AJEEMAL🌬 STORY AND WRITING By Oum amreesh❤ DAGA ALKALAMIN Khaleeseart Raeeys💦💦 ........... .... 08105565439 or 09031917169 DM .........Free book😍 ............ Page 4⃣8⃣.............................. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 ....... .. G'yara tsa yuwa heelah tayi baki bude heelah kebin Ajmal da Nisha da kallo yayin da Nisha ke serving dinshi ta shaka abinci a plate ta tura masa plate din gabanshi, jikake dadda d'an kamshin abincin gabaya daya ya cika parlourn Heelah jitayi tamkar ta isa garesu tarufesu da duka tadauki plate din abincin tajuyewa nisha atsakiyar kanta , da kar fi Raheelah ta ciza lips dinta daga bi sani cikin sauri ta haura upstairs tabar arean parlour , tsit kakeji parlourn kamar bakowa , Nisha tunda ta gama serving din Ajmal taja baya ta tsaya tana bin Aheel da kallo gwanin ban tausayi ya shige jikin papansa tamkar mai shirin ko mawa ciki, se ajiyar zuciya yake saboda tsawar dayasha gurin mommynsa dazu , itade kullum tausayin Aheel da kaunarsa sake karuwa yake kullum sake tasiri yake cikin zuciyarta , jitake inama ace Aheel daga cikinta yafito da ya sha ta rai raya kulawa tareda shagwabashi , wacce baisamu daga mom dinsa , Ajmal kuwa hankali kwance yakecin abincin yana latsa phone dinsa, yau wajan cin abincin nasa harwani lumlumshe ido yake da alama yana amsar sakon girkin yanda yakamata , kamar wanda akace yadago kai , karaf idonsa yasauka akan nisha wacce ta zura masa ido yuwa zata lasheshi seai zuba murmushi take , ganin yanda taga ajmal keta lumlumshi ido kamar maijin bacci , har kullum face dinsa kara kyau da kwarjini yake ga kyakykyawan dimple dinsa dake lo tsawa yayin da yake cin abincin , duk wanda yasanya ido kansa bazaiso yajanye idonsa daga kansaba" He! are you okay ajmal yatambaya yana hade gira , " I'm okay nisha tafadi adan razane because yakamata tana masa kallon kwaf, jin haka yasa yacigaba da cin abincin , yana kammalawa , yajuya gefe yakalli kyakykyawan dan nashi aheel wanda tuni yasuma gyangyadawa jikin papanshi , ajmal hanu yasa yasun kuci aheel yadaura saman cinyarshi aheel tar idonsa akan papanshi yashiga zuba murmushi, ajmal shima kallon dan nasa yake tareda fadin," My little boss aje ayiwasu hajia gaisuwan safe ajmal yafadi yana masa alamar yabi nisha sutafi aheel kamar jira yake dama cikin hanzari yazame daga cinyar papansa ya isa gun nisha yana washe mata baki, itama se murmushi take zubawa, nan tamatsa tashiga tattare saman table din tareda daukan tray din tana shirin barin parlour, "As from now bana bukatan breakfast lunch ko dinner daga side din su daddy , duk wani abun bukata na tanadesu cikin store dina , kululu yan hanjin nisha yakada meyake nufi ?kitchen dinsu zata shiga tanamasa girki ? " Bakiji bane? " ajmal yatambaya jin shiru bata amsashiba, nisha murya asanyaye tace " To naji " daga haka tadauki hanyar fita tareda aheel dake biye da ita , ajmal tunda tajuya yakurawa bayanta ido hartafice ,karun farko daya tsaya yasanya ido akan yarinyar yau shigar da nisha tayi skirt and blouses yayi matukar yimata kyau gashi yafitar mata da shape sosai ajmal baisamu daman kallonta da kyauba har seda tajuya baya sannan yasamu daman yimata kallon tsaf yanda take tafiya slowly kamar wata macijiya gwanin daukan hankalin mai kallonta ba laifi yarinyar akwai tsari da yanayi maikyau duk da ba tsayawa wani kallonta yake da kyauba, balle yasan sauran baiwar da Allah yamata wani gauron numfashi yasauke daga bisani yamike yanufi upstairs yashiga bedroom dinshi tunda yashigo dakin yafahimci kamar ankimtsa bedroom din ba kamar yanda yafita yabariba , koda yashiga toilet ma haka angyarashi an wanke duk dadai gyaran bawai dari bisa dari bane yasan bazai wuce aikin heelah ba. tadaiyi kokari because bawani iya aiki tayiba just kinibibine irin nata, koda yashiga toilet din bakinsa ya wanke tareda face dinshi sannan yafito yanemi sofa yazauna , laptop dinshi yashiga dannawa yafada wani aikin jim kadan heelah taturo kafa tashigo kallo daya ajmal yamata yakai dakai yacigaba da abunda yake, tana karisowa tanemiguri kusa dashi tazauna ," "sannu da hutawa honey " Heelah tafad'i tana dan murmusawa, batareda yakalletaba yagyada mata kai batareda yace komai ba, dan silent Heelah tayi daga bisani tadaura head dinta a shoulder dinsa tashiga raira masa kuka, mamakine yakama Ajmal jin sautin kukan Heelah ya doki kunnuwansa , rantsa ido yayi tareda zame shoulder dinsa yajuyo suna fiskantan juna , "what are you cry" yatambaya yana kallon Heelah dake matsar kwalla, head dinta tamayar saman cinyarshi cikin kuka take fadin, "Pls honey meyasa duk abunda zanyi naburgeka bakaso ? why? inwani laifi nayi aiseka sanar dani nabaka hakuri pls !" Heelah tafad'i gamida tasowa tarike hand din Ajmal, " niba abunda kikamin, kuma niban hana kiyi abunda zaiburgeniba duk da burgeni abune mai walaha kema kin sani yafad'i yana dan zame hand dinshi, "But meyasa kazabi waccan yarinyar amatsayin mai hidama dakai bayan gani amatsayin matarka, "I'm not choosing her abunda yakamata kiyine tanuna miki amatsayinki nayadda kikafada koba komai tafara maido dake cikin sense dinki" Ajmal yabata amsa tareda mikewa yadauki phone dinshi yana kokarin barin dakin, takaici duk yacika Heelah jin abunda Ajmal yafad'i mai yake nufi da ita tadawo da ita hankalinta, dasauri Heelah tawuce gabanshi tana fadi'n, " to daga yau banason sake ganin kafarta cikin side dinnan idan ba hakaba sena karyata gida uku.., ihu heelah tasake sakamakon damko gashin head dinta da Ajmal yayi , rai amatukar bace yake magana," baki fiska danayi bashi yake nufin kimin rashin kunya ba , sake murda gashin nata yayi yanacigaba da fadin " yarinyar dakike magana akanta kuma she is my staff nitakeyiwa aiki bakeba barunki da ita , yana gama fadin haka yasaketa yajuya yafita abunsa , daganan Heelah tafad'i kan gwiwowinta tasaki sabon kuka tamkar wacce tayi sabon hauka ,.... dariya suke sunashewa gwani sha'awa ana breakfast anatafa hira kamar yanda aka saba , su Hajia Goggo rabi ammi ga daddy wanda Aheel kecinyarsa yanashan fruit salad , gefe su yan matan ammi Reeda da a Fadeelah sekuma Nisha dake gefen hajiarta "Niko nace ya maganar komawar takine , ko kincanza shawara ba yanzu ba" Daddy ke tambayan Goggo rabi , tambayetade ya kama tasamu takoma tabar bar gidanta tamakale anan, Hajia takarb'i zancen tana kallon Goggo rabi, dan zumbura baki Goggo rabi tayi kamar wata karamar yarinyar tana fadi'n," ba fasawa nayiba jira nake atsai da bikin yaranan nan saboda nasamu daman dawowa bikinsu nan kusa , " Hhh wasu yaran wai? Daddy yatambaya yana yar dariya , " gasu agefenka kana kallonsu Goggo rabi tanuna su reeda dasuke zazzare ido , " yo banda abunki yaranda suke karatu basu tsaida samariba balle asa ranar auraddasu gwarama ita fareeda yar gd za ayi ba matsala but ita hajia karama ( fadeelah ) babu saurayin ma balle ayi tunanin hadasu Daddy yafadi yana dan kurban ruwan tea dariya duka suka bushe dashi suna kallon fadeelah wacce taturabaki tashagwabe fiska," To albishirunku , itama fadeela anyi mata miji lokaci kawai mukejira, gabaki daya hankalinsu suka mayar kan ammi wacce takemagana, " ina mijin yake akawo manashi mugansa Goggo rabi tafadi suna koma dariya, ," seriously last week MODIBBO yasameni da maganar cewa yayiwa Fadeelah miji nasanarwa Daddynsu atsaida ranar bikinsu, " Amma ai ba asanar da nidinba , amma waye yayi babban sa'a haka Daddy ya tambaya gaba daya suka koma maida kallonsu ga ammi suna jiran amsa harda Fadeelah dayi tsuri tsuri da ita tana jiran tajiwaye akayiwa sadakanta haka , murmushi ammi tayi tana dan juya ido takalli Fadeelah miji nagari zabi mai kyau aboki ga yayansu kuma Doctor gida da waje doctor fu' ad Allah yasa zamin yayi miki ammi tafad'i tana kallon Fadeelah data zaro ido waje , tsan tsan farin ciki batasan sanda tafurta," Alhamdulillah abaiyane wanda yasa tayi hanzarin mikewa dasauri tabar gurin tanufi bedroom da gudu , nan fa su Nisha da Reeda suka rufa mata baya , daga nan fa dukansu suka shigayin hamdallah lallai yayansu yayiwa k'anwarsu zabi nagari sede fatan dacewa , " Masha allah komai yayi kyau yanda akeso , duk da tafiya tasameni cikin week dinan ammade zanje muzauna da dan uwana (abu)muga abunda yadace se musamu mutsaida bikin ko nan da 1 month tunda bawani abunda zamu tsaya jiraba, sede muyi fatan Allah ya aramana tsawon rai da lokaci, nan su ammi suka shiga amsawa da "Ameen , yau kowa farinciki fal zuciyarshi , Fadeelah kamar tazuba ruwa akasa tasha saboda tsan tsan murna da farinciki , haka suka wuni suka kwana cikin nishadi , washe gari da safe karfe 8 Nisha tayi wanka tafito takimtsa jikinta tashirya tsaf cikin duguwar gown tareda yafa mayafi bisa kanta tanufi fita side din Ajmal , kamar yanda ya fada baya bukatan wani abu daga bangaransu , tana isa part dinshi kamar kullum seda suka gaisa da securityn dake wajan sanan tasamu daman shigewa ciki, koda Nisha tashiga ciki hamdallah tayi ganin bakowa cikin parlourn sidi sidi , tashiga kitchen, seda tafara g'yara kitchen din takimtsa komai daga bisani tashiga duba kayayyakin da zatayi amfani dasu bada wani bata lokaciba tashiga hada masa dadda dan delicious data saba , cikin dan kankanin lokaci ta kammala komai tafito tajerashi komai slowly takenyinshi gudun kar wanan masifaffiyar matar tajiyuta, nan tasuma kokarin komawa kitchen din but kankace kwabo heelah tabaiyana a parlourn kaikace kamar jiratake, " Mayya dama nasan kece mai mini buruntu a kitchen, tundaga sama nakejin motsi akasa mai kikazo dauka? heelah ta tambaya yayinda take kokarin karisawa ga nisha wacce tayi tsayowar soja batare da tawaiwayoba , " tambayarki nake kibani amsa kinyi ajiya a kitchen dinne da kikazo dauka , Heelah takuma tambaya tareda juyo da nisha suna fuskantar juna, " Uhm breakfast nazo na hadawa papan aheel, Nisha tace tana zare ido," Uhm yayi kyau dakinbar wannan muzuran dakikeyi ba koranki zanyiba , because ke yar aikin mijinane Mai mana hidima , Bakomai kicigaba da aikinki , sede warning dina dake shine banason wadanan kazamun kafafuwan naki yasake taka bedroom din mijina da sunan g'yara , wannan nikeda hurumi da hakki akanshi inafatan kin gane,? but babu laifi kig'yaramin nawa bedroom din , dan matsawa Heelah tayi dining table area tashiga duba girkin da Nisha tashiryawa ajmal, dan tabe baki tayi sannan tace," Inada bukatan abinda zanci yanzu wadannan abubuwan DA kika shirya banida ra ayinsu, ko zaki iya shiga kitchen kigirkamin abinda nakeda bukata ," kiyi hakuri aunty niba yar aiki bane bazan iya sake girkawani abin yanzuba because inada abunyi yanzu, nisha tafadi tana mai kokarin barin parlourn ," ke tsaya Heelah tafad'i gami da janyota baya, mekike nufi dake ba yarki bane bayan aikatau kekawoki side dina kuma akarkashin mijina kike , dole kikasance akarkashin matar shi, dan haka kiwuce kije kiyi abunda nasaki , cike da takaici Nisha tadubi Heelah tana fadin" Eh akarkashin mijinki nake but kekuma ban kasance akarkashinki kiba because ni yar hidiman mijinkinkine bakeba , dan uwa kuma yayana nadauki mijinki ba uban gida ba,, incede kima macece kamarni , zaifi kyau kishiga kitchen kiyiwa kanki abunda zakici , ni inada abunyi nisha tana fadin haka tajuya zatafice , aiko cikin takaici da bakin ciki heelah batayi wata wataba tasha gaban nisha tadauketa dawani gigitaccen mari wanda yasa nisha zubewa kasa ta tallafe gefen face dinta tasaki kuka wuiwui kamar karamar baby , " tas Nisha taji andauke heelah damari itama wanda yasa nisha mikewa daga durkuson datayi tana kallonsu, Ajmal ne tsaye jikinsa sanye da white jallabiya wanda yake tsaya tundazo daga sama yana hango rikicinda Heelah keyi, ganin marinda Heelah tayiwa Nisha yasa yayi saurin sakkowa cikin bacin rai yadauki Heelah DA mari seda taga wasu taurari, " nikamara? heelah ta tambaya tana kallon ajmal wanda shima Itan yake kallo cikeda takaici," saboda namari wannan mara kunyar yarinyar shine kasa ahanu afiskana da sunan mari , abunda bantaba fiskanta daga garekaba wlh azim yau kajawo mata kwanan kabari Heelah tafadi akidime tayi wajan dining tazari wata yar karamar wuka zatayi kan Nisha dashi, Nisha kamar wacce aka dasa agurin gaba daya tatsorata takasa yin gaba ko baya , ganin abunda Heelah ke kokarin aikatawa yasa Ajmal yashiga gaban Nisha yatare Heelah daga abunda takeson aiwatarwa rike hand din Heelah yayi tareda fisge dan karamin wukar dake hanunta yacillashi gefe , daganan yasa hanu ya sunkuci Heelah saman shoulder dinsa ya haura da ita sama, direct bedroom dinta ya nufa da ita , seda yakata harsaman bed ya wullar da ita daga bisani cikin hanzari yabar dakin tareda baida kofar yarufeta tabaya da key, Heelah kamar wanda hauka yasuma taba kwakwalwarta haka take dukan kofar da karfi tana fadin Ajmal yazu ya bude yau seta kashe nisha, ajmal ko ajikinsa haka yanufi downstairs cikin sauri , amma kafin isowarshi , Nisha najin motsin sakkowanshi ahanzarce tasamu daman watsawa dagu tayi waje, Ajmal naganin fitarta yasa yakoma yazauna kan sofa , yadau mintuna yana zaune agurin daga bisani yamike yahaura sama yanufi bedroom din Aheel, koda yashiga yasamu dan nasa se bacci yake tasha hankali kwance , hakan yasa Ajmal ya fice daga bedroom din Aheel yanufi nashi dakin , yana shigowa yadauki phone dinsa domin duba time karfe 9 dawasu yan mintuna gakuma miss call dayasamu cikin wayarsa jikin screen din wayar anrubuta " My blood , phone din ya ajiye yanufi toilet yayi wanka yafito yashirya cikin shiri maikyau daga bisani yanufi kasa, kotakan breakfast din biyeba yawuce yafita abunsa , Aban garan Nisha kuwa tana barin side din Ajmal tanufi part dinsu direct bedroom dinsu tawuce tasamu su reeda se bacci suke basuda niyan farkawa yanzu, itama kwanciyar tayi tana share hawayenta tareda maida ajitar zuciya , bakaramin takaici tajiba da marin da Heelah tayimata, amma ko bakomai taji radadin da takeji yarago tunda agabanta Ajmal yasa hanu yawanke matansa da mari saboda ita , bakaramin jindadin hakan tayiba , ko bakomai da lamamun tana da dan mutunci aidonsa tunda ya iya marin matarsa akanta abunda baitabayiba kuma yanuna baccin ransa sosai afili, to kuwa itama yanzu takejin takudiri damaran farantawa mijinta tareda yimasa hidima yanda yakamata tunda ita tagaza daha bacci mai nauyi yadauketa because dama tagaji gashi jiya batayiwani bacci sosaiba saboda kwana tayi tana karantu exam dazatayi na jam gobe gashi dasafe ta tashi dawani aikin kuma, Misalin karfe 11pm nisha bacci mai nauyi take , cikin baccin taji anataba mata tafin yan kafafuwanta, but takasa bude idanunta because baccine sosai acikinsu haka cikin muryan bacci Nisha kefadin ," Uhm uhm Banaso! cankuma sejitayi ankoma anakokarin jan pillown data kwanta Kai ahankali, jin head dinta nakokarin barin saman pillow yasa tabude ido ahankali , tar tabude idonta gamida tashitsaye tsakiyar gadon tana zazzare idanu , farkon bude idonta ganitayi kamar Ajmal tagani yana tsaye kanta, daga bisani kuma data murza idon dakyau Kamal tagani tsaye yana washe mata baki yana fadin," Surprise! da mamaki take binshi da kallo sekuma tamaida kallonta ga dakin ita kadai su fadeelah basanan sekuma takalli kamal wanda keta zubamata murmushi kamar gonar auduga, " Ya kamal! Kaine? nisha tafad'i ahankali, dariya yakwashe dashi kafin yace," Year I'm nacanza mikine? yafadi yana mata kayataccen murmushi, sakkowa nisha tayi daga bedroom din tana fadin, " saukan yaushe? Ina aunty nabilah? dan matsowa yayi kusa da ita yana fad'in " Nayi surprising din kune because duk gidan nan bawanda yasan da zan dawo ya ajmal ne kaide yasani in fact ma shiya daukomu daga airport, kallonshi kawai Nisha keyi tana murmushi," Ina Aunty Nabilah Nisha tasake tambaya karo nabiyu, kamar bazaiyi magana ba sekuma taji yace," tana sashin Hajia a can muka sauka duk family anacan kekuma kinanan kina bacci, cikin hanzari nisha tashiga fadi'n, " Muje can musameso to tafad'i tana kokarin yin gaba , ga mamakinta setaga Kamal yanuke, bakin bed yanema yazauna tareda hade raii, " Zomuje mana! Nisha tafadi gamida jiyowa tana kallonshi, amma kamal senukewa yakumayi yaki tashi, dariya nisha tasaki ganin yanda kamal yayi tamkar wani baby harda wani nuke shoulder, " Please meyasa? Nisha tafadi tana d'an shagwab'e fiska " Naki d'in da murna da d'auki nataho gareki but ko tambayan yanake bakiyiba balle. adanyi hugging dina amatsayina na brother dinki, dariya nisha takumayi tana fad'in, " I'm sorry bro ya kake let me shaking hands nisha tafadi gamida mika masa hanu , haka kamal yadauki hanu yamika mata amma ga mamakinta setaga kamal gam yarike mata hanu tareda janyo hanunta tafado jikinsa tsam yarungumeta akirjinsa kamar wata baby, cikin hanzari nisha tajanye jikinta akunyace tafice da gudu tana murmushi, shima mikewa yayi cike da farin ciki da nishade yana murmusawa yabi bayanta, Nisha bata tsaya da gudunba harseda ta iso door din Hajia taja tatsaya ganin Ajmal dake kokarin fitowa wanda harsuna kokarin karo da juna , kallonta Ajmal ya tsayayi da mamakin hanzarin metake gashi harwani haki take kamar wacce tayi tsere , daga kanda zaiyine ya hange Kamal dake biye da ita wanda ganin yayansu yasa yarage saurin yashiga tafiya slowly yana sosa keya irinta marasa gaskiya " wato shiyasa akane meshi cikin family aka rasa ashe gun wannan yarinyar yaje yatare Ajmal yashiga maganar zuci , baitsaya jiran isowar Kamal ba yasamu daman barin wajan yanufi side dinshi, wanda hakan yabawa Nisha daman shigewa part din Hajia cikin hanzari kamal shima yasamu daman biye mata baya, Ajmal yana isa cikin parlour ya hangi Aheel da mom dinsa wacce tayi amfani da extra key wajan bude kanta tazuba musu abincin da Nisha ta girka sunaci , Aheel naganin papanshi yashiga washe baki yataso da gudu ya rungumeshi , cidak ajmal yadaga Aheel suka karisa dining table suka zauna, " Your welcome dear Heelah tafad'i kamar ba ita tagama daru dazuba, shiru yayi baice mata kala ba sema kallonta dayake idonta sunyi subul subul dasu saboda kukan datasha dazu , mikewa tsaye tayi tashiga yin serving din Ajmal ba tareda yanemi taimakon taba , shikuwa baiyi kokarin dakatar da itaba hartagama tatura masa plate din abincin gabanshi tareda duk wani abun bukatu , bamusu yasuma cin abincin , yana tsaka da cin abincin kamar wanda aka tsikareshi idanunshi suka shiga hasko masa nisha dake tafe cikin hanzari kamal nabiye da ita, Nan kuma ya kauda wannan tunanin daga ransa, lokaci d'aya kuma yaji abincin yafita daga ransa ma' ana yakoshi , haka yasoma kokarin mikewa , " Papa ina zakaje ? Aheel ke tambayan papanshi ganin yamike" I'm going to the rest kazauna kusa da mom dinka ,gyada kai aheel yayi tareda cigaba dashan cornflakes dake gabanshi , heelah bayan ajmal tabi da kallo tana tab'e baki harya kurewa ganinta ,.. , Ab'an garansu nisha kuwa tunda suka shiga sashin Hajia , a parlour suka tararda sauran familyn anatashan fira cikin raha Daddy Ammi Hajia da Goggo rabi sesu fadeelah da reeda wanda suka sanya Nabilah a tsakiya sunata zuba mata surutu da tambayoyi, itakuwa Nabilah duk hankalinta nakan Kamal da nisha wanda sukashigo yanzu atare , duk yanda Nabilah tayi iya kokarinta wajan mantarda Kamal soyayyan nisha amma abun yaci tura , yanzu gashi daga saukanso zuwa gida ita yafara cigiya , koyanzuma da ake tsaka da hira tafahimci yanda suke jefawa junansu wani kallo suna murmushi, shiyasa koda sukashigo cikin parlour Nisha data dagawa Nabilah gaisuwa ba harzuci ta amsa mataba saboda yanda kishi ke d'awai niya da ita, itakuwa Nisha kallon Nabilah take ganin yanda takara canzawa tayi kyau taciko kuma takara haske ,da alama hutu yakarbeta Masha allah wasa yayi kyau kamal kundawo cikin SAA sai dai kuma kasam mashemu because bawanda kafadawa , yanzu yakamata mubarku kuje kuhuta kaida matarka dan nasan baza arasa gajiya atareda kuba, Daddy yafadi yana kallon kamal daga bisani kuma yamaida kallonsa ga Ammi yacigaba da fadin," yakamata kiyiwa Barka magana ta tanadar musu da abuntabawa , daga bisani kuma munada bukatar ahadamana kayataccen dinner in the night saboda farinciki wannan ranar , " Insha allah yanzu kuwa Ammi tafadi cikin farinciki tareda mikewa tafice , sundan taba hira sosai yayinda Kamal yaciga ba dabasu labarin yanda wasansu ta kwallon kafa takasance, seguraran azahar tagabato kai suka suma watsewa domin gabatar da bautan ubangiji, koda suka fadeelah suka shigo bedroom dinsu Reeda ne kadai tashiga toilet tagabato alwalanta sukuwa Nisha da Fadeelah suna fashin sallah ya bakon nasu kusan atare yaziyarcesu, cikin Nisha da yamurda matane nayunwa yasa tatuna tunsafe ba abunda tasawa cikinta , hakan yasa tamike tafice tabar fadeelah dake kwance saman bed tana latsa wayarta , Nisha direct kitchen tanufa ta tadda barka tana tsaka da aikin da ammi tasata , barka naganin nisha tasaki murmushi, "yar nan yau koma ina kika shiga kolekoni ba kiba inata cikiyarki "murmushi nisha itama tayi tana fadin "kinsan yanzu papan Aheel yace nadaina kawo masa breakfast daga nan sede naje can part dinsa nayimasa girki dana dawo kuma bacci nakomayi shiyasa yau bakijiniba ai " . " Kai amma yayankun nan yana wahalar mana dake amma ko bakomai zaki samu lada ai, amma koya kikeji da wannan masifaffiyan matar tashi mai bala'in kishin tsaya duk ita take kore masu mata aiki saboda rashin hankali irin nata , Barka tafad'i gamida jimami" "Uhm baba barka taimakeni da a binda zansawa acikina because yunwa nakeji sosai tunsafe namance banci komai ba Nisha tafad'i gamida kaiwar da zancen barka," "laa ai ammi tafadamin bake a breakfast din dazu sabida bacci kike baki tashiba shiyasama nakillace miki naki breakfast din amma inda wani abunda kikeso kifadi yanzu sena miki shi," "aa basekin wahalar da kankiba iya wannan dinma yayi ," "To shikenan kede jekizauna a dining table yanzunan zanfito" Barka tafad'i, bamusu Nisha tayi abunda Barka tace ba dadewa Barka tafito daga kitchen tajerawa Nisha plate agabanta plate din Irish and chicken dawani hadin salad agefe se dan madaidaicin kyakykyawan bowl mai daukeda fruit salad wanda yaji madara Yakuma sha sanyi ,bawani tsayawa jira Nisha tasoma ci seda taci takoshi takauda yunwar dake tareda ita daga nan tadauki plates din tanufi kitchen, tana shiga ta ajiyesu daga bisani tashiga taya Barka da aikace aikacen da take ,sannu ahankali sunayi suna fira hatsuka kammala daga nan suka shiga jera kayan lunch bisa dining table daga nan Barka takoma kitchen tadauko try din abincin data tanadarwa kamal da matarsa masu lunch din tasuma kokarin ficewa, "Baba Barka ina kuma zaki bayan gani ? nasan lunch din su ya kamal ne da Aunty Nabilah please bani nakaimusu na hutar dake ," "Aa yar nan baza ayi hakaba, tunsafe kika gama bautan yayansu yanzu kuma nabarki kikare Dana kaninsa gaskiya baza ayi haka daniba kibarshi kawai yanzu zanje nadawo " "Please baba Barka kibari nakai mana " nanfa Nisha taita mata magiya tareda dagewa Barka wanda yasa dole Barka tahakura tabata try din abincin nisha ta amsa tareda sa kai tafice , Nisha nakarisowa door din Kamal tashiyin knocking bugu daya zuwa biyu aka bude, koda budewa kuwa Nabilah takagani tsaye cikin shirin kananun kaya t shirt da wando skintight wanda yawuce gwiwar kafarta kadan tasakalo sumarta har baya yakwanta lub tayi kyau da ita, murmushi Nabilah tasakarwa Nisha cikin sanyin murya tace , " Please come in! ahankali nisha tasakalo kafarta takariso cikin parlour yayinda Nabilah tamaida door tarufe ta dawo kusa da Neesha ta tsaya tana cigaba da murmushi, itama nisha murmushi take daga bisani tashiga fadin, " " Am..dam.ma lunch dinku nakawo muku ," "Ayya thanks you so much" Nabilah tafad'i gamida karban try din abincin takarisa dashi saman table ta ajiye ganin haka yasa cikin hanzari nisha tace," " se anjima daga haka tajuya tafice tabar nabilah tsaye tana binta daga kallo hartafice , Neesha nafita tundaga nisa ta hangi ajmal hanunsa dauke da na Aheel se kamal da Daddy wanda yanzu dawowarsu daga masallaci sunjero suna tafiya gwanin sha'awa da burgewa Kamal daga nesa ya hangi nisha tafito daga part dinshi amma kafin su iso harta shige bangaransu cikin sauri, direct Ajmal yanufi side dinshi shida dansa hakama Daddy yanufi nashi sashin , daga nan Kamal shima yakarisa nashi part din, Da dare guraren karfe 9:pm gabaki daya ahalin abubakar modibbo bature sun hade guri guda suna gudanar da kayataccen dinner, dining table medauke da gurin zaman mutum 12 kowanne acikinsu yakasance daga daya daga ciki wasu suna facing din wasu gwanin burgewa da ban sha'awa harda Heelah wacce Ajmal ya gayyatota badan komai because Daddy yace yana bukatan kowa yakasance gurin dinner, Heelah batasan da dawowarsu kamal ba kwata kwata seyanzu da tashigo ta ganewa idonta wanda hakan ba karamin mamaki tayiba , Nisha kuwa tayi tsayuwar daka wajan taya Barka kawo abinci anajerewa wanda komai tare suka gudanar dashi seda suka kammala jera komai Barka tajuya takoma ciki nisha kuma tasamu daman zama kamar yadda kowa yazauna ,daga nanfa kowannensu yashiga serving din kanshi da abunda yakeso yana zubawa a plate, banda ajmal dako motsi baiyiba bayida kuma niyar motsawaa "yade kowa yadibi abunda yakeso yana ci kaikuwa kasa phone agaba kana dannawa?" Daddy ke tambayan ajmal dayayi sunkuye da kayi yana latsa phone dinsa, dan dago kai yayi ba tareda yace komai ba ya ajiye phone din gefe daga bisani yagyara zama ya kallo nisha wacce idonta ke kanshi because kujerunsu yana facing najuna, yanda yakora mata ido tasan serving dinshi yakeso tayi amma ita kuma nisha setashiga kallon heelah wacce takecin abinci tana yamutsa fiska kamar wacce akasa dole ko kallon inda sukema batayi, nan kuma taimada kallonta ga ajmal wanda ya hade rai yabata fiska wani kallon da yakuma watsa matane yasa nisha mikewa tsulum wanda hakan yayi sanadin dawowada hankalim ahalin guresu, daga Hajia Daddy suwa Ammi suka shiga murmusawa ganin yanda Nisha ke serving din ajmal gwanin shaawa da burgewa duk da dama sunsan ajmal inde tawannan fanninne to komai se amsa abincin ma inda zaisamu adinga bashi abaki ajiye spoon zaiyi , Goggo rabi bakinta kamar zai taba kumatu tsabar murmushin jin dadi, kamal kuwa da mamaki yake kallon nisha ganin bani na iya irin na yarinyar dayin abunda ba asataba gaba daya yarinyar tanasun bawa kanta wahala , taban garan heelah nunawa tayi ko ajikinta amma cikin zuciya allah kadai tasan kunar zunda take gaba daya nisha Rana shigar mata hanci amma ba dadewa zata facuta, Nisha harta gama serving din ajmal takoma tazauna kamal kebinta da kallo , nabilah kuwa duk motsin mijinta idonta nakansa , abincin dake gabanta bawani ci sosai takeba kawai tsakura take tana juya spoon ajmal kuwa nisha nagama serving dinshi yashiga gunar da nashi cin abincin, Jim kadan ta bangaran nabilah tafarajin kanta na bala'in sarawa to, jitayi duniyar najuya mata ahankali ta ajiye spoon din hanunta adan dafe tamike daniyar tashi , "Bade harkin kammalaba" Ammi ta tsareta da tambaya , nabilah bude baki tayi daniyar magana sekuma takasa because wani yunkurin amai dayataso mata aiko cikin hanzari ta toshe bakinta tawatsa aguje tafice daga parlourn, gabaki dayansu se bin bayanta da kallo suka shigayi harta fice banda kamal dayayi yunkurin tashi yabita, "mekatsaya jira da ka kasa bin bayan matarka kamata yayi kabita idan da wani abunda yaci karfinku sekazo kayi magana" Hajia tafad'i tana kallon Kamal wanda keta zare ido shibai zaunaba baikuma tsayaba but jin abunda hajia tafad'i yasashi jin karfin gwaiwar bin bayan matarshi dan haka cikin hanzari yabi bayanta, " " Masha allah , ikon allah kai allah abin godiya, tsarabar Canada har gida kai alhamdulillahi" Goggo rabi tafadi tana daga hannuwa sama, hajia da Ammi farinciki harsun kasa cewa komai , Daddy kuwa kai kasa se murmushi yake heelah se hararo Goggo rabi take wacce keta kwararo godiya ga ubangiji", " dama kinbar wannan godiyar dakike dan abunda kuke tunani insha allahu zubewa zaiyi bade tahaifeshi cikin gidan nanba heelah ke maganar zuci , gefe kuwasu reeda ne ke magana kasa kasa tsakaninsu, "Awwwn nabilah fa kamar cikine gareta ko" fadeelah tafad'i ahankali, " bakamar bane cikinema" reeda tabata amsa yayinda sukacigaba da cin abincinsu kamar basu suka gama kuskus yanzuba, duk abunda suka gama tattaunawa tsakaninsu nisha najinsu se murmushi take gefe gefe aheel zaisamu kani zasu samu little baby, shikuwa gogan ko ajikinshi tamkar baisan me akecikiba abincinsa yakeci cikin kwanciyar hankali, Kamal nakarisawa part dinsu koda yashigo parlour ba nabilah aciki hakan yabashi daman karisawa cikin bedroom nan yaci karo da sautin nabilah cikin toilet tanata faman zabga amai cikin hanzari yakarisa baking toilet din ya tsaya harseda ta gamayin aman tawanke bakinta tafito ta tararda kamal bakin door yana jiranta, "sannu! meyake damunkine" Kamal ya tambaya gamida tallafota suka karisa bakin bed suka zauna, " "Please tell me what's wrong ? "Kamal yakuma tambaya, " " bakomai nabilah tafadi gamida sunnar dakai kasa ,cikin hanzari kamal yadauki phone dinshi yasuma lalubar wata number, "Wait! what are you doing?" Nabilah ta tambaya gamida rike hanunshi, " doctor fu'ad zankira yanzo ya dubaki yafadamin meke damunki" Kamal yabata amsa cikin damuwa Nabilah karban wayar tayi ta ajiye gefe daga bisani takalleshi yana fad'in, " bakasan me yake damunaba? gyada mata kai kawai kamal yayi daga nan nabilah tadauki hand din shi tadaura saman cikinta tacigaba da fad'in, "You are doing to be father soon insha allah" Cikin murna da farinciki gamida d'auki kamal ke kallon nabilah, "Oh god waiyanzu ciki gareki ? "d'an g'yad'a kai nabilah tayi tasunnar dakai tana murmushi, "Oh Allah nagode maka zanzama Daddy yanzu nakara girma nima " kamal yafad'i tareda rungumo nabilah yana cigaba da fad'in, "Nagode Allah yamiki albarka ya kareki keda babyna " , daga nan nabilah tarungumishi cikin tsatsan so da kauna tana fad'in " Ameen sannu ahankali suka suma lulawa duniyar maaurata cikin shauki da begen juna , .... Abangaransu Daddy koda sukajira suga dowowar kamal sukaji shiru hakan ya tabbar musu lapiar kenan da haka suka cigaba da gudanar da dinner d insu , koda suka kammala daga nan kowa yashiga watsewa don yau ba tsayawa dugun hira kasancewa dare yayi sosai , dama ajmal baitsaya wani dugun cin abinciba yatashi yafice, matarshima tarufa masa baya tareda aheel daketa rigima shi bazai mom dinsaba gurin auntynsa zai kasance , daker heelah tasamu tayakiceshi daga jikin nisha suka fice , sude hajia har kullum suna mamakin sabonda aheel yayi da nisha , dan haka suma suna gama kammala cin abincin suka suma watsewa kowa yanufi turakarsa , zuciyoyinsu cike da farin ciki da nishad'i, washe gari guraren karfe 8:am bayan ammi tayi breakfast di'nta yanda tasaba tayi shirinta nazuwa office, nan tafito daga part dinsu direct tanufi part din kamal , seda tazo daidai door d'in tashigayin knocking, bugu daya zuwa biyu aka bude kamal ne yafad'e door d'in yanda sanye cikin black jallabiya ganin ammi tsaye bakin door yasan yashiga sakin murmushi yana fad'in, "Please Ammi yakika tsaya shigo mana" ,murmushi itama ammi keyi batareda wani musuba takarisa shiga cikin parlourn, can doguwar sofa ta hangi nabilah takishingida wanda ganin ammi yasa tamike zaune tana yar murmushi gamida sun kuyar dakai "Ai dama kinyi kwanciyarki karna takuraki , ammi tafad'i gamida karisawa kusa da nabilah tazauna," Ammi ina kwana antashi lapia, "Lapia qlu yajikin nakikuma dafatan ba abunda yake damunki yanzu, d'an gy'ada kai nabilah tayi tana fad'in "Bakomai !" ", that's good dama yanzu nake shirin tafiya office shine nace bari nazo naga jikin naki , kuma natambaya Inda akwai wani abunda kikeda shaawa nasa akawo miki because karkicigaba da wahalar da kanki, " "Yauwa Ammi tambayeta de yanzunan nakita tambayanta tafad'i min metakesu taci naje nayi mata order but taki wai bata shaawar komai, kinga wadannan kayan fruit din sune kadai tasamu tadan tabasu Kamal yatare maganar yana nunawa Ammi plate d'in kayan fruit dake ajiye saman table, Yana kuma kallon Nabilah dayi sunkuye da kai , "sudinma babu laifi suna da amfani amma fruit kad'ai bazai wadaceki keda bari naje zansa barka takawomiki abun tabawa wanda zaki'iyaci , karkidinga barin cikin ki dayunwa, d'an g'yad'a kai nabilah tayi taga haka ammi tamike tana kallon kamal tana fad'in" Nizan wuce kakula da kyau , " To ammi kamal yace daga haka yarako ammi harbakin door daga bisani sukayi sallama kamal ya maida door yarufe tareda komawa kosa da nabilah yazauna yamata matashi da cinyarsa kamar yanda suke dazu kafin shigowar ammi , ahankali yakeshafa sumar kanta yana fad'in, " allah yasa kihaifamin baby mai kama dake kamal yafadi yana kallon nabilah da face dinsu ke fiskantar najuna, dan wani cool smile nabilah tasake tana fad'in, " Nikuma nafison nahaifi baby sak irinka , because of what? Kamal ya tambaya " Because kafini kyau da komai nabilah tafad'i cike da murmushi, shima murmushin yake yaname jan dugun hancinta yana fad'in, " And you ba fatanmu de allah yasauke ki lpy " Ameen nabilah ta amsa cikin sanyin murya ,Jim kadan suna tsaka da yar firan tasu sukajiyo knocking din door, " come in! kamal yafadi ba tareda ya motsa daga inda yakeba gaba kidayansu suka tsirawa kofar ido dan ganin maishigowa ganin Barka dauke da try din abinci yasa kamal yasake jingina da jikin sofa yana murmushi, ita kuwa Nabilah kokarin tashi daga cinyarshi tashigayi amma kamal ya hanata dan haka yasa tahakura da tashin , " Megida Barka da safiya fatan antashi lpy baba bakar tafadi tana yar dariya because kamal mutumintane sosai , tasu tazo daya kasancewanshi mai barkwanci da sun wasa wani lokacin bakamar yayansuba shikadai yafita zaka cikin gidan bayida wasa kuma bayidason magana sosai wani lokacin kuma inyajuye kamar bashiba," Yauwa barkade uwar daki ya aikin kamal yabata amsa yana yar murmushi, dama Ammi tace nakawowa madam wannan Barka tafadi gamida ajiye try din abincin saman table dinda ke gabansu tashiga kallon nabilah dake kwance saman cinyarshi tayi lamo takamar mai bacci wanda ganin shigowar barka yasa takulle ido because yanzu gaba daya kunyar kowa take ko hada ido dakowa batasonyi, amma daga kaga yanda eye lashes dinta kerawa zaka fahimci ba baccin takeba rufe ido kawai tayi dan murmushi Barka tasaki gamida kada kai tana fad'in, " Megida bari naje nakarisa aiyukana se anjima allah ya inganta , kamal cikin farinciki ya amsa da " amin mungode daga haka Barka takama hanyar fita still de murmushi bai gushe daga face dintaba harta karisa ficewa tajanyu musu door din tarufe, kamal kallonsa yamayar kan nabilah yayinda yakuma jan dugun hancinta yanda fad'in, " To yanzu kam semi samudaman bude idon iyayen kunya , waima kunyar mekikejine haka shigowar ammi dazu kigabi kika takura kanki sewani nuke nuke kikefa , bude ido tayi tana kallonshi daga bisani tatura baki tana fad'in" Ni wallahi kunyar kowa nakeji yanzu ko hada ido dakowa banasonyi ," meye dalili ko saboda kintaho musu da tsaraban Canada kamal yafadi yana yar dariya, dan bugu takaiwa shouldern kamal tana fad'in, " Kaikam bakajin komai ko ? " To maizanji kuwa bayan nasan kokarin danayi tashi muyi breakfast dan yunwan nakeji kamal yafadi gamida tada nabilah zauna yashiga bude food flats din abincin, pepper soup din kifine da soyayyiyar irish tareda wani hadin salad nakayan itatuwa masu kara lafiya da kuzari se wani dan madaidaicin bowl wanda ke rufe da Yugo fruit salad ancika madara acikinsa, bawani tsayawa bata time kamal yashiga serving din su , yana gama zuba abincin a plate yashiga bawa nabilah abaki kamar karaman baby shima yanaci ba laifi komai tadan tabashi taji kuma jidadin abinci sosai especially hadin salad din tafi bashi ma himmanci dadin dadawa yanda kamal yayi tsayuwar kaida fata wajan ganin taci takoshi bakaramin dadi hakan tajiba koba komai yana kula da ita sosai but hankalita yaki kwanci ganin kamal da nisha Inuwa daya suke zaune suna haduwa dajuna wanda hakan baya mata dadi kokadan , *_IG AJEEMAL*_ Story and writing by Oum amreesh Nisha hanunta har rawa yake gurin kunna light din bedroom din aiko tana kunnawa haske maikyau da inganci yabaiyana cikin dakin , ahanzarce tajiyu tamaida hankalinta ga saman carpet , kwance yake ya dunk'ule guri guda kamar mejin sanyi still yana rungume da pillow tsam a chest dinshi yana sanye cikin kyakykyawan milk jallabiya gashin kansa duk sun hargitso face dinsa sun manne saboda zufanda suka tsatstsafo masa , idonsa arufe jin motsin mutum da kuma kuna light da akayi yasashi kokarin bude ido ahankali yasaukesu kan Nisha dake kokarin karisowa inda yake lips dinta se bari yake, idonsa yamayar yarintse wanda sukayi jawur dasu because haske yayiwa idonsa karfe " Ya ilahi Nisha tafurta ahankali yayinda tagama karisawa gareshi gefe ta sunkuya kasa tana kallonshi" meyasa sameka? are you okay? Nisha tashiga jera masa tambayoyi cikin rawar murya, jin shiru bai amsa mataba yasa takuma tambayan shi still shirun yakumayi ba amsa hakan yasa tayi tunanin tashi tabashiguri domin atunaninta maybe hanlin nasane na miskilanci yamotsa , amma ayanda taganshi yanzu kamar Wanda bashida cikakkiyar lapia saboda yanayinsa gaba kidaya yanuna hakan gashi yayi shiru baya magana balle tasan abinda ke damunshi, can gefe takalla inda wayansa keta faman ruri saman bed sekuma ta maida kallonta gareshi shiru bai motsa ba baikuma sake bude idoba se ajiyar zuciya dataji yana saukewa , gaba kidaya tagama tsorita anya papan aheel kalau yake kuwa ? gashi haryanzu kiran phone dinshi aketayi ba adenaba da alamar mekiran ya k'agu , Ahankali Nisha ta isa ga bed din tasa hanu ta dauki wayar daga fiskar wayan taga maikiran sunan doctor fu'ad ya baiyana jikin screen phone din , nan Nisha ta fahimci yau ana duba file din ajmal that means bashida lapia kenan Nisha karisawa tayi tareda wayar inda ajmal take kwance taduka kusa dashi tana fadi'n," ga phone dinka anata kira , halwayude bai kumace mata kalaba idonsa arintse se red lip dinsa daketa faman bari yana motsi, " Allah sarki maybe yanajin jiki sosaine da hartayi tunanin daga masa wayar tafadawa doctor fu'ad halinda ta iske ajmal aciki to amma wayakaita wannan karan banin dan haka seta ajiye wayar agefensa tana fadi'n," sannu bari naje nafadawa su hajia azo akaika asibiti Nisha na gama fadi'n haka tamike cikin hanzari, charab taji yariko kasan riganta cikin sauri Nisha tajuyo takalleshi still idonsa a rufe se bakinsa dayaketa kokarin motsawa yanaso yace wani abin , Nisha dawowa tayi kusa dashi tasunkuyu tana kallonshi,tana kuma kallon lips dinsa meyakeson fadi" Help me! abunda taji yace kenan slowly araunace Nisha tashiga tambayanshi," wani abun kakesone kafin takomacewa wani abu sejitayi yace ," d'agani ! dan tsaro ido Nisha tayi tana kallonshi kafintace ," indagaka zuwa ina ? " Bed kawai taji yakuma fadi yana mai sake rungume pillow jikinsa da alamar sanyi yakeji sosai , kallonshi Nisha tashigayi sama da kasa yanzu inba neman magana irin na papan aheel ba ina ita ina iya dagashi , gaba kidayanta in aka hadata guri guda bata wuce lumansa dayaba ga tsayi gajiki tasan ba karamin nauyi zaiyiba to amma yazatayi tunda ya nemi taimakonta dole ta taimaka mishi yaka karfinta , dab dashi taje takuma tsugunawa ta dan janye pillow dinda yarungume ita kanta pillow seda tayi dumi saboda zafin jikin ajmal, dan koda ta matso dab dashi numfashinda yake fitarwa shima dumine jikinsa yayi zafi sosai, da ganan Nisha shiga taimaka mishi wajan tashin takamo hand dinshi tadaura saman shoulder dinta dakyar da sidin goshi tareda taimakonsa cikin karfin hali suka samu daman mikewa , sede koda suka tashi taku daya zuwa biyu suka shigayin tangal tangal da juna ajmal karfenshi ya gaza because jikinsa ba kwari sosai bayajin karfi ajikinsa jikinsa duk amace yake haka Nisha taji yasake mata ragaman jikinsa gaba daya duk yanda Nisha tayi kokarin tallafoshi amma se jikake luuu ajmal na kokarin faduwa aiko cikin sauri da fargaban faduwar tasa Nisha taja hanusa da karfi suka fada saman bed tare kamar kifan mazar k'waila haka suka kife ruf ajmal yarufe Nisha da faffadan k'irjinsa ko burbud'inta ba agani, wani dugun numfashi ajmal yashiga saukewa jinshi saman lallausan bed din shi zamu iyacewa gaba daya ajmal baya cikin sense dinshi Sam yamance yana kwance kan halittan da adam , itakuwa Nisha tunda suka kife takasa motsi se zazzare ido tashigayi face dintama ba agani balle hancinta yashaki numfashi taririn zafin jikin ajmal sebugunta yake gashi bayida niyar dagata hala ko suma yayi taji shiru bai dagataba bugun heart dinshi da yanayin yanda yake sauke ajiyar zuciya duk tana iyaji , shikuwa mutumin jin dumin jikin Nisha yabashi wani yanayi mai dadi da kozari ajikinsa yasa yashiga sake tattarota jikinsa yarungume kamar yanda yasaba rungume pillownsa jinwani wawan runguma da ajmal yamatane yasa idanunta suka fito waje tsabar tsoro dakidima Nisha tasaki wani kara tana fadi'n," Wayyo Allah wayyo ummana zaikashenii.., tar ajmal yabude ido jin muryan Nisha datake sumbatu, cikin zafin nama dakarfin hali ajmal ya kauce gefe cikin sauri yasa hand yadafe goshinsa face dinsa yana kallon sama yarintsa idonshi, Nisha najin kaucewan ajmal tayi hanzarin zamowa daga bed din tana sauke ajiyar zuciya tareda tattaro numfashin ta dake kokarin tsayawa hanu takai tadauki mayafinta dake saman bed din Wanda yafice daga kanta tamaidashi mazauninsa , sidi sidi tasuma kokarin barin bedroom din kanta asunkuye hartazo bakin door tajiyu takai kallonta gareshi, lokacin harya yasan gyara kwanciyarshi yakai hannu yaja blanket yarufo jikinshi , Nisha juyawa tayi tafice daga bedroom din ajmal yabi bayanta da kallo akunyace yarasa wani irin zazzabine yarufeshi haka da har yakasa control kanshi har seda yanemi taimako, rintse ido yakumayi gashide yarufe jikinsa da blanket but baisamu irin relief dinda yasamu dazu da yarungume Nisha ba amatsayin pillow shine mai wannan dumi me dadinba dan mintunan daya samu yayi ajikinta har yafara jin saukin abunda ke damunshi, gaba daya ji yayi ransa yadagule masa yarasa meke masa dadi , Nisha kuwa tana fitowa daga bedroom din tanufo downstairs gudu gudu sauri sauri haka take sakkowa idonta duk sun fito waje tsabar o, tana gama sakkowa taja ta tsaya ganin doctor fu'ad zaune bisa kujeran parlourn yanata faman Kiran line din ajmal, ganin sakkowan Nisha arikece yasa hankalin doctor fu'ad dawowaa gareta wanda yasashi mikewa yashiga yimata murmushi, itama murmushin tashiga kirkirowa tana shafa gefen wuyanta daga nan tashiga dagawa doctor fu'ad gaisuwa, cikin fara'a ya amsa da mamakin yanda yariyar ta canza kyanta yagara baiyana dan da ace baisan tabama ba lallai yace yataba ganin taba ," mutuminfa nakirashi bai daukaba doctor fu'ad ya tambaya," yana bedroom din shi Nisha ta bashi amsa asanyaye," Alright barinaje naduashi doctor fu'ad na gama fadi'n haka yanufi upstairs tareda akwatin agajinsa yana kuma waiwayen kallon Nisha yarinyar akwai kyau da kwarjini ba amagana gurin yarinyar ga hankalin da nitsuwa ga kuma shiga zuci, yana isa bakin door din yatura door din yakarisa shiga bakinsa dauke da sallama yanda Nisha tafita tabarshi haka doctor fu'ad yazo ya taddashi idonsa arintse kamar mai bacci, ajmal jin bude door anshigo yasashi bude ido ahankali ganin doctor fu'ad tsaye kansa yasashi kara bude idon dakyau yana kokarin gyara zama doctor fu'ad dakanshi ya taimaka masa wajan gyara masa zamar ganin cewa yau abokin nashi jikin ba kwari sosai, " sannu boss yajikin ?doctor fu'ad yafad'i tareda duba yanayin zafin jikinshi , " tunyaushe kake fama da zazzabin maizafi haka? doctor fu'ad yakuma tambaya, Dan numfasawa ajmal yayi cikin cool voice yake fadi'n " Problem din da kasanine ya tasomin after that bayan sallahn asuba zazzabi yabiyo baya , " meye amfanin pills in problem din yatasu meyasa kakeson wasa da lapian kane ? " I'm tired ajmal yafad'i yana Dan ya mutsa face, Dan murmushi doctor fu'ad yasaki yana kallon abokin nasa wanda ya hade gira yabata fiska " Hmm naji tunda ka gaji dashan pills se ka sauke miskilanci dake kanka kafahimci rayuwar aure kadinga sauke hakkin dake kanka kabar cutar da kanka da bokiyar zamarka duk da nasan matsalar ka da ita amma hakan bazai hana katauyewa kanka hakkiba, so gaskiya inde zaka cigaba da cutar dakanka haka zanyiwa Daddy da ammi bayani Dan bazan tsaya insa maka ido kana kokarin cutar da lapiyar kaba , kana daya daga cikin maza masu bukata over so kama tayi katafiyar da lapiyar ka yanda yakama karka tsaya cutar da kanka because wannan problem din bakaramin effect garetaba lokaci daya zaiyi affecting naka ba tareda ka ankara ko kashirya masaba so you have to be very careful with that issue ajmal shiru yayi yana sauraron zantukan doctor fu'ad duk da ba yau yasaba jinsuba yasaba tunatar dashi duk lokacin da suka kasance tare shima duk yarasa meke damunshi , idan yace baya bukatan mace yayi karya to amma feelings akan matarshine Sam bayida ita kwata kwata bayajinta aransa balle yaji shaawar neman wani abu daga gareta , some times itake bibiyanshi tana shishshige masa wani lokacin yabiye mata wani time dinkuma inta dameshi haka zaizame yafice yabata guri , duk da wani lokacin yakanso yiwa kansa fada Dan yasan ba karamin cutar da ita yakeba baya bata kulawar da tadace , to amma ya zaiyi rayuwarsace tazu da haka amma yana fatan canzawa , sauke ajiyar zuciya yayi yana kallon doctor fu'ad wanda ya mike tsaye yabude akwatin agajinsa ya zaro allura seda yayi arranging din alluran kafin ya kalli abokin nasa yana fadi'n," Allura zan maka wanda zazzabin zai sauka daga haka yanufoshi ba musu ya gara yamasa alluran daga bisani yakuma dauko daya alluran yakalli ajmal yace wannan kuma alluran baccine zan maka because kanada bukatan kahuta sosai nasan jiya baka iya bacciba , shide ajmal binsa yake da ido bayacewa komai harya gama alluransa ya kuma ya tsaya yana fadi'n," Zuwa anjima bacci zai iya daukanka kafin doctor fu'ad yagama ida zancensa seji sukayi anturo door anshigo Nisha ne tafe bakinta dauke da sallama tashigo hanunta dauke da try din abinci tanufi table din tsakiyar dakin ta ajiye daga bisani takai hanu tadauki cup din dake bisa saman try din Wanda ta hadowa ajmal hot coffee din daya saba sha yakeso especially yau datake tunanin baisa komai acikinsaba saboda rashin lapiyan da yatashi, dashi , gabaki daya zuba mata ido sukayi barinma ace doctor fu'ad yakalleta yakalli ajmal wanda ya zuba mata namujiya yana kallonta gaba daya itama Nisha setaji wani irin nauyin ganin irin kallon da suke mata , " am dama coffee na hadu maka kokanada bukata Nisha tafadi muryarta harsakewa yake harta suma kokarin kasa kasa da hannuta ganin bai karba cikin sauri doctor fu'ad ya amsa yana fadi'n," sannu da kokari sister kamar kinda abunda yake da bukata kenan doctor fu'ad yafad'i yana mata kataccen murmushi, itama dan murmushin tayi jiki asanyaye takalli ajmal wanda yasuma lumlumshi ido allura yasuma ratsashi daga bisani tamaida kallonta ga doctor fu'ad wanda keta zuba murmushi kamar gonar auduga kafin tajuya tafice tabasu gari , doctor fu'ad naganin fitanta yajiyu yakalli ajmal wanda ya lumshe ido bacci ya fara cinye idonshi doctor fu'ad cup din coffee ya mayar ya ajiye bisa table ya kai hanu yadauki akwatin agajinsa daga nan yasuma kokarin ficewa ganin mutumin nasa yasamu bacci seda yarage masa hasken dakin kafin doctor fu'ad yasamu daman ficewa daga bedroom din yajanyo masa door din yarufe , yana fitowa daga side ajmal yashiga motarshi mai gadi yabude masa geat yafice yaso yashiga sugaisa dasu hajia but saurin dayake bazai bari yakarisa cikin gidan ba yabari sewani lokacin da ya ware na musamman, yaumade kamar kullum bayan sun kammala dinner dinsu suka koma parlour akashiga taba hira kamar yanda kasaba gabaki daya family da kakalli fiskokinso zaka fahimci suna cikin nishadi da jin dadi , daya yasanar dasu gobe Daddy zaiyi tafiya kamar yanda yafad'i musu abaya , kuma sanar dasu cewa sun zauna da dan uwansa sun tattauna tsakaninsu yakuma sheda musu yanda sukayi sun tsayar da bikinsu fareeda da fadeelah zuwa 2 month masu zuwa inshallah, su hajia ba karamin dadi sukajiba da wannan kyakykyawan labarin ," Masha Allah to allah de yakaimu yasa albarka cikin lamarin , hajia tafadi cikin murna da farin ciki goggo rabi Daddy da ammi sukashiga fadi'n," Amin Banda su reeda da suka shiga kallon junasu suna muzurai farin ciki ba amma magana Nanda dan wasu lokaci suma zasu zama matan aure gurin mazajensu , sede ita hajia karama( fadeelah) ta dan damu because gashide ana maganan tsaida ranar bikinsu but ko saudaya basu zauna da mutumin nata sun tattauna tsakaninsu balle kowannensu yabada labarin yanda yake feeling dan uwansa to amma de tazubawa sarauta Allah ido taga yanda lamarin zai kasance, " Alakullihalin tunda alamaru suntafi yanda yakamata nimade zuwa jibi jirgina zai daga zan koma gida nima, " Au wai tafiyar zakiyi baza kitsaya ayi bikin da keba seki koma gaba daya naga month din bayawa Daddy yafad'i cikin zolaya yana kallon goggo rabi wacce tafiddo ido waje ," wani ! rufamin asiri gida yayi kewata nafa jima anan tun bikin kamal yau kusan wata daya kenan gashi har ansamu rabo inanan ina zaune ai gwara natafi daga baya nakuma dawowa ga baki daya family dariya sukashigayi jin batun goggo rabi sunsa ba karamin miss dinta zasuyiba zayi miss barkwancinta , sun raba dare suna hira har guraren 10 daga bisani sukashiga yiwa juna sallama kowa yanufi makwancinsa , gari yayi shiru gida yayi tsit su nisha duk sunyi shirin bacci sun kwanta , reedane kawai take zaune bisa sofa tana waya da habibinta Wanda take sanar da ita zaizo seda suka kammala wayan tadawo bed takwanta zuciyar ta fari tas farin ciki da annashiwa ba a magana , aka har bacci ya dauketa , Nisha kuwa lumshe ido kawai tayi but bacci yakasa daukanta ta juyanan ta juya can bacci yaki , nan tunanin ta yashiga tuna mata yanayin da suka kasance dazu da ajmal, yanda tayiyo zafin jikin ajmal bisa jikinta time din dasuka fad'i bed dakuma time dinda yarungumota Wanda yasanya tsikar jikinta tashi , mikewa tayi zaune tazauna ," oh Allah koya jikin nasa yanzu ? Phone din ta tadauka ta sakko daga bed din tanufi parlour shiru parlourn ba kowa harta doshi hanyar fita se kuma taja ta tsaya ganin dare yayi sosai gashi tasan wannan uwar tsiwar Heelah tanan batasan ya zasu kareba but tamatsu taga ya yanayin jikin nasa yanzu, haka tanemi guri tazauna tana ta sakawa da kuncewa mafita dayane yazo mata Kiran line din Ajmal kamar yanda yace zata iya kiranshi taji koyanada wani bukatan duk da ba kowani lokaci yake daga kiranba balle yanzu dayake cikin halin rashin lapia, ba wani tsayawa bata time tashiga kiranshi kamar yanda tunanin ta ya bata, Ajmal wanda tashinsa kenan tun bayan da Doctor fu'ad ya masa allura bai farkaba se yanzu 11 cikin yanayin kasala da rashin karfin jiki Ajmal ya yaye blanket din jikinsa saboda zufanda yasuma tsatstsafo masa alamar cewa zazzabin ya sauka adafe yanufi toilet wanka yayi sosai tareda alwala ya fito, sam bai lura da Heelah wacce take kwance saman sofa tamike bacci yayi awungaba da ita se yanzu daya fito idonsa yasauka kanta, kauda kanshi yayi yashiga zaro wata jallabiyar yasanya sannan yashin fida sallayan yashiga jera sallolinda suka biyoshi, seda yamika sallonshi duka sannan ya sallame ya ninke sallayan yadawo saman sofa ya zauna abincin da Nisha takawo masa dazu yashiga budewa because yunwa ya tashi dashi acikinsa, Heelah jin buruntun bude food flakes yasata motsawa tabude ido tana kallonshi," Dear wani irin bacci kayine yau din nan? Heelah tashiga tambayan Ajmal cikin muryan bacci shiru yayi mata yana kallon try din abincin da Heelah tajera a table din Heelah mikewa tayi ta taso tamatsu gareshi tana fadi'n," bari nayi serving dinka nan tashiga kokarin serving dinshi ya tsaya kawai baice mata komaiba gaba daya jiyayi ransa yadagule masa ganin ba abincin da Nisha tashigo masa dashi dazubane wani sabon girkin heelah tayi daban, kallon abincin yashigayi time din da take serving dinshi pepper soup din kazace da soyayyiyar doya da kwai girkin ko kamshi mai dadi baya bayarwa balle kasa ran zaimaka dadi abaki komawa yayi yajin gina da jikin sofa haryaji yunwar da yakejima tatafi, sam bai ji dadin canza masa girki data yiba kusa dashi Heelah tasamu tazauna tadaura hand dinta saman cinyarshi tasuma fadi'n," kayi shiru Dear meya samekane yau? tun bayanda muka dawo nadauko Aheel daga school mukazu muka taddaka kana bacci still har dare yayi sosai haka Aheel da mararin son farkawanka yayi bacci baka bude idoba nima naita yawo akanka shiru baka bude idoba ni harna tsoritama nace ko mutuwa kayi amma sena fahimci kana numfashi meyasameka kaketa wannan baccin haka kalau kake kuwa?" I'm fine yabata amsa a takaice, Alright kasamu kaci abincin ga gashashshiyar cheese burger with sausage pizza danayi mana order time din da muke dawowa nasan kanaso Heelah tafadi tana mai kai hanu tadauki plate din burger da pizza tamika masa ba musu ya gyara yamasa jin order tayi dan haka seya Kai hanu yadauki lallausan cheese burger yakai baki yasuma ci, barina hadu maka coffee daga haka Heelah tamike tafice bajimawa ta dawo dauke da cup din coffee tamika masa ya amsa ba tareda da wani jinkiriba , ataikace burger da pizza kadai ajmal ya iya ci papper soup din baiwuce tabi daya yayiba ya kauda plate din gefe ya Kai hanu yadauki phone din shi, 4 miss call yagani ankirashi koda yaduba yaga 2 miss call from staff and another miss call from Doctor fu'ad phone din nashi a silent take shiyasa ko karanta baijiba idonsa yarintsa ya kuma budewa time yakai idonsa ya duba 12 dan haka seya ajiye wayar baikira kodaya daga cikin suba because dare yayi sosai, mikewa yayi yanufi bed dinshi ya kwanta ya rintsa ido Heelah naganin haka itama tabishi tahaye saman bed din nashi takwanta ajmal yanajin motsinta agefenshi amma yaki bude idon shi harseda yaji takai hanu saman k'irjinsa ta rungimushi tashige jikinsa kamar mai komawa ciki yasa yabude manya manyan idonsa yana kallonta wacce itama shidin take kallo tana masa murmushi, ahankali yadan zame jikinsa ya mirgina yajuya mata baya because kwata kwata baya son farkawanka ita kuma heelah takasa ganewa itade heelah har kullum mamaki ajmal kebata seyaita zille mata yana gudunta se yanzu take kokarin yarda da kalamun faruk nacewa mijinta bayida maraba da mace da yar uwarta mace take rayuwa gashide aido namiji har namiji but abu yake sekace mace anya kalau yake kuwa? ita tarasa gane wannan lamarin ace kullum ita ke nanike dashi yana zille mata se yaga dama tukun yake iya amincewa da ita gaskiya tagaji da abunda Ajmal yake mata na guje mata da yake itade tasan ba kazama bace tana tsafta daide gwargwado to meye matsalar ne? wani kuka takawo tasake harda shashsheka cikin hanzari tamike daga bed din tafice daga bedroom din da gudu tana kuka, Ajmal najin fitan Heelah cikin yanayi kuka yasa ya mike daga kwanciyar da yayi yakoma ya jingina da jikiin bed , shiru yadanyi nawani lokaci yadau tsawan mintuna ahaka kafin yamike yasakko daga bed din yafito daga bedroom din shima , bedroom din aheel yanufa yana zuwa yatura door din yashiga, kwance yasamu Dan nasa yarungume wata big teddy bear yana ta baccinsa cikin kwanciyar hankali karisawa yayi yazauna gefen gadon yashafo gefen fiskan dan nasa yanajin sonsa da kwanarsa yana kara shiganshi, daga nan kuma yamike ya gyara masa rufowan blanket din daga bisani yarage masa hasken light din bedroom din yarufo masa door ɗin , bedroom din heelah ajmal ya nufa yana shiga yasameta tagama kukanta tahakura har bacci barawo yasaceta gaba daya jiyayi ba dadi tabashi tausayi , duk da bayajin karfi ajikinsa daniyar rarrashinta yazo ya kuma bata abunda tanema to ganin cewa tayi bacci yasa ya gyaleta yakashe musu light din dakin ya haye saman bed dinta ya kwanta tabayanta ya janyu musu blanket yarufe su daga haka yarintsa ido, bajimawa shima bacci yayi awungaba da shi, tun bayanda Nisha tayi kiran ajmal a phone kusan sau 2 baiyi picking ba yasa ta hakura dasake kira takuma bedroom din su takwanta cikin yanayi na sanyin jiki da rashin jin dadi, dakuma kulla aniyar gobe da safe zataje taga yanayin jikin nasa __________________________________ washe gari da safe 8:00 Nisha tayi wankanta tashirya cikin shirinta me kyau kananun kaya riga t shirt mai dogon hanu pink color mai laushi tana dauke da adon me alamar heart agaban rigar , se dogon skirt black se hulan dake kanta shima black tayi matukar kyau da ita fitowa tayi daga bedroom din tabarsu fadeelah da reeda da suketa baccinsu kamar yanda suka saba because dama su basu cika tashin safe dawuriba inba school suke dashiba suna sallahn asuba suke komawa sukwanta bacci, direct side din shi tanufa seda suka gaisa da securityn dake tsaye wajan kamar yanda suka saba gaisuwa yabude mata door din tashiga, koda tashigo parlourn azaune ta iske heelah bisa sofa da bowl din cornflakes tana sha gefe kuwa saman table plate ne dauke da kayan snacks tana ci tadaura daya kan daya tana kallon tv jin motsin shigowar Nisha yasa tamaida hankalinta gareta , gamida hararota yayinda take karisowa cikin parlourn," barka da safiya abunda Nisha tafad'i kenan kanta kasa tana kokarin karisawa da nufin tafiya kitchen," Hee uwar iyayi dakata! Heelah tafad'i tana wurgawa Nisha harara, Nisha tsayawa tayi tana kallonta ba tareda tace komai ba, mikewa heelah tayi tana kallon Nisha sama da kasa kafin ta tabe baki tana fadi'n," yau uban gidan naki baya bukatan komai already yayi breakfast dinshi yayi fitarsa but zaki iya shiga kitchen akwai wasu wanke wanken da ban iyayiba kihada da wadannan plate da bowl din kitafi dasu daga haka Heelah takuma watsawa Nisha wani hararan kafin tamatsa daga wajan tanufi upstairs tabar Nisha tsaye awajan tana binta da kallo tareda takaici umarni da take bata hala yar aikinta takeson maida ita , Nisha hartayi niyar barin parlourn sekuma tafasa takai hanu tadauki kayan tarkacen da Heelah tayi amfani dasu tanufi kitchen, tunda tashiga kitchen din take karewa gurin kallon ganin yanda akayi kaca kace dashi ga tarkacen wanke wanke da heelah ta tarashi agurin bata iya wankesuba har kullum Nisha mamakin Heelah take da irin lalacin da takedashi amatsayin ta na mace kwata kwata ba tsabtace muhalli ba karamin fama papan Aheel yake da Heelah, bawani bata time Nisha tashiga kimtsa kitchen duk wani abunda kitchen din dake bukata Nisha seda ta mishi ta gyara ta tsaftace, tana kammalawa Nisha tafito daga kitchen din tana yarfe zufar face dinta because ba karamin gajiya tayiba , daidai time din da aka turo door din a parlourn, Ajmal ne yashigo tareda kamal Wanda suka dawo daga raka Daddy airport, suna tafe cike da nishadi kamal ganin Nisha cikin parlourn Ajmal se raba ido take ga zufa duk ya wanke mata face se yashiga mamakin ganinta ita nan suka karisa shigowa cikikn parlourn suka zauna bisa kujera still kamal se kallon Nisha take shikuwa Ajmal kamar baima san da tsayuwarta jikin parlourn ba Nisha matsowa tayi tashiga daga musu gaisuwa kamal yane ya amsa da ganan Nisha tashiga tambayan Ajmal ya jikinsa kansa sunkuye hankalinsa yana kan phone dinsa ya amsa mata da fadi'n," Alhamdulillaha! ba tareda ya kalli inda takeba dan tabe baki Nisha da mamakin kamar ba ita yanemi taimako gurin taba har numfashi fashinta yaso tsayawa sobada shi amma yanzu tana tab bayarshi yajiki kamar bazai amsaba balle ya dago ya kalli inda tak yanzu da lapia tasamu za acigaba da halin Nisha sid'i sid'i Nisha tasamu tafice daga parlourn kamal se waiwayanta yake harta fice, " Bro meyasameka? Kamal ya tambayi y'ay'an nasu cikin nuna kulawa da damuwa, dagowa ajmal yayi ya kalli kanin nasa tareda sakar masa murmushi yana fadi'n, "Nothing wani dan zazzabi nayi but now I'm okay, cikin sanyin murya tareda sauke ajiyar zuciya Kamal yace ," Masha Allah , Allah yakara lpy bro " Amin! Ajmal ya amsa fiskarsa dauke da murmushi ," yaushe zaka koma office kaci gaba da aiki ko baka gama hutawaba ? Ajmal ya tambaya yana kallon Kamal, dan shafo gefen wuyansa Kamal yayi yana yar murmushi yace ," am da yau nakeda niyar komawa but nabari se zuwa gobe because akwai dan Shirin da nake kamal yabashi amsa cikin girmamawa ," That's good daga haka Ajmal yamaida hankalinsa ga phone din shi but ya lura da yanda kamal yaketa muzurai kamar bakinsa yana bukatan cewa wani abun se wani nuke nuke yake ," Eheem ina jinka kace kanaso muyi wata magana but kayi shiru kuma what happened? Ajmal ya kuma tambayan Kamal yayinda ya ajiye phone din shi saman table din parlourn yana kallon Kamal tareda sauraron shi, Kamal bude baki yayi daniyar magana but jin rurin karan wayan Ajmal yasashi dakatawa daga abunda yakeson fadi'n, Ajmal hanu yakai yadauki wayan nashi ba tareda ya daga Kiran ba ya kalli Kamal yana fadi'n," I'm very sorry zan fita office yanzu but zan nemeka any time , " Okay bro kamal yafad'i because dama maganar dayazo dashi nauyin fadawa yayan nasa yake dan haka Kamal yayiwa Ajmal sallama yafice daga parlourn, Ajmal yana ganin fitar Kamal shima ya mike yanufi upstairs bedroom din shi yashiga daga nan yashiga cire kayan jikinsa yanemi towel yadaura a waist dinshi yanufi toilet wanka yayi yafito yasuma shiryawa cikin shiga maikyau black suit yayi kyau matuka yasanya black glass da takalmi se wani agogon gold ta hanu daya sanya kyau kan kyau abun ba amagana, fitowa yayi daga bedroom din shi yanufi downstairs daga bisani yafice izuwa haraban gidan parking space yanufa yashiga daya daga cikin motocinsa white color tsadaddiyar hadaddiya abun kallo da ban sha'awa me gadi yana ganin fitowan Ajmal cikin barin jiki ya bude masa geat Ajmal yayiwa motarsa key yasa kai yafiice, Karfe 11:30 Hajia da Goggo rabi dasu Reeda suna zaune parlour wanda tun bayan kammala breakfast dinsu suka yada zango gurin suna dan taba hirarsu da suka saba ," yaude yakamata naje saloon din nan da shopping kafin tafiyata gobe Hajia karama (Fadeelah) fatan zakimin rakiya , Goggo rabi ta tambaya tana kallon Fadeelah dake washe baki gami da faɗi'n," Eh Goggo rabi zan miki rakiya Fadeelah tafad'i tana kallon Reeda gamida yimata g'walo Banda Nisha datayi sunkui da kai tana murmushi , Fadeelah da Reeda suna kaunar fita yawo because basu cika fitaba daga gida se makarnta barin ma yanzu dasuke hutu ba zuwa school duk se zaman gidan ya ishe " Goggo rabi dukansu uku taso suyi fitan tare zaifi armashi but ganin cewa Nisha da igiya uku akanta baikamata sufitaba ba tareda sanin mijin taba , to gwara sutafi da Fadeelah Reeda ta Taya Nisha debe kewa kar abarta shiru ita kadai, itama taban garan Nisha da Goggo rabi cewa tayi tare zasuje amma ganin cewa tacanza zabi se bata damuba , Hajia itama tasan dalilin dayasa Goggo rabi tayi hakan amma da tare duk yakamata sufita tunda dukansu suna shaawar fitan, " Allah sarki yarinyar batasan nauyin da ya rataya wuyan taba wannan duk ninayi sanadin hakan amma nan ba da jimawaba zata San nauyin dake kanta duk da batasan ya Nisha zata kalli lamarin takuma karbeshi batareda wani damuwaba duk da tasan hankali da nitsuwa irin na yarinyar, Hajia ke maganan zuci yayinda take kallon Nisha cikin tausayawa da hukuncin da tayanke ba tareda tayi la akari da wani abunda zaije ya dawoba , tana matukar kaunar yarinyar tana kuma jinta sosai cikin zuciyar ta bazataso tayi wani abunda zaicutar da itaba, sunyi firansu sosai gabatuwan sallahn azahar ne yasa duk suka Mike suka nufi muhalinsu domin gabatar da sallah , Goggo rabi da Hajia suka nufi sashinsu sukuma yan matan suka nufi bedroom dinsu' bayan sun idar da sallansu suka daura aniyar zuwa side din Kamal gurin Auntyn su Nabilah yar uwa kuma kawarsu suna jin dadin kasan cewa da ita ba kaman Heelah ba da ko kallon side din ta basayi balle suji sha' awan zuwa duk da ita din yar uwarsuce tajini but halinta yasha ban ban da nasu because Heelah akwai bakin hali da rashin kunya shiyasa basa shiri balle suje inda take " Ke bazaki biyomu muje firan bane gurin Aunty Nabilah, su Reeda ke tambayan Nisha wacce take zaune bisa bakin bed tana kallonsu," A'a ni bacci nakeji kuje kawai, Nisha ta basu amsa , basu takura mataba because sunsan kwanan zancen dan haka suka fice daga bedroom din cikin rawar jiki sukabar Nisha wacce ta gyara kwanciyar ta bisa saman bed din , nanfa tafara g'yan'gya dawa bacci yanason cinye idonta Karan shigowar message ne yasa tabude ido da kamar bazata duba wayarba sekuma ta janyota tashiga dubawa , tsulum tamike tazauna ganin message din Ajmal ne Wanda yake bata umarni tashirya masa lunch hulan kanta tazara da sauri Wanda yafice daga saman kanta tamai dashi mazauninsa, dan turo baki tayi ita batasun komawa side din shi ta tarar da wacce masi faffiyar matar tashi tunda matarshi tana nan mai zai hana ta mishi lunch din kamar yanda tamasa breakfast , mikewa tasomayi daniyar tafita daga bedroom din ganin shigowar Kamal yasa taja ta tsaya tana kallonshi da mamakin me yakawoshi ," yade wannan kallonfa? Kamal ya tambaya yayinda yake karisowa yanemi sofa ya zauna , still de Nisha kallonshi take ba tareda ta motsaba kotace wani abinba ," sisy kizauna mana wata magana nazo muyi Kamal yafad'i yana kallon Nisha wacce tadaga kafa ahankali takoma tazauna bakin bed tana kallonshi, murmushi Kamal ya sake yana kuma fadi'n," Ko kina wani uzurinne nazo nakatseki , murmushin itama ta kwakwalo tana faɗi'n," A'a bakomai, " Alright barinaje kan batun da yakawone ba tareda bata lokaciba, " yarda da amincewarki nakeda bukata, dan zaro ido waje Nisha tayi tana faɗi'n," Amincewata akan me ya Kamal,? dan gyara zama Kamal yayi hankali kwance yana mata murmushin kashe zuci yace," tunbayan da nabada labari abaya gaban Nabilah friends da sisters dina yanda sonki da kaunar ki yadinga d'a wainiya dani har kawo yanzu damuke gida daya dake but ta ban garanki bansan ya kika dauki soyayya taba inaso naji daga gareki ya matsayin kaunata agareki ? yakike feeling soyayya ta cikin heart dinki? shin kina sona kamar yada nabai yana miki ko aa? inason sani wannan shine tambayoyin da Kamal yajerowa Nisha Wanda yasatayin shiru tana kallon kasa kamar mai nazarin wani abu, " sisy what are you silent kamata yayi ki amsamin tambayoyina ," Ya Kamal tambayarka bata da amsa Nisha tafad'i ba tareda tadago sun hada idoba, "means bak'ya sona? nikaɗai nake ta dakon soyayya? shiru Nisha tayi batace kalaba bata kuma ɗago kai takalleshi ba , shima Kamal shirun yayi tareda sunnar da Kai kasa tsawon wasu mintuna kafin ya ɗago kai yakuma kallonta idonsa duk yayi jawar kamar mai Shirin yin kuka , mikewa yayi jiki ba kwari yasuma tafiya asukwane kamar wanda aka zarewa lakan jiki, wani dariya da Nisha tafashe dashine yasa Kamal dakatawa daga tafiyar dayake yajuyo ahankali yana kallonta, ganin yanda Kamal yajiyo yana kallontane yasa ta kai hanu takulle bakinta tana me cigaba da dariyan kasa kasa tareda mikewa daga zaunen da take tashiga karisowa inda yake tsaye seda tawurga masa wani murmushi kafin tace, "tafiya zakayi ba tareda kaji mai zan faɗi' ba" "mekikeson na tsaya naji bayan kince ba k'yasona , still kin ɓige dayimin dariya like kinga wani mahaukacin" Kamal yabata amsa tareda hararota yana mai kauda kai gefe, murmushi Nisha takuma yi tana fadi'n "ya Kamal yaushe kaji nace bana sonka?" Nisha takuma tambaya still ta tsareshi da ido , rintsa ido Kamal yayi ya bude tareda sauke ajiyar zuciya ahankali kafin ya jiyo da face dinsa suna facing juna yace "I'm hearing you talk me kinasona kamar yanda nakesonki ko a'a ?" Kamal yakuma tambayan Nisha yaname tsareta da ido , dan juya mishi baya Nisha tayi kafin tashiga fadi'n, " Ya Kamal wata macece zaka mata tayin soyayya taki amsa , tun ranar da muka soma haduwa nayabawa hankalinka duba da yanda ka durkusa kana bamu hakuri bisa rashin hankali da dan uwanka yamana duk da ba laifin ka bane haka kuma baka sareba kabimu har lnda muke kaci gaba da bamu hakuri, juyowa tayi takalli Kamal wanda ya tsura mata ido yana kallonta yayinda take maganar kafin taci gaba da faɗin " Ya Kamal baka da girman Kai zuciyar ka kyakykyawa ce kuma kana da tausayi duk da ilartar da kai danayi cikin rashin sani sana diyar zalunci irin na dan uwanka hakan bai hana nazo da damuwata gareka ka kasa kashare min hawayeba a lokacin da narasa me taimakona ,amm tunani na....... "shiiiii Kamal ya katsare ta daga surutan da take tafaman kwararo masa " har yanzu banji amsar da nakeson jiba daga gareki do you love me or not" Kamal yasake jefo mata tambaya, dukar dakai kasa Nisha tayi kafin tace "Ina sonka ya Kamal but Aunty Nabilah.., cikin hanzari Kamal ya dakatar da ita daga maganar da takeson yi yashiga fadi'n, "karkisa wani tunani game da ita kibar komai hanuna , kwai abunda zan gaya miki shine bana tsayawa buye abunda nakeso dan haka zan sanar dasu Ammi cewa muna soyayya kuma aure zamuyi banason bata time, dan zaro ido Nisha tayi tana faɗin, " da sauri haka ? Ya Kamal yaushe ma akayi auren naku gaskiya idan akayiwa Aunty Nabilah haka ba amata adalciba maganar aure tsakanina dakai yayi sauri gaskiya please ajin kirta, " I'm sorry bazan bari ina kallon muna rayuwa gida daya ace nakasa mallakankiba , bazan iya jiran dugun time ba , karki mantafa nina mijine , mijin mata 4 kuma Allah ne ya bani wannan daman to me Zan tsaya jira nifa ko daga yau zuwa gobe nace ina bukatan Karin aure ba mecemin a'a ko ayi kokarin dakatar dani because sunnace nakeson rayawa kinga kuma bamaija da sunnar annabi (s .a .w ), da ace tun farko kowa yasan tsakaninmu kuma nasan matsayin soyayyata a gareki dayanzu matsayin matata kike, dan haka banaso kisawa kanki wani damuwa kibarni zanji da komai , shiru Nisha tayi jikinta duk ya mutu sam bataji dadin hakan ba 'yanzu yanda Aunty Nabilah take cikin halin laulayin nan taya zaifara tinkaransu da wani zancen aure' jin shafo gefen face dinta da Kamal yayine yasa ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi ɗago kai tayi tana kallonshi yayinda yake tazuba mata murmushi, "Am dama akwai wani tambaya da nakeson nami, but inkin bani dama kuma ban takurakiba, kan Neeshi kasa taɗan girgiza masa kai alamar bai takurataba , bude bakin Kamal keda wuya wajan kwararowa Neesha tambaya phone dishi datashiga yin rori yasa ya dakata da maganar yashiga zaro wayar cikin pocket din wandonsa ganin mekiran da kuma mahimmancin shi yasa yadauki kiran ya kara akunne , Nisha bataji mai ake faɗa daga cikin wayarba seji tayi Kamal yace "I'm coming" daga haka yakatse wayar yakalli nisha daketa faman kallonshi yayinda yake wayar "Excuse me bari naje nadawo so zamuyi magana back" daga haka Kamal yafice ahanzarce ya bar nisha tsaye tsakiyar dakin , daker ta tattaro nitsuwarta tasamu daman daga kafarta tabi bayanshi, Nisha naganin time din da Kamal yashiga motarshi ya mata key mai gadi yabude masa geat yafice, daga itama tasamu daman karisawa side din Ajmal, bata kaiga karisa shiga tsakiyar parlourn ba taci karo da Heelah dake sakkowa daga upstairs taci uwar ado tarayo mayafi gefe guda tareda back dinta se hararo Nisha take yayin da take sakkowan , kan Nisha kasa bata kuma dagowa takalli Heelah ba , itakuwa Heelah still harran Nisha take bata daina ba seda takariso gefe da ita tazuba uban tsaki tareda wani dugun kwafa takalli Nisha tana fadi'n "mayya" kafin takuma hararnta tashige tayi ficewarta tabar Nisha agurin kai sunkuye , girgiza Kai Nisha tashiga yi ita tarasa wani kaddarace takawota gidan nan har takasan ce ak'ark'ashin bayan Allah nan gaskiya takaji da wannan wula kancin dan haka tana dab dayiwa tufkar hanci, kitchen din Nisha takarisa shiga tashiga hadawa Ajmal dinner kamar yanda ya bukata , tadau lokaci tana aikin kafin daga bisani tasamu daman kammalawa but har tagama bata ji motsin dawowar shiba gashi haryamma tayi amma shiru kakeji nan tasuma kokarin jira masa abincin bisa dining table kamar yanda tasaba tanemigu tazauna tana jiran shiguwarshi, hankalinta ta mayar kan TV dayake kunne yana channel din boolywood ana gabatar dawani drama na larabci duk da bajin labcin takeba haka tazubawa TV ido tana kallon yanda aketa zuba soyayya ciki gwani burgewa da ban sha'awa Nisha tayi nisa cikin kallon soyayya , jidatayi anfadu saman cinyartane yasa cikin yanayin tsoro da firgici tashiga fida ido tana kallonshi cikin kayan uniform yanata washe mata bakin nan nashi daya yasaba , "Sorry Aunty nabaki tsoro ko ?" murmushi Nisha tayi tana sauke ajiyar zuciya tace, "Aa akomai" daga ido tayi takalli bayanshi but bata ga kowaba jin motsin mutum tabayanta yasa tajuya bayan Ajmal ta kallah wanda tuni ya haura upstairs yana shirin nufa bedroom din shi, kallonta tamayar kan Aheel Wanda haryanzu washe mata baki yake cike da murna da farin ciki, kaje sauya kayanka kadawo kaci abinci , Nisha tafad'i gamida Kai hanu tana kokarin karban lunchbox din shi takarisa dashi kitchen, but sai taga Aheel yanuke shoulder ashagwabe yake fadi'n, "Aunty muje kitayani , like father like son shima komai se ammsa , dan karya wuya Nisha tayi tana fadi'n Oya muje to nan takama hanun Aheel suka haura sama suka nufi bedroom din Aheel, sam Neesha bata gajiya da kallon gwanin sha'awa ga kyalekyale da akayiwa dakin Wanda zai nishaadan tar da yara ga teddy iri da kala kyan wasa bedroom din Aheel ba a magana Nisha seda tasa Aheel yayi wanka duk da bawai ya iya wankan sosai bane yadai dauraye jikin sane kwai yafito, Nisha tashiga kimtsa shi, ta tayashi ya sanya kyawawan kayanshi marasa nauyi Wanda bazai takuraba, daga nan ta janyo hanun shi suka nufo downstairs, koda suka kariso Nisha bataga Ajmal cikin parlourn ba alamar cewa haryanzu bai fitoba kenan, dining table din takarsa da Aheel tazaunar dashi tashiga serving dinshi da daddadan delicious food dinta, vegetables cuscus with liver soup and macaroni salad shine abinda Nisha tayiwa Aheel serving sedan wani madaidaicin bowl wanda ta zuba masa pepper soup chicken curry mai dadin gaske, duk da tasan Aheel bawai wani cin abinci yake sosaiba amma tanaso kowanne yazamu yasa masa albarka, gefe kuma tashiga tsiyaya masa sassanyan mango smoothie juice, ganin yanda Aheel yake bin abincin da kallo yasa Nisha tasake murmushi gamida shafo gefen face din shi tana fadi'n "naba abakine, aikuwa kamar jira yake Aheel yashiga daga mata Kai alamar " eh" Nisha kujera taja tazauna tana facing dinshi tashiga dibo abincin cikin spoon tana kaiwa bakin Aheel yana ci, cikin matsuwa take bashi abincin yanaci yana mata surutan nan nashi daya yasaba, "Aunty abincin nan akwai dadi sosai kece kika dafa? " Eh mana saboda kaima nayi Nisha tabashi amsa tana murmushi, dan tabe baki Nisha taga Aheel yayi yana fadi'n "Mommy na bata iya irin wannan abincin mai dadin ba but zaki koya mata? Aheel ya tambaya yana kallon Nisha, " shiii !be quiet kaci abincin ka " Nisha tafad'i gamida shafa bayansa, daga bisani Aheel yashiga kaɗa kai rin nayarinta yakai hanu ya dauki cinyar kaza yakai baki ya suma cin yana Santi, har wayaude zuwa yanzu shiru kakeji ba motsin Ajmal ba kuma alamar zai sakko har Aheel ya kammala nashi cin abincin papanshi bai sakkoba gashi har magarib ya gabato kai dan haka yasa Nisha taja hanun Aheel suka fice daga parlourn, Nisha tana isa bedroom dinsu Reeda kaiɗai tagani cikin bedroom din alamar daya batacewa Fadeelah suntafi saloon din da Goggo rabi Reeda jin motsin shigowar su yasa tadago kai tana kallonsu gamida sakar musu murmushi yayinda suke karisowa ciki, da sauri Aheel yasake hanun Nisha yanufi sofa inda Reeda take zaune tana danna waya cikin hanzari Aheel yafada cinyar Reeda tareda fashe mata da kyakykyawan da riyanshi irinta yara " My little yaron k'irk'i antaso daga school anzu acikamu dasu rutu koh? Reeda ta tambayi Aheel yayinda take sakar masa murmushi tana jan dan kyakykyawan dugon hancinsa, k'yelk'yale mata da dariya yayi gamida gyada mata Kai yana kallonta, "Oh no ba dani ba wannan surutan naka sede Aunty Nisha kaga tafiyata ni alwalama zanje nayi oya ga phone dina kayiwa Angela wanka kayi feeding nata kafin nadawo Reeda tafad'i gamida zame jikinta daga na Aheel tamike masa phone dinta because tasan shi masoyin game ne especially game din Angela hanun Aheel har rawa yake wajan amsan wayar yana washe baki, Nisha de kallonsu take tana murmushi har fareeda tashige toilet danyin alwala itakuwa Nisha tamike tadawo kusa da Aheel tazaunar tana kallon yanda yake gudanar da wasan angelan nashi,,.. karfe 9 na dare familyn an hadu cikin kata faren parlourn bayan kammala dinner suka shiga gudanar da fira a tsakaninsu gwanin sha'awa, Ammi Hajia Goggo rabi, tareda yan matan Ammi, gefe ga Kamal tareda muhaiseen Wanda Kamal ya daukoshi daga airport dazu ba Wanda yasan da zuwanshi hatta mom dinsa Goggo rabi batasan da zuwansa ba se ganin shi tayi shima Kamal din muhaiseen kirashin kawai yayi yace gashi ya sauka Kamal yaje ya daukoshi , Aheel dake zaune cinyar Ammi ya nata zuba hamma da alamar bacci cikin idanunsa because duk ya gama yin laushi, " da alamufa yaron nan bacci yakeji naga se g'yan'gya dawa yake gaba kidaya bacci ya kama idonsa" Goggo rabi tafad'i tana kallon Aheel da idonsa sukayi ciki sun kankance, Ammi s hafo gefen face din Aheel tayi tana kallon shi daga bisani takalli Nisha wacce itama hankalinta yake kan Aheel " ya kamata akai little ya kwanta because dare yayi sosai " aiko kafin Ammi tarufe baki Aheel yatashi sukuf dashi yanufi Nisha yasuma kokarin kama hanuta sutafi, bamusu Nisha tabishi suka fice daga parlourn su hajia se murmushi suke tareda cigaba da hiransu , Jim kadan Kamal da muhaiseen suka tashi sukafice daga parlourn suna dan k'usk'us atsakanin su "kije ki gyara bedroom din da yayanku yasauka a shimfuda bedsheets , komai yazama clean" Ammi tafad'i cikin yayi na bada umurni tana kallon Reeda, ba bata lokaci Reeda tashiga fadi'n "to" daga haka tamike tafice , bajimawa suma suka shiga watsewa because sundau tsawon lokaci suna firan, koda Reeda ta isa bedroom din da ya muhaiseen yasauka baya ciki da alamar bai kariso bedroom din ba suna tareda Kamal, bedroom din a tsaftace yake komai fine because dama ba abarin ko ina da datti agidan ko dayaushe anasharewa a tsabtace shi agoge ko ina bedsheet dine kadai ba ashin fidawa se time din da bako ya ziyarci dakin , karisawa Reeda tayi ta bude wardrobe tadauko wani kyakykyawan bedsheet mai taushi tareda blanket tashiga shinfida bedsheet din saman bed daga bisani tadaura blanket saman bedsheet din , tana tsaka da gyaran muhaiseen ya turo door yashigo idonsa yasauka kan Reeda dake kimtsa masa bed nan yashiga sakar mata murmushi tareda karisowa ciki, itama Reeda murmushi tamayar masa tareda maida hankalinta ga abinda take but bata ankaraba seji tayi muhaiseen bisa bayanta yarungumu waist dinta gafi da sakalo face dinsa ta gefen wuyarta yana fadi'n," I miss you very much my pretty gaskiya nayi kewarki dayawa na kagu adaura auramu na daukeki natafi dake , nifa banki gobe ashafa mana fatiha nawuce dakeba , but Daddy yakaimu har 2 month wanda hakqn yamin nisa gaskiya ya muhaiseen yafad'i yayinda yake sake rungumar Reeda a jikinsa yanajin yanda sonta da kaunarta yake sake zama sabo fil cikin zuciyar shi, jin yanda ya muhaiseen ya rungumuta tamakar zai maidata jikinsa yasa gaba daya setaji wani irin yanayin da tunda take arayuwa bata taba jinsaba ga kamshin turarensa mai masifar dadi dayasa takasa janye jikinsa daga nata bata ki sutabbata hakaba har tsawon rayuwa , ba karamin kewarsa takeba itama ganinsa yayiwa idonta tsada se adau tsawon lokaci basuga junaba sede suyiwaya ko video call nan ma se inyana free because kullum cikin busy yake bugu dakari gari ba daya kuma baicika zama kasarba, jin shiru batayi maganaba ta tsaya kamar sak'aguwa yasa yajanye jikinsa tareda juyo da ita but seyaga ta lumshe ido murmushi ya muhaiseen yayi yana fadi'n "Yadai " tareda shafo gefen face dinta, bude ido Reeda tayi dasaure gaba daya tafada duniyar tunani ta mance ida take nan tasuma yar kame kame "Uhm am ba abunda kakeda bukata? Zan iya tafiya ?" " That's means ke bakiyi missing dina ba" muhaiseen ya fadi'n tareda yin baya ya zauna bisa sofa dakin yana kallonta, girgiza Kai Reeda tayi tana fadin "Aa ya muhaiseen meyasa zakace haka?" "gashi kuwa kina fadi'n zaki tafi kibarni cikin kewarki maimakon kizauna kitayani fira har wayewar gari , fito da ido waje Reeda tayi tana fadi'n," " wayewar gari fa kace ? "Eh mana bawani matsala ai Dan munraya dare kina min firan soyayya mai dadi" muhaiseen ya amsa yana mata k'ayataccen murmushi, dariya kawai Reeda tayi gamida tabe baki tana fadi'n " Muk'wana lapia " tana fadi'n haka tajuya zata fice , "ba ki jiba " jin muryan muhaiseen na magana yasa Reeda dakatawa daga fitan da take kokarin yi tajiyo tana kallon shi Wanda ya mike yanufi inda take , kallon kallo sukashiga yiwa juna kafin muhaiseen yadan numfasa ya Kai hanu ya janyo hand din reeda sannan ya sanya dayan hand dinshi bisa pocket dinshi ya zaro wani box dan karami gwani sha'awa wanda ke dauke da kyakykyawan rings na gold mai haske da kyalkyali zoben ya zaro daga box din yasaita yatsar Reeda natsakiya ya sanya mata akwai ya zauna mata damas gwani kyau rings din ba karamin sake fito da kyakykyawan hand dinta tayiba, "I'm sorry pretty wannan karamin kyautace daga gareni but zoben nan yayiwa hand dinki kyau ko mace hand din ki yayiwa rings din kyau, muhaiseen yafad'i gamida murmushi yana kallon Reeda wacce tasake baki ta zaro ido waje yayinda take kallon hand dinta tana juyashi gamida karewa zoben kallon, " wow ! wow!! Ya mu muhaiseen gaskiya rings din nan ya yayi kyau sosai ya burgeni matuka thanks you so much gami da sunbatan zuben tana murmushi farin ciki, " but wannan kyakykyawan sumbatar niyakama ta ayiwa ba zoben ba , dagowa Reeda tayi takalli muhaiseen wanda ya miko mata face dinsa gamida rintsa ido yana mata alamar nuni da yatsansa ta sunbaci kumatunsa aikuwa ba tsammani yaji saukan k'ayataccen kiss bisa kuncinsa saide kafin yabude ido tuni tajuya baya tabude door tafice da saurin, lumshe ido yayi tareda shafa kumatunsa inda ta sumbace shi sauke ajiyar zuciya yayi kafin ya tattaro nitsuwarsa ya shiga cire kayan jikinsa ya sanya towel yanufi toilet wanka yayi sosai daga bisani ya fito ya sanya white jallabiyar sa yanemi saman bed ya kwanata yadau lokaci yana dan tunane tunane face dinsa yana kallon sama sannu ahankali bacci b'arawo ya saceshi, itama Reeda koda takarisa bedroom dinsu tasamu Fadeelah tayi d'aid'ai tana bacci da alamar baccin ta yayi nisa sosai ga wayarta dake gefe saman bedside table yanata kawo hasske alamar Kira but phone din ta sanyashi silent shiyasa baza aji karantaba dan leka phone din reeda tayi domin ganin mai uzurawa da wannan Kiran ganin boyayyiyar number ne wato ( private number) yasa ta share tashiga neman Nisha cikin bedroom din but ba ita ba alamarta ,. 'bade tunda takai Aheel side din su bata dawo ba' Reeda ta tambayi kanta ganin cewa bata da amsa tambayar ta yasa ta d'an tabe baki daga bisani tashiga yin Shirin bacci kafin ta kwanta tareda rungumu hand dinta tana kallon d'an ya tsanta wanda ke sanye da kyakykyawan zoben gold da hubbynta ya yasanya mata yaude da mutukar murna gamida annashuwa cike da tunanin gwarzon masoyin nata bacci yayi awungaba da ita,.......... 'haba Nisha ashe duniya zata iya rudanki ki mance da mahaifinki ? asha akwai rayuwa cikin daula da jin dadi zai iya mantar dake tushenki , Nisha Ina alkhari da kikayimin akan kasance wa da mahaifinki atare dake? ashe zakiya mancewa da abbanki cikin sauki haka? shin kinsan wani irin hali yake ayanzu ? "wakeup! wakeup !!mana yanzu dan fitowar nan da mukayi daga gida harkin kiyi bacci, Fadeelah ke magana yayinda take tashin Nisha daga d'an gajeren baccin da tayi, nan Nisha tashiga zazzare idanu tana kallonsu se zuba ke tsatstsafo mata idonta yayi jawur dashi yayinda zuciyar ta kuma keta maimaita sunan umma because mafarkin datayi da ita yanzu bisa tuhumar da take mata akan abbanta na nauyin da ta daura mata , " Lapia kike kuwa? yanaga kamar arazane kike ko mafarki kikayine? girgiza Kai Nisha tayi tana fadi'n "Aa" "kode bakijin dadine because tunsafe nake ganinki so silent " Reeda tajefo mata tambaya, gyada Kai Nisha tayi tana fadi'n "kaima ked'an ciyo" Nisha ta bawa fareeda amsa cikin kosawa da magana, "Sorry kijira mu a motar bari muje muyi shopping din mudawo but bari na sauke miki glass din motar saboda iska yadinga shigo miki" gyada Kai Nisha takuma yimusu daga nan Reeda ta sauke mata glass din motar because dama itace ke driving dinsu daga suka fice daga motar suka nufi cikin babban plazan suka bar Nisha cikin morta wacce take ta faman sauke ajiyar zuciya idanunta suncika tab da k'walla karo na farko da tayi mafarkin umma wanda ya bata tsoro yakuma farkar da ita daga shagalan da tayi dan haka takudiri aniyar fita daga motar tagudu tashiga duniya neman mahaifinta, fitowa tayi daga motar tareda handbag dinta da phone din ta tasuma tafiya, harta danyi nesa da plaza sekuma taja ta tsaya ganin wani mutum dake tin karota yana gudu yana haki, yana sanye cikin manyan kaya riga da wando but sede kayan sunci ubansu da dotti shikanshi mutumin yayi kura yayi futu futu dashi fiskarshi tayi baki sosai gashin kanshima tayi kura gakuma tacika akansa cunkus ga gemanya gaba daya de kallon daya zaka masa yuwa kaga tsohon mahaukaci , nanfa Nisha cikin tsoro tafarayin baya jikinta har rawa take nan tashaga waige waige da neman inda zatayi tunda da alamar gurin wannan mahaukacin yake yiyuwa, harta juya da gudu zata koma gun motarsu saitaji sautin wannan mutumin yana ihun neman agaji "taimako! taimako jama'!! dan Allah a taimakamu suna bina zasu kamani sucutar dani dan Allah a taimakeni, cak Nisha tatsaya daga kokarin guduwan da take tamaida hankalinta ga mutum dan ganin ina yanufa still gurinta yanufu gadan gadan hakan yasa tarintsa ido gam jiki se bari yake, jin shiru yasa tabude ido bata ganshiba nan tashiga waige waige seda tajuyo bayanta tanganshi ya dukunkune face kanshi da hand dinshi jikinsa se kyarma yake nan tamaida kallonta daga hanyar dataga yafito nan made bakowa bakuma wanda yake binnashi 'to taimakon mai yake nema' jiyuwa tayi takalleshi tashiga tambayan shi," " malam suwaye ke binka bacin banga kowa dake biye dakai ba "? "gasu can suna kuma biyoni" mutumin yabata amsa ba tareda ya dago face dinshiba sake duba hanyar tayi da kyau still de ba k'yallin kowa dan haka Nisha tasauke ajiyar zuciya takalli mutumin ciki da murmushi tace, dago fiskarka ka kalli bakowa dake binka duba kagani, jin abunda tafad'i yasa mutumin cire hand din shiga face dinshi yashiga kyalla ido yana dube dube kafin ya sauke ajiyar zuciya yana dariya yana fadi'n," " Alhamdulillah wallahi natsira sundaina biyoni kasan cewan yanayin gari da hadari sosai nan take ruwa mai karfi ya sakko ganin haka yasa gaba kidayansu suka shiga neman mafaka nan taga mutumin ya watsa da gudu yanufi wata runfa ya shige domin fakewa Nisha itama cikin sauri tabi bayanshi tashige tana rawan sanyi tsayawa tayi tana kallon mutumin yasanya hanu yana taran ruwan yana kaiea baki da alamar yaji k'ishin ruwa seda yasha yakoshi sannan yashiga wanke fiskarshi datayi baki abar tsoro seda ya wanke face dinsa sannan yajiyu yakalli Nisha wacce ke gefe ta zuba masa na mujiya tana kallonshi, kauda kaiyayi yacigaba da wanke gabban jikinshi but jin motsin mutum kusa dashi yasa ya dakata ya kallo inda take idonta cika tab da kallo amma bakinta se murmushi yake yana barin cewa wani abin daker bakinta ya iya furta "Abba?abbana kaine haka" Allah nagode maka Nisha tafad'i yayinda take matsowa gareshi da sauri yaja baya yana kallonta cike da mamaki amma bai iya cewa kalaba ganin haka yasa Nisha sake fadi'n," "Abba baka ganeni bane yarkacefa Nisha"tafad'i tana kuma tinkaroshi da kokarin fadawa jikinsa cikin murna but seyaga yasake ja dabaya 'to ko ta canzane bai iya ganetaba' tashiga tambayan kanta " " Abba fa nice Nisha dinka ka kalleni da kyau nice , gamamakinta setaga ya watsa aguje yashigayin gudu itama cikin sauri tashiga bin bayanshi duk da ruwandq ake gudu yake sosai tamakar yaga wani abin tsoron itama Nishi se karayin saurin take but yamata nisa sosai , wata tsadaddiyar motane taga yaz o yasha gaban Abba aka bude murfin kofar motar aka kutsa abbanta ciki bataga ko suwayeba suka jashi csuka maidakofar suka rufe sukaja motar sukatafi dashi, "Innalilahi wa'ina ilaihi rajuun" Firgit Nisha ta tashi daga mafarkan da tashigayi tana kuma maimaita" inna lillahi wa'ina ilaihi rajuun abbanaaaaaaa!" bedroom din tashiga bi da kallo nan ta ganta wance kan gadon Aheel wanda tun kawoshi yakwanta yashiga rigimar sede su kwanta tare dalilin dayasa ta kwanata a domin ta samu yayi bacci seta sulale ta tafi but se bacci mai nauyi ya dauketa hardasu markin umma da Abba gaskiya mafarkin da tayi da Abbanata da irin halinda takaganshi ba karamin daga mata hankali yayiba, duk da sassanyan AC dake aiko cikin bedroom din but zuba take sosai kallon Aheel tayi wanda ya yabaje yanata sharan baccinsa wayarta tazaro tashiga duba time 4 na asuba zaro ido tayi tasakko daga bed din tanufi downstairs cikin sauri ahanzarce take sakkowa daga benen koda ta karisa sakkowa se tsayawa tayi jinin jikinta yatsaya cak yabar aiki ganin Ajmal kwance saman duguwar sofa yana sanye cikin kyakykyawan jallabiyar shi yana karatun Qur'an tacikin phone dinshi , saka makon jiya da takawo Aheel basu ganshi a parlourn ba shima kuma Aheel bai nemi papan nashiba ya nace mata sede sukwana tare harda yar kukanshi karta tafi tabarshi atsorace tajuya cikin sauri zata koma atunaninta bai lura da itaba but setaji yace "You! come back here, "nan Nisha tashiga mis mis da ido tana Shirin kuka ita tarasa wani tsautsayim bacci mai dugun zango ya kamata cikin side din Ajmal ahankali tashiga takowa, jikinta sai rawa yake gaba kidaya bata hayyacinta saboda mafarkin da tayi gaba daya hankalinta atashe take kuma tana cikin tsoro sosai hankalin takarisa inda yake tadurkusa saman carpet kanta na kasa gaba daya zufa yagama wanketa tas gashin kanta duk ya manne jikin face dinta yayinda da idonta kuwa hawayene fal ciki suna kokarin gangaruwa kumatunta sosai take sunkuyar dakai saboda hawayen dake kokarin zubu mata, kallo Ajmal ya tsareta dashi sosai yake bin sumar kanta da kallo baki wuluk dashi se wani shainin take jin shiru baice komai ya tusata agaba yasa ta dago kai ahankali ta kai kallon ta gareshi daidai time din da sirarun hawaye suka sauka kuncinta ganin kallon da ya kafeta dashi kamar mai Shirin ganu wani abu a face dinta yasa tamaida kanta kasa tarasa shirun me Ajmal yayi yana kallonta ko wani irin kallone yake mata haka takasa ganewa kode kallon tuhuma yake mata na kasan cewa da tayi a side din shi, "Aheel ne ya bukaci na tayashi kwana bayaso natafi nabarshi shine..,,, dakatar da ita yayi da ga surutan da kefaman jero masa because ba a bunda yakeda bukatan tambayar taba kenan dama yasan Aheel da fitina ayanda ya kwallafa rai da Auntynsa dayake fad'i wataran cewa zai ta dawo side din ma gabaki daya yasan halin d'ansa Ajmal yanason d'ansa sosai yanda Aheel keson Nisha yake kaunar kasancewa da ita da kuma kulawar da Nisha take bawa Aheel yasa Nisha tasamu sassauci daga tsana dakuma ki dayake mata abaya , shiyasama yanzu bai cika fargaban halinda Aheel yake ciki ba because yasan akoda yaushe tana kasancewa da shi kulawar da take bashi ko uwar data haifaishi Heelah bata bashi , Aheel raunin mahaifinshine baiso alakar Aheel da Nisha tayi nisa haka bas because Ajmal hankalisa Sam yakasa kwanciya da yarinyar yakasa karbarta kamar yanda agdn suka karbeta hanu biyu wani tunani yake da ban akanta da kuma shakku , wani lokacin kuma tausayi take bashi yanda take wasu abubuwan cikin tsoro da rawar jiki kamar mara gaskiya wannan yana daya daga cikin abunda yasa yakeda alamar tambaya akanta, "you can go" abunda Ajmal yace kenan , kamar jira take because tagaji daga dukawan da tayi dan haka cikin sauri tamike tafice taname goge hawayen face dinta , lumshe ido yayi tareda tunanin cikin zuyarshi yarasa meyasa yarinyar sometimes cikin fiskar damu take yanzuma harda hawaye yagani saman kuncinta Wanda yasa yakasa tambayar takamar yanda yayi niya lallai akwai bukatan sanin wacce ita da kuma labarin ta, mikewa yayi danufin haurawa upstairs kamar ance ya daga kai sukayi ido biyu da Heelah wacce take tsaye tundazu daga saman bene tana kallonsu kauda kai yayi irin na ko inkula tareda haurawa upstairs yana kokarin nufan bedroom din Aheel Heelah kamar jira take yagama karisowa tayi sauri shan gabanshi tana fad'in "ahala wannan stupid girl din harcikin dare kanada bukatar ta , wai nikam me kuke nufine because nakasa ganewa lamarinku , Heelah ta tsareshi da tambaya cikin yanayin tuhuma but bai kulataba yaka kauce mata danufin ci gaba da tafiya amma se ta sake shan gabanshi tana cigaba da fad'in "ina magana kashareni to mezai hana ka aureta da irin wannan maden da kukewa juna... damko gashinta dayayi da karfine yasa tahadiye sauran maganar da take kokarin yi tashiga kiciniyar kwace kanta " a kullum ina fada miki kidinga nan na de harshenki daga warwareshi da kike kina furta abunda kikaga dama ni ba d'anki bane kuma niba sa'anki bane so be careful with me yana fadi'n haka ya kuma jijjiga gashin kanta da karfi kafin yayi wurgi da ita gefe yawuce yanufi bedroom din Aheel domin tabbatar da lapian shi, koda yashiga yasameshi cikin aminci yana tashan baccinsa harda minshari dan matsawa yayi kusa da bed din nan yaci karo da hulan Nisha da ta mance saman bed din Aheel wanda bata lura da shiba a takaicema batasan baya kantaba tsoro da far gaban mafarkin da tayi da kuma baccin da yasaceta a bedroom din Aheel side din Ajmal besa ta lura da shiba , hanu yasa yadauki hular yana jujjuyata daga bisani ya ajiye ya gyarawa Aheel blanket yarufishi dakyau kafin yanufi hana hanyar fita, koda yadawo parlourn ba takoma bedroom din ta cikin kuka , bedroom din shi yashiga daga bisani ya ajiye phone dinsa kafin ya nufi toilet danyin alwala domin time din sallah ya kawo kai yana idar da alwalan yafito da nufin shiga masallaci koda yafito suka hadu da Kamal wanda yafito shima danufin tafiya dan haka suka hade hanya suka tafi a tare duk da kasancewa masallacin a gidan yake but se kafita geat kafin ka iya shiga masallacin because kofar tawaje take ba ta cikiba, Nisha kowa cikin hanzari tashige bedroom dinsu tasamu duk suna bacci Fadeelah nabisa gado Reeda yayinda Reeda kuma tamike saman sofa tana bacci slowly kamar mara gaskiya tadauki towel direct toilet suma kokarin shiga sekuma ta tsinkayi muryan Reeda wacce tayi likimo ta kira sunanta , Nisha tsayawa tayi jikinta duk asanyaye , karisowa Reeda tayi tana mai karewa Nisha kallo wacce ta jingina kanta da jikin bangon dakin cikin damuwa "yadai Nisha Ina kuma kikaje bade a side din ya Ajmal kika kwanaba because bamu iya ishashshen bacci ba tareda keba, Nisha fada mata yanda sukayi da Aheel tayi irin rigimar da ya shiga mata sede sukwana tare bacci ya dauketa garin rarrashinsa but bata san time yaja hakaba, " Alright no problem sede kuma kamar yanayin ki nagani cikin damuwa what's wrong? girgiza Kai Nisha tayi tana fadi'n " Bakomai" "okay" Reeda tafad'i tareda ja baya domin bata damar shiga toilet da takeda niyar yi , Reeda komawa tayi tazauna bakin bed da tunanin keyasamu yar uwan tasu taganta haka bade yayan nasu bane yamata wani abin haka Reeda tazauna tana ta sake sake har Nisha tafito daga wanka hade da alwalan because ta kammala period dinta dan dama tarega Fadeelah farawa wardrobe tanufa ta zaro riga da hijab ta sanya daga nan tashin fida sallayan ta tada sallah ganin haka yasa Reeda Jan wani goron numfashi sannan itama tamike daga zamar da tayi tanufi toilet tayiyu alwala tanemi hijab ta sanya ta jera da Nisha itama ta tada sallahr daidai shigowar Amma domin tayar dasu sallah kamar yanda ta saba but setaga yau yaran nata sunyi hankali yau suntashi da kansu sun hutar da ita Fadeelah kawai ta hango saman bed ta baje se bacci take wacce tasan matsalar ta murmushi kawai Ammi tayi tafice da ga bedroom din tanufi nata dakin, kamar yanda kowa yasani yau jirgin Goggo rabi zai daga zata koma karfe 10 na safe bayan kammala breakfast gaba daya family suka kasance compound din gidan domin sallama da Goggo rabi because yau zatatafi Hajia Ammi Nabilah gefe su Reeda banda agogo sarkin aiki Heelah tun farar safiya tafice daga gdn, su Fadeelah sunyi jigun jigun dasu lamari babu dadi zasuyi miss din Goggo rabi comedy bazasu sake ganintaba kuma se biki dama bawani zuwa takeba sosai se sa'i da lokaci, sekuma wani taro mai mahimmanci biki ko suna, Nisha da bata santaba abaya yanzu setaji yanzu tafi kowa shakuwa da ita , an kammala sanya kaya a mota komai ya zama ready, " To saduwan alkhari se biki kuma in Allah yanuna mana muna cikin rayayyu " Ammi da Hajia suka shiga fad'in "Amin " daga nan Goggo rabi tashiga daga musu hanu suma suka shiga daga mata hanun daga bisani tashiga rantsatstsiya motar Ajmal wanda dashi acikin rakiyar kuma a motarshi shiyake but Kamal ke driving dinsu se Ajmal ke gefensa muhaiseen da Goggo rabi suna daga gidan baya nan Kamal yayiwa motar key mai gadi yabude musu geat Kamal yaja motar suka fice, harsuka fice Fadeelah da Reeda basu daina bye bye ba sun sake baki se daga hannu suke "To malamai sun bacewa ganinku daga hanun ya isa haka" Ammi tafad'i tana hararosu yayinda tajuya tanufi cikin gida,su Reeda sauke hannun sukayi jiki asanyaye ko wannensu ya nufi muhallin shi , ,...... rayuwa yanzu yayiwa Nisha kullin huhun goro kullum cikin tunani da far gaba take tunanin mahaifinta da sanin wani hali yake ciki kullum shine aikinta hatta kyakykyawan cin abinci ta dainayi alwalantama ba kamar da ba wanda yasa hankalin su Hajia ya dawo kanta ganin canjij da sukayi atareda ita, but sun tambayi mai yakawo sauyi a tareda ita mai yake damunta setace "babu" dan haka sesuka daina tambayan suka cigaba da janta ajiki cikin kulawa tareda wasa da dariya domin a tunanin su kewar mahaifiyar tane ya dawo mata sabo, wanda kuwa ba haka bane yanzu ba abunda take ga umma da yawoce addu'a gareta da fatan dacewa ga mahaliccinta tunanin ta daya shine tasamu hanyar fita daga gidan nan because taji gidan ya ishe tunaninta ya koma kan abbanta tun mafarkin da tayi da ashi da kuma halinda ta ganshi yana bukatan tai mako sede duk hanyar da tabi na kokarin barin gidan abu yaci tira because ko barawone yasamu nasaran shigowa gidan nan tofa fita zaiwuya agareshi matukar da kafarshi zaifita , sede in ba cewa zaiyi domin security ne abaje ko ta ina gashi ko kyakykyawan bacci basayi balle kasamu daman silalewa , gashi su gdn bawani fita akeba kullum ana jikin gida duk wani shopping din gidan barkace kezuwa tareda wasu securities din, but tabarwa kanta sanin cewa ta tsaida lokacin tafiya tabar gidan nan ko ta halin yayane domin taje gurin tushenta wannan karon tashiryawa Mami koda tsiya tsiya setaga mahaifinta sai tafad'i inda ta kai Abba because taga alamun ba gaskiya alamarinta, ranar wani lahadi da Nisha takasa mancewa dashi cikin rayuwarta tana kwance tana kwance bisa sofa cikin bedroom dinsu Fadeelah da Reeda sun kaiwa Aunty Nabilah ziyara kamar yanda suka saba sunacan sunata zuba mata surutu wanda hakan bakaramin dadi yakewa Nabilah hakan yana mata dadi sosai kasan cewar su kawaye yan uwa uwa uba kuma tana auran yayansu , but rashin jin dadinta daya takasa gane meyasa Nisha ke gudunta bata zuwa tareda su Reeda suna hira kodai ta dauka haryanzu tana fushi ko kishi da itane ita sam duk ta yada wannan mukaman zuciya daya tariketa yanzu , koda ace ya Kamal auranta zaiyi yanzu bazata wani damuba because yanzu yarinyar tausayi take tun wancen lokacin but itade tadaina kishi da ita musamman yanda Kamal yake kulawa da ita sosai ko bacin rainta bayason ganin yanzu duk wani abunda yakeso ko zaisashi farin to itama tana son shi saboda tsantsan so da kaunar da take mishi zataso duk abunda yakeso koda ita bai mataba, ta rintsa ido tana ta faman tunanin da tasaba koda yaushe tadaurawa kanta tunani da damuwa bude ido tayi tazauna tareda dafe goshinta cikin tafin hannunta , nan ta sakalo kafarta kasa ta sakko daga sofan tanufi window, daga labulen window tayi tana ta kallon geat inama ace ana bacewa da tabace yanzun nan because duk tunanin ta ya ta al laka ga barin gidan motsin shigowar da tajine yasa tamaida da hankalinta ga door din ganin Kamal tsaye bakin door din face dinsa yayi jawar idonsa duk yacika da kwallah yasa tajiyo gabaki daya tana kallonshi tareda karisawa inda yake tsaye, kallonshi take sosai cike da mamaki mutumin da kullum yake cikin raha da dariya but yau face dinsa ya canza "ya Kamal what's happened naganka cikin wannan yanayin? " Nisha ta tambaye shi ciki kaduwa Amma setaga ya juya baya yadafe hanunshi jikin bangon dakin ya sunkuyar dakai kasa " Ya Kamal kasani cikin damuwa naganka cikin yanayin da ban saba ganin ka ahakaba, please kasanar dani damuwarka" "Nisha dama ke ba tawa bace " ras gaban Nisha yafad'i jin abunda Kamal ke fad'in " but meyasa zakace haka ni takace mana Nisha tabashi amsa cikin damuwa narashin sanin dalilin dayasa yazo mata cikin wannan yanayin yana irin wannan maganan, "Ke batawa bace Nisha because da aure akanki kika boyemin kuma nazo miki da soyayyata kika amsa ba tareda sanin igiyar aure ne akanki ba , why kika boyemin baki sanar da niba why Nisha? Kamal ya fad'in cikin daga murya gamida damuwa da baccin rai yana tambayan ta, Nisha turos tayi tana kallon shi da mamakin maganganun da yake fitowa daga bakinsa, 'anya ya Kamal yana cikin hankalinsa kuwa Ammi tagani tazo da sauri kusa dashi ta dafa shoulder dinsa tana fadi'n "Kamal mekakeyi haka ne? kamata yayi ka tsaya kaji abunda zan fad'i ba kafito ka kyaleniba yayinda nake magana kasaita natsuwarka mana haba Ammi tafad'i cikin sigan fad'a "Ammi idan kowa zai boyemin ita bai kamata ta boyemin ba because tasan inasonta kuma na baiyana mata soyayya na agareta ta amsa batare da ta fad'amin matsayin taba, am,. "Ya isa haka Kamal itama ba tasan komai gameda auran nan ba haka zalika shima Ajmal baisan da auranta akanshi ba iya tsakanimu magnar ta tsaya sai kai yanzu da kabijiromin da batun soyayyarku da na nemi na fahimtar da kai kaki saurarata". Ammi tafad'i cikin sigan shiga damuwa sam bataso abun ya kasance ta hakaba taso abi abun asannu ahankali but taurin kai irin na Kamal yakasa fahimtarta balle ya saurareta gashi yanzu yasa tayi subul da baka sirrin ciki yafito fili, "Innalilahi wa'ina ilaihi rajuun" abunda Nisha take furtawa kenan ahankali yayinda ta dafe goshinta wanda takejin yamata nauyi saitaji mak'ok'oronta ya bushe yawun bakinta ya kafe dib ' Aure! Aure dai ' Nisha keta maimaita wa cikin zuciyarta ba jimawa idonta tasuma ganin walkiya walkiya haske haske hazo hazo kankance mai dakin yafara jiyuwa mata kafin su ankara tafad'i kasa sumammiya, sallallami sukashiga yi harsuna gwaral wajan karisawa wajanta tso da fargaba duk ya dabai bayesu "Kaga irinta ko Kamal ga irinta nan da ka saurareni munyi maganan cikin nitsuwa da duk haka bata faruba da batajiba bare hankalinta ya tashi yanzu ga abunda taurin kanka ya haifar", Ammi tafad'i cikin rudu da tashin hankali "Please Ammi kibar wannan maganan yanzu bashine solution ba mudagata mukaita asibiti don aceci lapiyar ta because karwani abin ya sameta" Kamal yafad'i cikin rikicewa da tunanin mezaije ya dawo "Kamal kira doctor kira doctor fu'ad please kirashi da sauri" "Why not bazamu kaita asibiti ba?" "Zaka sake taurin kainne ko zakayi abunda nace " Ammi tafad'i a tsawace , cikin hanzari Kamal yamike yazaro phone dinsa cikin pocket dinsa marmaza yashiga dealing number doctor fu'ad yana dagawa Kamal yasanar dashi ana bukatarsa agida yana gama sanar dashi ya katse wayar ya kalli Ammi yana fadi'n "Ammi taimaka min mudagata izuwa bed kafin doctor fu'ad din yakariso ba musu Ammi tasa hanu suka sunkuci Nisha wacce ke maga shiyar kamar macecciya suka daurata saman bed Ammi tazauna kusa da ita ta janyo hanun Nisha ta daura bisa nata tana murzawa idon ammi duk ya ciko gaba daya tausayin yarinyar ya kamata ita dama kwata kwata bataso al amarin nan ya kasance ba Hajia ce tayanke hukunci ba tareda tayi la akarin abunda zaije ya dawo ba da ace tasan kaunar da Kamal yakewa Nisha tabbas bazata taba bari wannan lamarin yafaruba gashi yazo mata time din da yariga ya makara wanda hakan yajawo tonu abunda aka rufe wanda dama duk daren dadewa zaibud'u,. duk da sunso abi abun daki daki Amma zuwan Kamal duk ya cakuda abubuwa saboda shegen zuciya irin tashi Ammi hararo Kamal tayi wanda keta safa da marwa cikin dakin cike da damuwa, ba ji mawa Kamal yaji ki ciniyar bude geat aiko cikin sauri yafice ya taroshi cikin hanzari suka kariso shigo cikin bedroom din, ganin Nisha kwance idanuwanta arufe Ammi na gefen ta cikin damuwa yasa doctor fu'ad saurin karisawa kusa da bed din yana tambayan ba'asin meyafaru da ita, saidai ba amsa saima Ammi da ta kai kallon ta ga Kamal wanda shima itan yake kallo ta kuma cilla masa harara wanda ya sa shi sunnar da kai kasa cikin na dama jin shiru ba wanda ya samu daman ba shi amsa yasa yace su ba shi guri ya dubata ba musu Ammi tamike tafice Kamal ma ya rufa mata baya haka suka fito sumu sumu da su. Gefe Ammi tazauna bisa sofa ta raf ka uban tagumi shi kuwa Kamal bai samu daman zama ba sai kaiwa da kawo yake tsakiyar parlourn, jim kadan doctor fu'ad ya fito wanda suna ganin fitowar shi yasa suka nufoshi suna tambayan shi ya jiki Nisha ya amsa musu da "Shi is fine but baku bani amsa ba maiyayi causing dinta shiga wannan ya nayin doctor fu'ad ya kuma tambaya yana kallonsu Kamal dai har yanzu bai iya cewa komai Ammi ce ta saukar da ajiyar zuciya jin kyakykyawan labari Nisha na cikin koshin lapia, takalli doctor fu'ad ko ma wa tayi ta zauna kafin tayiwa doctor fu'ad nuni da ya zauna dan yi masa ba ya ni. Dan muskutawa Ammi tayi tagayara zama kafin takalli doctor fu'ad wanda ya mata zoro yana sauraron abinda zata fad'i, doctor fu'ad kai ba mutumin da za abuyewa komai bane, kamar yanda kasani shekarun baya da suka wuce Hajj mama itace silan hada auran Ajmal da Heelah , to halinda ake ciki yanzu wasu kwanaki dasuka wuce Hajia tasake hada auran Nisha da Ajmal but tayanke hukunci ne cikin bacin rai bisa rashin kunya da rashin girmamawa da Heelah da mahaifiyarta suka zo suka gabatar kwanakin baya akan wata yar hatsaniya da ya faru tsakanin Raheelah da Nisha nan Ammi tashiga korawa doctor fu'ad yanda lamarin yakasance da kuma dalilin da yasa Hajia ta zarta da wannan hukunci ba tareda tayi la akari da afkuwan wani matsalaba dan kauda kai Ammi tayi tana murza hannayenta irin na shiga damuwa tace," "Duk tsawon kwanakin nan inata kokarin na fahimtar da ita cikin natsuwa bisa auran Ajmal da ke kanta amma senaji nakasa maganar tayimin nauyi because bansan da wani ido zan kalletaba kuma bansan wani irin kallo zata mana ba bisa amanarta da mukaci nadaura mata aure da da' nmu ba tareda yarda ko amikamatrta ba , sam bamu san Kamal yana da ra ayi akantaba se yanzu yasameni da batun soyayyarsu wanda yanzu shiyayi causing wannan problem din banso ta tsinci lamarin ta wannan sigarba, Ammi tafad'i tana sunnar da Kai kasa , wani goron numfashi doctor fu'ad ya sauke tareda jinjina kai yana mai mamakin lamarin, yama rasa tacewa but tawata fiskar yaji dadin kasan cewar hakan because tun randa yafara ganin yarinyar ya yabawa hankali da nisuwarta koma ba komai yasan zata kula dashi sosai fiye da tuna ninsa to amma yanda zai karbeta amatsayin mata yake tunanin because koda yakarbeta amatsayin mata yasan Nisha bazataji dadin zama dashi especially yanda bai gama gamsuwa da itaba, dan gyaran murya Doctor fu'ad yayi kalli Ammi yana fadi'n "Amma senake ganin kamar bai kamata acigaba da boye batun aure tsakaninsu ba duk da ita Nisha tasani yanzu shima Ajmal yana da hakkin yasan nauyin da aka daura masa or yayi accepted or rejected dan haka boyewa bashi dawani fa'ida kamata yayi yayi azauna dasu ko duk susan matsayinsu wannan shine shawaran da zan iya bayarwa doctor fu'ad ya fad'i yana kallonsu Ammi da kamal wanda yayi zoro daga gefe yana jimami, dan gyada kai Ammi tayi alamar gamsuwa da maganar tashi batare da ta iya sake cewa komai ba, "so nizan wuce zuwa gobe zandawo naga yanayin jikin nata duk da ba wana matsala bane kawai tsoro da firgici ne yayi causing," doctor fu'ad ya fad'i tareda mikewa nan idonsa yasauka kan su Fadeelah da Reeda wanda suke tsaye bakin door Wanda basu ankara da suba balle susan da tsayuwarsu sungama jin komai jikinsu duk asanyaye cikin sauri suka kariso ciki suna kokarin nufa bedroom din dan ganin halinda Nisha ke ciki cikin hanzari doctor fu'ad ya dakatar da su gamida fad'in," "Please karku dameta yanzu because tana bukatan hutu, so kudan kara hakuri" jiki ba kwari suka nemiguri kusa da Ammi suka zauna suka sanyata tsakiya kowaccensu tajin gina head dinta jikin shouldern Ammi cikin damuwa, doctor fu'ad binsu kawai yayi ganin yanda sun wani lagwabe jikinsu duk yayi sanyi dan girgiza kai yayi daga bisani yayi sallama da Ammi yafice Kamal ya rufa masa baya jiki amace, seda Kamal yaraka doctor fu'ad harbakin motar sa kafin sukayi shaking hand doctor fu'ad ya shige motarsa yamata key mai gadi yabude masa geat yafice daga bisani Kamal shima ya juya cikin gidan direct part dinsa ya nufa inda ya iske Nabilah bisa sofa tana danna wayarta jin motsin shigowar Kamal yasa tamike cike da murmushi but lokaci daya kuma murmushin ya kawar kan face dinta ganin Kamal cikin wani yanayin wanda bata saba ganisa cikiba, Direct bedroom taga yajufa ko inda take bai kallaba aikuwa cikin sauri itama ta tashi tabi bayanshi, koda tashiga bedroom din bakin bed taga ya yazauna yayi juguk dashi hakan yasa Nabilah karisowa inda yake tadurkusa saman carpet tadaura hand dinta saman cinyarsa tashiga tambayansa meke damunsa amma se shiru yayi bai kulataba, " Please ya Kamal kafada min meke da munka ni matace agareka bai kamata kaboyemin matsalar data damekaba" "ko nice nayi wani laifin ban saniba kasanar dan" ganin yanda take masa magiya duk tashiga damuwa ganinsa haka yasa yace "Please Nabilah banason yawan tambaya ni ba abunda yake damuna so kidena damun kanki" yana fadi'n haka yamike yanufi toilet jiki ba gwari Nabilah tamike tafito daga bedroom din takoma parlour tanemigu tazauna tana tunanin meyeke damun Kamal taganshi cikin wannan halin, jim kadan taga ya fito cikin wani shirin ya fice ba tareda ya kalletaba balle yace mata wani abin, komawa tayi ta kwanta kankance me hawaye suka shiga zarya cikin idanunta sam bataji dadin kasan cewar sa cikin wannan yanayin ba to kowani laifin tayi masa bata saniba kamata yayi yasanar da ita ba yadau zafi hakaba,. Guraren karfe 9 na dare Nisha tasaki wani dugun nufashi kafin tashiga kiciniyar bude ido seda takarewa bedroom din kallo sannan tasauke ajiyar zuciya tadauka zata bude ido ta ganta agushewarta because yanda zuciyarta wani buguwa da karfi time daya sam ba tayi tsammanin bude ido ta ganta araye ba dakin shiru yake ba kowa sai ita kadai dake kwance anrufeta da blanket, yaye blanket din tayi ta mike zaune ta najin yanda kanta yai mata nauyi tamkar an aza mata kaya maganganun Ammi ne ya shigadawo mata cikin kai yana mata yawo cikin kwakwalwarta, cusa kanta tayi tsa kan kanun kafafuwanta tashiga rera kuka har da shashsheka. Ringin din k'aran wayarta ne yasa ta tsagaita da kukan ta shiga leka phone dinta daketa faman ruri saman bedside table but kafin ta dauki phone din I kiran ya katse jawo wayar tayi tashiga duba mai kiran 5 miss call tagani daga kawarta salma wasu sabbin hawayene suka sake kwaranyo mata ganin k'iran salma wacce ta turo mata da IV dinta tun last week auranta cikin wannan week din Nisha ba k'aramin buri ta ci ba na auran kawarta salma sai dai kafin auran salma ita andaura nata auran wani sabon k'iranne ya kuma shigowa Nisha kamar baza ta daga k'iran ba saboda yanayin da ta ke ciki bazata iya magana ba harya kusa katsewa sannan ta dauka tare da kara wa akunne ba tareda ta ce komai ba, "Haba Nisha tun yaushe naketa kiran wayanke ba kya picking kuma baki biyoniba ni ba wannan ba yaushe za ki zo ne because ya kamata a fara komai dakefa" " Hello wai ko ba kya ji nane kam "salma ta tambaya jin shiru ba magana sai shashshekar kuka da ta ke ji kasa kasa "Wai mai yake faruwane Nisha naji kinyi shiru inata magana kinyi shiru qalau kike kuwa, ?" dib Nisha ta katse wayar ta sake phone d'in saman bed tashiga rera wani sabon kuka ta na cikin wannan ya nayin sai ji tayi anturo door ana kokarin shigowa wanda yayi saurin mayar da ita sense d'inta cikin hanzari tashiga goge hawayen face d'in ta ta koma ta kwanta ta rintsa ido kamar mai bacci, cikin natsuwa HAJIA ta turo door ta shigo hade tura kofar ta rufe, girgiza kai Hajj mama tayi ganin Nisha kwance yanda suka barta kamar mai bacci saka makon zuwan ta bakin door din ta jiyo sautin shashshekar kuka wanda kuma Nisha ce keyi karisowa tayi kusa da bakin bed d'in ta zauna tare da shafo kan Nisha tashiga fadi'n "Ki ga far ceni y'ar nan na yanke hukunci ba tareda izini yarda ko amincewarki ba nayi hakanne ba dan na cutar da ke ko saki cikin damuwa ba " tar Nisha ta bude ido jin Hajj mama ke magana ta na kokarin matsar kwalah Manyan idanuwanta wayanda suka kumbura ta sauke akan Hajia wacce tayi sunkuye cikin kunya da na dama tana ta faman sharce , hawaye da gefen zaninta hankali Nisha tasuma kokarin gyara zama wanda yayi sana diyan dago da kan Hajj mama cikin sauri tashiga taimakawa Nisha wajan gyara mata zaman tana fadi'n "Sannu 'yar nan ya jikin naki dan allah ki gafarce ni ba na son ki shiga da muwa sabida ni hak'ik'a nayi babban kuskure wajan yanke hukunci ba tare da sani ko yardarki ba amma dan allah,.. cikin hanzari Nisha tariko hanun Hajj mama wacce duk ta da burce ta shiga da muwa cikin sanyin murya Nisha tasuma fadi'n "Please Hajia kidaina neman afuwa agareni aganina kun isa da ni shiyasa kuka zabamin miji kuma nasan ba dan kucutar da ni bane yasa kukayi hakan, inde nakasance daya daga cikin y'ay'an gidan nan to kunada kowacce irin dama akaina ba zabin da zakuce kunyi nace AA ko nayi musu please Hajia kidaina damun kan ki zabin da kukayi agareni shiya dace dani because ni yar kuce, Nisha ta karishe zancen da rintsa ido saboda hawayen da yacika idanuwanta, "Aa Nisha kema kina da naki ra'ayin kuma kina da zabi, hakika naji komai daga bakin Ammi soyayyarku da Kamal wanda kuwa da nasan hakane kokusa ko alama da bazan fara wannan katubaran ba nide burina kikasance daya daga cikin sirikar gidan nan alakarmu dake takara kusanci sosai , hakika nice sila aurarraki dayawa daga cikin family nan saboda dauren family na , kama daga auran habu d'ana(Daddy) nina hada auran sa da yar wajan k'anwata hafsa wacce Allah ya azurta ta da yammata biyu Bilkilsu da Maryam, wanda daga baya Allah yamata rasuwa nina cigaba da rikeso lokacin Ina tareda mijina Alh Muhammad bature wanda shi balaraben saudia ne a saudia muke da zama acan na haifi y'ay'ana maza guda biyu Abubakar wanda muke kiransa da habu(Daddy) da Muhammad wanda muke cemasa modi(Abu) sai Rabi'atu itace karama, Bayan rasuwar k'anwata hafsa can natafi dasu kasan cewar ita a Nigeria tayi aure kuma tana kusa da baffa Sani wanda yakasane wan mahaifinmune shiyarikemu yarenemu saboda mu marayune duk mahaifanmu sun rasu shiya cigaba da rikemu bisa amana kulawa da kuma nuna mana gata because iyayenmu sunada wadata sosai bamusan meye wahala ko taluciba alhamdulillah muna cikin rufin asiri bayan rasuwar baffana da kuma k'anwata ba karamin shiga damuwa nayiba because narasa dangina yanzu banida wasu family da wuce y'ay'ana 5 da mijina dan haka sena rungumesu muka cigaba da rayuwar farin ciki dajin dadi yayinda kowannesu yake karatu gurare daban shi Abubakar a Paris yake ban garan kasu wanci yayinda shikuma modi yazabi Landon ban garan likitanci sukuma y'ay'a matan agabana suke karatu because ni ban yarda da karutun y'ay'a mata awani gurin da ban ba shiyasama kikaga Fadeelah da Reeda suke karatunsu a maryam abacha komai zasuyi ido nakansu, Bayan kammala karatun kowannesu yacika burinsa yayinda modi ya zama babban doctor nan kasar Landon din yake aiki yayinda yabude hakararren hasibiti nashi nakanshi dake gida Nigeria da sunana HAJIA MADINA hospital inda yarsa Heelah take ai kenan kuma ita take jagorantar asibitin ,shikuwa habu yazama babban dan kasu but shi rayuwarsa harta ban garan siyasa ya taba yayinda yashahara wajan kasu wancin gwala gwale anan kasar England yayinda ta ban garan siyasa yake na hanun daman shugaban kasa, ganin kowannesu yacimma matsayan dayakeso tsayawa yasa nabijiro musu da batun aure cewa kowannesu ya gabatar min da macen da yakeso kuma yakeda burin aure ban garan habu yanuna min shide tukunna bashida wanda yake so yanzu baisaniba ko nan gaba but azahiri yanda naga sunfi shakuwa da Balkisu kullum suna tare suna fira nayi tunanin soyayyace a tsakanin su but saiya tabbatar minda ba abunda nake tunanibane to amma banida zabi wannan alkawarine da nayiwa zuciyata hada auran su dukansu 4 saboda sake dankun zumunci because a ganina nagida bai koshiba ba abawa na wajeba, Kasancewar modi shine babba senayi tunanin hadashi daHafsa because yarinyar akwai nitsuwa sosai ga hakuri but shi modi akwai taurin kai gaskiya wani lokacin baya jin magana ga fada ba kamar habu ba dan shi yanada saukin kai ga raha but shima wani time inya juye baka gane masa shiyasa nayi tunanin shikuma na hadashi da Balkisu (Ammi) Balkisu yarinyar tana da raha ga suruta kamar aku saide kuma akwai tsiwa wani lokacin shiyasa nake ga zasufi dacewa da habu tasu zaifi zuwa daya saboda ita Hafsa tanada shiru shiru sosai batafiye maganaba kuma itace karama akan Balkisu, koda nakawo shawaran hada junansu aure bawanda yakawomin cikas se modi dama nayi tunanin hakan domin kuwa yaki amsan tayin da namasa na auran Hafsatu yakawomin azurin yanada wacce suka d'aid'ai ta a Nigeria take da zama azirga zirgan dayake tsakanin Nigeria da london suka hadu, har ya gabatar min da hoton ta sunanta Jumanah azahirin gaskiya yarinyar bataminba Hafsatu naso na hadasu amma sam yadage se waccer yarinyar mai ido atsakarka ganin banasu natakura masa yasa nazuba masa ido yayi yanda yakeso yayinda shikuma habu ya amince da zabin da nayi masa, haka itama Rabi ta gabatar min da wanda take so saide shima asalinsa dan Nigeria ne shima babban dan kasuwane yau yanaca gobe yana nan but yafi zama Nigeria, dan haka aka daura aure kowannesu, Koda aka daura aure modi cewa yayi a Nigerian zasu tareda domin acewarsa amaryarsa tace bazata zauna inda yakeba because bazatabar dangintaba saide shiyabiyota suzauna acan domin bazata zauna inda ba kowa nataba modi duk abunda tace masa kamar yanka wuka haka zaidau lamarin a tak'aice dai yabita can Nigeria acan suka tare , itama Rabi tana can tareda mijinta a Nigerian karatunta da komai ya koma can, nida maihaifinsu wanda yake kwance jinya da habu da amaryasa mukadai muka kasance anan duk da shima habun bai wani cika zama sosai ganin yanda Balkisu take zama cikin kadaici yasa nace yadinga tafiya da ita matsawar bazata takurawa aikinsaba dan haka seyabi maganata yakan tafi da ita sa'i da lokaci kasan cewa itama karatu take bawai ta kammala bane inda take bangaran alkalanci, Hafsatu ita kadai takasan agabana da batayi aureba tacigaba da karatunta inda take da burin zama shahararriyar barrister saide kafin kammala warta tasamu miji inda wani malaminsu yanuna ra'ayinsa akanta ma'ana yanason ya aureta aikuwa ba bata lokaci akayi auran, saide kafin agama warware gajiyan bikin rai yayi halinsa watansu 3 yayi hatsarin mota Allah ya dauki rayuwarsa tadawo gida muka zamana yayinda ta cigaba da karatunta alokacinda Balkisu take dauke da tsohon cikin Ajmal a wannan yanayin mijina Alh Muhammad bature Allah yamasa rasuwa bayanda Balkisu tahaihu ta santalo santalelen jarumi d'an wanda yaci suna Muhammad anakirasa da AJEEMAL idan kinji ance Ajmal ananufin abu mafi kyau, mai kya , kyakykyawa, tunda suka haifi Ajmal sama da shekara 8 sannan ta sake samun cikin Kamal wanda kusan tare suka haihu da Rabi tsakanin muhaiseen da Kamal bai wuce sati 2 ba Saida aka hafi muhaiseen bayan sati 2 aka haifi Kamal shiyasa tsakaninsu ba yawa wanda tunda taga haihuwan muhaiseen Rabi bata sake samun wani cikin ba shiyasa ta dauki son dunya ta dau rawa muhaiseen because shi kadai Allah yabata, Kamal nada shaira 6 Ammi ta sake samun cikin yan biyun ta Fadeelah da fareeda ita fareeda sunan k'anwata taci yayinda ita kuma Fadeelah ni a kayiwa mai suna, ina matukar alfahari da family na mun zama tsintsiya madaurinki daya saidai gaba daya hankalina ya koma kan Rabi da Modi da suke Nigeria especially Modi da hankalinta ya kasa kwanciya da shi g'wara ita Rabi hanun namiji take but shi Modi ahanun mace yake saboda ita ta jashi sai yanda tayi da shi wannan abu yana d'agan hankali., Bayan da su Reeda da Fadeelah suka kammala primary School nayanke shawaran komawa Nigeria tushe na domin hankalina ya kasa kwanciya da rarrabuwan kan ahalina saidai Kamal da babban yayansu karatunsu yayi nisa shi Kamal yana Americans shikuma Ajmal yana Dubai kowannesu da inda yake karatu dan haka koda Habu ya dawo nake sanar da shi hukunci da nayanke na komawa Nigeria tun da dalilin wanda nake aure anan din Allah ya masa rasuwa dan haka zan koma mahaifata Habu baimusa mi ni ba saidai yace mu d'an basa lokaci domin duba mana gidan da zamu zauna, aikuwa cikin satin yazo ya nuna mana amincecen gidan da ya siya mana a gida Nigeria cikin babban birnin kano gidan yayi kyau fiye da tunanin mai tunanin dan haka sai muka soma shirin komawa Nigeria , . Koda muka dawo Nigeria muka sauka agidan da Daddy ya siya mana gidane mai kyau na alfarma babu abunda babu acikinsa komai na bukata an ta na daishi acikin gidan sai dan abunda da ba arasa ba bayan kwana biyu da zuwan mu na bukaci Daddy da ya kira Modi ya sanar dashi zuwan mu saboda ni inna kirashi baya shiga saidai shi ya kirani wani sa'i bayan lokacin watakil shi akwai yanda suke sadarwa kwana biyu da yin hakan aikuwa Modi ya turo da wata kyakykyawan mota acewarshi ad'ibomu akawomu inda suke aikuwa hakan akayi duk mukayi shiri muka shiga motar da ya aiko domin mu shi kuwa Habu motarsa na bayan mu yanabin duk inda yaga munyi har Allah yasa muka isa gidan Masha Allah gidan da modi yake rayuwa aciki yanada kyau matuka Saida kyansa zai biyo bayan wanda Daddy ya siya mana Wanda muke kokarin fara gina sabon rayuwa a ciki, balaifi anyi mana kyakykyawan tarba an gabar mana da abubuwa kala kala kama daga a bubuwan ciye ciye da na lashe lashe. Alhamdulillah naga d'ana cikin aminci da kwanciyar hankalin da alamu shima yaji dadin ganin mu tare da jin kyakykyawan labari dawowar mu Nigeria Saida abun lura dashi tun shigowar mu Modi ke tabin Hafsatu da kallon bakinsa keson cewa wani abin ita kuwa Hafsatu ba ta shima take ba hankalinta gaba daya yana kan yarinyar da ta ke ta shiga tana fice wajan d'a wainiya da mu duk wani abunda ake da bukata ita ke samarwa cikin hanzari kaida ka ga yarinyar baka kalar y'ar aikatau ko wahala ba kyakykyawan yarinyace kuma ga hankali yarinyace karama da bata wuce sa'arsu Fadeelah 13 year's sai girman jiki da suke da shi kai ka ce yan 20 year's. Gaba daya nima hankalina sai ya karkata yakoma kan ta nan nefa nake tambayan Modi tunda nazo banga giftawar jininsa ko guda daya ba nan yake sanar dani duk suna can ture suna karatu but nan da karshen shaikara zasuyi hutu zasu dawo insha allah daga nan zai gabatar dasu gareni amma ga k'anwarsu Nabilah Abu yafad'i yana nuna min Nabilah wacce tasunnar da kai kasa tana jiran abata umarni tayi nace dashi yanzu wannan din yar kace na tambaya da mamaki dan k'wata k'wata ba zakayi tunanin yar gidan bace duba da yanda taga Jumanah tana ta tsawata mata d'an kuskure kalilan zata hantare ta gaba daya dai yanda take mata zakayi zammani aikatau take wanda kuwa ba haka bane, nan ya fara neman da nayafe masa ataikace dai yayi aure shaikarun baya da suka wuce auran bai jimaba matar tarasu saka makon jinya da taita fama dashi wanda aka kasa gane kan lamarin har Allah ya karbi rayuwarta. Tabbas Modi ya shayar dani ruwan mamaki ban dauka zai iya mai dani ba a bakin komai na keba a garesa da har zai iya kula wani al amarin ba tari da nasa ni ko naji labari ba ban bi takanshiba ballai nasan sauran zancen da yake natashi na nufi gurin jikata tare da janyo ta jikina wanda ya sanya yarinyar sakin wani kuka mai tsuma zuciyan mai saurare gwanin ban tausayi take parlourn ya dau shiru bawanda yake magana daddy tunda muka shigo parlourn bayan gaisawa bai iya sake cewa kala ba ya zubawa sarautar Allah ido yana ganin yanda dan uwan nasa gaba daya ya koma sususu, fareeda da Fadeelah kawai na kallah na basu umarni dasu je ciki su ta ya Nabilah hada kayanta domin kuwa tare zamu tafi zama yakare mata agidan nan, amma Jumanah ba kunya babu tsoron Allah tashiga mita mai ya sa za adauke Nabilah daga gidan bayan ansan ita ta ke mata hidman cikin gida saboda Jumanah tamkar y'ar aikin ta haka ta dauki Nabilah duk wani ayuka na gidan ita takeyi amma ban bi takan ta kan surutan ta ba su Fadeelah suka hada kayan Nabilah suka fito muka wuce har muka fice daga parlourn HAJIA Jumanah mita ta ke wa Modi mai ya sa bazai dakatar damu daga kokarin tafiya da Nabilah da mukeson yi ba shikuwa Modi ya kasa tsaida mu kuma ya ka sa jure mitar da matarsa keyi haka muka tafi muka barso,,. Turo door din da a kayine ya sa HAJIA da ka ta wa daga labarin da take bawa Nisha suka shiga zurawa door din ido don ganin mai shigowa, ganin Ammi ne tashigo bakinta dauke da sallama yayin da hannayenta ke dauke da trary din abincin tashigo ta tsaya daga gefe tana aikawa Nisha da kallon tausayawa kafin ta ce " Hajia ya ka mata ki je ki ki kwanta kihuta ni because kin ga ke ma ba k'oshin lapia ga re ki ba d'an numfasa wa Hajj mama tayi kafin ta gyada kai takByalli Nisha tare da shafo gefen face d'in ta tana fadi'n "Zan tafi saida safe ki kula da kan ki" gyad'a kai Nisha tayi daga haka Hajj mama ta mike ta fi ce daga bedroom fadi'n "To yanzu bari natafi na baki guri ki kwanta ki huta good night" Ammi tafad'i tana yi wa Nisha kyakykyawan murmushi itama Nisha murmushin yak'e ta shigayi tana g'yad'a kai daga haka Ammi tafice daga bedroom din cike da jin dadin yanda Nisha ta sake jiki, nan Nisha ta koma ta kwanta because jikin ba k'wari kuma amace duk wannan sa kewar da Nisha tayi taci abinci cikin raha da rashin damuwa kawai ta danne zuciyarta ta ne because bata son su dinga shiga damuwa ta dalilin ta but Allah kadai yasan kukan zucin da ta ke. Washe gari da asuba Nisha yanda taga dari haka wa ye wan gari because bacci ya kasa daukar ta gefe Fadeelah da Reeda sai bacci suke cikin kwanciyar hankalin amma ita bacci ya kasa ziyartarta sam tunani duk yabi ya adda bi k'wanyarta ta kasa gaskata wannan lamarin wai ita aka daura wa aure da Ajmal papan Aheel mutum da Sam baya kaunar kasan cewar ta atare da shi in ba ya ka sance dole ba taya ma zata iya kasan cewa da shi tare da wannan ma sifaffiyan matar tashi Heelah mai bala'in kishin tsaya duk time din da taji wannan al'amarin tasan saita konata da ranta, haka Nisha ta dinga juyi saman bed ta juya nan ta juya can daga karshe taga kwanciyar ya gagara haka yasa ta sab'ulu daga saman bed tanufi bathroom because asuba tayi anata kiraye kirayen sallah ga mai niya . Wanka tayi sosai daga bisani ta fito ta naimi duguwar gown sannan ta sanya hijab tare da shinfida sallah tashiga jera salloli, karan ringin din wayar Fadeelah wata sai ta arlam na asuba shine ya tashesu daga nan nauyan baccin da suke, koda suka tashi idanuwan su ne ya sauka kan Nisha wacce ke zaune bisa sallaya bayan idar da sallolin ta tashiga yin lazumi ko waccen su mikewa tayi tasakko daga bed daya bayan daya sukayi alwala suka fito suma suka ta da sallah gefen Nisha, koda suka idar da sallah sukayi addu'a daga bisani suka mike Fadeelah tanufi bakin bed ta zauna yayin da Reeda ta ne mi saman sofa ta zauna gaba daya suka tusa Nisha a gaba suna kallo wacce kanta ke sun ku ye gaba daya yinin jiya bai musu dadi ba du ba da ya nayin da y'ar uwarsu ta kasance a ciki na rashin jin dadi ta wani ban ga re kuma ba karamin farin ciki suke da kasan cewar wannan lamari ba ko ba komai alak'a ya kara karfi tsakaninsu. Jin shirun ko wannen su ya sa Nisha juyawo suka hada ido da su Fadeelah wanda ya sa su ka yi saurin sakar mata murmushi, itama Nisha murmushin ta mayar musu hade da jawo alqur'ani mai girma ta shiga karanta ko damuwar da ke zuciyarta zai kawo , tayi nisa cikin karatun yayinda kakejin yar siriruwar muryanta wanda ka ke ji kamar ana busa sarewa tsabar zakin muryar ahankali ta ke karatun saboda gudun shiga hakki, sai guraren 7:30 kafin ta samu daman tsagai tawa time din har su Reeda bacci ya sake kwashesu daga inda suka k'ishin gid'a ita Fadeelah ta G'yara kwanciyar saman bed itakuwa Reeda ta mike saman sofa sunata baccin su, ajiye alqur'ani Nisha tayi tare da ninke sallayan ta ya ye hijab din da tarufu ta nemi ma ya fi ta sanya bisa kanta tanufi hanyar fita daga bedroom din direct kitchen ta nufa ko zata tarar da barka cikin kitchen din but sai ta tarar ba ta ciki kamar bata fito ba kenan sometimes zaka iya tarar da ita guraren 6: ta na aikace aikace Harta wu ce za ta koma sai kuma taji kamar shashshekar kuka ana jan akanci da surutai kasa kasa da ya ke kofar Barka yana gefe da kitchen shi ya sa Nisha ta jiyo sautin, ba da wani jin kiri ba Nisha ta matsa jikin door din Barka tare da murda handle din kofar ahankali bakin ta dauke da sallama ta tura kofar ta shiga, ko da Nisha ta shiga bedroom Barka a zaune ta sa me ta bisa sallaya tana addu'a yayin da ta daga hannuwa sama tana rokon Allah jin motsin shigowar mutum ya sa Barka saurin shafa addu'a tare da mutstsike hawayen face d'in ta tashiga k'irk'iro murmushi tana kallon Nisha yayin da ta kariso gefenta ta t'suguna "Baba barka lapia kuwa mai yafaru?" Nisha ta tambaya tana kallon Barka wacce ta ke mammatse ido cikin damuwa, "Bakomai y'ar nan lapia qalau na ke ya yau baki koma baccin ba kenan ya jikin naki ashe bakiji dadi ba Barka tashiga jero mata tambaya ta na murmushi da nuna ba wani da muwa da ke damun ta, "I'm okay but sai na ke ga kamar kinada damuwa because ga face din ki ya nuna hakan" "Lah ke kuwa y'ar nan mai zai da me ni a duniyar nan da ya wuce tsofa da tunanin mutuwa yau ko gobai" girgiza Kai kawai no Nisha tayi dan ba wai ta gamsu bane dan yanayin da taga Barka ciki ba ta saba ganin ta haka ba infact ma bata taba ganinta cikin damuwa ba balle harta kaiga zubar hawaye kullum cikin walwala da raha tareda wasa da dariya ta ke, d'a n numfasa wa Nisha tayi tana fadi'n "Shikenan daman naje kitchen ne ban sa me ki ba shine nace bari na duba ki a bedroom din ki muje na ta ya ki aikin kafin Ammi ta fito idan kuma bakijin dadine sai na karba miki aikin "Tab rufamin asiri y'ar nan kin gani qalau na ke yanda baki da koshin lapia ko aikin ban isa ki ta yani ba kije kiyi kwanciyar ki kihuta" tura baki Nisha tayi tare da b'ata fiska tana fad'in "Nifa lapia ta kalau muje kawai Nisha tafad'i tare da juyawa tayi gaba Barka nabin bayanta tana murmushi hade da girgiza kai tana tunanin halin kirki irin na Nisha, karfe 8:30 Ammi tazo kitchen d'in ta tadadda Barka tare da Nisha sunyi nisa cikin aiki daga bakin door din kitchen din ta tsaya tana kallonsu ba k'aramin jin dadi ta yi ba kuma hankalinta ya k'ara kwanciyar ganin yanda Nisha ta sa ke sosai kai ka ce ba abunda ya faru hankali kwance su ke hiransu da Barka suna raha, "Sannun ku da aiki" Ammi tafad'i time din da ta karisa shiga kitchen din duk juyo sukayi suna kallon Ammi wacce ta ke ta zuba murmushi kamar gonar auduga, cikin nishadi Barka tashiga dagawa Ammi gaisuwa sai da suka gaisa kafin Nisha tashiga mika nata gaisuwan "Ina kwana antashi lapia" "lapia qalau kyakykyawan y'ata ya kwarin jikin? ashe har kinfito kuma kika shiga wahalar da kanki" "Wallahi kinga nima sai da na ce ta bari taje tayi kwanciyar ta ta huta amma taki kinsan mutumiyar ta ki akwai son aiki" Barka ta karbi maganar murmushi Ammi tayi gamida shafo gefen face d'in Nisha tana fadi'n "Allah dai yamiki albarka but tafi wayance shashashon da basu da aiki sai bacci da danna phone zanga ya zasu kare da mazajen nasu idan basa bukatan y'an aiki kamar yayansu" dariya Barka tayi tana fad'in "Aiko dai" Nisha dai shiru tayi tana murmushi wanda bai kai zuwaci ba because yanzu bata da aikin da ya wuce murmushi yak'e ko dariyan dole saboda k'wata k'wata hankalinta ba akwance ya ke ba kwai dai danne zuciyarta ne karta nuna damuwarta afili tasasu cikin damuwar su ma, Ammi kallon Barka tayi tana fadi'n "So fatan breakfast ya zama ready? but zanje nayi wanka na shirya asamar min da breakfast please" "To ba damuwa yanzu kuwa" Barka ta amsa cikin b'arin jiki irina karb'an umar nin nan, daga haka Ammi ta juya ta fice daga kitchen d'in, ba bata lokaci Nisha da Barka suka shiga gabatar wa da Ammi breakfast d'in ta bisa dining table guraren 9 Nisha ta zame daga kitchen d'in ta fito tanufi hanyar fita daga parlourn. Side din Ajmal ta nufa security da ke can gefe ganin Nisha na karisowa yasa ya mike da sauri ya shiga kiciniyar bude mata door din parlourn sai da tayi masa sannu kafin ta sa kafa tashige, shi kuwa security sai zuba murmushi yake harda na sayarwa kafin ya maida kofar ya rufe, bakowa cikin parlourn shiru kakeji kamar ba masu rayuwa ciki, direct kitchen ta nufa yau ta ci sa'a bubu uban tarkacen wanke wanke da Heelah ta saba tarawa cikin kitchen d'in da alamar jiya bata musu mahaukacin girkin da ta sa ba ba da yanzu kaga kitchen kaca kaca da tarin wanke wanke, ba tare da bata lokaci ba tashiga gyara kitchen d'in ta tsaftace shi daga bisani tashiga daurawa Ajmal breakfast mai dan sauki because ta gaji sosai, Daga ban fitowa tayi ta dauki vaccum cleaner ta shiga tsaftace parlourn k'wata k'wata parlourn bai cika dutti ba kamar ba a zama cikin sa, tana ga mawa da parlourn sai kuma ta shiga haurawa upstairs, Bedroom din Aheel ta nufa tabude ta shiga wani murmushi ta sake har kullum dakin Aheel ya masifar burgeta especially kyawawan Teddy's d'insa masu kya da ban sha'awa duk ya watsasu ko ina har saman bed, karisawa tayi ta zauna bisa gefen bed din lokaci diya tasaki wani murmushi mai sauti big teddy bear d'in da Aheel ya yake kwanciya da shi lokacin shitaga ya sanyawa Teddy bear d'in shi dariya ne ya kufcewa Nisha tare da daukan teddyn tana kallo, daga bisani ta rungume Teddyn kafin ta maida shi ta ajiye nan tashiga g'yarawa Aheel shin fidarsa tareda tattare masa kayan wasa da Teddy's d'insa guri guda kafin ta fito ko door d'in Ajmal ba ta kalla ba balle tayi tunanin ta shiga ta g'yara du ba da gargad'in da Heelah tayi mata akan shiga bedroom d'in mijin ta so duk randa tayi katari ta shiga tofa sai d'an buzun ta shiyasa ma ta dawo downstairs ta koma kitchen domin ci gaba da aikinta , Guraren 9:35, motar Ajmal ya sako kai cikin gidan time din da mai gadi yabude masa geat sai yayi parking kafin ya fito ya nausa kai cikin side din shi har security ya taho da niyar bude masa door Ajmal ya dakatar dashi sau da dama yakan hanasu yi masa duk abunda yasan zai iya wa kansa tofa yafi gane yayi da kanshi shiyasa bude masa door mota ko door din parlourn ko wani rakiya private bai cika son amasa hatta door din office d'insa da hannunsa yake budewa baya bukatar taimakon kowa sai dai irin wani taron biki ko taron siyasa ko wani taro na musamman da zai kasan ce awajan to nanne yake bukatan girmamawa kasan cewar shi shugaba koma shararren dan kwangila,. Yana shiga parlourn saman table d'in parlourn ya ajiye key d'in motarsa tare da phone d'insa daga bisani shi kuma ya zauna bisa duguwar sofa ya mike yana sauke ajiyar zuciya remote ya dauka ya kunna television, dai dai time d'in da Nisha ta fito daga kitchen hanunta dauke da tray d'in abincin ganin Ajmal da tayi zaune bisa kujera ya kurawa TV ido yana kallon News channel, shi kuwa jin motsin mutum ta ba yanshi ya sa shi ju ya wa suka hada ido . Kallon kallo suka shiga yiwa juna daga bisani Ajmal ya dauke kai ya maida shi kan TV yayin da ita kuma Nisha tashiga ta kowa ahankali ta kariso tsakiyar parlourn tare da ajiye tray d'in abincin bisa table kafin ta dago kai ta kallai shi. "Ina kwana antashi lapia?" Kamar bazai amsa ba amma kamar wanda akasa dole daker ya motsa baki ya amsa mata da "Fine" Mikewa tayi da nufin tashi ta fita but sai ta ji ya ce "Zo nan" Jiki asanyaye Nisha ta dawo ta t'suguna ta sauraron mai zaice, "Mai yasa kika daina g'yara bedroom d'ina" Ajmal ya tambaya yana tsareta da ido daker ta iya motsa labenta wajan fad'in "Am., damman Aunty Heelah ce ta ce karna sake shiga inba haka ba zata karya kafata" Nisha tafad'i kanta sun kuye, saura "Nina saki aikin ko ita ?" Ajmal ya tambaya yana b'ata fiska tare da hade gira, cikin rawar murya Nisha ta amsa da "Kai.,kkaine" "So kar nasake miki tambaya akan hakan " "To" Nisha ta amsa tana g'yada kai nan yayi shiru na dan wani lokaci bai sake magana ba ita kuma Nisha kanta na sun kuye jin shiru ya sa tayi tunanin ya gama korafin nashi hakan yasa cikin hanzari Nisha ta sake mikewa da shirin barin parlourn still sai ji tayi ya sa ke fad'in "Come back ban ce kitafi ba" Ajmal ya fad'i yana hararota , cike da k'osawa Nisha ta dawo ta kuma duk'awa ba karamin ga jiya tayi ba tana bukatan ta huta but ya tsaida ita yana mata surutai gaba dayaa sai taji haushinsa ya kamata duk abubuwan da take masa ba gani yake ba, jin knocking anturo door yasa Ajmal da katawa daga maganar da yake kokarin yi ya kurawa door din ido don ganin wa ke shigowa haka babu excuse. Doctor fu'ad ne ya turo door ya shigo bakinsa d'auke da sallama ganin haka yasa Ajmal g'yara zama time d'in da doctor fu'ad ya karisa shigowa ya nemi guri ya zauna face d'insa cike da fara'a yana kallon Ajmal da Nisha wacce tayi sunkuye da kai tana d'urk'ushe saman carpet tayi ladab " Yallabo'i amin afuwa nashigo babu karban izini Doctor fu'ad yafad'i yana kallon Ajmal wanda shi d'in ma shi yake kallo, Ajmal bai ce masa k'ala ba dan yasan halin doctor fu'ad ko yaushe cikin tsokana da wasa yake " Ina kwana?" Doctor fu'ad ya tsinci y'ar siriruwa muryan Nisha tana mai d'aga masa gaisuwa cikin kankan da kai . " Lapiya qalau ya jiki naki " Doctor fu'ad ya amsa yana mai tambayar ta dagowa tayi ahankali kafi ta amsa masa da cewa "Da sauki" " but now naje duba ki aka shaida min kina nan shine nabiyo naga yanayin jikin naki but alhamdulillah naganki garau dake masha Allah" murmushi kawai Nisha tayi masa tana g'yada kai becauseause ta kosa ta tafi shikuwa Ajmal mamaki maganganun doctor fu'ad yayi because dama tambayar da zai mata last kenan, Ajmal komawa yayi ya kuma manne wa bayan shi da jikin sofa yana kallon Nisha karfin yayi gyaran murya hade da fad'in " Sai nace ki zuba abincin" mamaki Doctor fu'ad ya shigayi ganin mulkin mallaka da Ajmal ke yiwa marainiyar Allah sid'i sid'i Doctor fu'ad ya ga Nisha tamike a sanyaye ta nufi kitchen wasu plates da spoons Nisha ta kuma dau kowa ta dawo ta bude foodflast tashiga serving dinsu wani daddadan kamshin na musamman ya shiga gauraye parlourn fried chips with plantain and vegetables soup with roasted chicken ga sandwich with pancake gefe kuma ga lemon iced tea Nisha sai da ta gama serving din ogan nata kafin ta janyo wani plate din tasoma kokarin serving din doctor fu'ad "No karki wahalar da kanki kibarshi kawai zanyi serving da kaina tunda kin sallami mai gidan naki ya wadatar" wani kallo Ajmal ya dago yabi doctor fu'ad dashi kafin ya maida hankali kan abincin sa ya suma ci , "Za,.zan iya tafiyaiki " Nisha ta tambaya tana kallon Ajmal yayinda ya kai yayinda ya kai lallausan pancake bakinsa g'yada mata kai kawai yayi ba tare da yayi magana ba cikin hanzari Nisha tamike ta fice daga parlourn sai turo baki ta ke shi kuwa Doctor fu'ad an barshi da mamakin abokinsa ganin yanda ya tusa yar mutane gaba yana bata umarni cikin isa da gadara wai dan ma bai san matsayinta gareshi ba ,yarinyar akwai hankali da nitsuwa kuma ba maisun ha ya niya bace balle yawan magana ,. sam baya so Ajmal ya dauki halhakinta da yawa because yasan halin Ajmal na ko in kula especially yanda yaga yamai da yarinyar tamkar mai masa hidamane y'ar aiki kawai yana fatan akan yarinyar nan Ajmal ya fahimci maiye soyayya kauna da kuma yadda akejin shaukin wadda akeso ya fahimci rayuwar aure da kuma ma'anarta, a iya sanshi da Ajmal duk bai fahimci wadannan a baben ba kuma ya kasa tsayawa ya fahimta , haka ma ta ban garan aurataiyya bai daukeshi da wani mahimmanci balle ya tsaya ya fahimci yanda alamuran suke tafiya but ya tsaya ya na ta wahalar da kanshi "What are you thinking?" Wani dugun numfashi doctor fu'ad yaja yana mai kallon Ajmal wanda ya tsare shi da tambaya kafin ya saki wata murmushi yana fadi'n "Nothing" daga nan ya kai hanu shima ya dauki lallausan sandwich wanda ya ke hango shi tamkar zane "Tun shigowa na hancina ya cikaro da kyakykyawan kamshin abincin nan nasan cewa ba gama garin delicious ake gabatar waba ashai amaryar muce ta karbi office " Doctor fu'ad ya fad'i yana kallon Ajmal ta gefen ido kafin ya danna daddad'an sandwich cikin bakinsa. shi dai Ajmal har wa yau bai kullashi ba dan yasan Doctor fu'ad inya fara zuba kamar fanfon kasuwa yake bakin ba burki kuma cikin maganarsa ya dinga sa wasa da tsokana aciki. "Bana manta wani delicious da naci time da Raheelah ke amarya only one spoon but ranan kwana nayi ina zaryan toilet I hope HAJIA karama ta iya kayatattun delicious irin haka like Nisha ba girman parlour ta ke kamar Heelah ba " Doctor fu'ad ya sauka layi sai barin magana yake maybe dad'in girkin Nisha ke sa shi wannan zuban, Ajmal bai san sannan da ya saki wani murmushi mai sautin ya na kallon doctor fu'ad da ke ta kada kai ya na ta faman surutu shi dai a iya sanin shi k'anwartashi ba ta da mara ba da Heelah duk ba abunda suka iya sai dai ta iya zuban surutu kamar shi "Please kaci abincin kadaina surutun nan haka" murmushi doctor fu'ad yayi gamida da dan buga head d'insa kadan yana fad'in Sorry fa dad'in girkin ne yasa nake ta surutu ban sani ba , honestly mutumi na yarinyar nan ta tsa moka daga k'angi ta taimake ka yanzu kayi bye bye da ordern restaurant, cikin ta kaici da maganganun Doctor fu'ad yasa Ajmal da katawa da cikin roasted chicken din da yake ya ya b'alli tissue paper ya shiga goge hannayenshi kafin ya koma ya jingina Jikinsa da kujeran yana hararo Doctor fu'ad ' wai ta tsamoshi daga k'angi ta na taimakesa, shi inbama na sihar da Ammi ta yi masa akan yarinyar da kuma nuna tana bukatan mu amalarsu tare ba da mai zaisa ma kafarta ya fara tako side din shi tun kafin zuwanta yana rayuwarsa ba cikin k'angi ko taimakon wani ba zuwanta ba zai canza komai ba kuma k'angi da taimako da yake fadi'n duk wani bauta ko hidama da take da shi biyanta zaiyi dan baya bukatar hidimar da ta ke masa a kalle shi a fiskar taimako ko fita daga k'angi,' Doctor fu'ad ganin kallon da Ajmal ke yi masa yasa shi ya saki sakin murmushin kasa kasa "Naji kana tambayar ta ya jiki mai ya sa me ta" Ajmal ke tambayar doctor fu'ad because kasan cewarta a k'ark'ashisa zaiso sanin damuwa ko matsalarta, zame hanu Doctor fu'ad yayi shima ya shiga goge hannayenshi kafin ya gyara zama yana fad'i "Eh to da farko dai a sumammiya naje na sa me ta Ammi da kammala suna ne suke kaiwa da kawo bisa kanta but da na duba ta bakomai bane fa ce tsorita ne da firgici duba da yanda zuciyarta ta ke bugu yana kaiwa da kawowa shiyasa mu likitoci muke da d'a wayar da kai ba kowace irin magana akeso adinga fad'awa mutum kai tsaye ba ko ya tsinci magana kamar daga sama ma'ana baiyi zato ko tsammanin jin maganar ba especially mutum mai saurin razana tsoro ko firgici ba kasan halinda zai fada ba like ita Nisha ,. " Ammi Kamal? su sukayi coursing matsalar kakeso kace" Ajmal ya tambaya yana mai tsare doctor fu'ad da manyan idanuwansa "Kusan haka but Ammi ta fada min dalilin faruwan hakan wanda lamarine da ya shafi tsakanin ka kai da Nisha , is very confident Ajmal ya gyara zama yana fad'in "Ina jinka banaso kana tsayawa yayin maganar ka dunkule min zance cikin kalama daya," murmushi Doctor fu'ad yayi gamida fadi'n "Bana tunanin zai dunkulu ta kalma daya shi yasama banso na sanar dakai yanzuba because banzo da Shirin yi maka bayani yanzu ba nayi tunanin wa re wani time da ban dan tattauna maganganun because tattaunawar is very important cikin rayuwarku kai da ita but why not na sanar dakai yanzu nasan zaka saurareni kuma zaka fahimce batuna kuma ka dau shawaran da zan baka, ". Ajmal ya k'osa ya ji kan zance but shi kuma doctor fu'ad sai dugun ba yani yake da ma fa matsalar su kenan likitoci nan ba zasu tsaya su maka zance kai tsaye ba sundinga kwane kwane kkenan harsai mutum ya hasala "Look idan zancen ba fa'idar na sani kabarshi kawai ina da abubuwan yii" Ajmal ya fad'i ciki takaici da bacin rai ya mike yana kokarin tafiya cikin hanzari doctor fu'ad ya kamo hanun Ajmal yana fadi'n "I'm sorry mutumina zauna na maka bayani" because yasan halin mutumin da saurin hasala komawa Ajmal yayi ya zauna cikin hade gira ya ce "I'm hearing you talk " cikin na tsuwa tare da kawar da wasa alamarin doctor fu'ad ya shiga zaiyyanu zantuka da labarain da ya samu da Ammi game da batun auransa da Nisha,.. ______Tun bayan da Nisha ta fito da ga side din Ajmal ta nufi sashinsu a kokarin ta na shiga parlourn time d'in kamal shima ya sako kai da nufin fitowa nan suka game da juna gefensa dauke da Nabilah wacce ke biye da shi , ganin su da tayi sai da kirjinta ya d'an buga. ja ba ya Nisha ta yi ta matsa gefe kad'an tana kallonsu, Kamal fiska dauke da murmushi ya suma tambayar ta "My sister! Ke muka shiga dubawa yanzu but ba mu tadda ke ba. " Ya jikin naki" Kamal ya ya tambaya yana duban Nisha cike da murmushin nasa da baya yanke sai wani ikon Allah "Da sauki Nisha ta masa cikin sanyin murya, jinjina kai kawai Kamal yayi yana fadi'n "Masha Allah haka akeso" kafin ya juya ya kai kallonsa ga na Nabilah gamida fad'in "Ni zan wuce sai na dawo take care of yourself" g'yada masa kai Nabilah tayi tana fadi'n "Allah ya tsare" Daga haka Kamal ya wuce ya nufi compound d'in gidan daidai parking space ya shiga motarsa tare da yi mata key mai gadi yabude masa geat yafice. har yabar ha raban gidan Nisha binshi da kallon ta fad'a tunani ba k'aramin mamaki Kamal ya ba ta ba kwata kwata ba wata damuwa kan face d'insa gani tayi duk tafishi shiga da muwa da kad'uwa, but shi hankalinsa akwance yake kamar ma ba shi da wani damuwa. 'kodai kwai da ma wasa yake da hankali da tunaninta ba wani sonta ya ke ba but ya cusa mata soyayyarsa da ra'ayinsa da sha'awar fara sabowar rayuwa tare da shi ' jin anruko hannayenta yasa ta dawo cikin hankalinta da tunanin da ta ta fi time din idonuwanta har sun ciko da k'walla tab. Nisha kallon Nabilah tayi wacce ke rike da hannayenta duka biyu tana kallonta cike da murmushi tana fadi'n "Idan ban ta kura kiba inaso mu dan tattauna wasu maganganun da ke amma fa in ban shiga time d'in ki ba, girgiza kai Nisha tayi tana fadi'n bakomai" still Nabilah ba ta da ke hannun Nisha ba fiiiii Nabilah ta ja hanun Nisha suka nufi sashinta. Ko bayan da suka karisa shiga parlourn Nabilah ta zaunar da Nisha bisa kujera kafin Nabilah ta koma dining area ta hadu musu coffee ta dawo ta mikewa Nisha cup d'in zazzafan coffee shekeke Nisha ke bin Nabilah da kal kafin ta karbi cup ta rike still idanuwanta ba su dainabin Nabilah da kallon mamaki ba ita kuwa Nabilah sai murmushi ta ke ta zubawa Nisha kafin itama ta nemi guri kusa da ita ta zauna tare da kai coffee d'in cup bakinta. Sai da ta kurb'a zazzafan coffee d'in kafin ta kalli Nisha wacce ta sa ke baki ta na kallonta kamar hoto ta kasa shan coffee d'in da Nabilah ta ba ta "Ki sha mana kin tsaya kina ta kallona kamar ba ki sanni ba "Nabilah ta fad'i gamida murmushi ta cigaba da shan coffee d'inta kafin itama Nisha ta kai bakinta jikin cup ta suma sha. dan kadan Nisha ta shaa ta sauke cup d'in ta sa ke Kai kallonta ga Nabilah ta na son jin dalilin da yasa ta jawo ta nan da kuma maganan da ta ce zasu tattauna, Nisha muryan Nabilah taji ta suma magana da cewa " Tun bayan da naji tsakaniku da da ya Kamal na ji duk ki yai yan da na ke miki ya kau infact ma ko auranki ya bijiro da shi bazan wani damu sosai ba duk da kasan cewa ta macece mai kishi sosai especially akan abunda nakeso kuma nake matukar kauna ranar. farko da na fara ganinku tare a guest house d'in Daddy naji kishi sosai raina kuma ya baci harma nayi tsammanin wani abu tsakanin ku wanda kuma bai kamata nayi wani zargiba but time din idona yarufe naita fadan maganganun da bai da ce na fa de su ba akan zargin da ban da hujja ko tabbaci, Sam awance lokacin banason ya Kamal fada cikin yanayinda ya Kb yayi nisa aciki duk da abaya ya dauki wani ban gare irin na rayuwar Kb,. Juyowa Nabilah tayi tana fiskanta Nisha ta cigaba da fadi'n Kasan cewa na taba rayuwa cikin gida nan wanda shine sana diyar haduwata da Kamal time din da ya dawo daga American HAJIA ta sa aka shirya kayataccen waliman taron dawowar jikokinta dakuma murnar haduwar ahalinta, Kamal da KB makaranta daya suke karatu but ba wanda ya San Dan uwansa ko ya taba ganin hoton dan uwansa balle su shaida junansu.sai bayan haduwarsu aliyafar ne sannan ne suka shai da juna nima sannan ne na ga ya Kamal mukayi amanna da juna kasan cewa ina rayuwa cikin gidan su shiyasa muka shaku alakarmu ta kara karfi sosai wanda kowa ya fahimci hakan. Kamal mutum ne mai fara'a sosai da sun wasa tsokana da ban nishadi wanda shiyasa na kara sa ke sosai na fara mance duk wata damuwa na Kamal ba kamar babban yayansu Wanda ke da fiskar fusatattu sam bayi da fara'a sai mutum ya ci sa'a yake iya tuzali da murmushi ko da dariyansa ballai ma ba na zaton yana murmushi balle wani dariya shiru yake maganan bata da mai Shi ba infact ma duk inda yake da hayaniya ko ake surutu wajan tofa baya zama yafi kadai tuwa shi ka dai Sam ba yi da son ha yaniya ni tsoronsa na ke ji sosai ko ido ba na yarda muhada da shi time d'in da nake rayuwa gidan nan but karfin hali irin na Aunty Heelah haka ta dinga cusa kanta cikin rayuwarsa da nuna sha'awar soyayyarta gare shi amma shi sam baya bata fiska ita kuwa Aunty Heelah sam babu kunya cikin idonuwanta zaman turai ya ba ta ta duk wata kunya da akasan ya mace na dashi to ga Aunty Heelah kam babu infact ma ba ta sanshiba. Dabi'un da Aunty Heelah ke yi cusa kai ba kwarjini kiri kiri ba kunya haka take binshi wani sa'in abun har kunya ya ke bani ,ba ni kadai ba ma kusan kowa yana hankalce da tarkon da ta fad'a duk da sunsan wannan cusa kai da shige masa da ta ke baya waiwayarta ballai yasan halin da ta ke ciki because ba yida lokacinta harkan gabanshi kawai yake kamar baisan da lamarin ta ba amma Hajj mama duk ba ta yi la"akari da ta ban garansa ba yana da ra'ayinta ko aa hajia ta sa aka shirya bai konsu duba da yanda Aunty Heelah ta k'walla fa rai da shi ta nuna sha'awar so da kaunarta gareshi,. Ya Ajmal duk da bai nuna interested akan Aunty Heelah ba but bai nuna ya na da ja ko musu a kan abunda HAJIA ke kokarin yi ba time d'in da Aunty Heelah ta kammala karatunta a kasar England aka tsaida ranar auransu already ya Ajmal ya Kammala masters d'in shi dan haka aka tsaida ranar auran tare da na Aunty Hafsatu kanwar ammi acewar hajia tunda har mahaifina zai iya cin amanarta yayi wani auran har asamu karuwa amma ace bai iya fada ma ta ba kuma bataji labari ba to yanzu bashida ikon da zai da katar da ita daga hukunci da tayanke na auran Aunty Hafsatu koya amince ko bai amince ba yana so ko baya so duk da abaya ya bijirewa hakan ba da son rantaba, bayanda da Aunty Hafsatu ta kuma gidanmu da zama amatsayin matar Abu to bayan wasu lokaci jima na koma gida na cigaba da da Auntynsa hafsatu. Aunty Hafsatu tana da dadin zama sosai ta rike ni bisa amana tana kula Dani sosai tamkar wacce na fito daga cikinta kulawar da take ba ni ko mahaifiyata tana raye iya kulawar da zata ban kenan, ba kamar sanda na ke hanun mommy ba time d'in jinke gidan kamar ba na mahaifina ba kamar ba cikin gidan na girma ba gidan ya zam ta tamkar akan k'aya na ke saboda ita time din ko yan aiki hana mahifina tayi ya kawosu ninake komai a gidan ga tsan g'wama da kyara na zama tamkar bora acikin gidan, wanda kuwa ba haka ta kewa su Aunty Heelah da yaya KB ba duk da nayi farin ciki da ban kasance ta bani irin tarbiyan da ta taso da yayanta ciki ba gaba daya ta ga ma sangartasu ba ta k'wab'ansu duk abunda suke so shi sukeyi walau mai kyau ko mara kyau . Sun kuyar da kai Nabilah tayi saboda wani hawayen da ke kokarin zubu mata na tuna wahalar da ta sha ahanun mommy gaba daya Nisha jikinta sai ya kara yin sanyi gaba daya tausayin Nabilah ya kamata wato kowa da yanda ake jarabashi arayuwa, parlourn ne ya dau shiru ba wanda ya yi magana cikin su jim kadan Nabilah takuma dagowa ta kalli Nisha tana fadi'n Kiyi hakuri bana kiraki Dan na baki labari ko surutu abunda ya shafi rayuwa ta bane sai d'an kinzama daya daga cikin family gidan nan kina da right din kisan wani ban garai da yashafi ahalin nan da kuma yanda rayuwar familyn ke gudana, because Kamal ya bani labarin komai daran jiya ganin yanda hankalinsa ya tashi sosai ya kasa nitsuwa wanda nima yasa nakasa nitsuwar hankalina ya kasa kwanciya har sai da ya labar ta min abunda ke faruwa matsayinsa na mijina kwantar masa da hankali tare da bashi shawarwarin da zai Kara matar dashi damuwarsa ya manta da ya cireki daga zuciyarsa ya manta ya ta bata jin wani abunda ya Dan ganci soyayya da ke because ke ba rabunsa bace ke matar yayansa ne yanzu alkar ku zaima yanzu yan uwan ta ka ne kawai ba batun so ko wani kauna ba. Sannan ke ma ina mai baki shawara ki mance da Kamal ki fiskanci rayuwa auran da zaki fara da wanda zai zama shine jigo yanzu cikin rayuwarki duk da kin tsinci rayuwar auranki ta wani siga da ban kuma ina tayiki alhinin hakan ina kuma taya ki bankincikin kasan cewar Aunty Heelah amatsayin wacce zaki zauna da mijin ta ku zama kishiyoyin juna., Ajeemal Page70 By oum amreesh Page 72 _______Nasan halin yar uwata sosai tamakar yanda nasan yunwa cikina ina mai baki shawara ki dage da addu'a sosai har lokacin da Allah yasa ta fahimci ma tsayinki awajan mijinta , ina fatan Allah ya yayyafawa lamarin ruwan sanye komai ya tafi daidai cikin kwanciyar hankali because nasan Aunty Heelah da kuma hali irin na ta, akarshe nima zan sanyaki cikin addu'ata kuma ina rokonki da kidaina guduna haka nan nima ki dauke tamkar yanda kika dauki su Reeda nima ki daukine daya daga cikinsu because muriga munzama daya yanzu Nabilah ta fad'i ta na riko hannayen Nisha,. jiki a sanyaye Nisha g'yada kai tare da sunnar da kai kasa maganganun Nabilah duk ya sa ke kashe mata jiki tsoron ta ya k'araru matuk'a bata san ya zata fara fiskantar wannan k'addaran auran ba sam ji ta ke ina ma duk wanda nan abubuwan da ke faruwa da ita ya kasan ce mafarkine ba gaskiya ba da kuwa inta farka bazata sake komawa wannan baccin ba girjinta sai bugun goma goma yake da ga Heelah har mijin nata tsoron su ta ke ballai kuma yanzu da ta ke kokarin fara rayuwa cikinsu wani irin yanayin zata tsinci kanta a tare da su a tuna ninta dukansu babu mai rang'wamen fiskar da zataji saukin mu'amala dashi. rintsa ido idanu Nisha tayi tana furzar da wani irin zazzafan ajiyar zuciya ta shiga karanto wasu addu'oi a hankali tana jin zuciyarta dan sanyi kadan kad'an kamar ana yayyafa mata ruwan sanyi, ganin halinda da ta shiga yasa Nisha ta bawa Nabilah tausayi nan ta cigaba da tausan ta tare da bata shawarwari masu kyau wadan da zasu amfane ta, haka wunin yau Nisha ta yi shi cikin sanyin jiki har wani zazzabi zazzabi ta ke ji ya dawo mata, da dare bayan sun kammala dinner sun zauna bisa parlour suna fira kamar yanda suka saba, wanda nan Ammi ke shaida wa su fareeda ce wa Saturday and Sunday suna da private class na koyan girke-girken zamani kasancewar bikinsu yana ta karatuwa kuma ba abunda suka iya na ciman zamani ballai na gargajiya wacce zasu nishadantar da mazajensu Dan haka ta yanke shawaran kaisu akoya musu delicious kala kala saboda afita kunya shi ya sa ta ware wadan nan kuwanakin because sauran lokutan basu da lokaci saboda karatunsu, ranar murana gurin su Fadeelah ba a cewa komai. Suna tsaka da firanne wayar Nisha ta shi ga k'ara alamar kira nan Nisha ta kalli screen d'in wayar salma ce ke kira duk duk da kasan cewar tun safiyar ranar ta ke ganin k'iran ta but takasa dagawa because bazata iya magana dan ta San da ta fara magana zata fashe da kuka shi ya sa ta ke gudun ta d'aga mata hankali ana tsaka da shirin bikinta dan ta san duk wani damuwarta damuwar salma ne haka duk damuwar salma da muwarta ne sun d'auki juna tamkar jini d'aya sam basu yi tsammanin rabuwa haka lokaci daya ba, abaya da suke rayuwa tare basa kwana d'aya ba su ga junansu ba ba tare da dalili mai karfi ba amma gashi yanzu sun rabu sai ayi wata basu ga junaba sai awaya kawai suke haduwa , yan zunma kifa wayar ta yi gefenta kanta kasa ta ci gaba da murza Dan ya tsanta tana ta karatun zuci "Ba kiran ki ake awayar bane?" Hajia ta tambaya tana kallon Nisha, Nisha dagowa tayi ahankali ta kalli Hajia gamida g'yada mata kai tana fadi'n "Eh kirane " "Waye ya ke kira ki ? d'auka ki je bedroom ki amsa kiran mana kar mu da meki da ha yaniyar mu" ba musu Nisha ta dauki phone d'inta ta nufi bedroom tareda neman guri ta zauna ta shiga kiran salma time d'in idanunta haar sun kawo ruwa, ba wani dugun rigin carab salma ta dauki wayar ta suma magana. "Haba Nisha why ba kya picking call d'in sai kinga dama duk kinsa hankalina ya tashi wai mai take faruwane "salma ta shiga jerowa da Nisha tambayoyi dan ko sallama ba tayi ba. "Bakomai" Nisha ta amsa mata can kasan ma koshinta, "Ko bazaki samu zuwa bikin nawa bane kika kasa fad'a min" "Eh " Nisha ta ce time d'in da ta ke dab da fashewa da kuka shiru salma tayi na Dan wani lokaci ba wanda yace kala acikinsu. "Nisha kodai dunyar tayi miki dad'in da zaki iya watsi danine haka daga jiya zuwa yau na kiraki ya fi akirga but ba kya picking yanzu koma naji yanzu kuma da muke magana sai na fahimci kamar baki son magana na da meki , ko dai wani laifin na miki duk da nasan yanzu munyi nisa da juna bana tunanin hakan, dan wani abune ya ke faruwa da ke ya kamata ki fad'a min because ni abokiyar fad'a wa matsalar ki da damuwarki ne ko abunda ya shafeki please ki fad'a min in wani abunne ke da munki" nan fa taji Nisha saki wani kuka waiwai kamar karamar yarinya, ba k'aramin ta shin hankali salma ta shiga ba jin yanda Nisha komai ta ke kuka kamar wata k'araman baby nan Salma ta rude ta shiga tambayarta ba sanin kukan but ba amsa, tambayar duniyar nan salma tayiwa Nisha amma ta ki kulata, nan Salma ta ka tse wayar daga haka Nisha ta kwanta saman bed d'in ta ci gaba da koke koken nata a hankali ba tare da sautin ya fito anlura da halinda ta ke ciki ba. Sai da ta yi kukan ya isheta kafin ta g'yara kwanciya dan ko kayan jikinta ba tasamu daman canzawa ba taja blanket ta rintsa ido tana sauke ajiyar zuciya kanta harya suma ciyo saboda kukan da ta sha yau ko tunanin kiran Ajmal taji ko yana da bukatan wani abin duk da tasan bai cika bukatan wani abin da dare ba infact ma bai cika dawowa da wuri ba koma ba dan hakan ba bazata bi ta kanshi ba, ta masa na Allah duk da ba wani koshin lapia garai ta ba, da safen nan ba k'abisa da aramin gajiya tayi ba ga kuma haushinda ya kuma bata tana cikin wannan yanayin har bacci b'arawo ya sace ta, washe gari karfe gusan 10 Nisha ta kammala ta shiga jerawa dining table kamar yanda ta sa ba parlourn shiru sai karan TV da ya ke ta aiki sai kuma ita da ta ke ta faman Kai kawo tsakanin kitchen da dining area tana shirya breakfast ,. Nisha harta gama komai ta kimtsa ko ina ba kwalkiyan ko mutum daya da taji duk da tayi tsammanin tun shigowa ta zata ci karo da Heelah ko ta ji motsin ta but sai ta ga sabanin haka wanda hakanne ya bata daman yin aikinta cikin na tsuwa, ta nufi upstairs direct bedroom d'in Ajmal ta nufa ta g'yara masa kamar yanda yayi korafi, tana zuwa bakin door d'in ta shiga yin nocking a hankali bugu daya zuwa biyu ba ayi magana ba hakan yasa ta murda handle door d'in ta ku tsa kai bakinta dauke da sallama ta karisa shiga, . bedroom din ba kowa ciki duk da anrage light d'in dakin ba komai ta ke iya gani ba d'an haka ta karisa cikin tsakiyar dakin ta nufi switch light d'in ta kunna nan haske mai kyau ya gauraye bedroom d'in nan fa idonta ya hango mata Aheel da ke kwance yana sharan bacci yana rugume da pillow kamar kamar zai shige ciki ya rungume shi tsam ajikinshi Nisha ba ta san sanda ta saki murmushi ba tana mai kallon kyakykyawan face d'in Aheel mai kaman antsaga kara da papanshi, karisawa tayi ta zauna bisa bakin lallausan bed d'in sai da ta lumshe ido tsabar taushi da laushin bed din, cike da murmushi Nisha ta kai hannu ta shafo gefen face d'in Aheel, kamar wanda ya yake jira a taba shi aiko tar ya bude idonsa bisa face d'in Nisha Aheel na ganij Nisha zaune gefen shi tana ta zuba masa murmushi, shima washe mata baki ya shigayi cike da farin ciki ganinta ya fad'a jikinta tare da rungume ta, cikin farin ciki da kyawan yaron Nisha ta dinga shafa bayanshi a hankali kafin ta dan zame jikinta daga nasa ta shiga tambayarshi "My little yau ba school ne naga Kanata bacci har wannan time d'in, "washe baki ya kuma yi yana fadi'n "Laaa Aunty jiya fa mukayi hutu, kuma hutu mai yawa aka bamu har 3 weeks Aheel ya fad'i ya na nuna da yan tsun hanunsa uku murmushi Nisha ta tayi gami da fadi'n "Good tasu muje to baccin ya isa haka" , nan ta juya masa baya alamar ya hau bayanta shikuwa cikin zumudi ya dale bayan Aunty Nishansa tare da sakalo face d'insa gafen wuyarta yana ta dariyan jin dadi daga haka suka fice daga parlourn bedroom din Aheel suka nufa ta sa ya cire wannan tausasun kayan baccin da ke jikinsa ta bashi dan k'aramin towel ya daura yashiga bathroom domin ya wanke jikinshi yayinda ita kuma ta nufi wardrobe ta dauko masa kyawawan kaya t shirt and jeans rigar white color sai black jeans tana jin yanda Aheel ke ta wasa cikin toilet Dd'in yana tsalle tsalle yana wasa da ruwa ganin bayida niyar fitowa yanzu yasa no Nisha mikewa tashiga toilet d'in ta taimaka masa yayi wankan kafin suka fito ta kimtsashi tare da sanya masa kaya kafin ta jawo hanun shi suka nufo downstairs. Dining table ta nufa dashi ta zaunar da shi ta dauki plate ta sanya masa breakfast duk abunda ya nuna ya naso shi ta sanya masa ta tura masa gabansa ya suma ci, daga haka ta zame jiki ta koma bedroom din.dining zuciyarta daya tunfi toilet domin fara wanke shi murda handle d'in tayi ta shiga , zaune yake cikin bathtub yayi tsam da ranshi idanuwansa a lumshemaganganun Doctor fu'ad sai d'a masa yawo cikin kunnuwa su ke sam ya kasa gas gata maganganun sa because yasan doctor fu'ad dasa zulaya cikin lamauransa in ba daga wajan su Daddy ko wajansu hajia ya ji bataun kai tsaye daga gare suba bazai taba gas gata hakan ba, idan kuma harta tabbata hakan lamarin bazai taba daina bashi mamakiba. ko Time d'in da aka aura masa Heelah ba waii dan ba yi da ikon hanasu ko da dakatar da su bane kawai ya kyalesune ya zuba musu ido ba wai dan ya rasa yanda zaiyi bane but hakan ba shi zai basu daman jogana masa wannan wata mace ba especially wacce baisan wacece ita ba bai kuma san daga ina ta ke ba ballai asan asalin wacce ita, turo door din toilet d'in da akayine yasashi bude ido da sauri don ganin wake kokarin shigo masa bathroom ba neman izini, Nisha ya gani ta shigo kai tsaye wacce itama da alamar ba ta lura da shi ba because toilet d'in yana da girma sosai tamakar parlourn wani gidan fiskarta dauke da fara'a takarisa gaban katafaran mirror da ke cikin toilet d'in da ya ke fara kallon mutum yayinda ya shigo tsayawa ta yi tana hango kanta ciki rabunta da ta tsaya ta kalli kanta madubi harta mance time d'in kallon kanta ta ke sosai tana karawa tare da shafo face d'inta ta jikin mirror ganin tayi har wani kumatu tayi kuma ta kara haske sosai. tabbas itama yau tayi mamakin yanda taga yanayinta ya canza gaba daya hutu ya zauna mata haka ta dinta juya lallausan hannayenta tana kallo kamar ataba jini ya fito time daya kuma fara'a ta ta dauke face d'inta ya koma face d'in jimami saka makon tunawa da maganar salma na cewa 'duniya yayi mata dad'in da zata iya mancewa da ita' duk da ba ta yi tsammanin wannan furcin daga gare ta ba because ita dai a iya saninta bawani jin dad'in da zata tsinci kanta aciki ta kasa tunawa da aminiyar ta kawar yarinta abokiyar cin mushe su kashe su bunne tare wasu zaffan hawayene suka gangaro mata kafin cikin hanzari ta shiga goge hawayen ta suma waige waige don fara aikin da ya kawota kar ogan nata ya zu ya taddata anan tana ta karanta wasikar jaki, wani ihu Nisha ta kawo sake tana sallati gamida rintsa idanunta because ganin Ajmal time d'in da ya mike ya na kokarin daura towel bisa waist d'insa tana kuma yin baya ganin Ajmal tsaye cikin bathtub yana kokarin daura towel bisa waist d'insa, baya Nisha ta kuma yi da sauri idanuwanta a rintsai jikinta sai k'yarma ya ke a aikuwa sai timmm kakeji ta zame santsin tailed ya zamar da ita a zafafe ta ta kuma mikewa tanufi door sai da ta bude ido kafin ta murda handle d'in tafito ta watsa aguje ta fice. Ajeemal Story and writing by oum amreesh Page 72 Aheel na zaune bisa dinning table yana breakfast kamar yanda Nisha ta barshi sai ganin Auntynsa yayi tafito fuuu kamar wata mota ta wuce ta fi ce da gudu daga parlourn ko waiwaye ba ta yi Aheel bin ba yanta yayi da kallo tare da kai kallonsa upstairs dan ganin mai ta ke wa gudun dan ba k'aramin tsoro ta ba shi ba sai zare ido ya ke amma ba kowa da ke biye da ita nan ya shi ga zamowa daga kujeran da nufin bin bayanta but sai ya ji muryan mom d'insa ta kira sunansa wanda ya sa ya mai da hankalinsa garaita ya shiga washe mata baki tare da kokarin karisawa gareta yayinda ta ke sakkowa ta na sanyi cikin kananun kaya wata half vest sai d'an wani gajeren wando iya gwiwa ta tufke gashinta a tsakiyar kanta sai lilo ya ke bayanta ta yi kyau da ita, Cike da murmushi ta kariso ga Aheel ta re da sa hanu ta sun kuci d'an nata tana fadi'n "Good morning in this morning my love" Morning Mommy Aheel ya fad'i gamida kwantar da kai jikin mommynsa " What are you doing here" Heelah ta tambaya tana mai kallon Aheel ta na kuma kallon dining table d'in da kawata shi da kyawawan girke-girke kala-kala ta shaida wannan aikin Nisha ne nan ta shiga hararo abubuwan da ke jere bisa dining tana tabe baki nan Aheel ya shiga zamowa daga jikin mom d'insa kafin Heelah ta direshi akasa ta na kallonshi. "Mom taho ki zauna kiye breakfast Aunty Nisha na ne ta yi mana delicious mai dadi " ta ho ki zauna ke ma " Aheel ya fad'i cike da murna yana washe baki gamida jawo mata kujera alamar ta zauna but Heelah sai Jan wani banzan tsaki tayi tana tabe baki tana kallon Aheel da ke ta rawar Kai wai Aunty Nishansa tabdi. "Come and seat Mom" Aheel ya kuma fad'i yana kallon mom d'in nasa wacce ke ta faman hararo shi da shi da table d'in gaba daya tana fadi'n "Kai da Allah rabu da ni mai zan zauna na ci a wannan tsiyar Allah kaidai yasan hade haden da ta ke cikin girke-girken nan da ta ke tana jan hankulanku da tunanin ku ku ke ta wani ribibi a kanta ta ga ma siye zuciyoyinku da yin nasara a kanku to nikam na fi karfinta ta Allah ba ta mutum ba muna fukar banza kawai Heelah ta karisa fad'i hadai da jan wani dugun k'wafa zuciyarta ta sai zafi ta ke ita ta rasa ya zatayi da wannan yarinyar gaba daya ta shige mata hanci da k'udunduni juya baya tayi yayinda ta hade hannayenta a k'irji ta na kada kai ta na tunano irin hanyar da zatabi da Nisha, shikuwa Aheel shiru yayi jikinsa duk yayi sanyi ganin yanda mom d'insa ke ta surfa masifa akan Auntynsa duk da baisan inda zantukan na ta suka do sa ba baikoma fahimce ta ba. Shiru yayi ya na ta kallon mom d'insa da ke tsaye ta na ta kaiwa da kawowa ta kasa zama gefe guda kuma ya hangi papansa wanda ya ke sakkowa daga upstairs yana sanye cikin kyakykyawan black suit and black shoes sai bakin glass da ya sanya ya tushe idanuwansa, da gudu Aheel ya taho ya d'ale jikinsa time d'in da ya gama karisowa, cike da murmushin nan na shi Ajmal ya dago Aheel ya sunbaci kumatunsa kafin ya sauke shi kasa karfin Aheel ya ja hanun papansa suka zauna bisa dining table Ajmal ko kallon inda Heelah ta ke baiyi ba ballai ya San da tsayuwarta ya nemiguri ya ya zauna, Heelah tunda ya sakko ta ke binshi da kallo harya karisa dining ya zauna kafin ta tabe baki gamida matsawa kusa da shi ta ja kujera ta zauna ta na fad'in "good morning dear" "Morning" Ajmal ya amsa cikin cool voice na shi ya na mai kokarin kai hanu dan serving din kanshi cikin hanzari Heelah ta a ga je shi ta shiga serving d'insa shikuwa bai dakatar da ita ba because ya na bukan hakan , tana gama serving d'insa itama tayi serving kanta ta zauna ta tusa plate agaba tana ya mutsa fiska sai ka ce wanda aka ce ta ci dole gefe kuma Ajmal breakfast ya ke cikin kwanciyar hankali yayinda Aheel ke gefe shima sai kada kai ya ke time din da ya ke shan daddad'an yoghur fruit ya na santi wayar Ajmal ne ya shiga ruri alamar Kira wanda ya sa shi dakatawa daga breakfast din ya kai kallonsa ga phone din ya kalli screen din wayar dan ganin mai kira, sharewa yayi ya ci gaba da cin abincin sa Heelah sai mika wuya ta ke tana kokarin hango sunan da ke makale jikin screen din wayar dan ganin wanda ya uzura da kira haka shikuwa Ajmal ya ki kula wayar tana a jiye saman table daga karshe ma silent ya sanya wayar ganin an matsa da k'iran, Ajmal mikewa yayi gamida goge hannayenshi ya kamu kan Aheel ya sunbaci goshinsa yana fadi'n " take care of yourself " bye yana fadi'n haka ya dauki phone d'insa tare da key din motarsa cikin hanzari ya fi ce daga parlourn Heelah har ya gama ficewa daga parlourn ya kurewa ganita binshi ta ke da kallo tana tab baki , shi kuwa Ajmal yana fitowa direct parking space ya nufa ya shiga mai gadi ya na ganin fitowar da rawar jiki ya tashi yabude masa gate haka Ajmal ya zo ya sa kai ya fice mai gadi sai daga masa gaisuwa ya ke Guraren4 yamma wasu kyawawan mota guda biyar duka danno kai cikin gidan time din da mai gadi ya bude gate motar ga ba Daddy ne aciki sai kammala da ke driving dinsu sai yan rufa masu baya mota guda 3 suka karisa shigowa su kayi parking daidai parking space daga nan Daddy da Kamal suka fito daga bisani sauran security gidan suka shiga yayiwa Daddy sannu da isowa daga haka Kamal ya karbi dan madai daicin travel bag ya karisa shiga masa da shi ciki, yau gurinsu fareeda murna ba a magana Daddy ya dawo yau kowa na cikin farin ciki duk da tafiyar tashi ba wani jimawa yayi ba but kowa yayi kewarsa sosai kasan cewar Daddy mai yawan wasa da dariya wani sa'in harda tsokana. a wannan rana Ammi ta kasa tsugul sai da ta zaiyyana wa Daddy duk wani abunda ya faru bayan ta fiyarshi wanda abun ba k'aramin mamaki yayi ba jin har suma Nisha ta yi ta kwanta rashin lapia tsabar girgiza da ta yi da lamarin ga kuma soyayyarsu da Kamal wanda basu san da shiba nan ya yanke shawaran neman Ajmal domin su zauna su tattauna a tsakaninsu ya ji ta ban garanshi kasan cewar abaya sun yanke hukunci ba tare da jin ta bakinsa ba duk da kasan cewar fatan Hajj mama kenan ba yi da ikon ja a kan duk wani maganarta hukunci ko k'udirinta but wannan karon ba zaiso a sa ke masa rashin adalci ba haka itama Nisha ba zaiso abunda zai sa ta shiga wani haliba ko a shiga hakkinta akan abunda ba ta da ra'ayi ba matukar ba ta son lamarin gwara Hajj mama tayi hakuri da lamarin a hakura babu cuta babu cutarwa matukar basuda ra'ayin junansu dan haka Daddy ya sa Ammi ta zauna da Nisha ta ji ta bakinta shima ta ban garansa zai zauna da d'an nasa. Kamar yanda Daddy ya nemi zama da Ajmal haka a kayi da dare guraren 10 Ajmal dawowarsa kenan ko side dinshi bai nufa ba duk da kasan cewar dare yayi sosai kuma ya gaji yana bukatan hutu hakan bai hanashi zuwa katafaran parlourn Daddy ya sa me shi kamar yanda ya bukata ba, ban garansu Nisha harsunyi shirin kwanciya bacci Barka ta shigo domin isar da sakon Ammi ga Nisha ta na bukatar ganinta upstairs cikin bedroom d'in ta Nisha haka kawai taji kirjinta ya buga jin Ammi na naimanta cikin wannan lokacin jiki a sanyaye ta mike ta fice tana sanye cikin kyakykyawan kayan baccinta riga da wando masu laushi da taushi launin pink, ta na isa ta tura door ta shige bakinta dauke da sallama . Zaune ta samu Ammi gaban dress mirror tana shafa kamsassun mayukanta da lamar wanka ta yi tana sanyi cikin duguwar rigar baccinta milk color bedroom d'in duk ya dau daddad'an kamshi, "Kariso mana " Ammi ta fad'i time dinda ta mike tana kallon Nisha wacce ke tsaye daga bakin door jin maganar Ammi yasa ta shiga karisowa hankali yayinda Ammi ta jawo hanun ta ciki da murmushi suka zauna bisa sofan dakin "Na sa antasoki ko? maybe ma harkin kwanta bacci " Ammi ta fad'i tana kallon Nisha still murmushin da ke kan face dinta bai goshai ba, itadai Nisha kanta sunkuye ba ta ce k'ala ba Ammi hanu tasa ta daura saman na Nisha ta tashiga fadi'n "Daddy ku ne ya bukaci na kiraki mu zauna da ke Dan jin ta bakinki bisa batun auranku keda yayanku because na labarta masa halinda kika shiga da kuma tsakanku da kamal wanda ya sa shi cikin da muwa da tunanin kamar anshiga hakkin ki an yanke hukunci a ba tare da an shawarce ki ko jin ta bakinki Dan haka matukar ba kyason auran gwara a hakura da lamarin a hakura a raba auran because bayaso kishiga damuwa ko wani hali ya damu matuka akan sumar da kikayi bayaso a miki rashin adalci yace kuma ce na lallasheki na baki hakuri bisa wakanar wannan lamari kuma ki daina saka damuwa cikin ranki". nan Nisha ta fad'a cinyar Ammi ta saki kuka saka kasa abin tausayi tana fadi'n Ajmal Story and writing By Oum amreesh "Please Ammi kudaina neman afuwa agareni matukar nima daya muke da su Reeda a gareku duk hukunci ko umarnin da zakuyi agaresu na dauka nima zata biyo ta kaina tunda nima tamakar ya'rda kuka haifa acikin ku haka kuka dauke ni to mai yasa zan butulcewa maganar ku , nasan iyaye su ne suke nemawa y'ay'ansu mazajen da su ka da ce wanda kuma kunsan zabin da kukayi a gareni ba zai cutar dani ba ko yayi sanadin shiga damuwata" daguwa Nisha tayi tana share hawayen face dinta kafin ta ci gaba da fadi'n " Allah bai nufa ya Kamal shine alkhari agareni ba kuma Allah bai sa shi zai zaima abokin rayuwata ba duk da kasan cewar munyiwa kanmu fatan hakan Amma Allah bai nufa ba, please Ammi karku raba auran ba na yarda na zauna da shi cikin mutunci da mutuntawa tunda shi Allah ya zabamin a matsayin miji" bakaramin jin dad'in maganganun Nisha Ammi ta yi ba ita tasan yarinyar ba zata basu kunya because ta san yarinyar akwai hankali da nitsuwa da kuma hangen nesa shiyasa ta ke da d'an shiga ranta ko da yaushe rungume ta tsam Ammi ta yi bisa jikinta hankalinta ba k'aramin kwanciya yayi da zantukan Nisha ba fatan ta Allah yasa dayan ban garan wajan Ajmal asamu rangwame yayi kawaici irin yanda yayi abaya na auran Heelah duk da ta San abune mai matukar wuya du ba da tun zuwanta gidan nan kowa ya karbeta hanu bibiyu but shikuma k'iri-k'iri ya ke gudun ta ra be shi saida zama yayi zama ya hakura. raba jikinsu Ammi ta yi cike da murmushin murna da jin dad'in ta ce Allah dai ya mi ki albar kyakykyawan ya naji dad'i matukar da gaske na san dama ke yariyace mai biyayya ga iyayen ta kuma ina miki fatan kan wannan zabin da Allah ya miki insha allah shine farin ciki agareki yanzu kije ki kwanta karna shiga time din baccin ki , jinjina kai Nisha ta yi daga bisani ta mike ta fice daga bedroom din tareda yiwa Ammi sai da safe.v Cike da murmushin Ammi ke bin Nisha da kallo zuciyarta na yi mata wani sanyi har Nisha ta gurewa ganinta, Nisha a fitowar ta kenan jiki asanyaye face d'inta yayi jawar da shi a hankali Nisha ta ke tafiya kamar wacce a ka zarewa laka a hankali ta ke sakkowa daga upstairs din sai motsi ta ji bayanta juyawar da zatayi sai ganin Ajmal tayi cikin hanzari ya nufo downstairs wanda yasa Nisha saurin kawar da faska tare da yayin gefe da sauri ta manne Ajmal ta matsa masa daga hanya kar ya banketa yanda ya dibo saurin nan. Ajmal har ya shige Nisha sai kuma ya ja ya tsaya tare da jiyowa ya Kai kallosa gareta yana mai cusa hannayenshi cikin picked d'insa ya na kallon Nisha sai da ya ya kalleta sama da kasa kafin ya ce "Follow me," daga haka ya juya ya ci gaba da tafiya, rass kirjin Nisha ya wani irin bugu mai kuma zai ce mata yanzu Nisha ta ta shiga tambayar kanta ganin Ajmal har yafice daga parlourn ko waiwaye baiyi ba yasa ta bi bayanshi cikin hanzari kafin Nisha ta isa haraban gidan Ajmal har ya doshi side d'insa. Zaune ta ke cikin kyakykyawan rigar baccinta ya'r siriruwar riga mai iya cinyarta tana zaune tana danna wayar ta Aheel na bisa cinyarta harya yi bacci ganin shigowar Ajmal be ya sa Heelah ta ajiye wayar hanunta gamida janye kan Aheel daga cinyarta ta mike tsaya tana lallausan murmushi ta shiga yimasa welcome gamida karisawa gabanshi ta rungume shi tana fadi'n Honey sai yanzu tundazu naga isowar ka but ba kashigo nan ba kawoce side din su Daddy kabarmu da kewarka har Aheel yayi bacci, time din Nisha ta turo door ta sa ko kai a hankali kamar mara gaskiya tsayawa tayi turos lokacin da ta kalli Heelah na rungume da Ajmal , Ajmal zame jikinsa yayi daga nata ya kai kallonsa ga Nisha wacce tayi tsamu tsamu da ita kamar a ce mata shiii ta gudu, harara Heelah ta bi Nisha da shi ta nasanye cikin sleeping dress riga da wando sai bin shape d'inta yake to waima mai ya kawota side din nan ne a wannan time din kardai a ce fakon time din dawowarshi ta ke tana biyo shi "What are you doing here? da daren ma sai kin biyoshi ko ce miki yayi yana bukatar wani abin" Heelah ta fad'i a zafafe but ga mamakinta sai gani tayi Ajmal ya juya ya nufi Nisha tare da jawo hand dinta fuuuu ya haura da ita upstairs wayaga idon Nisha kamar ana jijjiga bera abuta Direct bedroom d'insa ya nufa da ita yayinda ya tura door da karfi ya janyo Nisha ya wurga ta ciki sai da ta shiga yin tangal tangal ta na naiman faduwa kafin ta sai ta tsayuwarta da kyau daga neman faduwar da ta ke kokari yi jikinta sai rayawa ya ke kamar mazari idonta tuni ya raina fata sun cicciko da hawaye tana neman yin kuka, kallon Ajmal ta yi wanda yayi mata k'uri da idanuwansa wanda su ka canza launi sai wani huci ya ke kamar wani tsohon zaki nan ta ga ya shiga ta kowa ya nu fo ta wanda yasa Nisha ta shigayin baya cikin sauri tsoro da firgici duk ya cika k'wanyarta gaba daya ta rasa inda zata shiga ganin yanda Ajmal ya nufota gadan gadan ta San ba lapia ba especially yanda ta ganshi cikin wani yanayin fusata., Nisha sai ja da baya ta ke har sai da ta zo karshin bedroom d'in ta kafin ta manne jikin bangon tare da hade hannayenta guri guda gamida rintsa idanu lips dinta sai bari ya ke ta na son cewa wani abu, time din da Ajmal ya kariso dab da ita har tana iya jiyo sautin zazzafan numfashinsa yanda ya ke fita, kallonta Ajmal yayi kafin iya bude baki ya na fadi'n "Look at me " Jin muryan Ajmal a fisge ya na magana yasa jikin Nisha cigaba da k'yarma kanta sunkuye ta kasa daguwa ta kalleshi kamar yanda ya umurce ta ba karamin tsoronsa ta ke jiba balle kuma hada ido da shi cikin wannan sigar da ya zo mata na rashin sanin dalili, "Dan Allah kayi hakuri" Nisha ta fad'i cikin barin lebe tana jinjina hannayenta "I say look me " Nisha ta ji ya kuma fad'i karo na biyu a tsawace gamida dafa hand d'insa jikin bango ya kareta cikin hanzari Nisha ta dago kai ta kalli Ajmal wanda ya matso dab da ita tamkar zai shige jikinta daddad'an turarensa mai wuyar mancewa sai dukan hancinta ya ke, ido cikin ido haka Ajmal da Nisha suke kallon junansu ko kyafta ido ba maiyi cikin su rirarun hawayen da suka makale cikin kwarmin ido ta suka shiga yin zaryan gangaruwa saman lallausan kumatunta still ba ta iya kauda idonta daga kallon kyakykyawan face din Ajmal ba mai cike da sirrukan kyau da kwarjini, haka shima Ajmal gaba daya ya shagaltu da kallon tsantsan sirrin kyau irin na Nisha karon farko da ya zubawa yarinyar ido ba tare da ko kyaftawaba ko dauke idonsa daga kallonta ba surutan da ke cikin bakinsa duk ya kasa yinsu saboda shagaltuwa da kallonta wanda ya sa shi kasa furta komai , lokaci daya kamar wanda aka tsikareshi kuma ya dauke idanunsa daga kallon Nisha gamida ja baya kad'an daga bisani ya juya mata baya ya shiga tattaro nitsuwarsa ya rasa wani irin shagala yayi da kallon yarinyar haka, Heelah ce ta turo door da karfi kamar wata za kanya yayinda idanuwanta su ka sauka kan Nisha wacce ta makale jikin bango ta rungume hannayenta jikinta sai hawaye ta ke shi kuwa Ajmal ya juya mata baya ya lumshe ido yana sauke ajiyar zuciya tare da sai ta nitsuwarsa, because ya rasa tunanin sa da nitsuwarsa time din da ya daura eyes d'insa bisa face d'inta gaba daya tunanisa ya juye, a zafafe Heelah ta karisa shigowa tsakiyar dakin tana cillawa Nisha wani banzan kallo tana fadi'n "Amma dai ke anyi mayya wallahi tirr da halinki zo kiwuce kufita, ki fitarmin daga daki kafin nayi kasa kasa da ke muna fukar banza dama nasan sai kin sanya mijina ya fad'a cikin tarkon ki kamar yanda kikasa yan uwansa, na tsaneki banason ganinki sam ban san ina tunanin su HAJIA ya ta fi ba ta dauko wannan annobar ta kawota cikin familynmu wallahi sai na kasheki kowa ya huta inba haka ba bazaki bar zuciyata ta samu salamaba Heelah ta fad'i kamar zatayi kuka ta nufi Nisha tayi kanta tare da kai hanu da nufin shako wuyar Nisha but sai Ajmal ya sha gabanta yatsaya "Please leave me yau sainayi ajalinta" Heelah ta fad'i cikin ta kaici "Are you mad kinsa mai kike fad'i kishiga hankalinki kisan mai kikeyi" Ajmal ya fad'i a tsawace cikin taakaici da bacin rai "Eh nafadi saina kasheta saidai nima akasheni bazan bar wannan yarinyar ba yau" Heelah ta fad'i cikin kunar rai gamida yin gefe tana shirin damko Nisha nan madai ya kuma tareta gamida ri ke ta yana kokarin hanata nanfa Heelah ta rike ce musu ita ala dole sai ta kashe Nisha, Nisha ganin Ajmal na rike da Heelah yana kokarin hanata abunda ta keson yi ya sa ta rabe ta gefensa ta fice da gudu ta bar bedroom din, ta kaici duk ya ishi Ajmal ganin haukar da Heelah ke yi tana kokarin bin bayan Nisha cikin bacin rai Ajmal ya dauke ta da mari sai da ta ga wasu taurare daga bisani ya cillata saman bed, sam baiso abun ta kai ga mariba but yaga sai ya kai hanu ta ke iya nitsuwa ta fiskanci yaren kuka sosai wuiwui Heelah ke yi tana birgima saman bed kamar wata karamar yarinya gefe Ajmal ya zauna bisa sofa yana kallonta yanda ta ke kurma ihu tana kuka tamkar wacce ta zauce Ajmal sai huci ya ke yana furzar da zazzafan iska cikin bakinsa cikin ta kaici Ajmal ya jawo hand din Heelah ya turata waje kafin ya tura door d'insa ya rufe, hanunta na kan face d'inta ta ruga da gudu ta yi bedroom d'inta ta kwanta saman bed d'inta ta ci gaba da kuka, Ajmal zama ya dawo ya kumayi yayinda ya dafe goshinsa da hand d'insa biyu Heelah ba k'aramin caza masa kwakwalwa ta ke ba gaba daya al'amuranta babu tunani da lissafi Sam ya rasa mai ke damunta duk da wasu dabi'un nata zuwan Nisha ne ta farayunsu wai ita kishi ta wani gefen kuma tunani ya ke wacce wannan yarinyar da ta saye zuciyoyin ahalinsa da harsukayi tunani daura masa aure da ita ba tare da wani tunani ko shakkan yin hakan ba ko dan sunga yayi shiru ya zuba musu ido da fari shiyasa suka sake yin wani iko kansa ba tare da tun tubarsa ko jin ta bakinsa ba to wai shin wacce wannan yarinyar kuma suwaye familynta inane tushenta duk ba su ta ba wannan tunaniba ta shi daya suka k'ak'aba masa ita babu wani shakku ko bincike, lumshe idanu yayi gamida jan wani goron numfashi kafin ya mike ya cire kayan jikinsa ya daura towel ya nufi bathroom, Sai da yayi wanka ya fito ko tsayawa wani shafa mai baiyi ba ya zira jallabiyar sa ya fito ya nufi downstairs tsabar saurin da yake na kiran Daddy d'an shopping d'in da yayima ya mance shi cikin mota gashi dare ma yayi sosai coffee kawai ya zauna ya shaa yana dan tunane tunane har ya gama ya mike ya nufi inda Aheel ke kwance saman sofa gefensa saman table kayan ciye ciye wanda suka gama kodumo da mom d'insa saman shoulder d'insa Ajmal ya daura Aheel ya nufi dashi upstairs daga nan ya wuce da shi bedroom d'insa ya kwantar da shi kafin shima ya kwanta gamia rage musu light daga nan ya lumshe idanu mai makon bacci ya dauke shi but sai face din Nisha ya ke hango wa da d'an k'aramin pink llips d'inta da ke motsawa a hankali bude ido Ajmal ya kuma yi da sauri yana zazzare idanu wai mai ya sa meshine yanzu da ya kasa bacci ya ke tunanin mara amfani irin haka, ya juya nan ya juya can haka Ajmal ya dinga yi har ya samu bacci b'arawo ya saceshi,. Bangaran Nisha tunda ta samu ta fice tashige part dinsu tanufi bedroom d'insu time din harsu Fadeelah sunyi nisa da bacci haka itama ta nemiguri ta kwanta gamida dunk'ulewa guri guda gaba daya duk a tsorace ta ke fatan ta Allah ya kawo mata dauki gamaida Heelah da Ajmal because zasu kasheta kwananta bai kareba especially Heelah da ke ikirarin zata kashe ta yanda ta fahimci zafin mahaukacin kishi irin na ta ko shakka babu zata iya aiwatar da abunda ta ke fad'i. Washe gari karfe 9 dawasu yan mintuna Daddy da Ammi ne zaune bisa dining table gefe Hajj mama suna zaune suna breakfast suna yar hiransu yayinda Hajj mama ta kalli Daddy da Ammi tana fadi'n "Yau bai fi saura wata daya bikinsu fareeda da tariyar Nisha ba amma hankalina ya kasa kwanciya ta ban garan Modibbo ko mai zai ce a kan hakan karon farko da nashiga alhini kan lamari inaga kamar wannan karon nayi kuskure da rashin adalci tsakanin y'ay'an nan" Hajj mama ta fad'i cikin jimami kallon juna Daddy da Ammi su kayi kafin Ammi ta sauke wani nan nauyan ajiyar zuciya tana fadi'n "Da ka fad'i mata yan da mukayi da y'ay'an nata ko itama hankalin nata zaifi kwanciya" Dan g'yara zama Daddy yayi gamida g'yaran murya still fara'arsa ba ta gushe ba ya kalli HAJIA kafin ya shiga fadi'n "Hajia karki wani da mu kanki Ammi ta bani labarin bayan ta fiyana halinda yarinyar nan ta tsinci kanta aciki sai naga adalcin da zan iya musu shi a zauna dasu dan jin ta bakin kowannesu akan lamarin idan da yiyuwar wakan lamarin fanillahilhamdu idan kuma da yiyuwa hakura da auran baza su iya zauma da junansu ba to cikin sauki sai araba auran," "To alhamdulillah ta bangaran Modibbo a yanda muka yida shi bai wani nuna damuwarsa ga lamarin ba sai dai ya bukaci ya zauna shikadai yayi shawara da zuciyarsa a takaice dai nasan yaran basu ki bin maganar muba because suna da hankali baza su bamu kunya ba ta ban garan yarinyar ma ba wani tsaya wa dugun tunani ta amince ta zauna da shi matsayin abokin rayuwarta kamar yanda Ammi ta labarta min", wani hamdalah hajia tayi gamida godiya ga Allah alamura sun ta fi cikin sauki ta yanda ba tayi tsammanin ba "Allah dai yayiwa yaran nan albarka ya sanya albarkarsa cikij lamarin" HAJIA ta fad'i cike da farin ciki da jin dad'i, "Ameen " su Daddy suka amsa Time din da su Reeda da fadeelah su ka kariso dining din su ka zauna tareda dagawa iyayen nasu gaisuwa cikin girmama wa "Yau har kun koshi da baccin kenan ko daukin dawowar Daddy ya sanya kuka tashi yau da wuri haka Dan nasan sai 10 ko fi " Hajj mama ta tambaya ta na kallonsu but ba su ce mata komai ba sai dariyar da su ke su na k'arawa nan su ma suka shiga daukan plate suka shiga serving din kansu breakfast yayinda barka ke ta kai kawo a tsakaninsu ta na dauko musu duk wani abinda suke so ko suke bukatarshi a gurin " wai ina Nisha ne ita banganta:anan ba" Ammi ta tambaya ta na kallon su Reeda wanda su ke tsaka da breakfast, carab Barka ta karbi tambayar da cewa "dazu muna tare da ita cikin kitchen din nan ta gama taya ni wasu ayyukan daga da bisani ta fice inaga side din yayansu ta nufa kamar yanda ta saba" "Okay" Ammi ta ce gamida jinjina kai ta ci gaba da yin breakfast d'inta suna mai ci gaba da hira, "Daddy ba ka kawo mana tsara ban komai bane" su Reeda suka tambaya suna kallon Daddy "Sannu yan gidan tsaraba to ce muku a kayi ta fiyan jindadi yayi da kuke tunanin tsaraba" Ammi ta cafke maganar gamida basu amsa tana hararosu, dariya Hajj mama da Daddy su kayi kafin Daddy ya ce "Kyalesu na kawo musu tsaraba babbama kuwa kuma na san zasuji dadinta" Daddy ya fad'i gamida murmushi yasanya hanu cikin picked din jallabiyar sa , fadeelah da Reeda sai tsili tsilli da ido su ke sunyi k'uri da ido dan ganin mai Daddy zai ciro cikin aljihu, nan suka ga ya zaro phone d'insa ya dan daddanna kafin ya mika musu har rige rigen karba su ke "Kuyi dai ahankali karku mini ta adi Daddy ya fad'i ya na kallon su fadeelah da suke ta fada kowa so ya ke phone din ya zama a hanunta akarshe Reeda ne ta damke wayar tana fadi'n "Ke dallah ki tsaya mugani a nitse" fadeelah sai hararanta ta ke tana cizon lips daga bisani suka shiga kallon wayar don ganin mai Daddy ya keson nuna musu, kayan furnitures ne kala kala masu ke tsadaddu Daddy ya musu order daga Dubai kafin zuwan bikinsu komai da amare suke bukata anta na daishi masu kyau gwanin sha'awa da burgewa su Reeda murna kamar ba gobe cike da murna su ka shiga nunawa su HAJIA da Ammi, Ammi dai mamaki da kallon y'ay'an nata ta ke yanda suka wani zage sai murna da farin ciki su ke bawani kunya atare da su oh yarinta kenan, Yau Nisha cikin fargaba da tsoro ta kammala komai ta g'yara ko ina fes Aheel na biye da ita duk inda tayi to ya na biye da ita ya na mata surutan nasa da ya sa ba da baya gajiya ita kuwa sai biye masa ta ke badan tana cikin ya nayi mai dad'i ba ,ta na tsaka da jera breakfast din bisa dining table kamar yanda ta saba sai wul wulga ido ta ke ta na sauraran sakkowan daya daga cikinsu aikuwa sai Ajmal ta gani cike da nitsuwa ya na sakkowa daga upstairs ya na sanye cikin black jallabiyar sa gwanin sha'awa, sau daya suka hada ido Nisha ta kauda kai gefe ta cigaba da abunda ta ke yayinda Aheel na ganin papanshi ya ruga aguje ya he ya rungomesa kamar yanda ya sa ba suka kariso dining table din suka zauna a dan su kwane Nisha ta shiga daga masa gaisuwa ganin ya zauna. "Ina kwana antashi lpy, daga mata kai kawai yayi ba tare da ya kalle taba ko bude baki ya amsa mata ba cikin damuwa da sanyin jiki Nisha ta shiga yin serving din Ajmal kamar yanda ta ke yi kullum daga nan shima Aheel Nisha ta yi serving d'insa da duk a bunda tasan yanaso kafin Nisha ta dan saci kallon Ajmal wanda ya ke breakfast ya na kuma danna waya hankalinsa ma baya kanta haka yasa ta tayi ba ya ta haura upstairs ta nufi bed din Ajmal domin ta gyara masa gudun karya kuma yi mata magana a kan hakan , Nisha sai da ta fara g'yara toilet ta wanke ta tsaftace kafin ta dawo bedroom ta suma g'yarawa shima a hanzarce ta ke yin aikin yau because ta kosa tabar sashin Ajmal. Tana tsaka da g'yaran Ajmal ya turo door ya shigo cikin bedroom din Wanda ya sa Nisha dagowa time din da ta ke tsaka da gyara masa bed, Ajmal kamar baisan da zaman Nisha cikin bedroom din ba yazo yawuce yanufi bathroom ya wanko bakinsa gamida hannyensa kafin ya fito because dama already yayi wanka kaya yake bukatan sawa, Nisha ta na ganin Ajmal ya fito hankali kwance ya nufi wardrobe domin duba kayan da zai sanya but duk wani motsinta ya hankale da ita , Nisha kama hanyar fita ta yi because ta kammala aikin da ya kawota . "Wait "Ajmal ya fad'i gamida jiyuwa yana kallonta, ras k'irjn Nisha ya buga, kafin ta tsaya kyam kanta kasa ta rasa mai Ajmal ya ke nemanta da shi kullum ba arasashi da abun fad'i ko korafi "Samu guri kizauna " Ajmal ya kuma fad'i still idonsa na kanta harta kuma tsakiyar dakin ta nemigu saman carpet ta duka da tunani iri da kala a ranta, shikuwa Ajmal bakin bed ya nema ya zauna gamida kai kallonsa ga Nisha wacce tayi ladab da ita dad'in sa da yarinyar akwai respect din mutum baisan tsantsan kwarjinin da ya ke matane yasa ba ta iya hada ido dashi "Look at me carefully magana nakeso muyi da ke but feel free banaso kina wannan rawar jikin da kike kuma ki bude baki kiyi min bayani sa'in da na tambayeki" Nisha shiru ta yi gamida sake k'ank'an da kai tana sauraren abunda zai tambaya ye ta , d'an gyara zama Ajmal yayi gamida kallonta da kyau kafin ya ce "Am tunda kikazo gidanan nan ba wanda ya nemi karin bayani akan ta rihin rayuwarki ko jin wani labari da ya shafi rayuwarki sai dai ayanzu ta bangarena kin kunna min sha'awar sun jin labarin rayuwarki da ta rihinki kasan cewar ina da right na san wacce ke sunan ki da kuma ta rihin iyayenki go ahead I'm hearing you " shiru Nisha ta yi idonuwanta sun cuko da kwallah ta na neman kuka ta na sonyin magana but kuka yana neman kwace mata Nasan mahaifiyarki ta rasu shine dalilin da yasa hajia tausaya miki ta dauko ki ta kawo ki cikin gidan but ina sauran yan uwanki da mahaifin ko shima ya rasune? Ajmal ya kuma tambaya Amma gamamakin sa abun ta kaici kuka ta shiga jira masa tana shashsheka wanda yasa Ajmal ransa ya suma baci duk tambayoyin da yake mata cikin sigan nitsuwa da kwanciyar hankali mai makon ta nitsu ta bashi amsa ta shiga yi masa kuka Ajmal tsabar takaici ya suma kokarin mikewa but sai ji yayi ta bashi amsa cikin cool voice Mahaifina bai rasuba Nisha ta fad'i tana share hawayen face d'inta gamida jan hanci Ajeemal Story and writing By Oum amreesh Book 2 Page 74 _____cike da mamaki Ajmal ya kuma ya gyara zama jin tana da mahaifi but ta zauna a nan tsawon lokaci tana rayuwa ba tare da sanar da kowa ko ta nemi mahaifin na taba duk da baisan dalilin ta akan hakan ba Ajmal g'yara zama ya kumayi da kyau kafin ya kalli Nisha cikin tsare gida ya ce I'm hearing you continue your talk, "Ni sunana Aisha Hashim yarima friends dina suna kirana da Nisha an haifeni a garin adamawa maihaifana yan asalin kasar Sudan ne fatauci ya kawoshi Nigeria, ni ba yar kowa ba ce amma Allah ya rufawa mahaifina asiri kuma Allah ya bun kasa masa samunsa ta hanyar kasuwancinsa wanda yayi sana diyar dawowarmu nan cikin garin kano da zama, ni kadai Allah ya mallakawa Abbana a matsayin y'arsa daya tilo ya kuma nuna min gata sosai kamar yanda a ke nunawa y'ay'aye mafi soyuwa wajan iyayensu sun kuma bani tarbiya daidai gwargwadon iyawarsu sun kuma sanyani makaranta mai inganci amma duk da haka hankalin Abbana bai kwanta ba ganin ni dayace jininsa banda yaya ko k'ani hakan yana damunsa kwarai da gaske, kasan cewar Abbana mutum ne mai sun yara da kuma son tara zuri'a, amma umma ta ba ta sa ke samun wani karuwa ba bayan ni hakan yasa ya kara wani auran, ya auro aunty faty wacce na ke kira da Mami wacce itace silan rugujewan farin ciki rayuwata da ta mahaifiya ta., Nan Nisha ta shiga baiwa Ajmal labarin rayuwarta da ki da ki ba tare da ta boye masa komai ba da ya shafi rayuwarta da ta iyayenta, da b'acewar Abbanta wanda har yau har gobe ba ta sa ke sashi idonta ba duk da bata cire tsammanin sa ke tuzali da Abban na ta ba kuma bakin cikin ganin nasa ne ta ke tunanin yayi silar rasa mahaifiyata saboda damuwa da rashin sanin halinda ya ke ciki ya kuma kasa zuwa inda suke, haka Nisha ta cigaba da bawa Ajmal labarin yanda ta ka sance a rayuwarta cikin kuka mai tsuma rai da ban tausayi sai dai kuma cikin labarin na ta tayi hide wani ban gare da ya shafi haduwar ta da Kamal, kamar yanda tayi tunani kar garin g'yaran gira arasa ido saboda tsonrata da bara zanar kb da yayi mata na cewa, ' duk ranar da Ajmal ya fahimci itace silan ilatasu kwanakin baya to fa k'oneta zayi da ranta ko ya daure ta sai igiya taisaura, da sauran uk'uban da ya dinga lissafo mata wanda Ajmal zaiyi mata duk randa dubunta ya cika, duk da ta su ta fada masa but tunanin ta ba ta san ta wani fiska zai dauki al amarin ba, maybe ma kafin ta gama sanar da shi zata tsinci harsashi cikin kwakwalwar kanta Nisha sai da ta kai karshen labarin karfin ta diga aya cikin kuka ta na jan hanci gamida goge hawayen face d'inta abun tausayi face d'inta yayi jawur dashi idanunta duk sun kunburu saboda kuka, parlourn ne ya dau shiru kai kace ba halittun mutane ciki, Nisha jin shirun da tayi kamar ba mutum a wajan ya sa ta d'an dago kai ta sato kallonshi carab idanunsu suka hade cikin na junansu Ajmal ya mata kuri ya na kallonta kamar wata tv tunda ta fara magana ya jingina jikin sofa yana sauraronta kamar wani radio ya naso ya gasgata labarun nata but bayi da tabbacinin abunda ta ke fad'i gaskiya ne ballai ya dauka ya sanya cikin mind d'insa,amma in har da labarain ta gaskiya ne akwai abun tausayi da rikita hankali, wani goron numfashi Ajmal ya sauke gamida duk'o da kai ya sanya hannayensa duka biyu kasan habansa kafin ya kuma duban Nisha da kyau yana fadi'n "You can go but but karki fita da wannan hawayen face din nakin, so Go and wash your face in side the bathroom Ajmal ya fad'i cikin cool voice na shi mai kamar rad'a wanda ya sanya Nisha sa ke marairaucewa ta na matse ido kafin ta mike ta nufi toilet kamar yanda Ajmal ya fad'i Nisha wanko face d'inta tayi sosai kafin ta fito tana goge ruwan face d'in na ta da gefen d'ankwalin ta wanda tuni yabar saman kanta dama bai cika zama ba saboda laushi da sulb'in gashin na ta, Nisha dai tv ta komawa Ajmal because sai kallo ya ke bin ta da shi ya na k'arawa da tunani iri da kala cikin ransa ita kuwa kanta kasa duk ta tsargo da kallon da Ajmal ya ke bin ta da shi to ko bai gamsu da labarun na ta bane oho because ta sanshi bai dasaurin yadda da mutum Sam, Nisha dai haka ta fito ta bar Ajmal na binta da ra kiyar idanu, A cci ta na jin mom din na ta tana magana but ta kasa amsa mata saboda bakin cikin da ke kwallace cikin zuciyarta. " magana fa na keyi shiru kinajina yau ina aikin kika taho sassafe inama kika baro Aheel idin ince dai ammusu hutun school suma" gamamakin ta maimakon Heelah ta tashi ta amsa ma ta tambayoyin ta but sai kuka Heelah ta fashi da shi cikin kuka ta ke fad'i "Mom yarinyar nan za ta sa zuciyata ta fashe saboda bakin ciki, ta rabani da kowa bawanda ya ke ganin da wani kima ko farin jini yanzu sunfi daukarta da mahimmanci fiye dani," zaman dirshen Heelah ta mike ta yi bisa gadon ta na ci gaba da fadi'n "Mom yarinyar nan ta rabani da farin cikin rayuwata d'ana Aheel mijina duk ta rabani dasu ke kadai na ke dashi yanzu" Heelah ta fad'i gamida fadawa jikin mom d'inta ta cigaba da jero koke koken nata, shiru Hajia Jummana ta yi tana tunani na rashin fahimtar zantuttukan Heelah inda suka dosa to wacce yarinyar da Heelah ke magana akaine because hajia Jummana ta ma mance da wata Nisha da ke rayuwa cikin gidan Daddy. "Kinga barwannan kukan ki tashi kimin bayani yanda zan fahimta kinsani aduhu kintayar min da hankali wai wace yarinyar da kike magana akai ne?" "Nisha ta ke ko nishii ita ce ta ke kokarin shiga min hanci da k'udunduni ta rabani da farin ciki na akanta ya Ajmal ya fara wulakanta har dukana ya ke kamar jaka a kanta kowa na gidan ya juyamin baya kamar ba susan da ni cikin gidan ba haka shima ya Ajmal matukar yana ganinta tana wulgawa komai ita ta ke yi masa kamar matarsa ni dai nazama yar kallo jiya da dare har side d'insa ta biyu shi shiko ya ja hanunta suka shige bedroom d'insa suka rufe shine da na shigo na ta da masifa ya rufeni da duka ya fitar dani mom Aheel ma ta kwaceshi daga gareni idan ya ganta jikinsa har bari ya ke idan ya ganta mancewa ya ke Dani kamar banice na haifeshi ba " Heelah ta karisa zancen cikin kuka. "Tab d'i lallai fa tsincecciyar magi ba ta mage akuyar sunce ta samu sake yanzu haka al amura suka cab'e daga zuwar wannan yarinyar cikin gidan shine suka hadu suka juya miki baya harta fiki kima da mutunci aidanunsu to wallahi bazai taba sab'uwa ba bindiga a ruwa dole su gayamin matsayin yarinyar nan agidan saboda zagewar yayi yawa wato har makwanci mijinki ta ke shiga idan kika hana akai miki duka?" Mom ta tambaya tana kama haba tana kallon Heelah. "Eh harda min warning hakan ta wai ko kallon banza karya sa ke shiga tsakanina da ita gaba daya ma fa kamar sonta ya ke sai kin gani" Heelah ta fad'i tana cizon lips " mom inban kashe yarinyar nan ba bazan hutaba Allah sai dai nima a kasheni" "Kul karna sa ke jin haka idan kika kasheta ke kuma aka kasheki inyi yaye kenan? ke kwata kwata ma bazaki ci moriyar zaman duniya ba wayace miki ta haka ake huce ta kaici sawa zakiyi ta gwammaci kida da karatu, duk dama wani ban garan hadda sakaci irin na ki da kika bata kofa ta rab'i mijinki gaba ki daya kin lalace kin susuce sai na rasa uwar mai kike a gidan ince daga kwanciya sai bacci ba aikin fari bare na baki duk yan aikin da ake kawo miki sai kin koresu kuma ke ba abunda kika iya sai zuwa office" "To duk ba ke kika sangartamu ba ko tsinkefa bana dauka a gidan time din da na ke nan hajjo da Nabilah ne keyi sai waccen Aunty amaryan gashi na tashi a tutar babu harwata na so ta kwacemin miji saboda tsabta da iya girki wallahi koni mace sai da na sarawa iya girkinta shiya sama na ke zagewa na ci nima" Heelah ta fad'i tana tura baki "Eh lallai kice kema aikin ta ya fara ta siri a kanki kenan ke wato nine ma na san gartaki na hana kikoyi abubuwan rayuwa? gatan da nanu miki saboda karki sha wahala shine sangarci to yayi kyau kin kyauta amma dai bazan bar wannan lamari ya ci gaba da ta fiya haka ba "To amma ya batun wancen complain din ince dai ya canza yana amsa gaiyatarki yanda ya kamata domin na san abinyi, ko haryanzu ke ce mijin shine mata sai ana binshi ana lallabansa?" tabe baki Heelah ta yi tana fadi'n Jiya I yau yanzu ba yadda da ni kwata kwata d'an da barun da na ke domin jawo tunaninsa yanzu abun ya fasskara hattakai yanzu baya yadda Dani wataran da fad'a muke karewa inna takura masa yamin k'eta ya fice ya barni da jinya ni duk na gaji da wannan halaiyan nasa", shiru Hajia Jummana ta yi tana jimami a kunyace ta kalli Heelah kafin ta ce "Kuma lapia yarsa qalau kuwa? wannan lamarin nasa akwai abin dubawa ace abar mace haka bawani kulawa ki ce hoto kawai kike ko TV n kallonsa?" "Mom TV ma ya fini ammfani tunda yana iya ya tsaya ya kalla na tsawon lokaci kuma karkiyi tunanin bayi da lapia qalau yake wallahi tunda harya iya jan waccen yarinyar turakarsa suna yiwa junansu mad'e" "Aikuwa bazaki ci gaba da zama haka ba saboda ke ma jinini ajikinki ba ruwa ba sanya mayafinki bari nazo " Hajia Jummana wardrobe ta bude ta janyo mayafinta tare da daukan handbag dinta ta kalli Heelah wacce ta mike tana g'yara mayafinta kafin ta janyo handbag d'inta itama suka jera suka fice daya na bin daya kamar wasu kifin gwangwami, A parlour suka iske Aunty Hafsatu ta na zaune tana cin y'ay'an ita ciya ta na kallon TV time ta kalli su Heelah da mom d'inta sun fito suna shirin ficewa daga Heelah har mom harara su ke bin Hafsatu da shi harsuka fice ita kuwa ko kallonsu ba ta kuma yi ba dan ta San ko adawo lapia tai musu sai sunje fe ta da maganar da bai mata dad'i ba shiyasama ta jira kanta da bakinta. da dare misalin karfe 9 ta dan gauta Nisha na zaune bisa bed da Aheel da ke kwance yayi matashi da cinyarta yayi bacci wanda ya wuni kas gurin Nisha ya gama rigimar sa yayi bacci sai fadeelah da ke gefenta tana nuna mata kayatattun furnitures din da Daddy ya musu order daga Dubai wanda ta tura cikin wayar ta d'an ta tununawa Nisha kayan alherin da Daddy yai musu order na auransu su duka, Nisha kuwa sai kallo ta ke tana karawa because kayan sunyi matukar kyau da kwatuwa, Yayinda Reeda ke gefe zaune saman stool gaban dress mirror ta na danna wayanta kafin ta dago kai tana kallon Nisha gamida fadi'n Salma ta kirani jiya na mance ban sanar da ke ba but na jita cikin ya nayin damuwa da ta shin hankali ta ce min ta yi waya da ke amma kinki ba ta hadin kai kuyi magana sai sautin kuka ta ke ji ta cikin waya ta tambayi dalilin kukan kin ki sanar da ita shine ta kirani domin ta tuntub'e ni gameda yanayin da ta jiki ciki ko Ina da masaniya akan halinda kike ciki Ban boye mata komai ba na sanar da ita duk abunda ya ke faruwa but ta damu da halinda da kika shiga, Salma ta na so kuyi magana na san kuma ta damune ganin bikinta ya zo amma ko duriyarki ba ta jiba wanda ba ta ki iwar haka kuna tare ba because duk duniyar nan ke ce babbar kawa a gareta yar uwa kuma aminiyarta mai zai hana ki kwantar da hankalinki ko ita na ta hankalin zai kwanta a yi bikinta cikin salama farin ciki da kwanciyar hankali,. Karkiso kiga yanda hanlalinta ya tashi jinki cikin wannan ya nayin ta damu da damuwarki hak'ik'a Salma kawace ta gari kuma ta na sonki sosai, Reeda ta suwa ta yi daga inda ta ke zaune ta dawo kusa da su ta zauna gamida kallon Nisha tana fadi'n "Please and please ki kwantar da hankalinki ki daina damun kan ki haka , na lura da ke tunda kika tsinci wakanar wannan lamarin kika ragewa kan ki farin ciki fara'a da annashuwa sometimes cikin kuka da tunani da kike ban san mai kike tunani gamida auran ba but rokona a gareki Ki ra ge damuwa ki rungumi kaddaran da Allah ya daura miki fatan hakan ya zamo alkhari a gareki, ya Ajmal da ya Kamal duk kusan abu guda ne sai d'an hali da yasha banban ya. Ajmal bamai wasa ba ne Kamal ya Kamal ba zaki ta ba gani kyakykyawan halinsa da ga fiska ba sai kin zauna kin fahimce shi da kyau zaki fahimci yana da saukin kai fiye da tunaninki duk da wani sa'in idan ya juye bazaki ta ba ga ne shi ta dad'i ba ina fatan ya zama farin ciki a gareki ki kuma sauya shi ta yadda kikeso". Shiru Reeda tana murmushi kafin ta cigaba da fadi'n "Allah dai ya kawomin time din da Heelah zata tsinci ke abokiyar zaman ta ce kamar daga sama ranar sai na zuba ruwa a kasa nasha," tintsirewa da dariya fadeelah ta yi tana fadi'n "Amin fa uwar yan kishi zanga yanda idanunta zasuyi" ita kuwa Nisha fargaban ta kenan wannan ranar duk ranar da Heelah ta fahimci hakan ba tasan mai za ta mata ba dan tun yanzuma ta fara mata ikirarin zata kashe ta ita dai Allah ya sa ma kafin lokacin a nemeta a rasa ta gudu dan yanzu burinta zai cika da zaran ta fara zuwa school zata gudu domin komawa gurin Abbanta ta san halinda ya ke ciki dan ba ta san ta ya zata fara rayuwa da wadannan fusatattun mutanen ba . Ta wani ban gare kuma ta na ganin kamar inta gudu batayi adalci ba ta yi butulci fatan ta dai Allah ya kawo mata mafita cikin lamuranta. " To yanzu ya ake ciki da batun zuwa bikin Salma ko haka zamu zuba ido har ayi bikin a kare bawanda ya je cikin mu? Idan mukayi haka kamar bamu kyauta ba" fadeelah ta fad'i tana kallonsu. " Gaskiya dai kam a duba lamarin" Reeda tafad'i tana kallon Nisha duk su biyun idanunsu ya koma kan Nisha, ita Nisha kallon nasu ta yi tana fadi'n "To ya zamuyi ni kunsan da aure bisa kaina i mala'iku tsine min zasuyi idan na fita ba da izini ba" "Why not ki tambaye shi zaki auran kawarki " fadeelah ta bata amsa " Tab di ke ma kinsan halin ya Ajmal abunda ba zai yiyu bane muma da yaya muke fita ballai ita da ta ke k'ark'ashinsa yanzu, dama da a sace zamuje mudawo ba tare da ya sani ba tunda ba wuni ya ke gidan ba balle ya san tafiyar mu da dowar mu but ita kuma bazai yiyuba mala'iku zasu tsine mata" ita dai Nisha jinsu ta ke koma ace zai barta bazata tambaye shi ba because ta san abun magana ba ya masa kad'an. " Yanzu mun hakura kenan?" fadeelah ta tambaya " Aa mudai zamuje muwakilce ta sai muje tare da ya Kamal tunda mijin na ta abokinsa ne, kinga ko ba komai zatayi farin ciki inta ganmu fareeda ta fad'i " Nima nayi farin ciki sosai Allah ya bar zumunci" Nisha ta ce gamida murmushin jin dad'i "Amin " suka amsa daga haka su ka ci gaba da firansu wanda daga bisani suka kwanta bacci sannu ahankali bacci b'arawo ya sacesu but ita kuma Nisha bacci ya kasa na sara a akanta daga ta rufe idanu zata hango kyakykyawan face din Ajmal tare da kyawawan fararan idanun Ajmal masu kamar madara time din da su ka k'urawa junansu idanu kowa ya kasa dauke ido daga kallon kyawun da Allah yayiwa dan uwansa. Lumshe idanu tayi ta bude kafin ta mike daga kwanciyar da tayi ta na kallon Aheel wanda ke ta bacci hadda minshari tsoronta daya kar ya tashi mata cikin dare ya na rigimar nan ta sa yace a kaishi gun papansa gashi side dinsu ba kowa ciki da Heelah har papan nasa ba wanda ya dawo cikinsu. Sakkowa tayi daga saman bed din ta nufi window gamida yaye labule tana sauke ajiyar zuciya gamida jin kyakykyawan ni'ima ta na kallon kyawawan bishiyoyi masu fitar da sassanyan mashi na musamman guri yayi shiru alamar dare ya ja gida ko ta ina ya dau haske kai kace ranane ba dare ba dan ba abunda baka iya gani tarwal, . Jingina kai Nisha ta yi jikin window ta na dan tunane tunane ta dau tsawon lokaci tana tsaye a gurin kafin ta hango mai gadi ya na kiciniyar bude gate saboda hon din da ake ta yi daga waje koda mai gadi ya bude gate motar Ajmal ne ta danno kai cikin compound din gidan daidai parking space yayi parking daga bisani ya fito ya suma nufan side d'insa cikin tafiyar ka sai ta irin na manyan mutanen nan . Nisha zuba masa idanu ta yi tana kallonsa wanda duk dama ya riga ya sanya ido akansa to zaiyi wuya yayi saurin janyewa, Ajmal haka kawai jikinsa ya basa ya dago ya kallo sama karab idanunsa suka sauka kanta duk da bawai ya gama kare mata kallo bane ballai ya samu tabbacin wanda ya gani Nisha tayi saurin sake labule ta yi baya da sauri ta haye saman bed ta kwanta Ajmal sauke Kai yayi gamida karisa shiga side din na sa. Nisha ta na ganin yanda Aheel ya ke ta juyi yana neman farkawa wanda tun bayan mangariba ya kwanta bacci har zuwa yanzu kusan 10:30 nan ta kuma ganin Aheel ya bude idanu tar yana wulwulga idanu wanda ya sanya Nisha saurin rintsa ido kamar mai bacci ko hakan zai sa ya koma bacci because dare yayi sosai bazata iya da wainiyar kaishi side dinsu ba Amma gamamakin ta sai ji tayi ya kwanto jikinta cikin muriyar bacci ya shiga kiran sunanta ya na tashinta ya na fadi'n zaije papansa because Aheel ya saba inba jikin papansa ba baya iya bacci mai kyau saboda ya wanci a jikinsa ya ke kwana ya ke ta shi. "Aunty ki kai ni gurin papana" Aheel ke ta fad'i ya na mai mai tawa ya neman kuka bude idanu Nisha ta yi ta zauna gamida kallon Aheel tana faskantansa sannan ta ce "Please kakoma ka kwanta ba ka ga dare yayi ba ne sosai kabari gobe da safe sai na kai ka gurinsa " Nisha ta fad'i but sai ganin Aheel ta yi ya langwabe kai gamida ma ke shoulder alamar ba zai yadda ba yanda ya marairaice mata ya na neman kuka ya sa dole ta sakko da shi ta dauki mayafi ta ya fa bisa kanta daga nan ta sunkuci Aheel ta daga shi bisa hanun ta suka fice. Ko da su ka fito gari yayi shiru sai kukan halittu kakeji security da ke gefe shima tuni ya kishingid'e yayi bacci haka Nisha ta tura door din a hankali ta shage parlourn da Aheel a hanunta da idanunsa su ka cicciko yana zaresu. Nisha maimakon ta kaishi gurin papan nasa sai ta wuce dashi bedroom din sa a hankali ta na sanduwa kamar mara gaskiya. Kwantar da shi tayi bisa lallausan be din nasa ta g'yara masa kwanciya ta rufe shi da blanket Aheel sai binta da kallo ya ke ganin ba ta kaishi gurin papan nasa ba ta kwantar da shi anan shikuma papan nasa ya ke son gani , Nisha ganin kallon da Aheel ke mata duk ya wani marairaice yasa ta sakar masa murmushi gamida shafo saman goshinsa ta na fadi'n "I'm here" nan Aheel ya ga ta kwanto gefensa gamida da daura hanuta bisa bayan shi ta na shafosa ta na dan bubbuga bayan nashi kamar wani jinjiri dan dai ta samu yayi baccin aikuwa harwani sauke ajiyar zuciya ta ji ya nayi daga nan Nisha ta rintsa ido kamar ta yi bacci daga nan shima Aheel ya kulle ido kankance mai ya koma baccin sa sai sauke ajiyar zuciya ya ke. Slowly Nisha ta zame jikinta ta sakko daga bed din gamida rage masa light ta fito ta janyo masa door din a hankali ta rufe, tajuya ta suma ta fiya cikin sanda tana jan ka farta dai dai time din da Ajmal ya budo door ya fito daga bedroom din sa daga shi sai towel da ke bisa waist d'insa sai wani dan k'aramin towel da ke hanunsa ya na goge suman kansa da shi da alamar daga wanka ke ya fito ya na shirin nufa downstairs kamar wanda aka ce ya kallo gefe idanunsa suka yi tuzali da Nisha wacce tayi tsayuwan cak ta kasa gaba ko baya tana sanye cikin duguwar rigar baccin mai laushi da santsi sam ba ta so haduwarsu da Ajmal ba but duk yanda ta so kaucewa masa sai da su ka hadu, . Kauda kai Ajmal yayi irin na ko in kula kafin ya tsaida abunda ya ke na goge suman kansa da ya ke ya sa ke dubanta still ko motsawa Nisha ba ta yi ba daga in da ta ke shiya rasa wani irin tsoronsa ta ke because duk sanda suka hadu ko yanai mata magana tsoro da rawar jiki ke fara bai yana ga yanayinta, Ajmal hanu yayi wa Nisha alamar ta kariso kusa kafin ta shiga karisowa da rawar jiki kamar yanda yayi tsammani kanta kasa ko kallonsa ta kasa yi ganin yanayin da ya ke ciki shikuma Ajmal ko ajikinsa har Nisha ta kariso gabansa ta tsaya, "What are you doing here " Aheel kawai ya iya jin ya fito daga bakin Nisha dan sai faman kame kame ta ke Ajmal kallonsa ya kai ga door din Aheel kafin ya sa ke kai kallonsa ga Nisha Wanda ya ka sa juran jiran abunda ta ke fad'i ya dai fahimci mai ta ke son cewa nan ya hade gira yana fadi'n "Kawomin coffee" dan dama abinda ya fito da shi kenan yana fadi'n haka ya juya ya koma bedroom d'insa tura baki Nisha ta yi tana sun ba tu kafin ta nufi downstairs jim kadan ta dawo dauke da cup din coffee bisa hununta ta nufo upstairs gamida karisawa bedroom din Ajmal ta tura door din ta shiga. kwance ta kalle shi syan bed ya kishingid'e yana sanyi cikin kyakykyawan rigar baccin sa yana danna laptop d'insa jin motsin shigowar Nisha ya sa ya dakata gamida kulle laptop din ya shiga kura mata idanu time din da ta ke karisowa, Nisha a hankali ta ke karisowa sai jan kafar ta ke kamar wani wanda ya mata nauyi kanta sun kuye ko kallonsa ba ta yi , daga gefe Nisha ta tsaya kafin ta shiga mika masa cup din coffee din ba tare da ta ce komai ba shi kuwa Ajmal bai amsa cup din coffee din ba time din da ta ke mika masa sai mata nuni yayi da ta ajiye shi gefe saman table. A hankali Nisha ta juya saman table ta ajiye cup din kamar yanda ya fad'i , juyowar da zatayi sai gani ta yi Ajmal ya mike tsaye hannayenshi na shafa gefen suman kansa ya shiga ta kowa gurin table d'in inda Nisha ke tsaye ta ajiye masa cup din coffee din kenan ta juyo suka hada ido kauda kai Nisha ta yi gamida zamewa gurin ta na kokarin barin wajan, cike da tsoro da mamaki sai gani ta yi Ajmal ya tsare mata hanya ya sha gabanta ya tsaya dam k'irjinta ya buga , shiru Nisha ta yi ba ta iya ko motsiba ganin ya na tsaye gabanta bai kauce ba haka ya sa Nisha kauce masa saboda a tunaninsa ko ita ta tsaya masa bisa hanya but sai gani ta yi ya sa ke ta kowa ya kuma tsayawa gabanta, a tsorace Nisha ta dago ta kalli Ajmal time din zufa ya suma tsatstsafowa goshinta gani ta yi idanun Ajmal na kanta ya tsareta da ido ya na jifarta da wani irin kallo wanda ta kasa fassarashi ko na mai ne ne koma bai iya ce da ita k'ala ba. Karo na uku Nisha ta sa ke yin gefe cikin hanzari tana kokarin barin gurin Ajmal kafarsa ya sanya cikin na Nisha Wanda ya sanya Nisha ta fiya luuu ta na naiman fad'uwa cikin sauri kuma Ajmal ya rikota gamida fisgota ta fado jikinsa, nan fa Nisha ta shiga yin wuri wuri da idanuwa , Ajmal yana jin yanda zuciyar Nisha ke bugu da cikin sauri kuma da karfi ta kumq kankameshi da karfi ta rike shi saboda tsorita da tayi jim kadan kuma ta shiga zame jikinta tare da tunanin mai yasa ya sanya mata kafa ya na neman yar da ita because ita dai ta San ba tuntub'e ta yi ba . But sai ji ta yi Ajmal ya kuma riko ta da kyau daga kokarin barin jikinsa da ta ke, rankwafo da kai Ajmal yayi daidai face d'inta numfashinsu ya na gamewa da na juna suna kuma kallon juna Nisha sai zare masa ido ta ke ta na kallon jin rokon da ya mata ya ki sa kinta. Nisha ba ta ankaraba sai jin Ajmal ta yi ya kai hand d'insa daya kan waist d'inta gamida da matsa waist d'in na ta da karfi wanda ya kuma sa Nisha zabura da sauri ta zame jikinta cikin hanzari ta yi baya gamida g'yara mayafin ta da ya zame ya bar saman kanta numfashin ta sai fisga ya ke aikin tsoro sai fiddu idanu waje ta ke ta na k'yarma kamar wata maijin sanyi. "Gudun mai kike? akwai wani abinda na yi da ba daidai bane?" Ajmal ya fad'i time din da ya ke karisawa ga re ta ganin haka ya sa cikin hanzari Nisha ta naimi hanyar fita ta fice a guje cike da tsoro da firgici duba da ya nayinda ta ga Ajmal ya koma ciki , duk da kasan cewar dare tayi sosai gari yayi tsit hakan bai hana Nisha fitowa daga side din Ajmal kamar wata mota ba fuuuu ta nufi sashinsu ta na isa bedroom d'insu ta nemiguri ta kwanta tayi lamo ta na sauke ajiyar zuciya cikin rawar jiki Nisha ta ja blanket ta rufo jikinta gaba daya har kanta ta shige ruf kirjinta sai bugun uku uku ya ke, . Shikuwa Ajmal saman sofa ya nema ya zauna gamida rintsa idanu ya rasa mai ya ke da munsa yanzu because yanzu duk sanda suka kasance da yarinyar rasa nitsuwarsa ya ke duk da yanzu k'ark'ashinsa ta ke kuma mallakinsa but ba yaso alakarsu ta yi wani nisa saboda hankalinsa Sam ya kasa kwanciya da ita because duk sanda suka hada ido yanayin rashin gaskiya da tsoro ke fara baiyana kan fiskarta, ko abu ta ke cikin tsoro ta ke gabatar da shi kamar a ce mata shhhiiii ta gudu , wani zazzafan iska Ajmal ya furzar gamida kallon cup d'in coffee din da yasa ta kawo masa duk ya suma hucewa nan ya mike jiki ba kwari ya haye saman bed d'insa ya kwanta face d'insa na kallon celling daga bisani ya rungumo lallausan pillown baccinsa ya rungume gamida rintsa idanuwansa, face d'in Nisha ne ya sa ke baiyana masa yayinda ta ke zaro ido waje time din da ya matsa waist d'inta tsoro ya baiyana kan fiskarta ta yi ba ya har tana shirin tuntub'e Ajmal baisan sanda murmushi ya kwace masa ba ko ba komai wani lokaci tsoronta gareshi ya na bashi nishadi. Bayan kwana biyu weekend guraren yamma wajan la'asar Nisha ta farka daga baccin da ta ke tun da azahar yau kusan ita kai ta wani because su Reeda su na can privet class inda Ammi ta kaisu wajan koyar dasu girke-girken zamani da na gargajiya , mike wa Nisha ta yi daga kwanciyar ta sakko ta nufi bathroom ta yi yo alwala ta fito ta gabatar da sallahn azahar idawarta kenan ta ninke sallayen ta ajiye sai ganin barka ta yi tashigo cikin bedroom din fiskarta dauke da fara'a "Antashi daga baccin ne dazu Hajia ke ta da kokonki ai Ammi ta ce kina bacci da alamu yau kinyi kewar yan surutan na ki" Barka ta fad'i tana kallon Nisha ta na murmushi gamida ba ta amsa da cewa "Dama yanzu na ke shirin fito wa na sa me ki ko da wani aikin da zan kama miki kar kewar ta min yauwa" "Ke dai ba kya ra ba kanki da aikin wahala dama na zo na sanar da ke ne yanzu yayanku ya turo a kirawo ki shine na ce bari na duba ko kin ta shi daga baccin" haka kawai Nisha murmushin face d'inta ya kau k'irjinta ya shiga bugu yanzu kuma komai zai ce mata oho "Ince dai lapia naga fiskarki ta sauya" Barka ta tambaya ganin yanda ta ke yanke fara'ar Nisha ta gushe "Ah bakomai " Nisha ta fad'i a hankali "To madallah maza hanzarta" Barka ta fad'i daga haka ta wuce ta fita daga bedroom din, Nisha sanye da hijab dinta wanda ta yi sallah ba ta samu Daman cireta ba ta fito ta bi bayan Barka da ga nan ta fice daga parlourn ta nufi side d'in Ajmal. Tura door din ta yi ta shiga bakinta dauke sallama, kwance ta sa meshi ya mike saman duguwar sofa ya na sanye cikin riga t shirt da guntun wando iya ka gwaiwarsa kana iya ganin yanda kyawawan gashin kafarsa suka kwanta su ka yi luf da su gwanin sha'awa phone dinsa na bisa lallausan hanusa ya na dannawa . daga gefe Nisha ta samu guri ta duka kanta kasa kamar yanda ta saba "Sannu da hutawa" Nisha ta ce cikin sassanyar voice d'inta, lumshe idanu Ajmal yayi ya bude ba tare da ya amsa mata kafin ya ajiye phone dinsa gefe gamida kai kallonsa ga re ta wacce ta ke sanye cikin duguwar hijab ta k'udundune kanta kasa kauda kai yayi yana fadi'n "So kike sai na daga murya? close to me" Nisha daguwa ta yi ta kalli Ajmal wanda ke hararo ta ya na magana , ba tare da musuba a hankali Nisha ta shiga matso dab da kujeran da ya ke sannan ta ajiye gwaiwowinta ta zauna kamar mai daukan karatu. " Kin sani cikin tunani labarin da kika bani game da rayuwarki while na kasa gasgata labarun na ki but inaso naga wasu shaida da zaisa na gasgata ki na yarda da ke". Dagowa Nisha ta yi ta kalle Ajmal time din da ya ke zance kamar mai wani rad'a "Wa., wata shaida kenan ?" Nisha ta tambaya cikin sarkewar murya "Gidan ku da kuma Auntynki da kuma mahaifin naki tunda kince suna cikin garin nan" g'yada masa kai Nisha ta yi alamar eh kafin Ajmal ya jinjina kai yana fadi'n I need to see them daga haka yamike ya na kuma fadi'n Ba sai gobe ba yanzu dan haka kishirya ki sa me ni , ya na gama fadi'n haka ya juya ya nufi upstairs, wani farin ciki ne ya ziyarci zuciyar Nisha yau kam Mami ta shiga hanun magark'ama ko da tsiya tsiya sai taga mahaifinta yau Mami zata fad'i inda ta kai Abbanta da ta ke hanasu ganin da zarar sunje, Da barin jiki Nisha ta fice ta nufi sashinsu sai murna ta ke tana shiga bedroom dinsu kaya kawai ta canza ta saka duguwar rigar atamfa ta daura mayafi bisa kanta dan ko dan kwali ba ta daura because ta san bazai zauna kanta ba kuma ita ba iya daura shi ta yi yanda zai zauna ba ko a gida time din da su ke tare da umma wani time din ita ke daura mata yau Nisha harda su lipstick da yar fauda gamida kwali abunda ta dad'e ba ta yi ba shape shape ta gama kimtsawa ta yi kyau da ita sai sanyen k'amshi ta ke a hanzarce ta fito parlour nan ta ci karo da Ammi wacce ta sakko daga upstairs ta na shirin nufan kitchen ganin Nisha cikin sauri ya sa ta ja ta tsaya ta na kallon ta, itama Nisha tsayuwar tayi ta kama sosa Kai irin na rashin gaskiya,. "Ke fa ina zuwa na ga kina ta sauri haka" Ammi ta tambaya gamida fiskanto Nisha ta na kallonta "Am,. dama fita zamuyi " Nisha ta fad'i ta na yan kame kame Ah aiyo to na fahimta ke da yayan na kune kenan " Ammi ta tambaya tana washe baki gyada kai Nisha ta yi alamar eh sai sunnar da kai ta ke "To maza kije karyaita jira adawo lapia," daga haka Nisha ta fice sumu sumu Ammi kuwa sai murmushi ta ke tana hamdalah da alama kansu ya suma haduwa gashi harfita zasuyi tare duk da ba ta san ina suka nufa ba. Nisha na fitowa shima Ajmal time din ya fito daga side dinshi yana sanye cikin kananun kaya yayi kyau da shi, tsayawa yayi yana jiran karisowar Nisha time din da ya ga tafito Nisha ta fiya slowly kamar baza ta taka kasa ba duk da dama yasan al'ardata ne haka sam ba zata maka abu cikin sauri da kuzariba. kallon daya ya mata time din da ta gama karisowa ya kauda kai ganin yanda ta ci uban lipstick kamar anyi barin mangyada sai shining ya ke yana kyalk'i , nan Ajmal ya kutsa kai ya shige motar driver ya maida kofar ya rufe yayinda itama driver ya bude mata murfin kofa gindan baya tashige sannan ya rufo kafar daga nan driver shima ya shiga because shine mai driving dinsu. Dalilin da yasa Ajmal ya bukaci driver because ba ko ina ya sani cikin garin kano ba but shikuma driver ba lungu da sakon da bai sa ni ba, daga nan driver yayi wa motar key mai gadi ya bude musu gate suka fice, sai da suka dau hanya kafin driver ya d'an kalli Ajmal da ke danna phone dinsa cikin girmamawa ya ce "Ranka shi dad"e ina muka nufa" Ki sanar da shi gurin da zamu Nisha da ke tsili tsili da ido cikin mota ta jiyo muryan Ajmal na magana ba tare da bata lokaci ba Nisha ta shiga yiwa driver kwantace da kuma inda zaiyi tsaf kuwa driver ya gane kwatancen Nisha ya canza a kalan mota suka nufi cikin unguwar da Nisha tai masa kwatance . Ba da daiwa hanya ta kawo su cikin anguwar Nisha sai mika wuya ta ke ta na leke zata iya cewa da ba dan tasan anguwar farin sa ni da zata iya cewa sunyi batan hanya ganin yanda anguwar ta canza cikin k'ank'anin lokaci anguwar sai ta koma kamar wata sabuwa because wasu ya na yi da zare tsare na tituna da aka shin fida a unguwar ga wasu gidan da ta ke gani rabi arushe titi ta bi ta kansu. Shidai har inda ta san gidan Mami ya ke sun shigu but sai ba gidan ba alamarsu yan hanjin cikin ta ne su Kai wani irin kadawa da zuciyarta da ke wani irin bugu idanunta kuwa kamar masu shirin bullukowa waje. "Hajia daga nan kuma ina zamuyi" Nisha ta ji driver ya tambaya jin shirunta ya sa shi kanshi Ajmal ya dago kai gamida ajiyiye phone d'insa gefe ya juyo ya kalleta " Ina magana kinyi shiru why" Ajmal gani yayi Nisha ta sanya hanu ta murd'a handle door din ta fice cikin sauri ko tsayawa ya g'yara parking ba tayi ba, gaba ki daya daga shi har driver bin Nisha sukayi da kallo wacce ta ke ta juye juye ta kalli nan ta kalli can gaba ki daya kanta ya juye anguwar gabaki daya ta sauya mata. Ajmal face mask d'insa ya zaro ya sanya ya Zama idanuwansa kadai a ke iya ganin kasan cewar yau cikin gari ya shigo ba mamaki ya zama abin kallo daga nan ya fito daga cikin motar ya nufi inda Nisha ke tsaye tayi suman tsaye idanunta na kokarin kawo ruwan hawaye "tsayuwar mai kike? Ina gidan mahaifin naki ya ke?" Ajmal ya shiga je ro mata tambayoyi ya na kallon ta. shiru Nisha ta yi ba ta kulashi ba sai kalle kalle da ta ke hawaye na gangarowa daga kyawawan fararan idanunta. "I'm talking to you so what are silent? Ajmal ya kuma fad'i Still shiru ba ta amsa shi ba ya sa Ajmal jan hanun Nisha but sai ya ga ta janye hannayenta gamida a zawa bisa kanta gamida Kiran sunan Abba saboda rudu da tashin hankali kanta harwani sarawa ya ke ya na juyawa ya ganin ba gidan ba alamarsa babu komai sai kwalta gaba daya ta firgita ta tsorata yanzu wata dunyar ta san Mami ta sa ke cilla mahaifin na ta . Ajmal ganin kame kame da Nisha ke gamida waige waige ta ma rasa ma kama daya ballai ta amsa masa tambayoyinsa , kallon ta kawai Ajmal ke yi irin na tuhuma because da ma ya San za arina hakan karshe a zo ta shigayin kame kame irin na marasa gaskiya wani yayyafi mai karfine na ruwa sama ne ya su ma sauka kasan cewar gari yanayi na hadari nan da nan ruwa ya su ma saukkowa. Wani kallo Ajmal ya wurgawa Nisha gamida matsawa dab da ita ya finciko hand dinta da karfi da nufin komawa su shiga mota su ta fi amma Nisha kyam ta kafe ta ci je da kokarin kwace hand dinta ta yi ba ya cikin kuka ta ke fad'in "Please ni dai ku ta fi ku barni anan ba inda zani na bar Abbana bansan halinda ya ke ciki ba please and please leave me alone" Nisha tafad'i cikin kuka harda shashsheka ta na yin baya gamida hade hannayenta guri guda alamar roko. Wani guntun tsaki Ajmal ya ja gamida sake fisgo hannayenta yarike gam ya na fadi'n "Let's go" nan fa Nisha ta shiga kiciniyar kwace hand dinta but ta ji ya ri ke gam daga nan ta shiga kokarin zamewa kasa ta na kiran sunan Abba ta na shirin ta ra musu jama'a duk da kasan cewar unguwar ba hayaniya sosai kuma ba yawan giftawan mutane gashi ruwa har ya su ma jikasu. Ajmal duk yanda ya su jan Nisha abun ya ci tura kamar akuyar daure ganin haka cike da ta kaici Ajmal ya sun kuci Nisha saman shouldernsa kamar wata yar tsana ya nufi mota da ita haka ta dinga wuntsila kafafu ta na buri , nan Ajmal ya bude motar gidan baya ya azata ciki but da mamakinsa ga rigimar yarinyar sai kiciniyar kokarin fituwa ta ke ganin haka ya sa shima ya shige ya zauna gamida rikota kam jikinsa da hannyensa biyu ganin irin salon rikicin da Nisha ke yi ta na kuka ita ala dole sai dai su ta fi su barta a gurin Ajmal duk yanda ya so ya nitsar da ita ta koma haiyacinta abun ya gagara gaba daya ta rikice masa. Ajmal Kallon driver yayi wanda yayi tsuri ya na kallon ikon Allah kafin ya sanar dashi ba gida zai mai da su ba ya wuce da su guest house d'insa kai tsaye cike da girmama umarninsa driver ya dauki hanya ba bata lokaci sam Nisha ba ta cikin tunanin ta ballai ta san abunda Ajmal ke fadi'. Luf ta labe jikin Ajmal gamida rintsa idanu tamkar mai bacci ta saduda because ba yanda ta iya but da ta na da yanda za ta yi da ko door d'in motar ne sai ta balla ta fi ce inyaso ko wani motar ne ta bi ta kanta ta mutum kowa ya huta , ko itama ta huta da wannan kaddaran rayuwar. Wani irin sauke ajiyar zuciya kawai Nisha ke yi cikin sauri sauri gaba daya hankali da nitsuwar ta ba ya tare da ita tunaninta naga rashin sanin wace duniyar Abba ya dosa ya na tare da waccer azzalumar matarsa wacce ba ta san wani hali ta sanya shi ba , sanadinta ya ba ce tsawon lokaci ya kasa ne mansu sai su ke ta yawon ne mansa. Time din da su ka kariso ruwan sama sai dad'a karfi ya ke nan da nan driver ya shiga danna horn sai da mai gadi ya leko kai dan ganin waye cikin hanzari ya koma ciki gamida ya yaye musu gate d'in gidan kafin driver ya kunno motar ta sako kai haraban gidan ya nufi parking space yayi parking. Ajmal zame jikinsa yayi daga na Nisha face d'insa babu alamar wasa time d'in Nisha ta bude idanunta wandan da su ka kumbura su ka k'ank'ance saboda kuka ta shiga wulga idanu a tunaninta gida suka dawo but sai ta ga sa b'anin haka , k'irjinta ne ya cigaba da bugawa sauri sauri ina ne nan kuma da su ka zo. Idan ba ta mance ba nan suka taba zuwa dashi ya shiga ganawa da d'an su mutane da ta tambaye shi ya ce gidan yankan kai har ya na mata ikirarin gidan da zai sai da ita ne . gwalalo idanu Nisha ta yi ta nabin Ajmal da shi fitowa yayi daga motar kafin ya rank'wafo Kai ya kallo Nisha wacce ta makale cikin mota sai muzurai ta ke ba ta da niyar fitowa Ajmal cikin hade gira ga ruwan sama da ke ta faman jikashi ya hararo Nisha gamida fadi'n " Come out" but sam ta nuke ta ki fitowa dama ya san sai tayi masa musu gashi duk ya gama jikewa da ruwa sharkaf dan haka bai sa ke yin magana ba ya jawota yafito da ita ya sun kuce ta bisa hand d'insa ya nufi ciki da ita. Direct bedroom ya nufa da ita ya di re ta saman lallausan gadon kafin ya fito cikin sauri ya mai da door din ya rufe yanda ba za ta ayi fitowa ba, ya nufi dayan bedroom din ya je ya sauya kayan jikinsa kasan cewar wadan can sun jik'e daga nan ya dauki umbrella ya fito hara ban gidan ya koma ciki motar daga nan suka sa ke ficewa daga gidan. Nisha jikinta sai rawa ya ke ya yana k'yarma yayin da ta ke bugun door d'in ta na kuka ta na rokonsa da ya bude ta tsoro da firgici duk ya cika kwanyarta Nisha cikin sauri ta nufi window inda ta ke jin kiciniyar bude gate yayinda ta ga motar Ajmal ya fice daga haraban gidan, wajan ta tsuguna ta shiga rero kukanta ta na shashsheka sai da ta yi kukan ya ishe ta wanda harsaida ta su ma jin ciwon kai kafin ta koma gaban bed saman carpet ta k'udundune jikinta duk ya dausanyi sai bari ta ke sanyi AC ga kuma kayan jikinta da ya jike haka ta takure gamida hada kai da gwaiwa ta na kukan zuci. 'Why ? ya kawota nan ya rufe yayi ta fiyarshi ko yayi matsayin ma karyaciya ce ita wacce ta bashi labarin karya a karshe suspect d'insa ya tabbata a kanta ta zama makarya ciya a idanusa ta kasa gasgata labirin ta ga re shi , duk da dama shi already ya gama tsanarta ya kuma kasa daukarta yanda halinsa su ka dauke ta ' 'Why ? tun farko zuwan ta gidan nan ta kasa musu bayanin family din ta da rayuwarta maybe ma da andad'e da samun mafita yanzu gashi alamura sun cabe mata ta rasa tsammanin Abba then makaryaciya' Zane Ammi ta ke bakin bed sanye cikin rigar baccinta ta rabka uban ta gumi ta na tunani Daddy ne ya shigo cikin bedroom din ya na sanye cikin duguwar jallabiyarsa black color fiskarsa dauke da fa'ara ya karisa shigowa but ganin Ammi cikin hali na ta gumi ta na jimami yiwa amma ta rasu ya sa Daddy karisa ya zauna bisa bakin bed din shima gefe da ita ya na kallonta. "Ince dai lapia naga kin rafaka wannan ta gumi haka mai kike tunani" cike da damuwa Ammi ta kalli Daddy gamida fadi'n "Kamar yanda na fad'i tun guraren yamma Ajmal su ka fita da Nisha but haryanzu ba ko kwalkiyan daya daga cikinsu har dare yayi kowa na shirin kwanciya na kira wayarsa a kashe ita kuma Nisha already ma ga wayarta ta mance shi gida" murmushinsu irin na dattawa Daddy ya sa ki gamida jinjina kai yana fadi'n "To inbanda abunke wannan ne abun tunani da d'aga hankali ince dai yarinyar da mijinta su ka fita ba da wani ba da har hankalinki zai tashi haka kina tunanin ina suka shiga" "Eh duk da haka but aiba ayi tariyar ba tukun sai ya bari sai ta tare kafin yayi ikonsa a kanta nidai gaskiya hankali ya kasa kwanciya yarinya mai rauni irin wannan" "Yanzuma yana da iko akanta tunda matarsa ce halal d'insa kuma da igiyarsa uku bisa kanta to mai zai tsaya jira" Daddy ya fad'i cikin rashin damuwa da lamarin. "Yanzu abunda yayi yayi daidai kenan kana goyon bayansa "Ammi ta tambaya ta na mai tsare Daddy da idanu "please kibar wannan tunanin haka kikwanta zuwa gobe insha allah zai iya dawo da ita" Daddy ya bata amsa ya na kokarin g'yarawa ya kwanta "Oh zaima iyane ba ya dawo da ita ba ?" Ammi ta fad'i ta na bin Daddy da kallo wanda ya ke ta dariyan kasa jin mitar da Ammi ke yi kamar k'aramar yarinya "I think so ki kwanta kawai kijira tsammanin su gobe in Allah ya nuna mana" Shiru Ammi kawai ta yi ba ta sa ke magana ba but hankalinta ya ka kwanciya sam wannan ranar bata iya irintsawa da kyau ba, bangaran Hajia kuwa zuciyarta fari k'al tunda ta tsinci labarin jin Ajmal da Nisha sun fita tare alamar cewa Allah ya suma hada kansu dan haka cikin farin ciki da walwala Hajia ta kwana yau. Haka ta bangaran su Reeda duk sunyi shirin bacci sun kwanta but babu Nisha ba alamar ta da tunanin duniyar da su ka shiga su kwanta bacci su ma duk da sun san da yayan na su ka fice gashi ta bance phone d'in na ta agida da sun kira sunji lapiyar ta daga haka su ma baccin ya dauke su ma. Guraren 11 na dare time din tuni ruwa ya tsagaita da sauka sai d'an yayyafi ka d'an da ke diga dis dis tare da kyakykyawan yanayi na ni'ima da daddad'an ya nayi da ke wanzowa ko ta ina . Motar Ajmal ne ta danno kai cikin gidan yayinda mai gadi ya bude masa gate ya shigo yayi parking gamida fitowa ya bude door din gidan baya na motar ya janyo wasu kyawawan ledar guda biyu kafin ya rufo door din ya nufi ciki yana isa parlour ya ajiye ledar daya bisa table din parlourn kafin ya kunna kai bedroom din da ya jefa Nisha ciki. Ko da ya bude door d'in dakin bedroom d'in duhu kake iya gani alamar light d'in bedroom d'in a kashe su ke karisa shiga ciki yayi gamida karisawa ya nufi light ya shafa ya kunna tar haske mai kyau ya wanzo cikin d'akin. Can saman carpet ya hangi Nisha ta k'udundune sai rawar sanyi ta ke ko da ya kunna light baiga ta dago ko ta motsaba karisawa yayi kusa da ita nan ya ci karo da idanunta wanda su ke lumshe sai faman rawar sanyi ta ke tana sauke ajiyar zuciya Ajmal duguwar rigar jikinta ya bi da kallo wanda ya bi jikinta saboda damshin ruwan sama da ya ta bata ga kuma sanyen AC da ke ta faman aiki cikin bedroom d'in Ajmal ledar hanunsa ya ajiye saman table d'in bedroom d'in kafin ya kai hanu ya dauki remote control ya kashe AC ya bar aiki cikin bedroom d'in daga bisani ya kuma kai kallonsa ga Nisha wacce ke kwance kasa abun tausayi, Ajmal duk'awa yayi kusa da face d'in ta ya na fadi'n "open your eyes ki tashi ki zauna inason magana da ke" Shiru Ajmal ya ji Nisha ta yi ba ta motsaba ballai ya sa ran zata amsa shi, " Ba da ke nake magana bane?" Ajmal ya fad'i a tsawace gamida hade gira yana kallonta , Jiki ba kwari Nisha ta suma mikewa ta na k'yarman sanyi face d'inta duk ya kumburu idanunta sun kankance sun koma ciki sai da Ajmal ya mata kallon tsaf kafin ya mike tsaye ya kuma gurin table din bedroom din ya sanya hand d'insa cikin ledar da ya aje ya ciro wasu kyawawan kaya kafin ya kalli Nisha ya na fadi'n " ki tashi ki sauya wadannan kayan jikin na ki " ya na gama fadin haka ya di re mata kayan saman sofa daga bisani ya juya harya nufi door ya bude ya na shirin fita sai kuma ya kuma juyowa ya kallo Nisha ya na fadi'n "Kisame ni parlour idan kingama" daga haka ya sa kai ya fi ce , Nisha rintsa idanu ta kuma yi gamida rungomu jikinta duk ta takure jikinta guri guda , Jim kadan Nisha ta shiga mikewa tsaye gaba daya ji ta kinta a ma ce kafafuwanta sun mata nauyi kanta kuwa ji take kamar an a za mata kaya haka ta ta rarrafa ta nufi bathroom. sai da ta cire kayan jikin na ta kafin ta shanya rigarta ta tare da mayafin na ta kafin ta shiga yin wanda da ruwa mai dumin gaske kasan cewar ta saba yin wanka finta kwanta kuma ta samu kuma ta samu kutsari sosai ba kamar da zufa sanyi da mutukar jiki duk ya kau. Towel ta ne ma ta daura bisa jikinta daga bisani ta fito daga bathroom d'in slowly Nisha ta karisa gaban sofa inda Ajmal ya ajiye mata wadansu kayan nan ta shiga kallon kayan gamida dagawa ta tana dubawa . Wata tsadaddiyar kyakykyawan duguwar riga ce a baya maroon cold tare da mafinsa rigar ta yi masifar kyau da k'ayatarwa Nisha gefe ta a jiye rigar kafin ta sa ke kai kallonta ga daya rigar ta dauka tana kalla. Shi kuma y'ar rigar bacci ne mai taushi gamida sulb'i tare da wandonsa pink color rigar baccin shima yayi kyau sosai bugu da kari Nisha na sun abu pink color ya na mata kyau ya na kuma k'ayatarta da ita sai dai tayi mamakin ganin rigar baccin kenan kwana za tayi anan bazai maida ta gida ba Nisha ba waya hanunta ballai ta san ko yanzu time na wa ne wasu sabbin hawaye a ne suka shiga zubuwa kyakykyawan kumatun ta kafin ta dauki kayan ta suma sa wa. Ajmal dake zaune parlour saman sofa ya mike kafafuwa ya daura daya kan daya yana shan zazzafan coffee yana kuma danna phone dinsa nan kuma ya a jiye wayar kafin ya gyara zama gamida a jiye cup din hand d'insa ya shiga jan wani gutun tsaki yana Kallon saitin door din da Nisha ke ciki canza kaya kawai shine ta jima haka ji yayi gaba daya ya ga ji da jira. jim kadan sai ji yayi ta murd'a handle door gamida fitowa a hankali sumu sumu da ita ta kariso tsakiyar parlourn gefe ta ne ma saman carpet ta zauna kanta kasa ko hada ido dashi ta kasayi, Ajmal Kallon Nisha ya ke sosai wacce ta sunnar da kai kasa kamar yanda ta saba da zaran sun hadu ko suna tare , "Close to me and have a seat" Nisha abunda ta ji Ajmal ya fad'i kenan ya na kallota Shiru Nisha ta yi kamar ba ta ji abinda ya ce ba sai kuma ta dago kai ta kalleshi suka hada ido kafin ta maida kai kasa ta mike jiki a sanyaye ba musu ta karisa inda ya ke zaune ta shiga neman guri kasa ta zauna, nan ta ji Ajmal ya janyo ta da karfi wanda ya sa ta fadowa jikinsa bisa cinyarsa. A razane Nisha ta dago kai ta kalle shi gamida kokarin zamewa daga jikin nasa but sai ta ji yarike ta gam ya na binta da wani kallo, nan ta ga Ajmal ya matso da face dinsa sosai har numfashin su na gauraya da na juna kafin taga Ajmal ya matso da lips d'insa dab kusa da nata kamar mai Shirin mata kiss wanda ya sa Nisha rintsa idanu gam duk tsoro ya cikata gashi ya mata kyakykyawan riko ba halin kwacewa, nan kuma ta ji ya kusa kai gefen suman kanta ya na shinshinar gefen wuyarta wanda ya sanya Nisha sa ke idanu da karfi ji ta yi kamar ta sake fitsari . A hankali Ajmal ya kai labb'ansa saitin kunnenta kamar mayin rad'a "I can't believe you! kin sanya ni cikin tunanin na kasa gasgata ala'amuranki wata zuciyar ta na son yarda da ke but wasu halayenki na sa nakasa yarda da ke ". "But tall me ya zan fara yarada da ke da kuma gasgata ki gameda rayuwar ki? " Ajmal ya tambaya yayinda Nisha ta jiya kai dayan hand d'insa yana mata ta fiyar tsutsa saman lallausan rigar baccinta zaro idanu waje Nisha ta yi cikin tsoro da firgici da rashin sanin mai Ajmal ke kokarin yi haka wanda ko a mafarki baza ta taba tunanin haka ba wantsilwa ta yi da sauri ta bar jikinsa tayi baya da sauri ta na kallonsa k'irjinta sai bugun uku uku ya ke sabida tsoro. "Please kayar da dani wallahi babu karya cikin lamarina ko dan gane da labarin rayuwarta but idan ba kayarda bani ba na amince nayi nesa da ku nabar cikin rayuwarku na kuma tawa rayuwar inda na fito na zanje na ne mi mahaifina da kaina kuma nayi alkwarin gabatar dashi gare domin gasgata ni Amma ni ba makaryaciya ba ce koma kadaina kallona haka" Nisha ta fad'i cikin kuka tana hawaye Ajmal kansa sunkuye ya rintsa idanu Ajmal ya na sarrafa tunani da nitsuwar sa jikinsa duk ya suma mutuwa shiyarasa mai yake shirin faruwa tsakanisa ga yarinyar duk da wani abun ya kanyi ne dan ya ga wannan tsoro da firgici na ta bawai dan wani abuba but zuciyarsa da tunanin sa da ke d'arsa masa wani yanayin dangane ga yarinyar ya ke kasa control din kasan wanda watarn zai iya wuce gona da iri wanda kuwa baya fatan hakan because zai da de yana da na sa nin hakan, daga nan ya mike tsaye wanda yasa Nisha sa ke zaro idanu ta na neman gurin shiga sai kuma ta ga ya suma kokarin barin parlourn. Sai kuma ta ga ya d'an tsagaita daga tafiyar da ya ke ba tare da ya juyo ya kalleta ba "Ga wadannan a bubuwan na saman table ki dauka ki ci " yana ga ma fadi'n haka ya juya ya nufi daya daga cikin bedroom d'in parlourn, wani nan nauyan ajiyar zuciya Nisha ta sa ki gamida lumshe idanu ta na jin yanda zuciyarta ke mata wani rin zafi komawa tsakiyar parlourn ta yi har time din zuciyarta ta ba ta daina bugu ba haka zalika tsoro da firgici bai bar jikinta ba. zubewa saman carpet ta yi gamida hade kai da gwaiwa ko ta kan ledar da Ajmal ya ajiye saman table din ba ta yi ba ta shiga riro kuka kasa kasa ta tabbata nan zata cigaba da zama maybe ma nan zata karishe rayuwarta sai randa ya ji ya gamsu da ita tunda ya kawota nan ya ajiyeta . Ajmal tunda ya shiga bedroom ya suma cire kayan jikinsa ya nufi bathroom, wanka yayi sosai kafin ya fito ya nemi duguwar jallabiyar sa ya zire ya nufi bed ya kwanta gamida janyo blanket ya rufo jikinsa, lumshe idanu Ajmal yayi gamida tunanin zantukan Nisha ta na shashsheka kuka mai tsuma rai da zuciya bacci ya kasa daukarsa sam sai juye ya kai shi kadai bisa gadon da kyar ya samu baccin ya ci karfin idanunsa. Da asuba jikin Ajmal duk a ma ce gashi ko wani baccin kirki bai iya yiba pillow da ya rungume jikinsa ya kawar gefe gamida sakalo dugayen kafafuwansa kasa ya sakko daga saman bed din a daddafe ya nufi bathroom ya yiyo alwala cikin bedroom din ya fito yayi sallah dan ko masallaci bai iya tunanin fita yanzu , bayan idar warsa ya dad'e zaune kan sallayan ya dan lazimi wanda daga bisani ya mike ko sallayan bai ninke ba ya koma bed ya kwanta gamida lumshe idanu, k'aran wayarsa da ya jine alamar kira ya sashi bude batare da ya motsa daga inda ya ke ba ya kai hanu ya janyo phone din ya saita face dinsa Dan ganin wake kira da asu ban nan ganin Ammi ce ke ta faman rangwada masa kira duk ta damu rashin ganin Nisha cikin gidan kuma hankalinta ya kasa kwanci duk kasan cewar ta a tare da Ajmal. Mikewa Ajmal yayi daga kwanciyar da yayi yana ganin har kiran wayar ta katse bai samu daman dagawa ba yarasa wani irin damuwa family dinsa su kayi da yarinyar gaba daya hankali Ammi ya kasa kwanciya tun jiya ta ke kiranshi da magarib wanda daga karshe ma kashe wayar yayi gashi yanzuma ta kuma kira da asuba d'in nan duk da baisan damuwarta a kan hakan ba tunda shi dai ya kasance miji a gareta mai kula da ita da duk wani halinda zata tsinci kanta ciki so bai ga abunda damuwa ko daga hankali ba. Ajmal gaba daya kuma sakkowa yayi daga bed din ya nufi parlour ko da zuwan sa tsakiyar parlourn ya cikaro da Nisha kwance saman carpet ta ruf da ciki gamida k'udundune wa face d'inta na kallon gefe gashin kanta duk ya har gitso ya rufe face d'in na kirif , gefe kuwa saman table d'in yanda ya bar ledar haka ya zo ya tarar da shi ko ta bawa ba tayi ba cikin na tsuwa Ajmal ya ta ku inda ta ke kwance ya tsaya gamida dukawa kusa da face d'in na ta ya sanya hand ya janye lallausan gashin nata wanda yake baki wuluk da shi shining ya ke nan ya matsar da shi gefe ya shiga karewa kyakykyawan face din ta kallo yana ganin yanda naman saman idanunta suka kumbura saboda kuka ba k'aramin tausayi ta bashi ba sam abin kuka baya mata kadan shi ya na gama kamar kukan dad'i ya ke mata shiyasa abu kad'an zai iya tsokano hawayenta. Ajmal hanu ya kai da niyar dagota daga kwanciyar da ta ke saman carpet izuwa cikin bedroom but Nisha kamar wacce ta ke ankare ko take jira a taba ta tar ta bude idanu ta shiga zareso time din da ta kalli Ajmal d'urk'ushe gaban ta ya kai hanu ya na neman dagota aikuwa cikin zafin na ma Nisha ta mirgina ta mike tsaye gamida yayin baya ta na kallonsa sai sose sosen Kai ta ke ta na ya mutsa fiska ta na neman yin kuka shikuwa Ajmal baki ya saki ya na kallota ya rasa tsoron uwar mai ta ke daga bude ido ta ganshi sai kawai ta kama gudu kamar ta ga wani dodon . Ajmal cike da ta kai ci ya mike shima gamida hararo Nisha wacce ta manne jikin bangon parlourn ta na muzurai, Ta kowa Ajmal ya kuma yi gadan gadan ya nufota cikin hanzari Nisha wuf ta zame ta shige bedroom cikin sauri ta maida kofar ta da tse, Ajmal tsayawa kawai yayi yana jinjina kai harwa yau mamakin tsoro irin na yarinyar ya ke ko mai ta kewa gudun oho, tunanisa randa a ka waye gari ta shiga ma komarsa ba halin guduwa ya kenan ranan kam ya naga sai dai ta hadiye ranta , wani k'ayataccen murmushi Ajmal ya saki wanda bai shiryawa yinsaba wanda daga bisani ya juya ya koma ya nufi cikin bedroom, koda ya shiga direct bathroom ya nufa wanka ya kumayi kafin ya fito ya kimtsa tare da shiryawa cikin ingantaccen shiri kafin ya dauki phone d'insa ya nufo parlour ya nemiguri saman duguwar sofa ya zauna. Hanu ya kai ya dauki remote ya kunna TV nan ta ke ta suma aiki daidai channel din BBC hausa shiru Ajmal yayi ya kurawa TV idanu wanda daga bisani ya mike kafafuwa gamida kwantar da kai ya maida kansa na kallon sama idanunsa na kallon celling shiru yayi kamar mai nazarin wani abu jim kadan kuma ya kuma g'yara zama gamida furzar da wani sassanyar isa cikin bakinsa wanda daidai time din ne phone dinsa ya shiga rori alamar kira daga zaune inda ya ke ya wurga manyan idanuwansa sa jikin screen d'in wayar ya hango sunan mai kiran kafin mike ba tare da ya amsa kiran ba Ajmal ya janyo phone d'insa ya wurgata cikin pocket d'insa. Ledar saman kan table din da ya ajiye tun jiya saboda Nisha Amma ba ta kulashiba bare ta bi ta kanshi ya dauka daga nan ya kama hanyar fita daga parlourn sai da ya zo har daidai bakin gate ya samu daman tsayawa mai gadi ya ta su cikin rawar jiki ya shiga rangwada masa gaisuwa gamida dukawa kamar zai masa sujjada cike da girmama wa,. Sai da Ajmal ya amsa kafin ya mikewa mai gadi ledar hanunsa mai gadi ya amsa sai faman sambad'a godiya ya ke ya na washe baki kafin Ajmal ya umarcesa da ya bude masa door zai fice cikin rawar jiki da hanzari mai gadi ganin mai gidan nasa na kokarin fita a kafa ya sa mai gadi tunani ko wani aikan zashi "Ah ya lallabo'i wani abun kake da bukata daga wajene yanzu aje akawo?" " No! Don't worry just open the door for me" jiki na bari mai gadi ya bude masa gate koda budewa sai hango wata kyakykyawar motar white color dalleliya gwanin sha'awa da burgewa da alamar motar tana fakene ta na jiran isuwar Ajmal sai dai ko wanda ke cikin motar ba ayi hangowa ballai kasheda wanene because glass din motar baki wuluk take . Ajmal ya na isa gaban motar ya bude kofar motar ya shiga daga nan akayiwa motar key motar ta d'aga suka bar area gurin, bangaran Nisha kuwa tunda ta shiga bedroom ta rufe ta nemiguri gefen bed ta zauna ta na zare idanu gamida maida ajiyar zuciya kirjinta sai wani irin bugu ya ke da karfi karfi, ta dau tsawon lokaci zaune haka ta yi shiru ita kadai bisa dakin ta na karanta wasikar jaki ita sam ba tasan asuba ta yi bama har gari ya suma wa yewa gashi ita ba waya ba haka zalika ko kiran sallah ba ta jiba ballai ta san time din sallah yayi because guest house d'in Ajmal yayi nisa da jikin gari sai time din ta shiga kallon bangon bedroom din sannan ta ci karo da kyakykyawan agogo manne jikin bangon bedroom din. a sukwane Nisha ta mike ta nufi bathroom ta dauro alwala daga bisani ta kai hanu ta janyo duguwar rigarta gamida mayafin ta fito kamar wani wanda akasa ta tsayawa kallon cikin bedroom din domin tsayawa ta yi musamman ta na karewa bedroom d'in kallo ta kalli nan ta kalli can bedroom din ya kwanto matuka komai na ciki blue and white gwanin sha'awa da burgewa komai fine Kai ka ce dama can da mutum wanda ke rayuwa ciki tsakiyar dakin ta koma ta shiga sauya kayanta daga rigar bacci izuwa duguwar rigarta gamida rufa mayafin jikinta kafin ta nemi sallaya ta shin fida ta shiga ta da sallah. Bayan idarwarta ta shiga mika hannayenta sama gamida kwararo addu'oi ga ubangiji mahalicci sosai da sosai kafin ta mike ko sallayan ba ta tsaya ninkewa ba ta sa hanu ta fisge mayafin jikinta ta cillashi gefe, can saman bed ta nufa ta kwanta ta shiga yin sana'arta ta da ta saba na aikin kuka da ba ya mata wahala, sai da ta yi ya sheta harkanta ya suma yin ciyo kafin ta iya tsagaitawa har bacci yayi nasaran cinye idanunta because dama daran jiya ba ta yi wani baccin kirkiba. Nisha ita ce ba ta samu farkawa ba sai guraren 10:30 wani azabeben yunwane ya ta data bawai baccin ba ne ya kare mata because rabonta da abincin tun lunch d'in jiya , da dare koma koda Ajmal ya ajiye mata abubuwan ta bawa kasa ci ta yi because ba ta yanayin da zata iya cin wani abu, jiki ba kwari ta sabulu daga saman bed din ta sakko. Slowly ta ke jan kafafuwanta jikinta kamar wanda aka zarewa laka haka ta nufi gurin door d'in ta cire key d'in da ta sanya ta murd'a handle d'in gamida budewa ta sako kai waje ta na yar leke leke ko zata hango inuwar Ajmal sai dai ba kowa cikin parlourn shiru kakeji sai karan TV da ke aiki cikin parlourn. Karisowa Nisha ta yi tsakiyar parlourn ledar da Ajmal ya ajiye mata jiya ta zo dubawa amma sai ta ga wayam ba komai gurin hakan yasa ta shiga yin mis mis da idanu ta na ya mutsa face kamar wata mai shirin yin kuka ta nemi guri ta zauna ta na shafa lallausan cikinta wanda ta ke ji tamkar ana gobara ciki , daga can bakin door din ta ji ana nocking wanda ya sa Nisha ta mike a zabure ta na shirin shigewa bedroom sai kuma ta ji wata kakkausan murya daga waje ana duka sallama wanda ya sa Nisha dakatawa tashiga kallon door din da sautin muryan da ake kwararo sallama cikin sassanyan murya Nisha ta shiga amsa sallamar wanda daga nanne a ka turo door akashigo. Mai gadi ne ya shigo gamida rawar jiki ya na washe baki hannayenshi dauke da wata kyakykyawan ledar ya karisa shigowa tsakiyar parlourn daga gefe ya ajiye saman table daga bisani ya kai Kallonsa ga Nisha wacce taimasa zuro ta na binsa da idanuwa. " Sannu hajjajo dama yallabo'i ne ya turo da wannan aikar akawo miki tundazo na keta zaryar sallama naji shiru ba amsa ba yasa na yi tsammanin bacci kike karna ta kuraki?" " Nagode" abun da Nisha ta fad'i kenan ta rakashi da idanu har yafice daga parlourn ya maida mata da kofar ya rufe, cikin hanzari Nisha ta isa gaban table gamida janyo ledar ta baje kasa ta shiga budewa tun kafin ta karisa bude ledar ta ke jin wani daddad'an k'amshi wanda ya sanya yawunta tsinkewa abubuwan ciye ciye dana tande tande gasu nan birjik Irish with plantain chips and crispy fried chicken gefe kayan itacuwane ingatattu ga snacks and drinks iri da kala ba tare da ba ta lokaci ba Nisha ta shiga sanyawa duk wani abunda ke cikin ledar albarka kafin ta yi hamdalah gamida sauke wani ajiyar zuciya jin cikinta ya dauka tam alhamdulillah daga nan ta shiga mikewa ta nemiguri saman sofa ta mike ta kwanta gamida kurawa kyakykyawan TV da ke kunne parlourn ya na aikin wanda Ajmal ya tafi ya bari a kunne ya na aiki. Haka Nisha ta zauna ita kadai parlourn cikin kewa sai TV da ta sanya gaba tana kallo wanda kura masa ido kawai tayi but tunanin da hankalinta sam baya gurin kwallon ya na can wani guri daban haka ta na cikin wannan ya nayin bacci ya kuma awungaba da ita daga inda ta ke kwance... Karan horn d'in mota daga waje ne yasa me gadi zaburuwa ya fito cikin hanzari ya shiga yayi gate wata bakar motar ta kunno kai cikin haraban gidan wannan karon Ajmal shi kadai ba kowa tare da shi ko parking bai tsaya g'yarawa ba ya fito cikin hanzari ya nufi ciki. Koda ya shigo parlourn kwance ya tarar da Nisha ta yi d'aid'ai ta yi nisa cikin bacci gefe kuma kayan ciye ciye da ya kawo mata ne wanda ta gama cika musu aiki ta koma gefe ta yi kwanciyar ta, Ajmal hannayensa ya zura cikin pocket d'insa ya kafin ya shiga ta kowa a hankali ya har ya kariso tsakiyar parlourn ya tsaya. Ajmal Nisha kawai ya zubawa manyan kyawawan fararen idanunsa ya na kallota tunda ga sirarun fararen kafafuwanta har izuwa kyakykyawan baby face d'inta yanda kasan mai k'wak'ulu mak'uran kyanta haka Ajmal ya zuba mata idanu ya na binta da su , time daya kuma Ajmal ya d'an waro idanu ganin wani wawan mik'a da Nisha ta yi gamida juyi da nufin g'yara kwanciya wanda ya sanya Ajmal cikin sauri ya shiga karisawa gaban sofan da ta ke wance ya sanya dugayen hannayensa ya taru ta ta fadu bisa jikinsa. A razane Nisha ta bude lumsassun idanunta cikin ya nayi bacci ta ji ta fadu but kada ta bude idanunta da tar ta sauke face d'in Ajmal wanda ke tallafe da ita idanunsa ke kanta a hankali Nisha ta shiga zamiwa jikinsa ta mike tsaye gamida yin baya ta na kallon Ajmal wanda shima ya mike tsaye gamida cillo mata wani harara kafin ya wace ya nufi bedroom ya bar Nisha tsaye tsakiyar parlourn sai faman sosa kai ta ke, jinki a ma ce Nisha itama ta juya ta nufi dayan bedroom din ta mai da kofar ta rufe . Zama bakin bed Nisha ta kumayi cikin damuwa ita tarasa zamar mai ta ke cikin wannan gidan gaba daya kadaici da kewa ya dameta sam gidan babu dadi cikin kwana daya har tayi miss yan uwanta su Reeda wanda suma suke cikin miss d'inta idanu ta shiga wulga jikin bangon dakin ta kalli agogo karfe 4 har ta wuce sam ba tayi tsammanin tayi bacci mai dugun zango hakaba dan hakan ya sa ta mike ta shiga cire duguwar rigarta tare da nemi towel ta daura daga nan ta nufi bathroom . wanka ta yi gamida alwala sannan ta fito ta nufi saman sofa ta janyo wannan duguwar rigar abaya wanda Ajmal ya kawo mata Nisha gaban mirror ta nufa gamida manna duguwar rigar jikinta ta na karewa rigar kallo ta jikin mirror abayar tayi matuk'ar kyau sosai dagani kuma kaga tsadaddiya gashi mannawa kawai ta yi jikinta ta ga yanda rigar ya haskota sosai, murd'a handle d'in da a kayine gamida turo door kai tsaye yasa Nisha juyawa ta kai kallonta gareshi lokacin da Ajmal ya kunno kai cikin bedroom din gamida mai da door din ya rufe face d'insa ba alamar wasa ciki rigar da ke rike hanunta tana kokarin sawa ba ta san sanda ya zame ya zubuce daga hanunta ba kamar wani wanda ta ga mala'ikan mutuwa haka Nisha ta shiga zare idanu ta na yar kame kame ganin daga ita sai d'an towel wanda ko gwaiwarta bai karis isaba. Kallo kawai Ajmal ke bin ta da shi ya na daga tsaye ya na kallonta yanda ta ke ta muzurai ta na zare idanu kamar ta yiwa sarki karya gamida sitirta jikinta da hannayenta biyu , Nisha direct bathroom ta nufa zata koma sai kuma ta tsinkayi maganar Ajmal cikin kakkausan murya , "stay here " jiki na rawa gamida k'yarman Nisha ta tsa cak daga inda ta ke jitayi kamar ta tuna rami kasa ta shige kanta kasa sai faman mammatse idanu ta ke gaba daya kirjinta ta sai wani irin bugu ya ke ya fahimci yanzu bayan tsoronsa da take ta koyi salon guje masa , cikin natsuwa Ajmal ya shiga ta kowa ya na kallonta daga sama har izuwa kasa sai da ya zo dab da ita sannan ya tsaya . Nisha ja da baya ta danyi ganin yanda Ajmal ya matso ta very close kamar mai shirin rungumarta carab ya riko hand d'in Nisha ya fisgota jikinsa gamida bin sirarun fararen kyawawan hannayen Nisha da kallo wanda take ta faman kankame jiki gamida rungume jikinta da hannayen na ta. Ajmal hanu ya kai bisa nata hannayen kafin ya sauke duk hannayen na ta kasa gamida bin duk ilahirin lallausan jikinta da kallo, nanfa jikin Nisha ya suma bari tamkar mai jin sanyi ko daga idanu ta kalleshi ta kasa yi dayan hand d'insa ya kuma sawa ya azashi kasan haban Nisha gamida dago habarta face d'inta na faskantar ta sa still de Nisha ta kasa daga idanuwa sai pink lips d'inta da keta faman rawa.v "Look at me" Ajmal ya fad'i cikin wata raunanniyar voice Amma mai makon Nisha ta sanya idanunta bisa nashi ta kallishi kamar yanda ya fad'i but sai gani yayi ta lumshe idanu tana shako daddad'an k'amshin turarensa mai dad'in gaske bisa hancinta zuciyarta sai wani bugu take da karfi kamar a mafarki ba tare da ta yi tunani ko tsammanin ba sai tsintar lallausan harshe Ajmal cikin bakin ta wanda ya Kai mata wani kyakykyawan sumbata mai wuryar mancewa yayinda ya kama lallausan lips d'in Nisha yana mata wani sucking cikin wani irin salo . Shi kanshi Ajmal baiyi tsammanin haka daga gareshi ba kawai ya tsinci kansane cikin wannan ya nayin ya kuma kasa dakatar da kasan daga aikin da yake. Nisha waro idanu waje ta yi kamar zasu fado kasa yayinda ta shiga fizgo numfashinta da ke kokarin nemansa ta rasa gaba daya jikinta ne yayi wani irin sanyi kamar kankara ya mutu murus kafafuwanta da sukayi raune cak suka tsaya daga rawar da suke nan Nisha ta sakewa Ajmal jikinta gaba daya because jitayi kamar anzare mata lakan jiki gaba daya . Jin yanda Nisha ta sake jiki wanda ya sa suka kusa kifewa kasa because shima Ajmal ya gama sake jiki ya fada can wata dunyar cikin yanayin na mutuwar jiki slowly Ajmal ya shiga zare lips d'insa daga na Nisha ya zuba mata irinanun idanunsa wanyanda suka canza launi duk ya gama fita hayyacinsa ganin yanda Nisha ta sake jiki ta lumshe idanu kamar wacce ta yi sumar tsaye yasa Ajmal g'yara tsayuwa da kyau ya sanya hannayensa biyu ya sunkuci Nisha ya karisa da ita izuwa bed ya kwantar da ita . Ajmal bin Nisha ya yi da idanu wacce ke kwance lamo shiru ko motsawa ba ta yi sai zallar sauke ajiyar zuciya da ta ke ta faman jerowa shima Ajmal d'in ajiyar zuciya ya sauke kafin ya dire idanusa saman santala santal fararan cinyoyinta da su keta faman shining yana kallo a hankali har izuwa saman kanta nan ma ya bi dugon suman gashin kanta da ke baje saman bed baki wuluk da shi daga nan kuma ya garzaya kyakykyawan face d'inta ya zuba mata idanu ya na kallon dan k'aramin tsukekken pink lips d'inta, Ajmal hanu ya kuma kaiwa saman lallausan lips d'in Nisha gamida jan leben kasan a hankali ya na jijjiga shi yana fadi'n "He! Open your eyes 👀" Amma sai jinta shiru yayi bata motsa ba bata kuma bude idanunta ba sai eyelashes d'inta da ya ke ganin yana ta faman motsawa yana rawa ta na son bude idanu but ta kasa because jima tayi gaba daya idanunta sun mata nauyin da bazata iya bude su ta daura su bisa face d'in Ajmal ba da ke zaune gefe wanda ya sanya ta cikin hannayensa ya rank'wafo Kai da jikinsa ya mata runfa. Numfashi su yana gaureye da na juna ko wannensu ya najin yanda zuciyar d'an uwansa ke buguwa especially Nisha yanda zuciyarta ke ta faman bugu kamar zai faso k'irjinta, Ajmal ganin shi bata da alamar bude idanu ta kalleshi kamar yanda ya fad'i ya sa ya zare hanusa daga saman lips d'in ta ya kai saman k'irjinta daidai madaurin towel d'inta ya suma kokarin kwancewa . Azabure Nisha ta bude idanu tar gamida kai hanun ta saman na Ajmal ta danne hannyensa da nata tana kokarin hanshi abunda ya ke kokarin yi Sam ba tayi tsammanin abun zai kaisu ga haka ba aikuwa nan Nisha ta shiga kokarin zamewa ta na so ta mike ta tashi but sai dai babu halin hakan. " Plea., Please! kayi hakuri dan., dan Allah" . Nisha ta fad'i tana girgiza masa kai duk ta wani langwabe ta rikice sai zare idanu ta ke saura kiris ta fashe da kuka time d'in har zufa ya suma keto mata. "Meyasa zanyi hakuri ?wani abin na ce zan miki?" .Ajmal ya tambaya ya na hade rai, girgiza kai Nisha ta yi gamida sunkuyar da kai ganin wani harara da ya cillo mata nan taga Ajmal ya zame hanusa daga jikinta gamida yin baya wanda ya sa Nisha ta samu kuzarin zamowa daga bed din cikin hanzari ta na g'yara madaurin towel d'inta da ya suma suncewa. Ajmal raka Nisha yayi da ido wacce ke ta ke faman rawar jiki da hanzari kafafuwanta sai gauraya suke da na juna kankance mai sai sautin faduwa tim kakeji Nisha Taci tuntub'e kafarta daya yashigewa daya garin sauri ta fad'i kan gwaiwowinta Nisha ba k'aramin zafi ta jiba but ganin Ajmal ya mike tsaye ya sa cikin hanzari ta karisa shiga bathroom d'in da rarrafe ta maida kofar ta datse i Ajmal wani guntun ajiyar zuciya ya sauke gamida rintsa idanu ya kuma budewa sam mamakin yarinyar da tsoro over irin nata baya kare masa jibi wani irin sauri da hanzari da take har da su tuntub'e inda zataje ta jiwa kanta wani raunin. A sukwane Ajmal ya mike gamida ficewa daga bedroom din ya nufi dayan bedroom din zama Ajmal yayi saman sofa ya mike kafafuwa jikinsa duk a mace duk wani motsi idan yayi tunani abunda ya faru tsakaninsa ga yarinyar nan ne ke dawo masa ya rasa ya akayi ya sauka layi ya kama wata hanyar da ban wanda ko kusa ko alama baiyi tunanin hakan zata iya kasancewa ba but ya je yana kokarin kunnowa kansa wata wutar lallai ya zama wajibi ya tattari yarinyar nan su koma gida if not zai iya kirawo kansa ruwanda bazai iya dakatar da shiba because ke b'an cewarsu tare da yarinyar zuciyarsa na d'arsa masa abubuwa dan gane ga yarinyar za iya samun mishkila bugu da kari kuma yanda Ammi ta sa shi gaba da rangwada masa kira gaba daya hankali ta ya kasa kwanciya tunda ya tafi da yarinyar. Ajmal ya jima zaune gurin yana sakawa da kuncewa kafin ya kai hanu ya dauki phone d'insa ya shiga duba time 5 saura kafin ya zura wayar cikin pocket d'insa gamida daukan key d'in motarsa ya kuma dawowa parlour. Nisha sai da ta kuma wani alwalar kafin ta fito still har yanzu jikin ta bai daina rawa ba a hankali Nisha ta dingiso kafarta saboda buguwar da tayi har cikin jikinta ta ke jin zafin buguwar direct door ta nufa ta tsaya gamida murda key kafin ta kuma juyowa ta nufi duguwar rigarta wanda ke ya she kasa ta dauka cikin hanzari ta zura jikinta gamida nannad'e mayafin bisa kanta ta fito fes d'as da ita kamar wata balarabiyar Saudia daga nan ta hau saman sallaya ta shiga ta da sallah sai da tamika duka sallolinda ke kanta kafin ta g'yara zama bisa gurin ta ci gaba da lazimi da yan yatsun hanunta. Ta dad'e tana zaune gurin ta na lazumi ta na jin yanda zuciyarta ke wani irin sanyi kamar ana yayyafa mata ruwan sanyi har wani lumshe idanu ta yi ta na bada himma , tana cikin wannan ya nayin a zaune ta jiyo nocking daga can bakin door wanda ya haddasa mata faduwar gaba da tsoro . Nisha ji tayi kamar karta tashi ta bude haka ta zauna ta na kallon door din ta kasa ta shi ta bude , Ajmal dake tsaye bakin door yana nocking amma shiru ba ta bude ba kuma ta na jin nocking din da ya ke gaba daya ransa ya suma baci ya gama hasala har Ajmal ya juya da nufin barin gurin sai kuma ya ji alamun budewarta wanda yasashi dawowa ya tsaya. Nisha murda handle d'in door din ta yi ta bude gamida fitowa ta tsaya daga bakin kofar kanta sunkuye. "Bakyaji ana nocking ne da kika kasa ta sowa ki bude?". Ajmal ya tambaya cikin fad'a ya na hararo Nisha wacce ta hade cikin kyakykyawan duguwar rigar abaya da ya kawo mata. "I'm sorry 😔 ? " . Nisha ta ce cikin sanyin murya. "Let's go" . abunda Ajmal ya ce kenan ya sa kai ya fice daga parlourn , Nisha bayanshi ta bi da kallo gamida mamaki ina kuma zasu Nisha komawa ta yi ta zura talkami bisa kafarta kafin ta kuma fitowa ta bi bayan Ajmal. Ajmal tuni ya shige mota ya mata key gamida canza ak'alar motar ya na shirin fita mai gadi tuni ya bude masa gate Nisha kawai ya ke jira ta shigo motar su dauki hanya Amma sai hangota yayi ta jikin mirror safaman jan kafa take kamar wacce kafafuwanta suka samu matsalan shanyewa. A hankali Nisha ta kariso jikin motar gamida bude kofar motar ta shige a sukwane Ajmal sai faman hararota ya ke ta gefen ido yawani hade gira gamida bata fuska kamar wani hadari nan ya figi motar suka d'aga suka bar compound din gidan. ******************************* "Aunty Nabilah anya ba twins zaki haifa mana ba kuwa only three months kalli yanda ya fito see it" . Reeda ta fad'i tana haga gira cikin tsokana yayinda take nunawa fadeelah dan k'aramin cikin Nabilah da ke kunshe cikin duguwar rigar ta har ya fara turowa gaba daga fadeelah har Reeda dariya suka kwashe dashi gamida kallon Nabilah wacce ta keta faman musu murmushi ta na girgiza kai ta na kuma sun kuyar da kai but bata iya ce dasu komai ba ta naji suna ta tsokanarta suna dariya. "Oh ni Allah ya ranan sam ba kuda kunya Nabilah fa ba matsayin da kuka santa da bane yanzu matsayin matar yayanku take ba abokiyar wasan kuba da ku ka wani sanya ta gaba kuna tsokana ". Ammi ta fad'i ta na hararo su fadeelah da Reeda wanda suka sanya Nabilah tsakiya suna mata surutai "Ah to kya fa d'a musu dai mijin na mune yaimusu nisa shiyasa daga dawowar ku kuntar muna d'an firanmu cikin hankali da nitsuwa kunzo kun ka tsaimu da shashanci idan ta haifo muku yan biyun zuwa zakuyi ku tayata rainone ? Hajia ta amshi zancen ta na kallonsu gamida tambayar su "Eh dama inta haifa muzamuyi rainon koya". Reeda ta kuma fad'i tana kallon fadeelah wacce ta yi saurin g'yada mata kai suna mai cigaba da darin ta su. Jim kadan Nabilah ta mike gamida yi musu sallama ta wuce part d'insu kasan cewar magarib ya gabato kai ta tafi tabarsu Hajia zaune suna yar hiransu sama sama daidai time d'in Nisha t ta sako kai cikin parlourn sumu sumu kamar ba kuwar kaza wanda tun kafin ta kaiga karisowa parlourn take jin muryoyinsu daga waje tun kan ta kaiga karisowa tsakiyar parlourn fadeelah da Reeda su tasu daga zaunen da suke sukayiyo kanta gamida rungume ta dukansu suna fadi'n sunyi kewarta kai kace shkekara sukayi basu sanyata idansu ba. Hannun Nisha suka ja cikin hanzari da daukin ganinta da nufin karisawa su zauna wanda yasa Nisha rintsa idanu saboda radadin da kafarta keyi ba ta iya wani tafiya cikin kuzari ita ta na tunanin ma kamar kafarta ta dargadewa yayi yanda take jin zogi cikin kafarta sai mis mis take da idanu tana cizon lips d'in ta cikin dauriya ta bi bayansu fuu suka karisa cikin parlourn suka zauna . Koda suka zauna bakin Nisha yayi nauyi ta kasa magana ko kyakykyawan d'aga kai bata iya yi sai su fadeelah ne da suka tusa ta gaba da tambayoyi ina sukaje akabarsu da kewanta ita dai Nisha ba ta samu daman basu amsan tambayoyin da suke ta faman yi mata ba. Daga Ammi har Hajia tun shigowar Nisha bakunansu ya kasa rufuwa jikinsu duk yayi sanyi kamar anjefi kaza da gishiri ganin yanayin da suka kalli Nisha time din da su Reeda suka jawota ciki sai wani mammatse idanu take ta na jan kafafu gamida cizon lips kamar wanda ta samu rauni kafafuwanta. Ammi da Hajia kallon juna sukayi daga bisani kowa ya kauda kai gamida sake kai kallonsu ga Nisha wacce tayi zuru da ita nan suka ga ta dago musu gaisuwa ta na sunsun da kai cikin fara da sakin fiska suka amsa daga bisani suka ci gaba da yar hiransu ta su da suke kai but hankali su gaba daya yanaga Nisha Kiran sallah na magarib ne yasa Hajia mikewa ta fice daga bisani Ammi itama Ammi ta mike gamida kallon su Reeda da suka sake baki kamar fanfon kasuwa suna zuba suna suna ta surutan nan nasu da basa gajiya ta umurce su da suje suyi sallah time yayi haka gaba daya yansu suka mike ba da wani jinkiriba suka nufi bedroom dinsu Ammi sai kallon Nisha ta ke wacce ta ke taman nuke nuken kafa, jiinjina kai kawai Ammi ta yi daga bisani Ammi ta haura upstairs ta nufi bedroom din ta itama. Bayan su fadeelah sun idar da sallah Nisha ne karshen ta na zaune bisa sallaya tana lazumi gamida addu'oi kafin ta mike tsaye ta ninke sallayen ta shiga warware mayafin kanta "Sis wai mai yasamin kafar ta kine kam tunda kika dawo kike ta jan kafar kamar dawani problem" Reeda da ke gefe ta cillo mata tambaya tana mai tsare ta da idanu fadeelah ma tsuri tai tana jiran ta ji amsa don dama ta su mata wannan tambayar Reeda ta rigata because abin ya damesu ganin dingishin da Nisha ke yi , dan kallato murmushi Nisha tayi gamida ba ta amsa da cewa. "Faduwa nayi" Nisha ta ce cikin sanyin murya gamida samun guri kusa da fadeelah daga bakin bed itama ta zauna, kallon juna fadeelah da Reeda su kayi kafin faddei ta kalli Nisha tana fadi'n "Omg 😱 garin ya ya ince dai ba targade bane buguwa ce " g'yada kai Nisha kawai ta yi alamar "Eh " tana mai mike kafafuwa , nan suka shiga yimata sannu kafin nan Ammi ta sako kai cikin bedroom din bakin ta dauke da sallama. Sai suka amsa mata kowannesu ya zuba mata ido suna kallon karisowarta, Ammi sai da ta kallesu daya bayan daya kafin ta tsaida idanunta ga su Reeda ta na fad'i "Kutashi ku bani guri but ina fatan kunyi sallah ba surutu ku ka tsaya yiba" Gyada mata kai su fadeelah sukayi alamar "Eh" daga bisani suka mike suka fice daga bedroom din a sukwane, Ammi zama tayi inda fadeelah ta tashi kusa da Nisha kafin ta kallo Nisha wacce tayi zuru da idanu kamar tayiwa sarki karya suna fiskantar juna. "Kyakykyawar y'ata ta ce dai ko lapia na ga kundawo but kafar taki kamar ba kalau wani abinne ya sa mi kafar?". Ammi tamabya Nisha cikin na tsuwa da kulawa, cike da sauke ajiyar zuciya Nisha ta ce "Tuntub'e na yi na fad'i " . ta bata amsa voice d'inta har na shakewa" . "Tuntub'e kuma yar nan garin ya ya ?". Shiru Nisha ta yi tama rasa wani amsa zata ba ta kuma garin gudun ne ta ci tuntub'e ta fad'i za ta ce mata koyaya? Daga Nisha har Ammi shiru sukayi ba mai magana Ammi ta gefen ido kawai ta ke kallon Nisha wacce ta sunnar da kai kasa tana wasa da d'an ya tsun hanunta. Sam ta kasa yadda da zantukan Nisha duk da ta san dawuya Nisha taimata karya tunda tasan ba d'a bi'anta bane but tunanin ta akwani abin da Nisha ke buyawa maybe ko kunyarta ta keji dan ta san ba yanda za ayi Modibbo ya dauki yarinyar ya sutafi can wani gurin su wuni su hantse ace ba abinda ya gifta zakaninsu tunda shi namiji ne ita kuma macce maccen ma wacce take halalinsa. Ita da farko ma tayi tsammanin d'an wani shakatawan zasu fita yi dan yawo shopping da sauransu but batayi tsammanin abun zai kaisu ga kwana ba. Ita dai bata isa ta hanashi fita da matarsa duk inda ya keso ba sai dai sam bazataso wani alaka ya suma shiga tsakaninsu tun yanzu ba tunda bawai ta tare bane sansamu ya jira har time din da aka dibar musu ta isa ga dakinta na sunna cikin mutunci kwata kwata bai wuce only three weeks bane ayi abun kowa ya huta. But tun yanzu ya tusu yarinya gaba tansan yarinyar da zurfin ciki ballai tai mata bayanin da zai gamshe ta ba duk da itama basai ta wahalar da kanta wajan tambaya ba, a sukwane Ammi ta mike tsaye ta na fad'i "Allah ya kiyaye na gaba ki dinga kula sosai " . Gyada kai Nisha ta yi alamar gamsuwa kafin Ammi ta kuma fadi'n. "Ta so muje muyi dinner the food is ready" . "Bayan nan aikwai wani manzafin da zan baki sai ki shafa a kafafun naki insha Allah zuwa safiya zakiji kamar ta ki da d'an dama". Ammi ta kuma fad'i "To " . Nisha ta ce tana g'yada kai , daga nan. Ammi ta tuso Nisha gaba suka nufi parlour dan gabatar dinner kamar yanda ya ke a tsari... Washe gari Nisha kamar yanda ta saba ta na yin sallah zata nufo kitchen ta kamawa Barka wasu aikace aikacen duk kasan cewar yau ta d'an makara zuwa ba kamar ko yaushe ba Nisha kafin ta kaiga kitchen d'in Ammi ta hango bisa dining table suna kaiwa da kawo ita da Barka suna tsaka da aiki Ammi na hango Nisha ta shiga yin fara gamida da sake kyakykyawan murmushi tana kallon karisowar Nisha. Nisha na karisowa dining d'in cikin nitsuwa tashiga dagawa Ammi gaisuwa wacce ke ta faman shirya abincin bisa dining kasan cewar in Daddy nan da kanta take shiga kitchen ta sarrafa masa abunda zaiyi kumallo dashi kuma dake shi yana rigata fita. Cike da fara'a Ammi ta amsa gaisuwan gamida tambayar Nisha ya saukin kafarta ta amsa da "Alhamdulillah" Daga Nisha ta juya ta na kokarin barin gurin wanda cikin hanzari Ammi ta daga tar da ita gamida fad'i "Please yau dai kam kije ki kwanta ki huta yar nan, nida kaina zan kai Modibbo breakfast am na gama kafar ta ki wahalar da kanki" . Wani irin sanyi Nisha ta ji cikin zuciyarta kamar ana zuba mata kankara dama sam yau ba ta jin haduwa da shi gaba daya ya sanya mata fargaban haduwa da shi ba musu Nisha ta g'yada kai gamida sakai ta koma ciki zuciyar ta fari tas __ Zaune ya ke saman stool gaban drees mirror yana sanye cikin tattausan duguwar bathrobe ( rigar wanka) white color yayinda hand d'insa ke rike da hair dryer yana ta faman busar da duguwar suman kanshi cike da nitsuwa. Heelah ce ta turo door din ta shigo gamida tura door din ta maida ta rufe face d'inta cike da fara'a yayinda take kokarin karisowa tsakiyar d'akin direct gurin Ajmal ta nufa sai faman zubu masa murmushi take tana kallonsa ta jikin mirror wanda ko ta kanta bai bi ba lallai ya san tanayi . Heelah hannayenta biyu ta sanya saman shouldernsa gamida kutso face d'inta gafen wuyarsa tana mai lumshe idanu. "Good morning dear" . Heelah ta fad'i gamida manna masa kiss jikin wuyarsa , shiru yayi mata dan ko daman amsa mata bai samuyi ba sai faman g'yara suman kansa yake, Heelah za ga yo wa gabansa ta yi gamida hayewa saman cinyarsa tashiga garban hair dryer hanunsa ta na fad'i "Let me help". But sai ji tayi ya rike gam yaki sake mata sai ma wani banzan kallo da ya ke wurginta da shi wanda yasa ta zame hannuta daga shishshigin da take kokarin yi masa gamida sakin murmushi cikin rashin zuciya Heelah ta shige jikinsa saman kirjinta ta kwantar da kanta ta na fad'i "Honey! am na mance ba sanar da Kai time din da muka fita daga Aheel can na baroshi gun Mommy I think can zai kare hutun school d'insa dafatan ba matsala?" Shi tunda ya dawo jiya baya cikin yanayin mai dadi zai iya cewa ji kwata bai ya ganewa jikinsa ba shiyasa ma ko ta kansu bai bi ba amma sam bai yi tsammanin Aheel baya cikin gidan ba, Sanin kanta ne Ajmal ba yason abunda zaisa yayi nesa da shi indan ba ya kasance dole ba ta ban garanshi ballai ma yasan Aheel ta kura zai because bawani sabawa yayi da can d'in sosai ba tunda ba taba kaishi da nufin ya dau tsawo lokaciba ba. Dan hade gira Ajmal yayi ba tare da ya bata amsa ba ya shiga zameta jikinsa ya mikewa tsaye gamida tufke suman kanshi guri guda daga nan ya zame jikin ya nufi wardrobe domin duba kayan da zai sanyawa jikinsa, d'an tab'e baki Heelah ta yi gamida g'yara zama gurin ta jifansa da wani kallo wanda bazakace gashi na mainene ba. Nocking din door da ake daga waje ne ya tattaro hankulansu daga Heelah har Ajmal su ka tsurawa door din ido, bugu daya zuwa biyu Heelah ta saki wani guntun tsaki gamida mikewa tsaye ta nufi gurin door din ba tare da ta bude ta ga kowa ye bane ta shiga magana cikin tsawa. "Madam bugun k'ofar ya isa haka idan wani uzurin muke fa kinwani ishi mutane da nocking sassafen Allah kin di bowa mutane jiki" . Heelah ta fad'i cikin fad'a tana huci a tunaninta Nisha ne kamar yanda ta yi tsammani but sai kuma ta ji an cigaba da yin nocking wanda ya sanya Ajmal dakatawa daga abunda ya ke ya suma kokarin karisowa gurin door din cikin hanzari Heelah ta sa hanu ta murda handle d'in door din bakin ta na fadi'n "Amma daike wannan anyi may.." sit Heelah ta kama bakinta ta tsuke ba tare da ta karisa abunda take son cewa ba ganin Ammi tsaye bakin door din time d'in da ta karisa budewa Zuru sukayi dagav ita har Ajmal d'in da ya biyo bayanta yana kokarin bude door din Heelah ta rigashi . "I'm sorry na yi zaton waccer shashashar yarinyar ce" Heelah ta fad'i ta na kasa da kai kamar wata ta Allah. "Ba sha shashar bace uwarta ce bani guri na shige" . Ammi ta fad'i cikin bacin rai tana hararo Heelah wacce take sanye cikin wata yar fingilar wando ko alamar ta ji kunyar ganinta haka ba tayiba. Heelah kai sunkuye ta zame jiki ta bar bedroom din sai faman tab'e baki ta ke kasa kasa ta na kallon Ammi ta gefen ido , ganinta dauke da tray d'in abinci hanunta, harta karisa ficewa Ammi kallon Heelah take tana jinjina Kai gamida mamaki. "Amma dai wannan anyi sakara, duk yanda akayi wannan yarinyar kanta ba daya ba" . Ammi ta fad'i cikin jimami tana kallon Ajmal wanda ya sauke wata ajiyar zuciya ganin shigowar Ammi sab'anin tunanisa. Karisowa tsakiyar d'akin Ammi ta yi gamida ajiye tray d'in bisa table din tsakiyar d'akin kafin ta dubi Ajmal wanda ya zauna bakin bed yana kallonta shima gamida dago mata gaisuwa. "Good morning ". "Morning ya wayewar garin?". Ammi ta tambaya cikin yanayin fara'a "Fine". Ajmal ya amsa a takaice ya na kallon Ammi "Breakfast na kawo maka but nazo na tadda kana tsaka da shiryawa incedaiba sauri kakeba?" . Ammi ta tambaya, girgiza kai kawai Ajmal yayi gamida cillowa Ammi tambaya. "But where is she". "Wai Nisha naga tun daworku jiya na fahimci bata jin dad'i shine nace na hutar da ita yau kam ni da kaina na hada maka kyakykyawan delicious wanda na san zakaso ". "Is not your work please kidaina wahalar da kanki" Ajmal ya fad'i cikin face d'in damuwa. "Don't worry just iya yaune but nasan kana matuk'ar son abinda na girka da hanuna nasan kuma kayi kewar hakan while indan kanaso ma har abiki saina iya baka na tuna maka yatintar ka because na sanka da son jiki idan ba ka canza yanzu ba? " . Ammi ta fad'i cikin tsokana tana yar dariya Shi kanshi Ajmal baisan sanda murmushi ta kwace masa ba harsai da kyakykyawan hushiryarsa ta bayana gamida lotsawan dimple d'insa ya na kallon Ammi wacce ta mike tsaye cikin annashuwa "Bari naje na baka guri kar na dameka da surutu, zanturo Barka ta zo ta kimtsa muku muhallin na ku idan da bukatan hakan" . Ammi ta fad'i harta juya zata fice sai kuma ta juyo ta dan kallo shi kad'an tana fadi'n. "Am nace ba tunda an tsaida ranar bikin adan jinkirta fita yawo da kwana wani guri sai zuwa bayan biki tunda ba ayi tariya ba tukun kaga kai babban mutum ne ba kowa yasan da batun auran ba" . Zuru Ajmal ya bi bayan Ammi da kallo wacce ta fice tana murmushi ta janyo masa door din tarufe . Shi dai ya kasa gane maiye tunaninta gameda shiba tunda suka fita da yarinyar hankalinta ya kasa kwanciya har kawo yanzu da take kokarin k'wab'ansa ga abunda ya ke k'ark'ashinsa, d'an jinjina Kai Ajmal yayi gamida mikewa ya shiga sunce madaurin rigar kafin ya cire ya shiga sanya kyawawan tufafinsa. ******************************* Nisha Karfe 4 dawasu yan mintuna yamma lis Nisha ta farka daga baccin da take ta faman yi tun bayan azahar, ita kadai bisa cikin bedroom din ta nasanye cikin riga t shirt mai dogon hanu white color gamida high waist skirt black colour, direct bathroom ta nufa ta gabato alwala ta fito ta shinfida darduma gamida sanya dugun hijab tashiga gabatar da sallahn la'asar. bayan idar da sallah ne ta shiga yin addu'oi daga bisani ta mike ta cire hijab din ta koma ta kwantar ruf da ciki ta rungumo pillow gamida janyo wayarta tana dubawa. Door din aka turo akashigo cikin bedroom din ita dai taji motsin shigowa but ba tasamu daman g'yarawa ta ga ko waye bane ta yi tunanin su Reeda ne yasa ta ci gaba danne dannen wayarta , dukan da taji ankaiwa gadon bayan ta ne yasa ta mike azabure ta waigo gamida zaro ido waje. Salma ta gani tsaye kamar amafarki ta ci ado sosai ta yi kyau da ita lullube cikin wata kyakykyawan sari yayi mata kyau kwarai. "Surprised" .Salma ta fad'i gamida lankwashe jiki tana juya idanuwa". "Salma!" Nisha ta fad'i cikin mamakin ganinta cikin wannan time din yau kwana uku dayin bikinta ta ganta anan to koma dai gizo tai mata ga idanunta gaba daya Nisha ta sake baki tana binta da kallo daga samma har kasa. "Please rufe bakin mana kin bude shi yana shan iska" . Fadeelah ta fad'i wanda suka shigo tare da salma , Nisha gimtse baki tayi tana bin Salma da kallo wacce ta zauna gefenta sai faman zuba kamshi take. "Kinyi mamakin ganine ? Na gaza hakurin ganin ki shiyasa nazo sam hankalina yaki kwanciya". cikin hanzari Nisha ta fad'a cikin Salma ta rungume ta gamida sake kukan farin cikin ganinta. lumshe idanu Salma ta yi gamida saukar da ajiyar zuciya ganin aminiyarta wanda ta ke jinta tamkar ciki daya suka fito , d'an zame jiki Salma tayi gamida kallon Nisha wacce ta keta faman goge hawayen farin cikin. " Godiya nazo na miki na musamman". Salma ta fad'i tana dan hararo Nisha wacce ta sunnar da kai a kunyace ba tare da ta ce komai ba ta na dan wasa da ya tsun hannayenta. Reeda ne ta shigo cikin bedroom din yayinda hannayenta ke dauke da tray ta ajiyewa Salma gefe daga nan kuma ta suma fadi'n "Bari mu koma gurin Hajia mu ba ku guri ku cigaba da tattaunawa ". Reeda ta fad'i ta na kallonsu wanda daga ita har fadeelah suka mike suka fice daga bedroom din daya na bin daya . Ganin fitarsu yasa Salma ta shiga g'yara zama gamida duban Nisha ta na fadi'n. "Hankalina ya kwasa kwanciya tun bayan da Reeda ta sanar da ni abunda ke faru nashiga damuwa lamarin na jishi kamar walkiya daga sama bugu da kari bansa halinda zaki sanya kanki ciki ba jin kaddaran Aure da ya fad'a miki ba tare da kin shiryawa hakan ba". "Shiyasa na daga hankali MB sai ya kawoni na ga halin da wannan kyakykyawan amaryan ke ciki, Allah sarki Kamal ashe ke ba rabonsa bace ". Salma ta fad'i cikin jimami tana kama haba. Jin shirun Nisha ba ta tamka taba yasa salma zunguro Nisha tana fadi'n "Wai ke kam kalaun ki kuwa inata magana kinyi shiru kina jina ko dai auranne ya nitsir da ke haka". tura baki Nisha ta yi ta na hararo Salma tana fadi'n "To mai kikeso na ce " "Labari zaki bani gameda sabowar rayuwar da kika fara da hadden angon naki kai gaskiya na miki murna ba kowa wacce mace bace ta yi sa'a da dace irin naki ba dace da babban mutum wanda duniya tasan da zamansa". "Ina miki murna gaskiya ai wannan ba abunda za ki tsaya kina tunani da daga hankali bane kamata yayi kizoba ruwa akasa kisha ki gode Allah because ya riga ya daga matsayin ki fatana Allah yasa ya zama silar farin cikin ki arayuwa". Wani kukane ya kwacewa Nisha wanda yasa ta fad'a cinyar Salma gamida rage sautin kukan na ta tana fadi'n., "Salma ba na tsammanin haka mutumin nan ya sakoni gaba daga shi har matarsa banajin akwai wanda zan iya rayuwa dashi cikin, wallahi sallama jinake kamar na gudu na bar gidanan". "Subhanallah wai mai kike fad'i ne haka guduwa kuma because of what?". Salma ta fad'i tana dago Nisha wacce ta nake jikinta,. "Tunda nazo gidan nan ya kyamace ni sam bai dauke ni yanda kowa na gidan ya dauke ni ba " . Nan Nisha ta shiga zaiyanu mata yanda zaman ta ke tafiya cikin gidan da kuma yanda akayi ta rab'i Ajmal da kuma halinda ta tsinci kanta gamida halayensu shi da matarsa Heelah Nisha ba ta boye mata komai ba har fitansu da Ajmal izuwa gidan taje ta tadda sabanin tunanita har kawo yanzu da take bata labarin tana karishewa da zubar hawaye. "Ikon Allah ashe ma har da wani love ya ke kokarin showing miki amma dai ke anyi yar k'auye ni harkin bani kunya ma ". Salma ta fad'i tana tab'e baki, Nisha kuwa sake turo baki gamida hade gira tana fadi'n "Wanna ba soyayya bace" "To menene ni duk cikin labarin da kika ban ni banga wani aibu cikin halayen shiba a fahimtar da nayi masa tun zuwana gidan nan na farko mutum ne mai tsare gida da baya son raini kuma irin mishkilin mutanan nan ne wanda ba su fiye son magana sosai ba but ke kuma a yanda na fahimta kina nuna tsoron ki fiye da kima wanda zaki iya sanya masa shakko bisa kanki har bukaci son jin labarin rayuwarki wanda su kansu yan gidan ba wanda ya yi tunani son ya jin labarin ki ko ya damu ya ji daga wani tushen kika fito ba ,but kinsa su kuma hukuma basa iya gani suyi shiru sai sun tantance mai kyau da bara gurbi cikin ahalinsu". "Kamar yanda ki kace kunje gida tare amma kin tarar da sab'anin tunaniki tun farko abun da na so sanar da ke kenan but baki bani hankalinki ba saboda yanayin da kike ciki". "Nima da kike gani yanzu ba wannan anguwar tunda aikin gwamnati ya biyo ta kan gidanmu da wad'ansu gida jen dake anguwar muka ta shi muka koma can wani unguwar but bana son ki wani daga hankali ki nasan insha allah zaiyi binkice bazai bar lamarin haka ba fatana Allah yasa Abba ya nacikin koshin lapia". Salma ta fad'i gamida sauke wani gutuwar ajiyar ta na riko hannayen Nisha biyu . Ameen Nisha ta fad'i a sanyaye gamida jingina kanta ga shouldern Salma ta na lumshe idanu "Amma fa cikin jarabawan da Allah ya daura miki ya hadaki da mahaukaciya a matsayin kishirya ki , zama da irin wadan nan sai mutum ya shirya shiri na gaske sai kin busar da idanunki but ke kuma yanzu na ga gabaki daya ma kin susuce kinyi sanyi sosai kamar ba Nisha da nasani ba ". "Kin barta ta na buga can da nan kamar wani ta muluta Harfa alwashi ta ke ci wai zata kasheki ". Salma ta fad'i ta na jan wani gutun k'wafa gamida kai hanu ta dauki sassanyan bottle water tashiga tsiyayawa cikin wani kyakykyawan glass cup ta kai baki. Sai da ta sha ruwan sannan ta kuma kai hanu ta b'alli ayaba ta kuma kaiwa baki kafin ta cigaba da fadi'n "Yanzu fa ba matsayin da ta sanki da bane duk da bawai ta sani bane but ya kamata ki busar da idanunki ki kwaci yan cikin tukan tafiya ta yi nisa karki zuba mata ido tana miki yadda ta ga dama kema matar shi ce kamar yadda ta ke matarsa, kamata yayi ki kashe ta a tsaye ko ba ta mutu ba tayi dugun jinya tunda ita iyayen kishine" "Kamarya in kashe ta fa kika ce sam ni bazan iya kisa ba ". Nisha ta fad'i tana mak'e shoulder gamida ya mutsa fiska "Kaji banza ninace kiyi kisane? ta shi ki zauna da kyau ke sam bakisan mai duniya ke ciki ba". Salma ta fad'i ta na mai ajiye b'awon ayabar hanunta saman tray gamida mai do da kallonta ga Nisha wacce ta g'yara zama ta fiskan to ta... Follow the Oum Amreesh channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaDtGp2G3R3lkDkO9T3H Ajeemal Story and writing By Oum amreesh https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATU WRITERS ASSOCIATION💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtatu ne kawai kan iya amfani da wannan k'asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauki.✏️_ Book 2 Page 86&87 ****************************** _____ Gaskiya na ji dad'in ganinki sosai Salma zuwan ki na kara ganin sauyi cikin face din kyakykyawan yata yau Nisha fara'a da nishadi abun ba acewa komai" Ammi ta fad'i cikin farin cikin tana kallon Nisha da Salma wacce keta faman zuba murmushi kamar gonar auduga yayinda suke tsaka da yin kataccen dinner. "Aiko dai ni da na ganta ma abun mamaki ya bani kwana uku da biki hankalinta bai kwanta ba sai da ta zu daga k'awarta wannan amintar ta ku ta gaske ne akwai amince sosai ku riketa da kyau Hajia ta fad'i cikin fara'a itama. "Insha Allah Hajia". Salma ta fad'i ta na kallo Nisha ta gefen ido wacce ke ta faman juya spoon cikin plate ta na juya wani tunani cikin ranta, kasan cewar wajan cin abincin ga kujeran Nisha ga ta Salma yasa Salma zunguran Nisha da ido ta mata alamar ta bar tunani ta ci abinci wanda yasa Nisha g'yada mata kai ba tare da kowa ya ankara da suba, nan su kaci gaba da cin suna yar firansu wanda annane Salma ta sake godiya gasu Hajia da abubuwan arzikin da su fadeelah da suka kai mata ranar bikinta nan suka nuna mata bakomai ta cancanci hakanne. Phone din Salma ce tayi kara nan ta ja wayar tashiga dubawa ganin angonta ne ke kira yasa Salma jan tissue paper tana share bakinta da hannayenta gamida mikewa ta na sanar da su mijinta ya zo daukarta , daga nan Ammi ta mike ta haura upstairs ta nufi bedroom jim kad'an ta dawo hannunta dauke da kyakykyawan ledar ta zo ta mikawa Salma tana fadi'n. "Gashi ba yawa mungode sosai da ziyara". Salma ta amsa gamida surfa godiya daga haka Reeda dauko mata handbag d'inta cikin bedroom ta dawo ta mika mata daga nan ta musu sallama su Nisha suka rufa mata baya dan yi mata rakiya. MB jingine da jikin motarsa wanda yayi parking d'inta compound din gidan Kamal na gefe tsaye suna yar firansu sama sama yayin da suke jiran fitowar Salma, hango su da sukayi suna ta howanne yasa kamal sake idanunsa kan Nisha wacce hannayensu cikin na juna da Salma suna ta fe suna fira. "Allah sarki wato akcewaba mutum abu ba rabunsa bane sai dai kallo da hakuri" . Mb ya fad'i yana kallon Kamal wanda ya shagala da kallon Nisha but jin abunda abokin na sa ke fad'i yasa Kamal kalloshi gamida hararoshi ya na kauda Kai. "Gaskiya kayi na mijin kokarin da saurin karaya koda ya ke fad'an da ya fi karfin mutum ai sai yamai da shi wasa". Shidai Kamal ko k'ala bai tufa masa ba yana jinsa yanata tsokanar shi duk da abun yana masa ba dadi but inya biyeshi zasu iya diban yan kallo. Nisha tundaga nisa da tangi mb da Kamal tsaye sai da ya sanya k'irjinta buguwa gaba daya nauyin haduwa da Kamal ta ke duk da kwana biyu ya bacewa ganinta kamar baya duniyar. "Afuwan mun barku kuna ta jira sallamar ce ta ki karewa jinayima kamar na kwana kawai abina". Salma ta fad'i tana ta fa hannaye gamida kallon angon nata da yake mata wani kallon wanda yasa ta tuntsirewa da dariya ta na mai kauda Kai. "Ah kidaiyi hakuri karkisa wannan angon naki mai rawar kai yaita mana zariya cikin dare ya hanamu bacci". Kamal ya fad'i cikin tsokana. "Ai batama isaba ai sai asanya ta cikin duniyar alajabi". Mb ya fad'i wanda ya sanya su kwashewa da dariya duk kansu daga nan mb suka shiga gaisawa da su Reeda gamida yiwa Nisha fatan alkhari gamida batun auranta daga nan suka shige mota gamida yi musu sallama motarsu ta d'aga tabar harabar gidan. Daga nan su Fadeelah suka suma kokarin juyawa su koma ciki Kamal kiran sunan Nisha wanda ya sanya duk kansu su ka juyo harsu Reeda. "Da ita kadai nake but kunwani juyo sai kace sunanayen ku na kira". Kamal ya fad'i yana hararo su Fadeelah. "Kuyi tafiyar ku da ita kadai na keson yin magana". Kamal ya kuma fad'i wanda yasa su Reeda suka bargurin suna dariya gamida waiwayansu suna yar gulma. Kamal kallon Nisha yayi wacce kanta ke kasa tana wasa da yan ya tsunta gamida tunanin abunda zaice. "Come here please follow me". Kamal ya fad'i gamida yin gaba alamar ta biyoshi baya, ba tare da wani musu ba Nisha ta bi bayansa suka karisa cikin kyakykyawan garden da kullum ta ke tunanin shigarsa because ba ta taba kai kanta gurin ba kuma tana da sha'awar shiga ta ji irin ni'imar da gurin ke da shi tare da shuke shukensa masu kyau da daukar hankali dake ba da wani sassanyan ni'ima mai dad'in gaske. Garden din ya k'awatu matuka fiye da tunaninta ga wanin haske tar wal mai kyau da inganci kai kace ranane ba dare ba, karisawa su kayi suka zauna saman wani k'ayataccen guri da aka killace dubin zama d'an nishadi babba table ne tsakiyar gurin gamida zagaye shi da akayi da kujero yan ma daidaita gurin sai wani ba da ni'ima mai dadi ya ke. Bayan da suka zauna kamal ya kallo Nisha wacce itama ke kallon shi wanda suka shiga kurawa juna idanu daga bisani kowannesu ya kauda Kai yanajin kewar wani gurbi cikin zuciyarsa. Sisy kinsan meye? Kamal ya tambaya gamida d'agowa yana kallon Nisha girgiza masa kai tayi kafin ya jinjina Kai ya cigaba da fadi'n "Wato fa abu in a kace ba rabonka bane tofa duk yanda ka kaiga k'wallafa rai ga abu ballai kasamu ba" "Bantaba kawo rai na bazan sameki matsayin mata ba sai gashi kin kasance babba Aunty a gareni". But bana bakin ciki da hakan because ni da shi kusan abu gudane sai hali da ya babanta kasan cewar wasu halayensa sunfi nawa tsafta because ni sabon tubane shiyayi kokarin daurani bisa hanya ina alfahari da shi . Shiyasa bana bakin ciki kasan cewarki abokiyar rayuwarsa but... "banasu wadannan zantukan please ". Nisha ta fad'i cikin damuwa na rashin son jin abun da ya riga ya wuce. "Alright my Aunty wadanne zantuka kike son ji to ?". Kamal ya tambaya gamida gyara zama yana tallafo kuncisa da tafin hannusa ya na kallonta, dagowa itama Nisha ta yi tana kallon na shi kafin ta ce "Labarin kwallon kafa". ta fad'i gamida sakin murmushi ta na sunnar da kai , wani dariya Kamal ya tuntsire da shi ya na fadi'n "Ke kuma maiye abunso ji a labarin k'wallo ke da mace ba na miji ba ". Ya tambaya yana dubanta. "To waya fad'a maka maza ne kad'ai wasan kafa ge burgersu ? Akwai wasu matan ciki kuma har da ni ". Nisha ta fad'i "Uhm to hakane but mafi akasari maza dai sunfi yawa akan mata". "To Amma dai labarin k'wallo ba aba da shi sai dai a kallah because idan labari zan baki bazai miki har mashi ba kamar kallo , dan haka ki zuba ido akwai wani wasa da zamu gabatar cikin satin nan dan haka sai ki saka TV gaba wajan kallo b". "Hmm to shikenan". Nisha ta fad'i , sun dau lokaci suna yar firansu cikin wasa gamida nishadi suna dariya Nisha ta sake sai zance ta ke daga nan Kamal ya mike ya na fadi'n "Bari na je na dakko Nabilah daga gida na ga dare ya suma rufawa". G'yada masa kai tayi gamida mikewa itama suka fito daga garden din tare daga nan yi masa sai ya dawo ya mata sallama ya wuce haraban gidan ya shiga motar shi mai gadi ya bude masa gate ya fice Nisha tana tsaye wajan harya kurewa ganinta kafin ta juya ta nufi part d'insu Ba jimawa motar Ajmal ta kuma kunno Kai wanda ya sanya mai gadi sake yayi gate shima ya kutso motar shi cikin haraban gidan daidai parking space yayi parking yau Ajmal yayi dawowan wuri. ya nayin parking ya fito daga motar ya nufi cikin side d'insa, Nisha ko da tashigo parlourn bakowa duk sun watse kowa ya nufi turakarsa, hakan yasa direct ta nufi bedroom din su time din da ta karisa shiga ta samu duk sunyi shirin bacci sun kwanta. Reeda hartayi bacci Fadeelah ne kawai ta rage idanunta biyu tana daga kwance tana chat tana murmushi da alamar tana nishadantuwa da chat din, bathroom Nisha ta nufa wanka tayi wanka gamida tsaftace jikin ta kafin ta fito ta nufi gaban drees mirror tashiga shafa kamsasun mayukan da ke wajan daga bisani ta koma wardrobe ta shiga neman seeping drees don ta sanyawa jikinta . wata yar half vest ne milk colour sai d'an wando mai laushi da taushi iya ka gwaiwa launin blue daga nan ta haye saman bed ta nemiguri ta kwanta gamida janyo wayarta ta shiga lazawa itama, guraren 10:30 Nisha ta suma g'yang'yad'awa phone din harta su b'uce hanunta Fadeelah itama tuni ta kashe datar wayar tajuya ta yi kwanciyar ta sai bacci. Phone din Nisha ne yashiga rori alamar kira wanda ya sa firgit ta bude ido because baccin na ta bai riga da yayi nisa ba phone din da ya tsulale hannunta ta shiga lalub'owa ta shiga duba jikin screen din wayar time din har kiran ya katse,. Daga saman bed din ta mike ta zaune ta na murza idanu ganin Kiran ogan na ta cikin wannan time din ko mai ya ke bukata kuma ? dan ta san wannan kiran da ya mata ya na bukatar ganinta ne . jim kad'an ta danyi na wani lokaci kafin ta mike ta bude wardrobe ta dauko wata zungureriyar hijab ta sanya bisa jikinta kafin ta fito ta nufi hayar fita......... Zaune yake cikin kata faran parlourn sa saman duguwar sofa ya mike kafafuwa ya daura daya kan daya yana karkad'asu a hankali cikin na tsuwa ya na sanye cikin wani riga t shirt mai guntun hannu gamida dogon wando dark blue yana ta aikin danna phone dinsa. Turo door da akayi aka shigo baisa ya dauke kansa daga abinda ya keba, cikin sanyin murya Nisha ta kutso kai cikin parlourn gamida sallama ta na mai karisowa cikin tsakiyar parlourn. Cikin zuciyarsa Ajmal ya amsawa Nisha sallamar ta but bai iya dago da kansa ba, can gefe Nisha ta duka saman carpet kanta kasa ta shiga fadi'n. " Sannu da hutawa andawo lapia?". "Fine ". kwai Ajmal ya ce kafin ya shiga nuna mata ledar da ke ajiye saman table ta dauka ta shiga cikin ta sanyo cikin plate ta kawo masa, ba musu Nisha ta nufi ledar gamida dauka ta nufi kitchen da shi. Tunda ta mike Ajmal ke binta da kallo daga ita har hijab din da ta sanya da yake ta faman sharan k'asa, ita kanta sai faman tattareshi take kar ya kayar da ita, kauda kai Ajmal yayi ya cigaba da abunda ya sanya gaba aikin danna phone dinsa. Nisha ko da ta shiga kitchen ta shiga bude ledar kayan snacks ne nau'ika da ban da ban da wanda baya gajiya da cinsu da kuma ka kasa sabawa cikinsa da abu mai nauyi irin na gargajiya, gefe kuma kayan marmari suma nau'ika da ban da ban . Plate ta dauko ta sanya wasu kayan snacks din ciki gefe ta kuma dauko wani kyakykyawan bowl tashiga hada masa k'ayataccen yoghur fruit da wadannan kayan itaciyar daga bisani ta dauki sauran raguwar kayan ledar ta sanya su cikin fridge ta dauki kyakykyawan tray din data shirya abubuwan ciki ta nufo parlour. Koda ta dawo parlour babu Ajmal ba alamar shi cikin parlourn hakan ya sa ta karisa cikin parlourn ta ajiye tray din bisa table ta samu guri daga gefe ta zauna tana jiran sakkowan shi maybe wani uzurin ya shigayi. Ta dau tsawon lokaci tana zaune gurin ta ga alamun bayi da niyar sakko gashi dare na dad'e yi yasa ta mike ta dauki tray din ta shiga haurawa upstairs. A hankali ta ke taka steps din zuciyarta na wani irin bugu jita yima kamar ta koma ta ajiye masa ta yi tafiyar ta but wani zuciya kuma ta ce karta yi hakan dakyar ta iya jar kafar ta gamida karisawa door din. Nocking ta shigayi a hankali jikin door din kafin ta jiya ya amsa mata da cewa. "Come in" cikin cool voice d'insa mai dad'in saurara , tura door Nisha ta yi ta shiga can ta hangoshi ya mike saman bed face d'insa na kallon sama yana rungume da pillow bisa k'irjinsa ya rintsa idanu shigowar Nisha ne yasa ya bude idanun nasa gamida janye pillow daga jikinsa ya shiga mikewa. Yana daga zaune bakin bed ya sakalo kafafuwansa kasa yana bin Nisha da kallo wanda ta karisa da tray din bisa table din bedroom ta ajiye. Damamakin duk jiransa da take ta faman yi akasa dama kwanciyar sa ya zo yayi cikin bedroom abinsa dan jiyowa ta yi wanda yasa suka hada ido da Ajmal wanda ya mike ya nufo wajan ya nemi sofa ya zauna gamida ya juyo table din gabansa. Nisha juyawa ta yi da nufin ficewa har Allah Allah ta ke ta tsinci kanta awaje but sai ji ta yi ya ce. "Come back and get a seat". Ajmal ya fad'i time din da ya suma taba abubuwan da ta kawo masa Lumshe idanu Nisha ta yi gamida yin baya ta kuma can saman carpet ta kuma dukawa zuciyarta kamar zai faso k'irjinta ya fito dan bugu. sai da Ajmal ya Kamal cin snack dinsa gamida daddad'an yoghur fruit d'insa kafin ya mike ya nufi bathroom ya wanko bakinsa kafin ya dawo ya tadda Nisha tsugune da hijab kamar mai karban gaisuwa kafin ya tsaya kusa da ita ya yana fadi'n. "Get up". gamida hade gira, jiki ba kwari Nisha ta mike tsaye kanta kasa cikin mamaki da tsoro sai ji tayi Ajmal ya sa hanu ya yaye wannan hijab din da ke jikinta ya cillata shi can gefe wanda yasa Nisha ta shiga zare idanu ta kankame jikinta gamida juya baya a kunyace ganin yar fingilan vest din jikinta ji tayi kamar ta sake fitsari gurin . Hararo ta Ajmal yayi gamida juya baya face d'insa ba alamar wasa ya wuce ta ya kuma can saman bed d'insa ya kwanta gamida mikewa yana kallon Nisha wacce ke rungume da jiki ta juya baya. "Come here". Ajmal ya fad'i adan tsawace Nisha kamar ta fashe da kuka time din hawaye fal idanunta ba musu kuma ta shiga ta kowa a hankali still idanun Ajmal na bisa kanta ya na karewa ilahirin lallausan suran jikinta kallo ya na lumshe idanu a zahi ko mace yar uwarta ta kalleta wannan time din ba zata so dauke ido daga kanta saboda Masha Allah tabarakallah. Sai da ta kariso izuwa bakin bed din ya ke kwance kafin ta ja ta tsaya kanta na kasa idon Ajmal ne ya sauka kan kyakykyawan bulin cibiyar Nisha kafin ya rintsa idanu gamida janyo pillow ya kuma rugumewa jikinsa yana fadi'n " Have a seat". dagowa Nisha ta yi ta kalleshi ba tare da tayi abunda ya ce ba harsai da ya sake bata umarni karo na biyu da ta zauna bakin bed kamar yanda ya mata nuni da ido, jiki a sanyaye Nisha ta nemiguri ta zauna Ajmal kamar jira yake ta zauna sai ji ta yi ya jefo mata dugayen fararen kafafuwansa bisa cinyarta wanda yasa Nisha cikin tsoro ta kuma zaro idanu tana kallonshi "Kiyi min massage". Ajmal ya fad'i yana lumshe idanu shiru Nisha ta danyi ta kasa cire hannayenta daga jikinta ballai ta yi abun da yace tayi. "Baki ji mai na ce bane". Ajmal ya fad'a cikin bacin rai gamida bude idanu yana kallonta. Jiki a sanyaye ta shiga zame hannuwanta ta time din da kyakykyawan rabin dukiyar funin ta ya baiyana farare tas kasan cewar vest din ya dan matseta kad'an hatta tudun nipples dinta ana iya gani. Ajmal lumshe idanu yayi time daya da yaji numfashinsa ya suma fisga yana kwatoshi da kyar, yana jin kuma yanda Nisha ta kai hannayenta kafafun sa ta shiga matsawa a hankali Ajeemal Story and writing By Oum amreesh https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Book 2 Page 88 ________Duk kafafuwan nasa biyu haka Nisha ta hadesu duka ta shaga mammatsasu da lausasan hannayenta da suke ta faman yi rawa a hankali tundaga tafin kafarsa har izuwa saman gwaiwowinsa. Ajmal kuwa sai faman lumshe idanu ya ke ya na kuma narkewa jikin pillow kamar k'aramin yaro yana sauke ajiyar zuciya, Nisha ta dau tsawon lokaci tana masa tausan Wanda yasa Nisha ta d'an kallo shi ta gefen ido jin shiru sai faman tausa shi take ba alamar zai ce mata ta dakata gashi dare sai da d'a ja yake. Shikuma Ajmal idanunsa a lumshe suke kamar mai bacci Nisha na zaune ta na masa tausa hannayenta har sun suma gajiya idanunta kum tuni suka suma mata nauyi saboda baccin da ke cikinsu................................., Bude idanu Ajmal yayi wanda tuni bacci ya dauke shi time din da ya ji lausasan tafukan hannayen Nisha yayinda da take masa tausa baisan sanda bacci ya cinye idanunsa ba sai yanzu farkawanshi da ya bude idanunsa ya sauke su kan Nisha da ke saman k'afafuwansa ta yi matashi da su. Lumshe idanu Ajmal yayi ya kuma budewa karo na farko da ya ji tausayin yarinyar ya d'arsu cikin zuciyarsa haka Ajmal ya bi Nisha da kallo wacce bacci ya sa ce ta tana tsaka da yi masa hidimar tausa. Ajmal kallonsa ya mayar kan dan k'aramin kyakykyawan agogon da ke ajiye saman bedside table guraren karfe 3 da wasu yan mintuna dagan nan ya maida kallonsa ga Nisha ya nason zame k'afafuwan nasa daga jikin Nisha wacce ta narke jikin kafafuwan nasa kamar ta samu pillown baccinta but baya so kuma ya katse mata baccin na ta haka Ajmal ya hakura ya shiga g'yara kwanciya nanfa ya ji Nisha ta suma mutsu mutsu ta na neman farkawa wanda yasa Ajmal komawa lamo jikin pillow ya narke gamida rintsa idanu. Nisha ji tayi gaba daya kwanciyar yau bai mata yanda ta keso ba ta takura sosai ta juya can ta juya nan daga bisani ma bude idanun ta yi gaba daya tar tashiga wul wulga su cikin bedroom din ta na zare idanu sam ta mance da inda take ba tasan bacci ya dauke ta ba sai yanzu da ta bude idanunta ta ganta cikin bedroom din Ajmal ta dafa kafafuwansa tayi matashi. Cikin hanzari ta daga kai tana mammatse idanu gamida maida kallonta ga kyakykyawan face d'in Ajmal wanda ya lumshe idanunsa kai kace bacci ya ke. A hankali Nisha ta suma kokarin zame k'afafuwan Ajmal daga cinyarta da gangan Ajmal ya kuma sake mata nauyin kafafunsa gamida bude idanusa ya kafesu a kanta suka hada ido time din da itama ta kai kallonta gareshi jin yanda ya sake mata nauyin kafafunsa. Nisha ji tayi k'irjinta ya wani bugawa , wanda yasa cikin tsoro gamida yar kame kame ta shiga fadi'n " Zan zan. tafi". Nisha ta fad'i cikin fiskar tausayi tana langwabe wa , sam Nisha ba tayi tunani cewar dare yayi sosai ba Ita a tunaninta yar g'yang'yad'awa kawai tayi ta farka . "Where? see the time". Ajmal ya fad'i cikin sassanyar murya ya mata nuni da dan k'aramin agogon da ke gefe, Nisha idanu kawai ta wulga kan agogon dan zaru idanu Nisha ta yi gamida yin rau rau da idanu kamar mai shirin yin kuka ganin yanda dare ya tsala sosai ba damar fita sam ba tayi tunanin time ya kure haka ba amma Allah ya gani bazata iya zama cikin bedroom din Ajmal ba . Cike da tsoro Nisha ta shiga wulga idanu ta na naiman hijab din ta da Ajmal ya cire mata yayi wurgi da shi, can gefe saman carpet ta hangi duguwar hijab din ta a yashe hakan ya sa cikin sauri ta suma kokarin zame k'afafuwan nasa da nufin dauko hijab din ta ta sanya ta fice but sai ji tayi Caraf Ajmal ya riko hanunta ya na tambayarta "Where are going ?". Jikin Nisha tuni ya suma bari lips d'inta sai faman motsi yake tama rasa mai zatace Ajmal fisgo Nisha yayi da karfi ta fado faffad'an k'irjinsa gamida da kafe idanunsa cikin na ta ya na kallonta. Cikin karfin hali Nisha ke kokarin zamewa daga jikinsa cikin tsoro da fargaba , hanu Ajmal ya sanya saman kan Nisha ya zare madaurin suman kanta nan da nan kyakykyawan dugun bakin gashinta ya shaga malalowa bayanta ya kwanta luf yana jin yanda zuciyar Nisha ke bugu da karfi kamar zai faso k'irjinta,. Daga nan Ajmal ya mirginata gamida maida ta saman bed ya kwantar shikuma yayi mata rufa da faffad'an k'irjinsa gamida matso da face dinsa daidai face d'inta numfashinsu na bugun na juna . Ita dai tsoro duk ya gama cikata sai rintsa idanu kawai ta yi gamida zubawa sarautar Allah ido, ta san yau kam ta shigo hanu gudu da tsoron da take tsawon lokaci duk da ba ta taba tsammanin Ajmal zai sake jiki da ita haka ba ko ya kalleta kamar yanda sauran maza ke kallon matansu sai kuma gashi ya share mata kokonto ba tayi zato ko tsammanin ba duba da yanda ya ke mata kallo abaya but sai gashi yanzu yana sa tana tuna da auransa bisa kanta. Ajmal hannyensa ya sanya cikin na Nisha ya rike gam gamida kutsa kansa gefen face d'in Nisha izuwa neck ya shiga sakar mata kyakykyawan sumbuta yana sauke ajiyar zuciya Nisha kuwa idanu ta kuma lumshewa jin yanda Ajmal ke manna lallausan lips d'insa jikin wuyarta yana yi mata wani hot kiss wanda take jin shi tundaga tsakiyar kanta har izuwa ta fin kafarta. A hankali Ajmal ya kuma mai da lips d'insa dab da nata idanunsa a lumshe haka zalika itama gaba daya ta gazayin ka tabus kyakykyawan motsima ta kasayi, lallausan harshensa ta tsin kaya yana mata yawo cikin baki ya kama dan tsokeken lips d'inta ya suma yi mata wani irin salo wanda yasa Nisha ta ji kamar ta sake fitsari gurin yanda ya ke mata sucking kamar zai cire mata lips tuni Nisha ta suma kananun kuka ta na kokarin kwace hannayenta wanda ya rike su gam cikin nashi. Ajmal sai da ya sucking lips d'in Nisha yanda ya keso kafin ya dan zame lips d'insa daga shi har ita sai fidda wani wahalalen numshe suke. Dagowa Ajmal yayi gamida bude idanusa ya sauke su kan Nisha wacce ta lumshe idanun hawaye sai gangarowa saman lallausan kumatunta yake nan kuma ya karisa da kallonsa izuwa kyakykyawan fararen dukiyar fulaninta wayanda ke ta faman shining gamida tudun nipples dinta da suke tsokano idanunsa wanda suke cikin riga. A hankali Ajmal ya zame dayan hand d'insa daga na ta gamida daura shi bisa k'irjinta ya shiga yawo da hand din nasa saman Brest d'inta yana shafo tudun nipples d'inta numfashinsa yana wani irin fisga . Nisha wani yar ta ji cikin jikinta tsikar jikinta na wani irin ta shi cikin ta fiyar tsutsa ta ji ajmal ya suma kokarin d'age d'an gajeren vest dinta ya na kokarin lalubar Brest d'inta wanda yasa Nisha ta zaro ido waje cikin mamakin mai ya samu Ajmal ya ke kokarin ya wuce guna da irin cikin tsoro da fargaba Nisha ta rike hand d'insa cikin tsoro tashiga girgiza masa kai ta na kokarin hanashi ta na kokarin fashe masa da kuka. Rinannun idanunsa wanda suka canza launi Ajmal ya dago yana kallonta yanda duk ta wani marai raice ta fita haiyyacinta cikin yana yi na tsoro da firgici shi dama baiyi niyar yi mata komai ba just romance ne shima kuma tsintar kansa yayi cikin wannan salon ya kuma kasa hana kansa ga a bunda yake yana kokarin tsokanowa kansa wata fitinar. Dan hade face Ajmal yayi ya lumshe idanu gamida zame hannayensa daga abunda yake kokarin yi gamida koma gefe ya kwanta ya na mai da nan nauyar ajiyar zuciya . Nisha na jin Ajmal ya bar jikinta aikuwa cikin sauri ta mirgina gamida zamowa daga saman bed din ta yun kura ta nufi inda hijab d'in ta ke yashe ta dauka ta sanya jikinta da yake ta faman bari saboda tsoro da firgici Ajmal na jin Nisha ta bude door ta fice cikin sauri time din idanunsa ma kasa budewa yayi ballai ya samu bakin yin magana tabbas da ba dan tunawa da hanzarin Ammi bisa kanshi da kuma karfin hali da yayi ba da a daren yau labari zai sha ban ban saboda yanayin da ya tsinci kansa ciki wanda ya dade bai tsinci kansa ciki kiba bugu da kari kyakykyawan surun Nisha ya sashi jin feelings din da baisan yana da shiba akan mace gaba daya yarinyar ta suma tafiya da tunaninsa...... Nisha ko tsoron fituwa waje ba tayi ba haka ta rungumo hijab gudu gudu sauri sauri Nisha ko waiwaye ba tayi har ta kariso part d'insu cikin hanzari ta nufi bedroom d'insu. Ammi ne ta fito daga kitchen hannunta dauke da cup ta na kokarin haurawa upstairs sai wulgawan Nisha ta gani tashige bed d'insu cikin sauri but ita kuma Nisha k lura da itama ba tayi ba. Mamakine ya kama Ammi sosai guraren 4 na asuba daga ina kuma Nisha ta fito mamaki duk ya gama isarta jinjina Kai kawai ta yi gamida haurawa upstairs ta na jimami . Ammi na shigaa bedroom ta nemiguri ta zauna bisa sofa ta yi kuri da ido tana tuna ni , Daddy dake kishingid'e bakin bed ganin shigowar Ammi tare da cup ta kuma dire cup din gefe ta shiga tunani yasa Daddy fadi'n " Ince dai ko lapia na ga kindawo kin zauna kin shiga tunani? What wrong with you". "Uhm ni wannan lamarin Modibbo yana damuna , wai kokasan shigowar da zanyi yanzu Nisha na gani ta fito daga waje cikin wannan time din kuma ba mamaki daga side din Ajmal ta fito".Ammi ta fad'i cikin jimami gamida juyowa tana fiskantan Daddy wanda ya tabe baki ya na jiinjina kai gamida g'yara zama ya na fadi'n. "Ni na rasa maiye damuwarki a kan hakan kinsawa miji da matarsa ido kin hanasu susha iska karfa ki mance mata da mijine kuma jini ke gudana a jikkunasu ba ruwa ba maybe time din da aka dibawa tariyarsu yayi musu nisa sun kasa juran hakan sai ki musu uzuri madam." "Maybe ma kafin tariyar tasu asamu karuwa kinga sai ayi gagarimin biki da murnan samun karuwa".Daddy ya fad'i yana yar dariya tsokana gamida mikewa ya nufi bathroom shi yarasa maiye damuwar Ammi ga yaran da ta musu ido cikin lamarin su. Kauda kai gefe Ammi ta yi cikin damuwa shi sam Daddy ya kasa fahimtar ta sai wasu maganganu ya ke ita tasan Nisha yarinya ce mai kunya da kuma ladabi duk abunda akace da ita ba musu zatayi shi ta san bazata biye wa Modibbo ba sai dai ya mata jan ido nasu na maza a karshe maganar Daddy ta tabbata asamu karuwa kafin bikin tariyarsu........... Wani duguwar mika Heelah ta yi gamida mikewa da duguwar baccin da ta kwanta tun bayan dawowar ta daga office ta shiga ta yi kwanciyar ta ba ta sake tuna inda ta ke ba sai yanzu da ta farka gamida bude idanunta ta na jan wata duguwar hamma. Jikinta na sanye cikin wani kyakykyawan sleeping dress wata yar duguwar riga sharara kana iya hango yan kananun Brest d'inta da basu wuce ta fin hanu ba daga ita sai d'an pink pant dinta da ake hangowa ta cikin yar shararan rigar, ta bazo dugun suman kanta na kwance luf bisa bayanta ta sabulu daga saman bed din ta nufi bathroom ta wanko face d'inta gamida wanke bakinta kafin ta fito ta nufi dressing mirror tasa hanu ta janyo wa yar kwalba ta bude ta shiga shafawa lungu da sako na jikinta ta fito daga bedroom din ta direct ta nufi bedroom din Ajmal because daren jiya ba ta iya jiran dawowarsa ba tayi bacci. Heelah turo door din ta yi ta shiga kwance ta sameshi saman bed face d'insa na kallon celling ya dafe hannayensa saman goshinsa idanunsa a lumshe , karisowa Heelah ta yi gamida hayewa saman jikinta ta kwanta luf ta na jin yanda Ajmal zuciyarsa ke bugu karfi karfi gamida sauke nan nauyan ajiyar zuciya wanda yasa Heelah dagowa ta kalleshi. Heelah hannu ta sanya ta zame hannayen Ajmal daga saman goshinsa wanda yasa Ajmal bude manyan idanuwansa da suka rine suka koma jaa yana binta da kallo. "Ya dai? what are you looking at me?". Heelah ta tambaya tana kallon Ajmal ganin kafe ta da ido da yayi kamar yau ya fara ganinta, shiru Ajmal yayi bai iya bude baki ya maiyar mata da martani ba sai ji kawai yayi ta na ta faman nuk'urkusashi tana shigewa jikinsa gamida kutsa face d'inta gefen wuyarsa ta na sarka masa wani zazzafan kiss cikin salo da kwarewa. Ajmal ya jin duk abunda ta ke ya kuma kasa hanata karshema sai tsintar kansa da yayi da mayar mata da martani na abubuwan da ta ke masa wanda dama neman agaji yake awannan time din sai kuma aka samu tazo a daidai wannan gaban hakan yasa Heelah sake zagewa wajan romance din Ajmal cikin rikita tunani da hankali sannu ahankali cikin kwarewa da iyawa cikin salo mai jan hankali har Heelah taja ra ayin Ajmal ya biye mata suka fad'a can wata duniyar ............. Ajmal kefe ya koma gamida lumshe idanu ya na sauke ajiyar zuciya haka itama Heelah zuciyarta fari tas farin ciki ba a magana yau hakanta ya cimma ruwa abun nema yasamu Heelah kallo Ajmal ta yi tana murmushin farin ciki gamida matsawa jikinsa tana wani shishshige masa wanda yasa Ajmal zame jiki gamida mikewa yana jin yanda hansa yaimasa nauyi ya nufi bathroom. Heelah mirginawa saman bed din ta yi tana kokarin g'yara kwanciya farin cikin da annashuwa dan hade face Heelah ta yi gamida sanya hanu ta janyo wani red ribbon din da ta ke hangowa saman bed din ta shiga jiyuwa hanunta wanda yasa ta mikewa zaune daga saman bed din. Ita dai tasan wannan ribbon din ba nata bane ko mai ribbon din yake saman bed din Ajmal oho to koma mai ya kawo shi nan din? Heelah ta shiga tambayar kanta tana kallon ribbon din. Tana cikin wannan ya nayine Ajmal ya fito daga bathroom daure da towel bisa waist d'insa hanusa dauke da wani k'aramin towel din yana tsantsame ruwan jikinsa Heelah dai kallonsa ta ke har ya nemi duguwar jallabiyarsa ya sanya. Heelah zamowa ta yi daga saman bed din gamida janyo yar rigarta ta sanya ta nufi Ajmal wanda ke gaban dreesing mirror yana g'yara suman kanshi. "Honey wannan kuma fa mai yake saman bed din ka na wacece?". Heelah ta tambaya tana tsare shi da ido Ajmal kallo daya yayiwa ribbon din yasan na Nisha ne time din da ya cire mata bisa kanta. "I don't know" . ya fad'i a takaice gamida zamewa daga gurin da ya ke ya nufi hanyar fita domin ta fiya masallaci ya bar Heelah tsaye baki bude ta bishi da rakiyar ido cikin ta kaici Heelah ta kuma bin ribbon da kallo abun da ta ke zargi bazai wuce ribbon din waccer sha shashar yarinyar bane Nisha because tasan ita kadai ke mata kutse cikin rayuwarta yau abin ya zu har saman bed cike da jan duguwar tsaki Heelah tayi wurgi da ribbon din gamida ficewa daga dakin gamida jan duguwar k'wafa,. Guraren 7:30 Barka ne cikin kitchen tana tsaka da aikace aikacen kamar yanda ta saba tana yan wake waken ta Nisha ta shigo ta isketa cikin kitchen din wanda jin motsin shigowar ta yasa Barka jiyowa ta dago ta kalleta cike da fara'a gamida murmushi. A hankali Nisha ta karisa shigowa cikin kitchen din tana sanye cikin kananun kaya riga t shirt mai dugun hannu white colour sai dugun wandon falazo mai fatsi fatsin black and white sai mayafin da ke dauri saman kanta tayi matukar kyau da ita kamar ka saceta ka gudu. Tunda ta shigo Barka ta bude bakinta yana shan isa gurin kallon dressing gamida tsantsan kyau irin na Nisha. "Kai Masha Allah tabarakallah irin wannan kyau kamar mai kokarin zuwa gurin gasar kyau ta duniya Kai koma ace nan zaki to ba mamaki ke zaki lashe kambun". Barka ta fad'i cikin gwad'a Nisha tana washe baki. Cikin fara'a Nisha ta shiga d'agawa Barka gaisuwa tana murmushi Barka ta amsa gaisuwan na ta cikin yar tsokana tana zolayanta daga haka Nisha ta sanya mata hanu cikin aikace aikace nata suka cigaba da yi tare kamar yanda suka saba suna yar firansu. "Yar nan nikam na ce na tambayeki ki mana?". Barka ta fad'i tana d'an duban Nisha yayinda suke aikin. "Ina jikin ki Baba Barka". "Wai nace ke yar wata kasa ce? amma dai mahaifinki ba yan Nigeria bane ko?". Barka ta jire mata tambaya Cikin yar murmushin ya ke Nisha ta amsa mata da cewa "Eh mahaifana yan asalin kasar Sudan ne neman kudi ya kawo mahaifina Nigeria suka haifeni cikin garin Adamawa". "To amma ya akayi kuma kuka tsinci kanku cikin birnin kano tunda kince garin Adamawa kuke da Zama?". Barka ta kuma tambaya cikin mamaki. "Bun kasan kasuwancin Abbana ne ya ya dawo damu garin kano". Nisha ta fad'i a takaice "To shikenan mahaifin naki fa shima Allah ya masa rasuwane?". Barka ta kuma watso mata tambaya Nisha dai wannan karon shiru ta yi ta kasa bata amsan tambayarta gamida fadawa tunani time din har idanunta sun suma cikowa da k'walla. "Yi hakuri yar nan na da meki da tambayoyi ko?". Barka ta fad'i Dan girgiza kai Nisha tayi tana fadi'n "Bakomai bari na je nayiwa papan Aheel breakfast kar time ya k'ure". Nisha ta fad'i gamida zame hannayenta daga aikin da take. "Ayya to ba komai saikin dawo". Daga haka Nisha ta fice daga kitchen din cikin sauri Nisha Barka ta bi bayanta da rakiyar ido harta fice kafin ta jinjina Kai ta cigaba da aikin da yake gabanta... Heelah ne ke ta faman zarya tsakanin kitchen da dining area tana ta faman shirya breakfast bisa dining table ta kai fari takai gauro tana cikin wannan yanayin Nisha ta sako kai cikin parlourn sai faman wul wulga idanu take hango Heelah da tayi can dining table tana ta faman shirya breakfast sai da taji gabanta ya fad'i but bata fasa takowa ta kariso tsakiyar parlourn ba. Heelah tsayawa ta yi daga gurin tana hango Nisha wacce ke faman karisowa da nufin shiga kitchen, harde hanu tayi bisa saman k'irjinta tana jiran Nisha ta gama karisowa. Nisha kanta tsaye ta suma kokarin shiga kitchen dan ko ta kan Heelah ba tayi ba direct ta nufi hanyar kitchen. "Wait madam come back what are going for ". Dan takatawa Nisha ta yi ta tsaya ba tare da ta dago ta kalli inda Heelah ta ke tsaye ba ta kowa Heelah ta yi har inda Nisha ta ke tsaye sai da ta mata kallon tsaf kafin ta tabe baki gamida ya motsa fiska tana fadi'n "Ina kike kokarin shiga baki ga ina tsaka da hidimar mijina bane ince ko ba ki lura bane". Heelah ta fad'i tana nunawa Nisha dining table wanda ta jera breakfast kallo daya Nisha tayiwa gurin ta kauda kai Ajeemal " I'm taking to you kunyi shiru kina kasa da kai sumu sumu kamar ta Allah, har wa yaude shirun Nisha tai mata ba ta kulata ba wanda yasa Heelah sake hasala ta dan ja da baya tana kallon Nisha cike da ta kaici tana fadi'n "Na fahimci raini ya fara giftawa tsakaninmu to daga yau na sallameki daga ban garan mijina ko area side din nan karna Kara ganin kafafuwanki because na fahimci mad'en da kikewa mijina ya fara kaiki ga shimfidarsa". Gaba daya kin sauya min tunanin miji Allah kadai yasan wani siddabaron kike kokarin yi masa Amma insha allah sai dai aniyarki ta biki daga ke har uwar ta ki ta daura ki kan layi ta tafi tabarki". Heelah ta fad'i tana ya mutsa fiska Cikin ta kaici Nisha ta dago ta kalleta Heelah gamida ba ta amsa da cewa "Ba ke nakewa hidima ko aiki ba wanda na ke zaune karka shinsa shi nake wa aiki, ba kuma matsayin yar aiki ko alfarma ba sai dan ya kasance hakki ne a gareni ko shi mai gidan na ki bai hanani saman aljannata wajan kula da shi tunda a hakkine a kaina na sarrafa na bashi ya ci ko ya sha matukar zai bukaci hakan daga gareni any way ko bai nema ba zanyi kodan ganin farin cikin sa but ke ba kida ikon dakatar da ni daga niman aljannata daga karkashin kafarsa" , Nisha ta fad'i cikin bacin rai tana fiskantan Heelah. "Aljannarki ? a k'ark'ashin kafar mijin? shin kina haukane komai? haka kiga uwarki ta ke neman aljannata a karkashin kafar mijin wata ba nataba?". Heelah ta fad'i a fusace Cikin ta kaici da rashin jin dad'in aunawa mahaifiyar ta zagi wacce take kwance cikin salama yasa Nisha jan wani guntun tsaki gamida kokarin barin gurin dan ba zata iya jure maganganun Heelah ba cikin hanzari Heelah ta sha gabanta ta tsaya ta na fad'in "Where are going ? ai tsayawa zakiyi ki bani amsar tambayar da na miki idan ba haka ba yanzu zansa ki raina kanki". "I don't have your time mijin ki zaki tambaya ba ni ba" . Nisha ta fad'i tana kokarin zamewa gefe ta shige ta yi ta fiyar ta amma cikin ta kaici Heelah ta janyo wuyar rigar Nisha ta baya gamida fisgota har tana neman faduwa "Ni kike kallon tsabar idona kike min maganar banza son rainki?" . Nisha sai da ta dai ta tsayuwarta kafin ta kallo Heelah wacce take ta faman huci na tambayarta. " Tunda ke ba kiyi tunani ki kama matunci ki kija girmanki ba ni kuma bazan cigaba da ta ya ki kamawa ba". Cikin taikaci gamida kunci Heelah ta nufi dining ta zaro wata yar karamar yan ka lemo ta nufi Nisha ta na tuna mata wukar tana fadi'n.. "Yau in ban kasheki kowa ya huta ba ba suna Raheelah ba". ganin yanda Heelah ta nufo ta da wukar gadan gadan yasa yan hanjin Nisha kadawa tashiga yin baya ta na tsare idanu da sauri Nisha takuma daukan hanya zata fice daga parlourn Heelah kamar wata mahaukaciya ta yun k'ura cikin hanzari ta janyo Nisha da karfi wanda ya sanya Nisha tangal tangal ta fad'i saman carpet ta shiga wuri wuri da idanu. Ajmal dake kokarin sakkowa daga steps hango abunda ke faruwa tsakanin Nisha da Heelah ya sanya shi karisa sakkowa cikin hanzari har yana kokarin tuntub'e garin sauri ganin abunda Heelah ke kokarin ai katawa. "Na tsane ki, kin kaini makura yau sai kin bakunci lahira kije kin tadda matsiyaciyar uwarki wata tayi asarar haihuwarki". Nisha kare face d'inta ta yi da tafukan hannayenta gamida lumshe idanu saukan wukar kawai ta ke jira ta ji a wani sashe na jikinta but karisowa Ajmal gurin wanda ya riko hanun Heelah daga ita har wukar gaba daya yayi wurgi da su gefe sai ji kake tab Heelah ta yi tangal tangal ta fad'i saman sofa. Jin sautin fad'uwan Heelah saman sofa yasa Nisha bude idanu ta kalli Ajmal tsaye cikin ta kai ci yana huci kamar tsohon zaki yana kallon Heelah tsabar ta kaici da bacin rai yama kasa bude bakin yin magana dan yau ya kara tabbatar wa da kanshi Heelah mahaukaciya ce ta gaske ba mamaki kwakwalwarta ya samu tabowa idanunta a rufe suke ba ta sanin mai take yi da ba dan Allah ya tun kud'oshi cikin wannan time din ba da ba wannan zancen a keyi ba yanzu. Heelah kuma yun k'urawa tayi cikin rashin na dama gamida taurin kai ta na kokarin sake tin Karan Nisha. Wani gigicecen maruka biyu Ajmal ya saukewa mata ne bisa kuncin face d'inta duka biyu wanda yasa ta ga giftawan wasu tauri da yasa ta d'urk'ushe gurin ta saki wani azabeben ihu ita kanta Nisha sai da ta tsorata da jin sautin marukan daga ji kasan cikin marukan ba wasa, Ajmal zaro belt din wandonsa ya shiga kokarin yi wanda cikin tsoro Heelah ta zabura ta mike tsaye gamida watsawa da gudu hartana tuntub'e ta haura upstairs da gudu kowai waye babu tana rike da kuma tunta biyu ta nufi bedroom d'inta ta da tse kofar tana ta faman kuka. Cike da ta kaici Ajmal ya ciza lips d'insa idanunsa duk sun canza launi saboda bacin rai, a fisge ya waigo ya kallo Nisha wacce ta yi nare nare da ita idanunta duk sun fito waje sabida tsoro ganin yanda Ajmal ya kallota cikin fusata ya sa itama ta mike gamida afkawa da gudu ta bar parlourn dan ba tasan mai zai biyo baya ba. Ajmal komawa yayi ya zauna saman sofa yana kuci cikin bacin rai, gaba daya tunanisa yanda Heelah ta zame masa da gaba daya ya rasa yanda zaiyi da ita because ta zame masa problem sosai tana bashi ciyon Kai, a jima kad'an ya tashi fuuu ya mike ya fice daga parlourn yanufi haraban gidan ya shiga daya daga cikin motocinsa mai gadi ya bude masa gate ya fice daga gidan. Ba jimawa da fitan Ajmal Heelah ta biyo bayanshi sanyi cikin wani shiri na duguwar rigar atamfa da d'an k'aramin mayafi bisa kanta hannunta dauke da handbag d'inta gamida key din motarta fitowa tayi ta yi tanufi motarta ta shiga sai faman matsar k'walla take zuciyarta kamar zata faso k'irjinta ta fito tsabar takaici da bakin ciki tunaninta tunda yarinyar nan tasa kafa ta shigo cikin rayuwarsu ya juya mata baya fiye da daaa sam baya ganinta da wani daraja face d'inta kuma ya koma tamkar ganga abun bugu da zaran tayi yun k'urin taba Nisha sai idanunsa su rufe , motarta tayiwa key daga nan tasa kai ta fice itama. Nisha direct part d'insu ta nufa koda ta karisa parlourn can dining area ta tadda su Hajia tare da su Reeda har sun suma yin breakfast d'insu ganin haka yasa Nisha ta shiga karisawa garesu sai zare idanu take ya yinda zuciyarta ta kuma keta faman bugu. Nisha sai da ta d'agawa Hajia gaisuwa Hajia ta amsa cikin nishadi gamida fara'a kafin Nisha ta samu daman jan kujera ta zauna, hankali Nisha Sam baya jikinta domin tunda ta zauna ta kasa ta ba komai sai idanunta da ta kafar dasu guri guda ta fad'a duniyar tunanin yau abunda Heelah tai mata ya tsorata ta matuka lallai kishi ya fara haukatar da ita ba ta banbance fari da baki. "Ince ko lapia naga kintusa table a gaba mai makon kisuma yin serving abinda kikeso kici sai kuma kika zauna shiru ko wani abinne?". Hajia ta shiga jero tambayoyi tana kallon Nisha wacce tayi sauran dawowa tunanin jin maganar Hajia, girgiza kai Nisha ta shigayi cikin sanyin jiki tana fadi'n "Bakomai". daga nan tashiga serving din kanta ga abinda takeso, tun shigowar ta Hajia ta ke lura da yanayin Nisha tunda ta shigo ta zauna suke ta faman hira dasu Fadeelah but ita kuma ba ta sanya baki gaba daya jikinta a mace yake ba kamar yanda ta saba ganinta ko yaushe ba duk ta nacin abinci ta lura gaba daya ba ta tunanin ta ballai tasan firan da suke. gaba daya yinin yau Nisha tayi shine cikin rashin walwala tsoro da kuma fargaban mai zaije ya dawo yana daya daga cikin abunda yasa takewa k'addaranta kuka shigowar Heelah cikin k'addaran rayuwarta, gaskiyar salma ne fadi'n ta na cewa zama da mahaukaci sai anshirya ballai hauka irin na Heelah kishi da ya zamto mata tamkar haukar dole sai ta nuna mata salon ta haukan maybe ta iya komawa cikin sense d'inta....... Guraren 4 Nisha tsaye bisa saman sallaya tana gudanar da sallahn la'asar wanda tun dazu take ta faman shan bacci sai yanzu farkawanta ta shiga gabatar da sallahn da ke kanta yauma ita kadai bisa bedroom din duk da kusan tare suka kwanta baccin da su Reeda but su sun rigata tashi sun gabatar da nasu sallan sunyi nasu waje kasance cewar kanta na ciyo tasha maganin shiyasa baccin nata yayi nauyi. Nisha na idarwa ta mike gamida ninke darduman gamida cire hijab din jikinta ta dauki dan k'aramin mayafin ta tamai dashi saman kanta daga nan takai hanu ta janyo phone di'nta nan ta cikaro da shigowar sako cikin wayar wanda yasa Nisha g'yara Zama gefen bed. Ajmal ne ya turo sakko yana umartarta da shiga sides dinshi ta g'yara masa bedroom d'insa idan ba shi takeso ya dawo ya g'yara da kansa ba cikin sakon harda alamar emoji na bacin rai alamar fad'a, Nisha gefe ta cillar da phone din gamida tura baki ' shi wannan papan Aheel din ya cika fitina a wannan halinda ake cikine zata yi katub'aran komawa side d'insa ta san mai zata tarar idan wannan mahau kaciyar matar tasa na nan dama ace yana nanne zata iya zuwa koba komai wani abin ya tasu zai iya tare mata but yanzu da baya nan sai dai aje a tadda dan buzunta dan bilhakhi da gaskiya ta ke tsoron haukar Heelah' Nisha ke maganan zuci, mikewa Nisha tayi a sukwane ta nufi door ta bude ta nufo parlour koda ta zo parlour bata iske kowa ciki ba dan haka sai tunanin ta ya bata suna can sashin Hajia dan haka daga nan ta fito haraban gida ta nufi side din Hajia........ " Ni Sam nakasa gane wannan alamar ansamu cikin duhu g'wara a fito da mu haske a fad'a mana matsayin yarinyar nan a cikin gidanan because zagewanta yayi yawa bazai yiyu na cigaba da zuba ido ana cutarmin da ya cikin gidan nan ba yarinyar ta zama kamar gangan church dan Allah ka duba fa kaga yanda yarinyar nan gaba ki daya ta zare ta fita haiyyacinta" Hajia Jummana ta fad'i tana huci gamida kallon KB wanda g'yara zama cikin na tsuwa kamar na Allah yana fadi'n. "Gaskiya dai kam Hajia ya kamata aduba lamarin gaba daya zuwan yarinyar nan ta canza mana alkibilan family yanzu kuma tana shirin shiga tsakanin ma'aurata da gani wannan yarinyar ba yar arziki bane" KB ya fad'i yana wani markwad'e baki irin na bugagun mutane "Kai da Allah can rufewa mutane baki kai yaushe ma kasan kan kance ballai ka iya banbance mai kyau da mara kyau kafara yiwa kanka fad'a kafin kayiwa wani dan haka karna sake jin bakinka anan kafita idona" Hajia ta fad'i cikin fad'a tana kallon KB wanda ya sake baki jin warning d'insa da Hajia ta yi jinjina kai KB yayi gamida komawa jikin sofa ya jingina yana ta faman cizon lips yana kallonsu, su Reeda kuwa idanunsa kamar zai fad'u kasa don harara su kalli KB su kalli Heelah wacce itama take ta faman jefo musu harara a fakaice tana wani langwab'ewa jikin mom d'inta Ajeemal Story and writing By Oum amreesh https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Book 2 Page 91 _______Baki Hajia jumana ta bude da nufin yin magana jin turo door da akayi ana kokarin shigowa yasa gaba ki dayansu suka shiga zubawa door din idanu don ganin mai shigowa. Nisha bakinta dauke da sallama ta turo door da nufin shigowa amma sai tsayawa tayi cak kamar wanda ruwa ya shanye sallamar bakintama sai cikin zuciyarta ta iya karishewa wani abune taji ya tushe mata mak'oshi wanda da k'yar ta iya hadiye miyun bakinta Nisha dai tsayawa tayi ita bata shiga ba haka zalika bata komaba k'afafuwanta sun mata nauyi ko k'wak'waran motsi bata iyawa idanunta da ke hango mata KB wanda ya mata wani k'uri yana binta da wani shu'umin kallo ya kasa dauki ido gefe kuma ga Heelah da mom d'inta wacce take ta faman hararo ta kamar idanunta zasu fice. Heelah tun shigowar Nisha take tawani kafura tana muzurai gamida huci cikin ta kaici da tsanar Nisha cikin zuciyarta jitake kamar tayi wani kukan kura tayi kan Nisha ta kai mata suraa . "Yar nan ya kika tsaya daga bakin kofa shigo kariso ciki mana". Hajia ta fad'i cikin fara'a tana kallon Nisha da tayi zuri da ita kamar ace da ita shiii ta gudu jin abunda Hajj mama tace yasa ba wani musu Nisha ta shiga d'aga k'afafuwanta gamida karisowa a hankali ta nemiguri kusa da su fadeelah ta zauna gamida kamewa tana zare yan idanu dan ko d'agawa Mom din Heelah gaisuwa ta kasayi dan ta san ba lallai ta amsa gaisuwanta ba yanda take ta faman wurginta da wani muguwar kallo. Dan g'yara zama Hajia tayi tana kallon Heelah da Mom d'inta tana fadi'n "To a takaice kun kawo k'orafine kan Nisha da aiyimata iyaka ko ince katanga daga zuwa side din Heelah?". Hajia ta tambaya tana kallonsu "Kwarai kuwa tunda ita Heelah ba kuturwa bace ballai ace ko gazawa tayi wajan kula da mijinta da d'anta ballai ace har sai wata banza can daga gefe ta taimaka mata wajan kula da mijinta da muhallinta". Hajia jumana ta fad'i tana kallo Nisha cike da ta kaici. "To ina so kusani ko shi Modibbo a yanzu bashida daman iya yakice Nisha daga tsaginsa saboda matsayin Raheelah da Nisha abu gudane ta ban garansa a yanzu". "Kamar ya Hajia mai kike fad'a ne haka? Heelah fa matarsace kuma yar uwarsa ta jini ba suda alak'ha da wannan tsincecciyar magen". Hajia jumana ta fad'i cikin kasa fahimtar zantukan Hajia da inda suka dosa. Wani k'ayataccen murmushi Hajia ta saki cikin rashin damuwa ta kuma kallon Hajia jumana tana fadi'n "Hakane kamar yanda Raheelah ta kasance daya daga cikin y'ay'an gidan nan kuma babban sirika cikin gidan to Haka itama Nisha ta kasance a yanzu" "What!!! ?".Heelah da KB suka fad'i a tare suna zare idanu kafin Heelah ta mike tsaye tana bin Hajj mama da kallon mamaki cikin maganganun ta . Hajia jumana Heelah ta bi da kallo wacce ta mike tsaye cikin al'ajabi tana bin kakartasu da kallo kan Heelah gaba daya ya dau zafi. Hajia jumana kallon ta tamayar kan Hajia cikin mamaki ta shiga tambayar ta. "Kina nufin itama sirikan gidan nan ce ?". ta tambaya Tana zare idanu "Kwarai kuwa sirikar gidan nan ce kuma matar Modibbo ce abokiyar zaman Heelah tun ba yanzu ba abunda ya dad'e yana rufene yau kuka bukaci sa ni dole sanar daku gamida yi muku bayani ina fatan kun fahimta?". "Innalilahi wa'ina ilaihi raju'un yanzu wannan abunne kushiyar Heelah wacce zatayi shi da ita?" "Kwarai kuwa kam ai ba ta fi karfin amata kishirya ba ko wannan da kike gani tafi Heelah sau dubu amfani". Hajia ta fad'i cikin alfahari tana kallon Nisha. "Haba Hajia wannan karun kuma ta kan Heelah abun ya biyo abunda aka min shi aka kuma na na tawa akan y'ata? haba Hajia mai na tare muku a rayuwar nane fisabilillah kuma arasa da waza a hada kishi da Heelah sai wannan yar k'aramar alhakin mai zubin muna fukan matan tsintacciyar mage da bata mage". "K'addarace ta zo da haka kuma kune silan faruwar hakan, kamar yanda kika amshi naki k'addaran haka itama zatayi hakuri ta amshi k'addaranta". Hajia ta fad'i tana mike k'afafuwanta cikin rashin damuwa na ko ajikinta, parlourn shiru yayi KB saki baki yayi yana kallon Hajj mama gefe kuma ya koma ya kalli Nisha wacce kanta ke sun kuye tana wasa da yatsun hannayenta dasuke ta faman bari daga ka ganta kasan a tsorace take kafin Kb ya kuma kai kallonsa ga Mom d'insu wacce ta ke cikin tsantsan bakin ciki da ta kaici zallah . Kb da Hajia jumana tare suka kai kallonsu ga Heelah wacce tunda tamike tsaye ta kasa tsugul wani zazzafan huci ta dinga furzarwa zufa sai faman ke tu mata yake lips d'inta kuwa sai faman rawa yake tana su cewa wani abun Amma yanda zuciyarta ke faman ta farfasa saboda bakinciki ta kasa magana. "Fadeelah ya kikaga sarakan kishi sai zufa ake kamar anyiwa sarki Karya?." Reeda ta fad'i k'asa k'asa. "Aikuwa kalli yanda ta koma kamar anjika mage a ruwa". Fadeelah ta bata amsa cikin rad'a Nisha duk tana jinsu Saura kad'an Fadeelah da Reeda su tuntsire da dariya sai kowaccen ta tushe bakinta saboda kar sautin dariyarsu ya fito fili. Wani ihun ta kaici Heelah tasake gamida zubewa kasa tayi zaman dirshen kamar ta b'abb'iya tana shure shure kamar yar bori, Nisha kamar ta sake fitsari gurin dan tsoro su kansu su Fadeelah sai da suka sha ruwan jikinsu ganin abinda Heelah keyi kamar wacce ta kune akai. Haka Hajia bayan mamaki abun har tsoro ya bata ta shiga zazzare ido tana kallon ikon Allah , Hajia jumana ne ta matsa ta shiga d'agota tana fadi'n "Innalilahi wa'ina ilaihi raju'un naga takaina ni jumana Yar nan ki kwantar da hankali ki karkije ki sawa kanki wani ciyon na rasa tudun dafawa taso mutafi kb taso ka tayani daga ta mukaita mota ". Mom ta fad'i cikin damuwa gamida bacin rai cikin hanzari Kb yasa hanu suka sun kuci Heelah sai faman fisge take tana fadi'n su kyaleta yau saita kashe Nisha . Ganin yanda take borin bilhakhi da gaskiya ta na neman kwace musu yasa Kb ya tattaro karfinsa ya sun kuceta ya azata bisa shoulder d'insa ya fice da ita daga parlourn Heelah sai faman bugun bayansa take da karfinta kamar ta samu ganga shikuwa ko ajikinsa kamar an tsikari kakkausa. Hajia jumana kuwa sai faman wai waiyansu Hajia da Nisha ta ke ta na kumbura baki daga nan itama ta bi bayansu ta fice .... Karfe 8:30 familyn zaune suke Dining table suna gudanar da dinner d'insu kamar yanda suka saba suna yar firansu wannan karon harda Daddy a cikinsu kasamcewar yau dawowar wuri yayi, Hajj mama tas ta gama kwashe musu abunda ya furu dazu da yamma zuwansu Heelah da Mom d'inta da kuma kb abun dariya abun takaici su farida kuwa dariya kamar ba gobe suna mai da yanda akayi "Ikon Allah abun mamaki basa k'arewa kodai almatsutsai gareta ba a saniba?". Daddy ya tambaya cikin mamaki "Bawani shashanci ne kawai gamida kishi idanuta sun rufe karfi da yaji zata maida kanta bitacan akan kishi banza Allah dai ya kyauta". Ammi ta fad'i tana tab'e baki "Amin ". gaba ki dayansu suka amsa gamida cigaba da gudanar da dinner d'insu suna hira banda Nisha da tayi shiru tana saurarensu yayinda suke hiran ta su jikinta duk a sanyaye Ammi kallon Nisha take afakaice cikin tausayawa tasan yanzu Nisha na cikin tsoron kasancewarta inuwa daya da Heelah tasan wannan ma kadai zai dinga sanya ta cikin tunani hankalinta yaki kwanciya. Wani nan nauyan ajiyar zuciya Ammi ta sauki gamida ture plate din gabanta ta mikewa tsaye tashiga yi musu bakwana zata shiga bedroom din ta kwanta tasanar dasu cewa gobe tana da uzuri a office dawuri zata fita shiyasa takeso tayi bacci da wuri gudun makara kafin dagan tanufi upstairs tashige bedroom din ta. Jim kadan shima Daddy ya mike gamida yi musu sallama ya bi bayan Ammi because ya lura da yanayinta da damuwa ta bargurin hakan yasa ya bi bayanta ya barsu Hajia gurin wanda suka cigaba da hiransu. Koda ya isa bedroom din Ammi zaune ya hangeta bakin bed ta rafka uban ta gumi tana tunani , karisawa Daddy yayi ya zauna kusa da ita cikin natsuwa ya kalleta gamida tambayar ta. "Lapia kuwa hajjajo", Daddy ya tambaya cikin kulawa "Uhm sam na kasa farin cikin kasamcewar wannan lamarin tsakanin Nisha da alh k'arami sam banso wannan k'addaran auran ya fad'a kan yarinyar nan ba". Ammi ta fad'i cikin damuwa. "Kash haba hajjajo mai yasa zaki fad'i haka kuma mai abun rashin jin dad'in acikin wannan Lamarin Allah ne fa ya had'a abinsa ". "Bawai ina ja da hakan bane kawai ina tausayin yarinyar ne ganin halinda ta tsinci kanta tsakanin mutane biyu duk da nasan Modibbo ba son Nisha ya keba kawai yayi biyayya ne ga maganar mu but nasan zai zauna da ita cikin aminci kamar yanda ya zauna da Heelah ba tare da k'yara ko hantara ba. "To amma duwana shine ina tsoron Heelah da mahaifiyarta ina tsoron abunda zaije ya dawo ina tsoron su saka yarinyar nan a gaba bana son abinda zai cutar da ita ko yasata cikin damuwa kasan Nisha ba mai son haya niya ko fitana bane kuma gata da tsoro ballai ace zatayi hobb'asan karbawa kanta yanci a zaman takewan su ita kuma Heelah rigimarta ma ya fi karfinta ranar ba kaji abunda take fad'i akan Nisha bane time din da nake nocking door d'insu a tunaninta Nisha,". Dan g'yara zama Ammi tayi gamida kallon Daddy da kyau ta cigaba da fad'in. " Ni son samu ne ma idan abun zai zo da fitana gamida tashin hankali araba musu gida kawai ita Nisha abar mana ita nan ita kuma Heelah ya maida ita can sabon gidanshi ta zauna acan suyi nisa da juna.." . "Shiii ya isa haka please insha allah ma ba abunda zai faru , muna nan zamu saka idanu akansu ba lallai rabe muhalli shine ma fitaba ganin motsawansu kan idanumu shi zaisa mudinga ankara da halinda suke ciki". Daddy fad'i cikin nusar da ita yanda zata fahmita., Shiru Ammi tayi tana sauraren maganganunsa cike da gamsuwa Ammi ta jinjina Kai tana fadi'n "Gaskiya ne zancen ka yana kan hanya yallabo'i to Allah ubangiji ya hade kawunansu". "Amin". Daddy ya amsa gamida mikewa tsaye yana fad'i " Bari naje nadan watsa ruwa because zafi nakeji sosai". Gyada masa kai Ammi ta yi harya mike da nufin fita sai kuma ya koma ya zauna yana fadi'n "Au na mance ban sanar dake ba gobe za akawo kudin auran hajia k'arama ya kamata a shiryawa zuwansu da yaune but ban samu dawowa da wuri bane saboda uzurirruka". "But insha allah guraren 4 na yamma zamu samu halartarsu zuwa cikin gidan nan ". "Masha Allah insha Allah Allah bari na sanarwa da Barka tun yanzu idan da akwai abin da babu a tanada duk da gobe fitana office zai kasance dawuri but zan dawo dawuri saboda ayi komai da ni". Ammi ta fad'i cikin farin ciki tana washe baki. "To shikenan ya kamata" . daga haka suka Mike a tare Ammi na biye da shi suka fito tare Daddy ya nufi bedroom d'insa ita kuma Ammi ta nufo downstairs. Koda Ammi ta sakko ba ta tadda kowa ba duk sun watse sun nufi makwancinsu bayan da suka gama Shan firansu hakan yasa direct Ammi ta nufi bedroom din Barka time din har Barka ta suma shirin kwanciya jin nocking bakin door d'inta yasa ta mike ta bude ganin Ammi tsaye bakin door din ta shiga washe baki "Sorry hala kinsuma bacci na katseki". "Ah rankiyadad'e bawani bacci shiri dai nake yanzu wani abin kike bukatane ?". Barka ta tambaya tana washe baki. "Am Barka dama gobe muna da bak'i cikin gidan nan so inason list din abunda kitchen dimu yake da bukata zuwa gobe da safe kafin na fita office". "To shikenan Hajia ba matsala insha allah kuwa". Barka ta fad'i cikin girmamawa, daga haka Ammi ta juya tanufi upstairs ta koma bedroom d'inta. Guraren 10 motar Ajmal ta kunno kai haraban gidan wanda mai gadi ya bude masa gate ya shigo yayi parking daidai parking space daga nan ya fito daga motar cikin ta fiyar k'asaita gamida kamewa ya nufi side d'insa.. Ajmal Story and writing By Oum amreesh https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/ ?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Book 2 Page 93 ______ Koda ya karisa shigowa komai fine kamar yanda ya zata parlourn sai wani sassanyan k'amshi ke tashi na air freshener, Cikin natsuwa Ajmal ya suma haurawa upstairs ya nufi bedroom d'insa yana isa bedroom d'insa ya tura door ya shiga ya maida motar ya rufo. Lumshe idanu Ajmal yayi jin wani laune k'amshi dake wanzuwa na musamman cikin bedroom din wanda yasashi karisawa a hankali ya karisa tsakiyar d'akin a kasalance sai wani lumlumshe idanu ya ke kamar mai jin bacci da alamun gajiya sosai a tare da shi. Daidai bakin bed d'insa ya karisa zauna ya na wani sake ajiyar zuciya a hankali daga nan ya kai hanu yasuma zare tie din dake mak'ale jikin wuyarsa yana daga zaune ya ra ba kansa da kayan dake jikinsa da yake jin sun ishesa sunyiwa jikinsa nauyi ya rage daga shi sai short cikin yanayin kasala da k'iwa Ajmal ya mike bisa lallausan bed d'insa face d'insa na kallon celling ya rintsa idanu. Jin motsin bude door din bathroom yasa Ajmal ya dan waro idanu ya kai kallonsa ga gurin nan idanun shi sukaci karo da na Nisha wacce ta bud'o door din cikin hanzari tana shirin fitowa wanda ganin Ajmal kwance saman bedroom yasa ta danyi jim tana wutsi wutsi da idanu duk saurinta kenan kar Ajmal ya dawo ya taddata sai yanzu take masa gyaran bedroom d'insa wanda tun ido na ganin ido ya sanya ta but ita kuma tuni ta manta da batunsa domin kuwa har tayi shirin bacci ta kwanta ta tuna da aikin da ke gabanta but wunin yau da hankali ta baya jikinta yasa ta mance shalaf. Shima tunani Ajmal kenan bata tashi masa gyara ba sai yanzu da tayi ra'ayi Ajmal dauke idanu yayi daga kallonta ya maida idanun ya rintsasu cikin rashin damuwa da lamarinta . Wanda yasa Nisha ta hadiye miyu mai daci kafin ta fitowa ta shiga karisowa tsakiyar d'akin tana kasa da kai ganin yanayin da Ajmal ke ciki da gashi sai short ya wani mike ko ajikinsa bare kuma ya damu. D'an tsaya ta yi daga gefe dashi cikin ladab ta dan lankwashe gwaiwowinta kamar mai shirin dukawa ta shiga fadi'n "San sannu da dawowa", muryanta harna sarkewa, amma bai amsa mata sannunta ba ya bude manyan idanuwansa ya shiga kari mata kallo da ita da yar night gown d'inta wanda ko gwaiwowinta bai isa ba mai tsantsi da taushi ita kanta sai faman ta kure kanta take saboda tsarguwan da kallon da Ajmal ke jifanta da shi. "What do you want". Ajmal ya tambaya murya can ciki yana wani hade gira ganin ta k'ikam ta masa tsaye bisa kansa , dugun hijab d'inta da Ajmal ya kwanta kai da bai san da zamansa ba Nisha taimasa nuni tana so ta dauka sai time din Ajmal ya mike da ga kwanciyar da yayi jiki ba kwari yana ya motsa fiska kafin ya kai kallonsa ga duguwar hijab din Wanda sam bai lura da shi ba kauda kai Ajmal yayi gamida da hade hannayensa ya shiga yin wata duguwar mika kafin ya mike tsaye cikin zafin nama wanda sai da ya sanya yan hanjin cikin Nisha suka kad'a tayi baya kad'an cikin tsoro ganin yun k'urin da Ajmal yayi wajan mikewa kamar mai shirin kawo hari shikuwa Ajmal dama da gangan yayi hakan Dan kawai ya tsukano tsoronta dan ya san abu kan ya ke tsoratata gashi yanzu ma hardayin wani baya da sauri na zare yan idanu, Wani harara da Ajmal ya watsa mata kai kace mace ne sannan ya juya abunsa ya nufi bathroom don wanke jikinsa, Nisha tunda ya bar gurin ta kasa dauke idanu akansa ta bishi da kallo tana sauke ajiyar zuciya gamida karewa zubin halittar jikinsa kallo ' masha Allah darirren namiji tsayayye san kowa kin wanda ya rasa wanda ko wacce mace ke fatan samu matsayin madubi a bin haskaka rayuwa gaskiyar salma ne da tace ta godiyawa Allah samun Ajmal matsayin a bokin rayuwa komai ya had'a a abunda ya rasa sai mishkilanci ' "Wai tunanin mai nake hakane ?". Nisha ta fad'i afili ta d'an bugi goshinta kad'an ta sauka kan layi sai faman zantukan zuci take hanu ta Kai ta janyo duguwar hijab d'inta tasanya ta yi ta fice daga bedroom din. Ajmal wanka yayi sosai ya sakarwa kansa ruwa mai dumi ya shiga tsaftace jikinsa kafin ya fito cikin bathrobe hanusa rike da wani k'aramin towel yana tsantsame ruwan dake bisa suman kanshi ko da ya fito bai tadda Nisha cikin bedroom din ba kamar yanda yayi tsammanin , mai mai sanyin k'amshi Ajmal ya nema ya shafa bisa jikinsa kafin ya nemi duguwar jallabiyarsa fari k'al ya sanya kafin ya fito daga bedroom din ya nufi downstairs domin hadu coffee kamar yanda ya saba ya zamar masa jiki sai yasha kafin kwanciyar sa. Koda ya nufo parlour ya karisa dining table nan ya lura da abubuwan da Nisha ta jere su gurin ta koma gefe tayi tsaye tana jiran sakkowan sa , Ajmal table din ya bi da kallo yana karewa abubuwan da Nisha ta shirya masa saman table din gwanin sha'awa, shi sam baya jin yuwa already cikinsa ma a ciki je ya ke ba space din saka wani abin kuma . But bayaso yayi miss special food na ta because yasan yarinyar akwai zakin hanu wajan girki bugu da kari yanda ta iya sarrafa abubuwa kala kala wanda yake so yake iya ci idan yana diban girginta har rasa tunanisa yake da yasan da hidimar data ta nadar masa da ba abunda zaisa ya cika cikinsa duk da yana jin a yanzu ba wani gurbi da wani abu zai iya samun g uri amma bazai gwalewa bajintar ta ba d'an haka ya sanya hanu ya jaa kujera ya zauna . Yashiga bude kyakykyawan bowl mai dauke da vegetables beef potato soup sai k'amshi kakeji ya nata faman tashi sai oat milk daga gefe cikin cup sai v plate d'in snack shima a gefe ,vegetables soup din nan da yake jin k'amshin sa na faman tsokano hancinsa ya suma da shi . taikace komai na gurin sai da Ajmal ya taba Nisha duk tana daga gefe tana sato kallonshi ta gefen ido ganin yanda ya zage yanata sanyawa abubuwan albarka, Ajmal yaso shanye oat milk din nan because ya masa dadi sosai but yakasa yanda yake jin cikinsa yayi bala'in cika yaukam yanaga harda koshin haramun yayi don baijin ko k'wak'waran motsi zai iyayi ballai ya mike . Shiru yayi yana shafo cikinsa wanda yayi masa nauyi kafin ya dago yan idanunsa ya kallo Nisha wacce suka hada ido tana kallonshi itama idanu su haka gameda na juna da hanu ya mata almar kira kafin ya dafa table ya mike tsaye. Nisha jan kafa tayi k'irjinta na bugu ta kariso kusa da shi ta tsaya sai ji tayi yana fadi'n "Cikina ya cika sosai help me". Ajmal ya fad'i gamida daura hanunsa shoulder din Nisha ya dafota gwalo idanu Nisha tayi cikin mamaki ta kalleshi gamida waro idanu jin yanda ya rungomuta jikinsa ya wani sake jiki . Ita duk yanda take ganin tayi masa dinner mai sauke mara nauyi wanda bazai ta kurashi ba nan ma bawai ya cinye duka bane amma yana mata k'orafin ya k'oshi dayawa har yana bukatan taimako wajan tafiya. "Rikeni da kyau ". Ajmal ya fad'i gamida dago hannun Nisha ya zagayo dashi wajan waist d'insa alamar tarikeshi a bun mamaki ba ya karewa Ajmal komawa Nisha yayi kamar yaro k'arami abunda yake " Muje to". daga nan Ajmal ya suma daga kafa Nisha na rike dashi kamar wani mara lapia haka suka haura upstairs Nisha har cikin bedroom ta kaishi daga nan Ajmal ya zame jiki a hankali yana fadi'n "Thanks". Nisha ji tayi zuciyarta tayi wani fari jin gode mata da yayi cikin dad'in rai da sakewan faska , Nisha na ganin Ajmal ya nemiguri ya kwanta luf ya lumshe idanu har Nisha ta juya da nufin fita sai ji tayi ya kuma fad'in "Ru fe ni". Ya ce idanu lumshe haka kawai Nisha ta tsinci kanta da murmushi yau sakalcin da Ajmal ke ji dashi ko dansa Aheel iya ka kenan. A hankali Nisha ta karisa ta janyo masa blanket ta rufeshi ruf daga nan Nisha ta juya tafice harda guzurin rage masa light din d'akin , Nisha kafin ta bar side din Ajmal sai da ta tattare saman table din kafin ta fice ta nufi part d'insu. Washe gari tun azahar su Ammi Nisha da Baraka suke kawai da kawowa suna aikace aikace har da su Reeda suma duk sun sanya hanu cikin aikin tunda suma alhamdulillah za ace hannayensu ya fad'a sosai ta fannin girke-girke cikin dan k'ank'anin lokaci ,kafin la'asar sun kammala komai anjerashi can sama parlourn Daddy ko yanzu baki suzu mai ya zama ready an gabarmusu da abubuwa na alfarma . Yammalis babban parlourn Daddy ya tare manyan mutune dattawa su rai uku cikin manyan kaya irin na manyan mutane mai fitar da zallar kima da mutunci mutum yayinda ya ke cikinsu mutum biyu suna zaune bisa duguwar sofa wata mahaifinsa da uncle's d'insa guda biyu gefe kuma Daddy zaune shida dan uwansa abbansu Heelah suna ta tattaunawa tsakanin su gameda lamarin auran y'ay'ansu. Sun kawo sadakin Fadeelah 500k cikin amince sai dai Daddy su Daddy sunki amsa 500k saboda a tunanusu kudin yayi yawa doctor fu'ad dansu ne basa bukatan kudi mai yawa kamar haka sakin Reeda Nabilah da na Nisha 300k dan haka na Fadeelah ma hakan zasu karb'a acewarsu ko lefe ko wani abu ta bangaran su basa bukatan komai da ya wuce sadaki shima saboda shine ginshikin aure but duk wani abu da ya biyo bayan haka ba su da bukatarsa. Wakilan doctor fu'ad sunji dad'in hakan matuka an mutunta tasu akuma karramasu sunci sunsha sunyi ni'an daga abubuwan da aka jera musu iri da kala wasun ma basu samu budewa ba............ Kwance tashi a Saran mai rai yau saura 2 weeks bikinsu Nisha, Goggo rabi tuni ta zo aka suma shirye shiryen biki da ita daga ita har ja amarta kawayenta da y'ay'an uwan mijinta aka ware musu sashi na musamman ita da tawagarta gaba daya amatsayin ta na uwar ango kuma uwar Amarya , Shikuwa ango Muhaiseen tare da Abbansa zasu zo saura 1week bikin . Ta bangaran Ammi tuni ta akasuma hada y'ay'an nata suka suma karban ingantaccen g'yaran jiki daga wajan kawar Ammi yar barno wacce take da shararan shagon g'yaran jiki nan jahar kano mai suna BARNO GIDAN KAM'SHI har gida Ammi ta sa ake zuwa g'yara mata y'ay'an nata cikin sati daya tuni su Nisha suka suma walkiya suna haskakawa farin launin jikinsu ya kara baiyana mai kyau jikkunansu yakara zama luwai luwai gwanin sha'awa . Haka Ammi ta zage tayi tsayuwar daka wajan g'yara y'ay'an nata yanda ya kamata especially Nisha da takasa yadda ba abunda ya wakana tsakaninsu da Ajmal ta din da ya dauke ta suka kwana waje duk da Nisha ta bata tabbacin ba komai but zuciyarta yakasa gamsuwa. Ta bangaran Goggo rabi itama da nata guzirin na abubuwan da ta tana darwa su Nisha wanda zai sa su zama yan lele abun riritawa wajan maza jensu tunda itama matsayin uwa take agaresu zatasu taimaka musu wajan g'yara rayuwar auran y'ay'anta . Yau kuma kamar kullum harsun kwanta goggo rabi ta shigo cikin bedroom d'insu hannayenta dauke da tray tashi ta ajiye saman carpet sannan ta kallesu gaba kidayansu da sukayi zuru da idanuwa suna kallon Goggo da abunda take tafe dashi. Murmushi Goggo rabi ta sakar musu tashiga fadi'n "Ta so y'ay'an nan yau wani abun arziki na kawo muku na san zakuso kuma zakuji dadinshi , taso maza kuzo kuci yan albarka" . Goggo rabi ta fad'i tana washe baki. "Allah yasa yau mai dad'i ne kamar na jiya".Fadeelah ta fad'i tana washe baki itace first din sakkowa Reeda ta bi bayanta sannan Nisha ta dan jajiki ta sakko sukayi zobe jikin tray din bowl ne guda uku kowane cikinsa dauke da yar shilan kaza nan Goggo rabi ta duka itama kowacce ta ajiye mata bowl guda gabanta kafin tamike tsaye suka bita da kallo. "Oya a cinye min ita tas a sha romo ko dis karna gani but banda kuskuren tauna K'ashi". "Goggo rabi ai wannan kazace kuma ai baza mu iya cinyewa ba ". Fadeelah takuma tambaya Reeda da Nisha kuwa sai idanu sun tusa bowl a gaba suna kallo. "Eh ita ce Amma ba irin wanda kuka saba ci bane wannan da ban yake nidai kuci ba suru tuba karna dawo na tarar ba acinye min shi ba". Goggo rabi na fad'i haka ta juya ta fice abinta, kallon junansu suka shiga yi kafin kowa ta maida hankali ga abunda ke gabanta ba wani bata lokaci suka suma ci. Abun kamar pepper soup din kaza yake tun sunaci amarmace har saida suka suma jin cikinsu ya cika haka suka dinga turawa Nisha ji tayi kamar zatayi amai haka ta dinga turawa kamar zatayi kuka sai da kowannesu ya cinye tas sannan suka gefe suna nishi kamar masu na k'uda koda Goggo rabi ta dawo tadda suncinye kazar tas sunsha romo sai kasusuwa kwai kamar yanda ta umarcesu. Bakaramin dad'i ta jiba ganin sun cinye ta tas haka Goggo rabi ta dauko tray ta fito sai dariya take musu ganin yanda ta baro kwance ba k'wak'waran motsi mai kyau... Ta ban garan Nisha sam Ammi ta dakatar da ita daga zuwa sashin Ajmal har sai ta tare ankai masa ita turakansa dan daga ita harsu Reeda ko kofar parlour basa fita ammi Baraka ta sanya da zaran Ajmal ya sanya kafa ta shiga ta g'yara masa side d'insa breakfast dinner tunda bai cikayin lunch a gida ba sai weekend Ammi da kanta ta dau nayin yimasa wataran ta kai masa da kanta wani lokaci Baraka ta kai. Saboda a cewar Ammi ga Ajmal anshiga week din biknsu a suma yiwa Nisha g'yaran jiki ko kad'an ba aso rana ya tabata dole ya danyi hakuri na dan wani lokaci because ko parlour basu cika fitowa any time ba , Ajmal bai wani damu da hakan ba ya cigaba da sabgogin gabansa. A satin bikin Ajmal ya samu kansa ga tafiya wani taro k'asar England a cewar sa zai halarci wani babban taro da aka gaiyaceshi kuma dole ya kasance wajan taro dan haka ya sanarwa dasu Ammi da Daddy batun ta fiyartasa acewarsa kwana2 kafin bikin zai dawo . Duk da abun baiyiwa su Daddy dad'i ba Amma basu da ikon hanashi tunda taron bai wuce kwana biyu, ranar laraba da misalin 10 na safe aka shiga gabatar da saukan alkurani cikin katafaran farfajiyar gidan yan uwa da abokin arziki makota da yan anguwa mazansu da matansu manya da yara haka aka cika makil ba masaka tsinke anci ansha yanda ya kamata kuma ansauke alqur'ani cikin amijinci da kwanciyar hankali, zuwa azahar aka suma watsewa. Washe gari alhamis da yamma ka shirya kyakykyawan amare cikin shiga na alfarma shiga mai kyau da k'ayatarwa sunyi kyau harsun gaji komai iri daya haka aka musu duk wanda ya kallesu idan bai sansu ba zai iya cewa yan ukune yanda komansu ya kusan kama da juna domin ko makeup din face dinsu iri dayane sai launi fari da Nisha ta dan darasu kad'an . Karfe 4 na yamma ka suma gabatar da k'ayataccen walima zallan mata a ka gabatar wa amare walima gamida wa azi mai shiga rai da zuciya sunsha waazi da nasiha yanda ya kamata ankuma ci ansha anyi guzuri bayan kammala walima aka shiga daukan hoton nan tarihi kawaye da abokan arziki gamida yan uwaa. Salma ba k'aramin hallaci tayiwa Nisha ba because ba wani program da aka gabatar da bata halarceshi ba kamar ba sabowar Amarya ba Nisha ba k'aramin dad'i ta ji ba dan harda yar k'walla na farin ciki bugu da kari gawasu friends d'insu ma da wad'ansu har ta mance dasu Salma ce duk ta tura musu katin gayyata Nisha tayi farin ciki sosai su Fadeelah ga tarin kawayensu burjik sai hutuna ake ta gabatar wa bayan daga nan kuma aka shiga watsewa kasan cewar duhu ya fara magrib ya kabatu kai...... Kwance su sunyi shirim dasu kowaccen su sai sauke ajiyar zuciya take gaba daya gajiyan yau da banta duk sun gaji gurin wali matansu manya da yara haka aka cika makil ba masaka tsinke anci ansha yanda ya kamata kuma ansauke alqur'ani cikin amijinci da kwanciyar hankali, zuwa azahar aka suma watsewa. Washe gari alhamis da yamma ka shirya kyakykyawan amare cikin shiga na alfarma shiga mai kyau da k'ayatarwa sunyi kyau harsun gaji komai iri daya haka aka musu duk wanda ya kallesu idan bai sansu ba zai iya cewa yan ukune yanda komansu ya kusan kama da juna domin ko makeup din face dinsu iri dayane sai launi fari da Nisha ta dan darasu kad'an . Karfe 4 na yamma ka suma gabatar da k'ayataccen walima zallan mata a ka gabatar wa amare walima gamida wa azi mai shiga rai da zuciya sunsha waazi da nasiha yanda ya kamata ankuma ci ansha anyi guzuri bayan kammala walima aka shiga daukan hoton nan tarihi kawaye da abokan arziki gamida yan uwaa. Salma ba k'aramin hallaci tayiwa Nisha ba because ba wani program da aka gabatar da bata halarceshi ba kamar ba sabowar Amarya ba Nisha ba k'aramin dad'i ta ji ba dan harda yar k'walla na farin ciki bugu da kari gawasu friends d'insu ma da wad'ansu har ta mance dasu Salma ce duk ta tura musu katin gayyata Nisha tayi farin ciki sosai su Fadeelah ga tarin kawayensu burjik sai hutuna ake ta gabatar wa bayan daga nan kuma aka shiga watsewa kasan cewar duhu ya fara magrib ya kabatu kai...... Kwance su sunyi shirim dasu kowaccen su sai sauke ajiyar zuciya take gaba daya gajiyan yau da banta duk sun gaji gurin walima saboda yanda aka dinga nan da su duk alumar gurin kowa na son daukar hoto da amare Nisha wani ji take kanta na wani sarawa b Baraka ce tashigo cikin bedroom din tadda su kwance Barka ta kalli Nisha wacce take ta faman lumshe idanu tanason bacci ko kwalliyar bikin bata samu daman cirewa makeup din face dinsu kawai suka wanke shima saboda sallah da sukayi banda Nisha da makeup din ta haryan yake face d'inta kamar yanzu akayi kasance ita tana fashin sallah. "Dama Ammi ce takeson ganin ki ta ce na kirawo ki gashi ma bacci na samu kina kokarin yi". Baraka ta fad'i na dan washe baki, Nisha jin Ammi na kira yasa ta wangale idanu tashiga mikewa daga kwanciyar da tayi ta nemi mayafi ta sanya saman kanta ,Fadeelah tuni tayi bacci tun bayan da ta idar da sallah ko kayan jikinta ba ta mu canzawa ba sai Reeda da take ta faman waya da Muhaiseen wanda ya ke can masaukinshi. Nisha da Baraka saida suka fito parlour bakowa parlourn sai d'aid'aikun mutanen goggo rabi da suke zaune parlourn suna hira wad'ansu kuma na kallo Nisha har ta na da shirin haurawa upstairs Baraka ta ja hanunta suka koma gefe suka tsaya kafin Baraka ta suma fadi'n. "Tsaya yar nan wannan Kiran da na miki ba na Ammi bane dama yallabo'i ne ya dawo Ammi ta ce na kai masa dinner d'insa to shine ya ce na turo masa ke". Tura baki Nisha tayi tana fadi'n "Ni gaskiya ba zani ba Ammi ta hana bazan saba maganar taba ni kaina ma ciyo ya ke bacci na ke ji kawai kiyi tafiyarki baba Baraka ni bazani ba". Nisha ta fad'i gamida juyawa zata koma. "Aa yar nan duk da Ammi ta hana ya kamata ki amsa kiran mijin ki kuma ai bawai kinsa ba wa Ammi bane dan kin amsa kiran mijin ki komawa ciki kik'i amsa kiran nashi shi zai iya jifa ki cikin fushin mahalicci ni sam banga wani alfanun hanaki haduwa da mijinki ba wata kilama kewarki yayi dayawa yake bukatan sanyaki idanunsa ki daure kije da Allah". Shiru Nisha ta yi dan tasan maganganun Baraka suna kan hanya but tasan bawai ni kewa , yashe ma ya damu da ita ballai yayi wani kewarta sai dai wani k'orafi ya keso kuma yayi daban dan tasan ba arasashi da k'orafe k'orafe "To bari naje ".Nisha ta fad'i tana tura baki gamada sakai ta fice daga parlourn ta nufi side din ajmal cikin shirinta mai kyau face d'inta dauke k'ayataccen kwalliya da takasa wankewa tana kokarin bacci da shi a face d'inta ..... Kwance ya ke saman duguwar sofa yana sanye cikin wani shirt mai ga jeran hanu sai wando Jeans iya ka gwoiwa face d'insa na kallon sama ya fad'a duniyar tunanin gefe saman table tray din abincin da Baraka ta kawo ta ajiye masa but ko takai bai bi ba dan wani time din ya tashi ya bude food flast din ma aiki ya kan Zama masa sai yaji gaba daya ganda ta kamashi Nisha ta gama shagwabashi ita take serving d'insa ta tura masa plate gaba sai dai kawai ya dau spoon ya suma ci . Hatta coffee idan yan gandan nasa suna nan ita yake kira ta kawo masa but kwana biyu da bai sanyata idanusa ba sai ya tsinci kansa da kewan rashin ganinta rasa tantance wa kewar ganinta ya ke ko kuma dai hidamar da take dashi ya ke yiwa kewa ? Ajmal Story and writing By Oum AmReesh https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 94 ___________ Turo door Nisha tayi bakinta dauke da sallama ta karisa shigowa cikin parlourn tun shigowar ta har takarisa shigowa tsakiyar parlourn ta nemiguri ta duk'a ya ke binta da kallo ganin yanda ta canza gaba ki daya cikin yan kwanaki ta kara cika sosai launin fatan ta kuwa sai wani glowing ya ke tana haskawa dan harwani yellow yellow ta yi kamar k'wai ga wani kamshin da ya ke tashi na musamman daga jikinta duk da bawai kusa dashi ta keba yana iya juyo kamshin jikinta daga inda yake makeup din face d'inta ya bi da kallo yanda gaba kiya daya kamaninta ya sauya kamar ba face d'inta ba ta kuma kamar wata yar tsana. "Sannu an wuni lapia". Nisha ta fad'i amma sai ta ji shiru bai ce da ita k'ala ba ballai ya amsa mata ya tusa ta gaba yana kallo, d'an kauda kai Ajmal yayi gamida lumshe idanu shi duk ya mance ya shagaltu da kallon kyakykyawan face d'inta sai kuma ya sake dago kai ya kalleta yana fadi'n "Kawomin coffee". Ajmal ya fad'i yana shafo sajin habansa jin abunda Ajmal ya ce saida Nisha ta dan turo baki a fili dama wannan shine kiran sai taji dama ba ta amsa kiran nasaba a ranar bikin nata ma ba ta huta ba kenan Ajmal yana ganin yanda Nisha ta turo dan tsukekken pink lips d'inta gaba tana faman jan jiki ta mike tsaye da nufin gudanar da abun da yace harta taso zata shige saijin tayi Ajmal ya sanya hanu ya janwota ta fad'o jikinsa gamida riko waist d'inta ya matso da ita jinkinsa sosai yana ji wani sirtaccen kamshi jikin Nisha ke bugu hancinsa wanda yasa lumshe idanu sai ya tsinci kansa da son kasan cewa tare da wannan daddad'an kamshin jikinta . " Na takuraki koh?". Ajmal ya tambaya yana binta da wani kallo Girgiza kai Nisha tashiga yi ,tsoro gaba daya ya da bai bai kunyar ta tashiga fito da idanu waje jin mazaunanta saman cinyarsa yana rike da waist d'inta gam. "A'a ba.,ka ta,.ku,.rani ba yan.,zu zanje na kawo maka". Nisha ta fad'i muryanta na carkewa tsabar tsoro, jiyo da ita Ajmal yayi suna fiskantar juna yana kallon tsoro da fargaban da ke saman face d'inta tana ta faman zaro idanu waje wanda yake bashi nishadi idan ya ganta wannan yanayin Ajmal hanu ya sanya ya zare mayafin saman kan Nisha wanda yasa jikin Nisha ya kama rawa. "Gashi kina turamin baki alamar na takuraki ". Ajmal yakuma fad'i cikin wata kasalalliyar murya yana bin dugon bakin sumanta wanda yake ta faman shaning yana walkiya saboda ingantaccen g'yara da ya sha sai zuba k'amshi ya ke dan matso da face d'insa yayi dab da ta Nisha numfashinsu na hadewa dana juna lips din Nisha ya suma motsawa tana kokarin bude baki da niyar yin magana kanakace mai sai ji tayi Ajmal ya cafke dan tsukekken pink lips d'inta wanda yayi sanyi k'alau ya sha lipstick ko ajikinsa ya suma sucking cikin wani gigicecen salo wanda yasa Nisha da ta fara kokarin kwace lips d'inta sai kuma ta koma ta nitsu tana amsan salonsa wanda take jinsa har k'ololuwan kanta zuwa tafin k'afafuwanta. Nisha wani irin yanayin ta tsinci kanta ciki wanda yasa takasa kwace kanta karo na farko da taji tsoronta ya kau sai tsintan kanta da sake masa jiki gamida lumshe idanu tana jin wani irin shauki na dibanta wanda tunda take bata taba jin irinshi ba . D'an bude idanu Ajmal yayi ya kai kwayar idanunsa ga Nisha wacce ta lumshe idanu ta nitsu sai faman sauke ajiyar zuciya take, mamaki ne ya kamashi ganin ko fitir fitir batayi irin alamun ba ta so dinnan but sai yaga akasin haka , Nisha jin ya tsaya da abunda yake yasa ta dan bude idanunta da suka suma canza launi suka hada ido da Ajmal wanda ya mata k'uri da idanu wanda yasa Nisha ta janye lips d'inta a kunyace ta sunnar da kai kasa gamida kokarin zamewa jikinsa a hankali tana fadi'n "Co,.ffee dinka zanje na kawo". Nisha ta ce cikin sanyi murya "Bana bukata". Ajmal ya fad'i yana hade gira still yana rike da ita bai sake taba dubanta Ajmal ya kumayi wacce tayi shiru ta sunnar da kai kasa ganin kallon da ya ke jifanta dashi da takasa ganewa kallon t,. 'tunda ba wani abu ya ke da buta ba mai sa ya tura ayi k'iranta' Nisha ta raya cikin ranta "How old are you ?".jin tambayar da Ajmal ya watso mata ne yasa ta dago a hanzarce ta dubeshi jin wani tambayar k'wak'wa kuma face d'insa ba alamar wasa ciki k'ank'an da kai Nisha ta kuma yi gamida bashi amsa da cewa "I'm 23 years". Jinjina kai Ajmal yayi gamida da dan tab'e baki ya koma ya jingina da sofa yana kallonta wacce ke zaune cinyarsa kai sunkuye 'She still young su Reeda ma sun girme mata ballai shi da ya ke Shirin haifanta idan da ace yayi auran wuri ' Ajmal ya raya cikin ransa a tunaninsa yayi mata girma sosai ko Heelah ba ya mata kallon babbar mace ballai wannan yar k'aramar alhakin da gaba daya ba ta wuce tafin hanunsa ba". " Ke yarinyar ce k'arama but mai kike tunanin zaki iya min a wannan kananun shekarun naki zaki iya daukana?" Ajmal ya tambaya duk da yasan ba wai zata fahimci ba tunsa bane sai kuwa ta bashi amsa da cewa. " A'a bazan iya ba ranan ma da k'yar na karisa da kai bedroom". Nisha ta fad'i tana girgiza kai gamida shagwabe baki ita ala dole da karfinta ta karisa dashi bedroom d'insa wacan lokacin, Saura kiris Ajmal ya tun tsire da dariya dama yasan ba lallai ta fahimci inda ya dosa ba "Ba wannan daukar na ke nufi ba let me show you". Nisha kanta ankara sai ji tayi Ajmal ya zuge mata zip din riga har kasa wanda yasa rigar ta bude gaba daya tana shirin zamewa cikin hanzari Nisha ta rungume jikinta cikin tsoro tana zare idanu tana bin Ajmal da kallon mamaki meye yake shirin yi . Idanunta ne suka kara fitowa waje sautin bugun zuciyarta ya karu sosai tsoro da fargaba suka baiyana saman face d'inta time din da Ajmal ya mikar da ita saman sofa gamida rike hannayenta biyu yayi mata runfa da jikinsa yana shinshinar wuyarta har izuwa hab'arta yana sauke wani ajiyar zuciya. "Please ka ji kaina Ammi ba ta san nazo ba please kabarni na tafi please .." hade bakinsu guri guda Ajmal yayi yasa ta hadiye sauran zancen nata ta shiga kukan zuci gamida dana sanin bin shawaran Baraka da batazo ba, gaba daya Ajmal ya k'ure mata lissafi canza ya canza mata lokaci guda ba ta taba tunanin zai na cewa jikintq haka ba ta dauka duk yanda yake kinta suran jikinta bazai bashi sha'awa ba but sai ta ga akasin haka maganar Salma yana kokarin ya zama gaskiya sai kana son abu zakayi sha'awar kasance wa da shi . Wani yar k'arami kara Nisha ta sake time din da Ajmal ya zura hanusa cikin rigarta ya matso Brest d'inta da karfi dan dama bawai ta sanya bra bane kasance war rigar ta d'an matseta sosai wanda idanta sanya bra zata takuraki shiyasa Ajmal ya samu saukin zira hannayensa yana mammatsawa jin laushi gamida taushi wanda yasa jikinsa wani sake tsuma nan da nan Ajmal ya soma rabata da rigar gaba daya saboda ya kare musu kallon da kyau. Nisha ganin zagewar tasa da yawa yake yana kokarin rabata da rigar jikinta hakan yasa ta shiga kiciniyar kwace kanta because numfashinta da k'yar take fisgoshi saboda tsoro dan da alamar ba wasa alamarin idan ba tayi tirjiyaba sai ayi cin amarcin a wannan lokacin duk da tasan ba ta da tsarkima dole duk aniyar da ya dauka ya sauke. "Wayyo Allah please ka kyaleni nata fi Ammi bata san nazo please ". Nisha ta fad'i tana ture shi , dama shi d'an kad'an yaso lugwigwaitata but sai ya samu kansa da zarcewa gaba daya . Nan Ajmal ya dan dagata a wahalce Nisha ta zamu kasa gamida mirginawa ta mike ta shiga g'yara zip din rigarta daga bisani ta janyo mayafinta ta daura saman kanta jikinta sai faman rawa yake direct Nisha ta nufi door ta bude k'ofar ta fice cikin sauri ko waiwaye babu . Ajmal yuuu haka ya dinga ji cikin kwanyar kansa idanunsa duk sun kad'u sun canza launi zuwa jaaa idanu ya lumshe gamida dafe kansa da hannayensa yana sauke wani wahalallen ajiyar zuciya ya jima yana zaune gurin na d'an wasu mintuna kafin ya mike a dafe ya suma haurawa upstairs ya nufi bedroom d'insa ...................... Washe gari jumma'a da misalin karfe 10:30 aka daura auran y'a'ya ga alh ABUBAKAR MODIBBO BATURE tare da angwayensu yan uwa da abokan arziki duk an hallara cikin farin ciki da kwanciyar hankali ba tare da tsawaita biki ko an jashi ba duk da so Doctor fu'ad sunso shirya kataccen dinner daran yau but fad'an Daddy bayaso aita wannan shagulgulan ana tsawaita biki g'wara ayi komai ya wuce gurin kowannesu ya dauki amaryansa ya k'ara gaba bayan . Haka ta ban garan Ajmal tunda Doctor fu'ad ya kawo zance dinner ya nuna mishi ba shi cikin wannan lissafin ko sun hada shi baza shi ba dan haka aka hakura baki d'aya. Ko bayan daurin auran Daddy ya hade gaba ki daya amaren cikin katafaran parlourn shi yayi musu fad'a gamida na siha mai jan hankali Ammi Hajia Goggo rabi ba wanda bai tufa albarkacin bakinsa ba kawaccensu jiki a sanyaye kai kasa suna amsar fad'a da na sihar da ake yi musu harda dan sharan k'walla kafin daga bisani aka sallamesu gamida shi musu albarka tare da fatan alkhari a zaman takewan su cikin rayuwar auransu..... Yammalis kyakykyawan motarci suka kashiga yin zarya cikin haraban gidan yan daukan amarya Fadeelah da kawayenta doctor fu'ad da abokansa , wayaga idanun Hajia k'arama ta shigaa zazzare idanu jin ita akazo dauka kankace mai ta haukace musu da kuka cikin gidan tana makalewa jikin su Nisha da Reeda tana fadi'n ita ta fasa auran ace su tafi sai dai ina bakin alkalami ya bushe . Suma su Nisha kuka suke kamar ba gobe zasu rabu da juna, gaba ki daya d'aki ya koma na jimami da alhini kawayensu fauzy Nabilah sai faman basu baki suke amma sun hada kai kamar kifin gwangwami suna kuka harsaida Goggo rabi da Aunty Hafsatu suka zo ka banbareta daga jikinsu cikin lallami da laluma kafin suka fice da ita sai da suka sa tayi sallama da Ammi gwanin tausayi Ammi itama kamar ta zub da k'walla idanunta duk sun ciko but sai ta matse saboda kwantar mata da hankali gamida bata kwarin gwiwa. Nan ma dai da k'yar aka zareta jikin Ammi daga nan ka fita da ita haraban gidan cikin lulubi sai faman shashsheka take suna bata baki, daga nan suka nufi da ita wata kyakykyawar motar wacce akayi musu alamar itace ta amarya aka kutsata ciki su Goggo rabi na biye da ita tare dasu fauzy da wad'ansu k'awayen nata da suka shiga wata motar da sauran yan uwa masu mata rakiya, Daga nan motarcin suka suma baya suna fita suka bar haraban gidan daga nan aka dauki hanyar gidan su doctor fu'ad inda za amika amanar amarya hanun iyayensa..... Da dare misalin karfe 8:30 time din Reeda da Nisha asa sun sake cin wata wankar cikin wani shirin suna zaune bakin bed kowannesu na juye tunani cikin ransa Nisha tun safiyar yau kamar mara lapia yau zata tare side din Ajmal fad'uwar gaba sai abinda ya karu idanunta har sun fito waje saboda tunani Salma na nanike Nisha har su Ammi suka shigo gamida Hajia suka kariso gurin Nisha suka kamu hanuta Ammi Na Fadi "Taso Yar nan". ta sauke mata mayafin Kanta ya rufe face dinta ruf Ammi ta kamu kannunta gamida janyota jiki suka fice Goggo Rabi da salma suka sufa Mata baya, hajja mama ta zauna da Reeda cikin bedroom din kasan cewar ita tariyarta sai gobe zasu wuce kaduna kasan cewar can aka mata jerenta. Nisha sai faman zare idanu take ta cikin mayafi kirjinta Ji take kamar zai buga aikin tsoro da fargaba, sai da suka kariso side din Ajmal dai dai bakin door Goggo Rabi ta tura door kafin Ammi ta ce "Yi addu'a kafin sanya kaf'af'unki". Gyada kai Nisha tayi duk tama rasa mai zata fara cewa addu'ar mai zatayi sai faman motsa baki take, Ammi karisawa da ita tsakiyar parlourn sukayi wanda parlour ya sha matukar gyara dan ubansu komai an canzashi sabo komai sai sheki yake yana yalk'i gawani kamshi da yake tashi namusamman. Ajmal Story and writing By Oum AmReesh❤️ https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=159698751105534&mibexti=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Book 3 Takun karshe Page 95 _______ Daya daga cikin bedroom din dake parlourn kasa inda kayiwa Nisha jeren kayan dakinta bedroom biyu bisa kasa duk kayanta ne ciki, nan aka shiga da Nisha ita kuwa tana biye da su duk inda akayi da ita nan takeyi haka salma itama na biye da su. Saman lallausan bed d'inta suka zaunar da ita jikin Nisha duk a sanyaye kanta kasa sai wasi wasi cikin zuciya, ruwan hawayen na tama neman su tayi tarasa duk sun kafe,. Ammi da Goggo rabi sai da suka taushe ta gamida na siha sosai kafin suka tafi suka barta tare da Salma Nisha najin fitarsu sai yaye mayafin face d'inta tayi gamida fadawa cinyar Salma ta fashe da kuka kasa kasa tana shashsheka sai yanzu kukan yazo mata. Lallashinta Salma tashiga yi kafin ta dago Nisha zaune tana kallon ta. " Please kidaina asaran hawayenki a banza because yaufa ranar ki ce kuma daren mafi daraja cikin rayuwar ki wanda ba zaki taba mancewa da shi ba" "Salma idan na ce Ina farin ciki da wannan ranar nayi karya Salma ji nake zuciyata kamar zata faso k'irjina ta fito" Nisha ta fad'i cikin kunar zuci "Please banaso kina fadin haka ki nitsu ki kwantar da hankali ki ki fiskanci rayuwar auranki, ki sauke duk wani nauyi da hakkin da Allah ya daura bisa kanki kibi mijin ki ki so abunda yakeso ko dake ba kyaso" . Salma ta fad'i tana dad'a tausan kafin Nisha ta kauntar da kai bisa shoulder d'in Salma tana sauke ajiyar zuciya gamida karewa kyalekyalen dakin yanda aka kawata komai cikin aminci sun dau tsawon lokaci suna zaune haka Salma na kwantar wa da Nisha hankali. Sallaman da suka jiyo can parlourn ne yada daga Nisha har sallama suka shiga zare idanu kafin Salma ta yi saurin jan mayafin Nisha ta rufe mata face tana fadi'n "G'yara ki kimtsa bari naje na duba". daga haka Salma ta g'yara mayafinta itama ta fice ta nufi parlourn , kamal ta gani cikin manyan kaya ya sha kyau kaikace angone da kanshi tare da Muhaiseen wanda ya sha ado shima suna tsaye tsakiyar parlour hannayensu dauke da manya manyan ledar suka ajiye bisa saman table din parlourn. "Aww ashe angwayene da kansu". Salma ta fad'i tana washe baki dariya su Kamal su kayi kafin Kamal ya ce "Sorry karmu dameku da yawa sako muka kawo but zamu rage wa amarya jin dadi mutumin fa yana jiranki a waje ya kira phone din bakiyi picking ba ". "Okay Amma banaso na tafi na bar Nisha ita kadai gaskiya gashi dare yayi sosai ni da farima shigowar ku nayi zatun tare kuke da shi angon nata". "Oh karki damu baiyi nisa ba yanzu saizo ke dai kiyi sauri karki bata masa lokaci" Kamal ya fad'i "To shikenan bari nayi mata sallama saina fito" daga haka Salma ta juya ta koma bedroom din cikin hanzari daga bisani suma su Kamal suka sa kai suka fice . Koda ta koma yanda ta bar Nisha haka tadawo ta taddata handbag d'inta Salma ta dauka ta rataya bisa shoulder d'inta Tana fadi'n "To ni zan wuce MB na jirana sai mun yi waya". Salma ta fad'i tana kallon Nisha "Wayene ya shigo". Nisha ta tambaya cikin sanyin murya. "Oh Kamal ne suka shigo da sakko da alamun angonki yana hanya shima kinga ni kuma ya kamata na tafi kar na hana ruwa gudu " . Salma ta fad'i cikin tsokana ga mamakinta caraf Nisha ta rike hannayenta gamida mikewa tsaye tana bude mayafinta tayi raurau da idanu tana shirin kuka "Please ni tsoro nake ji karki tafi ki barni",. Nisha ta fad'i tana karewa kata faran d'akin kallo, murmushi Salma tayi jin abinda Nisha ke cewa tana zare idanu "Karki bani kunya mana tsoron meye kuma shima angon naki yanzu zai kariso na tabbatar duk yanda yake yanzu yana kan hanya karki sawa kanki wani damuwa". Salma na fadi'n haka ta maida ta ta zaunar da ita tana kuma fadi'n "Sai da safe sai munyi waya". Nisha ba ta iya ce da ita k'ala ba haka tabita da rakiyar ido harta fice daga bedroom din daga nan Nisha ta kwanta bakin bed din gamida ta kure kamar mai jin sanyin........ Ta ban garan Heelah duniya gaba ki daya yayi mata zafin ta kaici goma da ashirin idanunta duk sun fito waje tayi bala'in rama da fari sam zuciyarta taki gamsuwa da abunda yake faruwa auran Ajmal da Nisha ji tayi kamar a mafarki gashi yanzu anyi mai kankat Nisha ta tare d'akin Ajmal ma tsayin kishiyarta because tun fara shagulgulan bikin tamkar akan idanunta ake kasance war ba abunda ba ta gani ba ko bata ji labari ba yanda shagulgulan bikin suka kasan ce saboda bikin nasu ba inda bai tasa ba duniya ta dauka ta ko Ina. Wani kuka Heelah ta saki mai sauti cikin ta kaici tunanin ta Nisha na can tare da mijinta ,Aheel na daga gefe kwance yana bacci , mom ne ta turo door ta shigo cikin bedroom din ta taddata ita cikin wannan halin wanda yasa mom saurin karisowa saman bed din kusa da ita ta zauna cikin damuwa da halinda ta ganta ciki " Haba Heelah mai kikeyi Haka ni na zatama baccin naki yayi nisa amma sai na zo na taddata kin tusa yaro a gaba kina kuka salon ki katse masa bacci komai?". "Mom bazan iya bacci ba wallahi wacce yarinyar tana can suna cin amanata wallahi ba zan bar yarinyar nan ba tunda kin kasa daukan mata kanta ni da Kaina zan dau mataki wallahi zamanta bazai daure gidanan ba ". "Da Allah rufe min baki ce miki nayi na kasa daukan mataki kanta komai ai yanzu labarin ya suma yanzun ta shiga gonarki yanda hukuntata ya zama wajibi". " hmm ke dai ki sha kurumin ki , ki daina d'aga akwatin hankalinki karkije ki sawa kanki wani ciyon tun da nace kibar komai hanuna sai ki zubamin ido kawai ta shigo hanu ai .," "Kwanta ki hutawa ranki, ki kwantar da hankali kamar kinyi pillow da gawa da duk kinbi ki daga hankali kin fita hankali da tunanin ki akan wata can yar guda d'aya wacce bata wuce attishawar tsaki ba ". Mom ta fad'i cikin lallashi da laluma tana g'yara Mata kwanciya kamar wata yarinyar ta rufe ta kirif daga nan ta mike zata fice, cikin raunin murya Heelah tace "Mom gobe zan koma d'akina bazan cigaba da zama anan ba ". "Uhm da dai kin d'an kara murmurewa ki karajin karfin jikin ki bakiga yanda kika fita kamanninki bane?" "Nidai k'alau nake na samu sauki gobe zantafi ". Heelah ta fad'i cikin kosawa , ganin yanda Heelah ta kafe yasa mom ta amsa mata da cewa "To shikenan Allah ya kaimu goben". Daga haka Mom ta fice gamaida rufo mata kofa damuwa da takai ci gurin ta itama ba a magana..... Guraren 11 Ajmal ya turo door din parlourn ya shigo yana sanye cikin kyakykyawar shiri mai kyau da jan hankali manyan kayane jikin sa ruwan zuma hade da babban gare wanda ya sha ingantaccen aiki ya fito tas cikin shirin mayan mutane yayi kyau matuka kamar ka sa ce shi ka gudu . Face d'insa ba yabo ba fallasa ya karisa shigowa tsakiyar parlourn sai faman wulwulga idanu yake gamida kai kallonsa door din Nisha sai kuma ya kau da kai direct ya nufi bedroom d'insa . Yana shiga ya sanya hanu ya cire hular saman kansa ya cilla gefe daga bisani ya zare babban rigar sai da ya raba jikinsa da manyan kayan jikinsa ya rage da gashi sai short kafin ya zauna saman sofa yana mai da ajiyar zuciya gaba ki daya yau yayi ba la'in gajia gurin partyn da suka gabatar yau da daren tsakanin angwaye da friends d'insu hayaniyar mutane duk ya sanyashi ciyon kai . Wani dugun ajiyar zuciya ya saki gamida mikewa tsaye yanufi bathroom ya wanke jikinsa gamida tsaftace jikinsa kafin ya fito shirya cikin kayan baccin sa riga da wando mai matukar laushi da taushi daga nan ya ya haye saman bed d'insa ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya. Yau ko takan coffee bai bi ba kasan cewar cikinsa tam yake sunyi ciye ciye gurin wani abun ma da da son ransa ya shiga cikinsa ba duk doctor fu'ad ne ke tura masa kafin yayi wani yun kurin ya tusa masa bakinsa............. Nisha jiki ba kwari ta mike daga kwanciyar da tayi dan har wani gajeren bacci tayi na wahala da tsoro idanunta duk sun shige ciki kanta kuwa kamar wanda aka daura mata wani abu bisa kai saboda yanda ya mata nauyi mikewa tayi ta sakko daga saman bed din ta nufi bathroom ta wanko face d'inta ta dawo bakin bed din tayi shiru tana karewa bedroom din kallo da tunanin shirun da taji Ajmal ba shigo ba duk ta takura a matukar tsorace take. Phone din ta ta janyo 11 ma ta wuce idanunta ne ya ciko da k'wallah tab sai faman kallon door take tana jiran tsammanin shigowar shi but shiru kamar anshuka dusa hakan yasa ta g'yara mayafin saman kanta tamike asukwane ta fice daga bedroom din ta nufi parlourn. Ko da tazo tsakiyar parlourn ba kowa shiru parlourn sai manyan ledar da ta gani an ajiye bisa saman table din hakan ya sa tayi tunanin Ajmal ya shigo da su Upstairs din ta bi da kallo da tunanin ta Ajmal ya dawo but bai yi tunin ya dubata ko ya waiwaye ta ba sofa ta nema ta dan d'ofana ta k'urawa guri guda ido tana tunani .. Allah yasa bawani babin wula kacin zai bude mata ba kasan cewar dawowar ta tsaginsa saboda a tunaninta ganin cewar ya tatare dakinsa but ba iya biyowa ta kanta ya duba ta ballai yasan mai take ciki, zare mayafin saman kanta tayi ta janyo ledar take kallah ta shiga dubawa , abubuwan da ake kawo duk wata amarya ce a ciki abubuwan ciye ciye barkate gasunan hanu ta sa ta ja goran yughourt ta bude ta kafa bakinta ba tare da wani ta raddadiba ta suma shaa because yunwa take ji sosai rabonta da abincin zata iya cewa tun safe shima cin sama sama ne. Sai da ta sha ya kusa rabi kafin ta sauke tana ajiyar zuciya gamida komawa tayi lamo jikin sofa ta k'udundune jiki tana wulga yan idanu Nisha yanda taga rana haka ta ga dare sam ta kasa tsugul ta kasa nitsuwa ga tsoro da take ji ita kadai parlourn shiru ga kuma ta kaicin rashin k'arama wannan dare da Ajmal baiye ba yayi mata banza ko in kula kamar baisan da zaman taba ya kasa fitowa ya dubata halinda take ciki. Haka Nisha ta dinga g'yang'yad'awa gurin tana farkawa a haka har bacci barawo ya sace ta gurin kwance, da suba k'iraye k'iraye sallah a kan kunne Ajmal ya sauka wanda ya sanya shi bude idanu gamida salatin annabi yana mika yana sauke duguwar hamma. A kasalance Ajmal ya yaye blanket din da yake lullube ciki ya zaro santala santala kyakykyawan fararen k'afafuwansa ya zamo daga saman bed din ya nufi bathroom ya wanko bakinsa gamida yin alwala ya fito ya sanya fara jallabiyar sa yanufi hanyar fita . Koda ya nufo downstairs ya iso tsakiyar parlourn sai Nisha ya kalla kwance saman sofa bacci yayi nisa tana sanye cikin adonta na amare ga mayafinta gefe yana lilo dan kallabin kantama ya bar saman kanta. lumshe idanu Ajmal yayi jin wani abi da ya tsikare zuciyarsa gaba daya sai yaji ba dad'i ganinta haka shi kansa yasan bai mata adalci ba but ba yanda zayi because jiya ya tsinci kansa cikin gajiyar sosai da bai taba jin irin ta ba ta wannan ban garen . Karisawa yayi har sofan da Nisha ke kwance yasa hanu ya sunkuce ta daga ita har mayafin nata wannan karon baccin Nisha yayi nisa don ko jin Ajmal ya daga ta ba tayi ba. Cikin bedroom d'inta Ajmal ya mai Nisha ya nufi bed da ita ya suma k'okarin kwantar da ita but sai ji yayi tsam Nisha ta rike hanunsa bisa k'irjinta ta run gume "Uhm please karka tafi kabarni, bana son kasake nisa dani na yi kewarka sosai". Nisha ta fad'i cikin muryan bacci tana sake shigewa jikinsa, Ajmal mamaki ya ishe sa yaushe daren ma yayi ba lallai gari yawaye ko mai take fad'i haka nan Ajmal ya sake janye jiki gamida jan hanunsa dan karfi yayi baya yana kallonta. Ita kuwa jin yanda ya janye yasa ta dan bude idanu ta ware su bisa face d'in Ajmal wanda ke tsaye yana binta da wani kallo cikin mamaki duk da yasan ba cikin hankalinta take wannan sun batun ba sake waru idanu tayi ganin Ajmal tsaye bisa kanta yasa ta mike daga kwanciyar tana zare idanu gamida kallon d'akin da tunanin yanda tasamu kanta ciki tunda tasan dai ba anan ta kwanta ba but ganin Ajmal cikin bedroom din shi ya bata amsan tambayar ta. Dan tura baki Nisha tayi gamida juya baya ba tare da sake kallon Ajmal wanda yake tsaye ba because haushinsa ne tab cikin zuciyarta saboda halin rashin ko in kula da ya nuna mata jiya time din da aka kawota ko lekata bai yi ba , yanzu harda dauko ta ya maido ta bedroom ko waya akesa oho Nisha sai tura baki take tana sumbatu. Shi kuwa Ajmal ko takan yanayin da take bai bi ba sai sake kallon Nisha yayi wacce ta juya masa baya yana fadi'n Asuba tayi ki kije kiyi alwala ki daura niyar yin sallah kafin Ajmal ya kai ga karisa maganar sai tsintar muryar Nisha yayi da cewa "Bana yi " . yanda ta bashi amsa a fisgene ba tare da kuma ta jiyo ta kalleshi ba yasa Ajmal suma lalub'o face d'inta dan ya tabbatar da itace mai ba da amsar ko dai yar yanzu cikin yanayin baccin take . "Mai kike nufi?". Ajmal ya tambaya yana hade gira ganin cewa cikin hankalinta take infact ma idanuta a bude suke , jin wata tambaya da ya kumayi yasa Nisha ta jiyu rigigine face d'inta na kallon celling tana fadi'n "Eh fashi nake ina period". ta bashi amsa ba tare da takalli sun hada ido ba, Ajmal bai iya ce da ita komai ba jin yanda take bashi amsa tana wani ya mutsa gamida tura baki yasa yayi tunanin ba sense d'inta take ba shiyasa take bashi amsa gaba gid'i . Ajmal yasa kai yayi yafi ce daga nan ya fito ya fice yanufi masallaci cikin hanzari because har yana shirin makara anshiga, ta ban garan Nisha ita kanta mamakin kanta ta karfin gwiwa wajan tsintan kanta dayi masa rashin kunya wanjan bashi amsa but Allah haushinsa ne fal cikin zuciyarta duk da tasan kad'anne daga halayensa bai kamata ta daurawa kanta damuwar hakan ba especially da tasan kallon jeka nayi ka yake wa auran.