*SON KI NE ƘADDARTA* ʂƚσɾყ&ɯɾιƚιɳɠ Ⴆყ Fateemah Abdullahi /Ⴆαƚσσʅ ƙαɱႦα/ *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•· _______ Wannan Labarin ƙagaggen labari ne. Wanda duk yaga ya yi dai dai da rayuwarsa ya yi hakuri a kasi Marubuciyar ta samu Please. Sadau karwa ga mahai fiyata Allah ya Kara tsawon rai my wold Gajeren labari No editing kuyi male ji *Page 1&2* *بسم الله الرحمن الرحيم* Niamey, Niger. Babban gida ne mai ɗauke da manyan Bedroom's. Ba kowa a tsakar gidan kasancewar safiya ce kuma ana iskan hunturu sosai. Wata matashiyar Budurwa ce zaune daga gefan pampo, ga wani uban tarin wanke wanke daga gefenta, gyan-gyaɗi take yi. Da ka gan ta kasan baccin wahala ne take. Duba da yanda fuskar take yamutse, babu alamar walwala. Wata Ƴar Dattijuwa wacce ta fito daga cikin wani ɗaki. Butar dake tsakar gidan ta ɗauka da alama banɗaki zata shiga, wucewa tayi ta gaban Budurwar sam bata ma lura da ita ba, har ta fito zata sake gifta wa, sannan ne ta lura da mutum a wurin. Kiran sunanta ta fara yi cikin mamaki "Maryam.! Maryam..." A hankali ta fara buɗe manyan fararren idanun ta, ta sauke su kan Dattijuwar. "Maryam ki tashi, kin san duk mutanen gidan nan suka fito baki kammala aikin nan ba, tabbas kin san menene zai biyo baya." Da sauri ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin dai-daita tsayuwar ta kasancewar tana jin jiri sosai. Cikin tautsayi Dattijuwar ta kalle ta tana faɗin "Hala dai baki ci abinci bane ko?." Gya ɗa ma ta kai ta yi alamar "E," girgiza kai ta yi cikin jin wani sabon tautsayin Maryam sannan ta ce "Ki kammala aikin kizo ɗakina ki ci abincin kin ji." Nan ma gyaɗa kai ta yi ta fara ƙoƙarin fara wanke wanken cikin ƙarfin hali, sai da ta kammala ba wanda ya sake fitowa, hakan ya ma ta daɗi sosai, da hanzari ta nufi Ɗakin Dattijuwar. Bata kai ga ƙara sawa ba ta ji wata murya mai amo da rikita duk wani bakon da bai saba jinta ba, duk da ta saba jin muryar hakan bai hana wani tsoro game da tashin hankali shigar ta ba "Ina zaki je?." Wata mata da ta fito ɗaya daga cikin ɗakunan ta tambaya tana mai kafe tada ƙananan idanun ta "Am dama iya ce taki rani Shshh..." Wani ban zan kallo tayi ma ta. Bata bari ta ƙarasa ba, ta katse ta da cewa "Uwar me zata miki?." Shiru tayi hadi da sadda kan ta kasa, wata tsawar ta sake daka ma ta "Ba tambayar ki nake ba?." Cikin rawar jiki ta fara magana, hankalin ta idan ya yi dubu ya tashi. "Yi hakuri Mamma, Allah wallahi yunwa nake ji zan je ne na ci abinci ne, Ƴan hanjina kamar zasu fito waje." Kallon baki da hankali tayi ma ta sannan cikin kumbar baki take faɗin "Dan uwarki wa zai miki sharar da sauran ayyukan?." "Zan yi, Insha Allah, wallahi yunwa nake ji sosai." "Idan kin kammala aikin sai ki je, muddun baki kammala ba, kika shiga wani Ɗaki a gidan nan billahil azim sai na lahira ya fiki jin daɗi..." Tana kai nan a zancen ta ta koma ɗakinta. Fuuu kamar zata tashi sama tsaban bala'i. Da shigar ta Ɗakin ta fara tashin ƴaƴanta dake nannade cikin bargo, ta shin su ta fara yi kasancewar ko sallar asuba ba wanda ya yi a cikinsu kuma tana sane da hakan. "Lafiya dai Mamma?." "Lafiya Qlau ku tashi magana zamu yi, waccen matar tana son ta ɓata mana shiri." "Kamar ya?. Wai kina nufin Iya ko. Hum hum dama nasan wannan munafukar tsohuwar ita zata kawo mana cikass a tsarin mu wallahi." Cewar ɗaya daga cikin Ƴan matan, a masifance. "Ni yanzu bama wannan ba, ku tashi bana son Papan ku ya same ta ita ɗaya tana aiki. Sannan Bance ku taya ta ba, amma ku fita wajen da kun ji alamar shigowar sa ku fara wani abin ta yadda zai dauka tare kuke yin aikin." Kallon kallon suka shiga yi a tsakanin su Ƴan matan "Kursiya ki tashi ni dai Allah ya san ba inda zanje wallahi." Wadda aka kira da Kursiya cike da bala'i take cewa "Ni ma babu inda zanje, cikin wannan iskar haba dan Allah." "Kuyi hakuri Ƴan albarka ku je kar ku ja min masifar Papan ku." Cike da rashin kunya da tsaban ji da tashen balaga, suka mimmiƙe suna zuzzunɓura baki suka yi wajen. Koda suka fita har ta kammala shara ta fara ɗiban ruwa tana zubawa a manyan robobin C̆̈ŏ̈m̆̈m̆̈ĕ̈n̆̈t̆̈😇☆☆M̆̈ŏ̈r̆̈ĕ̈ T̆̈y̆̈p̆̈ĭ̈n̆̈ğ̈📲 ✍️αʅƙαʅαɱι ყαϝι ƚαƙσϝι🤙 *SON KI NE ƘADDARTA* ʂƚσɾყ&ɯɾιƚιɳɠ Ⴆყ Fateemah Abdullahi /Ⴆαƚσσʅ ƙαɱႦα/ *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·• *Page 3️⃣&4️⃣* ________________________✍️ Kallonta iya tayi tana mai faɗin "Kiyi haƙuri Maryam Papan ku yana iya ƙoƙarin sa, amma haryau shiru kakeji Allah yasani ina tausaya miki sosai, domin wannan matar batada tausayi ko kaɗan, kanta kawai tasani sai kuma yaranta." Share kwallar idanunta tayi. "Iya ban san menene yake damuna ba. haryau nakasa sanin ni wacece?. Wai dama mutum yakan manta ko shi waye?. A'ina ya fito?, suwaye danginsa? Hatta mahaifiyata nakasa tunawa fa." Ta ƙarasa maganar tana mai sake fashewa dawani sabon kuka mai cike da ƙunar zuciya. *Abuja, Nigeria* Zaune yake a gaban Dressing Mirror yazu bawa wani katafaren zane da akayi na Art kyawawan idanun sa. Kallon zanen yake yi yana zubar da zafafan kwalla, magana yake tamkar wani zautacce. "A'ina kike ne?, me yasa kika min hakan, Shinko kin san wani kalar raɗaɗi nake fama dashi a silar rashin ki?, Me yasa biki yi tunanin irin halin da zan shiga ba, a dalilin rashin ki?..." Kai duba na nayi kan fuskarsa kyakkyawan Namiji mai cikar kamala da kwar jini ma abucin kyawun fata dana fuska, fuskar tasa zagaye da siririn gemu irin na gayun wannan zamanin. Duk da cewar a zaune yake hakan bai hanani gano tsayin da Allah ya hore masa yana da tsayi dai dai misali, ƙara duban sa nayi sai yanzu nagano wai ashe yanada tabon sallah ago shin sa. Yanda yake magana zaka ɗauka tare yake da wani ko wata a Bedroom ɗin, duba da yanda yake kallon gefe ɗaya. Turo ƙofar akayi tare da sallama, ko motsawa bai yi ba yadai amsa sallamar sanin muhimmancin ta. Macece matashiyar tsohuwa mai ki manin shekaru Arba'in a duniya. Kallonsa ta tsaya yi nawasu Ƴan mintuna sanna ta ƙaraso kusa dashi, dafa kafaɗar sa tayi. hakan yasa ya juyo ya kalle ta bata ce masa komai ba ta fara share masa hawayen fuskarsa. Har ta kammala bai yi magana ba. cikin muryar rarrashi ta fara magana. "Marwan kayi haƙuri mana kaza ma Namiji mai juriya mana. Tabbas na sa ni abin da ciyo, amma ya zamuyi da hukuncin Allah?. Insha Allah za'a ganta kaji, nan bada jimawa ba. Kasan Doctor yace 'Ka ra ge tunane tunane sosai, Please karka ja mana ciwon ka yatashi zamu wahaltu sosai." Kallon mahaifiyar tasa ya yi cikin karayar zuciya Yake faɗin "Momy juriya fa kika ce?, Zan iya juriyar komai a duniya tabbas, banda rashin ta. Bazan iya jurewa ba. Haƙuri Momy taya zan yi haƙuri?, Zuciyata ba za ta ɗauka ba ji nake kamar zan yi hauka Momy. Please Momy ki gaya min inda ake cire soyayya, naje a cire min soyayyar ta daga zuciyata, wata ƙila zan samu sassaucin abin da na ke ji.." jin yadda yake magana yasa Momyn fashewa da kuka ita ma cikin tausayawa ta ce "Haba Marwan dan Allah kayi shiru mana kasan baka da wata isasshiyar lafiya, so kake ciyon ka ya tashi ne?." Cikin zubta kwalla mai zafi ya girgiza kai "A'a Momy nakasa jure wane kawai." "Kayi hakuri Marwan taka kalar ƙaddarar ke nan." Rarrashin sa ta ci gaba dayi har tasa mu ta shawo kansa ya daina kukan da suru tanda yake yi, ta fita ranta na mata suya. Kasan cewar Ranar Friday ne yasa shi miƙewa yanufi toilet. A kalla yashafe one hour kafin ya fito ɗaure da towel. A wurin da ya tashi a nan ya koma zauna, nan ya fara shafe jikin sa da Body Lotion na maza masu matuƙar tsada da ƙamshi dama shiɗin ma'abocin ƙamshi ne, yakai kusan twenty minute's yana abu ɗaya kafin ya miƙe ya nufi zuwa Closet ɗin sa yaciro wata arniyar Shadda Golding color. Kama daga Takalman ƙafafunsa A gogonsa, Hularsa duk Golding color's ne.. Sai da ya kammala feshe jikinsa da daɗa-ɗan Turare masu ƙamshi, sannan ya kalli kansa a Mirror idanun sa suka ciko da kwallar baƙin ciki, duk lokacin da ya yi shirin fita wani wajen sai ya tunata ita wato Tauraruwarsa. Saurin kawarda tunanin ya yi ganin zai makara. Farfajiyar gidan ya fito gidane ƙaton gaske mai ɗauke da manyan part guda huɗu, gidan zagaye yake da flowers masu ƙamshi da sanyaya rai. Securities suna hangosa suka ta so da han zari dama all ready a shirye suke. Buɗe masa motar ɗaya daga cikin securities ɗin ya yi yana mai ƙamewa alamar girmamawa. M̆̈ŏ̈r̆̈ĕ̈ C̆̈ŏ̈m̆̈m̆̈ĕ̈n̆̈t̆̈😇☆☆M̆̈ŏ̈r̆̈ĕ̈ T̆̈y̆̈p̆̈ĭ̈n̆̈ğ̈📲 αʅƙαʅαɱι ყαϝι ƚαƙσbi Following up to my channel 👇 https://whatsapp.com/channel/0029Vb7UctgDOQIUVRtDaM22 https://chat.whatsapp.com/Gn6wOkxz4N6KBN3JbMkPiZ?mode=ems_copy_c *SON KI NE ƘADDARA TA* Your love is My distiny STORY & WRITING BY FATIMA ABDULLAHI Batool kamba *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·• This book by dedicated to my mom love you so much _________________________________________________ *5️⃣&6️⃣ ____________________✍️Buɗe masa ƙofa ɗaya daga cikin security ɗin yayi yana mai ƙamewa alamar gir mamawa, haka suma sauran suka ƙame tare dasara masa sanna suka shiga sauran motoci nandanan suka bawa mitocin wuta kasan ce war yau sun soma makara yasa muka fara gudu, kallon driver yayi cikin rashin son yin magana yace karage gudunnan acikin gari muke." "Cikin gir mamawa drivar ya sassauta gudun motar." "Koda suka ƙarasa malallaci baifi min tuna talatin daya sauraba atayarda Sallah." "Bayan sun kammala Sallah, su biyo hanya daniyar komawa gida,i da nunsa alumshe suke,yace "muje JRA " Yes sir drivar yafaɗa haɗi da ɗaukan waya yakira sauran securiti's da ke gaban su ya shai da musu inda zasuje " "Bakin wani ma dai²cin gida sukayi perking kasan cewar motocin bazasu shige gidan gaba dayaba dasauri security's suka fito suka zagaye motar dayake ciki cikin isah dataƙama yafito daga motar kai taye yanufi ƙofarda zata sada shi da gida noking ya yi gate man ɗin datun farkon tsa yuwar su aƙofar kidan yaji ya yi saurin buɗe ƙofar . Saida suka gaisa da gate man ɗin yashi ga ciki " "Kai tsaye falon gidan ya wuce nan yatarar da matar gidan tana ganin sa ta fara washe baki "A'a yau munada man yan baƙi marwan zuwan ka kenan." Saidaya zauna yafara magana "Bar kan muda juma'a mama ,munsa meku lafiya? " Lafiya ƙalau marwan ya mom ɗin ? "Tana lpy , tace ma na gaisheku amsa" Sanin ba wani abu zai sake cewaba yasatace Haladai kanyi ban hannu da abokin naka? Shima yacemin zaize gaida mom inya tashi daga Masallaci. "A'a nazo gai ashe kune kawai " Har ranta taji daɗi nan tashiga kiran mai aikinta. Haule! Haule! Amsawatayi na'am hajiya ina zuwa. Kika wowa marwan ruwa tafada bayan ta fito,dato ta amsa saurin dakatar da ita ya yi . "A'a mama zan wuce gidane yanzun" A'a daga zuwanka? "E"akwai abinda zan yine" To badamuwa kagai sar minda mom ɗin "Ok"kawai yace yamiƙe yafice security's naganinsa suka buɗe motar kai tsaye yashige amai makon su je gida sai cewa yayi akaishi wani hadadde rastuarent Kasan cewar sunsan wane restaurant yake nufi yasa suka nufi hanyarda zata kai su can ɗin Tafiyar 20 minute sukayi saigasu gaban wani ƙaton retuarent sukayi parking. Bai fitoba kuma baiyi maga naba amma securiti's duk sun fito sun zagaye motar, wata kata shiyar mataca tafuto daga retuarent ɗin da alama itace mamalla kiyar wajen Sanin ko ita wacece baisa securiti's sunbata damar isa inda yakeba ya tsun ya biyu yahaɗa suka bada wani sautin ɗas ɗas, a lamar subarta taƙaraso dasauri suka bata hanya . Gai sawa suka farayi sannan tace yalla ɓai meza akawo " ? Shiru yayi nawasu mituna Kafin yace "snacks and shawarma ok" Dato ta amsa tayi ciki bata wani ji maba tafito da leda , umar tar securiti's yayi da ya kar ɓo ledar' tacƙe away ɗin Cikin han zari ya isa wajen ya amshi ledar tareda bata kudin ,yajuya sukafara shiga motar. Kaitsa ye suka dau hanyar gida kasan cewar s state ɗin su ba yada suna yasa ba bazan iya tannan cemukuba suna isa ƙofar gidan ɗayan security dake gefen drivar yadanna wani remot nan take gare ɗin yabuɗe dakansa baima bari an kammala pakin ba yaɓalle murfin motar yafito Ganin haka yasa securiti's sukayi luf amota ,sanin inyayi hakan me yake nufi ledar dama tana gefen sa ɗauka yayi yashi ga wani part saɓanin wanda yafito ɗazun wanda nake kyau tata zaton nasane . Da sallama yashiga "Assalamu Alaikum" Wani matashin saurayi ne ya amsa masa sallamar Ameen Wa'alai Kassalam Cikin shakiyanci yake kallon sa Marwan wanna cin wankan duk na juma'a ne koka samu wata santa leli yarne Kallon bakada han kali yayi masa kafinyace "Jamil banason iskanci ba san ta leliya nasamuba zuƙekiya nasamu yaƙarasa maganar cikin jin haushi'' To kace kasa mu zu ƙekiyar kenan ,Shiyasanaga dukka sauya. Ganin Jamil zaimai dashi mahaukaci yasa yayi han yarda zata sada shi da bedroom ɗin mom Mom na kichin Jamil yafaɗa yana ƙunshe dariyarsa. Baice masa ƙalaba yanufi kichin ɗin tunkan ya ƙarasa yaji ƙamshin gir kin lumshe idanu yayi yanajin wata sabuwar yun wa "Assalamu Alaikum'' Yayi sallama tare dakutsa kai cikin kichin ɗin wani daddaɗan ƙanshine yadaki hancinsa mom dake juya.miyardake kan gas tajuyo tareda amsa masa sallamar ganin leda hannun sa yasata kallesa da mamaki '' son wai bakadaina zuwa restuarent ba? kuma ai nahada ma shawarma da snacks da kaina. Kallon tayayi da lumsassun kuma shan yayyun idanunsa yace ''sorry mom'' '' bansan zaki yiminba daban biya retuarent nayi thack away" shi kenan Allah ya kyauta dadyn ka fayakusa dawowa Nigeria "Allah yakawo sa lpy" 'Ameen mom ta amsa ' Komawa parlou yayi bayan yabarwa mom ledar thank away ɗin da yayi Jamil yakalleshi yace ina ledar Banza yayi masa Au zuƙe kiyar budurwar kace tabaka shine kake min rowa "Dan Allah ka kyaleni naji da abinda ke damuna haba" Tausayin sane yakama jamil yamatso kusa dashi, Please marwan karage damuwa kasan yanayi ciyon ka bayason tunani. Nan Jamil yayi tabashi baki danuna masa haka kalar ƙaddarar sa take Saida yatabbata yarage damuwa 70% sannan suka cigabada hira har mom takawo musu abinci sukaci suna ɗan taɓa hira. Bayan sun kammala sukanufi part ɗin marwan tundaga parlou ya fara rage kayan jikinsa, murmushi Jamil yayi kasan dai niba bawan ka bane bale ɗau kema kaya "To wayace ka ɗau kemai nace ina sone,kar ka gayawa mutane magana malam " nandai Jamil yaci gaba da tso kanarsa. *Neimey Niger* Kwance take kan wata yamu tsats tsiyat tabarma, yau tun safe take jin cikin ta na ciyo dakyar ta gama aiyu kanda tasaba juyi kawai take jin an yaye labule yasa ta ɗago dakyar ta kalli ƙofar sadiya ce riƙe da ƙugu tana tau nar cingam. Kizo papa na kiranki tafaɗa awula ƙance kamar taga kashi dakyar tamiƙe tafita, kaitsaye dakin Papan taje yanazaune bakin bad ɗinsa,yanaganinta yace Maryamu inah Isah .... F 🌹A🌹k {🖤Batool kamba 🖤} More comments more typing 📲 https://chat.whatsapp.com/Gn6wOkxz4N6KBN3JbMkPiZ?mode=ems_copy_c *SON KI NE ƘADDARA TA* 🌹Your love is my destiny 🌹 STORY & WRITING BY FATIMA ABDULLAHI {Batool kamba Wannan littafin sadaukarwane ga mahaifiyata, Allah yaƙara inasan kwana dalafiya mai amfani, love You so much * Page 7️⃣➡️8️⃣ ____________________________✍️Yana ganinta fara Murmushi, ''maryamu innah Isah, zonan kusadani'' ahankali tataka har inda yake yaɗanjima yafara magana kamar haka. 'Maryam tafiyata kama ni, kuma banjin zan dawo nankusa kiyi haƙuri da duk abinda Mamman kuza tayi miki, kizama mai juriya da jajir cewa arayuwar zaman duniya' Saida yayi mata nasiha mai ratsa jiki Sannan yabata kuɗi sukayi sallama takoma ɗakinta Kwana biyu tsakani iya ma tayi tafiya sakamakon rasuwarda akayi musu Rayuwa taƙara yiwa Maryam zafi Don tun ranarda iya tabar gidan Maryam tarasa abinci batada rabo ko andafa, Wanisabon mugunta da mamma tatsiro dashi kullum sai Maryam taje habu bene aƙafa tundaga banda bari har habu bene kullum aƙafa take zuwa Yauma kamar kullum kwance take aɗaki gayunwa,gaciyo abiyu ke cita Mamma ce taleƙo ko sallama batayi ba tayaye labulen tafara masifa Maryam najinta amma takasa magana ganin komotsi batayiba yasa mamma harzuƙa tashigo dakin Kallon maryam tayi taga idanunta biyu aikunwu tasake fusata nantake tahau jibgarta kamar kayan wanki Allah sarki dukda irin dukanda mamma keyimata hakan baisa yayi wanimotsin kirkiba Mamman batausayi batadaina fukantaba, Tanadukanne tamkae wadda tasamu wani ƙaton gardi Tsabar rashin imani batamasan Maryam ɗin asume takeba saidatagaji dankanta takalli fuskarta taga komotsi batayi hakan baiwani razanataba, tanemo ruwa masu azabar sanyi tasheƙamata,wata wawuyar ajiyar zuciya tayi tama kasa kuka sai numfashi take saukewa nawahala cikin rashin imani Mamman tace wallahi 'inbakitashi kinyomin aikenaba sainakasheki kowaya huta ganta lalliyar banza munafuka tamba ɗaɗɗiya' Duk abinda tafaɗa maryam najinta amma takasa koda motsa yatsarta Kukanma ta gaza tarasa wanna wace iriyar rayuwatake marar ƴanci dagalihu ''Ya Allah kazamo gatana, kajiɓanci lamarina, Allah kasassautamin wannan jarabawar, katallafamin '' sai asannan tasamu wasu zafafan hawaye sukasulalo tagefen kuncenta kasancewar Mamman tabarɗakin yasa taƙarfafa jikinta tafara rarrafe ɗakyar taƙarasa waje gana mazko ɗinta tafara laluba ɗakyar tasamowani yamu shashshen hijab taɗora akanta taɗan jima tana tana addu'a sannan taji ɗan kwari tamike tsaye tana ambaton sunan ALLAH, fita tayi daga ɗakin tafito tsakar gida Kaitsaye ɗakin mamma tanufa da sallama tashiga amma ko arzikin kallo batasamuba balle ammasa sallamar, cikin mutuwar jiki da zafin zazzaɓi tace, Mamman gani Ko kallon ta batayiba tacigabada sabgarta, takai 20 minute atsaye kafin tajefamata kuɗin kasancewa seface suka tarwatse cikin wani irin ƙunci dabaƙin ciki tadurƙusa tana tsince kuɗi, batasan lokacinda hawaye suka shiga gangaro mataba hartakammala tsince kuɗin ta fita dantarigada tasan mezatasiyo Kasancewar tsakanin banda bari da habu bene baƙaramartafiya bace gashi dukjikinta ciyo yake mata gawani zazzafan zazzaɓi dakeson rufeta, jintatake kamar ba'a duniyaba, dakyartake tafiyar muradinta Allah yasa takai bakin titi kotasamu wani yarage mata hanya, aikuwa bstasamudamar ƙarasawaba wani wawan jirine ya ɗibeta tafaɗi aƙasa tana sauke numfashi wahala, tauikusan eminti Uku ahaka kafin Allah yajefowani ,mai mota yazo giftawa har ya wuce saiyadawo ganin mutum kwance ba alamar motsi kumafa macece yafaɗa cikin hanzari tare da fitowa daga motar yanufota Baiwar Allah! Baiwar Allah! Shiru ba amsa hakanyasa yaumarci matarsa dake mota tafito takama masa ita cikin masifatace wallahi ba inda zanfito Dakaganin mace dukkaruɗe Kazomuje inhar baso kake raina ya ɓaciba shima cikin ɓacinrai yace Waike mekedamunki macecefa ƴar uwarki Dasauri takatseshi dacewa niba ƴar uwatabace danzata iya yimin wuf da miji tafaɗatanawani basarwa tabashi dariya sosai amma saiya matse Ganinkamar yayi fushine yasa tafito daga motar , Amma kasanbazaka taɓatabako? girgizakansa kawai yayi shiyarasa wannan wane irin kishine da ita Tozaki iya ɗagatane? Zandai jarraba nagani , ƙarasawatayi kusaɗa maryam taɗan taɓata saitaga ashema ba'a sume takeba Kallo ɗaya tayi mata tasan agalabaice take nantake tajitausayinta cikinsauri tajuyo gamutunan wanda ina kyautata zaton mijintane tace hubby zokataimakamin Allah yarinyar tajigata sosai ashema ba'a sume takeba. 'Cikin mamaki yakalleta yanzufatace batason yataɓa yarinyar amma yanzu dakanta take neman ya taimakawa yarinyar Haba mana hubby katsa kana wani kallona Ahankali yaƙaraso yadauki maryam yanyata amota yazagaya amazaunin drever yatada motar kaitsaye wani haɗadden asibiti suka nufa emergency aka karɓeda sosai liki tocin sukayimasa faɗa danyace musu ƙanwarsace ganin jikinta duk shatin dukane kuma aulcar tayimata mummunan kamu Sakamakon rashin cin abinci dabatayi sosai yatausaya mata kumayaji tausayinta Dayake asibitocin Niger bakalan namubane na Nigeria mukomai anbarmu abaya sunada kayan aiki isasu yasa kodatafarka taji ƙarfin jikinta sosai Anso ariƙeta amma tace taji sauki gida zata tafi ganin tadagene yasa mutumin karɓamata sallama Kasancewar tundasuka kawota yakai matarsa gida yasake dawowa Sosai maryam tayimasa godiya akan taimakon da yayi mata Yanuna mata bakomai tunawa tayi batafa yiwa mamma cefanentaba kuma gashi yamma tayi sosai batamasan ina tajefarda kuɗinba Bayan sunfito daga asibitin yakalleta Ƴammata yadunanki? Kawaddakaitayi jikin muryarta mai matuƙar sanyi tace sunana maryam daga haka takamabakinta tayi gum Maryam inazakije dakika fito balafiya? Kamar bazata tankaba saikumatace habu bene Saurin kallon ta yayi yanamai zaro idanunsa cikin tsananin mamaki yace 'Yanzutundaga banda bari kike zuwa habu bene da zazzaɓi ajikinki ' Shiru tayimasa ganin yaɗau hanyar komawa gida yasa tace '' dan Allah ka ajiyeni anan Allah inahar bada cefane nashiga gidannan ba mamma zata iya kassarani'' Baiwani tsaya sauraron taba yacigabada draving ganin haka saitasanyamasa kuka cikeda mamaki yake kallon ta sannan yace Kinga maryam bakida lafiya kumafa gida zankaiki bawani wajenba cikin shash sheƙar kuka tace ''kayi haƙuri ka'ajiyeni anan cefane aka aikeni nayo '' 'Cefane yamai maita cikin wani sabon mamaki 'kyadamasa kai tayi alamar eh 'Agidan ba'a san bakida lafiya bane' Shiru tayi danbatasan mezatace masaba ganin hakan yasa yayi parking ɗin motar yamayarda hankalin sa kanta Maryam! Yakirata cikin sanyin murya tace ansamasada ''Na'am'' bawandake yin aikenne saike? ''Eh '' ta amsa masa tambayar cikeda ƙosawa shiru yayi naɗan wani lokaci yajuya akalar motar zuwa kasuwar habu bene wata sassayar ajiyar zuciya tasauke batare data kalleshiba tace ''Nagode, Allah yasakamaka da mafificin alkairi, yabiyamaka buƙatun kana allkairi yasakagama da duniya lafiya'' Sosai yaji daɗin waɗanan addu'oin nannata ammakuma yayi mamakin yadda tajidaɗi ganin yakama hanyar kasuwa Parking yayi sannan yadubeta yace 'dame dame zakisaya '' kifi kilo ɗaya, madara ma kilo ɗaya'' Jintayishiru yasa yace shikenan kyaɗa masa kai tayi alamar ''eh''. F🌹A🌹K Batool Kamba More comments more typing {🖤Batool kamba 🖤}. ALKA LAMI YAFI TAKOBI 🗡️ https://chat.whatsapp.com/Gn6wOkxz4N6KBN3JbMkPiZ?mode=ems_copy_c 💋*SON KI NE ƘADDARA TA*💋 {🌹 Your love is my destiny 🌹} STORRY & WRITING BY FATIMA ABDULLAHI {Batool Kamba} Dedicated to my lovely mom ALLAH yaƙara tsawonrai da rayuwa mai albarka * 1️⃣1️⃣&1️⃣2️⃣ ___________________________✍️wai papane dakansa yakoreta, tome tayi masa hartakusa shiga ɗakin mamma tace hijab kawai zaki ɗauko Batareda ta amsaba tashige ɗakin wani kukane yasake kufcemata Kukane irin wandake fitowa tun ƙasanrai , kukane maihaɗeda ƙunar zuciya Kukane mai cinrai, Kukane narasa mafita, Kukane na neman dauki awan maha licci, ''Inna lillahi wa'inna ilaihirra ji'un! '' ''Inna lillahi wa'inna ilaihirra ji'un! '' Inna lillahi wa'inna ilaihirra ji'un'' ''Alhamdu lillahi ala khulli halim '' ''Alhamdu lillahi bini imaathihi thathi mussalihun '' ''Alhamdu lillahi wakhhafa '' ''Alhamdu lillah '' ''Alhamdu lilah'' ''Aljamdu lilah'' Abinda take nanatawa kenan afili jinzuciyarta take tamkar zatafashe ''Wayyo! Allah nashiga ukuna ni Maryam inazansa kaina Allah yakawomin agaji nibaiwarkace mai tsananin rauni Allah natuba '' ''Astaqfi rullah '' ''Astaqfi rullah'' ''Astaqfi rullah wa'atubu ilak'' Jin anfara kwala mata kirane yasa tayi saurin fitowa bayan ta ɗauko hijab ɗin kallon motar papa tayi kasancewar atsakae gidan suke, nufar motar tayi cikin sanyin jiki papa naganinta yayi saurin ɗauke kai durƙusawa tayi agaban papa bayan ta isa wajan cikin murya mai rauni tafara magana ''papa bansan dawacekalma zangodemakaba, bansan dawane harafi zan godemakaba, haƙiƙa kazamomin wani jigo arayuwata , wanda bazan taɓa mantawaba, kazamomin bangon jingina alokacinda narasa majin gina, kazamomin tudun dafawa alokacin da narasa madafa papa Allah yabiyaka bazan gushe dayimaka addu'a ba, zantafi kamar yanda kabuƙata nabarmaka gidanka amma kasa aranka bazan taɓa mantawa dakai ba arayuwa katallafeniii '' Kasa ƙarasawa tayi saboda wani irin kuka daya tasomata, dasauri tamiƙe tayiwaje mamma takalli matar tace kuɗinfa? Murmushi matar tayi sannantace Hadiza bakida sauƙi akan kuɗi Kallon bakida hankali mamma tayi mata tace ke awannan zamanin kuɗi ai sune rayuwa malama kibaninkawai Buɗa jakarta tayi taɗauko damen kuɗi tamiƙawa mamma washe baki tayi kafintakarɓa tanafaɗin yanzun naji zance hajiya sa'ade karki manta ƙasararda nabakifa maitsadace dan Allah kisamomata gurri mai gwaɓi kindaigane taƙarasa maganar tanamai kashe mata ido Murmushin ƴan duniya hajiya sa'ade tayi, karkisamu damuwa Hadiza wannan yarinya aisai manya kumanasan baƙananun kudi za'a samu akantaba . Nandai sukayi sallama papa najikuma yana gani amma yakasa cewa ƙala shifa acikin ransa tausayin Maryam yake amma yarasa dalilin dayasa yace tabar masa gidansa shidai yasan bahakane aranshiba , jiyake bakinsa yayimasa nauhi hakanyasa yakasa magana har matar tabar gidan wani abin haushima lokacinda Maryam keyimasa magana yasu yaceda Ita wani abu amma yakasa Fitarsu daga gidan kaitsaye sukaɗau hanyar barin garin neimey Maryam tatsorata sosai dan itadai bata taba ganin irin wannan tafiyaba gashi kuma ba'itakadai bace sunfi su talatin amotar kuma duk mata bawanda yakulata itama bawanda takula saikuka datake matar dake gaban motarce ta juyo amasifance tafara magana Ke Malama kiyimana shiru kowaye kikaga yana kuka a nan dazakidami mutane *MARWAN* Guduyake shara rawa kantitin garin abuja kaida ganin wannan kasa tuƙin gangancine dubada yanda yake draving baya damuwa dawanda ke kan titin burinsa kawai yakai inda yake so jamil dake gefensa duk atsorace yake Allah ne sheda yayi danasanin biyosa dayayi, yasan waye marwan bai iya fushiba cikin shakkar sayace ''please, marwan come down mana karka kashemu abanza naga ai gaskiya suka faɗa da tana sonka aibazata gudu ajajibirin ɗaurin au.....'' Wani irin birki dayajane yahana jamil ƙarasa maganar Cikin wani maɗaukakin ɓacinrai yace ''stop Please jamil ''yafaɗi atsawace wandayasa jamil ɗin jan bakinsa yayi shiru Yashiga bashi haƙuri kosau raronsa marwan baiyiba yafita daga motar yana huci Allah mayasa lokacinda zai jabirkin yagan gara gefe da anyi ɓarna, tsaye yayi yama rasa mezai yiwa jamil dasu haroun yahuce Shima jamil fitowa yayi ''please marwan kafahimta ada inagoyon bayanka kaci gabada son yarin yarnan amma ayanzu nadawo daga rakiyar ka dama ai anfaɗa tsintacciyar mage aibata mage '' Baikula dayanayin dayashigaba yacigabada cewa "Marwan sanin kankane bawanda zai ɗauke hotu nanta inhar ba itaba wamaysan inda suke? Kuma aiii'' Wata muguwar shaƙa marwan yakai masa, nan yafara dukansa baji bagani Wani ikon Allah jamil baya ramawa saidai yana ƙoƙarin kare kansa da dukkanin hanna yensa wani mai motane yatsaya ganin abinda ke faruwa nan yafara rabasu dayake shi Jamil baramawa yakeyiba faɗan yayi saurin rabuwa kallon marwan yayi cikin zaro ido da maɗaukakin mamaki yace marwan! Haba yallaɓai dagir manka meyayi zafi? Ko kallonsa marwan baiyiba yagiftashi yashiga mota A 360 yabar wajen kallonsa mutunan yamayar kan jamil yace yalla ɓai meyahaɗakada yallaɓai baka gudun abinda zaije ya dawo kasan masu kuɗin nan basada mutunci Barinma wannan shakwa ɓaɓɓen yaro waye bai san shiba? Kab garin abuja dakaceee ''abokinane'' Jamil yakatse shi Yanafaɗin haka yabar wanjen Allah mayasa ba mutane ke yawan wucewa kan titinba hanyace hara hayaniya Kaga inazakije tunda shi yawuce loko ESTATE jamil yafaɗa kaitsaye Muje na saukeka Allah ya ki yaye gaba Bamusu Jamil yabishi ganin yakama hanyar ganinzasu wuce gidansu yasa yadakatar dashi fita yayi ''Nagode ɗan uwa '' Jamil yafaɗa haɗida juyawa yashige gida Marwan tun barinsa wajen yake jinsa wani iri, magan ganun haroun da jamil ke faɗomasa arai Shifasam bayaganin guduwa my soul ɗinsa tayi yafi yarda da saceta akayi kowani abun badai guduwaba duk cikin kalaman jamil bawanda yayiwa marwan ciyo kamar tsintacciyar mage kenan ma gori yake mata ''No never wallahi my soul bazatayimin hakaba mema zaisa tayimin haka, tana sonafa haba kai bazai yiyuba '' Shikaɗai yaketa magana tamkar wani zararre harya isa bakin gate ɗin katafa ren gidansu hone ɗaya yayi saiga gate man yazo dasauri yabuɗe Kaitsaye parking space yanufa ko parking arziƙi baiyiba yafito direct yanufi part ɗin mom ''Mom! Mom!! Mom!!'' Yashiga kwalamata kira tamkar zaifasa gidan Mom dake farlou tamiƙe tanafaɗi lafiya dai? Wani irin rungumeta yayi tare dafashewa da kuka tamkar ƙaramin yaro Sosai mom hamkalinta yatashi ,zaunardashi tayi sannan tamiƙe taɗauko masa ruwa maisanyi a freg saidayasha sosai Yafara magana ''mom wai dagaske my soul batasona shiyasa tagudu, mom dagaskene dan Allah kiga yamin? Yanamagana hawaye na tsiyaya a idanunsa Daman tatsuniyar gizo ai bata wuce ƙoƙi sosai ran mom yaɓaci Kaga banason wannan tayar da hankalin dayake A'a bagaskiya bane kamanta dawacece my soul ɗinkane? Yazakayimin wannan tambayar Please ka kwantar da hanka lin ka kaji Shiru yayi yana sauke zazzafar ajiyar zuciya Miƙewa yayi yanufi part ɗinsa kaitsaye haban wadrop yanufa yaɗauko wani allon zane wani irin zaro idanu yayi waje 👁️👁️ cikin tsananin tsoro yajefarda allon yana ja da baya tamkar wanda yaga mala'ikan zare masa rai Too masukaratu aganinku me marwan yagani dahar yabashi tsoro haka? Amsarku nanan a page 14 & 15 Inhar banga ruwa comments ba sainan da One monch zakusa ke gani post inkuwa kun shirya nima ashirye nake SON KI NE ƘADDARA TA 🌹your love is my destiny🌹 STORRY & WRITING BY FATIMA ABDULLAHI {Batool Kamba} Wannan shafi sadaukar wane ga duk wata marubu ciya dake faɗin duniya ina sonku writters *1️⃣3️⃣➡️1️⃣4️⃣ ___________________________✍️ma gana yake son yi amma yakasa ''Mom!'' Yakwala wa mom kira afir gice yana mai miƙewa yanufi fita waje yana mai mai ta kiran mom Tun aharabar gidan yadinga faɗi yana tashi abun mamaki securiti's zuba masa 👁️sukayi dan basu taɓa ganinsa ahakana gashidai bai daɗe dashi ga part ɗin nasaba mom dafe kai tayi ji kiranda yake yimata, lamari marwan nabalain bata mamaki mutum kamar ba namiji ba Mom! Yasake kiranta lokacin daya shigo part ɗin akiɗime Lafiya marwan? Ta tambayeshi ganin yanda yake zaro ido kamar tsohon kwarto ''Mom dan Allah wa yashigar min part ɗina daba nanan? '' Kallon mamaki tayi masa cikin halin ko inkula tace Wakasan yana shigar maka part ko wayasan password ɗinka? ''Mom dan Allah zo ki gani Please yafaɗa out of control'' Ganin kamar baya hayyacin sa yasa mom binsa , koda suka isa part ɗin bedroom ɗinsa suka nufa kaitsaye gurin allon zazen yakaita ɗagoshi yayi ''mom kinga sauran maganarce tamaƙale saka makon ganin wayam . Menene? Kasa maga yayi saboda ɗimauta saida yaɗau dogon lokaci sanan yaja numfashi "Mom kinsan menazana? A'a Mom face ɗin my soul nazana amma natarar yakoma kwaran kwal Yanzukuma bakomai Please mom meke shirin faruwa ne? *MARYAM* Sunyi tafiya takai ta 5 hours suka huta sannan suka cigaba daga nan bazatace ga abinda yasake faruwaba saida ta buɗa ido taga duhu yamutsa fuska tayi ganin suna ƙoƙarin tsayawa yasa duk jikinta yayi sanyi "Niyanzun inane za'akaini gunsuwa zan zauna Allah kajikaina ka agazamin Allah karkabarni na wulaƙanta aduniya " Tsawarda aka dakamatace tadawo da ita hayyacin ta Fito malama kinwani zaunawa mutane amota inajin bakitaɓa shiga motabane Wasu zafafan hawayene suka wankemata fuska jin irin tsawarda yakemata aka "Yihaƙuri" tafaɗa cikin muryar kuka Tsakiyaja kafin yayi gaba abinsa, Shin yanzun ita menene makomar rayuwar ta "Ya Allah kajiƙaina " Wani gida tagani da alama nanne masaukinsu domin sauran yanmatan duk sun shige ragiwar kuma suna ƙoƙarin shiga itama hanyar tanufa. Gidane da ɗakuna ajere barandace doguwa yawan ɗakunan mayasa bansan adadin suba A tsakar gidan suka tsaya, wasu ƴan mata kusan su goma wasukoma suka shige ɗakunan da'alama sunsan yanda gidan yake wata matace dafito dagawaniɗaki dake gefe ɗaya, hannunta ɗauke da sigari tana busawa, jan sigarin take irin nakwararru kuma ta tattun ƴan bariki, kallon wula ƙanci tayimusu tareda yatsina baki Kune baƙi annan dafatar kunsan meyaka woku nibana ɗaukar iskanci dole gobe kufara aiki danbazan baku ɗakuna kushare kuzaunaba . Cire glas ɗin idanun tatayi tabisu da kallo ɗaya bayan ɗaya idanutane yasauka kan Maryam saida taƙre mata kallontsaf yafito ta da hannu Cikin ɗari ɗari dajiki tanufi inda matar take sake kallon sauran tayi bangaya muku sunanaba ko?tatambaya cikeda iskanci Taɓebaki tayi da alama hakan yazame mata ɗabi'a "Zaku iya kiranada uwar gida ko anty kundai gane ?" Jinjinakai sukashigayi itadai Maryam duk atsorace take kasan cewar bata sababa. kallon Maryam tasakeyi cikin iskanci tace my love yasunanki? "Mar r y a m" tafaɗa cikin rarrabewar harshe murmushin ƴan duniya tayi Dagayau sunanki qutty kinji? Kyadakai tayi alamar Ehm Nan akashiga bawa kowa ɗakinsa har maryam ɗin ɗakine maiɗaukeda madaidai cin bad, Waldrop sai mirror dakujera two sitter, da bathroom . bathroom ɗin tashiga taɗauro alwala cike da damuwa tafara sallah. Harta idar taci gabada tunanin makomaer rayuwarta, taɗau alƙawarin dul wuya bazata sayar da mutuncin taba, danta soma gano wani abu dangane da wannan gida amma zata bi ahan kali tagani har Allah yasa tasamu hanyar gudu. Washegari tunda tayi sallar asubahi tarinƙajin hayaniya dataso tayi zamanta saigawata matashiyar yarinya taahigo waitafito waje inji Uwar ganta lalli hijab ɗinta tasanya tafito ganin gidan yacikada mutane daban daban yasata fara tambayar kanta "wannan wane irin gidane? " Muryar Uwargida ce taji tafara magana. qutty zonan. Dakar kartaje saikuma tanufeta, matsawa tayi ta zauna cikin ladabi tace "ina kwana " lafiya cewa uwar gifa Sannan tace da alama ke bakisan wannan inaneba amma zakisani naga kowa ya fahinta kece kawai kikeson bamu problem amma You don't worry qutty zaki gane, yanzun jekiyi wanka natanada miki costomer yananan zuwa zaki tayashi kwana baƙone kisaki jikinki kikwashi rabonki karki kuskura kimai musu komaiyace Saurin katseta Maryam tayi dacewa "hajiya kiyi haƙuri ban fahimtaba , wani kuma? A ina yasanni nida nazo jiya wana sani, waya sanni dahar zaizo wurina . kuma naji kinazancen costomer nida bana kasu wanci meya haɗani da costomer?" Sosai wurin akashiga dariyarta ciki kuwa harda waƴan dasukazo jiyan Kumin shiru cewar uwar gida kinga qutty aiki bata ƙananun mutane bace so karkidami kanki cos kinada abinjan hankalin ɗa namiji karkiyi wasa da damar ki wanna dakike ji nace zanhaɗaki daahi babban mutunne a Nigeria so kiyi amfani da damar ki wajen sa Kan Maryam yasake kullewa itafa bagane wannnan kurman zance takeba "Please hajiya let me go to the streat point zanfi ganewa " tafaɗa cikin yatsina tana son tabbatar wa dagaake wannan gidain karuwai ne Cikin ɗanjin haushinta uwar gida tace jeki kiyi wankan zan aiko miki da kaya idan kunje zaki gane nufina ok yamutsa bakitayi kamar tayi magana kuma tafasa , kamar yanda uwar gida ta, Umar ceta wasu ƴan isan kaya takawo mata taso taƙisakà kayan amma saita tuna karfa tayi ƙoƙarin ja inja da ita takoreta Allah mashaidane wani abu takeji maikama samun freedom, wato ƴanci . sosai kayan yakarɓi jikinta kasancewarta Black beauty kayan kuma golding colour kamar dan ita akayisu the best colour ɗin ta kenan . Ridane dawando rigar iya gwuiwa shimadai wandom baikai ƙasaba. "zuwa yanzu tacire komai daga ranta zatata fuskanci rayuwarta tayanzun. Motsin mutum taji dasauri tajuya ganin wani tayi atsaye yana mata wani irin kallo data kasa ganesa, tarigada taranfo uwar gida zata yarda tabishi daganan zatasan abinyi.. More ✨comments ✨ more ✨ typing F🌹A🌹K 🖤BATOOL KAMBA 🖤}forever SON KI NE ƘADDARA TA {🌹 Your love is my destiny🌹} STORRY & WRITING BY {🖤 Batool Kamba 🖤} Wannan littafin kacokan sadaukar wane ga mahaifiyata abar alfaharina Allah yabani ikon kyau tatamiki ameen *1️⃣5️⃣ &1️⃣6️⃣* _______________________________✍️ Ganin baiyi mata sallamaba yasa tacigaba da sabgo ginta, baƙarya taji haushisa sosai, ƙato dashi bai iya sallamaba. mtsuu taja tsaki saida yaƙare mata kallo off and down sanna yayi kyaran murya, batakula shiba yazo inda take yazauna dab da ita yazauna , matsawa tayi saboda tafara jin tsoro "Allah yasani taso tadaure amma bazata bari wani gardi yataɓamata marta bartaba basadaki. Tashi tayi takoma ɗayan kujerar dake ɗakin dama bakin katifa tazauna . juyawarda tayi shiya fallasa asirin manyan hips ɗinta, Aiko yana tozali dasu yawu yasar ƙeshi yahau tari baƙakƙau tawa, taso tashare saikuma ta ga rashin dacewar hakan Amma ai baiyimiki sallamaba wata zuciyar tagaya mata hakan yasa tashare , Ganin yafita yasa tasake kallon jikinta, bazatace garanar datasanya kaya masu kyauba irin wannan.amma tanaji kamar dama tasaba sanya kalar kayan. Sake shigowa yayi yazo inda take, baizaunaba sai cewa yayi "Am dafatar hajiya tayi miki bayani, "Bayanin me kenan" Yanda tayi da bakinta yafi komai riki tashi. Kinada kyau wannan yarinyar Allah yazuba miki kyau, uwar gida batayi ƙaryaba keɗin tadabance kizo kibini zakiyi mamaki dan zan sakar miki kuɗi, zan baki duk abinda kikeso aduniyar nan matuƙar zaki yimin abinda nakeso. Awannan karonma taso shareshi amma takasa azafafe tafara magana "waikai kanada addini kuwa? Murmushin ƴan duniya yayi yace me kika gani? Nantake zuciyarta takwaɓeta "Ambakomai zanyi maka yanda kakeso ɗin. " Yaji daɗin amsarda tabashi hakan yasa yazauna kusada ita yace "kinga yanzun rana tasomayi dan ana neman ƙarfe 11:30 ne kozaki bini muje hotel " Yaƙarasa maganar yana kanne mata ido ɗaya Abin dariya mayabawa Maryam "gashida girma kamar buhun masara kumawai soyake na aminta dashi kamar wani mijina, kutt Allah bazai yiyuba wannan kan ai zan iya mutuwa" "Kina kallona kobazakije bane Saurin saita kanta tayi sannan tace "Bakomai muje " Tayi maganar cikeda tsoro haryasoma ganewa yace Kisaki jikinki baby akwai kuɗi "Shiwai atunanin sa kuɗene nazo nema uhumm , ko zannemi kuɗi bata wanna hanyarba " duk wannan maganar tanayintane azuciyarta. Miƙewa tayi tanufi ƙofa, shima bin bayanta yayi suka fita, sosai gidan yasake cika damutane. "ikon Allah sai kallo " maryam tafaɗa cikin maɗau kakin mamaki, ganin ƴan daudun dasuke kwasar rawa ana musu liƙi. Jin ankama hannun tayasa tayi saurin juyowa, karaf suka haɗa ido yayi saurin kauda nasa idanun. "Kinga kidaina kallona da kwala kwalan ida nunnan naki😃, nitsoro suke bani." yayi maganar da iya gaskiyarsa. Sosai wannan karon takasa ɓoye dariyarta saida ta murmusa Wow kunga wani irin kyau da dariyar tayi mata Ahankali tacire hannunta daga nasa tayi gaba ƙirjinta nawani irin bugawa narashin sabo tanaso ta ƙarfafa zuciyarta sosai tayanda zata cimma manufarta. "Allah kajiƙaina kasa wannan shine ƙarshen shiga ta wannan baƙin gidan " Wata arniyar mota tagani a fake daidai motar tatsaya , Saurin ƙarasowa yayi yabuɗemata. Shigar ta motar yayi daidai da saukar hawaye akuncinta, lokacin dayashiga bailura dahalinda take cikiba yatayarda motar Baby bangaya miki sunanaba ko, "Uhumm" kawai tace saboda wani ɗacin rai dake ɗawai niya da ita "Sunana Alhaji surajo, Amma ana kirana da Alhajin manya danni bakowace mace bace nake kulawa saiwadda tasan kanta acikin mata,kamardai ke ɗinnan , Nibaƙone daga Nigeria nake ina zaunene a Abuja nida iyalina. Yaɗan tsagaita dacewa "kinsan komeyasa nake yimiki wannan bayanin inason inhar zaki amin cemin na aureki *Abuja Nigeria* Damisalin 9:20 nadare marwan nezaune a parlourn sa mom na tsaye da alama magana take yimasa "Nidai Allah yasani bazan iya zuwa koinaba, Please mom kuje kawai inya iso gida ai zan gansako? " cike damamaki mom take kallonsa. Marwan dady nefa za'a tarba bawaniba, kumakace bazaka je tarbarsaba. " Mom dan Allah kuje kawai banason haya niya wallahi" Mom ko aranta cewa take kodai yafara zaucewane bamada masaniya. Kamar yasan metake faɗi yace "Nifa dahankalina kawai banajin ƙafafuna zasu iya kaini airport ne". "Uhumm Allah yashige managaba" kawai mom tace tajuya . Airport babban farin dattijo maijikar kamala da da Dattaku , cikeda natsuwa yake saukowa daka ma tattakalar jirgin, tunlokacinda yafara saukowa yake baza idanunsa dangani ta inda zai hango farin cikinsa kuma sah lelensa, Bamaya takan ƴan jarita dasuke son yin magana dashi, gamamakinsa mom kawai yagani itada securiti's. "Momyn boy inaɗan naki? ". yafaɗa daidai yaƙaraso inda suke . Uhumm marwan Sarkin rigima yana gida waibazai iya zuwaba, inaji bayajin daɗinji kinsane. Afirgice dady yace "what, bayajin daɗi kuma kika barmin shi agida Haba momyn boy kinsan kalar ciyonsafa sokike natarar yamutu kome " yafaɗa da ɗanjin zafinta ganin yafara masifa kuma agaban securiti's yasa tashige Mota batare data tamka mishiba. Shima motar yashiga tareda kallon ta yace " sorry momyn boy naman ta a inda muke kinsanfa boy shikaɗaine gareni dole na tashi hankalina." Bakomai kanada gaskiyar ka. dady baigane wace gaskiyar take nufiba yace yawwa momyn boy . Tunda suka baro airport yake jin badaɗi yamatsu yaje gida yaga wane hali boy ɗin sa yake ciki Allah mayasoshi yau duk kwakkwafin yanjarida basu samudamar magana dashiba dan basuma ƙaraso inda yakeba, hakan yasa ya isa gida da wuri kaitsaye pat ɗin marwan yanufa buɗe ƙofarda dady yayi Yasa yayi daidai da lokacin da marwan kecewa "Wallahi nikam nagaji da wannan rayuwa haba my soul, mena miki dakika zaɓi cutarda bawan Allah, wallahi na azabtu fiye da tina ninki , dan Allah kidawo gareni zuciyata daf take da bugawa muddin nakasa samunki arayuwata sosai yake kuka kamar mace , numfashinsa na ƙoƙarin tsayawa yana fizgarsa jirine yafara ɗibansa aiko yatafi luuu. Dasauri dady yaƙaraso indayake amma inaa jiri yaɗaukeshi nan yazube yana dafe zuciyarsa Sosai dady yashiga tashin hankali da ɗimuwa ganin tilon ɗansa naneman rasa rayuwar sa... Menene ra'ayin ku awannan page? Anya Maryam zata amince da buƙatar Alhaji surajo nason aurenta kubiyoni a next page danjin yanda zata kayaaaaa Kunason ganin post duk bayan kwana uku Kubiyoni a facebook group na maisuna BATOOL KAMBA NOVEL'S✍️ Taku har kullum Fatima Abdullahi Please share https://chat.whatsapp.com/Gn6wOkxz4N6KBN3JbMkPiZ?mode=ems_copy_c SON KINE ƘADDARA TA 🌹 Your love is my destiny 🌹 STORRY AND WRITING BY F🌹 A 🌹 K Batoool kamba Dan Allah masoya kumin afuwa page 17&18 tabata nayi nema ban samuba dafatar hakan bazai rage muku kar sashiba _________________________________________________________________________________________________________✍️ *1️⃣9️⃣& 2️⃣0️⃣* _________________________________________________________________________________________________________✍️wanan shine sanadin canzawar rayuwar su Khadijah domin doctor sadiq yayi musu gata yabiyawa Sani kuɗi yaje London dansamun karatu mai inganci Khadijah ma tacigaba dazuwa school, Dantana ss2 ne Matar doctor sadiq hajiya Habiba macece mai karamci dason mutane, tariƙi su Riƙayya tamkar ƴaƴanta tanada ƴaƴa uku Umar shine babba yanada shekaru 28 ya kammala degree ɗin sa da master's a ɓangaren low yanzun haka yana aiki agarin Kano sai Hajara mai shekaru 10 sai ƙaninsu Haruna mai shekaru 7 kasancewar lokacin da ta haifi Umar tasha wahala saida akayimata aki doctor's sun tabbatar bazata sake haihuwa ba saboda tasamu matsala amahaifa, Saida wani ikon Allah Umar nakai shekara 18 taɗanyi zazzaɓi doctor sadiq na dubata yaga ciki bai gamsuba hakan yasa yayita aunata harso babu adadi ganin dan dagaske cikin ne yasa yafara muurna bayan ta haifi Hajara da shekara Uku saiga cikin Haroun daganan kuma har yau dayakeda shekaru 7 batasake ko ɓatan wataba. Soyayya ce ta ƙullu tsakanin Umar da Khadijah lokacin da doctor sadiq yaji yayi matuƙar farin ciki bai tsaya wani kace naceba yagayawa Sani, shima yayi farin ciki, doctor yaso yagayawa ƴan uwansu na mahaifi amma Sani yace ai su basada wasu ƴan uwa sai shida mamee ( hajiya Habiba kenan ) ba'a ɗauki dogon lokaci ba aka sanya rana wata ɗanya. Ƴan uwan malam Muhammad sunyiwa doctor tijara lokacin da sukaji labarin zai aurar wa ɗansa Khadijah batare da izinin suba , Maganafa ta girmama dan har kotu saida suka je nan Sani yasha yardasu mamaki , agaban alƙali yace, "Ni Sani nine waliyin Khadijah domin nine yayanta bamada wasu ƴan uwa sai baba doctor dan haka anan nakeson alƙali yazama shaida nabawa Umar auren Khadijah , kuma anan nakeson aɗaura auren matuƙar shi Umar ashirye yake " "Kallonsa alƙali yayi yace bakada wannan dama saboda kanada ƙan nen mahaifi " "Yamai girma mai Shari'a nagayama bamada wasu ƴan uwa " Cikin ƙunar rai yashiga karantowa alƙali duk abinda aukayimasu yaƙara dacewa "tundaga ranar nayan ke alaƙata dasu yamai Shari'a ayimana adalci so suke su salwan tarmin da rayuwar ƙanwa kuma wallahi ko da sunce zasuje da ita ni bazan yardaba, dan yanzu Allah yamana sutura yabamu baba doctor , danhaka aduba mana. Alƙali yagamsu da baya nan Sani yabuƙaci ganin Khadijah dan ya tabbatar shin tanason auren ko bataso, bawani ja inja ta amsa da tanaso anan alƙali ya umarci wakilan da sufito, alƙayayiwa Umar wakilci yayinda doctor yayiwa Khadijah anan cikin kotun aka ɗaura aure Wannan auren shiya ƙarasa yanke alaƙa tsakaninsu da ƴan uwan babansu hatta ɗangi danda suka bar musu ada yanzun sun kwace acewarsu babansu baida wani gida Wannan gidan baba Salisu ne yake zama dan haka yakarɓi abinsa . Baba salisu ƙanin malam Muhammad ne uwa ɗaya uba ɗaya sai baba Isyaku wanda suke uba ɗaya. Doctor yaso yayi magana amma yashare Sani ko ajinsa , tunda sunyine dan su cusa musu baƙin ciki ,sai suka nuna ko'a takalmin ƙafa bale akwalar riga. Umar da amar yarsa Khadijah suntare a babban gidansu dake rijiyar zaki agarin kano # AGUR GUJE Bayan shekara bakwai haryau khadija bata taɓa ko ɓatan wataba, lamarin na damunta amma Umar yana nuna mata itafa hai huwa Allah ke basheta alokacinda yaso, akuma inda yaso , gawanda yaso, danhaka lokacin samun tasu haihuwar baiyi bane, Ikon Allah sai kallo Khadijah tasamu ciki haryakai wata Uku bata ganeba shima Umar baiwani luraba saida sukaje Birnin Kebbi babbar Sallah doctor yake cewa Umar dafatan kana kula da jikan nawa, nagama baya wahalda maman tasa unbon Chile ɗin naku ɗan baiwane. Cikin rashin fahimta Umar yace "baba doctor mekake nufi? " Kasancewar haka suke Kiransa ina nufin cikin da khadija ke ɗauke dashi. "Ciki Kuma? Khadijah ce keda ciki? " Ganin kamarma raina masa hankali zaiyi , saiya share maganar shima Umar baisake maganaba. Zaune suke a farlour gabaki ɗayansu Haruna nakan ƙafafun khadija, fira suke cike da nishaɗi "Baba doctor Allah kwana biyun nan banajin ƙarfin jikina kuma inajin marata tayimin nauhi sosai. Duk kallota sukayi, baba doctor ne yafara magana " Wai dagaske bakusan kina cikiba? Waro idanu tayi cikin jin kunya tace "Ciki kuma baba doctor? " "To idanma kunsani kuke raina mana hankali abar maganar ranarda kuka shirya faɗamana saiku faɗa " "A'a baba doctor wallahi bansan khadija nada cikiba saida kafaɗa " Mamee dai kallon ikon Allah kawai take Haruna ne "yace anti khadee zaki haifa mana baby ko " Cikin kuka tace "Eh harun " Mamee ce ta kallesu dukkan su "Waiku kuna nufin dukka ninku bawanda yasan dacikin? Amma khadija kinbani mamaki kamar ba maceba? yaushe rabon kiga piriod ɗinkin" " Cikin kuka tace wata uku da sati daya " "Amma kika kasa fahimtar komai " Faɗa ammee tayi musu sosai akan rashin kula da lafiya, dan da suna kula da sun fahimta Baba doctor ma bakunya tsakaninsa da Umar dan haka yabashi sha war warin yanda zasu kula da cikin. Kwanci tashi asarar mairai cikin khadija yashiga watan haihuwa sundawo birnin Kebbi mamee tace saita haihu tayi arba'in sannan sukoma satinsu ɗaya da dawowa tahaifi ƴarta mace, Ana gobe suna da dare misali 1:20 nadare, hayaniyace tafara tashi kaɗan kaɗan baba doctor nakan sallaya yaji an banki ƙofar ɗakinda suke ciki baiyi auneba yaji bindiga akan maƙo garonsa bazoto bare tsammani ɗaya daga cikin ƴan fashin yaharbesa a'hannu ƙarar harbin ita ta tayarda duk wani maha luki dake gidan. Tarasu sukayi a parlour gaba ɗaya, Sani ɗaya daga cikin ƴan fashin yaƙira, cikin wani ma ɗau kakin mamaki yace na'am kasan me mukeso? " A'a" wannan mutumin mukeson ka kashe mana. Arazane yaɗaga kai yakalli baba doctor "Me!" Yafaɗa arazane yana kallon kowa dake perlourn Eh so muke ka kashe manashi saimu tafiyarmu batareda munta ɓi kowaba, idan kuma kasan ya mana taurinkai zamu kashekune gabaki ɗaya muyi tafiyarmu, Babban cikinsu ne ya ƙurawa hajara ido don kayan barcinda ke jikinta sunlafe sosai sun fidda duk wata sura tajikinta. ke babban ɗan fashin yadakawa Hajara wata raza nanniyar tsawa tashi muje narage zafi yafaɗa yana lasar leɓe Cikin wani aza babben tashin hankali Sani ya kalleshi "Mekake nufi? yafaɗa yana kafesa da ido Tambaya makake kubashi amsa faɗin hake keda wuya wani ya harbi baba doctor a ka, ko shurawa baiyiba, ihunda yasoyine yamaƙale saboda wani harbin dayaji tare da ihun khadija, baigama tan tan cemeke faruwaba yaji wani ihun , sun harbi Umar kanyasake wani yunƙuri yaji ihun Hajara yadda wannan ɗanfashin yake keta mata rigar mutunci batausayi bare imani 😢😢😢 MUHAƊU A PAGE NAGABA DAN JIN YANDA ZATAKAYAAA ............. SON KI NE ƘADDARA TA 🌹Your love is my destiny🌹 STORRY & AND WRITING BY F🌹 A🌹K 🌹 BATOOL KAMBA ________________________________________________________________________________________________________✍️ Page *2️⃣1️⃣ & 2️⃣2️⃣* Numfashin Sani ne ke bara zanar fita daka gangar jikinsa wani kalar abu yakeji dabazai misaltuba, ahan kali ida nunsa suke lumshewa wani irin kalar jiri jiri ke ɗibansa adurƙu shenda yake, baigama Sanin yanda zai faraba yazube aƙasa su mamme. Saida sukagama komai daya kawosu sannan suka juya da nufin fita daka gidan sukaji kukan jinjiri, da sunso tafiyar su saikuma ogansu ya umarci ɗaya daga cikinsu yaje yadubo, Shigarsa ɗakin kedawuya yahangi jinjira kwance kan bad ɗin jarirai, sam basu lura da itaba lokacinda suka shigo, ɗaukan yarinyar yayi, bawani dogon bata lokaci yasakai yafice daga ɗakin. Oga jinjirace kuma inaganin baƴar wannan bace yayi maganar yana nuna hajiya Habiba. Eh baƴarta bace ƴar wannan ce kuma munrigada munkasheta so kawaimuje daƴar wannan hajiyar itakaɗai tarage bamu kasheba sai muna fukinnan yayi maganar yana nuna Sani, A'a oga kamanta har wannan ɗantayin yanadarai sumane sukayi dukkansu. Juyawa ogan yayi yanufi inda Haroun yake baiyi wata Wata ba ya harbeshi "Mujeko " Bawanda yasake magana acikinsu sukafice daka gidan. Washe gari damisalin 8 :00 nasafe dandazon mutane nafara gani tundaga gate har babban farlourn gida kukane ketaahi ba ɗaɗɗaukawa, mamee nahanga cen daga gefe, Zaune take saibin mutane takeyi da ido ba imm ba im im, Tun farkawarta take ahaka haryanzu , kusan hawa ɗaya kenan . Wani farin dattijo ne yashigo yana tambayar sauran mutanen ina Haroun da jin jirarda akahaifa. Bawanda yayi alamar tankawa cikin mamaki kowa ke kallon Mamee dake magana. "Kosuma sunkashe sune dan Allah kugayamin inaɗana Haroun da jikata." Saikuma tafashe da wani azababben kuka mai cinrai, saurin taushe bakinta tayi da hannayenta tana kallon dattijon tace sunkashe kowa ko? "Har da doctor basu barminba,? sunkashemin khadija, sun kashemin Umar ɗina ɗan albarka sunkashemin Haroun waimeyasa nisuka barni darai? " "Meyasa nima basu kasheniba sukabarnida ciyon zuci har ƴar jinjirar sunkashe ko? " "Memuka yimusu"? Duk wani mahaluki dake parlourn bawanda bai zubadda kwallar tausayintaba Kasa bata amsa akayi lokacin datake tambayar ina Hajara dan ita taganta anfita da ita tamkar wata matacciya tagansa anfita dashi saɓani suda sauran da'aka rufawa ƙaton bargo Fita dattijon yayi dan yakasa magana, shima zuciyarsa akarye take dan bazai iya cema uwa anyiwa ƴarta fyaɗe tana hospital yanzu haka batasan wake kantaba Haka akayimusu wanka akakira mamee tayi musu addu'a ganin kawar wakin har uku tarasa yazatai kawai akaga tafaɗi ƙasa sumammiya. Haka mamee tashare sati ɗaya batasake maganaba anyi sadakar bakwai kowa ya watse akabarta da ƙunar zuci, dama batada wasu ƴan uwa nakusa shiyasa abin yaƙara yimata yawa. Yauma kamar kullum tana zaune a parlour Sani yashigo riƙeda Hajara hannun sa tamkar wata jinjira takuwata lafe tamkar tasamu katifa Zumbur mamee ta miƙe sai alokacin tasamu ƙarfin magana Hajara! Sani! Dama kuna nan ina jinjirar khadija da Haroun? Sauke Hajara yafarayi sannan ya zauna cikin rashin kwarin jiki yace "Mamee dan Allah kikwantar da hankalin ki komai dakikaga yasami bawa dasanin uban giji Haroun ma yabbi Yan uwa jinjirar itama Allah ya amshi abarsa, tunranar da suka dauka tafi da ita" Ajiyar zuciya mamee tasauke koba komai zata godewa Allah da wannan jara bawar Allah shine abin kodiya akowane halie, akowane lokaci. "Sani ina kasamu wannan labarin" mamee tajefa masa tambaya. "Mamee bincikene ya nuna haka yanzuma anason karɓo kamasunr Dan anganosu , daya daga cikin su na hannu DSS , anbin cikeshi ya tabbatar musu danginmune suka turosu, tunda tun farko sun nuna babsa son aren kadija da Umar, shinefa wallahi mamee Dan adam abin tsoron ne." Sun jimanta Al amarin kafin takai kallonta Kallon Hajara tayi ita muma meya sameta? Kasancewar tunda aka harbe doctor ta sume awajen "Mamee firtatace kawai saikuma ɗan zazzaɓi " Zazzabi? Mamee ta maimaita tana kallon sa haryaso ruɗewa kodai wani nuna fikin yagaya mata komaine "Eh Mamee" Kyara zamansa yayi ya kalli mamee sosai yace "Mamee dan Allah alfarma nake nema agunki" Kallon mamaki tayi masa alfarma kuma Sani? "Eh mamee" "Kuma ina fatan samunta agunki dan Allah mamee " Faɗi maganarka inajinka matuƙar baifi ƙarfinaba zanyi maka koma menene "Mamee inason yau aɗaura min aure da Hajara dan Allah" "Wannan ce alfarmar "? "Inhar nina haifi Hajara sani nabaka aurenta kariƙeta amana kazamar mata uwa , uba, dangi, daduk wani abu data rasa " "Kekuma takalli Hajara kiyi masa biyayya dan Allah kizamar masa mace ta gari abar alfahari ako ina " Kasan batada dangin mahaifi kona mahai fiya dan haka kakiramin malam liman na gidannan yazo ayi muku jagora, "Bansan dalilin ka nason auren Hajara ba kuma ayau bazan tambayekaba amma kasani kai marayane itama ahalin yanzu tazama marainiya kaine uba, yaya,Kani ,Kuma miji agareta, kaine bangonta ayanzu, kareeƙe alƙawari dan Allah sani karka canza da gayanda nasanka kaji " "Namiki wannan alƙawarin insha Allah zakisameni mai cika alƙawari " "Ya Sani dan Allah karka aureni baka sona Please indai ƙaddararda tasame nice yasa zaka aureni wallahi nayafe kuma nagode da kulawarka agaremu amma ni bazan aurekaba " Hajara ce ke wannan maganae cikin kuka mai ban tausayi Mamee ce ta kallesu cikin rashin fahimta, kantasamu damar magana Sani yarigata dacewa "Ƙaddarar maraici ai bake kaɗai ce marai niyaba kawai inasonkine tunkafi zuwan wannan abin dan Allah karki sake cewa komai Hajara wallahi harcikin raina nake sonki..." Ababban masallacin anguwar aka ɗaura auren Sani Muhammad Kebbi da amaryarsa hajara Abubakar Kamba akan sadaki naira dubu hamsin lakan ba ajalamba. Bayan ɗaurin auren da kwana biyu sani yasamu kiran gaggawa daga London, hakan yasa yashirya yatafi yabar mamee da Hajara. Tafiyar sa da kwana biyar Mai Hadi yaysin vci yar akofar gida tare da wasika,bansan me wasikar ta kunsaba Amma sun rike yarone ,suna kiranshi da Haroun Aikin da sani yajeyi yasamu nasara hakan yasa suka riƙesa tunyana tunani nadan lokacine haeya gaji. Nan yaƙira mamee yashaida mata garanar dawowa dan haka yaturo musu da komai su shirya zuwa jibi za'a kaisu Legos sushiga jiri suzo. Mamee kan tace ita ba inda zataje matarsa dai nanan zuwa kasan cewar sun sanar masa da yaron hardashi zuwa "Mamee Haroun fa dan Allah kibari suzo tare koya samu ingan taccen karatu ..." Dakyar dai ta amince Haroun yabi hajara amma itakan ba inda zata.. Kamar yanda rayuwa ke gudu tana juyawa tamkar juyawar gudun agogo haka rayuwarsu tajuya Sani yasamu ƙarin girma a wajen aiki koda. Yabiyawa mamee kujerar haji dashi kanshi . Hakan baƙaramin daɗi yayiwa Mamee da Hajara ba yakoya mata sonshi da ƙaunarshi duk wani abu datake gudun faruwarsa akan rasa budurcinta datayi yakau domin tunranarda taje London sani ke bata wata riyar kulawa tamu samman wadda bata taɓa mafarkin samuba.. basu Wani jimaba yabiwawa mamee kujerar hajji F🌹 A 🌹K BATOOOL KAMBA ✍️Alƙalami yafi takobi 🗡️ Typing 📲 https://chat.whatsapp.com/Gn6wOkxz4N6KBN3JbMkPiZ?mode=ems_copy_c SON KI NE ƘADDARA TA 🌹Your love is My destiny 🌹 STORRY & WRITING BY FATIMA ABDULLAHI BATOOL KAMBA 2️⃣3️⃣&2️⃣4️⃣ ____________________________✍️ Sunje aikin haji sundawo lafiya sosai Mamee ta roƙawa Hajara samun ƴaƴa masu albarda , Dasamun ɗaukakar Sani. Allah kuwa ya amshi addu'ar ta domin cikin ƙan ƙanin lokaci sani yazama masha hurin maikuɗi wanda duk faɗin Nigeria bawanda baisan daza mansaba... Matsalar ɗayace haryau dasuke shekara uku da aure Hajara bata taɓa ko ɓatan wataba.... Tun abinna damunsu har suka fauwalawa Allah komai kullum Hajara nakukan rashin haihuwa, haka Sani zaita rarrashinta , yana kwantar mata da hankali,.... Yauma zaune take kan dining table ta tasa abinci agaba sai kuka take shigo warsa kenan yahangeta hakan ysa yanufeta cikin rarrashi yafara magana ... "Please kidaina sawa ranki damuwa my hajar kinsan aure, arziƙi,mutuwa,haihuwa duk lokaci garesu kinmanta ko Mamee tadaɗe batasamu hai huwaba saidagabaya Allah yabata kisawa ranki salama mana uhmm ..." Idonta ciketab da hawaye takalleshi harzatayi magana yagairgi zamata ka alamar tayi shiru nan yashiga ciyar daita dakansa harta ƙoshi yakalletà kokefa tawan, kinsanme? Yayi tambayar yana kallonta a'a kemafa inaganin wannan shekarar dake za'ayi aikin hajji. Wani irin ihun murna tayi tareda ƙan ƙameshi tanazuba masa godiya, ɓata fuska yayi Kafin yace "Mena godiya banason hakafa Please kidaina, komai nawa ai nakine " Hakarayuwa tacigaba da gun gurawa akwana atashi bawuya awajen maiduka. Barina leƙo muku ya Sani da Hajara suke Zaune suke parlour yanayi mata matsar ƙafa , waro manyan idanuwana nayi waje ganin ta zaune kan two seater sani na durkushe agabanta yana mata tausa cikeda so dakuma ƙauna haɗida tsan tsar kulawa Kallonta yayi cikeda so da ƙauna yace my hajara baki faɗamin wane suna ne za'a sanyawa baby ba. Ɗago dakai tayi tasauke idanunta anasa kafin tace idan Mace Habibah nakeso Dasauri yatari numfashinta dacewa "inkuwa namijine sunan baba doctor ko? " "A'a marwan nakeso, cos inason sunan sosai." Murmushi yayi " kamar kimce wani abufa domin sunan yayi sweet sosaifa ririn sosai ɗinnan " yafadi yana kanne mata ido ɗaya. " Yauwa kinsan zamuje Nigeria jibi cos mamee tadameni wainakawoki kihaihu gida to Allah ƙafata ƙafarki tare zamuje ko my hajar? " Ehmana my sani kosokake naje nakasa samun natsuwa, amma mufara bi ta kano muhuta ko yakagani? "Waike menene haɗinki da kano?" "Kawai inason zuwane Please my Sani" "Ok zamuje ammafa two days zamuyi saimuwuce kebbi " "Bakomai saimubarshi gidan dady sadeeq koya kagani? "Eh hakanma za'ayi" # Aminu kano International airport# Tuda suka sauko hajara kecemasa yanema musu motar haya amma yaƙi datagaji dole taja bakinta tayi shiru Wata dalleliyar motace tayi parking agabansu kafin hjara tace komai yabuɗemata gidan baya bamusu tàshige shima zagayawa yayi yashiga Rigiyar lemo awani kata faren gida motar tayi parking kasancewar ba gateman agidan driver neyafito yaboɗe gate ɗin kana yakoma yashiga motar saida yayi parking kafin sufito mamaki takeyi " wannan gidan waye kokasan wanine a kano ?" Murmushi yayi baice mata ƙalaba sanda suka ƙarasa tukun yace "kifara hutawa, kiwatsa ruwa, kici abinci zanmiki bayani yanakai nan yashiga wani ɗakin. Saida tayi duk abinda yace tadawo perlou tazauna jim kaɗan shima yafito "Tinkan tayi magana yace gidankine kenasiyama, kuma zakiga ƴan aiki zuwa gobe cos nasan kina son zama a kano bansan dalilinba shiyasa nasiya miki gida.. Cike da mamaki take kallonsa harta buɗe baki domin yimasa godiya yayi saurin katseta dacewa " Banason godiya idan nayi miki abu tamkar nayiwa kainane so Please banaso . Fashewa tayi da kuka "taya zanrama maka wannan alkairan dakake yimin" Kuma fa sake katseta yayi nace miki banaso Please kidaina kinji kukan name nene uhumm Rarrashinta yayi tukun suka fara fira cikin so daƙauna ... *********Wayace a han nunta sai faman kiran layin sani takeya ama baiyi picking ba agala baice tamayar da akalar kiranta ga P.A ɗinsa shima saida tayi masa five miss call kafin yayi picking Assalamu alaikum yayi mata sallama, bata samu damar amsa masa sallamarba sabida gala baitarda tayi, saima ƙoƙarin magana take amma takasa buɗe bakinta, nishinda yaji tanayine yaɗansa yatsagaita, jinhar kusan minti Uku batayi maga naba saima salatinda yaji tanayi yaruɗashi "hello hello mada kina jina hello" dakyar tace Please dady help me zanmutu ina shi maigidan naka, dan Allah kuzo karna mutuuuu" dif yaji bataƙara maganaba ai awani irin ruɗe yafaɗa hool ɗin direct yanufi sani dake yin jawabi kasancewar shi baƙo aewan, Tunda yahangi P.A ɗin sa afujajan yasan balafiya, tinkan yaƙaraso yanemi excuse . Sir madance takirani tana nishi inajin balafiya saboda naji tanacewa natai maketa zata mu Tinkan yaƙarasa yayi saurin barin waje direct motarsa yanufa securiti's ukune agefen motar suna hangosa suka buɗemasa yanashiga driver yaja suko sukashiga motarda kebayansu, dagudun gaske sukabar wajen, koda suka isagidan baijira angama parking ɗin motarba yaɓalle murfin yafito dagu yashiga gidan yana kwala mata kira tamkar maƙogaronsa zaiɓalle "Hajar! Hajar !! Hajar!!! Kina inane? " Dagudun gaske yake haura matattakalar benen cikin hatsamnacin tashin hankali yakebin jininda yagani da kallo rarraba idanuwansa yafarayi,canyahangota kwance sharkaf kamar gawa, dasauri yaƙarasa wajen baitsaya wani ɓata lokaciba yasa hannu ya cicciɓota yafito yana kwalawa P.A ɗinsa kira harya sakko yanufi compound ɗin gidan, securiti's naganinsa sukabuɗemasa gidan baya nasanyata shima yashiga a 360 sukabar gidan Kyakkyawar hospital ce privet nan take akakarɓesu akawuce da'ita labour room. dukyanda doctor's sukaso cetan rayuwarta abin yafaskara bayan tahaifi santalelen ɗanta kyakkawa jini ya ɓalle mata dasauri ɗaya daga cikin doctor's ɗin wani yafito yana neman Sani, jiki narawa sani yashiga ɗakin, ganin halinda takecikine yasa yafashe dawani matsanancin kuka kamar wani yaro ƙarami Kallonsa takeyi agalabaice yace "Dan Allah kayafemin karoƙarmain mamee tayafemin nasan bazan rayuba kakulamin da abinda nahaifa . Cikin kuka Mai hade da shash sheƙa yace "bazaki mutuba Please karkimanta namiki alƙawalin zanrayu dake nahar abada" Murmushi tayi kafain tace "bazan rayuba naji hakan ajikina". fatana kasamawa abinda nahaifa uwa tagari wacece zata nashi tar biyyaaa tanakainan tafarayin malmar shahada yanajin haka yashiga girgizamata kai hannunsa dake cikin natane yaji yasake alamar rai yayi halinsa sandarewa yayi kukanma yatsaya cak Wata iriyar ƙara yasaki yana kiran doctor's gabaki ɗaya yafita hayyacin sa haƙuri doctor's ɗin suka shiga bashi P.A ne yayi ƙarfin halin kiran mamee yace tazo kano balafiya kasan cewar tasan suna kano nan tashiga kiran driver domin itama bata Kebbi tana kd wajen auren ƴar wata ƙawarta nan take sanar da ita P.A ɗin Sani yakira kuma dadukkan alamu balafiya Nan hajiya nana tasanya driver yakaita kano , koda taisa har sunkoma gida sani natakuka kamar maxe duk yafice hayyacin sa tundaga bakin gare taga mutana sosai tacika da mamaki domin satinsu ɗaya ne a kano kodai hajara ce tahaihu tinda yaukusan kwana uku da wucewar edd ɗinta a compaund ɗin gidan motar tayi parking dasauri tafito tindaga shigarta parlour taga mutum an lulluɓe da fari ƙalle sosai tashiga firgici yayinda tahangi sani zaune gefen yana sharɓar kuka ga jinjiri riƙe ahannunsa shima sai callara ihu yake ..... Taku harkullum F🌹 A🌹 K 🌹 BATOOL kamba *SON KI NE ƘADDARA TA* 🌹Your love is my destiny 🌹 STORY & WRITING BY FATIMA ABDULLAHI {Batool kamba} _________________________________________________________________________________________________________✍️ 25& 26 _________________________________________________________________________________________________________ Ƙarasawa tayi gaban gawar nanta durƙushe cikin matsa nancin tashin hankali take ƙoƙarin buɗe fuskar wasu siraran hawayene ke gangaro mata lokacinda tayi arbada Hajara matsayin gawa share hawayen tayi tanamai kwara rowa ƴar tata addu'o'i saida kamma yimata addu'a sanan wasu mutane suka shigo aka kamata akafita dan asallaceta. Bayan ankaita makwancinta sundawo anan akashiga ƙarɓar gaisuwa gashi bawani jimawa sukayiba amma hajara tasami mutane sosai . Ranar sadakar bakwai aranar akasawa yaro muna Marwan. Bayan sadakar arba'in Sani yashirya don komawa London wajen aikinsa amma mamee tace saodai yaje shikaɗai bazata bashi jinjiriba yatafi uwa duniya dashi bayanda yaiya haka yakoma . Bayan shekaru Uku Haryau sani baisake yunƙurin wani aurenba yadai samu ya rarrashi mamee tabashi marwan suntafi London yasanyashi a school, shima Haroun yaji daɗin zuwan Marwan cos inhar sani yaje gun aiki sai magrib yake dawowa gida, shiko Haroun mutunne maison hayaniya, gashi dagashi sai nany dinda aka Samar masa Marwan yarone marajin magana sosai kuma gashi da ɗanbabzan surutu hakan yasa suka ƙulle da Dan uwan nasaɗinnasa . Mamee naƙoƙari wajen ganin sani yasake aure amma fur yace shi yagama aure . Abin mamakin kosati ɗaya baiyi da maganarba marwan yafara takura masa ina momeensa . Sometimes idan yadameshi saiyace tana Nigeria awane garinee dady a kano ko abuja hakazaita tambayarsa Watarana sani bayanan shiko Haroun baidawo daga school ba marwan na dawowa nany ɗinsa tamai wanka yaci abinci, saida yabari takoma khiching yasuɗaɗa yafita securiti's sam basu lora dashiba harya fice daka gidan Tashin hankali. Lokacin da Haroun yadawo yake tambayar nany ɗin tasu ina marwan dan yaduba badroom ɗansa bayanan kuma yadoba toilet nanma baigan shiba Wasa wasafa ba'aga Marwan ba nan akakira sani ana shaidamasa baimajira Haroun yaƙarasaba yakatse wayar yanufo gida yana kan hanyar ne doctor sadeeq yakirashi yana faɗamasa marwan na inane ," please doctor kodai yana hannunka? " Kamarya daga tambayr yaro saikatuhu meni sani najin haka yajuya akaral matarsa zuwa gidan doctor sadeeq nan yatardda marwan zau ga kayan sweet nan agabansa saiwasa yake hankalinsa kwance Doctor neyafito yana kallon yanda sani ke kallon Marwan . "Dadyn boy yane" doctor sadeeq yatambayi sani cikin shaƙi yanci irin na abokai Ƙaraso ciki mana kawani tsaya daga bakin ƙofa Ƙarasa shiga cikin perloun yayi bakinsa ɗause da sallama Follow this link to join my WhatApp group 👎 https://chat.whatsapp.com/CJPOk88Ckuw8zFUcXRbuoN "Assalamu alaikum " "Wa'alaikas salam " Doctor sadeeq ya amsamasa "Doctor please dan Allah a’ina kaga boy ? " "Kabari kasha ruwamana doctor" Saida yazauna shima doctor sadeeq yazauna kafin doctor yafara magana "Doctor sani ksan meke damun boy harafito dakà gida? " Girgiza kai sani yayi alamar A'a Doctor sadeeq neyaɗaura dacew Uhumm Sani wanna yaron nabuƙatar mahaifiya akusa dashi nany bakamar uwa bace musamman wadda baƴar Africa ba nahaɗuda boy anesa daginka kaɗa yazauna saikuka yake yana kiran momee, nayi rarrashinsa amma yaƙi shi adole akaishi Nigeria gun momeensa doctor kai kanka kana buƙatar mace akusa dakai , Hajara tarigada tatafi kuma bazata sake dawowaba , ldan da Allah bai kaini anguwar takuba harna boy mekake tunanin zaifaru? Shiru yayi saican yace doctor banaƙi aure bane banason boy yatashi cikin tsan gwama kamar yanda muka tashi shiyasa kaga nahaƙura da Aure amma insha Allah zanyi tinda shi yanaso zaiyi masa momai danyasami farin ciki . # Bayan wata shida Doctor sani yashigo parlourn gidan hannunsa riƙeda na marwan, wata farar macece ke zaune a parlourn tinda tahangesu take zabga Murmushi . Sam marwan bailura da idaba juyowarda zaiyi sukayi four eyes dagudun yaƙarasa yana faman zabga mur mushi, itama rungumeshi tayi tana cewa "oyoyo my boy" harkun dawo kyaɗamata kai yayi alamar eh shima sani ƙarasowa yayi nanacewa kinga boy ɗin ki koki kulani yayi maganar cike da zolaya ahaka rayuwa tacigaba da gun gurawa cikin farin ciki hajiya Ruƙayya matar sani wato mom ƴar asalin garin kano ce marainiyace ahannun kawunta tatashi dakawunta da baba doctor aminaine sosai sani yaje gaidashi lokacin dasuka je Nigeria shine yaganta anan dai suka daidaita harya aurota mamee tayi farin ciki sosai da sani yayi aure , Bayan shekara shida itama mommy tashare shida zuwa bakwai haryau balabarin ciki bale haihuwar sutun suna damuwa har suka fwwa lawa Allah daga karshe suka yanke shawarar zuwa gidan marayu suyi addoting na ya mace tunda Allah ya bazu mazan har biyu Nigeria sukaxo gidan maratyu uka nemi Alfarma Kuma alhamdu lilah sun samu Haka suka rika renon yayan su uku cikin so da kauna da kulawa da MUSAMMAN .. # Dawowa labari💫💫 Cikin tashin hankali yake kaikawo , bayanda ba'a yida dady ba akan yzauna amma yakasa, kusan two hour sannan wani doctor yafito yana sharce gumin dake gishinsa . Dasauri dady yanufesa yana Tambayar ya jikin boy ɗin? Cikin kilawa doctor yace sir kabiyoni office yana.faɗin haka yayi gaba Bayan sunshiga office ne doctor yace sir wai ita wannan yarinyar batarayene daharyau ankasa samun koda labarintane? Yanzu duk bawannanba yajikin boy ɗin? Coll down your mind Sir yasamu barci yanzuhaka amma maganar yarinyarfa? "Bansaniba doctor nikaina abin yagirmi tuna nina boy bai iya sanya abu araiba tunda naɗauko yrinyae nan gidan marayu yaƙwallafa ransa akanta ada ina ɗaukar abin kamar wasa saida yatabbatarmin ita yakeson aura dafari, taƙiyarda bansan dalilin ta na amincewa dabayaba ashe danta haukatar min da yarone nakasa yarda guduwa tayi doctor duk irin nanda mukeyi mata sam bawandayazo mana dabayanin komai kama da ita abinda kebani mamaki doctor duk photunan tabakoɗaya abaya boy yace idan yazana photo ɗin fuskarta saiya goge to kwanaki yacemi wai kwaran kwalma photo yakoma , narasa samun solution nawannan ƙaddararren so {sunan sabon book ɗina dazafito amma nakiɗine } Nisawa dady yayi cikeda shakku yace sir koza'ayi malamarin nan duban tsanke , nisainake gani kamr da sihiri awannan lamarin .. Nayi yunƙurin yin hakan amma nakasa narasa dalilin amma insha Allah zanyi iya ƙoƙarina ,, # Maryam Tunda suke tafiya amotar takasa sakin jikinta, sosai tsoro yakamata ganin sun ƙaraso wani ƙaya taccen hotel dama yariga dayayi boking ɗaki kaitsaye sukanufi ɗakin jikin ta ko'ina yayi sanyi gatsoronan yabayyana ƙarara atareda ita bayan sunshiga ɗakin yacemata tazauna shi zaishiga bathroom yawatsa ruwa yafito Abin mamaki kusa 1 hour dashigarsa amma yaƙi fitowa gajiya tayida jira hakan yasa tanifi ledojinda yasa akayomusu odaring abinci harta kammala cin abincin baifitoba 1 hour tasake shuɗewa nufar bathroom ɗin tayi jikinta duk amace taɗan kwankwasa taji shiru kusan minyuna biyar tana bugun ƙofar bathroom ɗin amma shiru hakan ysan taɗan tura tare daleƙawa jikinta narawa tashiga rarraba ido taga ta inda zata hangoshi Tashin hankali! Wani irin faaɗuwa gabanta yayi rasss rasss ganinsa kwance cikin jini babu alamar rai atare dashi , ƙarar buɗe ƙofa taji dasauri tajuya danganin kowaye police tagani kisan guda biyar , kaitsaye suka tunkareta da bindiga tsabar tsoro daruɗu batasan tasaki fitsari atsayeba Koya Maryam zatayi dagawar alhajin manya oho? toma waya kasheshine? Kozata samu taƙuɓuta kokuwa alhakin kisan alhj surajo yahau kantane ?😢 Kukasanceda Da F🌹A🌹K 🌹 BATOOL KAMBA🌹 Kibiyoni dan samun waɗannan amsoshin naku a https://chat.whatsapp.com/Gn6wOkxz4N6KBN3JbMkPi Z?mode=ems_copy_c 🌹𝙎𝙊𝙉 𝙆𝙄𝙉𝙀 𝙆𝘼𝘿𝘿𝘼𝙍𝘼𝙏𝘼🌹 𝙎𝙩𝙤𝙧𝙧𝙮 & 𝙒𝙧𝙞𝙩𝙩𝙞𝙣𝙜 𝘽𝙮 𝙁𝙖𝙩𝙞𝙢𝙖 𝘼𝙗𝙙𝙪𝙡𝙡𝙖𝙝𝙞 𝘽𝙖𝙩𝙤𝙤𝙡 𝙆𝙖𝙢𝙗𝙖 Page 27&28 Ganin yanda ta tso race yasa plolice din daka tawa da yun kurin isa inda take macen cikin sauce tafara magana tasigar da zata fa hinta, all ready an kama kmaashin, amm a Zaki biyomu office Zaki amsa wasu tamba yoyi , tana gama faɗin haka ta tasa ke yarta suka tafi.. 💐💐*BAYN KWANA BIYAR *💐💐 Qutty !! "Kitashi mana wanna wane irin barci nekike haka bayan kinsan kinada baki " Mika tayi tare da hamma tamike zaune tana cewa "hajiya wai har takwas din tayine "?Eh mana harta gota dubi agogo kiga. "Allah anty haryau idan nakwanta sainayi mafarkin kama ninda akayi" Kyaji dashi cewar hajiyar tanayin gaba Shirye tafito cikin rigada wando, wandon tait ne sosai ,sairiga iya gwuiwa . Taciwata uwar kwalliya tamkar wacce zataje gasar kyau, kaitsye gofar gidan tanufa . Wata dalle liyar mota fake agofar gidan kaitsye taahige ciki batare da bata lokaci ba matukin motar yafizgeta dakarfi suka hau titi waini Baki bani labari yanda kika tsiraba ahan nun yansanda , kinsan yan sandan Niger bakamar Nigeria ba Bakama saniba waifa sun san banida laifi Amma Saida nakwana acan Kumafa Saida suka nemo hajiya wai tayi belina itako tace lalalala "Ban bido mata kudiba bazata kashe minba In ta Kai ce maka Saida Wani allajin yayi belina da sharadin zantayasa kwana daganan har ranarda zai koma dan bakone ". Uhhhmmm kasan Yana gudu daga hanun sa ? harmunje hotel room dinda Yana shiga toilet nadudu Lallai Maryam Amma kinsan yauda gone tafi garfin wasa dole wata rana asamu akasi "Uhumm shiyasa nabiyoka ai , sonake kasa mamin jirgi Dan bazan bi motaba Dagas ke kike ko wasa ? dagas ke mana toyaza kiyi dani ? "Kamar yaya kenan ? haba mana Maryam kinsanfa ina matukar sonki yaki keson nayi ? audama dagas ke kake ? Hara rarta yayi kafin yace a a wasane Allah sarki ni duk soyayyar da zanyi tadan Loka cice Dan Allah Maryam kifahimta . Uhumm narasa mezan cema nasandai yau Kwa nanmu biyu da haduwa ya kakeson nadau wan nan nakasa gane me Nene ainahin gas kiyarka , bayan haka taya zamuyi soyayya ? Kaman tane bansan kowa nawaba, banida dangi, banida ahali, banida kowa taya zanyi wan nan gan gancin. Wani raza nan nen kallo yayi mata kafin yace me kike nufi ne waya gayaiki bakida dangi bakida ahali kowa ne Dan adam danasa Kalar kaddara danhaka kidaina cewa haka kinsan bawa baya wuce zanen kadda rarsa Dan Allah Maryam kifahimta kibani damar shiga rayu warki "Kayi hakuri Fu'ad bawai nakika bane a a Duba kaga kalar rayuwar danake , sanin kankane daba cewa kayi zan taya kwana bane hajiya bazata barni nafito ba please kafahimta mana kaima Haka zakace kana Sona kalli rayuwar danake " Kinga basai kinmin Wani kwana kwana ba kawai kice kinfi karfina nahakura . "Nagode dawan nan cin mutun cin Allah yasaka maka da Mafi ficon alkairi" Bawai cimutunci bane Maryam kifahimta mana ina sonki ne tsakani da Allah kinsako dole naji badadi tunda kin nuna bakya bukata ta Shiru tayi nadan Wani lokaci kafin tace" kasanme ? A a sankin fada iya yenka zasu bari ka auri wace batada asali, batasan kowa nataba , Batada tabbaci ita wa Cece Kuma tayi zaman gidan karuwai, ? bakowa zai yarda bantaba aikata zinaba saboda Nazauna gidan karuwai , kayi tunani sosai kafin kayanke hukun ci please kajii". Shiru yayi nadan lokaci kafin yace "Banida matsala da dady na saidai mom zataji abin Wani iri so Zan fahim tarda ita insha Allah Parking din motar yayi bakin Wani kata faren botic na sayayyar kayan makulashe Bismillah my qutty Mumushi tayi San nan tafito daga motar " Mezan muyi anan please banaso hajiya fa tasan zan gudune, kasan bazata rasa wa yanda ke San yamata Ido akaina, nalura tana shakku akaina . "Muje " Kafin tace komai yayi gaba abinsa batada zabi haka tabi bayansa dukda yanda gaban ta ke Wani irin faduwa 🌹Abuja Nigeria 🌹 Marwan kasamu Kaci abinci ko yaya ne sai kasha magani please mana my friend. daddy ketayiwa Marwan wan nan magiya tun bayan Farka warsa yaki cin komai , yaki magana , yaki kallon kowa Bakaramar damuwa yashiga ba ganin yanda tilon Dan nasa yakoma saboda mace Sosai yake tausayawa Dan nasa Dan yanada tabbacin duk inda Maryam take batadarai Bakalar cigiyar da Bai bayarba tun daga gidan tv radio gidan jaridu mujallai dasau ransu yasanya makudan kudi gaduk Wanda yasami Koda labarin ta amma shiru malam yaci shirwa bawanda yace ko Mai kama da ita ya taba Gani balle ita. Kaga my son kayi hakuri kasan bawa baya wuce kadda rarsa Wan nan abinda kake ba mafi tabace zaka iya rasa rayuwar kafa kamanta abinda doctor yace kana matakin karshe nefa Dan Allah kasas sautawa kanka idan darabon aganta za aganta kasan matar mutum kabarin sa dan Allah Marwan mana.. Sassanya num fashi yasauke tun alokacin da dady yafara magana yaji yasami Sa i da dakyar sannan yace "daddy bakasan kalar azabarda nakeji anan dina bane" yafara Yana nuna saitin zuciyar sa. Karika nanata hasbanallahu Wani imall waqill Allhuma ajirni fimusi bati waaqqilni kairan minnhaa Kaji kyada Kai yayi alamar Eh yaji Bayan sati daya aka sallamesu tun lokacinda aka kawoshi mommy bata sake taka kafarta asi bitin dasunan dubashi ba abin yayiwa daddy ciyo amma bai nuna mataba, kasan cewarsa mai hakuri . Cikin tsananinso da kauna yake nunawa Marwa kulawa ,hakan yadan taemaka masa sosai amma dukda haka radadin zuciya da kincinta bai barsaba . Tafiya takama daddy ta gaggawa bayanda baiyi da Marwan ba yazo sutafi kozaisha iska yadan huta amma yaki saima cewada yayi hala shi yarone da duk inda yaje sai yabishi "dan Allah daddy kayi tafiyarka zan iya kula dakaina ". "My son kayi hakuri muje ina fargabar barinka anan ". "Hadai daddy kamarwani jaririne ni katafi kawai idan naga bazan iya zamaba zan je wata kasar nahuta insha Allah " kayi alkawali ? Insha Allah daddy" "Shikenan Allah ya rufa asiri my son" amin daddy " Muje karakani air port kaji , kyada Kai yayi alamar to San nan yamike jalla biya kawai yasauya daga ash dake jikinsa zuwa fara, atare suka fito dama shi daddy nashirinsa tana hakimce parlor kan one siter, tadora kafa daya kan daya , han nunta rike da robar dabino tanaci ganinsu, baisa ta motsaba balle tayi wani yun kurin kallaonsuba balle susanu arzikin magana . "Mommy zanraka daddy air port nadawo" Allah yakiya yeminkai my son " wani lokaci mommy nabashi mamaki saitayi abu kabar batadamuba saikuma yaga kamar tadamu dashi abin na dauer masakai . Kadawo dawuri kaji my son ,to mommy insha Allah. Kokallon daddy batayiba Shima baice komai ba ya fice Wata ran tsats tsiyar mota suka shiga securities natake musu baya , motocine na alfarma uku gaba uku baya sune atsakiya Cije le'bensa nakasa yayi dasauri daddy yakallesa lafiya kuwa my son kayi ahankali fa dan Allah karage tunani sosai kasan condition dinkafa ba____ "daddy bafa wata matsala bace dan Allah ka kwantarda hanka lilnka " "My son Allah ma shaidane inajin tsoron tashin ciyon ka wallahi " Insha Allah bazai tashiba daddy Zaitashi inhar baka rage sawa kanka damuwaba .. Maryam sannu ahan kali take saukowa daga matat takalar jigi sai wani uamutsa fiska take alamar agajiye take taxi ta tare tare dashigewa tana zama wani zazzafan hawaye ya kufce mata tasani sarai bawajen kowa tazo a Abuja ba batasan mayanzu inda zata nufaba .. Hajiya inazamuje Saida tadanyi shiru kafin tace restaurant zaka kaini mai kyau, tafadi hakane saboda wata aza babbiyar yunwa takeji Hajiya Zara'u special restaurant abinda ta iya karantawa kenan bayan mai taxi yayi parking Saida tasalla meshi sannan tashiga cikin, zama tayi kan daya daga cikin kujerun wajen wayanda suka zagaye table, daya daga cikin ma aikatanne ya iso wajeta yatambayeta Meza a kawo hajiya? Faten doya nakeso akwai ko babu? Akwai " to kawomin Ruwaza akawo ko "Exotic " okay ma Bayan tacika cikin tane tafara tunanin inda zata dosa, ma aikacin wajen ne ysake da wowa zai dauke pleat , wata dabarace ta fado mata dasauri ta kalleshi , " ammm naceba " Inajinki " Dan Allah mai wurin nan fa "? Meza zata yi miki ? Dan Allah kahadani da itamana Bari nayi mata magana " to nagode Bayan minti biyar yadawo taso muje , mikewa tayi tabi bayanshi wata yar mata shiyar mata hakimce kan kujera , saida suka gaisa sannan Maryam tafara magana " Dan Allah hajiya kidaukeni aiki Koda wanke wankene dan Allah kite makamin kamar yadda Allah yate makeki, kirufamin asiri kamar yadda Allah ya rufa miki " Kallon tsaf hajiyar tayi mata kafin tadan numfasa tace Ina iya yenki ? "Banida kowa iyayena duk sun mutu ina hannu wani kawuna ne , shine yaturoni aikatau " Tazabi yimata wan nan karyarne saboda bakowa zata fadawa ainahin ita wacece ba Meyasa shi kawun nakibai kawoki da kansaba ? Nima bansani ba dan Allah karkice bazaki daukeniba hajiya Dan Allah Shikenan Zaki fara aiki yanzu dafatar kin shirya ? "Insha Allah " Zaki rika tarbar masu shigowa kiji " naji hajiya" Bari na fada miki dokokina idan kin kiyaye zamu zauna ply dake. Banason kazanta, banason bata lokaci, banazama da maci amana, bana zamada 'barawoIdan kin kiyaye banada matsala . "Zan kiyaye da izinin Allah" Yafara aikin kamar yadda hajiyar ta Umar ceta Marwan Son muje restuarant naci wani abu inajin yunwa sosai wllh cewar dadi cikin yamu tsa fiska To daddy muje amma bari akai mu inda nake zuwa ta iya abinci sosai wllh okay Bayan sun shiga wajen sun zauna securities zagaye dasu sukayi oder Tunda suka shigo yakejin Wani rin fillings dabai taba jiba yakasa fassara yanayin ga wani irin mugun bugawa da zuciyar sa keyi wanda ya wuce kima Maryam ce dauke da ture zata Kai VIP tunda ta tunkari wajen gabanta ke faduwa har jikin ta na rawa 💃 𝕞𝕠𝕣𝕖 𝕔𝕠𝕞𝕞𝕖𝕟𝕥 𝕞𝕠𝕣𝕖 𝕥𝕪𝕡𝕚𝕟𝕘 𝔸𝕝𝕜𝕒𝕝𝕒𝕞𝕚✍️ 𝕪𝕒𝕗𝕚 𝕥𝕒𝕜𝕠𝕓𝕚🗡️ *💋SONKI NE ƘADDARTA*💋 ʂƚσɾყ&ɯɾιƚιɳɠ Ⴆყ Fateemah Abdullahi /Ⴆαƚσσʅ ƙαɱႦα/ Page 2️⃣9️⃣➡️3️⃣0️⃣ Meyasa shi kawun nakibai kawoki da kansaba ? Nima bansani ba dan Allah karkice bazaki daukeniba hajiya Dan Allah Shikenan Zaki fara aiki yanzu dafatar kin shirya ? "Insha Allah " Zaki rika tarbar masu shigowa kiji " naji hajiya" Bari na fada miki dokokina idan kin kiyaye zamu zauna ply dake. Banason kazanta, banason bata lokaci, banazama da maci amana, bana zamada 'barawo Idan kin kiyaye banada matsala . "Zan kiyaye da izinin Allah" Yafara aikin kamar yadda hajiyar ta Umar ceta Marwan Ajikin daddy barci ya sacesa amota Son muje restuarant naci wani abu inajin yunwa sosai wallhi cewar dadi cikin yamu tsa fiska To daddy muje amma bari akai mu inda nake zuwa ta iya abinci sosai wllh okay Bayan sun shiga wajen sun zauna securities zagaye dasu sukayi oder Tunda suka shigo yakejin Wani rin fillings dabai taba jiba yakasa fassara yanayin ga wani irin mugun bugawa da zuciyar sa keyi wanda ya wuce kima Maryam ce dauke da ture zata Kai VIP tunda ta tunkari wajen gabanta ke faduwa har jikin ta na rawa , addu a tashiga yi ba kakkau tawa assalamu alaikum tayi sallama cikin mutuwar jiki da sanyin murya Wani irin mikewa yayi yana kallonta, kanta aduke batasan meke faruwaba Saida taji yakirata cikin wani yanayi dabazata tan tanceba Dagokanta tayi cikin sauri Wani wawan jirine ya kwaceta nan take tasilale kasa su mam miya , Maryammm!!!! "Dan Allah karkiyimin haka please kitashi my sould inada bukatarki arayuwa ta" Magana yake tamkar zau tacce yakasa karasawa inda ta kuma yakasa daina magana , daddy datun lokacin da Marwan yafara magana ya kame yakasa motsi Saida yayi tamaza San nan ya mike yanufi inda Maryam take a kwance , Dasauri Marwan yakarasa yatallafota zuwa jikinsa Yana jijjiga ta Please my son could dawn mana abi komai ahan kali please Baimasan daddy na maganaba daukanta yayi yanufi kofar fita da ita dasauri securities suka bi bayansa suna fitowa hajiya na Kara sowa dan taji yar haya niya na tashi Lafiya kuwa Sir lafiya balauba bari muje dake yarin yar ta suma zan miki bayani acan ba time yanzu Bamusu tabi bayansu , ko acikin motar ajikinsa ya Kwan tarda ita sai jijjiga ta yake daddy please kace ta tashi dan Allah itace rayuwata daddy itace munfashina. Specialis hospital suka kaita nan take aka shiga emergency room da ita, sunshaya kusan 1 hour kafin sufito da ita dasauri Marwan yasaha gaban likitan "Yajikin nata,Tafarfado ? " Aa amma nanda 30 minutes zatafarka Wani sanyin dadi yaji kamar wanda aka bawa kujerar makah . Firgigit yafarka daga guntun barcinda ya kwashe shi amota 😃 Har sun iso airport bai saniba "Muje mana " daddy yayi maganar cikeda kulawa . "Daddy wai mafarki nayi kodai da gaskene ? "Anga my soul ne ? "Aushe , munafa tare dakai , kodai mafarki kayi ne " ? "Wata kila ". "Bakama tabbatar ba kenan " ? "To mafarki kayi My son ni na tabba tarmaka fito muje " Maryam Yau kimanin sati d'aya dafara aiki a restuarant na hajiya Zara'u, matar akwai Karam ci da mutunta jama'a, lafiya kalau suke zauneda Maryam idan sun tashi daga aiki gidan hajiyar take zuwa takwana bakyara ba tsan gwama hajiya Zara'u akwai zuciyar tausayin mutun ko kadan batada wula kanci Duk lokacinda tatunada Papa saitayi masa addu'ar alkairi, itakuwa baba hadiza takan yimata addu'ar shiriya. Yama kamar ko yaushe idan sun dawo daga restuarant sukanyi zaman Hira itada hajiya Zara'u , sunahira kawai taji kantana juyawa wasa wasa abu yazama babba don kan kaceme tarikice bashiri hajiya Zara'u ta nemi temako sukayi hospital da ita Koda doctor yadubata yake cewa hajiyar Inaganin ciyon nan nata bana asibiti bane, kugwada kaita gidan malaminda ke rukiyya zaifi Baki ahangame hajiya Zara'u ke kallonsa "doctor kodai tanada Aljanune ? To gaskiya bansani ba amma kugwada kaita inda nace , Marwan yau kimanin sati d'aya daya raka daddy air port tuda yadawo yarasa sukuni, duk yanda mommy sa taso kwantar Masada hankali abin yafas kara, ta bala in shiga damuwa. Yau tun safe yake son zuwa spicial restuarant yaci wa ni abin acan amma yakasa fita, dayayi yun kurin fita zaiji wata mummu nar faduwar gaba da tsin kewar zuciya. damisalin 12:00am "Mommy zanje gidan mama, na jima ban leka taba " okay kagai sarmi ita" Motoci ukune ke sharara gudu kan babban titin garin Abuja kafin suyi slow down suka yanka ta cikin kudafi esstate, Marwa na ko Karin fitowa daga corridor din parlon gidan yahangi shigo warsu, cikeda mamaki yake binsu da kallo "Daddy! lafiya kuwa kadawo?" Lafiya kalau my boy turfune fuska yayi "haba daddy saunawa zance adaina cemin boy ina laifin my son ai yafi " Sorry zan kiyaye "Lafiya daddy" bakomai ina kewar kane " Ina zuwa haka My son? "gidan mama dagacan zan biya restaurant nayi kewar abincin matar nan". Uhumm My son kenen mufara zuwa restuarant din nisai nadawo gida kaiko kaje inda zaka "Okay daddy amma kafarta shiga gida mom taganka saikafito " Muje bazan jimaba ai Suna bayan mota driver na tukasu suna hira har suka karaso restaurant din abin mamaki sun tararda restaurant din akulle dayake Marwan nada number Wani ma aikacin su nan takwe ykirashi cikin gir mamawa suka gaisa , "Mus'ab yanaga wajen naku arufe lafiya kuwa " Sir madance kejinyar daya daga cikin ma aikatanda ke gidan ta . "Okay" "Daddy Mai restaurant din tana jinyar wata ma aikaciyane dake zaune agidanta , bara musaukeka gida , zamuje mudubata ". A'a my son muje ainima zan samu ladan duba mara lafiya, kakirashi yabamu location inda suke sai muje "To daddy" Maryam !! Bayan sunje wajen Wani malamin addini yayi mamaki ace karamar yarinya da irn wan nan sihiri kallo daya yayi mata yagano haka , addu'o yayi mata sosai sannan yabada magun guna, natura, dana Sha, dana shafawa uabasu kwana uku idan basuga canjiba sudawo alhamdu lilah sauki yasami sosai,Saida bata magana . Yau tun safe take kuka lamarin yadgawa hajiya Zara'u hankali sosai , dakyar da sidin goshi tasamu tatsa gaita dakukane Abuna farko data fara tambaya bayan taji bakinta ya bude shine inaa my soul hajiya dagskene abinda nahani ko mafarkine ? Bansan me kika ganiba Maryam Amma inaso kibani labarinki Dan jikinna nabani bagaskiya kika gayamin ba kiji tsoron Allah . Cikin kuka tafara da cewa "Kamar yanda kika sani hajiya sunana Maryam ni yar asalin garin Nance nimarai niyace allhaji sani Mai Dala shine yadaukoni gidan marayu tare da matar shi hajiya mommy mace Mai karamci , " "'Dan allhaji sani Mai dala daya tall aduniya, shine Marwan, kikisa ko alam. basafifitashi akanmu ko ko amafarki nida haroun bamusan basubane iya yenma shi haroun yanamin kallon yar riko agidan, batare dayasan Shima ba asalinn dan gidan bane, Niko dukkan su ina musu kallon Yan uwana uwa daya uba daya, sunrenemu ciki so dakaina , muntashi cikin gata da soyayya " "Bayan na kammala secondry yaya Marwan ya bijiro da maganar aurena, matsalarda aka samu Shima yaya haroun Ashe Yana Sona" "Kasan cewar yaya Marwan shiya fara furtawa daddy yasa aka bawa yaya haroun hakuri, yanuna yahakura amma azuciyar sa ba haka bane domin takanas yazo dakaina yashedamin halindake cikin, nasha mamaki hankali na yatashi Jin ba daddy da mommy bane iya yena , domin Ayanda Yaya haroun yagayamin cewa tsintoni sukayi Kuma daddy yaje waje Wani boka yace ahada aure tsakanina da Yaya Marwan shine daddy zai samu mukaminda yakeso , kasan cewar Yana neman amber Sardou Nigeria akasar UK anawa gekanajeren tunanin hakane saboda dalilanda yasanar Dani harna kawnkwa da tunanin meyasa daddy zaimin haka , nayanke shawararr zan auriYayaMarwan kodan halaccin iyayen shi , " # Bayan sati daya "Kamar kowan cen karon har dakaina Yaya haroun ya rutsani , nagaya masa zan aure Yaya Marwan, ranar naga asalin tashankali kali dankuwa yafitomin da asalin Manu farsa harda bara zanar inhar na amince da auren sainsga abinda zaiyi kuba wan nan auren inhar Yana raye to ba wan zajjen al'amari bane, ban fahicesaba amma nakasa fada kowa kamar dawasa ranar wata Monday daddy yakirani parlon sa yayimin cikakken nayanin asalina Wanda yasami yayi mamaki da ban nuna komaina , Daga karshe yace "Maryam Dan uwan ki yanuna Yana muradin aurenki to azahirin gaskiya banaso nayi Miki dole kije kiyi tunani inhar kin ji Zaki iya aure sa to alhamdu lilah 🥰 idanko baki ra ayinsa zan gaya masa yayi hakuri ." "Daddy insha Allah zan zamemaka yar halak kawai kazar tarda hukunci insha Allah zanyi maka biyayya daidai gwargwado". "Yaji dadin wannan maganar tawa danhaka yace najee zai ne Meni sati biyu tsakani yasake kirana yasanarmin an aza ranar aure na da Yaya Marwan nanda sati uku masu zuwa. Ranar juma'a kenan" "Ana gobe daurin aurenmu, Yaya haroun yakirani, nadaisan nashaki Wani bakin hakyaki Mai azabar wari Loka cinda na Isa inda yace nasa meshi, nantake nakasa tan tance a Ina Nike sai farkawa nayi naganni a Niger gidan Wani bawan Allah yatambaini daga ina nakasa tuna komai ,har hospital yakaimi aka tabba tarmai lafiyar Kwaakwal wata , yazaunar Dani yagayamin shi agefen kasuwa ya tsin ceni , bana umm bana um um, hakan yasa ya kawonigi gidansa, yau kwana uku kenan " Tadora mata da labarin irin rayuwar da tayi agidan harkawo yanzun Sosai hajiya Zara'u ke kuka Allah yabimiki kadinki, Kuma insha Allah zan kaiki har gidan allahji sani Mai dala , "a'a hajiya bayanzuba . Bata Wani mtakurataji da lilin ba tamike ta shige kuryar dakinta Marwan da taimakon location dinda aka basu suka iso gidan haji Zara'u bawani Bata lokaci suka ran gada sallama..... 𝕞𝕠𝕣𝕖 𝕔𝕠𝕞𝕞𝕖𝕟𝕥 𝕞𝕠𝕣𝕖 𝕥𝕪𝕡𝕚𝕟𝕘 𝔸𝕝𝕜𝕒𝕝𝕒𝕞𝕚✍️ 𝕪𝕒𝕗𝕚 𝕥𝕒𝕜𝕠𝕓𝕚🗡️ 💋*SON KI NE ƘADDARTA*💋 ʂƚσɾყ&ɯɾιƚιɳɠ Ⴆყ Fateemah Abdullahi /Ⴆαƚσσʅ ƙαɱႦα/ *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️ ____________(✪)______________ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•· No editing KUYI malejii 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 Hajiya Zara'u dake kuryar daki tafito tare da amsa sallamar dayake tana sanye da hijab yasa yanufi kofar gidan ganin motoci manya manya yasa takarasa fitowa , Daddy ganin babbar mace yasa shi fitowa, Shima Marwan ganin daddy yafito yasa shi fitowa Saida suka gaisa kafin Marwan yace "Hajiya munje restuarant muntararr arufe shine nakira ma'aikacinki yace kina jinyar wata ma'aikaciyar kine . Eh wallahi, Allah sarki nagode sosai amma kushigo daga cikin mana ai mararr lafiyar na kusa shidai Marwan tun tsayiwarsa kofar gidan yakejin jikinsa kamar banada ba ,gawata iriyar faduwar gaba data sameshi , sallamarda daddy yafara yice tamakale Saka makon Ido hudu dasu kayi da Maryam, wata wawuyar ajiyar zuciya yasauke asirran ce, Marwan daya daskare atsaye dakyar ya fizzo maganar My sould!!!,yafada da karfin dagaske kece, Kodai gizone, please don't forget me , don't touch me yafada ganin ta taso da biyar tabashin Ganin yanda yake kokari faduwa yasa daddy taryosa Shima, daddy jikinsa rawa yake kamar mazari Saida suka kare mata kallon tsaf San nan hajiya Zara'u tanemisu karaso ciki su zauna Saida suka natsu San nan daddy yace Hajiya Zara'u ina kikasamu Maryam dan kaffa tanin faɗin garin Abuja da kewaye ba inda labarin batan Maryam bai jeba . Allhaji dafari ban ganetaba Saida baya Kuma dasio tambaya ta Allah bai nufaba tafara wan nan rashin lafiyar Nan ta kwashe komai da fada masa tun farko har yau da Maryam ta Bata labarin yanda tayi rayuwa a Niamey har kawo yau din nan Daddy yayi bakin cikin sosai Jin wai haroun ne Silar komai , shine silayashiga Wani hali da Marwan yashiga . Ba yanjajan tawa juna daddy yadubi hajiya Zara'u yace "hakika kincika uwa wan nan abu dakikayi bako wace mace bace zata yi saboda lala cewar mutanen , kinyi babban jahadi ubangiji yasaka Miki da jannatul fiddaus" Ameen yarabbi allhaji, aishi da nako wane danhaka kidaina yimin godiya. Shidai Marwan kallon Maryam kawai yake, ji yake kamar ama farki,yakasa nutsuwa harsaida yamatso ya tabata, daddy ne yakatse su ta hanyar cewa Maryam kigo dewa Allah domin shine abin godiya ako wanne hali Alhamdu lilah ya Allah Alhamdu lilahi ala kulli halin Hajiya ina neman alfarmar Maryam taci gaba da zama agurinki nan da wata daya zuwa biyu kafin auren su "a a dan Allah daddy kaman auren Yau " cewar Marwan cikin mmagiya Nima nayi wan nan tunanin, cewar hajiya Zara'u Saida daddy yayi Dan tunani San nan yace ba matsala insha Allah zan kira Ameen namata bayani (kakar Marwan tawajen uwa kunsafa tanada ranta ) hakan ma kayi tunani Mai kyau Allah ya rufa asiri Ameen yabbi "Daddy kakirata kamanta bayani awaya mana" Mumushi daddy yayi maganar yabashi dariya haryau idan Marwa n yayi abutamkar Dan shekaru goma alhalin yanzu shekarunsa ashirin da bakwai cif aduniya ,Kuma Banda abinka Marwan uwata cefa kayi hakuri mana zuwa gobe idan Allah ya kaimu sai mubi plait muje mudawo Dakyar ya amince dasha radin anan zai zauna bayanda daddy ya iya haka ya hakura yakoma gida cike tunanin mezai cewa mommy Baita rarda kowa a falon gidanba ,danhaka Kai tsaye bedroom yanufa harya watsa ruwa maiji motsinta ba kasan cewar Saida ya tsaya yayi sallar la a sar yasa shi zama a bedroom Mommy na Jin shigo warsa ta share shi After magrib mamee ta iso gidan daddy, cike da mamaki daddy ya tarbeta, komin tuna biyu bata yi da zuwa ba saiga Marwan Yauwa Dan al barka shigo ina maryamu n take mommy cike da mamaki tace Maryam Kuma yaushi aka ganta, tayi tambayar tana Mai ysare daddy da ido Mamee ya akai kika ji labarin nan? Wan nan Dan al barkar shiya kirani kuma yabiya min jirgi nazo gobe idan Allah ya kaimu sani ka daura musu aure s, shiko dan bazan ya ron nan ina yashiga ? Ko rufe baki bata yiba gate man yazo dasauri ko sallama babu, Yana faɗin alhaji Haruna! Haruna haka kawai yake Fadi yakasa magana Hakan yasa daddy cewa bari yaje yagani Lamarin ba dadin kallo Dan yanda haroun ke fizgar jikin sa Yana dariya da kuka lokaci daya Yana faɗin Bawanda ya isa ya auri Maryam matukar inada Rai Marwan bazai taba auren taba Saidai ciyon zuciyar ya kashe shi Daddy baice komai ba yajuya ya kalli securities Kukira ma ai katan gidan mahau kata suzo su tafi dashi , Yana ganmafaɗin haka yabar wajen zuci yarsa na suya, koma warsa falo yayi dai dai da Loka cinda mamee ke cewa mommy ki Kara hakuri kinsan lamarin sani wani zubin kamar ba bab ban mutum ba, Ba komai mamee ni ai ya nuna min bani na haifi Marwan ba, tun loka cin da yadawo yake Wani sharewa shiyasa nima na Sha re shi Zo sani mamee ta fada ganin yayi tsaye Yana kallon su fatda tayi masa sosa, kiyi hakuri mamee insha Allah zan kiyaye Allah yasa Ameen yabbi mamee nagode da nasiha Washe gari da misalinn karfe 1 na Rana aka daura auren Maryam da Marwa a Sentral masjid na garin Abuja, daurin aurwa da en da tasamu halartar manyan mutanen , kamadaga Yan shiyasa Kai hair goernor na Abuja, bayan daurin auren jamil da sauran abokan sa suka shiga yimasa tsiyar Bai kulasuba yanufi gidan hajiya Zara'u, Yana shiga yanufi dakin , can ya hangota tana Shan Wani abu a cup, da aza mar sa ya nufeta ya run gume atare suka sauke ajiyar zuciya hajiya Zara'u ce tashigo La lala la lala me zan gani,dasauri yasa keta Yana juyawa Yana Sosa Kai Fita kabani waje mara kunyan yaro Baice kalaba yafice Da misalin 8:30 nadare moto cine man ya man ya sunkai ashirin akofar gidan hajiya Zara'u , Maryam ce wasu manyan mata suka bito da ita acen gefe na hango mommy ana fitowa da Maryam Kai tsaye farar motar dake tsakiya suka ksanyata Loko esstate Anguwar da aka Kai Maryam Gidane na Gani nafada nakere sa a bayan kowa ya watse ango yashigo, gefen gado ya samu amar yarsa jiran sa , zama yayi kusa da ita yace "my sould, nagode Allah daya nuna min wan nan rana Mai dumbin tarihi hakika Allah shine abin godiya yau San raya daran nan da na fil filu Dan nunawa uban jigiji irin farin cikinda nake ciki" Kallon sa tayi cike daso da kauna tace "alhamdu lilah ya Allah" # Bayan shekaru goma Yarana guda uku ke wasa a tsakiyar wani kata faren gida, wata mata shiyar matace tafito tare da kwala musukira, hakjya Maryam kena nan Khadija, Abdallah, Ameena kuzo mutafi, wacce aka kira da Khadija da alama itace babbar a cikin su tace mama gidan grammar zamuje ? "Eh koba zaki jeba?". Batakai ga Bata amsa ba Marwan yafito Daddy suka fada atare suna yi kansa, kuzo muyi hoto, maman yara zokema nala baki zun bura baki tayi "bana so kuyi abinku" "Sorry my sould". Mur mushi tayi San nan ta isa suka fara hotu na cikin farin ciki da kau nar juna., bayan sun kam mala suka nufi gidan mommy Mommy na kan 1 siter mamee Kuma nakan Three siter suka shigo Khadija dagu ta nufi mommy ta hahe kan cin yarta ita kuwa Amina mamee ta nufa s, Saida yagaishe su ga Baki daya, san nan tace ina Mai ran kwano, ko gama maga nar Bata yiba sai ga daddy ya sauki Yana ganin su yace A a amaren nawane agidan ba notice Amina ce tafara magana " kafin kace haka kayi mana kyay kyawar tarbar Kuma kabamu chocolate , cake , chips da kan ta karasa Maryam tab kateta kewai ance Miki dadady na irin nakine so please ki shafa masa lafiya gabaki daya paeror alasa dariya kallon su daddy yayi cikin farin cciki yac alhamdu lilah ya Allah nagode maka DAKA nunamin wan nan Rana Allah shine abin godiya...... Tammat biham dallah Alhamdu lilahi Alhamdu lilahi Nan nakawo kar shen wan nan Gajeren labari Allah kaya femin kus kurenda nayi acikin sa abinda na rubuta dai dai Allah kabani ladar sa Godiya Lodi lodi ga Khadija sabu'u yahaya nainarh Kd's,hakika ke kawace ta gari, Kuma yar uwa, bazan taba manta wa da ha laccin ki aga re niba, uban jigiji ya Kara tsawon rai da Nisan kwana Allah ya raya Muna Ahmad 🥰🥰🥰 Ina godiya Fatima Yusuf Alaramma Allah yabar zumun ci Saimun hadu asabon littafi na Mai suna WATA KADDARAR pind book Akan farashi Mai rahusaaa labari Mai cike da da russa, rudani ban dariya.. sai mun hade ku kasan ce da Fatima Abdullahi F🌹A🌹K Batoool kamba 🥰 🌹 𝔸𝕝𝕜𝕒𝕝𝕒𝕞𝕚✍️ 𝕪𝕒𝕗𝕚 𝕥𝕒𝕜𝕠𝕓𝕚🗡️ . o please ki shafa masa lafiya gabaki daya paeror alasa dariya kallon su daddy yayi cikin farin cciki yac alhamdu lilah ya Allah nagode maka DAKA nunamin wan nan Rana Allah shine abin godiya...... Tammat biham dallah Alhamdu lilahi Alhamdu lilahi Nan nakawo kar shen wan nan Gajeren labari Allah kaya femin kus kurenda nayi acikin sa abinda na rubuta dai dai Allah kabani ladar sa Godiya Lodi lodi ga Khadija sabu'u yahaya nainarh Kd's,hakika ke kawace ta gari, Kuma yar uwa, bazan taba manta wa da ha laccin ki aga re niba, uban jigiji ya Kara tsawon rai da Nisan kwana Allah ya raya Muna Ahmad 🥰🥰🥰 Ina godiya Fatima Yusuf Alaramma Allah yabar zumun ci