugawa direban gidan, tace maza ya fito da mota. Ta taimakawa zainab din, saida suka shiga direba ya dauki hanyar asibiti data ke zuwa awo. Mansura ta fito da wayarta tana neman layin Aliyu amma bata sameshi ba, har suka isa asibitin, ana kokarin shigar da ita dakin haihuwa, ta samu lambar Aliyu ta shiga. Ringin uku ya dauka, hello! . Aliyu muna asibiti da zainab ba lafiya. Kafin ta karasa cikin kara yace mata what? Tayi saurin cire wayan daga kunnenta, don jin yana barazanar tsorata mata dodon kunne. Daga nan ya hawo motarsa ya nufo asibiti, ya tarar da ni'ima da sadiya dasu umma sunata zarya a kofar dakin data ke ciki. Yana zuwa bai tsaya ba ya banka dakin haihuwar tayi wujiga-wujiga tana salati, wata likita tana tsaye a kanta. A galabaice ta rinka miko masa hannu, tana cewa wayyo yayana zan mutu, yaya ka yafemin, yaya haka mamana tayi shiyasa ta rasa ranta. Yazo ya zauna a gefen gadon ya rungumeta, yana rarrashinta kiyi shiru zainab, kita addu'a Allah zai saukeki lafiya kinji? Ya rinka murza mata bayanta, yana karanata addu'o'i ya tofa a ruwa ya bata tasha. Taji ciwon ya lafa mata, ta bingire a jikinsa ta fara bacci, can wani gigitaccen ciwo ya farkar da ita, cikin lokaci kankani ta rikice da salati ta kankame Aliyu likitan tana taimaka mata, katuwar 'yarta ta fado fara tas da ita. Wata irin dariya Aliyu ya saka, tare da jerawa ubangiji kirari, yana nuna godiyarsa ga Allah. Ya dauki 'yar ya rungumeta, yanata aikin kallon babyn, likita tana gyara zainab, kamar wanda aka mutsina yayo waje da gudu yana kiran umma, mama, ummi, gaba daya suka yo kansa suna masu farin ciki. . Ummi ta karbeta, kai tubarkallah masha Allah. Su ni'ima da sadiya sai lekenta suke yi a hannun ummi, su naso su dauketa, amma Aliyu ya hana, wai kada a jagwagwalaa, ko ya manta suma sun a haihune. Likita ta fito cikin kalmar turanci take ce masa likita baka tsoro bebyn tayi mura ne, ka fito da ita take shakar iska? Aliyu yace ato ku kawota. Ya karbeta da sauri yayi cikin dakin da ita. Su umma duk suka bishi don ganin jikin zainab din. Zainab tana ganin su umma ta rufe idonta wai kunyarsu take ji, ni'ima da sadiya sunata yi mata dariya. Mansura kuwa tana tsaye a gefe tana mamakin irin murnar da Aliyu yake yi, kamar wanda bai taba haihuwa ba. Mansura ta fito daga dakin, don bazata iya kallon takaici ba. Ya wani zauna dirshan a gadon zainab din, jikinsa yana gogar nata, kamar zai rungumeta, sai wani dariya yake. Ta dauko wayarta ta buga, hello yaya saratu, yarinyar nan fa ta haihu yanzu, haba dan Allah meta haifa? Um du wannan iyayi da akeyi ta bige da haihuwar mace. Saratu tace "A me bambacin mace da namijin,kema ai yaya saratu kinsan mace da namiji akwai bambanci. . Ai namij shine magajin gida bare ahmad shekara takwas fa kenan, a hada da 'ya mace ta mintuna amma kinga yanda shida kannensa da iyayensa yanda suke ta wani murna da farin ciki. Saratu tace gaskiya mansura sai anyi miki uzuri, wannan hali naki sai an taimaka miki da addu'a, ni kinga bazan iya sauraran wadanan kananun maganganu naki ba, ta kashe wayar. A ranar aka sallamesu saboda mai jego da baby lafiyarsu kalau. Ummi itace a gun zainab. A ranar da dare saida ta kori Aliyu bangarensa, da asuba talatu ta girka garwa kan kuka gas, ruwan ya tafasa ta kwashe, ummi tayi wa zainab cikakken wakan jego, tana zillewa tana wash a haka aka gama. Zainab tana shiryawa ummi tana yiwa baby wanka talatu tana goge lokaci daya du suka gama. Me jego da baby sun fito dagwas shar dasu, gaba daya bangaren nata ya rikice da kamshi me rikita zuciya. Karfe takwas Aliyu ya shigo, ya durkusa ya gaida ummi, ya karbi babyn a hannunta, yace ummi zeey din tana ina? Tana daki. Ya mike da babyn a hannunsa ya shiga dakin , sai yaji kamshin da dakin yake yafi na ko ina dadi. Tana zaune a gefen gado ya shiga da dariyarsa, me jego kinsha kamshi. Tayi murmushi yazo ya zauna kusa da ita. Ta durkusa kasa, yaya ina kwana? Lafiya lau, yaya babyn ta kwana? Gata nan ka ganta. Ya dago zainab din ta zauna a jikinsa, zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? . Zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? Saboda me yaya? Wallahi tunani babyn nan tawa 'yar kyakywan nan ta zauna min daram a rai, tunda na taso ranar da aka haifeki, na ganki kika zauna daram a zuciyata, ban taba tunanin za a samu abunda zai kuma shiga zuciyata ya zauna min irin haka ba, sai gashi kin haifa min kyakyawan diyata da tafi komai shiga zuciyata. Zainab ta kalleshi cikin shagwaba tace, yanzu yaya kafi sonta dani? Yayi murmushi ya shafi fuskarta, yace ai ke dabance zeeyta, kaunar danake miki bata da misali, amma kinga bebyn nan tawa ma ta maye ruhina gaba daya. Zainab kin gama min komai da kika haifomin bebyn nan, bani da bakin da zan miki godiya, bani da abunda zan baki. Babbar addu'a da zan miki Allah ya miki tukuici da gidan Aljannah amin yayana. Bebyn ta dan motsa, ya balle marfin swan water, ya tsiyayo kadan a kofin azurfa ya bata tasha. Yace bata nononta tasha. Yaya wallahi data kama jiya, baka ji zafi ba. Yi hakuri ki bata a hankali zai daina zafin. Zainab din taba bata tana cije baki tare da cewar wash. Lallabata yakeyi yana cewa, yi hakuri zeeyta, tasha ta koshi, yauwa bata dayan. Da haka babyn tasha ta koshi, ya karbeta ya dorata a kafada, yana shafa bayanta har tayi gyatsa taci gaba da baccinta. Zainab ta dora kanta akan cikinsa, yana tambayarta me da me take so ayi shagalin suna? Suka jiyo karadin ni'ima da sadiya suna buga kofa yace su shigo. Suka shigo, sadiya tace yaya ka hade zeey din da bebyn du ka rikesu anan ga jama'a ga jama'a can sunata zuwa barka ba me jego ba beby. Yace nifa bana son yawan daukan nan fa, saboda shi yake kawowa yara ciwon jiki. A fitar da kan gadonta falon a sakata a ciki, a rufe da net din, du wanda yazo ganinta ya ringa lekata kawai, a ganta haka basai sun dauka ba. Ranar kwana hudu aka kawo kayan barka akwatuna shidda uku na beby akwatuna uku na mai jego fadan kayan da suke cikin akwatin bata lokacine. . Mansura ta mike fuu tayi bangare Aliyu, ta banko kofar dakinsa, babu sallama ta tsaya masa tsegege aka, yana kwance akan gado yana kallonta. Tace Aliyu nagaji da wannan rashin adalci naka, ni bazan iya zama ba, kana nuna min iyakacina, ka dubi uban kaya daka jibgawa zainab da jaririyarta, ni wallahi bazan yarda ba saide kome zai faru ya faru, ya daga mata hannu ki saurara kada kiyi min hayaniya aka, fita ki bani waje. Ta fito ta kwashi akwatunan daya bata ita da Ahmad tasa aboot din motar da ya bata da akwatunan ta tafi gidansu. Mansura tana isa gida, tasa kannanta suka shigo mata da akwatunan, iyayenta suna falo da saratu da hauwa, suka tareta da lafiya? Tace wallahi Alh na gaji da rashin adalcin mutumin nan, ka dubi 'yan kayan da ya bamu nida Ahmad, amma ita ya hada mata akwatuna shidda ita da 'yarta kuma ya bata irin motar da ya canja min. Saratu ta bude kayan tana gani, super da holland da les da material da shadda ganila ga takalma jaka da sarkar gwal. Akwatin Ahmad ma kananan kaya masu tsada, sai shadda da boyel masu tsada sun sha aiki, kala goma sha daya, ga takalma da huluna masu kyau da tsada, harda glas mai ruwan gwal suka gama gani, saratu ta rufe kayan, hajiya tace mun gani Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya kara buda masa. Mansura tace, hajiya nifa na taho gida, ku kirashi kuyi masa fada bazan iya zama da wannan rashin adalcin nasa ba.... Kafin ta rufe bakinta Alh ya wanke mata fuska da mari, hajiya ta rufeta da duka. Dabbar yarinya mara hankali, dazunan ya kawomin makullin mota sabuwa kar. Ya aikowa da mahaifiyarki katon injin kankara don ta rinka sana'a dashi shine kike kokarin tozarta kanki, da yake bakisan abun arziki ba, to du ranar da kika sake zuwa gidan nan kika kawomin karar mijinki, saina karyaki, bare kuma kiyo yaji, wannan kasheki zanyi murus har lahira. Fita ki bani waje, ya biyota tayi waje da sauri, . kananta suka mayar mata da akwatunan cikin mota, taja ta koma gida tana hawaye, fuskarta da yatsun babanta daya mareta. Tazo ta wuce ta babban falo tana kuka Aliyu yana zaune yana kallo, ko kallonta baiyi ba, ta wuce bangarenta. Ranar suna aka sawa jaririyar sunan maman zainab, suna kiranta da ihsan. Taron suna yayi kyau angama lafiya aka watse. Kyaututuka da zainab ta samu baza su lissafuba, daga kawayenta, abokan Aliyu 'yan uwa da abokan arziki, kayan kamar a bude sito dashi. Yaya ni'ima tace, kinsan kuwa yau shekarar ku uku cif da aure da yaya. Shida yayi alkawari saikin shekara uku sannan zai kusanceki, sai gashi shekara uku tazo da 'yar diyarku ko? Zainab tace ke kika jiyo, ni ba ruwana. Suka sa mata dariya. *** ***** kwanci tashi rayuwa ta mika, zainab tuni sunyi arba'in, harta koma abuja, taci gaba da karatunta. 'yar diyarta saida daddynta ya nema mata tsari sosai, saboda kyan Ihsan du wanda ya bude baki, sai yace hu! Wannan yarinyar da kyau take. Ihsan watanta shidda kenan tayi 'yar kubibi abun sha'awa da 'yan hakoranta biyu abakinta, tayi sabo da Aliyu du sanda ya dawo gida, yana tare da ita, don haka data ganshi tana bayan talatu zata rinka zillo. Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta... [8:01AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**4 Tabbas badan tasan zafin zuciyar Aliyu ba, ba zaiyi mata ta dadi ba, da sai ta barar da abincin. Fuu! Ta tashi tayi daki, kamar kububuwa, su kuwa basu kula da ita bama. Sati yana cika suka koma Abuja, Aliyu yaci gaba da rainon zainab da cikin da yake jikinta, taci gaba da zuwa makarantarta, Aliyu shi yake dada ganar da ita gun da ya shige mata duhu, don haka kwakwalwarta ta sake budewa, take da kokari sosai. Don ma yanzu cikinta yayi nauyi, wani abun yana yi mata wahala, tana daurewa ne, don saboda Aliyu kokari yake ya hanata zuwa makarantar, wai tana wahala. Ga hajiya tanata damunsa da waya ya kawo zainab ta haihu a gida, du sanda yazo wkend hajiya ta sashi a gaba kenan tai ta mita. Dole sai ya kawo zeey din ko kuma tasa a kawota, har abujan ta taho da ita. Yace hajiya kiyi hakuri, exam suke yi, yanzu saura sati biyu su gama, suna gamawa zan dauki hutun shekara saimu taho tare, tace to yanzu naji magana. Suna gama jarabawa kuwa, da sukayi hutun wata biyu suka taho gida kano. Du wata siyayyar haihuwa ta kayan baby da mai jego Aliyu ya wuce dubai zaiyo musu acan. Satinsa daya acan ya dawo ya tarar cikin zeey dinshi ya kara girma, don komai a wahale take yinsa, da kyar take daga kafa. Har baya so yaga ta tashi don sai yaga kamar ya ciro cikin ya dawo dashi jikinsa. Da ta tashi zai dawo da ita, menene ne, ina zaki? Yaya lemo zan dauko maka, ya kwantar da kanta a kafadarshi yana lallaminta kamar karamar yarinya, ki bari zan dauko da kaina, don Allah ki daina wahalar da kanki, ni nake jin ciwon ajikina. Sai kuma ta langwabe a jikinsa ta kama kuka ya rinka jijjigata, yana rarrashinta, ya rada mata a kunanta menene, gaya min me akayi miki? Yaya ba kaine kayi tafiyarka ka barni ba, har kwana bakwai?ya rinka shafa bayanta, shikenan yi shiru, bazan kuma tafiya na barki ba. Shikenan yi shiru kada kanki yazo yana ciwo. Mansura tazo kansu tana huci, tace, ai saika mayar da ita ciki, karewar shagwaba da sangarta, ko kuma ka sakata a jaka, ka rinka yawo da ita du inda zaka je. Kuma wallahi rashin adalci da ake yi min na daina yarda, bazan kuma zama anan ka dauketa ku tafi abuja ba, kana tura mata kudi kana kashe mata kudi acan, taci abunda du ranta yake so, ka kalli yanda kuka canja kamar masu rayuwa a turai. To wallahi ko mu rinka tafiya abujan gaba daya, ko kuma wananan intaje tayi watanni wannan ma taje. Ya daga mata hannu ya isheni, tunda ke baki iya sannu da zuwa ba, sai kananan maganganu kika iya. Ta tafi tana kunkuni a dakeka a hanaka kuka, nidai bazan yarda da zalunci ba, ko gware kuka yi kuka fito karewar 'yan uwantaka. Ta bar wajen. Aliyu ransa ya baci, ya rinka huci yana kokarin tashi, zainab ta sake langabewa ajikinsa, tana shafa kirjinsa, yayana menene dan Allah? Ka huce kada damu yayana. Da safe zainab tasha kwalliyarta da wata ganila shadda bulu tayi kyau, Aliyu ma yasha wata lallausar farar shadda, sai kyalli takeyi kamar boyal, sai tashin kamshi suke yi, kamshin da yake tsoratar da mansura, ta rasa wani irin kamshine dasu. Du da ya hanata yin komai amma ranar girkinta bata iya hakuri saita yi masa girki. Yau ma ita ta hada break din suna kan tebir din, shida mansura suna ci amma ita ta kasa cin komai. Aliyu yace zeeyta kici mana. Tace, yaya bazan iya ci ba. Nasa talatu ta gasa min hanta ita kawai zanci. Ya ajiye kofin tea din, yace, bakya jin dadi zeey, tun jiya ina kula dake, taso na kaiki asibiti. Tace, yaya bana jin ciwon komai bakina ne kawai ba dadi. Mansura ta tabe baki ta yamutsa fuska, tace kyaji da gulmarki, haihuwa dai ba abar wasa bace, in kin tsaya iyayi kyasha wahalarki ke kadai. Aliyu yace Allah zai rabata da wahala, lafiya lau zata haihu, na samu jaririn dana dade ina mafarkin samu. Mansura tace Allah sarki wane dare ne jemage bai gani ba? Ai sai daran mutuwarsa. Talatu tayi sallama ta shigo ta kawo mata gashin hantarta, Aliyu ya karba ya yanka yasa wa zainab a baki, ta rinka tauna tana yamutsa kamar mai cin magani. Shi kuma du ya damu, sai lallabata yake yi da taci, mansura kuwa ta kumbura tayi tim, haushi da takaici suka cikata. Ni'ima tayi sallama ta shigo tana dauke da yaronta hanif, zainab ta kama dariya, Oyoyo 'yar uwa naji dadin zuwanka, bani yarona naji duminshi. Aliyu yayi saurin karbarsa yana cewa, zeey ai bazaki iya daukansa ba, tubarkallah yayi nauyi. Aliyu ya rinka yi masa wasa yanata dariya, ni'ima ta gaishe da yayan nasu. Ta juya tana gaishe da mansura, ta amsa a ciki, ni'ima ta shareta don intana cikin wannan yanayin bada sauraronta. Ni'ima ta fito da atamfar super hollan da les masu kyau, tace zainab ga ankon suna mun fito dashi. Zainab tace yaya ni'ima har wani anko za ayi? Tace ke kada kimanta dan autarmu nefa da babban yaya, ai dole muyi abubuwan da zasu kayatar masa da taron sunan dan dangi (kuji ni'ima da tsokana) zainab ta debi kayan ta mikawa mansura, aunty ga ankon suba nan su yaya ni'ima sun fitar. Ta watsar da kayan ta doka mata tsaea, dan Allah can yimin shiru kwaji da munafuncinku, maga dai abunda za a haifa ko dan gwal ne ma gani. [8:02AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**5 Aliyu ya dago kansa yayi mata wani mummunan kallo, ya rinka wani huci na bacin rai, mansura ta juya ta shige bangarenta. Aliyu ya mike zai bita zainab ta rikoshi ta marairaice fuska, kamar me shirin yin kuka, tace yaya don Allah kayi hakuri, kaji ka huce, bani break din zanci. Ya koma ya zauna, yayi ajiyar zuciya, ya rinka bata break din du da ba dadinsa takeji ba, amma ta daure taci sosai, don ta kwantar masa da hankali. A yangace tace, yaya na koshi, yayi murmushi, ai naji dadi ma da kika ci wannan din, hankalina har ya kwanta. Ya mike ya dauki makullin mota, bari naje ofis, na tabbatar da kayan da suka iso jiya, an gama jibgesu a sito. Ta mike a hankali ya riketa, kiyi zamanki ki huta, ta makale kafada, tace um-um nidai saina rakaka. Ta dauko masa jakarsa, suka jera suna hira cikin nishadi, suna murmushi, suna zuwa kofar falon ya karbi jakan yace, ta koma ciki, ta rinka daga masa hannu yana daga mata, har ya shige mota, ita kuma ta dawo falon, ni'ima ta mike suka yi bangarenta. Ni'ima tace wai ke zainab ke wacce irice? Ta rinka yi miki abu iri-iri bazaki dau mataki ba, kuma ki rinka hana yaya yi mata komai. Tace haba yaya ni'ima, Allah du abunda take yi baya sakamin bacin rai, ko daya a zuciya. Kuma in na mace zan ringa biyeta, ai kullum yaya bazai samu kwanciyar hankaliba, du inda yaje yana tunanin halin da gidansa yake ciki. Yanzu kuwa ko ina yaje hankalinsa kwance, yasan bazan saurareta ba, kuma dan habaici tai tayi mana, nasan ko giyar wake tasha bazata kai hannu ta dake ni ba. Hayaniya kuwa taita yi, wata rana zata gaji ta daina, dan karfe daya baya amo. Ni'ima tace hakane. Suka ci gaba da hirar abunda ya shafesu. **** **** ***** mansura tana shiga dakinta ta dauki wayarta ta bugawa tayarta saratu. Hello! Mansura ya akayi ne? Tayi tsaki hum yaya saratu, gaskiya matsalolin gidan nan sun fara isata. Tace menene kuma meya faru? Tace, um mutumin nan du ya wani rikice akan cikin yarinyar nan, saika ce wanda bai taba haihuwa ba, zaita lallbata tana wani yanga da yamutsa ga shagwabar tsiya (komai girman namiji wani lokacin yana son ana masa shagwaba), ta kama kukan gulma ya rikice yanata rarrashinta, sai kace wata 'yar kwai. Yarinya ina ganinta gidahuma kamar ba wayayyiya ba ina ganin bazata iya aikata abunda take yi ba, kinga yanda take zama dakyar ta tashi da dakyar amma du ranar girkinta, ita zata yi masa du wani abun da kanta. Kuma shima da yake munafikine, ranar girkina idan kuku yayi girkin iyakacinsa yaci cokali biyu, ko uku ya ture. Ranar girkinta kuwa ta sashi a gaba tana loda masa abinci yana ci yana santi tana dariya, sai yaci dayawa. Baki ga yanda yake daukin cikin nan ba, kullum addu'arsa da fatansa ta haihu lafiya inda kika san ba a taba yi masa haihuwa ba. Gashi ya mayar da Ahmad din irin makarantar dasu zainab din suka yi, bazai dawo ba sai shidda na yamma wannan ai zalunci ne. Gashi ya debi yayunta ya dorasu akan dukiyarsa, wannan kamfanin nasa fa a hannunsu yake, daya darakta daya manaja. Saratu ta katseta to ina ruwanki ba 'yan uwansa bane? To idan 'yan uwansa ne ni bazaiyi min kara ba? Kamfaninsa na motoci ya daura kannensa, da suke uwa daya uba daya da ni'ima su biyu da nasa kannen biyu. Shi kenan arzikinsa saide suci su isu? Ni banda nawa dangin kenan? Saratu tace kedai mahaukaciya ce wallahi, ki jawowa kanki abunda zai sakeki, kizo mu sake zama. Kina kallona gashi miji yaki samuwa, kuma kice yana yiwa danginsa banda naki. Kina ina ya dauki rabi'u da hamisu ya kaisu kamfanin nasa ya basu aikin yi. Ko kin manta da zaman banza suke yi. Gashi yana zuwa yana gaida iyayenmu, ya kawo musu kudi da kayan abinci. Du ya dauke wasu sabgogin gidan nan ba tare da kin sani ba ko yayi shawara dake. Nidai bazan gaji da baki shawarar ki rike mijinki da kishiyarki ku zauna lafiya. Mansura tace, kai yaya saratu abunda nake nuna miki daban abunda kike hange daban. Sai anijima tunda kinki ganewa. Bayan sati daya da dawowan Aliyu daga dubai, ranar a dakin zainab ya kwana. Da safe ya taimaka mata tayi wanka, da kwalliyarta ya bata break taci. Ta langabe ajikinsa, ya dago kanta, menene zeey, tana limshe ido tace bacci, yace bai isheki ba baccin? Ta daga kai alamar amsawa. Ya kwantar da ita a hado a hankali ya rinka matsa mata jikinta, da bayanta data fi yawan kuka dashi saboda ciwo ya rinka murza mata shi, sannu-sannu tayi bacci, yayi ajiyar zuciya ya mike ya fara shiri ya gama shirinsa yana fesa turaruka. Wayarsa tayi kara ya dauko yana amsa wayar ta bude ido tana kallonshi. Ya gama wayar yasa a aljihunsa, ya dauki makullin motarsa yazo ya durkusa a gabanta, yasa hannu yana shafa kanta, yace, an shammaceni anyo min waya, kararta ta tasar min dake, da nasan za a yo wayar nan da falo zan fita. Da baki tashi ba, bana so ki samu matsala kanki yazo yana ciwo. Tace yaya bakomai, normal nake jina, tace yaya ina zakaje? Ofis din su Abba znje kona zauna? A'a yaya kaje Allah kiyaye hanya, ya dawo dakai lafiya. To koma baccinki ya rinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya harta koma bacci [8:03AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**6 Yarinka lallaminta yana jijjigata kamar karamar yarinya, harta koma bacci, sannan ya mike ya tafi. Be dade da jan motarsa ya tafi ta farka da wani gigitaccen ciwon baya da mara, ta farka tana salati, ta matsa kararrawar kiran talatu shiru bata shigo ba ta tuna fa ashe tun dazu ta tafi gidan yarta. Ta taso a hankali tana dafe da kugu, tana salati ta fito babban falo. Mansura tana zaune tana kallo, ta jiyo salatinta da nishinta, ta juyo tana kallonta, ta tabe baki ta juya taci gaba da kallonta. Zainab ta durkusa a gabanta ta daura kanta akan cinyarta, tana salati. Aunty dan girman zatin Allah ki taimaka min ki tallafawa maraicina, ki dubi girman Allah aunty kinsan abunda nakeji. Saita ji jikinta yayi sanyi, taji tausayin yarinyar ta tuna irin gigicewar dayi sanda tana nakudar Ahmad, da yanda yarinyar tai ta kuka. Ta juyo ta kalleta, ta murkususu a jikinta, ta dauki waya ta bugawa direban gidan, tace maza ya fito da mota. Ta taimakawa zainab din, saida suka shiga direba ya dauki hanyar asibiti data ke zuwa awo. Mansura ta fito da wayarta tana neman layin Aliyu amma bata sameshi ba, har suka isa asibitin, ana kokarin shigar da ita dakin haihuwa, ta samu lambar Aliyu ta shiga. Ringin uku ya dauka, hello! Aliyu muna asibiti da zainab ba lafiya. Kafin ta karasa cikin kara yace mata what? Tayi saurin cire wayan daga kunnenta, don jin yana barazanar tsorata mata dodon kunne. Daga nan ya hawo motarsa ya nufo asibiti, ya tarar da ni'ima da sadiya dasu umma sunata zarya a kofar dakin data ke ciki. Yana zuwa bai tsaya ba ya banka dakin haihuwar tayi wujiga-wujiga tana salati, wata likita tana tsaye a kanta. A galabaice ta rinka miko masa hannu, tana cewa wayyo yayana zan mutu, yaya ka yafemin, yaya haka mamana tayi shiyasa ta rasa ranta. Yazo ya zauna a gefen gadon ya rungumeta, yana rarrashinta kiyi shiru zainab, kita addu'a Allah zai saukeki lafiya kinji? Ya rinka murza mata bayanta, yana karanata addu'o'i ya tofa a ruwa ya bata tasha. Taji ciwon ya lafa mata, ta bingire a jikinsa ta fara bacci, can wani gigitaccen ciwo ya farkar da ita, cikin lokaci kankani ta rikice da salati ta kankame Aliyu likitan tana taimaka mata, katuwar 'yarta ta fado fara tas da ita. Wata irin dariya Aliyu ya saka, tare da jerawa ubangiji kirari, yana nuna godiyarsa ga Allah. Ya dauki 'yar ya rungumeta, yanata aikin kallon babyn, likita tana gyara zainab, kamar wanda aka mutsina yayo waje da gudu yana kiran umma, mama, ummi, gaba daya suka yo kansa suna masu farin ciki. Ummi ta karbeta, kai tubarkallah masha Allah. Su ni'ima da sadiya sai lekenta suke yi a hannun ummi, su naso su dauketa, amma Aliyu ya hana, wai kada a jagwagwalaa, ko ya manta suma sun a haihune. Likita ta fito cikin kalmar turanci take ce masa likita baka tsoro bebyn tayi mura ne, ka fito da ita take shakar iska? Aliyu yace ato ku kawota. Ya karbeta da sauri yayi cikin dakin da ita. Su umma duk suka bishi don ganin jikin zainab din. Zainab tana ganin su umma ta rufe idonta wai kunyarsu take ji, ni'ima da sadiya sunata yi mata dariya. Mansura kuwa tana tsaye a gefe tana mamakin irin murnar da Aliyu yake yi, kamar wanda bai taba haihuwa ba. Mansura ta fito daga dakin, don bazata iya kallon takaici ba. Ya wani zauna dirshan a gadon zainab din, jikinsa yana gogar nata, kamar zai rungumeta, sai wani dariya yake. Ta dauko wayarta ta buga, hello yaya saratu, yarinyar nan fa ta haihu yanzu, haba dan Allah meta haifa? Um du wannan iyayi da akeyi ta bige da haihuwar mace. Saratu tace "A me bambacin mace da namijin,kema ai yaya saratu kinsan mace da namiji akwai bambanci. Ai namij shine magajin gida bare ahmad shekara takwas fa kenan, a hada da 'ya mace ta mintuna amma kinga yanda shida kannensa da iyayensa yanda suke ta wani murna da farin ciki. Saratu tace gaskiya mansura sai anyi miki uzuri, wannan hali naki sai an taimaka miki da addu'a, ni kinga bazan iya sauraran wadanan kananun maganganu naki ba, ta kashe wayar. A ranar aka sallamesu saboda mai jego da baby lafiyarsu kalau. Ummi itace a gun zainab. A ranar da dare saida ta kori Aliyu bangarensa, da asuba talatu ta girka garwa kan kuka gas, ruwan ya tafasa ta kwashe, ummi tayi wa zainab cikakken wakan jego, tana zillewa tana wash a haka aka gama. Zainab tana shiryawa ummi tana yiwa baby wanka talatu tana goge lokaci daya du suka gama. Me jego da baby sun fito dagwas shar dasu, gaba daya bangaren nata ya rikice da kamshi me rikita zuciya. Karfe takwas Aliyu ya shigo, ya durkusa ya gaida ummi, ya karbi babyn a hannunta, yace ummi zeey din tana ina? Tana daki. Ya mike da babyn a hannunsa ya shiga dakin , sai yaji kamshin da dakin yake yafi na ko ina dadi. Tana zaune a gefen gado ya shiga da dariyarsa, me jego kinsha kamshi. Tayi murmushi yazo ya zauna kusa da ita. Ta durkusa kasa, yaya ina kwana? Lafiya lau, yaya babyn ta kwana? Gata nan ka ganta. Ya dago zainab din ta zauna a jikinsa, zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? A daure anayin comment please [8:04AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**7 Zainab kinsan kuwa jiya da kyar bacci ya daukeni? Saboda me yaya? Wallahi tunani babyn nan tawa 'yar kyakywan nan ta zauna min daram a rai, tunda na taso ranar da aka haifeki, na ganki kika zauna daram a zuciyata, ban taba tunanin za a samu abunda zai kuma shiga zuciyata ya zauna min irin haka ba, sai gashi kin haifa min kyakyawan diyata da tafi komai shiga zuciyata. Zainab ta kalleshi cikin shagwaba tace, yanzu yaya kafi sonta dani? Yayi murmushi ya shafi fuskarta, yace ai ke dabance zeeyta, kaunar danake miki bata da misali, amma kinga bebyn nan tawa ma ta maye ruhina gaba daya. Zainab kin gama min komai da kika haifomin bebyn nan, bani da bakin da zan miki godiya, bani da abunda zan baki. Babbar addu'a da zan miki Allah ya miki tukuici da gidan Aljannah amin yayana. Bebyn ta dan motsa, ya balle marfin swan water, ya tsiyayo kadan a kofin azurfa ya bata tasha. Yace bata nononta tasha. Yaya wallahi data kama jiya, baka ji zafi ba. Yi hakuri ki bata a hankali zai daina zafin. Zainab din taba bata tana cije baki tare da cewar wash. Lallabata yakeyi yana cewa, yi hakuri zeeyta, tasha ta koshi, yauwa bata dayan. Da haka babyn tasha ta koshi, ya karbeta ya dorata a kafada, yana shafa bayanta har tayi gyatsa taci gaba da baccinta. Zainab ta dora kanta akan cikinsa, yana tambayarta me da me take so ayi shagalin suna? Suka jiyo karadin ni'ima da sadiya suna buga kofa yace su shigo. Suka shigo, sadiya tace yaya ka hade zeey din da bebyn du ka rikesu anan ga jama'a ga jama'a can sunata zuwa barka ba me jego ba beby. Yace nifa bana son yawan daukan nan fa, saboda shi yake kawowa yara ciwon jiki. A fitar da kan gadonta falon a sakata a ciki, a rufe da net din, du wanda yazo ganinta ya ringa lekata kawai, a ganta haka basai sun dauka ba. Ranar kwana hudu aka kawo kayan barka akwatuna shidda uku na beby akwatuna uku na mai jego fadan kayan da suke cikin akwatin bata lokacine. Mansura ta mike fuu tayi bangare Aliyu, ta banko kofar dakinsa, babu sallama ta tsaya masa tsegege aka, yana kwance akan gado yana kallonta. Tace Aliyu nagaji da wannan rashin adalci naka, ni bazan iya zama ba, kana nuna min iyakacina, ka dubi uban kaya daka jibgawa zainab da jaririyarta, ni wallahi bazan yarda ba saide kome zai faru ya faru, ya daga mata hannu ki saurara kada kiyi min hayaniya aka, fita ki bani waje. Ta fito ta kwashi akwatunan daya bata ita da Ahmad tasa aboot din motar da ya bata da akwatunan ta tafi gidansu. Mansura tana isa gida, tasa kannanta suka shigo mata da akwatunan, iyayenta suna falo da saratu da hauwa, suka tareta da lafiya? Tace wallahi Alh na gaji da rashin adalcin mutumin nan, ka dubi 'yan kayan da ya bamu nida Ahmad, amma ita ya hada mata akwatuna shidda ita da 'yarta kuma ya bata irin motar da ya canja min. Saratu ta bude kayan tana gani, super da holland da les da material da shadda ganila ga takalma jaka da sarkar gwal. Akwatin Ahmad ma kananan kaya masu tsada, sai shadda da boyel masu tsada sun sha aiki, kala goma sha daya, ga takalma da huluna masu kyau da tsada, harda glas mai ruwan gwal suka gama gani, saratu ta rufe kayan, hajiya tace mun gani Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya kara buda masa. Mansura tace, hajiya nifa na taho gida, ku kirashi kuyi masa fada bazan iya zama da wannan rashin adalcin nasa ba.... Kafin ta rufe bakinta Alh ya wanke mata fuska da mari, hajiya ta rufeta da duka. Dabbar yarinya mara hankali, dazunan ya kawomin makullin mota sabuwa kar. Ya aikowa da mahaifiyarki katon injin kankara don ta rinka sana'a dashi shine kike kokarin tozarta kanki, da yake bakisan abun arziki ba, to du ranar da kika sake zuwa gidan nan kika kawomin karar mijinki, saina karyaki, bare kuma kiyo yaji, wannan kasheki zanyi murus har lahira. Fita ki bani waje, ya biyota tayi waje da sauri, kananta suka mayar mata da akwatunan cikin mota, taja ta koma gida tana hawaye, fuskarta da yatsun babanta daya mareta. Tazo ta wuce ta babban falo tana kuka Aliyu yana zaune yana kallo, ko kallonta baiyi ba, ta wuce bangarenta. Ranar suna aka sawa jaririyar sunan maman zainab, suna kiranta da ihsan. Taron suna yayi kyau angama lafiya aka watse. Kyaututuka da zainab ta samu baza su lissafuba, daga kawayenta, abokan Aliyu 'yan uwa da abokan arziki, kayan kamar a bude sito dashi. Yaya ni'ima tace, kinsan kuwa yau shekarar ku uku cif da aure da yaya. Shida yayi alkawari saikin shekara uku sannan zai kusanceki, sai gashi shekara uku tazo da 'yar diyarku ko? Zainab tace ke kika jiyo, ni ba ruwana. Suka sa mata dariya. *** ***** kwanci tashi rayuwa ta mika, zainab tuni sunyi arba'in, harta koma abuja, taci gaba da karatunta. 'yar diyarta saida daddynta ya nema mata tsari sosai, saboda kyan Ihsan du wanda ya bude baki, sai yace hu! Wannan yarinyar da kyau take. Ihsan watanta shidda kenan tayi 'yar kubibi abun sha'awa da 'yan hakoranta biyu abakinta, tayi sabo da Aliyu du sanda ya dawo gida, yana tare da ita, don haka data ganshi tana bayan talatu zata rinka zillo. Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta... via # Abdul azeez muhammad Ina 'yan gidan nan kowa ya fito ya bani Happy sallah nah [8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**8 Ya karbeta ya rungumeta, yana murnar ganinta, yasata a gaban mota, yaita yawo da ita. Tanada wata takwas ta fara takawa, dadi ya ishi Aliyu, komai ya gani sai ya siyo wa ihsan. Ihsan tana sanye da dan jeans din dogon wando da 'yar riga yalo ta dan kama mata jiki, anyi mata indomie akanta, ansa mata kananan ribon yalo. Da takalminta yarinyar tana ta kamshi, tana tura 'yar motarta a falon, tana binta. Aliyu yayi sallama ta taho da gudu tana cewa Abba! Har tana kokarin faduwa. Ya sureta ya rungumeta ta Abba. Zainab ta fito cikin kayataccen kwalliyarta ta kananan kaya, ta sake komawa yarinya sharaf, saboda hutu ya kara samuwa. Ta taryeshi ta rungumesu gaba dayansu yana me jin farin ciki, da nishadi a zuciyarsa. Ta karbi jakansa ya zauna kan kujera yana rungume da ihsan, zeey ta cire masa takalman kafarsa da safa ta cire masa kakin jikinsa, ta barshi daga shi sai ves da gajeren wando. Ihsan tanata tsallenta a jikinshi. Zainab ta kai masa kayansa dakinsa. Ta dawo ta dauke ihsan, tare da cewa, daga Abba yaje yayi wanka. Ya shirya ya fito cikin kananan kaya suka nufi tebir, sai da suka gama cin abinci suka nutsu, suna kan kafet suna wasansu, Aliyu ya daure ido da farin kyalle yana bin ihsan da rarrafe, tana gudu tana dariya. Zainab ta taboshi yayi saurin juyawa baya, yana lalume zai kamata, ta zille dayan gefen tanayi masa dariya. Ta rankwafo gabansa taja masa hanci, tayi saurin zillewa, yakai hannunsa bai kamata ba, zata gudu yasa mata kafa ta fado kansa, yayi saurin shafa kanta yauwa na kamaki. Tace "a wlh ban yarda ba wayo kamin. Ihsan ta fado kansu tana gwarancinta, gaba daya suka sa dariya. Ya bude idonsa duk suka zube kan kafet din suna maida numfashi. Tace Abban Ihsan, yace na'am maman Ihsan. Tace don Allah tunda na gama diploma, kafin na fara karatun digiri, muje gida kano mu huta, yaya rabona da gidan tun bayan arba'in din Ihsan. Wallahi inason zuwa gida. Yace haba zainab du fa sati ina zuwa, kuma ina gaya miki sakon gaisuwar da suke yi miki. Ga waya kullum kunayi kuna hira dasu kuna jin dadi, ko yaushe fa kuna tare dasu a waya. Ta langabe masa tanayi masa magiya, Abban Ihsan don Allah kayi hakuri ka amince mana muje, wallahi suna son ganin Ihsan, sunce hotunan ta baya gamsar dasu, yaya kada fa Ihsan ta tashi bata san dangita ba. Yace "I gaskiya hakane da wannan ku shirya wannan satin zamuje tare. Ta rungumeshi tana mai cike da murna da farin ciki, nagode yaya Allah ya saka da alkhairi, ubangiji ya kara maka budi da son zumunci. Amin zeeyta. Ranar da suka sauka 'yan uwa sunyi farin ciki sosai da ganinsu, kowa sai daukan Ihsan yake yi. Ahmad ya rungumesu, yana cewa barka da zuwa aunty mamina, nagode da kika kawomin 'yar uwata. Ta shafa kansa Amadina naji dadi dana sameka lafiya ka girma ka kara wayo da hankali. Gidan nasu ya kasance kullum a cike saboda 'yan sanda zuwa. Ranar da suka yi sati biyu da zuwa sukayi wanka sukayi kwalliya ita da Ihsan, ta shiga motarta ita da Ihsan da kanta tajasu zuwa gidansu. Ihsan tana da shekara biyu kenan, amma wayonta da surutunta saika zata tayi shekara hudu. Ni'ima ce ta sake haihuwa, suna gidan sunan Aliyu yayo wa zainab waya, Ihsan tanata rigima ta hanata amsa wayar, yanata yi mata fada wai ta shiga cikin jama'a da ita zafi ya dameta. Y kashe wayar mintuna kadan ya isa gidan ni'ima, ya yowa zainab waya yace ta fito ta kawo masa 'yarsa. Ihsan tana ganinsa ta rungumeshi, tana murna, Abba ka daina tafiya kana barina in ban ganka ba kuka zanta yi. To na daina Ihsan dita, dake zan rinka zuwa ofis ko? Ta daga kai. Yauwa bebyna. Yai tafiyarsa da Ihsan din sai mangariba ya koma gida, Ihsan tana rungume a jikinsa tayi bacci. Mansura tayi sallama, ta shigo ya amsa mata sallamar yace ina Zainab? Tace, kajika da wani zance, motata daban tata daban zance taho mu tafi ne, tare dai muka fito daga gidan ni'ima, ban san yanda akayi ba nura tsohon saurayinta yasan ana suna, sai ganinsa mukayi a zaune akan motarsa yana ganin zainab ya kama washe baki, ta tsaya suna gaisawa nikuma nayi tahowata. Yayi wata irin zabura ya mike yana huci, dai-dai lokacin da zainab din tayi sallama ta shigo, a fusace yace mata daga ina kike? Cikin sanyita tace yaya wace irin tambayace wannan? Kafin ta karasa maganan ya dauketa da mari, tuni ta dafe kuncin nata, ta wani durkushe a kasa saboda gigitaccen zafin marin. Ya nunata da yatsa uban waye ya baki damar tsayawa da nura, har ku gaisa dashi? Kanta yana sunkuye, tana jin haka da sauri ta dago kanta ta kalli mansura, tace aunty kiji tsoron Allah, wai me na tare miki a doron kasa ne kike so kiga kinsani bala'i? Ya kamata ku sani wannan duniyar ba matabbata bace. Aunty idan kin kashe aurena da yaya me kikayi tunda dai kinsan dole a gabanku zanci gaba da zama, har lokacin da zangama idda na samu wani mijn da zan aura, kuma duk matsalar data faru dani dole ku zan kwaso na gayawa. Aunty duk matan arziki bazata bari mijinta yayi fushi da ita ba, ni gashi kinsa ran nawa mijin ya baci dani, yana fushi dani alhalin bada hakkina ba. Via #Justice_Hamzat [8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**9 kiyi hakuri aunty, gaba kike dani, kuma ke auntyna ce, bazan taba bari wani batanci ya shiga tsakaninmu ba, amma dan Allah ki rinka jan mutuncinki da girmanki. Tace, yaya kayi hakuri, amma ban aikata abunda kake zargina dashi ba, rabona da nura tun ranar da ka koreshi, ko labarinsa ban sake jiba bare na ganshi. Ta mike tsaye zata nufi dakinta jiri ya kwasheta, tayi baya zata fadi, Aliyu yayi saurin tareta ta fado hannunsa, ta shide, numfashinta ya dauke a gigice sukayi asibiti, saida likitoci sukayi ta gwaje-gwajensu, suka jona mata karin ruwa ta farfado, sai dai takoma bacci. Mansura kukan nadama takeyi, tana bawa Aliyu hakuri, shi bakin cikin marin da yayiwa zainab yafi komai daga masa hankali. Likita ya shigo yace, yallabai saika kula da madam sosai, ka daina bata mata rai, don tana da karamin ciki na wata biyu a jikinta. Wani irin farin ciki ne ya lullube zuciyar Aliyu, ya rinka dariya yana nuna farin ciki da godiya ga Allah. Mansura ta rinka mamakin irin farin cikin da yake yi, wai yana son haihuwa haka amma bai hanata planin din data keyi ba, du da dai bashi yasa ta tayi ba. Amma ai wataran yana ji tayi waya asibiti, tace zato zo allura, bai ce mata komai ba, to me yake nufi da itane, ko bai dauketa wata tsiya ba? Tayi waje da saurinta, ta zaro wayarta ta bugawa yayarta saratu tana dauka tace, hello kinji yarinyar nan ciki ne da ita, kinga murnar da Aliyu yake yi kamar wanda akayiwa bushara da gidan Aljanna, yanzu dama mutumin nan yana son haihuwa ya barni inata faman planin. Au dama planin Aliyu ya saki kiyi shiyasa baki sake haihuwa ba tsawon lokaci? Tace wlh yaya saratu gaskiya ba Aliyu ne ya saniba, don na taba gaya masa zanyi tsarin iyali, yace ba ruwansa, kuma bada yawunsa ba, idan kuma nayi bai yafe ba. Ni kuma naga shi dan gayu, ga son ya huta, sai nake ga kamar tara 'ya'ya zai iya zame masa matsala, yaga baya samun yanda yake so watarana yayo min kishiya, sai duk da haka ban tsira ba. Amma tunda naji labarin zainab tana da cikin Ihsan, na daina planin din, amma gashi harta haihu ta kuma samun wani cikin, ni kuma ba labari. Saratu ta daka mata tsawa tare da cewa, ke kika yiwa kanki, kin cuci kanki abanza a wofi. Ga dukiya nan yana samu kamar kasa, ita kuma taita tara masa 'ya'ya kya zama 'yar kallo ai, yanzu ma ya fara baki kujerar makka biyar, kin kawowa Alh, to gaba muka san me zaiyi mana, bare ace kin cika gidan da 'ya'ya, ni bazan iya sauraran takaicinki ba sai anjima. Ta kashe wayar. Mansura ta dawo dakin a sanyaye da ita. Zainab ta farka Aliyu yace sannu zeeyta. Ta dago kanta cikin sanyita tace yaya kayi hakuri dan Allah ka yafemin, wallahi ba wani namiji dana gaisa dashi. Kayi hakuri yaya zuciyarka ta huce. Ya shafa kanta zainab ki daina tuna wannan magana dakin san yanda raina ya rinka suya da tukukin bakin ciki, ina tuna ni na mareki da wannan hannun nawa sai nake tunanin irin hukuncin da zanyiwa hannun ko zuciyata ta huce. Zainab nayi abunda Allah ya hana, yanke hukunci cikin fushi. Zainab ba laifina bane, shirin mansura ne kawai don ta bataki awajena. Kiyi hakuri zeeyta. Tayi saurin sa hannu ta toshe masa baki tana murmushi, don Allah yaya ka daina bani hakuri, wlh na yafe maka, ka gayawa aunty ma na yafe mata. Babban jin dadi na da zuciyarka ta huce, bakayi fushi dani ba. Zainab jiyan ma bacin raine da zafin kishinki, wai har na mareki. Tace don Allah yaya kadaina tuna zancen marin nan, kaifa yayana ne, kayi min marin ne a matsayinka na wana, ba miji ba ko yayana? Mansura tana tsaye a gefe daya tayi shiru tana jinsu. Aliyu kamar baisan tana wajenba, bare zainab da bata san tana nan ba. Zainab tace, dan Allah yaya kayi hakuri kada kayiwa aunty wani abu, kasan dan adam ajizine, kowa zai iya kuskure kayi hakuri yaya ka yafe mata. Ya daga kai shikenan naji na yafe mata, mansura kawai saita juya ta fita daga dakin. Likita ya rubuta musu maganguna na karin jini da lafiyar dan tayin cikinta. A daren suka dawo gida wani irin tattalin so da sabuwar kulawa da yakeyi, kamar zai mayar da ita ciki ita kuma sai sangarta take zuba mai da shagwaba ga cikin nata mai tsurfa ne du daurewar data keyi, amma abu kankani sai ya daga mata hankali yasata amai. Hankalin Aliyu ya kasa nemansa akeyi awajen aikinsa, ga zeey dinshi bata cika lafiya ba. Amma dole ya dauketa su tafi Abujan, ta karasa warware wa acan. Yace wa zainab ki hada abunda zaki tafi dashi don jibi litinin zamu tafi. Yana fita yayi bangaren mansura, yace mata kiyi lis din du abunda zaku bukata, don jibi zamu koma abuja. Tace, kaida wa? Yace dawa muke tafiya? Tace, kana nufin wai da zainab din zaka kuma tafiya ne? Yace ya wuce wai. Ta mike tsaye tana tafa hannu, to wlh abunda bazai taba yuwuwa ba kenan, na gaji da yi muku gadin gida wlh, wlh bazan zauna ba, na gaji da rashin adalcinka, ka rinka kwasar wadanda kake so kuna tafiya. Ya daga mata hannu, tare da cewa ya isheni, kada ki kawomin maganar banza, haka nayi niyya baki isa ki canjani ba. Ya fice ya doka mata kofar, ta tabe baki dan rainin hankali zaka gane kurenka. Via #Justice_Hamzat [8:07AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**10 Dan rainin hankali zaka gane kurenka, tauraruwar taka dole ka barta, ko kuma ka tafi damu gaba daya, don wlh bazan zauna ba, sai na bika. A bangarenta ya kwana da safe ya sake yi mata maganar ta bada lis din abunda zasu bukata. Tace masa saidai ka nemi lis a wajen zainab, don ni kaga akwatuna na can nagama shirin binka. Ya daka mata tsawa ke baki isa ki raina min hankali ba. Ga cek nan ki rubuta abunda kike bukata a karbo miki a banki, idan kinga zaki zauna ki zauna, idan kinga bazaki zauna ba to ki tafi gidanku. Ta dafe kirji ni zaka yiwa wannan wulakancin Aliyu? Ko kallonta baiyi ba ya fice ya bata waje, tana jin fitarsa itama ta shirya ta fice, gidansu Aliyu. Da suka gaisa da umma, sai tayi bangaren ummi ta gaisheta, sannan ta shiga bangaren su zainab, ta gaisar da maman sannan tace mata, don Allah daddyn zainab yana nan? Mama tace "I yana ciki. Tace don Allah mama inason magana dashi. Tace, to bari nayo masa magana. Ta mike shiga bangarensa ta gaya masa. Yace mansuran ta shigo, mansura ta rissuna ta gaisheshi, saita fashe da kuka daddy yace, lafiya menene, me suka yi miki, wani abu ne ya faru? Tace daddy wai dan Allah Aliyu yace zasu koma abuja da zainab, sai nace ya rinka kwatanta adalci a tsakaninmu, mu ma yaje damu abujan nan, shine ya hauni da fada wai bazamuje ba, anan yaga damar ajiyemu, in zan zauna na zauna, in bazan zauna ba na fice na tafi gidanmu. Dady yace subhanallahi, me yayi zafi haka? To kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da shirinki, zai tafi daku kinji. Tace to dady nagode Allah ya saka da Alheri. Yace bakomai tashi ki koma gida. Ta fito tayi musu sallama ta koma gida. Dady yayi waya ya kira Aliyu, ya zo da saurinsa, yace dady gani. Bayan sun gaisa, yace haba Aliyu kaifa yaro ne, amma me halin manyan mutane. Haba Aliyu kada rudin duniya ya debeka, ka kaucewa fadin Allah, kazo kana fadawa halaka. Yata masa nasiha daga karshe yace to yanzu tunda bata amince ba, to an shiga hakkinta, don haka ka tafi da mansura abuja ka bar zainab anan kano. Aliyu ransa ya baci wato mansura kararsa ta kawo kuma tasan inda bai isa yayi musu ba. Yace to dady na tafi da itan. Yace yauwa ko kaifa dana, nagode. Aliyu ya taho gida ransa a bace saboda abunda mansura tayi masa. Magoronsa ya rinka daci na tukukin bacin rai, sai yaji zazzabi yana neman rufeshi. Ya shiga falon zainab ya zauna ya zuba tagumi zainab ta fito daga kicin ta ganshi, ta karaso gabansa da sauri tace lafiya yayana, meya faru, meya sameka kayi tagumi? Tasa hannunta ta cire mishi tagumin, ya akayi yayana menene? Ya danyi tsaki yace bana jin dadin jikina, ina jin dan zazzabi ajikin nawa. Oh! Sorry yayana sannu, ta dafashi tana lallaminsa kamar yaro. A hankali ta zame masa kayan jikinsa, daga shi sai gajeren wando. Ta shiga kicin ta kawo mishi ruwa mai sanyi, da lemu ta zuba a kofi tasa masa a bakinsa kadan ya iya sha saboda bacin rai. Ta debo ruwa a tasa ta dauko karamin tawul tazo ta rinka dangwalar ruwan tana daddana masa ajikinsa, yana lumshe ido a hankali ya fara jin yana watsatsakewa, saida taji jikinsa ya huce daga dumin, sannan ta bashi magani yasha. Ya kishingida akan kujera, ta rinka yi masa tausa, sannu a hankali yana lumshe ido tare da cewar wash. Bacci mai dadi ya ringa fisgarsa, ya kwantar da zainab ajikinsa ya rungumeta, bacci ya daukesu a haka. 50 min suka kwashe suna bacci, a haka zainab ce ta fara farkawa, ta runkura a hankali zata zame tabar jikinsa, ya kara kankameta, ya bude ido ya sumbaci lebenta, dariya, yayana ka farka. Tunda zaki bar jikina ai dole na farka. Yaya lokacin sallah yayi hudu saura. Ya mike da sauri, ta shiga toilet ta hada masa ruwan wanka, ya shiga yayi wankansa a nitse ya fito zuciyarsa wasai, ya manta da wani bacin ran mansura, yayi saurin sa kaya ya fita masallaci don sallar la'asar. Lokacin daya dawo daga masallaci ya tar zainab ta canja masa shiga ta kananan kaya, irin shigar da yake so. Ta tare shi tana murmushi, ta riko hannunsa suka wuce tebir don cin abinci. Ta rinka tattalinsa, tana bashi abinci abaki, sai kace yaron goye. Suna ci cikin nishadi da faranta ran juna, sai santi yake zuba mata, yana sata kyalkyala dariya. Tasa shi cikin farin ciki da walwala kwata2 ya manta da bacin rai da mansura ta dasa masa. Ya dauki waya bari na bugawa ni'ima ta kawo min Ihsan dita, bana jin dadi idan bana jin karadin bebyna. Zainab ta rike wayar don Allah yaya ka bari, tace saida daddare idan zasu zo yi mana sallama zasu taho tare. Yayi wani dif saboda yanda zuciyarsa ta buga da ya tuno fa bada zeey dinshi zai tafi ba. Gashi du ta hada kayansu da abunda tasan zatayi amfani dasu. Ta kula da halin da yake ciki, tace wayyo yaya don Allah kayi hakuri idan ranka ne ya baci bari na tura direba ya dauko maka ihsan din kaji yayana. Ta mike ya riko hannunta dawo ki zauna, ba fushi nayi ba, dani da ni'ima ai duk daya ne. Tace to meye yayana nafa duk ka canja? Yace kiyi hakuri zainab bada ke zan tafi abuja ba. Ta dafe kirji yaya me nayi maka, saboda me bazaka tafi dani ba? Ya kwanto da ita jikinsa. Via #Justice_Hamzat [8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**11 Ya kwanto da ita jikinsa yana rarrashinta, kiyi hakuri zainab ba a son raina ba, mansura ce ta kai karata wajen dady yace na tafi da ita. Tace shikenan yaya, saikun dawo Allah ya kiyaye hanya. Ta mike tayi cikin dakinta ta kwanta tana hawaye. Ya taso ya biyota, ya dagota "zeeyta menene fushi kika yi? Kiyi hakuri nasan dole ranki ya baci, amma ni nafiki cutuwa da rashinki kusa dani. Zainab kici gaba da shirinki, saimu tafi gaba daya, kinji. Ta tashi tace haba yaya ya zanki jin maganar mahaifana? Dady abunda ya fada gaskiya ne, hakan shine adalci yaya kuje Allah ya kaiku lafiya, zan tayi muku addu'a daga nan. Ta tashi ta shiga toilet shiru-shiru yana jiranta bata fito ba, ya dafe kansa tabbas yasan zeey dinshi fushi tayi, ya tashi ya fita daga dakin. Lokacin ni'ima da sadiya suka zo musu sallama, sannan Aliyu baya nan, zainab bata gaya musu cewar ba tare da ita za a tafi ba. Sai goman dare suka tafi, sunyi mamakin rashin dawowan yayan nasu gida da wuri. Sha daya na dare zainab ta kasa bacci, tana tunanin ina Aliyu ya shiga ne? Tayo alwala ta shimfida dadduma tana sallar nafila, tana addu'a Allah ya bata hakurin jure rashin mijinta kusa da ita. Ya kuma hade kansu da mijinta da kuma abokiyar zamanta, ya kuma kare su daga sharrin mahassada da makiya. Ihsan ta farka da kukanta tana kiran dadynta, bata ganshi yau ba ta taso ta kwanta abayan zainab tana kuka, tana cewa aunty mami ina Abba na, ki kaini wajen Abba kinji aunty mami. Zainab tana kan addu'a tana hawaye tana jin ihsan a kwance a bayanta tana kuka. Ya dade da shigowa yana tsaye yana kallonsu, tsananin tausayinsu ya gallabi zuciyarsa. A hankali yae ya durkusa a gaban ihsan ya shafa kanta, ta dago ta ganshi, ta fada jikinsa tana dariya Abba na ina ka tafi ka bani? Ya rungumeta sosai yarinya ta rinka ajiyar zuciya ya rinka shafa kanta. Tayi lamo a jikinsa har tayi bacci ya shimfideta ya dawo wajen zainab. Yace yanzu zainab haka zakiyi min kiki sakin ranki ku rinka shiga kunci keda ihsan. Keda zaki rarrasheta amma ke kina kuka ita tanayi, a haka kike so na tafi na barku, taya zuciyata zata samu nutsuwa, bayan nasan bakwa cikin kwanciyar hankali. Kayi hakuri yaya wlh ni ba haka bne, ni abunda ya daga min hankali naga har sha dayan dare baka dawo bane, yaya ba dole na damu ba? Yaya ina kaje ka kai sha daya baka dawo ba? Yayi murmushi yace ina zanje kuwa, ai kinsan bazan iya fita wani waje a wannan lokacin ba, ina falon saukar baki muna lissafi da su sadik yanzu nan suka tafi. Tayi murmushi ya kamo hannunta zo muje na kwanta kada na makara. Da safe ya fito falo shida zainab yana dauke da ihsan, sunci kwalliya kamar masu shirin zuwa fati, sunata murmushi da fara'a ke ba kyace da wani kunci a ransu ba mansura suka shigo falon ita da Ahmada sunci kwalliya tana taunar cingam, Ahmad yayo wajen zainab yana cewa aunty mami mu tafi gaba daya. Ta shafa kansa kada ka damu yarona idan mun gama shirinmu zamu biyoku, inkaje ka kula da karatunka, kaga za a canja maka makaranta saika kula sosai. Yace to aunty mami naji. Mansura ta kallesu ta tabe baki, takaicinsu da bakin cikinsu ya isheta, wato du yanda taso ta kuntatawa zainab donta ga bacin ranta, yarinyar taki nuna damuwarta. Har mota ta rakosu, Aliyu ya mikowa zainab ihsan ta karbeta, ya shiga motar suna daga musu hannu, direba ya fara jan motar tana tafiya, Ihsan ta kwala wata gigitaccen kuka tana zamewa daga jikin zainab. Motar tana kokarin fita daga get Aliyu yacewa direba ya tsaya, ya fito da sauri ya karbi ihsan ya rungumeta, ta rinka cewa Abba jani. Yaya to ku tafi da talatu, ta taho da ita. To shikenan turo talatun. So kuyi hkr wllh banda lpia ne [8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**12 To shikenn turo talatun. Ta shige gida da sauri talatu ta fito ta shige gaban mota kusa da direba, ihsan na kwance jikin babanta, yana lallashinta Ahmad yana tsunkuninta suna dariya. Mansura takaici ya cikata, wai me zainab take yiwa Aliyu ne da yake musu irin wannan kauna? Kafin su karasa airprt Ihsan har tayi bacci. Suna fitowa daga mota talatu ta karbeta, ta koma motar direba yasu suka tafi. Mansura kanta ya kwance da ganin gidansu na abuja, du da dai na kano da suke ciki yafi shi girma da kyau, amma tsarin wannan din ya burgeta sosai, kamar gidan turawa. Tuni Aliyu ya fice cikin sauri ya nufi ofis. Mansura da Ahmad sun zagaye ko ina, bangare daya ne a kulle, ta tabbatar wajen zainab ne, tunda bai bude musu ba. Sai dare Aliyu ya dawo abun haushi ga yunwa ga wahala, amma yana zuwa ya tarar da mansura da Ahmad du sunyi yaushi, wai yunwa suke ji basu ci komai ba. Ya hauta da fada dan me ga kayan abinci nan bata girka ba? Tace ai babu gas kuma ta masa waya taji ta a rufe. Yace baki bude jakunan da akwatina da muka zo dasu kin jere kayan ba? Tace ai bata yi komaiba, yayi tsaki matsalarki kenan har yau baki san yanda zaki kula dani ba. Ya tashi da kanshi ya bude kayan ya fito da soye-soyen da zeey ta musu, dambun nama, kec, meat fy, samosa, cin-cin da wainar shinkafa, da sinasir da fukasau da soyayyen miya. Kawai sai mansura tayi turus, lallai zainab tayi nisa wajen siye zuciyar Aliyu, ita yaushe tayi tunanin haka ma bare tayi, abu daya tasan tana da yaji. Aliyu yasa Ahmad ya shiga kicin ya dauko filet da cokala, ya bawa Ahmad shima ya diba. Yaja gefe ya fara ci, yace wa mansura ki debi abunda zaki iya ci, ki zuba ragowar a firij. Ki debo mana ruwa da lemu tunda komai sai ance kiyi. Ta zumbura baki, ta tashi tayi yanda yace, ta zuba nata abincin ta zauna tana ci. **** ***** **** zainab ta shiga damuwa sosai, na rashin tafiyarta, tana son zaman kano saboda iyayensu da 'yan uwansu. Amma gaskiya tafi son zaman abuja, saboda tafi kusa da mijinta, tasan halinshi tasan damuwarsa. Tasan yayanta mai son a kula dashine wajen cikinsa da biya masa bukatarsa to tasan auntynta tun tana ita kadai ta riga tayi sakaci da hakan. Ta kalli Ihsan data gama rigimar neman abbanta tayi bacci. Ta mike ta shiga toilet ta dauro alwala tazo ta kama nafila tana musu addu'ar neman zaman lafiya a tsakaninsu da cikawa da imani. Tana shafa taji nutsuwa ta saukar mata, taji zuciyarta wasai, babu kunci ko damuwa. Tahau gadonta ta kwanta, wayarta kamar jira take tahau burari, ta dauka da murmushinta, tace "hello gudan raina, ya kake? Ina auntyna da dana? Yayi wata irin sanyanyar ajiyar zuciya, yace rayuwata ina Ihsan dina tayi bacci kota nata rigimar nemana? Um-um ta hakura tayi bacci. To saka min naji munsharinta don na tabbatar da lafiyanta. Tasa a wayar a hancin Ihsan, yaji numfashinta yana sauka a hankalo, tasa a kunanta kaji ko? Um Alhdllh naji bebyna kalau take. To ya dan bebyna baya tare da matsala ko? Kinsan tunda nayo miki waya mun sauka, to tun daga lokacin ban samu kaina ba sai bay isha inata aiki. Cikin tausayawa tace, wayyo yayana, ka wahala, sannu yayana, koda yake ai ka huce gajiyar yanzu dan nasa aunty ta gasa ma jikinka da ruwan zafi, kuma tayi maka tausa, nasan gajiya ta gudu sai wacce zaka sake dauka yanzu ko yaya? Yace, don kinga bana kusa kika samu bakin gaya min haka ko? To bashi du ranar dana dawo na ware gajiyar akanki. Tasa dariya tace yaya kayi hakuri bazan kuma ba kaji? Yace nasan ranki ya baci sosai rashin tahowarmu tare. Amma don ki kwantar min da hankali kika dake, kika nuna min bakomai kina goyon bayan nayi adalci a tsakaninku, don kina so ranar lahira na tashi cikin maza salihai, masu adalci a tsakanin matayensu, baki nuna son zuciya ba. Tace yaya dare fa yayi, kada mu shiga hakkin auntyna, yaya saida safe. To Allah ya tashemu zeeyta. Kwana hudu ranar jumma'a da azahar ya baro ofis ya taho yayi shiri, ya taho kano. Zainab kuwa tana cike da doki anata yi masa girke-girke da soye2 da lemuka. Taci kwalliyarta ita da Ihsan. Ihsan tana cikin 'yar shimin riga ruwan hoda me adon les, a kirjin da hannun rigar sai dan jeans ga dan takalminta me madauri kasansa na glass, yarinyar tayi kyau matuka. Tanata tsalle2 ta acikin motarta a harabar gidan, motar Aliyu ta shigo yana ganin Ihsan yaji zuciyarsa ta cika da farin ciki da annashuwa direban bai gama tsayawaba da motar ya bude ya fito da saurinsa Ihsan tana ganinsa ta kama dariya, tana dago masa hannu da cewar Abbana! Abbana ya dauketa ya kankame yana murna, ya jiyo da daddan kamshi sahibar tasa ya daga kai yana kallonta tana masa murmushi, ya dago mata hannu ta taho ta shige jikinsa, suna dariya yayi mata kyakyawar runguma yasa hannunsa a mararta, ya rada mata a kunanta ya bebyna? Ta rangwadar da kai lafiyarsa lau sai maraicin Abbansa da yayi. Ya rada mata ai gani nazo zamu kasance dashi na tsawon awa biyar. Ta kwace jikinta tana dariya, "a nifa yaya ba haka nake nufi ba. Yace ai kin manta da bashina da kika ci ta waya? Tasa dariya niba ruwana. [8:09AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**13 Tasa dariya nidai ba ruwan ga 'yarka nan me shegen wayo tana jinka. Ya sumbaceta yace Ihsan din Abba yarinyar tayi dariyarta tace Abban Ihsan, gaba daya suka sa dariya suka fada cikin gida yana rungume da iyalansa. Suka zube a falo, ina Amadina. Yana can ya fara zuwa makaranta yau. Ta rinka cire zare masa kayn jikinsa ta barshi daga shi sai gjrn wando taja hannunshi zuwa toile inda ta hada masa ruwan wanka. Yana fitowa ta tareshi da tawul ta goge masa ruwan jikinsa, ta shiryashi kamar karamin yaro, ta rikoshi zuwa tebir. Yana cin abincin yana zuba mata santi, zainab kici gaba da tallafin rayuwata, kina min tattalin so, kada ki barni naje kasa don kece farin cikin rayuwata. Ta taso da sauri ta rungumeshi, ta hada bakinta da nasa, tana yi masa hot kiss da ya rikitashi, yake kokarin mantar dashi a wacce jiha yake. Ta cika shi tasa bakinta daidai kunnensa, i luv u yayana, i care 4 u, life iz gud. Ta rikitashi da kalamanta inda ita kuma ya rikitata da soyayyarsa, tuni ya manta da batun cewar abinci fa yake ci a falo. Sai da ya samu nutsuwa shi kadai ya rinka yiwa kansa dariya, zainab kuma abun ya bata kunya. Ta fada dakinta ta shiga toilet, shima dakinsa ya shiga ya fada toilet. *** *** ***** Rayuwa mai dadi zainab tana zamanta cikin kwanciyar hankali, bata da damuwar komai tana cikin danginta da 'yan uwanta, kowa yaso ganinta zai zo gidanta su wuni suna hira, amma ita bata fita ko ina, sai dai in fitar ce ta kama dole. Sai dai in Aliyu yazo du inda take son zuwa zasu je tare. Mansura kuma tana abuja, amma du abun duniya ya isheta, saboda bata saba da zaman kadaici ba. Ahmad in ya fice tun safe ya tafi makaranta sai yamma zai dawo. Haka Aliyu tun safe zai fice ofis sai dare zai dawo da ya gama abunda yake yi bacci zaiyi don gudun kada ya makara. Bata da lokaci na samun hira dashi ko magana dashi, gashi ba wanda ta sani, kuma baya barinta fita ko ina. Kokari me aiki tazo tayi mata gama abunda take yi ta fice. Abun duniya ya isheta, bata da wani aikin yi sai kallo, sai dai idan ta gaji ta kwanta ta dauki waya ta bugawa iyayenta da 'yan uwanta. Da abokanan arziki suyi ta hira dasu. Take gayawa yayarta saratu matsalarta dake damunta, kawai inba babu dama kice ya dawo dake gida, ba gwanda zaman ki acikin dangi da 'yan uwa ba. Ko wani abune ma ai inkin ga danginki kyaji sauki. Tce to bari inya dawo daga ofis nayi masa maganar zuwana tunda gobe jumma'a zai zo to sai anjima kya bugo naji yanda kuka yi dashi sukayi sallama kowacce ta ajiye. Karfe takwas na dare Aliyu ya shigo saida ya kammala du abunda zaiyi ya zauna. Tace Aliyu. Yace um hum, inajinki. Tace gobe inaso in bika naje gida. Yayi mata wani irin kallo, yace zancen ne baki gaji dayi ba. Na gaya miki keda gida ba yanzu ba. Tasa kuka, wannan wane irin al'amarine, kai baka da lokacin da zaka zauna a gida Ahmad sai yamm yake dawowa, ana biki ana suna da mutuwa amma bazaka kaini naga gida ba? Yace itama wacce kike kishi da ita tana nan din kika bambareta ke kika dawo, itama haka take zaune. Kuma baki ga ina yawan kaita gida ba, saita shekara, don haka wlh kema saikin shekara sannan zakije gida. Ta dora masa hannu aka ta kurma masa ihu wayyo na shiga uku, baya son jin kukan dan haka ya tashi daga falon ya koma daki ya kwanta. Ta zauna a falo taci kuka saida ta gaji dan kanta tayi shiru. Ta tashi ta koma dakin ta rabe kusa dashi ta kwanta, tana ajiyar zuciya ya jawota jikinsa, baki daina kukan nan kina so kanki yazo yana ciwo ko? Tace ko meye ai kaika jawo min, nagane bansan abunda yasa baka kaunta ba, iya bakin kokari dai inayi maka don na kyautata maka, kuma kai baka so kasani farin ciki, kafi so kaita ganin raina a bace. Yace mansura inkika fadi haka bakimi adalci ba, tun kafi na auri zainab naso na mayar dake kaduna wajen aikina, kika nuna min baki da ra'ayi, ashe don na dawo da zainab wajen da nake aiki har kyace nayi miki rashin adalci? Kika je kika hadani da kawuna, wanda shine mahaifin yarinyar nan, ya rinka min fada akan bana miki adalci. Yasa aka bar jikarsa da 'yarsa aka taho daku. Makarantar Ahmad mai tsada yaron nan yana ganewa, kika sa aka rabashi da makarantar, aka canja masa wata, gashi nan saida suka maidashi baya, saboda karatun nasu ba iri daya bane. Sannan yanzu kuma kice min zaki koma kano ki rinka min wasa da makarantar yaro, ni da ke waye mijin? Ko ina tsoronki ne, bare a fara cemin mijinta ce? Don haka keda zuwa gida saikin shekara, anwa suma Ahmad hutun shekara. Se kuje. *** *** *** Ranar wata jumma'a yake ce mata mansura zan kai tsawon sati uku fa a gida ban dawo ba. Ta dafe kirji saboda me? Yace. Lokacin da sakanni din cikin zainab ya nuna ya kusa, kinga dole na zauna kusa da ita, don kada haihuwar tazo mata bakowa tayi masa wani irin kallo saboda in haihuwar tazo kai zaka cire mata ciwon? To wllh bazan dauki wannan rashin adalcin ba. Ko mu tafi tare ko kuwa kayi kwana ukun ka ka dawo. Ya daka mata tsawa, ki rinka sanin irin kalmar da zaki fadamin, ko kuma zan bar matana da tsohon ciki ne kullum ina farga bar halin data.. [8:09AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**14 Kina tunanin zan bar matana ne da tsohon ciki, nazo na zauna anan kullum ina fargabar halin data ke ciki? Kinyi kuskure nasan darajar da, da haihuwa, bazan iya kwatanta miki yanda nake kaunar 'ya'ya ba, ya'ya na daban suke a zuciyata. Ki kiyaye abunda kika san zai tabamin 'ya'yana, koda harara ce wllh saina dauki mummunan mataki akai, ya fice ya barta. *** **** **** Ranar talata, ranar kwanan Aliyu hudu a kano, cikin dare zainab tana rungume a jikin Aliyu yana lallabata. Cikin baccin taji an mintsineta, ta farka firgigit, tana salati Aliyu ya mike a rude, yana tayata salatin, saida suka kai karshe sannan yace mata menene zainab? Yaya ciwo, Abban Ihsan wayyo ka taimakamin, ya rungumeta yana rarrashinta, tare da lailaya mata bayanta, tare da busa iska kadan2 a kunnenta har bacci ya dauketa, ya shimfideta yasa kayansa da sauri ya fito mata da nata kayan. Ya dauki Ihsan ya kaiwa talatu ita. Yana dawowa dakin ya samu zainab ta farka da wani azababben ciwo tana ta murkususu. Yayi saurin rungumeta sannu zeeyta, ya salube mata rigar baccin yasa mata kayanta, ya dauketa zuwa mota. Da kyar suka karasa asibiti, tana ta salati tana murkususu, gashi tana jikinsa ya lafe da hannu daya. Suna isa asibiti likitoci suka karbeta, mintuna goma sha biyar da shiganta dakin kukan beby ya cikawa Aliyu kunne, wani farin ciki da murna suka baibaye shi. Ya daga hannu sama yana tayiwa Allah godiya, saiya ga hakan ma baiyi masa ba, yayi alwala ya shiga masallacin asibitin yayi nafila raka'a biyu ta nuna godiyarsa ga ubangiji. Ya nufi dakin da zainab take, sun gama gyarata ita da jaririn fes dasu, kamar ba ita ta haihu ba. Ya karaso da fara'arsa, sannu zeeyta Allah yayi miki albarka, nagode zainab, ya dauki jaririn fari sol dashi ya rungume dan yana jin wata irin kaunarsa tana ratsa shi. Yace zainab yanzu wannan yaron ma nawa ne? Zainab nagode, kin kawomin Alheri cikin gida, kin sadani da farin ciki mara yankewa zainab 'ya'ya rahama ne, inason 'ya'ya da yawa, zeeyta ki daure kita haifo min kinji? Ya shafi kanta. Tace yaya haihu ta uku, amma sai sambatu kake yi, kamar wanda bai taba yi ba? Yace, zeeyta kin san kuwa yanda nake son haihuwa? Inaso naga na tara 'ya'ya da yawa, naga na hada family kamar mutum guda arba'in ace du nawa ne. Ta bude baki, A yaya arba'in fa kace kana sha'awar kara aure kenan? Yace um-um du ke zaki haifamin da auntynki. Tayi dariya yaya ai sunyi yawa, ba zamu iyaba. Zaku iya tunda kuna tare da gwarzon namiji. Ya dauki waya ya buga gida, karfe uku na dare ya fada musu albishir din haihuwa. Da sha daya na safe aka sallamo su ta taho gida da tawagar 'yan uwanta. Saida suka dawo gida Aliyu yayiwa mansura waya, yake gaya mata zainab ta haihu a daren jiya tace "me kuma ta haifa? Yace kyakyawan , sankacecen dana fari kal dashi me kama dani sak dana miji. Gabanta yayi wata irin mummunan faduwa, dakyar ta iya cewa Allah ya raya. Suna gama wayar, ta bugara yayarta saratu, take gaya mata abunda ya faru, tace kin gani kin cuci kanki da yanzu kina da 'ya'ya hudu ko biyar dole du abunda zata haifa a bayan naki suke, yanzu kuwa fa ba gashi harta fiki ba? Tace na shiga uku yanzu ni ya zanyi, kina gani a abujan ma nayi ziyartar asibiti yafi guda nawa, likita yace mahaifata normal ba abunda ya sameta, a shirye take ko yaushe zan iya daukan ciki. Amma har yanzu shiru babu labari. Kedai ki samu ki lallaba shi ya barki zuwa sunan nan, sai musan abunda za muyi akai, don dole sai an hada da rokon Allah. Ranar kwana biyu da haihuwar tayiwa Aliyu waya tace zasu zo wajen suna. Yace a'a aina gaya miki sai kun shekara zaku zo dan bazan yarda ki cutar min da ki rinka yi masa wasa da karatu ba. Tasa masa kuka, ni gaskiya ba yarda da abinda ka shirya yi wanda ba kaso in gani shiyasa kawai zaka hanani zuwa. Du abunda naga damar yi kin isa ki hanani ne? Karki manta fa da na samu, zan iya kyautar da abunda na mallaka don nuna bajinta, da godiyar Allah bisa kyautar mutum da yayi min. Kema ga key din mota sabuwar kira, ta yayi na baki, ki hada da dayar sun zama biyu, albarkacin wannan haihuwa da akayi min. Tasa kuka banaso bana farin ciki da kyautar da kayi min, ka barni ni kawai nazo naga abunda xa ayi. Ya kashe wayar yayi murmushi kawai ya girgirza kai. An sha shali ranar suna, a ranar kuma aka aiko masa da takardar karin girma, a ranar Aliyu yayiwa 'yan uwansa bajinta kanansa su hamza dasu sadik da faruk yayun zainab, ya basu gidajr guda hudu a jere da aka gama ginasu, yace su nemo matan aure, ya fito da keys na gidaje kanana ya bawa sadiya da ni'ima, yace gashi kuma kwasa 'yan haya. Ya bawa Abba da daddyn zainab mukullayn gidansu da aka gama. Tsawon wata uku basa cikin gidansu suna na gidan zainab data zauna aciki. Haka ya rinka bin 'yan uwa da dangi yana musu alheri, aka radawa jariri sunan Abbansa, suna kiransa Arfat. Aliyu yaje da kansa ya bawa maihaifin mansura key din gida mai kyau. Du abunda akeyi mansura tana samun labari ta waya, hankalinta atashe yake don ita gani takeyi bari da dukiyarsa yake yi kamar zata kare. via #Justice_Hamzat [8:10AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**15 Rayuwa ta mike, jin dadi da kwanciyar hankali sun saukar musu, basu da matsalar komai Arfat yayi bul-bul dashi, fari sol kyakyawa. Watan arfat hudu dai-dai wannan lokacin ne kuma mansura suka cika shekara a Abuja. Ranar litinin da yamma mansura, tayi masa maganar zuwansu gida, yace su fara shiri saura kwana shidda su tafi. Tace kayi mana alfarma mu tafi jibi, kaga saura kwana bakwai bikin yaya saratu, ma fara shirye- shiryen da zamuyi. Ya girgiza kai kwana shidda na fada miki in kinje kwayi shirin da zaku yi. Taso tayi magana ganin ba fuska ta zumbura baki ta bar wajen. Da dare suna cin abinci da Ahmad mansura tana gefe daya tana kallo Ahmad yace, Abba dazu fa da ina waya da Ihsan cikin maganarta tace min arfat bashida lafiya. Cikin sauri Aliyu yace, um-uhum? Har yana kwarewa, yace dazu da mangariba fa munyi waya da zainab, amma bata gaya min ba. Ya dauki wayansa ya kira zainab ringin daya ta dauka, yace zeeyta me yake damun babana? Wallahi yaya zazzabine, inaga dai awon hakorine, don yanata amai ya daka mata tsawa da gaske bashida lafiya kenan, amma baki gaya min ba? Yanzu me kika yi masa ina kika kaishi? Tace ba ko ina? Ya doka mata tsawa kina haukane ki barmin yaro da ciwo? Dif ya kashe wayar ya bugawa hamza, "hamza maza kaje gidana ka dauki arfat ka kaishi asibiti. Yanzu nan zanyiwa doctor waya. Yana kashewa ya mike yana zagaye falon, hannunsa goye a bayansa, yanata busar da huci. Ya sake buga wayar yauwa doctor za a kawo maka yarona. Ai gashima sun iso. Yauwa dr ka kulamin dashi sosai likita yace kada ka damu, zan kula sosai. Yauwa nagode. Yana kashe wayar ya kalli mansura ke ki hada abunda zaki hada, da asuba zamu tafi. Ta kalleshi cikin mamaki ba cewa kayi sai nanda kwana shidda ba? Ya girgiza kai bazan iya ba, bansan wane hali yarona yake cikiba. Karfe tara na safe suka shigo gidan ba wanda yasan da zuwan su. Gidan a gyare, mansura tayi bangarenta, Ahmad ya biyo Aliyu bangaren zainab. Zainab tana zaune cikin kwalliyarta tana ta kamshi. Umma da mama da ummi sunzo tun bakwai na safe duba arfat, yana hannun ummi tana bashi magani ta dabara, Aliyu yayi sallama, zainab ta bude baki cikin mamaki a ranta tace jiya da sassafe ya tafi. Kallo daya yayi mata ya dauke kai, tace yaya sannu da zuwa. Ya daga mata hannu kawai, Ihsan ta taho da gudu ta rukunkumeshi ya dauketa yana sumbatarta. Ya durkusa yana gaida iyayensa, ya ajiye Ihsan ya dauki arfat, yana duddubashi yayi tsaki, yaro jikinsa du ya saki, babu kuzari, babu wani karfi. Ummi tace sharrin amai ai yafi ga haka, ya dauki maganganun yana dubawa ya fice dashi a kafada. Yace musu, umma bari na maidashi wani asibitin. Ihsan ta biyo shi a guje, Abba zanje, ya riko hannunta suka fita Ahmad ya shiga da gudu ya fada kan cinya zainab, ta rungumeshi amadina tare kuka taho da aunty? Umma tace me gidan saukar yaushe? Sannan ya kula dasu, ya nufi wajensu yana dariya, ya gaishesu ya fice da gudu ya nufi bangaren mansura, yana gaya mata su umma suna nan dole tazo ta gaishesu, tayi musu barkar haihuwar zainab. Tare da tambayar ya mai jikin? Suka ce da sauki. Zainab ta dan rissina aunty ina kwana? Ta dago ta kalleta, a zuciyarta tace wai wani irin kyau da kullum kamar kara mata sabuwar halitta ake. Ashe ba rayuwar abuja ce tasa ta wannan kyaun ba? Ko ina take kyan nan bazai gushe ba. Zainab ta sake maimaitawa aunty ina kwana? Firgigit tayi ta amsa lafiya lau. Ta ttashi ta fita daga dakin. Ummi ta bugawa Aliyu waya, lafiya kuwa mukaji shiru? Aliyu yace bakomai ummi sun canja masa magani ne, sun kuma sa masa karin ruwa, yana karewa zamu taho. Tace to shikenan yanzu mu zamu biya muga jikin nasa, sai mu wuce gida. Suka yiwa zainab sallama suka tafi zainab ta mike ta shiga kicin ta dafa musu wannan, ta soya wacan wai duk kokarinta ta faranta masa taga yayan nata yana fushi da ita. Sha biyu dai-dai suka shigo, abun mamaki Arfat ya ware, yanata wasansa da dariya. Zainab tayi kwalliya ta daukan hankali, tana ta zuba kamshinan nata mai dadi, ta tareshi yaya sannu da zuwa. Ya kauce ya barta a tsaye ya wuce ciki, ya shimfide arfat ya shiga wanka, ta dauki arfat tanayi masa wasa yanata dariya, tasa masa nono a bakinsa yasha ya koshi. Ahmad ya shigo aunty mami naga sun dawo, Ihsan tana gurin mama kawo arfat din. Tace gashinan Amadina. Ya daukeshi, kai aunty mami kin iya haihuwar turawa, masu kyau, ni dadi nakeji naga kannena masu kyau haka. Tayi dariya, Allah Amadina, zoka kaiwa mama abinci kazo kuci kaida Abbanku. Yace to aunty mami rikemin kanina yanzu zan dawo. Ya dauki ya tafi, ta saka arfat a ruwa, ta sake masa wanka, ta canja mishi kaya yanata kamshin hoda ta sashi cikin kekensa na zama. Aliyu ya fito ya nufi arfat, ya daukeshi, Abbana ya jikin? I luv u Abbana, ta zauna kusa dashi, yaya barka da dawowa ga abincinka. Bana ci. Haba yaya don Allah kayi hakuri meyasa bazaka ciba? Ki kyaleni kawai zeey kin batamin rai, ki barmin yaro da ciwo ki ki yimin waya, to da ya mutu saidai na tarar da gawa kenan? Ya tsaya bakin taga yana kallon Ahmad da ihsan suna ball. Via #Justice_Hamzat [8:13AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4***16 Ya tsaya bakin taga yana kallon Ihsan da Ahmad suna ball a harabar gida. Yaji dadi a ransa, zainab ta taso ta daura kanta abayansa tana magana, cikin sanyinta. Kayi hakuri yayana ka gafartamin naga baka dade da tafiya ba, kuma ka barshi lafiya lau, saina kasa gaya maka, ina gudun tashin hankalinka. Saina rasa ya zanyi da yaron, ga talatu ta tafi duba jikarta ba lafiya, na rasa ya zanyi dashi, ni nasan bazan iya fita bada izninka ba, shiyasa kawai nasa yaron a gaba ina kuka. Yaya ka yafe min, bada niyya nayi hakan ba. Ya juyo ya rungumeta yana share mata hawayen, yaji tausayinta, ya juyo da ita ya rungumeta yana rarrashinta. Shikenan naji, ya isa daina kukan, na hakura muje ki bani abincin. **** *** ****** da yaje gida yake cewa Alh yana so zai rubuta takardar neman alfarma a dawo masa da ofis dinsa kano, saboda ya zauna cikin danginsa da iyalansa. Alh yace wannan shawara tayi daidai, tunda ka fara tara iyali dole ka zauna a waje daya, ko don kulawa da ilimin 'ya'yanka ma. Hakan akayi kuwa baisha wata wahala ba, wajen amince masa, aka bashi ofis a kano. Ga harkokin kamfaninsa komai yana garawa yanda yake so. Zaman mansura da zainab babu irin kyara da wulakanci da cin mutunci da mansura bata yiwa zainab, amma zainab saita kwantar mata da kai tana binta a sannu, bata kuma bari Aliyu ya sani, bare yayiwa mansura fada, ita dai zainab ta dage da gayawa Allah basu zaman lafiya. Cikin hukuncin ubangiji kuwa, Allah ya amsa addu'arta. Ta shiga falon mansura arfat na biye da ita, watansa sha biyar yanata yawonsa ko ina, amma bata yaye shi ba. Tace aunty zanje dubo jikin hajiya, ga arfat nan kafin Ahmad da Ihsan su dawo islamiyya. Har zata fita, mansura tace ke dawo ki dauki danki. Zainab tayi murmushi tace dana ko danki aunty? Ai kin fini karfi akan 'ya'an nan dani dasu du mallakarki ne. Mansura tace wai 'ya'yanki da kike turowa su wuni a bangarena ke kina naki bakya tunanin na cutar miki dasu, kona dakesu, ko nayi musu wani mugun abu? Zainab tace haba aunty na dade fa da sanin halinki, tun ina 'yar shekara takwas nake hannunki, da kina da mugun abu dani zaki fara yiwa. Aunty kina da kirki da hakuri kullum dauriya nake yi, har nake iya hada ido dake. Amma ina mai jin nauyi da kunyar aure miki miji danayi. Tasa kuka. Mansura ta taso ta rungumeta, kada ki damu zainab na dade dayin nadaman irin abubuwan da na rinka yi miki, don kin auri Aliyu wanda wauta nayi da son zuciya, tun fil-azal Allah ya rubuta ke matarsa ce, to ya zanyi da wannan rabon? Tunda kika haifi Ihsan Allah ya cusa min kaunarta a raina, haka arfat gani daya nayi masa naji kaunarsa ta ratsani. Kiyi hakuri zainab da abunda nayi miki. Ta rungumeta, wayyo aunty dan Allah ki bari ban taba rikonki da komai a raina ba, na yafe miki aunty nima ki yafe min. Na yafe miki zainab. Aliyu ya fito daga daki yana yi musu tafi, yace nagodewa Allah da kuka hade kanku, ga cek na milyan biyar-biyar kuja jari. Suka yi tsallen murna suka rungumeshi, suna masu yi masa godiya. Sun hade kansu bame jin kansu, tare suke harkar business dinsu. Dubai zuwa kano suna harkar gwala-gwalai, mansura ta samu ciki ta haifii 'yarta mace. Ansha murna da bidiri, akasa wa jaririyar Ikram, Ihsan du tafi 'yan uwanta murnar zuwan Ikram don gani take yanzu ta samu abokiyar shawara. A tsakanin mansura da zainab baka iya gane 'ya'yan, don gaba daya sunfi zama bangaren mansura. Aliyu kullum yana cikin godiyar Allah. Kamar yau da kullum nima da nake cikin godiyar Ubangiji. TAMMAT BI HAMDULILAH. Sai wani jikon kuma @Khadija Idris ringing