*ZAFIN RANA* *_Shafi na Daya_* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *Masarautar Biram* "Ta ko ina ya rurufe kofa da window din dake cikin dakin, kallan juna sukai hankalinsa a tashe" "yace ""Yaya!""" "Kusa dashi ya zauna tare da rike hannunsa, wanda ya kira da yaya ya kalleshi cikin matsanancin" "jin jiki, hannunsa ya matse yace ""Abdul-Salam!""" "Da sauri yace ""yaya.""" "Yaya ya kalleshi yana magana dakyar, yace ""Abdul-Salam ga Amanar Junaid nan, ka kula dashi, in" "da dama ka fitar dashi daga masarautar nan, dan sam Bana sanshi da mulki.""" "Cikin mamaki Abdulsalam ya kalli yayansa yace ""yaya? Wani irin magana kakeyi bayan Junaid shi" "kadai ne dan da ya cancanci ya gajeka? Shikadai ne danka namiji, babu wanda ya dace da mulki sai shi.""" "Kai ya kadamai da sauri yana magana a hankali yace ""A'a kai kayi mulkin, dan Allah ka barshi yayi" "rayuwar da ya dace dashi, kasanshi yaro ne mai ilimi, da san kwanciyar hankali, banaso ya taso cikin wannan yanayin wanda rayuwarsa ma take cikin garari.""" "AbdulSalam yace ""yaya to ya kakeso ayi?""" "Idanunsa ne suka shiga lumshewa, rigarsa ya riko yace “ka kula da Junaid dan Allah" "Abdul-Salam, na barma mulkin nidai ka barshi da rayuwa ”" "Yanda yanayin jikinsa ke rawa ne ya hanashi karasa magana, zuciyarsa ce ta daina bugawa," "numfashinsa ya tsaya, wanda hakan ya nuna rai yayi halinsa." Hankali a tashe AbdulSalam ya dinga jijiga yayan nasa wato Sarki Zubair. "Fitowa yai jikinsa duk a mace, bayi da kuyangun dake tsaye a gun ne suka kalleshi." Matar da ta taho tana kokarin shiga gun mai gidan nata ne tai turus tana kallan sa. Idanu ya runtse sannan ya girgiza mata kai alamar babu. "Nan bayi suka fara kukan rashin Sarki da akai, ja da baya da baya ta fara yi, tana girgiza kai, da" "sauri ta matso tana neman shiga gun mijin nata? Matsa mata yai ta shiga, a kwance ta ganshi wanda hankalinta ya tashi da sauri ta sa hannu ta jijigashi, sai dai ganin jikinsa ya koma ya kwanta yasata ta saki wani irin kuka." "Kan kace me zance ya shiga lungu da sako na cikin masarautar, harma cikin gari inda mutane" "suke, ta ko ina tururuwa ake ana zuwa ana mika gaisuwa, gidan ya cika makil." Washe gari.... "Matansa da yaransa wadanda duk mata ne kowa ya hallara, yaro ne dan shekara 8 zaune kusa da mahaifiyarsa, kuwa kallan tausayi suke mai, wasu kuwa kallan soko suke masa, shikam yana makale da mahaifiyarsa har ganin ana neman yima mai martaba sallah yasa ta kalleshi tace" “Junaid aje za’ayima Mai Martaba sallah.” Kuyangar dake kula dashi ta kalla tace “kuje.” Nan ya mike yai waje. Yana fita wata tace “yanzu ya za’ai da Junaid?” "Sarauniya wacce itace mahaifiyarsa ta kalleta, yanda ta mata kallan ne yasa taja bakinta tai shiru." "Anyima mai martaba sallah kowa sai gaisuwa yake yima Abdulsalam, a wannan lokaci babu" "wanda yabi takan Junaid, duk mutanen da ke zuwa gunsa da kula dashi yau suna can gun Abdulsalam ba wanda yabi ta kansa." "Shikam da yake yaro ne, mikewa yai yace “zan koma gun Mamana.”" Bawan daya rako shi gun ya bude mai hanya suka juya. "Yana zuwa bakin kofar bangaren Mahaifiyar tasa, yaji ana kwalla mai kira “Yarima Yarima.”" "Waigawa yai ya kalli mai maganar, da sauri ya karaso inda yake cikin gudu, yana haki, sai daya" dan huta sannan yace “Hakimi AbdulSalam yana nemanka.” "Juyawa yai suka koma, mutumin daya gani cikin mutane sosai dazu yayi mamakin ganinshi a" cikin bangaren Sarki mahaifinsa shi kadai a wannan lokacin. "Yana shiga Abdulsalam ya kalleshi, Junaid wanda ya shiga kif kif da ido kawai yasa kuka, da sauri" "ya matso ya rungumeshi, Junaid ya shiga yin kuka yana cewa “Kawu wai Baffana ya rasu?shine" wanda akama Sallah dazu?” Abdulsalam ya rungumeshi cikin tausayawa yace “Junaid.” Kuka sosai Junaid yakeyi kafin ya tsagaita. "Abdulsalam ne ya kalleshi yace “yanzu zamuje a kaishi makwancinsa, nazo ne da sauri dan na" sanar ma wani abu.” Junaid sam bai fahimta ba sai dai kallansa kawai da yakeyi. "Abdulsalam yace “yanzu zaka bi wannan, ya fada yana nuna saurayin daya kirashi dazu, tare" "zamu tafi dakai sai dai kai zakabi wannan zakuje wani guri, wanda ba dadewa zakuyi ba zanzo na" daukeka.” "Kai ya jinjina alamar to, sannan yace “kar kuma ka fadawa Mamanka, kadai ce mata zakaje inda" za’akai Mai martaba.” "Kallansa yai ba tare da wani zargi ba ya daga kai, nan ya juya ya fita, wannan saurayin yabi" bayansa. "Shiru Abdulsalam yai, indai yanaso yai yanda Sarki yace to lalai dole ne ya fita da yaran nan ana" "cikin hargitsin nan, dan inhar ya bari sai an lafa to ko za’a mutu mahaifiyarsa bazata taba yarda da wannan lamari ba, shiyasa tun a daren jiya shi da yaran nan wanda yake jarumi ne shi sannan mutumin ne wanda ya yarda dashi, suka fita cikin dare dan neman inda ya dace yaran ya zauna," "ya debi kuyangu ya kaisu, da sassafe da bayin da zasu kula dashi." "Junaid ya je gun Mahaifiyarsa, sai dai yawan mutanen dake shigowa yi mata gaisuwa ya" "hanashi karasawa kusa da ita, sai dai hangoshi datai daga nesa, saurayin ne ya kalleshi yace" “Yarima lokaci yayi.” Junaid ya kalleshi yace “muje in na dawo na fada mata.” "Nan ya juya ya fita, sam yayinsa ma da suke mata ba wanda ya damu dashi, kowa najin haushin" shi kadaine namiji dole ne kuma ya gaji mai Martaba. Sun fito suka shiga cikin jerin masu kai Mai Martaba gidansa na gaskiya. "Ana kokarin shiga inda za’a birneshi, saurayin yaja hannu Junaid suka bar gun, Junaid ne ya" kalleshi sannan ya kwace hannunsa suka fara tafiya yana cemai “ina zamu?” "“Ba dadewa zamuyi ba can kauyen ne, yarima ai kanasan hawa doki ko?”" Da sauri Junaid yace “eh sosai ma.” "Saurayin yai murmushi, dan wani kauye suka nufa, wani gida ya shiga sai gashi ya fito da doki." Junaid cikin murna ya kalleshi yace “aikuwa da gaske kake.” Nan ya hau da Junaid gaba shi kuma ya hau suka harba doki sukai gaba....... "Sundanyi tafiya mai nisa kafin su isa wani kauye, Junaid cikin sha’awa yake kallan mutanen" "kauyen, ta ko ina kowa hada hadar sa yakeyi, kallan saurayin yai yace “sai yau na taba shigowa cikin mutane haka, zanci wancan..”" "Ya fada yana nuna mai wani abu da suke saidawa, kamar mazarkwaila." Saurayin yace “Yarima kayi hakuri in munje zansa a zo a duba maka mai kyau ba irin wannan ba.” Junaid yai dariya yace “ina binka bashi kenan.” Sauka sukai akan dokin suka karasa dan karshen kauyen kadan. "Gini ne wanda kana ganinshi kaga gini na sarauta, mamaki ya kama Junaid ya kalleshi yace" “gidan waye?” Saurayin yace “gidan Sarki Zubair ne.” “Babana?” "Ya fada cikin mamaki, saurayin ya daga kai, yana murmushi dan shi kansa bai taba ma sanin kauyen nan ba sai a daren jiya da sukazo da Abdulsalam, wanda Sarki zubair ya sanar dashi inda kauyen yake da gidan dayasa aka ginama Junaid tun sanda ciwo ya fara kamashi, wato shekara" biyu da suka gabata. Masarautar Biram..... Nasan duk wanda yaji sunan Biram zai fara tunanin ina ne? Sai dai nasan wasu daga cikin mu su san sunan. "Biram shine asalin sunan garin Hadejia wanda mutane suka fi sani a wannan lokaci, gari ne" "wanda aka gima shi tun asalin hausa bakwai da banza bawai, gari ne wanda ya kafu tun Alif Dubu daya da dari takwas da takwas (1808)" "Yana daga cikin kasashen da Bayajidda ya kafa, gari ne na hausa da fulani, gari ne wanda suka" "taso suna shuke shuke, kiwo da sauransu." *Ayusher Muhd* *ZAFIN RANA* Haske Writers Association Na Ayusher Muhd Shafi na biyu "Junaid suna shiga ya shiga kallan gida cikin tsananin jin dadi, dan abin ya birgeshi, yaje zai shiga" cikin falo ne ya hango kuyangun gidansu. "Mamaki ne ya kamsashi ya nufo gun yana cewa ""Hari kece?""" "Juyowa tai da sauri jin muryarsa, ta nufo inda yake tace ""Yarima!""" "Kallanta yai yace ""me kike anan?""" """Da sassafe aka kawomu nan akace mu zauna zaka zo.""" "Ba tare da yai tunanin komai ba yace "" ke dawa?""" "Nan ta shiga kiran ragowar kunyangun, yana ta dariya, cikin gidan ya shiga yana tattaba" "abubuwa, mamaki sosai yakeyi ta yanda duk wani abu dayake fadawa Mahaifinsa yanaso akwaishi a wannan gidan, kallan saurayin nan yace ""kai ya sunanka?""" """Azi sunana Yarima.""" "Junaid ya kalleshi yace ""Ali ko Azi?""" "Yace ""Azi.""" "Dan dariya yai sannan yace "" kace zaka sa a siyomin wannan abin?""" "Azi yace ""eh yarima amma sai ka zauna anan ka kwana baka kuka ba.""" "Ba tare da damuwa ba yace ""to, amma in mun tashi zamu gun Mamana ko?""" "Azi yace ""in munyi bacci sau haka, ya fada yana nuna yatsun hannunsa." "Junaid ya kalleshi yace "" to.""" *********** A can masarautar Biram kuwa anata shige da fice wanda ya hana Gimbiya Azeema samun "nutsuwa harya fahimci dan nata baya nan, har sai zuwa dare bayan anyi sallar magrib ta kalli kuyangar dake kula da ita tace ""Kicema Yarima yazo yaci abinci anan.""" "Da sauri tace to, Gimbiya Azeema ta zubama tiren abincin ido, bata taba kawo Sarki Zubair zai" "rigata rasuwa ba, yanzu ya zatai da rayuwarta? Tun tana yar mitsitsiya aka aurar da ita gareshi, ta taso shine mahaifinta, mijinta kuma abokin shawararta yanzu ya zatai?" "Kanta ta kwantar a jikin gado, zuciyarta duk ba dadi, Duk yawan mata da kwarkwarorin dayake" "dashi baya damunta sam, saboda a koda yaushe yana nuna musu matsayinta." "Dole ne ta mike tsaye ta kula da kanta kodan rayuwar Junaid, bazata taba yarda ace Abdulsalam" "shine yahau mulki ba alhalin asalin sarauta ta Junaid ce, dole ta jajjirce taga wannan al'amari ya faru." Shigowar da Kuyangar tayi ne yasa ta kalli kofa da sauri tana jiran ganin Junaid. "Ganin har kuyangar ta karaso bata ganshi ba yasa ta kalleta, kuyangar tace ""Gimbiya baya" "bangarensa.""" "Batai mamaki ba tace ""ki duba bangaren su Hanna, da can babban gida.""" "Da sauri tace to, juyawa ta ta fita, Gimbiya ta mike daga kan sallayar ta zauna a bakin makeken" gadonta wanda aka mai ado. "Da gudu wannan kuyangar ta shigo, ran Azeena ya baci ta mata wani kallo wanda ya sata saurin" "tsayuwa daidai, Barira ta kalleta sannan ta maida kanta kasa tace ""Gimbiya ba'aga Junaid ba, kowa na tambaya sai yace shi tun rana a gunki ba wanda ya ganshi." "Mikewa tai da sauri tace ""ina ya shiga?""" "Muje in duba da kaina, nan suka fito ta shiga bi ta ko ina tana nemansa, tun abin bata maidashi" "na tashin hankali ba, sai da duk inda taje nemanshi suma su fito dan tayata nema, taga an hadu dayawa sai dai ba wanda ya ganshi." "Kanta ne ya fara juyawa, ta ko ina a cikin daren nan nemansa akeyi, ga gida dama a cike saboda" yan zuwa gaisuwa. "Kowa da abinda yake sakawa a ransu, dayawa daga cikinsu kuka sukeyi sai dai kana gani kasan" "wannan kukan na gulma ne, Gimbiya Azeema kam jitai jiri na debanta wanda ya hanata tsayuwa, kallan Babban yarta tai wacce take kusa da ita cikin rada tace mata rikeni mu wuce." "Riketa ta tai ta mike sosai, tare da yin murmushi tace “kuje ku kwanta ba wani abun, da alama" yaje wani gun ne bacci ya kamashi.” "Tana fadan haka suka juya a tare, kallan yarta tai wasu Sameera tace “Sameera ina Hakimi" yake?” Sameera a hankali tace “kinsan dare ne ba kila ya kwanta.” "Idanunta runtse sannan suka cigaba da tafiya, tana shiga dakinta ta zube a kasa saboda gaba" "daya kafarta ta gama saki, da sauri Sameera tace duk kuyangun su bar dakin, ta kalli Gimbiya tace" “Umma kina tunanin wani abin ya sameshi ne?” Gimbiya Azeema wacce gaba daya ta gama rudewa tace “Sameera mutane nawa ne suke san mulkin nan?” "Sameera tace “kannan Abba su biyar maza, sanan babban yaran Hakimi AbdulSalam Su shida" kenan.” “Kina tunanin zasu bari Junaid ya hau mulki yana karami dashi? Bayan su kansu mutum shidan nan fada suke a junansu?” Hankalin Sameera ya tashi tace “Umma kina nufin sun mai wani abu kenan?” "Gimbiya ta kalleta idanunta sun ciciko gaba daya kirjinta ne taji ya mata nauyi, rike hannun" Sameera tai tace “Sameera munyi kuskure da muka nunawa mutane Junaid baya cikin masarautar nan.” "Sameera ta kalleta a tsorace, tacigaba “yanzu duk wanda ma bai sani ba ya sani, kinga wanda" yake neman cutar dashi zai iya bi ya cutar dashi ba tare da ansani ba.” "Gaba daya hankalin Sameera ya tashi, tace “ya zamuyi kenan?Umma junaid yaro ne, taya dan" rashin imani zasu nemi cutar dashi? Nawa yaran yake? Yaran da baisan me ake ciki a duniya ba?” "Azeema tace “shine dalili da zaisa su cutar dashi, saboda baisan me ake ciki a duniya ba, shine" "zaisa su halaka shi ba tare da wata matsala ba, kina tunani zasu jira ya girma? Bayn sun san in ya" girma zai kwaci kansa?” "Sai a yanzu itama wadannan tunani suke zuwa mata, jikinta ne ya hau rawa, tace “meke" "damuna Sameera? Gaba daya banyi wadannan tunanin ba sai yanzu, Sameera ya zanyi in wani" abin ya samu Junaid? Na shiga uku. ” "Hankalin Sameera yayi tsananin tashi, ta kalleta tace “Umma yanzu ya zamuyi?”" "Gimbiya tai shiru, ganin wannan ragwantar ba inda zata kaita ne yasa ta mike tsaye da sauri, tace" “ina mai gidanki?” Tace “Mahmud yana gida.” "“In har aka kai gobe da rana ba’aga Junaid ba, ki aika a kai masa wasika, tunda shi ba lalai" "mutane su fuskanci halin da yake ciki ba, ya nemo Junaid ta ko ina ya nemo Junaid, mu kuma idan" "aka tashi da safe muce ya dawo yana daki, kar mu bari a fahimci wani abun.”" Cikin mamaki ta kalleta tace “yana daki kamar ya?” "“Idan mutane sun ji yana daki maganar zata lafa, sai muyi dabara duk wani abu da zai nuna" "musu bayanan mu kauceshi, in yaso shi kuma Mahmud kinga yana can yana nemanshi, nan kuma" sai musa Barira ta kara duduba ciki a hankali.” Samira ta jinjina kai tare da cewa “nagane Umma.” "Gimbiya Azeema ta zauna a bakin gado tace “malaman da sukazo kwanaki, akan suna yin karatu," kinsansu?” Kai ta girgiza alamar a’a sannan tace “karatu kamar ya?” "Shikenan, zan sa a bincika, kema cikin dabara ki dinga duba cikin Masarautar tamu.”" Da sauri tace “to Umma.” "“Dole na nemi ganin Abdulsalam, sai dai bansan yanda zanyi ba.”" Sameera tace “me zakiyi?” Kallanta tai kamar zatai magana sai kuma tace “karki damu.” "Jekinki kwanta, kar yaranki su nemeki." Juyawa tai cikin sanyin jiki ta fita. "Gimbiya sai zagaye cikin dakin takeyi gaba daya hankalinta ya kasa kwanciya, gashi bata san me" "akeyi ba inza’ai adduo’i dan karatun sallah Sarki ya koya mata shima kadan, saboda aikacin" "addini baiyi zurfi ba, an iya karatu kadan sai dai ba’a san yanda za’ai addu’oi sosai ba, sai yanzu da malamai ke ta kokari suna yadawa." *********** Kuka yake sosai cikin daki saboda ya saba duk sanda zai kwanta sai Umma tazo ta dan mai karatu sannan yake bacci. "Jin kukan dake fitowa daga dakin ne yasa Hari tai saurin shiga ciki, yana zaune ya takure guri" daya. "Hasken fitilar kwai dake cikin dakin ta kara, sannan ta matso tace “Yarima! Lafiya?”" Da sauri ya kalleta yace “Hari ki kaini gun Umma banasan nan.” "Ta kalleshi cikin tausayawa tace “Yarima nima bansan ina bane, rufemu akai a buhu aka" kawomu bansan taya mukazo ba wlh.” Yace “kiramin Azi.” Kallansa tai cikin tausayawa tace “Yarima kayi hakuri amma banaji zakaga Umma yanzu.” Da sauri ya kalleta yace “kamar ya kenan?” Idanunta ne suka ciciko tace “duba da yawan abinci da duk wani abin bukata da aka kawo aka ajiye anan na tabbatar bazaka koma yanzu ba.” “To me zanyi anan?” "Ya fada cikin damuwa, kallansa tai tace “dan haka ka kwantar da hankalinka ka kwanta kai bacci, kai sauri ka ci abinci kai bacci ka girma kila lokacin za’a barka.”" "Idanunsa ne suka dan firfito, bakinsa ne ya fara rawa kafin ya fara kuka......" Haka dai ya kukansa harya gaji yai bacci. ******** "A cikin masarautar Biram kuwa da safe kowa sai shigowa yake dan yin gulma, sai dai duk wanda" yazo zai ga takalminsa a inda ya saba ajiyewa sannan ga rigarsa nan ta alkyabba a gefen Gimbiya. "Tana nan zaune, duk wanda ya shigo sai tace “ai kasa barci yai jiya ya tafi dakin Sarki acan ya" "kwana, baiyi bacci sosai ba shiyasa yanzu ya kwanta." Wasu sun yarda wasu kuwa jinta kawai sukeyi amma bacci ace tun dazu har yanzu? Kuma baccin yaro ma? *********** AYUSHER ************ *ZAFIN RANA* *Haske Writers Association* Pg 3 "Gaba daya yau cir haka Gimbiya ta kwana tana sake sake a ranta, ana sallar asuba ne ta kira Barira tace mata ta je jikin massalaci daga gefe kafin Hakimi ya shiga turakarsa tace ""masa a idon na ne.""" Barira bata tambayeta ma'anar hakan ba ta fita. Yana fitowa Barira ta sanar da bawan dake kula da Hakimi shi kuma ya sanar mai. "AbdulSalam yanajin haka ya kalli bawan nasa yace ""ku je" "ciki ina zuwa.""" "Bai jira komai ba yai gaba, tafiya yo mai dan nisa har ya isa wani dan kango, wanda an fara gini amma ba'a karasa ba" kuma da alama ginin ya dade a kangon. "Yana shiga ya taddda ta a tsaye, kallanta yai yace ""me kike" "anan? Ke da zaki shiga takaba?""" "Kallansa tai cikin tashin hankali tace ""na sani, ina" "Junaid?""" """Junaid? Baya gunki?""" "Wani banzan murmushi tai sannan tace ""baya guna? Ka" "dauka bazansan kai ka daukeshi ba?""" """Azeema me kike san cewa?""" "Ranta a bace tace "" AbdulSalam ina Junaid, kafi kowa" "sanina Allah in wani abu ya samu dana wlh kasan abinda zai biyo baya.""" "Ya kalleta yace "" yanzu duk duniya ki rasa wanda zaki zarga da yima Junaid illa sai ni?""" Kallansa tai ta kuramai ido tana san gano ko karya yake "mata, saboda tasan AbdulSalam sosai, dan kusan tare" "za'ace suka taso, tayi aure tana karama sosai, alokacin shi" sa'antane. "Ganin yau fuskarsa ba alamun data saba gani na inyai karya yasa tace ""Abdulsalam ka taimakeni ka nemomin" "Junaid? Dan Allah.""" "Ta fada idanunta suna neman kawo ruwa, tausayinta ne ya kamashi, ya sani sosai ga rashin mijinga rashin da abin ya" "mata yawa, kallanta yai yace "" Azeema.""" "Kamar ya tabota kawai tasa kuka, durkushewa tai tana kuka tace ""Ka taimaken ka nemomin Junaid bazan iya" "rayuwa babu Junaid ba kaima ka sani.""" "Idanu ya runtse, tausayinta ya kamashi, sai dai yasan in har ya fada mata zata dawo dashi ne wanda yana karami rayuwarsa zata shiga garari, in ma an barshi da ransa" kenan. "Zan nemoshi, sai dai kema ki taimaka ki daure, kallansa tai ta share hawayenta tace ""zan sanar ma mutane bashida lafiya an kaishi Daura gun Mamana dan Allah kafin" "mutane su farga ka nememin shi.""" """To Gimbiya.""" "Kallansa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa, juyawa tai ta fita daga kangon." Da idanu ya bita tare da dan runtse idanunsa. "Bangarenta ta wuce gaba daya hankalinta ya kasa kwanciya," "in jiya ba'a samu matsala ba tasan yau za'a samu, ko a wani halin dan yake?" ********** "Mahmud yasha nema harya gaji, ita kam Azeema duk ta rame, duk da ta sanar akan Junaid yana daura ba kowa ne ya yarda da hakan ba." "Bare da akaga yanda ta canza, kowa sai gulma, yan jaje ma da biyu suke zuwa, dayawa suna nata dariya a ransu, na" yadda take ji da dan da kuma fatan zamar dashi sarki. Haka tana ji tana gani aka ba AbdulSalam mulkin garin "Biram, ranar da akai nadin nan kam da wani zazzabi ta tashi." "Tayi nema tayi kuka harta gaji, duk tagama fitarda rai" akan Junaid gani take halaka mata shi akai. "Gaba daya matan sarki nada a wancan lokacin ana ba Sarki nai ci damar zabar wanda yake so, wanda kuma bayaso za'a nemi fitar dasu ne amaidasu can karshen" masarauta. Bayan sun fita takaba ne Uwar Gidan Abdulsalam wanda "a wannan lokacin ta zama sarauniya ana cemata Hajjo, turakarsa ta nufa, yana zaune yana cin abinci ta shiga." Zama tai gefensa sai data jira ya kammala sannan ta "kalleshi, kallanta yai yace ""kinada magana ne?""" "Tace ""Takawa ya zakai da matan Sarki Zubair?""" "Kallanta ya sakeyi yace ""kamar ya kenan?""" "Tace ""na yarda kazabi wacce kake so tunda dai matanka" "mu biyu ne sai dai ban yarda ka auri Azeema ba.""" "Ido ya zuba mata kafin ya sha ruwan dake gabansa yace ""a" "wani dalilin kenan?""" "Kallansa tai sannan tace ""kana tunanin bansan tsakaninka da ita ba?""" "Shiru yai wannan karan sai kallanta kawai da yake," "tacigaba, dukanmu mu biyu matan ka aura maka mu akai" "babu wacce kakeso, me kake tunani ya hanaka san mu duk" "wannan tsawan lokaci da mukai tare?""" "Kofin ruwan ya ajiye yace ""ko ma menene bai dameni ba, sai dai kinfi kowa sanin baki isa ki sani na fasa abinda nai" "niyya ba.""" "Kallansa tai kawai sai tasa wata dariya ta takaici tace ""na sani ai, nasan wlh dama bazaka bar Azeema ba.""" "Mikewa yai yace ""karki dorawa kanki abinda bazaki samu ba, ke kanki kinsan bazan yadda da maganarki ba to" "menene na fada?""" "Kallansa tai tace ""mene?""" "Yace ""inkin gama ki je ki kwanta da alama bacci kikeji, sannan wlh zan miki sharadi karki kuskura ko da wasa naji maganar nan a gun mutane, kinsan abinda zanyi da wanda" "bazan aikata ba.""" "Gaba daya sakar baki tai tana kallansa, wayaga a dakeka a" "hanaka kuka, shikam mikewa yai daga gun ya bar mata dakin ya wuce ciki." "Ta fi minti ashirin a zaune agun, tama rasa me zatayi, tazo da zarginta gashi ya tabbata dan tana zargin yana san Azeema ne amma bata tabbatar ba sai a wannan lokacin, lalai akwai tashin hankali, dan bazata taba yarda tai mulki" da sannan yanzu tayi ba. ********* Shikam Abdulsalam suna fita daga takaba ya sanar zai auri "Azeema da Salma, wacce itama matar sarki Zubair ce." "Azeema kam damuwar rashin danta ma ta isheta ko bi takan abinda ake batai ba, haka aka daura musu aure aka nemi in tanaso a canza mata fadar ta ko a gyara mata, tace" a barta haka. *********** "Junaid kam yasha kuka har ya gaji sai dai a hankali Azi ya dinga daukanshi yana kaishi cikin gari yana kallan yanda mutane ke hada hadar su har shima ya fara sakin jiki," abinka dama da yaro. "A hankali garin ya fara mai dadi, kamar yadda suka saba yau ma sun fita kallan gari su hudu yana ta kallan mutane yana dariya, suna kokarin wucewa aka cillo kaya, da sauri suka kare Junaid, dan sun dauka wani abin cutarwa ne, sai dai kaya ne ya fado, Junaid yadan turesu, ya matso inda kayan suka zubo, wata mata aka hankado waje, saura kadan ta begesu ta fadi kasa, wata yarinya ce ta fito tana kuka ta taho gun matar da alama mahaifiyarta ce, mutumin ya kalleta yace "" nace banayi ana aure dolene? Ki tafi gidanku, au ashe fa baki san ma gidan naku bako? Ai dama ance tsintaciyar mage bata mage, munafuka kawai," "na sakeki saki uku.""" Yana kaiwa nan ya koma ciki tare da rufo kofar da karfi. "Kuka kawai takeyi yarinyar ma tana ta kuka, Junaid" "tausayinsu ya kamashi, yana neman karasawa gunsh Azi yai saurin rikeshi alamar karyaje." Junaid ya zare hannunsa yaje kusa dasu kallan yarinyar da bata wuce shekara uku ba tana ta kuka yai. "Kallan matar yai itama yace ""Hajiya inaje gidanku?""" Kallansa tai tana kuka tare da girgiza kai alamar bata sani ba. "Kusa da Azi y dawo yace ""Azi mu tafi dasu kaga basuda" "inda zasu zauna.""" "Da sauri Azi yace ""A'a yarima taya zamu dauki mutanen da" "bamusan su ba? Bamusan halinsu ba? Kana kallo kuma korosu akai.""" "Junaid yace ""kalli fa yarinyar nan kuka take.""" Ya fada yana neman yin kuka shima dan yanda take kuka yasa ya tuno da Ummansa. "Da sauri Azi yace ""to Yarima amma da sharadin in sukai" "wani laifin zan korasu.""" Yace eh naji. "Da sauri Junaid ya matso ya kalli yarinyar yace ""kinasan" "shan mazarkwaila?""" "Kallansa tai sannan ta daga kai, ya kalli maman yace muje" gidanmu ku zauna. "Maman ta kalli su Azi, tana tunanin wannan kuma wanene?" Su waye? "Ganin ba inda zata zauna yasa ta mike sukabi bayansu, Junaid ya rike hanun yarinyar suna tafiya, har suka isa gidan, suna shiga ya jata ya bata mazarkwaila, tana amsa" "yace ""ya sunanki?""" "Tace ""Ke.""" "Kallan mamaki ya mata yace ""ke kuma? Sunane?""" "Kai ta daga alamar eh, fitowa yai waje inda Azi yake cema Hari ta samar mata makwanci sannan in har zata zauna anan sai ta taimaka da aikin gida, Junaid ya fito ya kalli" "Mamar yace ""ya sunanta? Tace wai ke sunan ta.""" "Mamar tai kasa dakai cikin kunya, Azi ya kalleshi yace ""ai" "bazata fada ba basa fadan sunan yan fari.""" "Junaid yace ""to ya kenan? Taya za'asan sunanta?""" "Azi yace ""sai dai a tambayi babanta.""" "Mamar tai saurin cewa ""a'a dan Allah karka tambayeshi zai san inda muke, duk kuma sanda ransa ya baci zai biyomu" "har nan.""" "Junaid yace ""shikenan sai in bata aran nawa sunan, itama" "adinga ce mata Junaid.""" "Dariya suka kwashe dashi duka, Junaid yace ""to an rasa sunanta, Azi ya ce to zan dinga kira miki sunayi in anzo" "kanshi kindaga kai.""" "Haka suka dinga Junaid nata dariya har sukazo kan Binta," nan ta daga kai. "Junaid ya juyo da sauri yace ""Binta.""" "Nan suka shiga ciki yana gaba tana binshi a baya, Su Hari" "suka bisu da kallo kafin suyi murmushin jin dadi, ganin ya sake sosai." *Ayusher Muhd* *ZAFIN RANA* Haske Writers Ameen Pge 4 Bayan shekara goma sha biyu. "Wata irin shakuwa ce mai tsananin karfi tsakanin Junaid da Fatima wato Binta, tare suke komai nasu, mahaifiyar Binta ta rasu shekara hudu da suka wuce a lokacin tana shekara goma sha daya, Binta tayi kuka har ta gaji, a lokacin ta kara sanin mahimmancin Junaid, shikam dama Binta ita ta maye gurbin Umma, kanwarsa, Abbansa da kuma aboki, sun taso komai nasu daya, dan hatta abinci ga nata kwanon ga nashi sukeci, daki kuwa dama a gefen dakinsa take kwana, shima sai sun ci hirarsu sun gaji, lokaci suna yara ma sai dai tai bacci anan Hari ta dauketa, a da Junaid yana kuka sosai na rashin su Umma amma" zuwan Binta yasa duk ya daina. Tun bayan daya kawosu ya umarci kowa na gida karya kara ce masa Yarima a kirashi da sunansa. Duk da basa so haka nan sukai dole saboda umarni ne wanda kuma sun san dole su bi. Kamar yanda suka saba yauma sunje can bayan gari suna zaune suna hirarsu. Yau yana saman bishiya ita kuma tana zaune a kasa tana bare gyada. "Kallanta yai yace ""Binta ni sai yaushe zaki ban gyadar ne?""" "Kallansa tai tace ""ka manta yau baka da ita?""" "Da sauri ya mike ya zauna yace ""ban gane ba?""" "Tace ""to wayace ka hau sama ka barni a kasa?""" "Yace ""wayace mutum har yanzu ya kasa koyon hawa" "bishiya?""" "Baki ta dan turo tace ""ba wani yaushe ma ka koyamin?" "Kullum sai dai kai ka hau ka kyaleni a kasa.""" "Dariya yai yace ""to ke kina mace wai me ke hadaki da hawa" "bishiya?""" "Fuska ta hade tace ""kusan duk matan garin nan nasan sun" "iya hawa sai ni.""" Matsa matsa zan sauko. "Bata matsa ba ta kawar da kanta gefe irin fishin nan, saukowa yai ya zauna gefenta ya debi gyadar ya fara ci bai ce mata komai ba, haushi ya kamata ta mike ta dau kwanan gyadar zata bar gun, hartai taku shida bataji yaje komai ba a zuciye ta juyo ta kalleshi, idanunsa na kanta yana cin" "gyadarsa, tana juyowa ya sakar mata murmushi." "Ta harareshi tace "" bazaka ce na dawo ba?""" "Kallanta yai sannan yace ""to dawo""" "Tace ""bayan baka ce ba sai dana fada?""" "Mirmushi yai sannan ya nuna mata gefe yace ""zoki zauna" "in baki labari.""" "Baki tadan zumburo ta karaso gun ta zauna, kallanta yai" "yace ""Kinsan me?""" Kallansa tai tare da girgiza kai alamar a'a. Mikewa yai yana dariya ya wafce kwanon gyadar ya fara gudu. "Mikewa tai ta bishi tana cewa ""Allah Ya Junaid ka bani.""" "Dariya yai tayi yana gudu har sai dayaga ta gaji sannan ya zube a kasa ya kwanta yana kallan sararin samaniya," "kwanciya tai kusa dashi tana dariya, cikin haki." "Sun danyi shiru kafin can yace mata ""Binta!""" "Kallan sa tai cikin nutsuwa saboda yanda ya kira sunanta," "yace ""Mama? Kina tunaninta?""" "Kallansa tai sannan tace ""wani sa'in, sannan kasan a" "makaranta ance mu dingama iyaye addu'a.""" "Murmushi yai sannan yace "" ni bana tuno fuskar Ummana" "yanzu.""" "Gaba daya jikinta ne yai sanyi, idanunta suka ciciko, tana" neman yin kuka. "Jikinshi ya bashi duk da ba kallanta yake ba, yace ""karki" "soma kukan nan.""" "Ta ce ""Nasan kanasan yin kukan kaima.""" "Juyowa yai ya kalleta yace ""yaushe na ce miki?""" """Nasan saboda kar na damune yasa kake nuna baka" "damuwa.""" "Murmushi yai ya mike zaune yace ""ko kadan, na girma ne" "shiyasa kema ya kamata ki daina kuka da wuri kinga kin girma kema.""" "Itama mikewa tai ta zauna gyada ya mika mata tace ""ka" "baremin.""" "Murmushi yai sannan ya fara barewa, kallansa tai tace" """wai ina Azi yake zuwa a duk bayan kwana 40?""" "Kallanta yai kamar bazai yi magana ba sai kuma taji yace """ "maybe gidan mu.""" "Cikin mamaki ta kalleshi tace ""gidan ku?""" "Yace ""eh kin manta nace miki Umma nada rai?""" Mamaki ne ya kamata dan da inya fada tana dauka wasa yake mata dan ta kwantar da hankalinta. "Ganin yanda ta bude baki tana kallansa yasashi dariya," "yace ""menene?""" "Cikin mamaki tace ""to wai me kake anan? Ka koma gida" "mana.""" "Kallanta yai yace ""bansan ina bane gidan namu, sannan abinda na sani kawai shine nasan Umma nada rai, shikadai" "kawai na sani.""" "Ajiyar zuciya tai cikin rashin jin dadi kafin tace ""ko mubi" "Azi in zai koma?""" "Kallanta yai yace ""oh ko mu bishi? Amma sai dai a boye" "dan bazai yadda ya kaimu ba, yau saura kwana. """ Sukai irge a tare sukace bakwai ya je. "Junaid yace ""karfa muje da nisa kisha wahala, sannan shi" "kinga da doki yake zuwa.""" "Shiru tai cikin rashin jin dadi, yace ""to ko na bishi in naga" "gidan sai nazo mu koma tare?""" "Da sauri tace ""a'a salan kaki dawowa.""" Ta fada tana rike rigarsa. "Dariya yai sannan yace ""inki dawowa kamar ya? Ta ina zan" "barki inyi rayuwa ta daban?""" Itadai bata yadda da wannan shawarar ba hakan yasa ya hakura ma da zancen. ********* Masarautar Biram "Zaune take akan kilisarta kuyangunta na gefenta, ita kuma tana zaune tana jin kidan da ake mata, murmushi ne" ke bayyana a fuskarta najin dadi. Bude kofar da akai ne yasata ta bude idanunta dake "lumshe, kallanta tai har ta zauna." Masu kida ne zasu ci gaba ta kallesu sannan ta musu alama da su fita. "Hajjo ta bude idanunta ta kalleta, sai da suka fita tace" """Menene?""" "Budurwar data shigo ta kalleta tace ""Umma nikam bazan" "auri dan Sarki Gobir ba.""" "Hajjo ta kalleta sannan tace ""to wa zaki aura? Wai mi meke" "damunki? Kowa sai kice bakyaso? Ko ce miki akai zabinki muke nema?""" "Kallanta tai tace ""ni haushi yake bani, bazan aureshi ba.""" "Hajjo ranta ya baci, tace ""kina kallo babban burin" "mahaifinki yaga ya aurar dake, amma ke sam bansan menene matsalarki ba.""" Shigowar Wani Saurayi ne ya sata kallansa. "Yarima Zubair ne ya shigo, babban dan Abdulsalam wanda ya haifa tun Sarki nada rai, ya samai sunan Zubair wato" sunan Yaynsa. "Kallanta yai yace ""ke kike biye mata? ku daura mata aure kawai ku kaita, sai muga me zatai.""" "Ya karasa tare da zama, Zeenat ta kalleshi tace ""kash ya" "akai haka? Gashi kai ba kaine babana ba.""" "Kallanta yai a zuciye yace ""mene?""" "Kafada ta daga mai sannan tace ""na manta.""" "Kallan Umma yai yace ""Umma yarinyar nan wlh ta gama" "rainani, kuma ni ba sa'anta bane.""" "Haushi ya kama Hajjo tace ""Ku rufemin baki ko? Ko kunyama bakwaji, gida cike da makiyanku amma ku dinga" "fada.""" Shiru sukai basu sake cewa komai ba. "Hajjo ta kalli kuyangar ta tace ""Takawa yana ina?""" "Kuyangar tai waje da sauri, bata dade sosai na ta dawo," kallanta Hajjo tai tace yana ina? Yana bangaren Gimbiya Azeema batada lafiya. "Hajjo tai tabe baki tace ""aikin kenan.""" ******* *Ayusher Muhd* *ZAFIN RANA* *Haske Writers Association* Pge 5 "Bubuga kofa yake iya karfinsa amma ba alamar budewa da take shirin yi, iya karfinsa yake" "jijigata yana kiran Binta, daga ciki itama kuka take sosai tana kiransa, gaba daya duhu ne agun babu haske ko kadan." "Daga kasan dakin ya hango hayaki yana fitowa, da sauri ya zabura ya mike daga baccin da yakeyi." "Gabansa ne ke dukan uku uku, gashi gaba daya ya jike sharkaf da zufa, kansa ya dafa sannan ya" fito daga cikin dakin nasa. "Tsakar gida ya nufa yana tafe yana tunanin abinda ya faru ynzu, ji yai ance ""Yari """ Juyowa yai ya kalleshi saboda garin tar yake da hasken farin wata. "Azi ya matso ya rusuna yace ""Junaid lafiya? me kake a daren nan?""" "Junaid wanda idanunsa sukai ja jawur ya kalleshi sannan ya cigaba da tafiya, da sauri Azi ya bi" "bayansa har suka fita daga gidan. Kara kallansa yai yace ""Ina zaka?""" "Junaid bai tsaya ba hakan yasa Azi kara binsa, sai da har suka fara shiga cikin gari, duk gidajen" "mutane a rirufe kowa ya kwanta, ga gari yai sanyi saboda lokacin sanyi ne." Zama yai akan wani dandali dake gefen wani gida. Azi ya karasa kusa dashi ya tsaya. "Junaid ya kalleshi yace ""zauna.""" "Azi ya zauna ba tare da yai magana ba, Junaid bai kalleshi ba yace ""Saura kwana nawa kaje?""" "Da sauri Azi ya kalleshi, Junaid yai murmushi yace ""akoda yaushe ina san tambayarka abu sai dai" "zuciyata na tsoron amsar dazan samu daga gareka.""" Azi ya kalleshi cikin tausayawa. "Junaid yai dan shiru kafin yace ""ada ina tunanin laifin me na aikata haka da za'a kawoni nan tun ina karami, ba wanda ya taba zuwa yaga a wani hali nake ciki? A yanzu kuwa komai ya fita a kaina gani nake rashin so ne yasa ba wanda ya damu dani.""" "Azi da sauri yace ""ba haka bane Yarima.""" "Junaid yace ""Yarima?"" Ya saki wata dariya na takaici." "Azi ya kalleshi yace ""Gimbiya batasan an kawo ka nan ba.""" "Kallansa yai, da sauri Azi ya rufe bakinsa, Junaid cikin mamaki yace ""wanene yasa a kawo ni nan" "kenan? In har Umma bata sani ba?""" "Azi ya kalleshi a tsorace, Junaid yai murmushin takaici yace "" kasan ba dadan kai ko Hari wani" "sa'in kuna cewa Yarima ba da tuni na manta ko ni wanene? Fadan sunan da kuke wani sa'in shi kesa nake rike wanene ni, sai dai hakan baisa na dau matsayin da daraja ba, nasan a yanzu ba" "wanda ma yake tunawa da anyi wani yaro mai suna Junaid.""" "Shiru yai tare da kallan Wata, yace ""in zakaje wannan karan zan bika.""" "Zanje naga mutanen da suka kulleni wace rayuwa sukeyi.""" "Gaban Azi ya fadi ya kalleshi yace ""Junaid """ "Junaid ya kalleshi yaga duk ya tsorata, dariya yadanyi yace "" binka zanyi ba a matsayin Junaid" "Yarima ba a matsayin yaran daka taho dashi daga can.""" "Azi haryanzu kallanshi yake yana tsoro, Junaid ya dafa kafadar sa yace ""ba abinda zai faru, dan ni" "dakai kawai zamu ko Binta bazan dauka ba, na tabbatar in kaga na bata anan ai kasan ba abinda zan aikata.""" "Azi ya jinjina kai yace ""to, amma. """ "Junaid yace ""mu fita da daddare.""" Azi yai murmushi dan yana mamakin Junaid yanda wani sa'in kan canki abinda yake neman fada. "Junaid yai gaba, Azi ya mike yabi bayanshi, suna zuwa gida mai makon ya shiga ciki ya samu gu" "ya zauna, yana tunanin mafarkin dayai mara dadi." *********** "Hannu yasa ya rikota yana neman jawota jikinsa ta dan zare jikinta daga nashi, kallanta yai cikin" "rashin jin dadi yace ""Azeema sai yaushe ne zaki saki jiki dani? Ni fa mijinki ne, shekara nawa kenan?""" "Kallansa tai kamar zatai magana sai ta fasa, mikewa zaune yai ya kalleta yace ""ko baki amince" "dani ba a kalla ki dawo yanda muke dake da ke kanki kinsan dake kadai nake iya shawara.""" "Kallansa tai sannan tace ""Abdulsalam, kace har yanzu ba'a samo Junaid ba?""" "Kallanta yai yace ""eh.""" "Ido ta kuramai kafin tace ""Taya za'ace kamar kai a garin nan neman yaro ya gagareka? Shekara" "nawa kenan?""" """Shine dalilin da yasa kika kasa sakar jiki dani?""" "Kallansa tai, jawota yai jikinsa ya rungumeta yace ""kina tunanin zan cutar miki da danki? Ni?""" "Tace ""a'a amma baka nemanshi.""" "Dagota yai yace ""ki sa a ranki Junaid na cikin koshin lafiya da kwanciyar hankali, bakya tunanin in" "kikai wannan fatan zakiga hakan ya tabbata?""" "Shiru tai tana kallanshi, yace "" ba neman mu'alama ta aure nake dake dole ba amma ki saki jiki" "dani dan Allah, kinfi kowa sanin bazan taba cutar dake ba.""" "Murmushi ta masa sannan tace ""kayi hakuri.""" Kara rungumeta yai a ransa yana cewa kiyi hakuri Azeema. "Su biyu ne a cikin dakin Hajjo ta kalleta tace ""kinsa an duba?""" "Kallanta tai tace ""Hajjo danaje gun malam cewa yai akwai mutum daya da zai hana Zubair hawa" "mulki indai kin halaka shi to lalai ba abinda zai hanashi hawa.""" "Tsaki tai tace ""dayan fa?""" "Yace ""ki sa masa a abinci indai yaci to lalai zai ji Azeema ta fita a kansa.""" "Ta karasa tana mika mata dan abu, Hajjo ta sake yin tsaki tace ""Ni wai ke Ramlatu haryanzu" "hankali bai gama shigarki bane?""" "Da sauri Ramlatu ta kalli Hajjo, Hajjo tace ""Takawa mijin wanene? Ba mijinki bane?""" "Tace ""miji nane.""" "Hajjo ta kalleta tace ""sai na fada miki abinda zakiyi ki jawo mijinki gunki? Wannan aikin ki ne ki" "rabashi da Azeema dan ya soki bawai aiki na bane.""" "Ramlatu ta daga kai da sauri alamar ta fahimta sannan tace ""Nagode Hajjo.""" "Hajjo tai murmushi tare da rike mata hannu tace ""duk yanda za'ai ki kwace mijinki daga gun" "Azeema, tasa kinyi boranci lokacin Marigayi karki bari yanzu ma ki kare a boranci.""" "Ramlatu ta ce ""nagode Hajjo ke kadai ke sona.""" "Hajjo tace "" Zancen Zubair da wani zancen wani zai hanashi hawa mulki da alama yayi kuskure," "dan kannen Zubair maza 'ya'ya nane kuma duk cikinsu kowa yasan Zubair ne mai mulki, kar ki damu ke dai kiyi aikinki.""" "Ramlatu ta daga kai alamar gamsuwa, sannan tai godiya ta fito." "Hajjo ta bita da kallo, matsalar ta daya Zeenatu, indai ta aurar da ita ta gama, Ramlatu zata kula" da Azeema. ********* "Cikin dare yaji mostin bude kofa hakan yasashi bude idanunsa, Azi ya gani a jikin kofarsa, mikewa" "yai daga kan gado, kayan jikinsa ya canza zuwa kalar tausayawa, sannan ya fito ya maida kofar dakin ya rufe, dakin Binta ya kalla jiki a sanyaye, jiya dama sai sakalci takemai, wai batada lafiya." "Ya dade a jikin kofar kafin a hankali yasa hannu ya murda, kallanta yai tanata bacinta hankalinta" "a kwance, ya zatai in ta tashi taga baya nan? Duk da gobe zai dawo amma ji yake gaba daya ba dadi, yasan gobe sai kuka in bata ganshi ba." "Ko dai ya hakura da zuwa? Da sauri ya maida kofar ya rufe ya kalli Azi dake kallansa, Junaid yai" murmushin yake yace muyi sauri muje mu dawo kafin hankali Binta ya tashi. Azi ya kalleshi tare da daga kai alamar to. Sun fito suka fara tafiya dan zuwa kauye na gaba inda ake hawa motar ice dan zuwa cikin garin Biram. Sun isa suka tadda an cika mota hakan yasasu saurin shiga aka dau hanya. ********** Ayusher pg 5 *********** *ZAFIN RANA* HASKE WRITERS ASSOCIATION *Na Ayusher Muhd* Shafi na shida Sun isa garin Biram tunda suka shigo Junaid yake bin ko ina da kallo gaba daya yanayin fuskarsa ya canza. Azi ne ya kalleshi yace “Yar ” Kallan da Junaid yamai ne yasashi dan murmusawa yace “Wali.” "Tare suka sa dariya dan Junaid yace har su koma da sunan Wali zai dinga kiransa, Junaid bayan" sun gama dariyar ya kalleshi yace “Allah ya sa bakin nan karya min tabargaza.” Azi yai dariya yace “ ni shigar taka ma tafi ban dariya.” "Junaid ya kalli kanshi wasu irin kaya ya saka, wando da riga daban, sannan ya kima wani nadi" akansa. Murmushi yai yace “karka manta da wuri zamu koma dan nasan Binta in taga ban dawo ba kuka zataitayi.” "Azi yace “to, dama kudin kayan abinci zan amso ba dadewa zanyi ba.”" Junaid ya dan tsaya sannan ya kalleshi yace “wake baka?” "Shiru yai yana kallansa, Junaid ya cigaba da tafiya kawai yana cewa “barshi ma dan banasan ji.”" "Sun isa masarautar Biram, Azi na isa suka fara gaisawa da dakarun gidan sarki, Junaid na binshi a" "baya, sun dau hanya zuwa can cikin masarautar, Junaid ya kalleshi yace“mu hadu a tasahar mota kafin rana ta fadi.”" "Azi yace to, har Junaid ya fara tafiya yace “Wali.”" "Junaid ya kalleshi, Azi ya matso yace “kayi hakuri da duk abinda zaka gani.”" Junaid ya kalleshi ba tare da ya amsa ba kawai yai gaba. "Azi yai shiru yana binsa da kallo, yana tausayinsa sosai, duk da su a tunaninsu gata suka mai" amma ta ina zai fahimci hakan? Bayan an rabashi da kowa nashi. "Junaid yana tafe yana kallan cikin masarautar, sam baya tuna abinda ya faru a ciki, duk kuwa" yanda yaso ya tuna din. ********* Yau kamar yanda suka saba akwai rana daya da suke warewa duk matan Sarki na zuwa gun "Uwargida sarauniya, a zauna a na cin abinci ana dan hira." Azeema ce ta kalli Bari suna kan hanyarsu ta zuwa tace “ni wai waye ya kawo wannan bidi’ar?? Bari tai dariya tace “kece ai Gimbiya.” "Azeema ta kalleta tace na sani ai, Bari tai murmushi suka karasa, dukansu kowa ya hallara da" alama itace karshen zuwa. Gaba daya ta kula ma gulmar ta akeyi saboda tana shiga kowa yai shiru. Wucewa tai ta zauna a gun da aka tanada duminta. Kallan Hajjo tai tace “Hajjo barka da war haka.” Hajjo ta kalleta fuska a sake tace “Azeema barka dai.” "Nan kowa ya gaisheta itama, ta amsa fuska a hade dan batasan wargi." Sun danyi shiru kafin Ramlatu tace “Hajjo ya maganar Gimbiya Azeema ne? An daidaita da Yariman Gobir din?” "Hajjo ta kalleta sannan ta kalli Azeema tace “ai Zubair ya mata magana, kinsan duk inda ‘ya’" "ya mata suke suna shakkar maganar ‘ya’ya maza, tunda ya mata magana da alama ta shiga hankalinta.”" "Azeema ta fahimci magana take neman fada mata, kallanta tai tace “sosai amma yawanci" zakiga indai kinsamu yarinya mai jin magana sai kiga kafin ma akai ga haka tafahimta.” Ran Hajjo ya kai matuka gun baci ta kalleta tace “Hakane sai dai akwai lokacin da maza kan taka "rawar gani sosai akan rayuwar kannensu, oh bama wannan ba a rayuwar mu ta bahaushi duk" yawan jikokinka indai daga gun ‘ya’ya mata suke to ba naka bane.” "Azeema ta jinjina kai tace “hakane, sai dai akwai yara dawa Hajjo da baki sani ba wanda daka" haifesu gwarama babu.” "Fuskar Hajjo ta canza sosai a wannan lokacin dan ranta yakai matuka gun baci, dan har fuskarta" sai data nuna. "Dariya ragowar mata suka sa saboda sun fahimci hakan, Ramlatu tace “ hakane sai dai kowa" nasan ganin nasa.” "Azeema ta dan yi dariya kadan tace “sosai, ai gani naka akwai dadi.”" Gaba daya hirar ta rage armashi saboda Hajjo tunda ranta ya baci bakomai ma take sa baki. ****** Yana tafe yana waige waige dan ya rasa ta ina zaibi. Ita kuma wacce ranta ya baci saboda haushin zancen Yariman Gobir din nan da ake mata ta taho "cikin bacin rai, tana shawo kwana shi kuma yana juye juye." Sam bai kula dasu ba yasha gabansu yana waige waige. Yauce rana ta farko da wani bawa zai tsaya a gabanta. Cikin tsananin zafin rai ta kalli Bawan dake kula da ita. "Kusa da Junaid ya isa yace “kai dan gidan bafaden, dan gidan asararru, dan gidan wanda basu" san kansu ba.” Cikin mamaki Junaid ya kalleshi dan baisan me ya aikata ba haka ake buga mai zagi haka. "Bafaden nan ya hankade Junaid daga kan hanya wanda hakan yasa shi ya fadi kasa, kallansa yai" sannan ya kalli mutanen dake bayan mutumin wanda sai yanzu ma ya kula da zamansu. Mikewa Junaid yai cikin mamaki yace “Bawan Allah me nai daka hankadeni?” "Bafaden ya juya ya kalli Gimbiya wacce ta kara kuluwa, kallan Bafaden tai tace “biyoni dashi.”" Tana fadan haka ya cafko Junaid wanda ya kara kallansa yana neman kwace kansa yace “kai "malam, meye hakan?”" "Jansa yai suka cigaba da tafiya, ganin duk maganar da yakeyi Bafaden bashi da niyyar sakarsa ne" yasashi yao shiru. "Zeenatu kam tana tafe tana masifa a ranta dan tabbas taji haushin wannan rainin wayan, wato" yanzu ko wani ma kazami rainata zai fara yi. Bangaren Hajjo tai dan dama can zata. "Tana shiga a harabar tsakar gurun ta kalli baiwarta ta mata alama da ta matso, tana matsowa" tace “Fure debo ruwancan ki watsama wancen bawan.” "Fure ba tare da musu ba tai hanyar bakin tulun, totulo ruwa tai ta matso kusa da Junaid dake" "kallan yarinyar ransa a bace, jiyai an shekamai ruwa ba tare da ya ankara ba." "Wani irin sheka yai sannan ya kalli jikinsa, sannan ya kalli matar, baki ta dan tabe sannan tace" “Fure karo.” Nan Fure ta kara tutulo ruwa ta kara shekamai. "Junaid yasa hannu ya goge fuskarsa idanunsa haryanzu suna kanta, wanda ita kuma tasa a ranta" sai ya daina kallanta zata daina sawa a zuba mai ruwa. Alama tama Fure nan Fure ta kara debo ruwa ta sheka masa. "An debo ruwa na shidan ne, Zubair yace “meye hakan?”" "Juyo tai ta kalleshi wanda ya shigo dan gaishesu, daga bakin kofa ya kalleta, kallansa tai sannan" "ta kali Junaid, ganin haryanzu ya kafeta da ido ta kalli Fure ta kara mata alama, nan fure ta juye shi" a jikinsa. "Ran Zubair ya baci ya wuce ciki, yana shiga ya kalli Hajjo yace “Umma kima Zeena magana.”" "Kallansa tai tare dayimai alama akan yai shiru, Zubair ya kalleta sannan ya kalli waje wanda" hakan yaba Azeema damar fahimta. Kallan Zubair tai tace “me autar tai?” Ta fada tana kallan Hajjo. Nan hajjo tace “kiramin ita.” Yana mikewa Azeema tace “bari naje na mata magana.” "Bata jira amsar Hajjo ba tai gaba, nan sauran mata suka mike, Hajjo kam tana tsoron kar Zeena" ace abu tai mara kyau yasa ita ma ta mike da sauri. Suna fita waje ana kara shekama Junaid ruwa. Cikin mamaki da takaici Hajjo ta kalleta tace “Zeenatu!” "Zeena ta kalleta sannan ta kalli matan dake gun, idanunta ta maida kan Hajjo tace “kalli abinda" yakemin.” "Nan kowa ya kalleshi, ya tsare Zeenatu da kallo haryanzu idanunshi na kanta." "Hajjo ranta ya baci ta kalleshi, Ramlatu ta matsa da sauri ta gauramai mari tace “ka dauke" idanka ko sai munsa an dauke mana su yanzun nan?” Junaid ya dago ya kalli Ramlatu yace “mene?” "Azeema kam idanu kawai ta kuramai, ya yake kama da Junaid dinta?" Wanene wannan? Zeenatu ta matso tace “mene kace?” Kallanta yai yace “to fadamin mena miki? Me na miki da zaki aikata min wannan abin?” Yai maganar cikin fushi. "Baki kowa ya saki, cikin tsananin mamaki, yauce rana ta farko da bawa ya taba magana haka." *Ayusher.* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Bakwai "Ran Zeena ya kai matuka gun baci, kara wanka mai wani marin tai ta kara daga hannu zata sake" "marinsa, Azeema tace “Zeena.”" "Zeenatu ta dakata amma ta kasa sauke hannunta, Kusa da ita ta karaso ta kalleta sannan ta" kalleshi tace “me zaisa ki nemi tada hankalinki? Bawa yayi laifi ki bari a hukuntashi amma yin hukunci da kanki ai wahalar da kanki kikeyi. Bafaden nan ta kalla tace “a kulleshi kar a bashi abinci yau.” Da sauri bafaden nan ya fizgi Junaid wanda ya zubawa duka mata ido yana san gane wacece "mahaifiyarsa, wacce tasa a kamasa ya kalla wacce kuma yafi zargin itace." "Azeema ta bishi da kallo, har suka fita." "Zeenatu ta kalleta tace “Ai naso na zaneshi kafin a kulleshi wlh, da dabulala zan zuzubamai.”" "Hajjo ta kifa mata wani kallo sannan ta juya ranta a bace, ganin yanda abu baiyi dadi ba yasa" kowa ya mata sallama ya tafi. Azeema suna fitowa Barira ta kalleta kadan tace “Gimbiya me yasa kika taimakeshi?” Azeema tai murmushi tace “kina tunanin taimakonsa nai?” Barira tace “haka dai jikina ya bani Ranki ya dade.” "Azeema tai shiru sai can tace “haka kawai nake kallan Junaid a cikinsa, hakan yasa nake tsoron" "abinda za’amai, sai kuma nai tunanin in na taimakeshi nima za’a taimaki nawa indai yanada rai.”" Azeema tai shiru tana tunanin lalai rashin Junaid ne yake damunta wanda gashi har ta fara ganin kamaninsa a kan wanda ta fara gani yau. ******** Hajjo ta zubawa Zeena wata muguwar harara tace “ni wai dan Allah meke damunki? Wato ke bazaki taba barina na samu kwanciyar hankali ba ko?” Zeenatu tace “yanzu laifina kike gani kenan Hajjo? Kina ganin bawa yana neman maidani kawar "wasansa, ta yaya bawa zai mun kallo haka? Wanda ko mutane basu isa su min ba?”" Hajjo cikin takaici tace “ba sai kisa a rufeshi a zaneshi a can ba? Kawo shi nan din na menene? Akoda yaushe in baki kaskantar dani agaban Azeema ba hankalinki baya kwanciya.” Zeena tace “to ni sam haushi daya dameni ba ina nai wani tunanin haka? Gabans fa yaja ya tsaya.” “Tashi ki ban guri kuma ki cire hannunki daga yi mai hukunci zansa Zubair yamai abinda ya cancanta.” Baki ta turo cikin jin haushin abinda Hajjo tace “ai wlh ko an hanata sai ta mai rashin mutunci.” "Mikewa kawai tai ta fita ba tare da tace komai ba, Hajjo ta bita da kallo tare da girgiza kai, dole" tasamu a aurar da Zeenatu shikedai ne zaisa hankalinta ya kwanta. ******* "Junaid kam na zaune a inda aka garkameshi, guri ne wanda duk kasa ne a gun, sai itace da aka" "samu akayi daki daki karami wanda kana iya ganin na ciki, dakunan da ake rufe bayi insunyi laifi." "Daga can gefe ma wani ne a garkame, kallan Junaid yai yasa dariya yace “me ka aikata kai" kuma?” "Junaid ya kalleshi ba tare da yce komai ba, saboda mugun sanyin dake shiga cikin jikinsa, ga gari" da sanyi ga kuma ruwan sanyi na tulu. "Amma wannan wace irin muguntace, me ya mata? Ransa yakai matuka gun baci, muryar na" gefensa yaji yace “da alama laifi kai sosai harda ruwa?” "Junaid ko kallansa yanzu baiyi ba, ya runtse idanunsa yanajin wani mugun sanyi na ratsashi." Yaushe zasu bude mu? "Abinda ya tambayi bawan kenan, mutumin yasa dariya yace “yaushe? Lalai yaran nan ka" "rainamin hankali, kanaso kacemin bakasan in aka kulle bawa sai yayi kwana hudu ba?”" "Da sauri junaid ya bude idanunsa ya kalleshi, kwana hudu? Bama awa hudu ba?" "Binta? Azi? Hari? Abinda ya fado mai kenan, yanzu in Azi yai ta nemansa fa?" In Binga taga bai dawo ba ya zatai? Hankalinsa ne yakai kololuwa gun tashi. Ya zaiyi? "Yana nan a zaune gaba daya hankalinsa ya gama tashi, balle dayaga rana ta fadi." ******* "Wannan littafin na kudi ne, ga duk mai san siya bai san yanda zaiyi ba ya tuntubi number daya daga cikin marubuta na Haske, mungode." ******* "Azi sai kara duba hanya yakeyi, sai dai ba alamar Junaid, ganin dare ya fara yi sosai yasa ya koma" "cikin masarautar cikin tashin hankali, da kuma fatan Allah yasa ba wani abin ne ya sameshi ba." "Abinka da gida katu, Azi duk ya rasa ina zai zagaya." "Junaid kam gaba daya hankalin sa ya gama tashi, gashi ba wanda yake a gurin sai dakaru." Ya ja baya yasa kansa akan itacen nan yana tunani. Kai! "Abinda yaji ance kenan, da sauri ya bude ido, yarinyar nan ce ta dazu." Kallansa tai tamai alama daya matso. Da kamar kary matso sai dai san ta yafemai ta bari ya fita yasashi matsowa. Kallansa tai tare da yin wani murmushin mugunta tace “Kana tunanin zamanka anan shine samun saukinka?” Junaid ya kalleta sannan yace “dan Allah kisa a budeni akwai abubuwa masu amfani daya kamata nayi yanzun nan.” Baki ta sake tana kallanshi kafin ta saki muguwar dariyar tace “masu amfani?” Kamar me da me kenan? "Junaid yai shiru tace “ayyya ya za’ayi dan wallahi sai kayi kwana goma a cikin nan, aso samuna" "na ma sai kayi wata, zaka san ni Gimbiya Zeenatu ni ka zubama ido.”" "Ta juya tana neman tafiya, da sauri ya sa kansa a jikin itacem yace “kiyi hakuri ki barni na fita.”" Kallansa ta juyo tai sannan tace“sai naga kana zubarda hawaye sannan kukan ma sai kayi na jini tukun na.” Ta juya ta tafi. "Junaid ya bita da kallo cikin mugun takaici, bawan nan ya kalleshi yace “wai Gimbiya kama" laifi?” Junaid bai kalleshi ba ya koma ya zauna. "Bawan yace “yaro kana ruwa, Allah ne kadai zai ceceka wlh.”" Junaid ya kalleshi yace “da gaske saita bari sai nai kwana goma?” Bawan yasa dariya yace “kai daga wani kauyen kake ne? Yo nasan ko a kauye kake kasan abinda zai yiwu.” "Junaid yai shiru, Bawan yace “ka nutsu in kayi sa’a ta sakeka nan da kwana goma.”" Junaid ya runtse idanunsa cikin tashin hankali. Ta ko ina Azi ya nemi Junaid har alfijir ya fito bai huta ba. "Ganin abu yaki yiwuwa kawai ya koma bangaren Mai martaba, dole ya fadamai, to amma yace" me? "Yana neman komawa yaji wasu da suka fito zasu nufi massalaci suna cewa, kace jiy yaji jiki?" "Dayan yai dariya yace “nima sai dare naji labari, ai da badan an hana kashe bayi ba inaji yaran nan da sai ya sheka barza’u." Gaban Azi ne ya fadi ya kallesu da sauri yace “wanene yai laifi?” Hannunsa da ya rike ya ture yace “ina muka sanshi? Muma labari mukaji.” Da gudu Azi ya juya ya nufi indai yake tunanin samunsa. "Junaid na kishingide ya gaji dajin munsharin dayan, ya mike ya zauna, daga nesa ya hango Azi," "cikin tsananin farin ciki, ya ke kallan Azi harya karaso." Azi idanunsa suka ciciko yace “waye yama wannan wulakanci? Waye wannan. ” "Muryarsa ce ta fara rawa saboda karayar zuciya, Junaid ya kalleshi yace “Azi.”" Kallansa yai yace “tunda nasan inda kake bari na sanarwa Mai martaba.” "Idanu Junaid ya zaro yasa hannu ya jawoshi dan kusa dashi, cikin rada rada yace “karka kuskura," ka wuce ka koma gida gun Binta dan nasan tana nan hankalinta a tashe.” Ni zan taho da zarar ta budeni.” Azi ya kalleshi yace “yanzu Yar wali kana cikin wannan hali zan tafi gun Binta? Kayi hakuri amma bazan iya barinka ba.” Shima cikin rada yai maganar. "Junaid ya kalleshi yace “umarni na baka, ka wuce yanzu ka koma gida, in hankalinka bai kwanta" ba nan da kwana goma sai kazo mu tafi.” "Azi kam hankalinsa ya tashi, ya kalli Junaid zaiyi magana wannan Bawan yace“ah wai har gari ya" fara wayewa.” Junaid ya kallo Azi yace “ka wuce kafin ya mike zaune.” Azi ya juya yana kamar wanda bashida laka a jikinsa....... ******** "Binta dukunkune cikin dakin Yarima sai kuka kawai takeyi, Hari tayi lalashi harta gaji, daga baya ma zazzabine ya rufeta, amma duk da haka idanunta bai bar zubar da kwalla ba, saboda jikinta ya gama bata gidansu ya koma ya barta anan." "Cikin kuka tace“mahaifinki ma ya cillar dake ko nemanki baya yi, ga Junaid shima ya yada ke.”" Kuka ta kara sakawa....... *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Takwas "Zaune take a bakin gado ta dafa kanta wanda yake sara mata, tabbas yaran nan kamarsa daya" "da Junaid ba idanunta bane yake mata gizo, mikewa tai a hankali ta fito falo." Bari na tsaye tana ba kuyangun umarni yanda zasu gyara gidan. "Tana ganin Azeema ta fito ta nufi gunta da sauri, Gimbiya lafiya? Da sassafen nan?" "Azeema ta kalleta tace ""Bari kaini inda yaran nan yake, inada tambaya da zan mai.""" "Bari cikin mamaki tace ""wani yaro?""" "Azeema ta kalleta, ""yaran jiya?"" Bari ta tambaya." "Kai kawai ta daga mata, nan suka shiga cikin daki, bari ta yafa mata wani dogon mayafi, suka fito." "Sum sum sum suke tafiyar saboda basa san wani ya gansu, da yake kuma safiya ce kowa na" "dakinsa, sai bayi suma kadan daga ciki." "Azi na jingine da ginin hankalinsa a tashe, yana tunanin gaskiya bazai iya tafiya ya barshi cikin" wannan halin ba. "Hango mutane biyu sun nufo gun ne yasa ya boye, wucewa sukai, Bari t leka taga dakarun gun" "basanan, dan dama Azi dazai shiga ne ya aikesu." "Ciki suka shiga da sauri, bari ta kalli Junaid sannan taga wani a gefe, gashi a kwance amma da" "alama idansa a bude yake, bari tace ""kuyi magana bari naje can.""" "Tana fada ta nufi dayan gun da yake, bawan Allah tambaya nake." "Mikewa yai daga kwancen, ta tare saitin da Azeema take ta fara mai tambayoyin shirme, dayake" mutum ne mai san magana ya biye mata yanata bata labari. "Junaid ne ya kalleta, ya ganeta, itace ta dazun nan." Shiru tai ta zubamai ido wanda harya fara tsarguwa. "Idanunta sun ciciko suna neman zubar da kwalla, gaba daya jikinta rawa yakeyi, gabanta sai wani" "irin faduwa yakeyi, a hankali tace “Junaid?”" "Kallanta yai zuciyarsa ta fara harbawa, itace kenan? Abinda yazomin a ransa kenan." Ganin yanda yai da idanunsa ne yasa tace “Junaid?” "Jikinsa ya kalla, ya tuno abinda ya faru dashi jiya a gabanta, kallanta sannan ya wawaiga ya nuna" kansa yace “ ni?” "Jikinta ne ya saki, ta kalleshi a tsorace tace “Junaid?”" Yace “wai ni?” "Hankalinta ne ta tashi ta kalleshi, idanunta suka zubo da kwalla ba tare data sani ba, shima nashi" "idanun ne suka fara rauni, daurewa yai ya kalleta yace “ wani kike nema Gimbiya?”" Kallansa tai tare da goge hawayen tace “ ya sunanka?” "Wali ta fada yana kallanta, kai ra jinjina gaba daya jikinta ya mutu, tai murmushin yake tace “ a" ina kake?” "Shiru yai yana kallanta itama kallansa take tace “ ba a nan garin nake ba, zuwa nai, sannan" inada iyaye da kane.” "Shiru tai tana kara kallansa, tace zaka iya cire rawaninka? Kasan kanka zan gani.”" “ kasan kaina?” Tace “eh.” Yace “ Me kikesan gani?” Yai maganar adan raunane. "Kallansa tai tace “ ina duba zan fadama, sannan bakai kama da bayi ba, ko daga kalamanka.”" "Mikewa yai yace “ dan Allah Gimbiya ki yafemin, ku barni sa raina, bansan mena aikata ba, yau" "na fara zuwa gidan sarauta dan Allah ku taimaka ku barni na fita, iyayena na jirana.”" "Jitai kanta yana kara sarawa, da gaske Junaid ne yake mata gizo a fuskar yaran?" "Bari ce ta mata alama da tai sauri, hakan yasa ta kalleshi tace “kayi hakuri in na bata maka.”" Harta juya tana neman tafiya yace “wa kike nema?” Juyowa tai ta kalleshi sannan tai murmushi mai tattare da bege tace “d’ana.” "Tana fada ta juy, Bari ga kalli mutumin tace “nagode fa zan duba abinda kacemin.”" "Ta juya suka fita, suna barin kofar kuwa dakarun na dawowa." "Azi dake tsaye yana kallansu sanda suka fito, shiru yai yana tunani, bari yabi umarnin Junaid ya" "tabbatar zai kula da kansa harya dawo, juyawa yai ya fita." "Junaid kam tana fita ya runtse idanunsa, gaba daya idanunsa suka kada sosai sukai jaa, dazu" "yunwa da fitsari sun matseshi amma yanzu sam baima jin yunwar, meyasa kace mata bakai bane? Bayan zata sa a budeka in taji kai waye." Kai ya girgiza yace sun yadda ni taya zan yarda ta gani a cikin halin tausayi? Bayan ta yarda danta tana rayuwarta yadda ta saba? ********* "Azeema na shig dakinta taga Mai Martaba a zaune a dakin, mamaki ne ya kamata dan ba zuwa" "yake ba sai dai ya aiko taje, yau lafiya?" Kallanta yai sannan yace “daga ina? Da sassafen nan?” Zama tai kusa dashi tace “jinai banji dadi shine nai yar tafiya.” "Murmushi ya sakar mata sannan ya riko hannunta wanda ya dau sanyi, hannunsa yasa ya rufesh," sannan ya fara hura hannun nata yana murzawa. "Shiru tai ta kuraws kasa ido, sai dayaji hannun yayi dumi sannan ya jawota jikinsa yace" “Menene?” "Dagowa tai ta kalleshi tace “wani na gani, kamarsu daya da Junaid.”" Kallanta yai jikinsa yai sanyi yace “ a ina?” Tace “jiya yayina Zeena laifi.” Bawa ne kenan? Tace eh "Da har gabansa ya fadi amma jin haka yasan ba shi bane, balle yasan jiya Azi yazo." "Kwanciya yai a kan gadon sannan ya kwantar da ita kusa dashi, yace “Zaki ganshi insha Allah.”" "Hawaye ne suka zubo mata, tace “da na dauka gyambon ya tafi, amma yau ganin yaran nan ji" "nake bazan iya rayuwa ba Junaid ba, Abdulsalam ka taimaka ka nemon Junaid.” Kuka ne ya kwace mata." "Zuciyarsa gaba daya ta gama karyewa, gaskiya zai kaita inda Junaid yake sai ya fada mata tayi" hakuri ta barshi a can tunda umarnin Sarki Zubair ne. ******* "Zeena tana zaune gaban abincin da aka jera mata, kallan Fure tai tace “jeki sa a kawon yaran" nan.” Fure cikin mamaki tace “Gimbiya.” "Zeena ta zabga mata wata harara, da sauri Fure ta fita, tana zuwa ta sanar dasu sakon Gimbiya" "nan aka bude Junaid, mamaki ne ya kamashi dan yasan wannan yarinyar bazata bude shi ba, ko Ummansa ce? In itace zai bata hakuri y fada mata." "Fure har ta fara tafiya yace mata yana san shiga kewaye (toilet) ban ta kalli dakawan, sukai" kewaye dashi. "Bayan ya gama ne ya tsaya ya kakkade jinkinsa, dan taimama yai yayi sallah a kasa, duk kayan" "sun baci da kasa,yadan gyara rawanin sa dayai sannan ya fito." "Fure na gaba yana binta a baya, tsayawa yai cak? Dan yanzu ya ganeta itace mai zubamai ruwa" "jiya, kenan yarinyar nan ce?" Fure ta juyo ta kalleshi tace “muje.” Junaid ya hade fuska yabi bayanta. "Tana zaune haryanzu bata fara cin abincin ba aka shigo dashi, kallansa tai sannan ta fara cin" abincinta. "Dayake yunwa yakeji kamshin abinci yasa yunwar ta motsa sosai, Zeena kam cin ahincinta take" "harta gama sannan ta kalli Fure ta mata alama da a dauke, nan Fure ta sa aka kwashe." Zeena ta kalleshi tace “fita waje ka tsaya a tsakiyar rana.” "Da sauri ya kalleta, tace me? Bazaka iya ba? Ko kafi karfi?" Mikewa yai ya fita waje ya tsaya a tsakiyar rana. "Daga ciki ta wangale kofa tana kallansa, murmushin mugunta tai sannan tace “bani hakuri.”" "Kallanta yai, Binta! Abinda ya fado masa a rai kenan, ya daure yace “yahkuri.”" Dariya tasa tace“haka ake bada hakuri? Ka ban hakuri sosai kace“Gimbiya Zeenatu ki yafemun ki taimaka kiyi hakuri.” Kallanta ya sakeyi tace “kafi karfi?” "Shiru yai kawai baice komai ba, iska tadan furzar tace “karkaga laifina.”" "Mikewa tai ta fito waje, ruwa ta debo da kanta ta nufo inda yake, ta daga hannu zata zubamai" yace “ me zai kareki in na fada?” Da sauri ta kalleshi rai bace tace “mene?” A hankali yace “ kina matsayin Gimbiya bakya tunanin kina kaskantar da kanki gun daga hankalinki akan bayi irin mu?” Idanunta ne suka fifito saboda bacin rai a zafafe tace “mene?” Da dan karfi Yace “Gimbiya Zeenatu ki yafemin ki taimaka kiyi hakuri.” "Huci kawai take saboda bacin rai, yace “na fada ki barni na koma gida dan Allah.”" Kallansa ai tace “gida?” Tasa dariya tace “na fasa kulleka ma bawana zaka zama zanga me zakayi.” "Junaid ya kalleta cikin takaici, yanzu wannan kanwarsa ce? Tunda babansu wa da kani ne? Wani" irin tarbiyya aka bata? *********** "Hankalin Hari ya tashi saboda zazzafan zazzabin da Binta keyi, sai amai take shekawa ta kasa cin" "komai, Hari ta rasa ya zatai, ta bata magani ta zauna kusa da ita tana tausarta akan tasan Junaid bazai taba yadda ita ba......." Nima nace gaskiya. lol *Ayusher Muhd* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Tara Ran Zeena yakai matuka gun baci da taga yanda ya kalleta. A zuciya ta ciklar da kwanan data debo ruwa tai ciki rai a bace. Tana shiga ta hau cillar da abubuwan dake cikin fadar tata. "Tana gamawa, ta wuce ta fito ta kalleshi tace biyoni." "Junaid bai musa mata ba yabita, bangaren Hajjo tai dashi, tace ya koma ya tsaya cikin rana, ita" kuma ta shiga ciki. "Hajjo ta kalleta tace ""kinga damar zuwa?""" "Zeena ta turo baki tace ""Yanzu na tashi.""" "Hajjo ta tabe baki tace ""kardai ki manta anjima zakije gun Yariman Gobir dan mai martaba jiya ya" "aiko a fada miki.""" "Kallanta tai tace ""Wai meyasa kuke san sai kun aurar dani dole?""" "Hajjo ta mata wani kallo tace "" kin girma gundin gundin so kike mu saki a gaba muna kallo kamar" "kawar mu?""" "Zeena ta hade fuska tana cewa ""ni wlh bana sansa da wani bakinsa kamar na. """ Kallan da Hajjo ta mata ne ya sata tai shiru. "Hajjo tace ""baki dai dauko yaran nan daga magarkama bako?""" Kallanta tai a ranta tace ya akai ta sani? "Hajjo ta kalleta tace ""kinyi ko?""" "Zeena tace ""ni ki barni da kaina zan koyamai hankali.""" "Hajjo tace ""ai rashin hakurinki nasan bazaki taba iya barinsa a can ba, wannan rashin hakurin" "bansan ya zakiyi ba in kakai aure.""" Zeena ta juya kai. Junaid na tsaya cikin rana yunwa kadai ma ta isheshi. Jin hirar taso da Hajjo bata mata ba yasa ta fito. "Kallansa tai taga yanda ya dan galabaita tace ""biyoni.""" "Nan Junaid ya bita, duk inda taje bata dadewa take fitowa gashi ko ina sai tasashi tsayuwa cikin" "rana, tun yana daurewa har yunwa ta fara sa kafafunsa dan rawa, rabanshi da abinci tun a gidansu daren shekaranjiya kafin su taho, to gwara a hanya da suka iso Biram sun dan sai gyada sun ci." "Zeenatu ta koma bangarenta, tana zama ana hera mata abincin dare." Daga waje tana kallan yanda Junaid yake daurewa da alama yunwa ta kusa mai ila. "Kallansa tai sannan ta kalli Fure tace ""zuba abinci ki ba wancan.""" "Fure cikin mamaki tace ""eye?""" "Zeena ta kalleta, hakan yasa ta yin saurin zubawa, fitowa tai da abincin ta kalleshi tace ""gashi.""" "Junaid ya kalleta sannan ya kalli Zeenatu wacce itama kallansa take, harya kai hannu zai amsa" "Zeena tace ""Fure? Uban wa yace ki zuba abincina ki ba wa wani bawa?""" "Fure cikin mamaki ta juyo ta kalli Zeenatu, Kin dawo nan ko sai ranki ya baci?" "Fure ta juya da sauri, Junaid ya kalleta, yanzu kam ya gane wani salan wulakanci ne yasata sawa" a kawo mai. Fure na komawa ta amsa ta ajiye sannan ta fara cin nata. Lomarta uku aka aiko akan taje Yariman Gobir na jiranta. Ranta ne ya baci wanda ko abincin ma bata iya cigaba da ci ba. "Haka Fure ta tayata ta canza mata kaya, ta mata kwalliya, fuskar nan tata a hade bakin ciki da" takaici duk ya isheta. "Tana fitowa tsa hannu ta dau gwaibar dake cikin kwano, ganshi tai a tsaye, kallansa tai tace" “biyoni.” Ta kalli Fure tace ku tsaya na dawo. Mamaki ya kama Fure tace “amma Gimbiya. ” Zeena tai gaba wanda ya hana Fure kara magana. "Junaid yabi bayanta yana tafe a baya tana gaba, juyowa tai ta mikamai gwaibar, ansa yai tare da" cewa “na meye?” Bata kalleshi ba tace “bansan ka mutu min a auramin laifin kasheka.” "Haushi yasa bai bata amsa ba, harta dan cigaba da tafiya sai kuma ta tsaya ta juyo tace “ina" "tunanin abinda zan maka, dan Allah wannan abinda ke yawo akanka sai na saitashi.” Ta juya." Wani kallo ya mata sannan yace “naji ko menene kimin amma dan Allah ki barni na koma gida na bar iyalaina cikin wani hali.” Kamar baza tai magana ba sai jiyai tace “ iyalai? Aure gareka?” Eh harda yara. "Baki ta tabe sannan ta cigaba da tafiyarta, Junaid yace “yaushe zaki sallameni?”" "“Ban sani ba, sai sanda ladabinka ya dawo?”" Junaid baisan sanda yace “mene?” Cikin sautin dayai maganar ne yasata juyowa a fusace tace “me kace?” "Shiru yai sai kallanta dayai, ranta ya kara baci tace “me kace?”" Yace “bance komai ba gimbiya.” Juya wa tai rai bace ta cigaba da tafiya. "Wani hadaden ginin ne a gun, anmai kwalliya sosai, tsayawa tai ta kalleshi sannan tace “bude" kofar.” "Da sauri ya haura ya bude ta shiga ciki, yana neman rufe musu kofar tace “shigo.”" Nan ya shiga sannan yaja kofar ya rufe. *********** Zaune take a gabansa tace “Takawa ka aika a kirani?” "Kallanta yai sannan ya mike zaune, hannu yasa ya riko hannunta ya dagota daga gun da take" sannan ya wuce da ita cikin turakarsa. "Kofa ya rufe sannan ya dawo kan gado ya zauna, kallansa tai tanasan magana sai dai yanda taga" yanayinsa yasata yin shiru. Zama yai a kusa da ita yace “Azeema!” A hankali ta juyo saitinsa yanda ya kira sunantane yasa ta kasa amsawa. "Kallanta yai yacw “nasan Azeema da rashin hakuri, rashin yafiya, daukar fansa, rashin barin" wani yai nasara a kanta.” Murmushi tai tace “shaidar dakamin kenan? Duk ba shaidar arziki?” "Yace “Sai dai macece wacce tasan kanta, bata shiga hakkin wani, bat taka na kasa da ita, bata" yin abinda zai jawo mata zagi gun mutane.” Dariya tai tace “to naji menene ke faruwa?” "Shiru yai tare da kura mata ido, tace “menene? Kasan halina banda hakuri ko na jira ne.”" Dariya yadanyi kadan sannan ya mike tsaye da sauri yace “dama fada miki zanyi jibi ki shirya "zamu wani guri dake, sai dai mu biyu zamuyi tafiyar sai dakaru guda uku.”" Kallansa tai cikin mamaki tace “ina zamu haka da sai a boye zamu?” Yace “in mun je kya gani sai dai wannan karan duk rashin hakurinki dole ki hakura sai munje can.” Murmushi tai tace “ya na iya? Na hakura.” *********** Ga duk mai bukatar siyan littafin nan ya tuntubi 07084161619. ********** "Zama tai daga inda aka tanada dominta, yarima na zaune ya kalli Junaid yace “dan bamu guri" ko?” "Junaid ya juya zai fita, Zeenatu tace “ni nace ya tsaya.”" Cikin mamaki Yarima yace “kinsan gobe zan koma ina bukatar muyi sallama ne.” Muyi sallamar a haka dan ni wlh bacci ma nakeji. "Shiru yai yana kallanta, murmushin rainin hankali ta saki, Junaid ya fahimci amfani take sanyi" dashi hakan yasa ya juya kawai zai fita. Jiyai tace “ina zaka?” "Junaid ya juyo yana kallanta, Yarima Sulaiman ya hade fuska sosai, balle dayaga Junaid ya kalleta" "ido cikin ido, kallanta yai yace “meye tsakaninki dsshi? Dan ba bawan dazai kalli Uwar gijiyarsa ido cikin ido.”" Junaid ya kalleshi yace “Tuba nake Yarima amma ina da aure.” "Ya juya y fita rai a bace, mexaiyi da wannan? Wallahi ko aura masa ita akai sai san yanda zaiyi ya" gudu daga gunta. "Binta ce ta fadomai, gwaibar hannunsa ya kalla,yai ajiyar zuciya anya binta taci abinci ma kuwa?" "Jiyai gaba daya kansa ya rike, ko ya gudu daga nan tunda ba mai kallansa." Kafin ka fita kofar masarautar ma an kamoks. Dole ya lalabata inta fito tabashi damar tafiya. A ciki kuwa Sulaiman ne ya kalli Zeena yace “wai Gimbiya meke damunki? Sai yaushe ne zaki tsaya muyi magana ta fahimta?” Kallansa tai tace “kafi kowa sanin bana sanka to akan me zaka damu da sai ka aureni? Akwai yan mata a gidan mu ka zabi wacce kake so ka aura amma bani ba.” Cikin mamaki ya kalleta yace “saboda yaran can?” Dama dalilin tahowa dashi datai kenan dan ya korar mata wannan cingan din. Kasa tai da kanta batace komai ba. A zuciye ya mike yace “saboda bawa? Kamar ke? Ina ganinki me aji da hankali? Tir da wannan kazantar.” "Yana fada a zuciye ya fito, banko kofa yak wanda Junaid ya mike daga gun da sauri, wani kallo" yamai sannan ya zubar da yawo a gefensa ya wuce. Junaid ya bishi da kallo. "Zeenatu ce ta fito tana yar hamma, kallansa tai tace “ashe kanada amfani.”" Jin haka yasa yace “dan Allah ki barni na koma gida.” Tace “zan barka dan in ban barka bama rayuwarka anan tana cikin hatsaru.” Bai fahimci me take nufi ba amma bai damu ba yace “ki barni na tafi yanzu.” "Shiru tai tana kallansa, kafin tace “bari nai tunani.”" ********* "Azeema ce ta kalleshi tace “sosai fa suke kama Allah, daka ganshi kaima zakai zatan Junaid ne.”" Yace “Tsabar kina san ganinshi ne amma taya Junaid zai zama bawa a masarautarsa?” Tace “kana tunani?” Tai maganar cikin sanyin jiki. "Yace “sosai, duk inda Junaid yake ai bazai taba zama bawa ba, sarauta a jininsa take.”" Mirmushi tai sannan ta jinjina kai alamar gamsuwa.......... *Ayusher Ce* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma "Suna isa kilisarta ta kalleshi ta taradda Fure a bakin kofa tana jiranta," "Tana ganinta ta sauko da gudu ta matso kusa da ita tace ""Gimbiya kije inji Hajjo?""" "A daren nan? Ta fada sannan tace ""bacci nakeji naje da safe.""" "Tayi wucewata zata shiga ciki, Junaid yace ""Gimbiya.""" "Juyowa tai ta kalleshi tace ""da safe.""" Haka kawai tace tai wucewarta ciki. "Junaid ya bita da kallo rai a bace, yace laifina ne ma dana yarda zaki ce na tafi." "Tana shiga tai kwanciyarta tai bacci, shikam Junaid yunwa ma ta hanashi baccin daya dace, koya" kankalli idanunsa zaka fahimci yana cikin wani hali. "Da safe bayan gari yai haske aka sake zuwa mata da umarnin taje inji Hajjo, yanzu kam ta san" "menene dalilin, ta fito tana neman zuwa, Junaid ya tareta tare da tsugunnawa yace ""dan Allah ki barni na tafi.""" "Kallansa tai tace ""jeka, ta kalli Fure tace ""fitar dashi.""" "Tai gaba, dan itama tana san yabarnan ko dan kar bincike yasa a gano shi." "Suna kokari fita sai ga dakarun bangaren Hajjo nan, shikam Junaid matsa musu yai yana neman wucewa." "Jiyai an cafkoshi, cikin mamaki ya kalle gabjejen mutumin daya kamashi yace ""lafiya?""" Mutumin bai tsaya wata wata ba ya dauremai hannu ya sabashi a kafada ya fita dashi ba tare da ya bar Junaid ko magana yayi ba. "Suna fita daga gun aka sashi a budu akai gana dashi, duk yanda yaso magana ya kasa saboda" "karar da aka sa mai a baki, ina za'a kaishi? Me kuma yai? Wannan tunanin sune suka sashi ya yake ta shure shure." "Zeena ta kalli Fure cikin mamaki tace ""me yai?""" "Fure ta girgiza kai alamar bata sani ba, nan sukai ban garen Hajjo dan tana san taji meke faruwa." "Tana bude kofa a ka kwado abu saitinta, da sauri ta goce cikin tsananin mamaki ta dago rai a" bace. "Hajjo ta gani, gefenta Zubair." "Hajjo sai huci take ranta a bace, Zeena na shigowa ta sallami kowa dake kilisar ya raga daga ita" sai Zeena sai Zubair. "Hajjo ta kalleta cikin takaici tace ""ni zaki zubarwa da mutunci a idan duniya?""" Zeenatu ta kalleta a gabanta na faduwa me tayi? Zubair ya kalleta rai a bace yace “dan iskanci kijewa Sulaiman da bawa kice shine kike so?” Yanzu ta fahimci meke faruwa wato saboda haka ne kenan aka kama Wali? "Zatai magana Hajjo tace “Wlh baki isa ina zaune cikin mutunci na ki zubar min ba, kuma daga" "wannan lokacin ki dawo nan ki zauna, dama na barki kin koma can ne saboda na dauka kinyi" "hankali, amma tunda harni zaki zubarwa mutunci ki fara soyayya da bawa. ”" “Wai Hajjo ke kin yadda? Wasa fa nake mai wlh. ” "Hajjo a fusace tace “wlh idan baki rufemun baki ba sai na fasashi, kuma wanda kika kira da" "saurayinki kin jamai, dan a dalilinki zai fiskanci kabarinsa”" "Zeena tai shiru tana kallan Hajjo, Hajjo ta cigaba “kuma ki lalaba Sulaiman tun kafin mai" "martaba yaji halin da ake ciki, kinfi kowa sanin abinda zan biyo baya in yaji.”" Zeena idanunta ya ciciko tace “Allah wasa nake.” "Hajjo tace “damuwarki ce, amma tunda Sulaiman ya san fuskar yaran bazan yadda wani abu ya" faru akan wani bawa ba.” Zeena tai shiru batace komai ba. ************* "Junaid kam ba’a saukeshi ba sai a wani daki wanda babu komai a ciki sai yayi, cillar dashi ciki" "akai suka ja kofa suka sa key suka fita, duk yanda yake biga kofar yake magana akan a bude mai amma ba alamar akwai wani a kusa, yayi bugun har ya gaji wanda yunwa da wahala suka sashi yin" bacci. "Yanzu kam gaba daya garin Biram ya gama fita masa akansa, da mahaifiyar data yadda shi, da yan" uwan da basuda mutunci sam bai ga abin birgewa a cikin sa ba. "Yanzu kam gaba daya idanunsa sun daina ganin daidai, yana kwance kamar mara rai." ******** "Gaba daya Azeema ta kasa samun nutsuwa, ta aika Bari bangaren Zeena tace mata ba yaran nan," "shiru tai a cikin daki, itadai tanata mafarkai kala kala wanda yanzu kam nemansa take ido rufe domin ta duba bayan kansa, in har taga bashida bakin tawadar da Junaid ke dashi ba to zata cire" ranta. "Safiyyace ta turo kofar bayan tayi sallama, Azeema ta kalleta tare da cewa “kingama zaki" wuce?” Zama tai kusa da ita sannan tace “Umma ni yaushe kika fara bari kowa na sanin halin da kike ciki?” Azeema ta kalleta tace “sharesu kinsan bana damuwa da abinda bai shafen ba.” Safiyya tace “Sarki ya aiko a fada miki wai karki manta.” Dame? Ta fada tana kallan Safiyya. Safiyyah tace “ni ina na sani? Da alama abu ne tsakanin ku.” Auu ta fada tare da cewa to sai da safe. Ganin yanda tai shiru da maganar yasa Safiyyah tasan batasan fada ne. Safiya na fita ta shirya bayan tayi sallar magrib ta fiyo daga dakinta. "Bangaren Mai Martaba suka nufa, suna shiga ciki ta taddashi a shirye yana zaune da alama" tunani yake yi. Shikam tun jiya yake tunani anya abinda yake shirin yi shine mafita garesu? Duk da umarni ne na "Sarki Zubair sai dai yana tunanin bazai iya cigaba da ganin Azeema cikin kunci ba, zai lalaba inta ganshi ta barshi a can yanda Yayan sa ya nema." "Jin an tabashi ne yasa ya dawo daga tunaninsa, ko muryar Zagi baiji ba sanda yake sanarda" isowarta. Juyowa yai ya kalleta sannan yace “muje?” "Kai ta daga alamar eh, nan ya riketa suka shiga wani daki, suka saki bude wani suna shiga ya" bude kofa sai gasu a waje. Cikin mamaki ta kalleshi tace “a yaushe akai wannan barauniyar hanyar?” Yace “tun yaya.” Suna fitowa suka shiga motar dake gefen kan hanya wanda dama jiransu suke. Tana shga ta kalleshi tace “yau na fara shiga abar nan.” Murmushi yai yace “zan dinga daukanki a boye ina yawo dake.” "Murmushi kawai tai batace komai ba, dakaru biyu ne a gaban motar daya na ja daya kuma yana" zaune. "Sunyi shiru a mota kowa da tunanin da yake, sam bata damu da inda zasu ba saboda ba shine a" "gabanta ba, sunyi tafiya mai nisa kafin yadan fara janta da hira, sama sama suke hirar ganin haka ya sashi yin shiru." "A bakin wani kauye yace su tsaya, kallan Azeema yai yace muje?" Cikin mamaki Azeema ta kalleshi tace “ina ne nan?” Hannunta ya rike bayan dogaran sun fita daga motar yace “ ki yafemin akan duk abinda zaki "gani, na sani ban kyauta miki ba, sai dai zan yadda da duk hukuncin da kika yankemin”" Kallansa tai cikin rashin fahimta sannan suka fito. "Dogaran na gaba su kuma suna baya, yana rike da hannunta kasancewar dare ne." "A bakin wani gida suka tsaya wanda ke bayan gari, cikin mamaki Azeema ta kalli gidan gini ne na" "sarauta, kallansa tai ya dan murmusa mata." Bubuga kofar dogarin yai daga ciki akace wanene? "Azi fa fada tare da bude kofar kadan, yana fatan gani Junaid." "Idanu ya zaro cikin tsananin tashin hankali, gani dogarai, shikenan an kashe Junaid." "Abinda kawai yazo mai kenan, yana neman sa hannu aka ne yaji ance “Azi!”" "Da sauri ya kalli inda yaji maganar, Azeema ta kalli wanda aka kira da Azi cikin rashin fahimtar" wanene. Azi cikin rawar jiki yace su shigo. "Nan suka shiga cikin gidan, yarinyace a bakin rariya take kwara amai, Bari na dan bubuga" bayanta? Jin motsin mutane yasa suka juyo. Binta ta dauraye bakinta tareda kokarin mikewa. Ido Azeema ta zaro ganin Bari ta matsa da sauri inda take ta riko kafadarta tace “ba bari bace?” Bari jikinta ya fara rawa ta zube a kasa tana cewa “Gimbiya.” Hankalin Azeema ba karamin tashi yai ba data kalli Takawa tace “meke faruwa?” "Nan ya umarci dogarawan da su fita, Azi ya nuna musu hanyar falan Junaid." Gaba daya Azeema neman zaucewa take tana cewa “ina yarona?” Sarki ya rike kafadarta ya jijigata sannan yazaunar da ita yana cewa “ya isa ya isa.” Hawaye ne suka zubo mata ta kalleshi tace “‘meke faruwa?” Binta dake tsaye jikin kofa rashin karfin jiki yasata tsugunna a gun. Nan AbdulSalam ya kwashe komai ya fada mata ya daura da cewa “Azi ina Junaid din?” "Azeema kam ji take kamar mafarki takeyi, sai zare ido take tana neman danta." Azi ya tsaya daga bakin kofa ya zube a kasa yana cewa “Ranka ya dade yana Masarauta.” Masarauta? Suka fada a tare cikin tashin hankali. "Azi ya sanar dasu abinda ya sani, dan dama bai san me yai ba waya wa laifi da sauransu." "Azeema jin wannan yaran shine Junaid ta tuno sanda ake zubamai ruwa jitai bata gani sosai, luuu tai ta zube a kasa." "Binta kam hawayene kawai ke zubo mata, yanzu kam jin halin da Junaid yake ciki ya kara tadda" "mata da hankali, hawaye ke zubowa kamar wanda ake korosu......" "Ba karamin bacin rai Mai Martaba ya shiga ba da jin zancen nan, had uban waye ya isa ya taba" Junaid a gidan sa? A masarautar da take hakkinsa? ******* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma Sha Daya Azeema tana dawowa hayyacinta ta tace su tafi maza kafin wani abu ya sami danta. "Mai Martaba ne ya kalli Azi yace ""ku shirya gobe da asuba ku biyo motar ice." "Azi yace ""to Takawa.""" "Sun fito AbdulSalam ya tsaya yana kallan Binta datake ta share hawaye, yanzu kam bayan tausayin harda tausayin kanta take? Ta tabbatar yanzu batada inda zata zauna." "Kallan Hari yai yace ""wace?""" "Zubewa tai a kasa tace ""wanda yarima ya taimaka ne, tun tana karama anan ta taso, mamanta ta" "rasu.""" "Shiru yai sannan ya kalli Azeema, bata fahimci me yake nufi ba hakan yasa batace komai ba." "Kallanta yai da alama rashin Junaid ne yasata shiha halin nan, yace ""ta fito mu tafi, in kuma bata" "shirya ba kwa taho gobe.""" "Da sauri Azeema ta kalleshi sannan ta kalli Yarinyar, itakam Binta jin haka ne yasa ta dago ta" "kalleshi, hawaye ne suka zubo mata ta sunkuya tace ""nagode Mai Martaba.""" Waje yai Azeema ta kara kallan yarinyar cikin rashin gamsuwa sannan tabi bayansa. "Binta ta mike da sauri ta kalli Hari tace ""Hari ki taimaka ki tahon da kaya na.""" "Bari ta fahimceta hakan yasa tace ""yi maza kisa takalmi ki bisu.""" "Takalmi tasa da sauri ta kalli Azi tace ""sai kun taho."" Tai waje." "Mai martaba ne ya kalli dakarun nan biyu yace ""daya ya zauna gobe da asuba ku taho dasu Azi," "zamu tafi da yarinyar can.""" "Nan suka amsa daya ya zauna, Binta ta fito ta tsaya a bayansu suka nufi wajen gari." Suna zuwa ya mata alama data shiga gaba ta shiga ta zauna tana tunanin zancensu kenan da "Junaid akan suna san su hau mota, yau gashi ta hau." Azeema kam ko kallanta batai ba dan sam abin bai mata ba. "Suna shiga mota tai shiru, tana tuno abinda Zeena tamai, idanunta ne suka ciciko tare da zubo" da ruwa. "Sarki ya kalleta yace ""tunda mun san inda yake dan Allah ki kwantar da hankalinki.""" "Kai ta daga tare da cewa ""Amma me ya kaishi zuwa a matsayin bawa?""" """Ko ma menene dalilinsa bazai wuce ke yaje gani ba.""" "Idanu ta runtse cikin takaici tana kallo aka wahalar mata da danta da akai, lalai sai ta dau mataki" dan bazata taba barin wannan abin ba. "Har suka isa batace komai ba, haka shima daya fahimceta baiyi magana ba." Meyasa Sarki Zubair zai mata haka? Abinda kawai ke yawo a kanta kenan. "Suna isa suka shiga ta lungun da suka fito, Binta na binsu a baya, sun isa ana alamun kiran sallar" "asuba, Sarki ya jata zuwa turakarsa yace ""Azeema ki jira gari ya waye sai a nemeshi, ki zauna anan.""" "Kai ta girgiza alamar rashin yadda tace ""bani na tafi inasan kadaicewa ne.""" Saketa yai jiki a sanyaye yasan tana ganin laifinsa ne shima. "Kallanta yai yace ""ki tafi da yarinyar.""" "Fita tai taga ta a inda suka barta, kallanta tai sannan tace ""biyoni.""" "Binta tabi bayanta sumu sumu, tana shiga bangarenta Bari ta fito da gudu, Kallan Bari tace ""bata" "guri.""" "Ta wuce daki, Bari ta kalli Binta wacce gaba daya ko kayan jikinta a wahale suke saboda ita kanta" ma ba'a hayyacinta take ba. "Nan ta shiga da ita dakinsu, tana kaita ta fito ba abinda tace mata, Binta ta zauna a kasa tadan sa" kanta a saman gado tare da lumshe idanunta tana tunanin abinda ke faruwa? Bata san sanda bacci yadan zare ta ba. "Azeema tai shiru a daki tana tunanin wannan lamari, hawaye kam sun kasa daina zubowa daga" idanunta. "Gari nayin haske ta fito kilisarta, Bari ta mike daga zaman datai da sauri tace “Gimbiya me" kikeso?” Azeema tace “Ina Zeenatu?” Cikin mamaki tace “Gimbiya Zeena? Naji ance tana gun Hajjo.” Hanyar fita yai wanda yasa Bari matsowa da sauri tace “Gimbiya can zaki da safen nan?” "Wucewa tai batace mata komai ba, da sauri Bari tabi bayanta." "Bangaren Hajjo suka nufa, Hajjo na dakinta tana kishingide tana bacci taji ana buga kofarsa," "ranta bace ta mike zaune tare da bada izini, kuyangarta ce ta shigo tace “Ranki ya dade kinyi baki.”" Cikin mamaki Hajjo tace “da safen nan?” Eh su Gimbiya Azeema ne. Cikin mamaki ta zura alkyaba dinta ta fito. "Azeema na zaune, ta fito sai da ta zauna sannan tace “Azeema lafiya da safen nan?”" Azeema ta kalleta tace “Zeenatu nake nema.” "Hajjo ta sake kallanta cikin mamaki, Zeenatu? Nan ta tura a kirata tana cewa “Laifi tayi ko?”" Zeena ce ta fito cikin abin bacci tana hamma. Azeema tana ganinta ta mike tace “Ina yaran da kika zubama ruwa rannan?” "Da sauri ta kalleta, gaban Hajjo ya fadi shikenan har magana ta kai? Amma meya sa taga Azeema" cikin damuwa me makon tai murna? Badai wani munafircin ta kullo ba? Azeema rai a bace tace “yana ina?” "Zeena ta zaro ido ta kalli Hajjo da sauri, Hajjo tace “ya tafi, cikin dare ya gudu.”" Azeema tai wani murmushi sannan tace “ya gudu? Yaran dake kulle?” Hajjo tace “fada mata bakin sakeshi ba?” Da sauri Zeena tace eh na sakeshi. Azeema tace “ko?” Zeena tace “eh.” "Azeema ta kalli Bari tace “Bari, jeki sanarma mai Martaba abinda Zeenatu tace a gama da inda" Junaid yake.” "Cikin mamaki Bari ta kalleta, Hajjo cikin rashin fahimta tace ta fada mishi inda Jun. ”" Sai yanzu kwakwalwarta takai dakyau tace “Junaid?” "Ta fada hankali a tashe, Azeema tace “ina d’ana? Ta kalli Zeenatu wacce idanunta suka firfito," Azeema ta runtse ido cikin fada tace “idan na kara magana baki fadamin inda yake ba duk abinda ya biyo baya karkiyi mamaki.” "Da sauri Hajjo ta rike hanunta, yauce rana ta farko dataga Azeema haka. Tace “Azeema me kike" san cewa? Wai bawan nan Junaid ne?” Azeema ta kwace hannunta tace “wuce?” Ta fada tana nunawa Zeenatu wacce gaba daya hankalinta ya tashi hanya. Zeenatu ta kalli Hajjo tace “Hajjo ce ta kamashi bansan inda yake ba.” "Azeema ta kalli Hajjo, Hajjo tace “zauna bari nasa a kawoshi, tashin hankalin na menene?”" Gaba tai tace “ya na ina?” "Hajjo ta kalleta da sauri, ta sa takalmi tace “bari muje tare." "Suna fita waje, ta kalli Hajjo tace “na manta da abu a ciki, nan suka tsaya ta dawo ciki." "Zeena tana tsaye inda suka barta, gaba daya kokarin jera abinda ya faru takeyi a kanta." "Ji tai an kifa mata mari, yanda taji marin ne yasa ta gigice, Azeema tace “duk garin nan ba" "wanda ya isa ya marar min da, duk matsayinsa kuwa.”" "Ta juya, Zeenatu ta zube kasa kawai tasa kuka, dan taji marin nan har kanta." Tare suka tafi har inda aka kulle Junaid gaban Hajjo sai faduwa yake tana fatan Allah yasa yanada rai. "Bawan da ya rakosu ne ya bude kofar, ido Hajjo tadan runtse dan jikinta y gama bata ya margaya" lahira. "Ana budeshi Azeema ta hango danta a yashe akan yayi, hankalinta a tashe ta shiga ciki da sauri" "tasa hannu ta dagoshi, jin yana numfashi ne yasa ta saki wani ajiyar zuciya hawaye ya biyo baya." "Kallan Hajjo tai wacce tai tsuru. Azeema ta shiga jijigashi tana hawaye a hankali yadan bude ido," baya gani sosai sai yaga kamar Binta ce kusa dashi dan sam bai kawo Azeema mahaifiyar sa ba. A hankali yace “bin.....bin. ” "Idanunsa ne suka rufe wanda ya kasa ko bude ido, Azeema ta kalli bakinsa duk ya tsage alamar" yunwa da kishin ruwa. Wanda ya bude kofa ne yazo ya daukeshi suka fito. Azeema ba abinda tace sai hawaye da takeyi. Bangarenta suka nufa Hajjo zata shiga Azeema tace “mun gode da rakiya.” Tana fada ta kalli Bari wace ta rufe kofa. "Hajjo tabi kofar da kallo tashin hankali, yanzu a wani hali zata tsinci kanta? Ita? Zeenatu? Da" Zubair dan tasan yanzu ko za’a mutu Azeema itama cewa zatai Junaid ne zai gaji mulkin nan. "Suna shiga Binta na tsaye a waje tana shan ruwa saboda gaba daya jikinta ba karfi, tana ganin an" "shigo da Junaid ta yadda kofin, da sauri ta isa gun tace “Junaid.”" Ciki ya shiga dashi ya kwantar dashi dakin Azeema. "Binta hawaye kawai take ganin yanda duk ya canza, ta kara cewa “Junaid.”" Azeema ce ta kalleta tace “Yarima Junaid.” "Binta ta daga kai alamar to, Bari ta kalla tace “yi maza ki kira wanzami.”" "Nan bari ta fita da sauri, Azeema ta fito falo dan bada umarnin abincin da za’amai da kayan" sawa. "Binta suna fita ta tsuguna gefen gadon tana kuka, dagowa tai tana kallan yanda duk ya canza," "hawayen da takeyi ne ya diga a kan fuskar sa, a hankali ya dan bude idansa sama sama." Kallansa tai tace “Junaid!” Binta? Ya fada tare da kokarin murmusawa sai dai a hankali idanunsa suka koma suka rufe..... "Tausayinsa ne ya kara kamata hankalinta ya kara tashi, hawaye kawai take." *Ayusher* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma Sha Biyu "Azeema ce ta turo kofa, dauke da kofi a hannunta, kallan Binta tai tace ""bamu guri.""" "Mikewa Binta tai zat fita, a hankali yace ""Binta!""" "Juyowa tai ta kalleshi, murmushi ta sakar mai hawaye suka gangaro tace ""Yarima kagane ni?""" "Kai ya daga sannan yace ""Yarima?"" Dan yaune rana ta farko data kirashi da haka." "Azeema ce ta kalleta wanda ya sa juyawa zata fita, mikewa ya shiga kokarin yi yana cewa ""Binta" "ina za. """ "Kallan mahaifiyarsa a gabansa ne yasa ya kalli dakin da yake ciki, sake kallanta yai cikin mamaki," "kofin hannunta ta mika mai wanda madara ce a ciki ta shanu, mikamai tai saboda yanda yakejin jikinsa ne ya amsa ya kafa kai bai sauke kansa ba sai da ya shanye ta duka." Ajiye kofin yai sannan ya kalleta yace “meke faruwa?” Kallansa tai cikin tausayawa ta zauna a gefen sa tace “Junaid!” "Shiru yai yana kallanta yana san jin abinda ke faruwa, hawaye ne suka zubo mata ta gogesu tace" “kasan kullum dakai nake kwana nake tashi? Amma Junaid kana ganina kaki sanar dani kai wanene?” "Abinda ke bakinsa ya hadiya, kallanta yai kamar zaiyi magana ya fasa, mikewa ya shiga kokarin yi" yana cewa “ni zan wuce ni da Binta.” Hankali a tashi ta mike tace “Junaid zaka koma ina?” Kallanta yai yace “yanda kike rayuwarki hankalinki a kwance nima a can hankalina a kwance "yake, tunda kin gani na ganki zan koma.”" Da sauri tace “kana tunanin zan barka ka koma wani gun? Junaid? Baka tausayin mahaifiyar data rasa danta tun baigama wayau ba? Shekarata nawa rabona dakai? Ka rasa abinda zakacemin sai zaka tafi?” "Juyowa yai ya kalleta, zuciyarsa ce ta karaya, shi kanshi yana kewar mahaifiyarsa amma gani yake" kamar mantawa sukai dashi. "Karasowa tai inda yake tace “ka koma ka huta na sa akira wanzami ya dubaka, Junaid bansan" "meke yawo a ranka ba anma ni mahaifiyarka ce, babu uwar dazata ajiye danta a wani gun tai" rayuwar datakeso.” "Shiru yai baice komai ba, ganin haka yasa tace “ kana san wani abu ne?”" Kai ya girgiza alamar a’a yace “Binta tana ina?” Kallansa tai tace “Junaid ” Sai kuma tai shiru tace “ka huta inka tashi sai a kirata.” Kai ya jinjina sannan yace “ina bandaki?” Nuna mai tai da sauri sannan tace “nasa a kawo ma kaya.” "Kaya? Ya tambaya cikin mamaki, tace “eh na tura gun masu dinkin mu na masarauta, nasan" baza’a rasa wanda suka ma Zubair ba.” "Baice komai ba dan baisan ma me zaice ba, juyawa tai ta fita, zama yai a bakin gado yai shiru" "yana tunanin wannan lamari, wai meya faru ne daga sanda aka kulleshi?" "Azeema ce ta turo kofa dauke da kaya, mika mai tana cewa “me kake tunani?”" "Shiru yai yana kallanta, murmushi ta saki tace “inada abubuwa dayawa danake san tambayarka" sai dai ganin yanayin da kake ciki yasa nake jurewa.” "Yanzu kam shima murmushin yai, tace “Junaid!”" "Kallanta yai tace “Nagode daka jure abinda ya faru,nagode wa Allah daya barmin kai da rai.”" "Tausayinta ne ya kamashi, juyawa tai da sauri tabar dakin." "Junaid ya dafa kansa, lalai bai kyauta ba da yake jin zafin mahaifiyarsa bayan abar tausayi ce." "Mikewa yai jikinshi duk ba karfi, wanka yai tare da alwala sannan ya fito, kayan ya saka sannan" ya tada sallah. "Bari ce ta kwankwasa jin shiru yasa ta koma, kara dawowa tai ta kwankwasa Junaid ya bata izinin" shigowa. "Abinci ta shiga jerawa a kan karamin carpet din dake dakin, haka tai ta shigowa dashi tana" "jerawa, data ajiye na karshen ne ta zube a kasa tace “yarina barka da dawowa.”" Kallanta yai yace “ina Binta?” "Tana dakinmu, taci abinci ne?" "Cikin mamaki ta kalleshi, tace an kai mata." Ki duba nasan bata fara ci ba kice mata ta dawo nan. "Cikin tsananin mamaki ta kalleshi, shima kallanta yai yace “da wani abin ne?”" Da sauri tace “a’a” Mikewa tai ta fito kilisar Gimbiya Azeema wacce ke bada sako akan a sanar wa Safiyah halin da ake ciki. Gaba daya Azeema ta kasa zama sai ake take gun yan uwanta na kusa dana nesa. Bari ce ta matso kusa da ita ta sanar da ita abinda Yarima yace “ shiru tai cikin rashin jin dadin zancen tace “ kice taje” Da sauri Barira ta kalleta tace “Gimbiya.” "Azeema ta juyo ta kalleta tace “ki bar Junaid yai duk abinda yake so, ni zan san abin yi.”" Barira ta jinjina kai sannan tai dakinsu. "Kamar kuwa ya sani tana zaune sai jujuya abincin take taki ci, Barira ta sanar da ita sakon Yarima" da sauri ta mike ta dau kwanan tai dakin. "Barira ta bita da kallo, cikin takaici." ********** "Hajjo kam sai matse hannayenta takeyi daga zaune, tabbas gaggarumin matsala na neman" afkowa a tare da ita. Zeenatu wacce ke zaune itama tayi shiru tana tunanin abinda ke faruwa. Zubair ne ya daure yace “wai da gaske yaran nan ne Junaid?” "Hajjo tace “da gaske wlh, yanzu ya zamuyi? Dan wlh akwai gagarumin matsala.”" "Zeenatu ta kalla wacce tai shiru kafin wani murmushi ya bayyana a fuskarta, Hajjo cikin mamaki" tace “ke kuma fa?” Zeenatu ta kalli Hajjo da sauri tace “ya akai bamu gane ba Hajjo? Yaran nan wlh sam baiyi kama "da bawa ba, ko daga yanayin maganarsa zakasan jininmu ne, ya akai idanunmu ya rufe?”" Ran Hajjo ya baci tace “to ke yanzu ana zancen abinda zai biyo nan gaba wato ke abinda ya faru a baya kike maimaitawa?” Zeenatu ta sake murmusawa tace “abin ne abin birg ” Uban hararar da Hajjo ta maka mata ne yasa ta kalli Zubair tace “yaya wai meye na damuwa? Milkin nan fa kowa yasan naka ne meye na wani tada hankali?” Zubair ya kalleta yace “kinba Sulaiman din hakuri?” Tace “kai yaya ana cikin wannan yanayi wake zancen wani Sulaiman?” Hajjo tai dan tsaki tace “aiki Fure ta kiramin Ramlatu.” "Nan Zeenatu ta mike, Hajjo ta kalli Zubair tace “Zubairu karka kuskura adan tsakankanin nan kai" "laifi, kabi kowa a sannu, kai luf kamar baka nan kafin na samo mafita, dan wallahi barin yaran nan" daidai yake da ajiye matsayinka.” Zubair ya kalleta yace “Hajjo kisan yanda za’ai.” "Tace “karka damu, in ta gama rama abinda aka ma danta sai musan abinda zamuyi.”" Yace “kina nufin sai ta rama?” "Hajjo tai wata dariya tace “bakasan Azeema bane, ita a tarihinta bata barin ta kwana ko a mutu" ko ai rai amma sai ta fanshe.” Zubair yai shiru yana tunani. ***** "Suna cin abinci yana tambayeta abubuwan da suka faru tana fadamai, ko mai ya bude sai ya turo" gabanta yace “binta ga kaza kin taba ci kuwa? "Dariya tai tace “Ya Junaid nifa bamu shirya bama wlh, ka taho ka barni.”" "Ahhhh ya rike ciki wai ciwo," Hankalinta a tashe ta kalleshi tace “ Ya Junaid?” Ganin yanda ta rikice yasa ya saki dariya yana cewa “yanzu mun shirya?” Hade rai tai tace “Ya Junaid.” Tai maganar cikin shagwaba. Azeema dake jikin kofa rike da kofar ta kalli Wanzamin dake gefe kansa a kasa tace “ko zaka bari sai anjima?” "Yace to ya juya tare da mata sallama, shiru tai tana tunanin wannan yarinyar, itafa danta bazai" "zauna yana biyewa yarinyar nan cikin masarautar nan ba, wanda tasan yanzu idan kowa kansa zai" koma. *Ayusher* "Dan Allah ku daina min sharing din littafi, ina iya bakin kokarina na ganin an zauna lafiya da kowa," dan Allah wannan littafin na kudi ne ku daina yadamin shi. Nagode *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma sha Uku. "Haka sukai ta hirar su kamar ba wata matsala a gabansu, wanda hakan ba karamin batama" "Azeema rai ba, zama tai a kilisarta tai shiru tare da zubawa kofar ido." Barira ta sunkuyo tace “Gimbiya haka zamu barsu?” Kallanta tai tace “kinsa a gyara bangaren Yarima?” "Tace “eh na tabbatar ma sun gama, badai tare zaki bar ”" Wani banzan kallo data mata ne yasa ta yin gum da bakinta. Azeema ta mike ta shiga dakin. "Suna dariya suna ganin ta sukai shiru, Junaid ya kalleta, Binta kam saurin mekewa tai tsaye ta ja" baya. "Azeema ta kalleta tace “Gashi ganinki yasa Junaid ya ware, angode.”" Binta tai kasa dakai tana kallansa. Murmushi ya sakar mata. Azeema ta zauna a bakin gado tace “Junaid!” "Yanda ta kira sunan nashi ne ya sa shi kallanta bayan ya amsa, tace “an gyara maka ban garenka," "zamuje yanzu ma kaika, dan gobe za’ai taron murnar dawowarka." Ta danyi ajiyar zuciya sannan ga cigaba “Sai dai inaso kai da Binta ku rage nuna mu’amalar ku cikin jama’a.” "Kallan Binta tai sannan ta kalli Junaid, Binta!" "Junaid ya kirata, nan bamu guri ya fada yana kallan Azeema." Binta ta mike tai waje. "Azeema ta kalleshi tace “Junaid kai yarima garin nan ne, idan kowa akanka yake, me kake" tunanin za’ace in aka ganka da mace budurwa?” Junaid yace “menene damuwata akan abinda zasuce? Binta kanwa tace wacce na taso tare da "ita a lokacin da banda kowa, ban fahimci dalilin da zaisa na ja baya da ita ba dan yanzu na zama" wani abin.” "Azeema tai murmushi tace “ba haka nake nufi ba, in kana cikin mutane ne sannan Junaid ko ba" dan kai ba ko dan ita ya kamata saboda inba haka ba mutane zasu takura mata.” "Shiru yai bai ce komai ba, tace “ka barta anan sai su dinga kwana da su Barira in yaso da safe sai" ta dinga zuwa.” Junaid ya kalleta da sauri tace badai tunani kake ku zauna tare ba? Yace “me zai haka? Bayan haka muka taso?” Tai shiru kafin tace “ Junaid kayi hakuri ka barta anan.” Kamar zai sake magana sai kuma yaga kamar bai dace haduwarsa ta farko da mahaifiyarsa ba ya dinga bijire mata haka ba. Shikenan. Azeema tace “Nagode Junaid Nagode.” “Ga amanar Binta nan.” "Tace “ni na taho maka da ita karka damu zan kula da ita, sannan Azi da Hari da ragowar bayin" da mukace su taho sun iso su suka gyara ma bangarenka.” "Cikin jin dadi ya kalleta, tace “Junaid!”" Naam "“Kai jinin mai Martaba ne karka yadda wani ya kawo ma raini, sannan duk wanda ya nemi yima" zancen banza. ” Sai kuma tai shiru ganin kamar bayasan maganar duba da yanayin da fuskarsa tai. Murmushi tai tace “Junaid yaushe zaka ban labarin rayuwar dakai.” "“Ba wani labari, mun daiyi rayuwar mu tundaga yarinta har kawo yanzu.”" Kai ta jinjina tace “Alhamdulila.” "Shiru suka danyi saboda rashin sabon dake tsakaninsu, kafin yace “meye dalilin sarki na kaini" can?” "Kallansa tai da sauri saboda batai tunanin tambayar ba, tace “ bansani ba wlh, sai dai nasan" yayi hakane dan hankalin ka ya kwanta.” "“Bawai ina inajin haushi bane, sai dai haryanzu ina ganin akwai dalili bayan waccan.”" Shiru Azeema tai jin kalamansa yasa itama ta fara tunanin tabbas dan kawai Junaid yai rayuwa "hankali a kwance bazai zama dalilin da zaisa ya dauke danta bada saninta ba ya boyeshi, tabbas akwai wani abin kenan? To menene?" Junaid ne ya kalleta yace “karki damu nayi maganarne ba tare da nazari ba.” Murmushi tai cikin jin dadi a kalla yana da dogon nazarin da akesan mai mulki ya kasance dashi. Mikewa yai yace “Su Harin suna ina?” Tace “bari nazo muje.” "Dakin huta, ta mikr tana cewa muje na fara nunama hanya." "Nan suka fito, Binta bata gun hakan yasa yace “Binta fa? Barira tace “ta shiga bandaki.”" Yace “bari na jira ta fito.” Azeema ta kalleshi tace “muje Junaid in ta fito sai Barira ta kawota.” Ya kalli Barira wacce tai saurin cewa zan fada mata inta fito. "Nan suka nufi waje, a hanya sai kallan Junaid ake ana gaisheshi, Suna kokarin yin kwanar dazata" sadasu da bangaren Junaid ne sukaji ance “Barka da Yamma.” "Juyowa Azeema tai, ta hade fuska tsam tare da binta da kallo, Zeena ta karaso fuska a sake," Junaid kam ganin ba dashi ake ba bai ko juyo ba. Zeena tace “Nazo bada hakuri naga zaku fita.” Azeema tace “hakuri? Laifin me kikai?” Tace “Tuba nake na yi abinda na bata miki rai.” "Azeema ta juya batace komai ba, dan bataji zata hakura tabbas sai ta fanshe." Zeena ta bi bayanta tana kallan Junaid tace “Yarima kayi hakuri bansan kai wanene ba lokacin.” "Juyowa yai ya kalleta, tsayawa tai tare da kura mai ido, maida kansa yai hanya baice mata komai" ba. Shiru tai bata kara daga kafarta ba wanda hakan yasa du Azeema sukai gaba. Fure ce tace “Gimbiya menene?” "Zeena ta kalleta da sauri sannan ta kalli gun da su Junaid suke, haushi ya kamata tace “uban me" kike da har suka wuce mu?” Fure tace “tuba nake Gimbiya.” Takaici ya kamata tace “meye ma amfanin fitowar? Ko so kike na bisu kamar jela?” Fure tace “tuba nake Gimbiya.” Cikin takaici ta juya ta koma bangaren Hajjo. Azeema kam wani irin dadi ne ya kamara dataga kallan da Junaid ya mata wanda ta san hakan ne ya tsorata ta tabbas jinin sarautar na nan na yawo a jikinsa. Yana shiga ya hango Azi na gyra harabar waje. "Azi na ganshi ya matso cikin tsananin jin dadi, kasa yai da kansa yace “Yarima.”" Junaid ya kalleshi cikin jin dadi yace “Azi kunzo lafiya?” Azi yai saurin zubewa a kasa yace “tuba nake yarima na barka cikin wani hali.” "Junaid yai murmushi yace “nina umarceka ka barni ai, ina su Hari?”" Suna ciki hala dan da suna nan. "Kai ya jinjina sannan suka shiga ciki, yanda aka gyara gun me gashi kato sosai ya birgeshi." "Azeema tace “Junaid nan asali da bangaren Mai Martaba ne, anan mahaifinka ya zauna, sai dai" shekaru biyar da suka wuce aka kara fadada masarautar wanda aka sakema Takawa wani ginin "shine ya tashi, dazu ya turo akan abude maka.”" Junaid ya kalleta yace “amma hakan ba matsala? Tace “ba wani matsala tunda umarnin Sarki ne.” "Junaid ya jinjina kai alamar gamsuwa yana kara kallan gun, Azeema ta shiga nununamai yanda" gun yake. *** Zeena hartaje zata shiga bangaren Hajjo ta kalli Fure tace “Fure ni me zasuje yi bangaren Takawa na da?” "Fure tai shiru, Zeena tace “kin fadamin ko kuwa?" Fure tai kasa dakai tace “Sarki ya bar ma Junaid.” Ido ta zaro tace “mene?” Kallan Fure ta karayi tace “Hajjo ta sani?” Fure ta girgiza kai alamar a’a. Zeenatu tace mu koma bangarena baza’a huce a kaina ba. ******* "Da sauri Binta ta shigo, sannan ta kalli Kuyangar data jata wai akan an aiketa, Barira ta kalleta" tace “kun dawo?” Binta tace eh tana kallan bangaren Junaid. Barira tace “kije ki huta shima ya tafi bangarensa saboda ya gaji wai yana san hutawa.” Binta tai shiru cikin rashin jin dadin ya tafi ya barta ta shiga ciki. ******* Azeema ta dade acan kafin ta fito ita da kuyanginta. Junaid ya kalli Hari yace “Hari haryanzu Binta bata karaso ba?” Tace “Yarima!” Itakam Hari girma duk ya fara zuwa mata ta kuma san zamansa da Binta bazai yiwu yanda yake "tunani na, sai dai batasan me xatace mai ba." "Junaid ya kalleta yace “Hari ki tura a dubo, dan tazo taga nan.”" Hari tace to Yarima ta fito. "Shiru tai tare da kallan Azi wanda shima kallanta yake, su sun san yanzu Junaid zai san me ake nufi" "da sarauta, ilolinta, matsaloli da kums kalubalen dazai fuskanta....." ********* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma sha Hudu "Har bayan sallar isha’i Junaid baiga Binta tazo ba, ga abincin dare an jera mai amma baibi" "takansu ba, hankalinsa ne ya tashi, fitowa yai ya kalli Kuyangun dake tsaye bakin kofa ya kalli ta" farkon yace “Ina Hari?” "Tace tana daki, yace “kinsan bangaren Umma?”" Tace “Gimbiya Azeema?” "Yace “eh, kije kice ma Binta tazo.”" Tace “to Yarima sannan ta juya.” ******** "Binta zaune a gaban Azeema, Azeema cikin sakin fuska tace “Binta nasan kin damu da Junaid" "sannan kin shaku dashi ta yanda bama zato a lokacin da bashida kowa sai ke, sai dai ina neman" alfarma daya daga gurin ki. "Binta ta kalleta kadan sannan ta maida kanta kasa, Azeema tace “dan Allah ki dan janye daga" Junaid.” "Gaban Binta ne ya fadi, hankali a tashe ta kalleta, Azeema ganin yanda abin ya shigeta yasa ta" murmusa tace “ba cewa nai ki janye daga gareshi gaba daya ba alfarma nake nema ki dan bari wannan uwar data rabu da danta shekara da shekaru ta dan samu damar shakuwa dashi na wasu yan lokuta.” "Idanun Binta ne suka ciciko. Azeema tace “nasan zaki fahimceni, kimin wannan alfarma kinji" Binta?” "Binta ta daga kai alamar to hawaye suka gangaro mata, Azeema ta rike hannunta tace “nagode" "kwarai da yanda kika taimaki dan nan nawa, ma tabbatar samunki kusa dashi ne yasa ya iye jure" rashin mu.” "Wasu hawayen ne suka cigaba da zubo mata, Azeema ta kalli Barira tace “kuje da ita gobe a" hado mata abubuwan bukata.” Barira tace “to Gimbiya.” "Nan Binta ya mike tai bangaren su Barira, tana shiga ta tsugunna tana hawaye, duk da ta fahimci" "Gimbiya sai dai tana ganin ba’a mata adalci ba ana neman rabata da Junaid wanda bataji ko yini zata iyayi bashi, a yanzu haka ma ji take kamar ta ruga inda yake." Binta na shiga daki Barira ta kalli Gimbiya cikin jin dadi tace “Gimbiya kinyi maganinta.” "Azeema ta girgiza kai alamar a’a tace “matsalar ba ita bace Junaid ne, me kike tunanin zai faru" in mutane sukasan ya dawo da mace sannan ba matarsa ba? Macen ma mara asali?” Barira tace “ya zamuyi gobe?” Da safe ki kiramin jakadiya. "Jakadiya? Barira ta tambaya, Azeema ta mike ba tare da ta amsa mata ba, taje shiga daki baiwar" da Junaid ya aiko ta shigo ta sanar da Barira sakon Junaid. "Barira tace “wayyo tayi bacci, tun dazu dama take cewa bacci takeji kanta na ciwo.”" "Kuyangar nan da jin haka ta juya, Azeema ta shiga ciki." "Zama tai a bakin gadon ta kalaman Junaid ne ke mata yawo, tabbas akwai wani dalilin dayasa" "Sarki ya daukeshi, to menene dalili? Baiso danta yai mulki? Kai ta girgiza da sauri dan tasan ba shi bane, tabbas gobe zata bigi cikin Jakadiya taji ko ta san wani abin, dan da dukkan alamu Abdulsalam ma baisan komai ba." Ta dade tana juye akan gado kafin ta samu bacci ya dauketa. *********** "Jin Binta tayi bacci yasa ran Junaid yadan sosu, sai dai baiyi zargin komai ba, yana nan a zaune" yana tunanin cin abinci Azi ya kwankwasa mai. Bayan ya shigo ne ya sanarwa Junaid akan Sarki AbdulSalam na san ganinsa. Tare suka fito da Azi dan dama bai sanshi ba bai taba ganinsa ba. "Sun isa fadar mai martaba, yana zaune an jera mai abinci a gabansa, Ji Zagi na sanarda isowar" "Junaid ne yasa ya kalli bakin kofa, har Junaid ya shigo ya zauna daga can gefe idanunsa na kansa, wani sansanyan murmushi ya saka ya nuna masa kusa dashi yace “dawo nan.”" "Junaid ya karasa sannan ya gaisheshi, Abdulsalam ya amsa cikin tsananin kulawa sannan yace" “Junaid!” Kallansa yai sai gani yai yayi murmushi wanda yasa Junaid din dan murmusawa kadan shima. Wai kaine ka zama saurayi haka? Wasa wasa in yaro ba agabam mutum ya taso ba saurin girman sa zaka gani. Junaid baice komai ba sai dai yanda yake maganar yasa ya dan saki jikinsa. Abdulsalam yace “bismillah.” "Ya fada yana mikamai spoon, Junaid ya amsa sannan suka fara cin abinci tare, sai turomai gabansa" "yakeyi wanda yasa Junaid din aake murmusawa, Sarki ya kalleshi bayan sun gama yace “Junaid!”" "Junaid ya kalleshi tare da maida hankalinsa kansa, ka yafemin nasan duk da umarni ne na" "mahaifinka ban kyauta ba na barinka danai, da alama san kai nane yamin yawa?" Junaid cikin mamaki tace “san kai?” "Abdulsalam ya jinjina kai alamar eh, yace “kamar yanda kasani mahaifinka ne sarki, ban taba" "tunanin amsar mulki daga gunsa ba aka sari maban taba kawowa zan mulki kasarnan tamu ba, sai" "dai daga sanda Yaya ya furta min naji sha’awar hakan, sai dai nasan in har kana nan dole wasu sai sunyi tunanin yin amfani dakai gun karya ni.”" Yadanyi shiru kafin ya kalleshi yace “san kai ko?” Junaid ya daga kai alamaf eh yace “san kai ne.” "Sarki ya kalleshi, Junaid ya murmusa yace “amma san kan mai amfani, akalla bakai kayi tunanin" "fotar dani ba, sannan baka taba tunanin sauke mahaifina ka hau ba, sannan sai daya furta sannan" kaji kanaso.” "Ido Sarki ya kuramai cikin tsananin jin dadin kalamansa, kafin yace “nayi mamaki.”" "Junaid yace “kayi hakuri in na bata maka, sau da dama nakanyi magana ne akan abinda raina ya" bani.” "Sarki yace “hakan akeso ai, ya zama ko za’aji haushi ka aji amma a kalla ka fadi abinda ka sani.”" "Junaid ya kalleshi suka murmusa a tare, Sarki yace “gobe za’ai taron dawowar ka zakaga" "mutane da dama da baka sani ba, yan uwanka da duk baka san dasu ba.”" Yace “haka Um ” "Sai yai shiru, sunan nama wahalar fada?" "Ya kalleshi tare da dan shafar wuyansa, Abdulsalam yace “gashi nima so nake ka dinga kirana da" Abba ba yanda kakecemin Kawu ba sanda kana karami.” "Junaid ya kalleshi da sauri, dariya sosai AbdulSalam yai wanda har fadawa sukai mamakin" "wannan lamari, yace “wasa nake ma, wato har ka fara hangowa ko?”" Junaid yace “ya nuna?” "Sarki yace “sosai, sai kayi kokarin gun nuna abinda ke ranka, dan nan masarautace za’ai amfani" da abinda kake so a cutar dakai.” "Junaid ya jinjina kai alamar gamsuwa, me yasa yaji ya sake da mutumin nan daga haduwa daya?" Lalai y cancanci a kirashi sarki yasan yanda zaiyi yaja mutum jikinsa. "Sunyi sallama Junaid ya fito fuskarsa a sake, Azi yace“da alama Yarima kaji dadin zuwan nan.”" Junaid ya kalleshi yace “ya nuna?” Azi yace “gashinan a fuskarka.” "Da sauri Junaid ya hade fuska yace “Azi, a duk lokacin dakaga ina kokarin bayyana abu a fuskata" "kamin alama yanda zan gane, kafin na saba.”" Azi yi dariya yace “koyarwar da akai yau kenan?” Junaid ya ce “eh.” Haka suka wuce bangarensa ya zubawa abincin nan ido kafin yasa a kwashe sannan ya shiga ya "kwanta, kan binta sosai yake mata ciwo? Yaso biyawa daga gun Sarki saidai yana tsoron karya tashesu daga bacci." *********** "Hajjo ranta yayi mugun baci mikewa zaune tai a kan gadonta cikin tsananin takaici, yanzu" "bangaren da take so ya barma Zubair har fadamai tayi shine ya ba wa wani Junaid? Fuskar tabta hade ranta yayi mugun baci, dan dama dazu da Ramlatu tazo haushi ya kamata da taga itama" "Ramlatun yanzu tsoron Azeemar take, yanzu kuma sai taji wannan zance?" Tayi tsaki yafi cikin kwano kafin bacci ya dauketa. Da safe tana tashi aka kawo mata labarin cin abinci da hirar da Junaid sukai da Sarki jiya wanda har ana jin dariyarsa har waje. "Cikin takaici ta cilar da kofin dake hannunta, wanda ya kusa bige Zeena datake kokarin shigowa" "yanzu, tana ganin haka ta fara kokarin juyawa." Cikin tsawa tace “ina zaki?” "Zeena ta juyo ta dawo ta zauna, Hajjo ta kalleta tace “kinba Sulaiman din hakuri? Kindai san" gobe zai koma ko? Da yau dai tafi ma Takawa yace ya bari ayi taro dashi.” "Kallan Hajjo tai tace “ni wlh ba hakurin dazan bashi, koma naje kara batamai rai zanyi dan wlh" ba sanshi na. ” Hajjo ta buga mata kallo tace “kema nema kike ki batamin rai? Dama tun shigowar yaran nan masarautar nan raina yake baci kema so kike ki karamin da wani?” Zeena tace “Hajjo kinga Junaid din ne? Baki ganshi ba da ya sa kaya har ” “Kin rufemin baki ko sai na sa an kulleki a daki?” "Zeena ta kalleta a tsorace, Hajjo tace “me kike tunani zamuyi a cikin wannan yanayi, dan in" muka bari abu yai gaba daga ni har ku ba wanda zai tsira...” "Zeena tai shiru dan tasan gaskiya Hajjo ta fada, dole su san mafita kafin abu yai tsamari......." ************* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma sha Biyar. "Bangren Azeema tun safe ake ta baki, sai hidima aketayi, Safiya kam itace shugabar taro, sai" "karban baki takeyi, suk ala ala take itama ta samu ganin kanin nata." "Jakadiya ce ta shigo ta baya, inda ta shiga dakinsu Barira, Binta na gyara dakin ta shigo, kallan" "Binta tai tace wacce ke gaisheta tace ""daga ina? Dan ban sanki anan ba?""" "Binta tai kasa dakai dan batasan me zatace ba, Jakadiya tai dariya tace kin dade anan ne?" "Binta tace ""a'a jiya nazo.""" "Jiya? A ranta ta maimaita sannan cikin dabara tace ""oh ko kece kikazo tare da Yarima Junaid?""" "Binta ta daga kai alamar eh, Jakadiya tace da mace ya dawo kenan? Boyeta ake anan?" "Jakadiya tace ""amma kamar ke ba baiwa bace bako?""" "Binta tace eh, Jakadiya tai wani murmushin gamsuwa da abinda take tunani, fuskarta a sake tace" """ina Barira kice na shigo.""" "Binta ta leko, ganin yanda mutane sukai yawa yasa ta koma ciki, Jakadiya ta leka sannan tace" """daure ki fita.""" "Binta ta kalleta tace ""ban hango Bariran ba.”" "Jakadiya ta leko da kanta, daga can gefe ta hango Safiya na hidima tace “jeki gun waccen kice" tazo Jakadiya na nan.” "Binta ta fito tana bin gefe gefe, ba wanda yabi ta kanta saboda sunata hirarsu, kusa da Safiya taje," "ta kasa mata magana saboda tanata magana da wasu, Jakadiya dake leke tana kallanta ta girgiza kai tace “tab harna tausayawa rayuwarki.”" Safiya ganin taki tafiya yasa ta kalleta tace “lafiya?” Binta tace “Jakadiya ce wai tana dakin can.” Safiya ta mike da sauri tai ciki gun Azeema. "Azeema na zaune, Barira tana gyara mata kai, ga kujerar da take kai daga kasa turaren sura ne" "aka sakashi yake turarata, kayan da zata sa na gefe." "Safiya ta shigo ta sanar da ita zuwan Jakadiyar, Azeema wacce idanta ke lumshe ta bude su ta" kalli Safiya tace “ki shigo da ita nan a boye.” "Nan Safiya ta juya ta nufi dakinsu Barira, Binta na tsugunr a gefe ta shigo nan tace “muje.”" Babban mayafi ta rufa mata suka wuce cikin dakin da sauri. Suna shiga Azeema ta kalli Barira da Safiya tace “ku bamu guri.” Nan suka juya suka fita. "Jakadiya na zube a kasa, Azeema ta kalleta sannan tace “Jakadiya! Ya zaman gun Hajiya inna?”" "Jakadiya ta dago tace “lafiya kalau sai abinda ba’a rasa ba, ya sabuwar Jakadiyar?”" Azeema ta kafeta da ido wanda yasa Jakadiya sauke idanunta kasa tare da shan jinin jikinta. Wani kasaitacen murmushi ta saki sannan tace “Me kike boyemin?” Kallanta Jakadiya tak tace “ni?” "Idanta na kanta batace komai ba, Jakadiya tace “me zan boye miki ni kuwa Gimbiya? Girma ya" kamani me zai sa nai abinda zai sani cikin tashin hankali?” Azeema ta murmusa sannan tace “ya akai ni kuma nakeji a jikina kina boyen wani abin?” Jakadiya ta kalleta tace “Wallahi Gimbiya ba abinda nake boye miki” Azeema tace “na yarda wasa nake miki.” "Jakadiya tai ajiyar zuciya, Azeema ta sake kallanta tace “lokacin Marigayi akwai wani abu daya" faru wanda har ya canza yanayinsa?” Jakadiya tai murmushi tace “Gimbiya dama ai dole akwai ranar da zakaji baka jin dadi ko a "batama rai, balleshi Sarki?”" "“Ba irin wannam nake nufi ba, yanayin da harku kuka san akwai matsala?”" "Jakadiya tai shiru tana nazari kafin ta kalleta tace “na kasa tuno komai Gimbiya, a gafarceni.”" "Azeema tace “shikenan, sai dai duk sanda kika tuno ki sanar dani.”" "Jakadiya ta mike, harzata fita ta juyo da sauri tace “Gimbiya!”" "Azeema ta kalleta, Jakadiya ta sake zubewa tace “akwai wani lokaci guda daya, wanda ko abinci" "dakyar yakecin kadan, fita inba fadaba baya zuwa ko ina? In baki manta ba ko ku matansa inkum" nemi ganinsa cewa yake ku koma.” "Azeema ta kalleta da sauri tace “na tuna, amma lokacin ya yanayinsa yake?”" "Tace “ba wanda ya sani, saboda shi kadai yake zama.”" "Azeema tai shiru kafin tace “nagode, zan aiko da sako.”" "Jakadiya tai godiya sannan ta rufa babban mayafin nan, tana fita Barira dama na kofa tai dakinsu" da ita. Jakadiya ta bude kanta sannan ta kalli Binta wacce haryanzu ita kadaice a dakin.” Tace “ina Yariman?” Binta tace “yana bangarensa.” "Jakadiya ta kalleta tace “inhar kinasan kasancewa dashi sai kin cire tsoron dake ranki, nan" masarautace in kika cigaba da haka rayuwarki ma bazaki tsira da ita ba.” "Tana kaiwa nan ta fita, Binta tai shiru tana maimaita kalaman nata, itakam Junaid take san gani" duk abin duniya ya dameta. Tunani tai ko ta fita ta kofar itama ta nemeshi? Ko kallansa tai ta dawo? Wannan shawarar tasata ta fita. ************* "Yana zaune yayi shiru, wata hadadiyar alkyabba dakakiya mai matukar tsada da kyau Azeema ta" "aiko mai da ita, kallo daya kayima Alkyabar nan sai ka sake kallanta saboda tsananin daukan idon da take dashi, ga wani hadaden takalmi na sarauta a gefe." Fuskarsa kawai inka kalla zaka san duk wannan abin baya gabansa. Azi ne ya shigo ya kalleshi yace “Yarima ya baka shirya ba?” Junaid ya kalleshi yace “an dubo Bintan?” Azi yace “anje itama wanka takeyi.” Junaid ya kalli kayan yace “jiranta nake tazo ga gani kafin nasa.” "Azi ya kalleshi yace “inka saka zaku hadu acan gun taron, kaga sai taci gani dakyau.”" Junaid ya kalleshi sannan yace “rikemin wannan nata ne.” "Azi ya kalli ledar ya bude ciki, dariya yasa yace “yanzu Yarima duk abinda kaci sai ka tafi mata" dashi?” "Yace “kaima kasan Binta, ba lalai ta iya cin abinci acan ba, shiyasa zanyi magana mu dawo nan" da ita.” "Hari dake shirin shigowa ta tsaya jikinta a sanyaye, sai dai tasan bazai taba yiwuwa ba." "Azi ma kallansa kawai yake, dan yasan rayuwar dayai acan shida Binta basu isa ko rabi suyi anan" ba.” "Junaid ya dau kayan ya shiga daki ya shirya, murmushi yai yace “harna hango idanki.”" "Aikowa akai akan ya fito, hakan yasa ya karasa shiryawa ya sa turare sannan ya fito." Hari na hangoshi ta hau guda tana cewa “Yarima Allah ya kara lafiya ya kawo zuri’a ta gari.” ************ Cikin fada Hajjo ta kalli Fure tace “bata gama ba?” "Fure ta kara lekawa dakin sannan tace “yanzu take karasawa, Hajjo ta kalli Zubair ta mai alama" daya mata magana sannan ta hade fuska tana cewa “ko uban me takewa kwalliya?” Fitowa tai tare da hade fuska tana cewa “dan Allah Hajjo ki bari na kara gyara fuska ba.” "Kallan mamaki Hajjo ta mata tundaga sama har kasa, bugagiyar hamshakiyar alkyabbar da akai" rabin shekara ana yinta saboda taron sallah shi ta sa? Zeenatu ta kalleta tace “nayi kyau?” "A hankali Hajjo ta kalli fuskarta, sannan ta maida idanunta kan kafarta, takalmin da Mai Martaba" ya kawo mata wanda ko sashi batai ba shi ta sa? Zeenatu tace “Hajjo!” "Bakin ciki tsabar ya cikawa Hajjo rai kasa magana tai, gaba kawai tai Zubair yabi bayanta, sannan" itama ta bisu. "Duk inda suka wuce kallan Zeenatu ake saboda tsabar haduwar datai, wanda koni sai dana sake" waigawa. ******* "Katan filin da aka gyara shi dan yin wannan taran suka nufa, masu hawan doki suna gefe suna jiran a fara dan suyi wasa." "Masu wasan takobi ma na gefe, masu kidan kalangu ma suna ciki, busar sarewa kawai ke tashi." Yarima wanda ya taho akan doki ne ya nufi bangaren Azeema dan su tafi tare kamar yanda ta aika a sanar mai. "Yana shiga yaga bangarenta makil da mutane, mamaki ne ya kamashi ganin jiya fa aka aika, ya" akai mutane dayawa suka samu halarta haka? "Nan ya fara gaisawa da mutane, kowa sai fara’a yake ana mai lale lale da dawowa, duk yanda" yaso ya hango Binta abin yaci tura saboda yawan mutanen dake ta matsowa gunsa. "Safiya ce tazo ta nemi da kowa ya tafi gun taro suma gasunan tahowa, nan kowa ya sa takalminsa" ya fita. Safiya tsayawa tai tana kallan Junaid hawaye suna gangaro mata. "Jiki a sanyaye ya kalli Azi, da sauri Azi ya matso ya radamai cewa yayarsa ce." "Junaid ya matsa kusa da ita, murmushin farin ciki ta hau yi tana goge hawayenta." Nuna mata yai da yatsarsa akan ta goge nan. "Nan ta goge tana dariya, tace Junaid Barka Barka" "Murmushi yai, fitowar Azeema ce ta sa suka maida hankali kanta." "Fadar uban gayun da Azeema tai ma bata lokaci ne, dan ta kashe lokaci ganin ta fito a yanda" takeso. Junaid ya matsa ya gaisheta. "Fuskarta dauke da fara’a tace “Yarima muje mutane na jira, dan wasu komawa zasuyi a yau.”" Kallan cikin gidan yai sannan yace “Binta fa?” "Tace “muje yanzu zasu taho da bata karasa shiryawa bane, kasan mu mata akwai wuyar shiri.”" "Nan suka tafi yana sake waigawa, barira tai daki da sauri dan su fito suma." "Sai dai me? Ba Binta ba alamun ta, idanu ta zaro a tsorace tai kofar baya dan nemanta." "A waje kuwa Binta tana tafe tana neman gidan Junaid, tun abin na mata dadi hartazo ta gaji, sai" neman gun take gashi duk wanda ta nema dan ta tambayeshi daga yaga yanayinta zaiyi gaba. Tana tafe tana share hawayenta dan itakam batama san inda take ba. "Daidai nan ne lokacin dasu Zeenatu da Hajjo suka taho ta kan layin, Binta na share hawayenta" "sam bata gansu ba, sai jitai an bigeta ta baya." Da sauri ta nemi juyawa wanda hakan ya bugi hannunta. Da sauri ta ja baya sannan ta kallesu. "Zeenatu ranta yakai kololuwar matuka gun baci, tana huci ta daga hannu ta sharara mata mari," wanda ya gigita Binta. Tace dago. Binta ta sake dagowa ta kara kifa mata wani marin wanda sai dayasa ta tafadi. "Ta daga wani zata kara mata, Zubair ya riketa yace “ya isa muje.”" Hajjo ta makama Binta harara sukai gaba. "Wani irin kuka tasa tana kiran Junaid, dan tabbas raban da a mareta haka harta manta." "Kuka take sosai, ta kasa ko mikewa." "A can gun tro kuwa duk wannan abin da ake hankalin Junaid baya gun, ganin Binta taki zuwa" yasa ya mike ya kalli Azi yace “muje naga taki zuwa.” Azeema dake zaune kusa dashi ta kalleshi tace “ina zaka?” Yace “naga haryanzu Binta batazo ba?” Haushi ya kamata amma ta murmusa tace “yanzu zata zo ko kuma Azi yaje ya dubo ko basu "gama ba, hakan yayi?”" "Junaid ya kalli Azi yamai alama dayaje, nan Azi ya juya." ************ Ayusher *********** *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* Shafi na Goma sha Shida "Azi na fita su Hajjo na shigowa gun, duk inda Zeenatu ta gifta zakiji ana gimbiya kinyi kyau, kanta" ne ya kara fasuwa ta tabbatar abinda ke kwance a kasan ranta zai karbu. Azeema tana ganinsu ta mike dan tarbar Hajjo wacce kowa keta gaishewa. "Azeema na karasowa Zeena ta matso ta wani riko hannunta, duk da suna shiri da Zeenatu amma yau ce rana ta farko data taba riketa haka." "Zeenatu cikin farincikin tace ""Umma karama barka barka.""" "Azeema tai murmushi duk da daurewa kawai tai saboda mutanen dake gun, sannan ta zare" "hannunta suka gaisa da Hajjo, tare da nuna mata gurin zamanta." "Hajjo ta kalli Zubair tace ""muje ka gaisa da kanin naka.""" Ta fadi haka ne dan ta batawa Azeema rai. """Oh hakane fa ashe Yarima Zubair baiga kaninsa ba.""" A tare suka jera inda Junaid ke zaune mutane duk wanda yazo sai ya gaisheshi sannan yake komawa ya zauna. "Suna karasowa Azeema ta kalleshi tace ""ka gaida Uwar gidan Sarki.""" "Junaid ya gaishe ta fuskar sa a daure, murmushi ta sake tana cewa lale lale Junaid." "Kallan Zubair tai tace ""babban dan sarki.""" "Junaid ya mika mai hannu, suka gaisa." "Ta bude baki zata gabatar da Zeena tai saurin cewa ""ni ai ka sanni.""" "Junaid sai yanzu ya kula da ita, kallo daya ya mata ya juya." "Wannan abu ya bata mamaki, dan har kasa boyewa tai tace ""Ya Junaid!""" "Kallanta ya sakeyi tace ""baka ganeni bane? Duk da nasan na bata maka amma a karshe ai" "nice. """ "Hajjo ce ta tabata alamar tai shiru, fuskar ta ce ta canza dan da a nishadance tazo gun amma" abinda ya mata yasa taji ranta ya baci. "Azeema ce ta nuna ma Azeema gefen Junaid ta zauna, Zubair ya zauna a gefenta, ita kuma ta" "zauna a dayan bangaren Junaid, Zeenatu na gefenta." "Zeena sai cika take, me mutumin nan yake nufi da kallan da ya mata? Kamar irin yaga shara? Ai" ko me tamai bada saninta bane balle ya tuhumeta. "Haushin kayan data saka da bata lokacin datai gun kintsawa ne ya kara kular da ita, meyasa to" takesan ta birge Junaid? Tambayar data zo mata kenan. Da sauri ta kalleshi ya zubawa shirin dawakan da ake ido sai dai inka kula dakyau zakaga idansa ba a gun yake ba. "A hankali ta bi inda yake kallo, hanyar shigowa taga yana kallo, a fili tace ""wani yake jira?""" "Azeema ta kalleta tace ""wa?""" "Zeenatu tai murmushi tace ""naga kamar kofa yake kallo.""" "Azeema ta kalli Junaid sannan ta kalleta tace ""wasa yake kallo""" Zeena ta kara kallansa tace hala ni naga daban. Ta fada itama tare da kallan masu wasan. Gaba daya hankalinsa ya kasa nutsuwa sam abinda ake ma bai sani ba. Busa da taken isowar mai martaba ce yasa Azeema cikin wani farinciki. "Kallansa tai tacemai ""mai martaba ya iso.""" "Hajjo ta kalli Zubair tace ""me yake anan shi kuma?""" "Zubair yace ""Hajjo karki nuna wani abin.""" Kallan Azeema tai wacce ke murmushin jin dadi. "Shigowar mai martaba ya dau hankalin mutane,dan ba wanda yai tunanin zuwansa." "Kusa da Junaid fadawan suka je, Azeema ta mike tana godiya, Sarki ya kalli Junaid yai gyaran" murya wanda yasa kowa yin shiru. "Kallan Junaid yai yace sai kuma ya dan murmusa yace ""ganin bansan me kake so ba yasa nai" "tunanin abu daya.""" "Ya kalleshi yace ""nama alkawari a wannan guri na baka izini ka zabi duk wani abu guda daya da" "kakeso, ko menene shi ni kuma na ma alkawarin yimakashi indai inada hali.""" "Junaid ya mike yai godiya nan aka hau tafa musu ana taya Junaid murna, Hajjo kam ta cika harta" "gama batsewa, yanzu kam ran Zubair ma ya baci dan hannunta ya dunkule da karfi." "Kowa ya gama sanin mezai faru domin abu ne mai sauki, Junaid zai nemi abashi mulki kuma dole" "ne Sarki ya bashi tunda alkawari yai, wannan al'amari ya batawa magoya bayan Hajjo da danta rai, Azeema kam wani dadi ne ya kamata ta sake yima Sarki godiya." "Sarki ya juya ya bar gun, Zeenatu tai shiru itama tana tunanin abinda ya faru a lokacin, me" mahaifinta ke nufi. "Sarki na juyawa Junaid ya kalli Azeema yace ""bari ma duba Azi da alama wani abin ya samu" "Binta.""" "Bai ko jira tayi magana ba ya juya da sauri, bayin dake kula dashi sukabi bayansa." "Kallan Junaid mutanen dake gun sukai, ina zaije bayan wannan taran anshiryashi ne saboda shi?" "Safiya dake gefe ta mike da sauri dan ta tareshi, sai dai kafin ta karasa yabar gun, ganin kar" "mutane su ankara da halin da ake ciki yasa ta wayance da zuwa gun Azeema wacce ta cika fal a kasan ranta, Zeenatu ce ta mike da sauri tana kokarin fita daga gun, da alama binshi take san yi" "taga ina zashi haka, muryar Hajjo taji tace “ina zaki?”" Kallan Hajjo tai sannan tace “kaina ke dan ” "Gun zamanta ta nuna mata da kanta, hakan yasa ta koma ta zauna fuska a hade." "Azeema ce ta mike, cikin nuna jin dadinta da wadanda suka hallari taran sannan ta sanar dasu" wasani kala kala da za’a gabatar nan gaba tare da basu hakuri akan Junaid yadanje ganin wanine amma yanzu zai dawo. Azeema ta kallo Safiya tace “Barira har yanzu bata zo ba ita ma?” Tace “eh bari na dubota” Kiyi masa kafin a ganshi da yarinyar.” "Yarinya? Safiya ta tambaya, Azeema ta mata alama dataje kawai, juyawa tai ta fita, Zeena da" kunnenta ke makale agun taji kalmar yarinya da aka ambata amma bata fahimci me ake nufi ba. Yarinya? Abinda ke yawo akanta kenan...... "Junaid kam yana fita bangaren Azeema yaje, sai dai ba kowa a bangaren, hakan yasa ya nufi nashi" "bangaren, yana zuwa a bakin kofar shiga ma yaga Hari yace “Hari tana ciki ne?”" Hari hankali a tashe tace “Yarima an rasa inda take.” "Idanunsa ne suka fito alamar tsantsan mamaki, hankalinshi a tashe yace “ba’a ganta ba kamar" ya?” Yanda yai maganar kadai zaka san hankalinsa ya gama tashi. "Harira tace “ina zaune Azi ya shigo shida Barira tagun Gimbiya wai suna neman Binta, ganin" bata nan shine suka rabu zuwa nemanta ni kuma na tsaya anan ko zata zo.” "Bai kara tofa komai ba ya juya hankali a tashe, Hari na kiransa amma inaa baibi ta kanta ba," bayinsa ne suka bishi a baya. "Yama rasa ta ina zai fara neman nata ganin yanayi guri ba kadan ba, tunda gashi ko Azi bai gani" ba bare Bari. "Haka sukai ta bi suna nemanta, itama Safiya ta fito da tata tawagar suna neman Junaid su kuma." "Gaba daya jikinsa ya gamayin sanyi gani yake ma ta bar masarautar ne, yana tafe yana dana" "sanim dawowarsa nan, danshi bai ga amfani dawowarsa cikin daula ba ita kuma ta koma ita kadai." "Wata bishiya ya gani, ya tsaya tare da kura mata ido yana tunanin yanda suke zama a bayan gari," yana saman bishiya ita kuma tana kasa suna hira. Baisan sanda murmushi ya bayyana a fuskarsa ba dan gani yake kamar a wannan lokacin akeyi. Harya juya yaji alamun ana cilla dutse karami. "Da sauri ya leka bayan bishiyar, tana zaune rike da kananan duwatsu tana cillawa daga inda take." Wata nannauyar ajiyar zuciya ya saki tare da jingina da jikin bishiyar. Binta jin yanda yaja ajiyar zuciya ne yasa ta juyo ta kalleshi. Idanu suka kurama juna yana daga jikin bishiyar ita kuma tana zaune. Kuka? Me akamin da zanyi kuka? To ya naga idanki haka? Tace “kawai na gaji ne.” Me kike anan? Tunani? A tare suka saki murmushi wanda ya bayyanar da begen juna da sukey. Matsowa yai kusa da ita ya zauna yace “bata kikai?” Ta dan harareshi tace “eh mana garin neman wani.” Dariya yai yace “Ahhh yazanyi da Bintar nan banaji zata ita yini bata ganni ba” Dariya tai itama tace “Ahhhh ya zanyi da Ya Junaid banaji inyaga bai ganni ba zai samu nutsuwa.” Yanzun ma a tare sukai dariya kafin tace “Allah yaya wannan gidan naku yai girma.” Yace “bakya sanshi mu koma?” Kallansa tai a ranta tace ta ina zan sake rabaka da iyayenka? A fili tace “in nace mu koma zaka yarda?” “Kina musu? Kin dai sanni ko?” "Da sauri tace “wasa nake Yarima, ban isa ba.”" “Kin tsorata kenan?” Tana dariya tace “tuni ma.” Mikewa yai yace “muje.” "Mikewa tai suka fara takawa a tare, suna tafe suna hirarsu yana bata labarin abinda akai batanan" duk da shima bakomai ya fahimta ba. "Suna shawo kwana Safiya ta hangoshi, da sauri ta karasa, tace “Junaid kazo ka koma, mutane" "na nemanka, karsuyi zargin wani abin.”" Kallanta yai yace “Ba’a gama ba?” Tace “eh karkasa mutanen da sukazo dominka suji ba dadi.” Ta karasa tare da kallan Binta. Yarinyar dazu? Junaid ne ya kalli Binta yace “muje?” "Kayan jikinta ta kalla, sai a lokacin ta kula da irin shigar dayai da kuma irin shigar da Safiya tai," "jitai tasha jinin jikinta, ta kalleshi tai murmushi tace “a’a kaje ni zan jiraka a inda ka ganni yanzu.”" Kai ya girgiza alamar a’a sannan yace “sai dai in mu tafi tare ko ki zauna gun Hari.” "Safiya ta kalli yarinyar itama cikin rashin jin dadin wannan abu, wacece? Ina ya samota? Da" "alama soyayya ce mai tsananin karfi tsakaninsu wanda ita kanta ganinsu na farko tare yasa ta fahimci haka, tab lalai da matsala......" Muryar Binta ce ta katseta tace “zan jira gun Harira.” Nan suka karasa bangarenshi sai dayaga ita da Harira sun rike hannu sun shiga sannan ya juya. "Harira na rufe kofa ta jawo Binta ta rungume, wanda jin haka yasa Binta sakin kuka, tabbas" "yanzu kam jikinta ya fara bata Junaid ya mata nisa, yafi karfinta........." *Ayusher * *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* *Shafi Na Goma Sha Bakwai* "Azeema ce ta zauna a bakin ta wuce ciki bayan ta gama sallamar da jama’ar ta, tana shiga ta" zauna a gefen gado cikin bacin rai. "Safiya ce ta turo kofar a hankali ta shigo, kallanta Azeema tai tace “ya wuce?”" Safiya tace “nayi nayi ya taho nan yace ya gaji ne amma ni nasan saboda yarinyar nan yake san komawa.” Safiya ta karaso tace “wacece wai?” Azeema tace “ina ma na santa? A can inda suka taso ya hadu da ita.” “Yanzu haka zamu bar yarinya mara asali tana juya Junaid? Taya zamu dawo da abinda muka rasa hannunmu yana haka?” Azeema ta kalleta a hankali ta saki wani lalausan murmushi wanda Safiya tace “Umma me kike tunani?” Kallanta tai tace “ke a naki tunanin Junaid nada wayau a wannan lokacin?” Tace “bangane ba.” "Azeema ta murmusa sannan ta mike tsaye tace “baisan komai ba, banda ita a wannan lokacin, me kike tunanin zai faru in aka kamata da gagarumin laifi?”" "Safiya tace “bangane ba, hankalinsa ne zai tashi?”" "Azeema ta kalleta sannan tai ajiyar zuciya tace “basu kwana biyu zan dau mataki a na ukun, kwana biyun zan barshi ne yai bankwana da ita.”" Safiya ta kalleta dan sau da dama in Azeema na magana ba komai take ganewa ba. Jin kamar ta sauke nauyin dake kanta ne yasa ta mike ta shiga toilet. Safiya ta bita da kallo. ******** "Binta ce zaune Hari na taje mata kai, Hari tace “hanzu kin ware da kikai wanka?”" Kai ta daga tana murmushi tace “Bansan ya akai naji kuka yaki daina zuwa min ba dazu.” Hari tai murmushi tace “Binta!” Naam "Hari tadanyi shiru kafin tace “sai kinyi hakuri dan rayuwar masarauta ba daya take da rayuwar da kika sani ba, sannan dole sai kinyi hakurin janye jikinki daga gun Junaid inba haka ba daga ke har" shi kuma bazaku tsira ba.” Kallanta Binta ta juyo tai tace “bangane ba Hari.” "Hari ta daure mata kanta tace “bazaki gane ba duk bayanin da zan miki sai dai inaso ki kula da mutanen masarautar nan, karki yarda da kowa inba Junaid.”" Binta ta daga kai alamar fahimta sannan tace “Mahaifiyarsa fa?” "Hari ta kalleta tace “itace mace ta farko da zaki kula da ita, dan kowa ansan cikinsa amma ita ba wanda yake sanin nata, sannan ba sarauniyar dazatai murna da danta ya kwaso mata mace wacce" ba yar mulki ba irinki” Binta cikin rashin fahimta tace “ni ai tare muka taso.” Hari ta mike tace “da alama an gama taran naji masu busa sun daina.” Binta na kokarin fitowa Junaid na shigowa bangaren. "Daga nesa ya kalleta cikin jin dadi, gashi tai wanka ta sa kaya duk da kayan ta ne nacan amma tayi kyau." Fuskarsa dauke da murmushi yake kallanta harta karaso inda yake. Tace “wai harkun gama?” "Fuskarsa ya canza yace “ko na koma?” Yai maganar yana neman juyawa, da sauri tace “wasa nakeyi.”" Kallanta yai yace “Muje?” Kai ta daga suka nufi cikin kilisarsa yana nuna mata. Sannan yace “dazu na tafin miki da abu amma Azi ya manta inda ya ajiye saboda nemanki da akai tayi.” Tace “ina binka bashi.” Dariya sukai a tare..... ********** Ran Hajjo yakai matuka gun baci dan abinda akai a tarancan ba karamin bata mata rai yai ba. Kallan Zubair tai tace “kaga abinda nake ce maka ko? Idan har bamuyi da gaske ba yan kallo za’ a barmu a gidan nan.” "Zubair ya kalleta shikanshi abinda ya faru ya bata masa rai, yace “Amma Hajjo abinda mai" martaba yai dazu ya kyauta?” Ramlatu wace ta biyesu ce ta kalli Hajjo tace “sai fa mun dage inba haka ba komai zai lalace ne ba tare da mun shirya ba.” Hajjo ta kalleta sannan tace “Zubair jeka zan nemeka.” "Nan Zubair ya mike ya fita, Hajjo ce ta maida dubanta kan Ramlatu tace “kin samo yanda za’" ai?” Ramlatu ta kalleta tace “karki damu ina tunanin ido zamu zuba komai zai wakana ne in muka sa hannu kadan.” Hajjo tace “me kike nufi?” Murmushi ti sannan ta kara matsowa tace “kinsan ya taho da yarinya daga can inda ya taso?” Cikin mamaki Hajjo tace “yarinya kuma?” "“Eh dazu bakiga ya fita ba ana taro, haka kawai jikina yaban akwai wani abu shine na tura abi bayansa.”" Hajjo cikin kaguwa tace “sai akai ya?” Ashe yarinya yake nema Hajjo mamaki karara ya bayyana a fuskarta tace “meye tsakaninsu?” Ramlatu tai dariya tace “meye tsakanin mace da namiji ai ko daga yanda ya mike yabar gun alamace ta tanada babban matsayi a gunshi.” "Wata irin dariya Hajjo ta saka wanda ki kaina ban taba jin tayi dariya haka ba, har kwallace ta" taru a idanta sannan tace “zanso ganin halin da Azeema ke ciki.” Ramlatu tai dariya itama tace “shiyasa zamu taimaka kadan muja baya muyi kallo.” Hajjo tace “kisa a sanar da cewar Junaid ya taho da mata daga can tana zaune a bangarensa.” Ramlatu tace “angama Hajjo.” "Dariya suka sakeyi, Hajjo tace “ashe fadan ba namu bane, tsakanin uwa sa d’a za’ai.” Ramlatu tace “sosai mu namu ido, har na kosa naga abinda zai faru.”" Hajjo tai murmushin jin dadi tace “nima.” "Zeenatu dake tsaye a kofa zata shigo ne taji suna zancen ta juya ranta a bace tana cijen lebe," yarinya? Itace kenan wacce Azeema ke magana dazu? "Tana shiga bangarenta ta wuce daki ta rufe kofa cikin takaici da jin haushi, shiyasa Junaid ko kallan mutumci bai mata ba dazu kenan?" "Tabbas sai ta dawo da hankalinsa kanta, shiru tai kafin tace meye nawa nasan kaida hankalinsa" kaina? Shiru tai tana tunanin sa tun daga sanda yazo a matsayin bawa har zuwa wannan lokacin data ganshi. "Idanu ta lumshe kafin ta kifa kanta kan gado, tabbas sam Junaid take kuma ta riga tayi alkawari" duk sanda ta samu namijin da takeso ko za’a mutu sai ta sameshi. **************** "Yau wani irin nishadi ya tashi dashi, fitowa falansa yai dan yaji motsin Binta, kallanta yai cikin jin" dadi yace “kin tashi?” Ta kalleshi tace “ ya akai kasan nice?” Murmushi yai sannan ya zauna yace “me kikeyi?” Gyara "Alama ya mata datazo ta zauna, nan ta matso ta zauna tare da kallansa tace “menene?”" Yace “fadamin zakiyi ya akai ranan? Ya akai su Sarki da Umma sukaje can?” Ajiyar zuciya tai sannan ta fara bashi labari. "Kallan bakinta kawai yake tanata magana, murmushi kawai yakeyi." "Safiya wacce tazo dan suyi sallama ta tsaya a jikin kofa, jin yanda abin ke mai dadi ne yasa tasan tabbas da matsala, kwankwasa wa tai sannan ta shiga." "Binta na ganinta ta mike da sauri, Safiya ta kalleta Binta ta mike zata fita, Junaid yace“ina zaki?” “Harira ke nemana.”" Tana kaiwa nan ta fita. Safiya ta zauna tana cewa “ko kunya ta take?” "Yace “kila dan tanada kunya gata batada saurin sabawa da wanda bata sani ba.” Safiya tace “hakane, zan wuce ne nace bari nazo dan nasan ba zuwa zakai ba.”" Yace “a’a bansan zaki wuce ba da zanshigo.” Ta kalleshi cikin kulawa tace “Junaid!” "Kallanta yai bai amsa ba, tace “dan Allah ka dinga zuwa gun Umma, sannan kayi kokarin sakin jiki da ita, bakasan tashin hankalin data shiga na rashinka ba.”" "Kai ya jinjina alamar gamsuwa sannan tacigaba “Umma duk duniya bata hada sanka da kowa," "kowa yasan haka, kai kanka sanda kana karami sanda kake mata daban ne, ya kake tunanin takeji" yanzu gaka a kusa da ita amma Kamar kana nesa da ita?” "Junaid yai shiru sai dai yanzu ya fahimci lalai bai kyauta ba, tace “kayi kokarin canzawa dan" Allah.” Insha Allah! "Abinda yace kenan, ta mike tace “zan wuce.”" "Nan ya fito har waje ya mata sallama, akan sai ta taho da yaranta dan ya gansu." Gana fita taji ana gulma akan Junaid ya taho da mata daga can wasu har da kari wai tana da juna biyu. Hankalinta ne ya tashi ta nufi bangaren Azeema. A zaune ta tadda ita akan kukerarta. "Safiya ta kalleta tace “Umma kinji abinda ke faruwa?” Azeema ta kalleta tace “naji, ynzu Barira ta jiyo a waje.”" Safiya ta zauna cikin tashin hankalu tace “amma ya naganki haka?” Azeema ta kalleta sannan ta dau madarar dake gefenta ta sha sannan tace “kin manta na basu kwana biyu?” “Wani kwana biyu Umma ana cikin wannan yanayin?l Azeema ta lumshe idanunta kadan sannan ta ajiye cup din tace “ki gaida Mahmud.” "Safiya ta zuba mata ido, kamar zata sake magana sai ta fasa, mikewa tai tare da yin sallama ta" fita. Azeema ce ta kalli Barira tace “matsan kafata wajen yatsuna.” Barira ta kalli kuyangar dake gefenta tai saurin matsawa ta fara matsa mata. ********************************** *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* *Shafi Na Goma Sha Takwas* "Kankace zance ya gama karade masarautar nan, ta ko ina zancen da ake kenan, wasu sunce ma" "ciki gareta, a cewar wasu ma wai ta haihu sun boye dan ne, zance dai kala kala." "Azi ne ya shigo da saurinsa ya nufi bangarensu Hari, suna zaune a waje suna tsincs shinkafa ya" shigo. "Daga yanda yaha alamunsa ta fahimci da matsala, mikewa tai ta taso inda yake tace “Azi lafiya?”" Yace “Hari kinji abinda ake cewa?” "Name kenan? Tai tambayar cikin mamaki, Azi ya kwashe abinda yaji ya sanar da ita. Gani yai ba alamun mamaki a tattare da ita yace “Hari kinsani ne?”" Ta kalleshi tace “bansani ba sai dai dama nasan za ai haka.” Kamar ya? "Ta kalleshi cikin damuwa tace “Yanzu ba wannan bane matsalar, matsalar da zata biyo bayan wannan lamari shine abinji.”" "Kallanta yai fuskarsa dauke da tambaya, ta kalleshi tace “indai munaso Junaid ya zama jarumi sannan ya karanci masarauta yasa abinda ya dace dashi dole sai ya shiga halin gagarin rayuwa, a yanda yake yanzu bazai taba yiwuwa ya kwace kansa ba, baka gani baya ji baya ganin komai? Abinda ya sani kawai Binta wanda a yanzu ya kamata yasan mutanen dake kusa dashi, makiyansa da kuma mutanen da zai taimaka, dan haka ka dauke ido, in har yaga Binta na neman shiga wani" "hali lokacin zan san abinda ya kamata yai, karka manta dan sarki ne jinin sarauta.”" Azi ya jinjina kai cikin gamsuwa yace “Nagane Harira Allah yasa komai yazo da sauki”tace Ameen Junaid na kwance a kan kujerar dake falan ya mike zaune ya kalli Binta dake zaune a kasa tana ninke kayansa da aka kakkawo mai. "yace “zo muje mu gaida Umma, jiya banje ba.”" "Ta mike tace “kai kadai ya kamata kaje yaya, bai kamata muje tare ba.” Dan ajiyar zuciya yai yace “bari na kira Azi muje to.”" Ya mike ya shiga daki ya shirya sannan ya fito yai waje. "Da kallo ta bishi a hankali tai murmushi jin dadi, domin ganin Junaid cikin kwanciyar hankali shine kwanciyar nata hankalin." "Azi na dawowa daga gun Hari ya hango Junaid cikin hanzari ya matso, Junaid ya kalleshi yace" “muje gun Ummah.” Azi da sauri ya amsa tare da cewa “ka kyauta yarima.” "Tare suka fito sai dai duk inda suka wuce sai nuna shi ake ta gefen ido, mutane sai kallansa suke" suna gulma. Kallan Azi yai kamar zai tambayeshi sai kuma ya fasa dan gani yake suna kallanshi ne akan basu sanshi ba. Azeema na zaune kuyangarta ta shigo da gudu ta sanar da ita Junaid ya taho. Kallan Barira tai tace “Barira sa a aikata can.” "Barira ta juya da sauri ta fita ta bayan kofa, Junaid ne ya shigo ciki, Azeema na zaune a kilisarta" "gabanta kayan marmari ne, kamar yanda ta saba yauma cikin kwalliya take tasha ado sai dai fuskarta ba kwalliya, sai ma alamun damuwa data nuna s fuskar." Junaid ne ya shigo ta gyara zamanta tana cewa “Junaid kaine?” Cikin halin kulawa ya taho gunda take da sauri yana cewa “lafiya?” "Kuyangar dake tsaye agunce ta kalleshi tare da zubewa ta durkusa tace “Yarima tun jiya Gimbiya bata jin dadi, sai dai tana fitowa ta zauna anan saboda bataso kazo kaganta a kwance. ”" "“Fita daga nan, banace karkiyi zancen nan?”" Da sauri ta sake durkusawa tace “tuna nake Gimbiya sai dai ganinki cikin wannan hali ne ya sani "na fada, ga rabanki da abinci tun jiya.”" "Wani kallo ta mata wanda yasata fita da sauri, Junaid ya kalleta jikinsa yai sanyi, haushin kansa ya" "kamashi, yace “kiyi hakuri Umma kina nan bakida lafiya ni kuma ina can ina bacci hankalina a kwance.”" Murmushi tai na karfin hali tace “karka damu Junaid ba wani abu bane dan ko Takawa bai sani "ba, gajiya ce kawai kila.”" Kallanta yai sannan yace “zaki iya daurewa ki tashi? Kamar gwara ki shiga ki mike akan zama anan.” "Mikewa tai a hankali, ya dauki kayan marmarin da kansa ya shigar mata dasu ciki, bayan ta zauna" ne yace “kina san wani abu?” Murmushi tai tace “bakomai Junaid ganinka ma ya isheni.” Kansa ya saukar kasa yace “ki daure dai kici wani abin.” Tace “shikenan bari nasa a kawon madara nasha.” Da sauri ya mike yace “zauna anan bari nasa a kawo miki.” Yana fita ta bishi da kallo tace waya isa shiga tsakanin d’a da mahaifiyarsa bayan wata tara yai a cikina ni kadai. Cikin ruwan sanyi zaka dawo inda ya dace dakai Junaid. ********* "Barira kuwa tana fita ta shige bangaren Junaid cikin sanda, kamar yanda Azeema ta zata kuwa" Binta na zaune a fadar sa. "Bata ma kula da abinda takeyi ba tace “Binta ashe kina nan, Yarima ne yace ki sameshi a raga.” Raga? Ta tambaya cikin mamaki, Barira tai dariya tace “bakisan gun ba nasan muje na nuna miki, dan shiyasa ma yace na raka ki.”" Tai dariya kadan tare da cewa “da yace zaije gun Gimbiya?” "Eh bandai san me yake nufi ba kamar cewa yai kije kamar kuma cewa yai ki dauko mai abu, kiyi" hakuri kwakwalwar tawace ta fara tsufa.” Binta tai dariya tace “nunamin gun in naje na gani in baya can sai na dawo.” "Barira tace “nagode Binta, suna tare da Gimbiya bansan ko sunje ba.”" Binta ta mike ba tare da dogon nazari ba. "Barira na fita Binta tabi bayanta, Hari taga alamar wucewar Binta sai dai bata hango wanda ya" "fara wucewa ba, hakan yasa bata kawo komai ba." Barira ta nuna mata ragar daga nesa tace “bari taje Azeema ta aiketa. "Binta ta wuce ta shiga, ba kowa agun harta shiga, katan guri ne wanda yake a killece, daga alamar" "yanayin gun kamar an dade raban da wani ma ya shiga ciki, a hankali tace “Ya Junaid?”" Ta shiga cikin dakin tana cewa “Ya Junaid? Yarima?” "Jitai an kulle kofar, da sauri ta juyo ta kalli kofar sannan ta kalli ciki, wanda ba alamar mutum," "dawowa tai da sauri ta tura kofar, sai dai me? Jinta yai tai a karkame, hankali a tashe ta fara bubuga kofar yana turawa, sai dai ba alamar zata bude." Da sauri ta juya ta kara kallan cikin dakin wanda sai yanzu ta kula da yanda yana ta gama zagaye gun tace “ina ne nan?” Tashin hankali da tsoro ne suka shiga ranta. ********** Gani duk yanda tai hankalinta ya kwanta ya kasa kawai ta fito daga bangarenta ta nufi bangaren Hajjo. Hajjo da Ramatu na zaune tana bata labarin yanda labari tasan kafin gobe ya isa gun Mai "martaba, Zeenatu ta fado ciki." Kallan Ramatu tai sannan ta kalli Hajjo tace “Hajjo inada magana dake.” Harara ta kifa mata tace “ke harkina da wani magana da zakiyi dani? Fadi anan.” "Zeenatu ta kara kallan Ramatu, wacce yanzu ta mike tace “ni na wuce Hajjo sai gobe.” Ta" rusuna alamar girmamawa ta fita. Tana fita Zeenatu ta zauna kusa da Hajjo tace “Hajjo nayi tunani na samo mana mafita.” Cikin kallan rashin damuwa tace “ke harkina wani tunanin neman mafita ne bayan kin kasa samosa kanki?” Zeenatu ta riko hannunta tace “me kike tunani in muka raba kafa?” Raba kafa? Hajjo ta fada tana kallanta. Zeenatu tace “Idan Ya Zubair bai samu mulki ba a kalla ni ma samu matsayin matar Sarki.” Yanda Hajjo take kallanta ne yasa tace “Hajjo?kinajina?” Mikewa Hajjo tai tace “wai na tabbatar bakida hankali.” Zeenatu cikin rashin fahimta tace “bangane ba Hajjo?” A zuciye Hajjo ta shiga dakinta ta rufe kofa. Zeenatu ta dafa kanta...... ********** *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* *Shafi Na Goma Sha Tara* "Mikewa tai daga gun ta fito waje inda Fure take, tace “Fure muje bangaren Gimbiya Umma" karama” Mamaki ne ya bayyana karara a fuskar Fure tace “muyi me?” Zeenatu tace “meye damuwarki da abinda zan?” Nan tai gaba tana yar mita. "A can bangaren Azeema kuwa Barira ce ta shigo dauke fa tire ta ajiye sannan ta gaida Junaid," kallanta yai ya mika mata hannu ta mikamai. "Sannan ta rusuna ta gaisheshi tace “bansan ka iso ba yarima naje sanarwa wanzan rashin lafiyar Gimbiya.” Ta kalli Azeema wacce itama ta kalleta alama ta mata da ta aiwatar, Junaid ne yace" “Allah sarki sannu.” Ta mike sannan tace “ina waje Yarima in da akwai abinda kakeso.” "Ya daga mata kai ta fita, kallan Azeema yai ya dara tiren akan cinyarsa sannan ya sa spoon acikin dan karamin kwanan dake dauke da faten wanke wanda yasha kifi da alaiyahu wanda itace tace" amata. "Amsar cokalin tai sannan a hankali ta debi abinci, loma daya tai ta ajiye cokalin tace ta koshi," "Junaid cikin damuwa yace “Umma dan Allah kici abinci, tace “Allah banjin yunwa sai dai in nai bacci na tashi.”" Kallanta yai cikin rashin jin dadin abinda ya aikata yace “to ki kwanta in kin tashi kyaci.” "Kai ta daga sannan ta gyara kwanciyarta, bargo ya ja ya rufeta sannan ya kalleta, murmushi tamai mai sanyi sannan tace “tafiya zakai ko?”" Yace “a’a zan zauna ki tashi.” Cikin jin dadi tace “nagode Junaid.” Ta fada tare da lumshe idanunta. "Zama yai akan kujerar dake dakin yana kallanta, gashi a dalilinshi mahaifiyarsa na neman shiga" wani hali. "Wani littafi ya gani a gefen gadanta a hankali ya jawoshi, murmushi yai daya dubawa da alama" rubutu take kokarin koya aciki. A hankali yaji muryar Barira tace “Yarima!” "Mikewa yai sannan ya bude kofar dakin a hankali, ta sunkuya tace “Yarima dama Gimbiya Zeena ce tazo neman Gimbiya.”" "Fitowa yai tare da rufe kofar a hankali, sannan yace “kice tana bacci.”" Tace “to Yarima amma Gimbiya dauka zatai karya nake mata saboda kowa yasan Gimbiya batasan baccin rana.” “tana ina? "Nan ta nunamai inda take, tana zaune a kilisar Gimbiya, a bakin kofar ya tsaya ya kalleta." "Tunda ya tsaya ta zuba mai ido, tuno abinda ya faru tai tsakaninsu a hankali murmushi ya" bayyana a fuskarta. Kallan Junaid tai wanda ya kalleta shima yace “Gashi kinzo ta kwanta.” Mikewa tai tace “Ya Junaid ka karaso ko gaisawa muyi mana? Ko na karaso?” "Kamar bazai karasa ba sai kuma taga ya nufo gun, zama yai fuskarsa a hade tsam, ta koma ta" zauna itama sannan tace “Ya Junaid haryanzu baka huce ba?” Dame kenan? "“Abinda ya faru tsakanin mu mana, daga yanda kake min magana kamar bakaso yasa nasan baka" huce ba.” Yanzu kam kallanta yai sosai yace “inban huce ba mai zai faru?” Tace “hakan nake so nima ai.” Hakan? "Tace “eh, nafisan ka rama yanda nan gaba bazanyi ta jin haushin kaina akan abinda na aikata ni kadai ba.”" “Ohhh tunda haka ne bari na nasa a rama.” Murmushi tai tace “sai dai kai ka rama da kanka.” "Mikewa yai yace “bani da lokacin wannan, zan koma ciki.”" "Da sauri ta mike tasha gabansa, kallanta yai cikin mamaki, tace “Ya Junaid me kake tunani in" mukaje gun Hajiya Inna ka ganta?” Kallanta yai kafin yai magana tace “baka santa ba ko? Ka gani? Ni zan kaika ka ganta.” In zan ganta sai ta hanyarki? "Ta dansa yatsarta ya dan sosa wuyanta kadan tace “sosai, dan batasan Umma karama kaga nina" dace na kaika.” "Bai bata amsa ba tai saurin cewa “ zanzo gobe ko jibi muje, in Umma Karama ta tashi ka gaisheta.”" "Ta juya da sauri ba tare da taji amsarsa ba, wani kallo ya bita dashi sannan ya juya yai ciki, kamar" yanda ya barta tana kwance tana bacci ya koma ya zauna yana kallan dakin.” *********** "Binta tuntana ihu tana kuka hartazo ta gaji da buga kofar ta gaji dayin kukan, Zama tai a jikin" kofar ta takure tana hawaye. "Harira kam bata kawo komai a ranta ba saboda a tunaninta Junaid tabi, tunda bata fada mata ba" shiyasa batai tunanin komai ba. "Mai martaba na dauraye hannunsa sabuwar Jakadiya tai sallama, hannunsa ya karasa" daurayewa sannan ya kalleta yace “Jakadiya!” Ta zube a kasa tace “ Lafiya Sarkin yakin Sarkin musulmi Lafiya maida garin wani kango Lafiya Barden mahadi Lafiya Sukukun bakaka Lafiya Darzaza amalen sarakuna Lafiya ba hau da wani ba sauke wani Lafiya hana kangara Murmushi yai tare da goge hannunsa sannan ya kalleta yace “meya faru?” "Ta sake kasa dakai tace “Takawa anata rade radin Yarima Junaid yana da aure a inda aka samoshi, matarma har ta kusa haihuwa.”" "Kallanta kawai Abdulsalam yake kafin yai wata dariya wanda shikansa baisan tazo mai ba, yace" “mata? Harda ciki? A ina kika samo shirmen nan?” Kallansa tai kadan ta kara maida kanta kasa tace“wallahi Mai Martaba wannan zance har wajen masarautarnan ya zagaya.” Yanayin fuskarsa ne ya canza yace “mene?” "Tace “tun jiya ake yawo da maganar, gudun kar hankalinka ya tashi yasa na jinkirta sai dai ance" "wai tare suke kwana a daki daya, shine naje na bincika kuma sai gashi na tabbatar akwai yarinya" dake kwana dashi.” Idanun Abdulsalam ne ya canza yace “mene?” "Ta sunkuya tace “gafara Takawa, laifina gagarumi ne ni na sani amma bazan bari wani abu ya" sameka ba.” "Abdulsalam yace “Binta ce amma a bangaren Azeema take, me zaisa kice suna kwana tare?”" Tace “wallahi da gaske Takawa da kaina na bincika.” "Yanda fuskarsa ta nuna bacin rai tsantsa ne yasa ta kalleshi, a hankali ya saki fuskarsa sannan" yace “a aika Azeema da Junaid suzo.” Mikewa tai da sauri ta fita. "Abdulsalam yai shiru yana tunani, bazai yadda da hakan ba harsai yaji da kansa." Azeema ta farka taci abincinta Junaid shima an kawo nashi yana ci. Wani irin dadi take ji wanda tunda taga Junaid bata taba jin irinsa ba sai yau. Kallanta yai yace “Umma ya akai?” Murmushi tai sannan ta mike zaune tace “mamaki nake haryanzu kana nan.” "Yadan sunkuyar da kansa yace “kiyi hakuri, maimakon na duba yawan shekarun da kikai kina jirana, sai kawai na duba yanayi na na rashin sabawa dake dabanyi ba.”" Kai ta girgiza da sauri tace “sam ba haka bane na fahimceka nasan kuma a hankali zaka saba.” Nagode. Murmushi tai sannan a hankali ta mike ta shiga toilet. Tana fitowa tace inka gama muje ka zagaya kaga yanayin gurina. Zaki iya fita? Tace “eh gwara nadan zaga ko naji karfin jikina.” Murmushi yai sannan yace to. "Tare suka fita suka zagaya cikin fadarta, ga gefen shuke shuke, ga hanyar da zata sadata da wani" "bangare, tace “nan ne asalin bangarenka.”" Kallan gun yai kamar mai shirin tunowa sai kuma yai murmushi yace “a bude yake?” Tace “eh muje ka gani.” "Nan suka shiga ciki, tsaf yake kamar wanda akwai mutum a ciki, ga komai akwai a bangaren." "Kallanta yai, tai murmushi tace “nasa an barshi a yanda yake ne akan tunanin kullum zaka dawo gurinka.”" "Tausayinta ne ya kara kamashi, ya kalleta jiki a sanyaye yace “nagode Umma, Nagode da kullum" nake ranki.” "Idanunta ne suka ciciko, ta juya kanta gefe tare da saurin fitowa." "Shima fiyowa yai Barira ce ta shigo gun da sauri, ta kalli Azeema tace “Gimbiya mai martaba na kiranku ke da Yarima.”" “Mai martaba?” "Ta fada tare da kallan Junaid, dakinta ta koma ta kara shiryawa, alkyabarta mai launin ruwan kasa" "ta saka, Junaid na aiken wata kuyanga akan taje tacewa Binta yana zuwa ta fito, bata kalleshi ba har kuyangar ta tafi sannan suka fito tare." Bangaren mai martaba suka nufa yana zaune shi kadai suka shigo. Sai da suka gaisa sannan ya kalli Azeema yace “Azeema meke faruwa?” Tace “name kenan?” Maida idansa kan Junaid yai cikin zargi yace “Junaid a ina yarinyar da muka taho tare take kwana?” Ba tare da wani tunani ba yace “Bangarena.” Da sauri Sarki ya kalleshi yace “mene?” Junaid ya kalleshi sannan ya kalli Azeema wacce ya kasa gane halin da take ciki...... ***** *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* *Shafi Na Ashirin* Mai Martaba yace “wani irin abu nakeji haka? Taya Junaid zai dinga kwana da ita? Bama a bangaren Bayi ba?” Azeema ce ta kalli Junaid sannan ta kalli Sarki tace “Nasan bai kamata ba sai dai ganin hankalin Junaid ya kasa kwanciya yasa na barshi.” “Dan hankalin Junaid bai kwanta ba sai ki bari yai abinda zai barmai tabo? Ke din?” "Junaid ne ya daure yace “Tuba nake ranka ya dade amma haryanzu banga aibu akan haka ba, na farko Binta ba a dakina take kwana ba.”" "Kallansa Mai martaba yai yace “zan ma tambaya, yanzu daka shigo nan a ina kake?”" "“Fadar ka, ranka ya dade.”" To waye ya san kana nan ko kana cikin turakata?” "Junaid yai shiru, yacigaba “yanzu inka shiga cikin dakina ko bandaki na waye ya sani?”" A hankali yace “babu.” To fadamin Yarinyar a ina take kwana?” Junaid ya kalleshi yace “a bangarena.” “Me kake tunani mutane zasu fassara? Abinda basu taba gani ba?” Junaid yai kasa dakai yace “A gafarceni.” "Sarki ya canza yanayin kallan da yakemai, yace “ka maidata bangaren Azeema ko ta koma bangaren bayi ta zauna, na taho ma da itane jin tare kuka taso, ganinta a kusa dakai zai debe ma" "kewa, wannan abinda kakeyi bakasan zai iya janyo ta shiga wani hali ba?”" Junaid jiki a sanyaye yace “Tuba nake.” Sarki yace “shikenan jeka huta.” Junaid ya mike tare da godiya ya fita. "Idanunsa ya maido kanta ya kura mata ido, fuskarta ta hade itama ta kalleshi, yace “me kike" tunani?” Tace “me kuwa? Na bari ne saboda karyaji ba dadi.” Wani irin murmushi yai sannan yace “ke din?” Kallansa tai tace “tundazu kake cewa nidin?me kake nufi.” Idanunsa na kanta yace “badai kishi kike da yarinyar ba?” Kallansa tai da sauri tace “kishi?” Yace “to fadamin menene na barinta ta kwana dashi bayan kinsan za’a yada akan suna kwana tare? Sannan kina ji har gulma ta gama yaduwa ba tare da kin dau mataki ba?” "Ranta ne ya baci ta mike zata fita, mikewa yai ya riko hannunta da sauri, juyowa tai ta kallanshe," hannunta yaja ya shiga da ita dakinsa ya zaunar da ita akan gado yace “haushin me kikaji? Haushin na fadi abinda kika shirya?” "Kallansa tai bakinta tadan motsa sai kuma tai shiru, menene ba haka bane?”" Hannunta ta kwace tace “ya kakeso nayi? Yarona ya dawo amma kamar ya sake barina? Bai damu da mahaifiyar datake jiransa shekara da shekaru ba? Bai damu da yayensa ba? Ba abinda ya dameshi da wace rayuwa nai? Bai damu ya sanar dani rayuwar dayai ba? Komai ka taba zancenshi "daya ne Binta, ya kakeso nayi?”" Shiru yai yana kallanta a hankali ya zauna kusa da ita ya jawota jikinsa ya rungumeta yace “hakan da kikai kina tunanin mafitace?” "Tace “bani nai ba, sai dai hakan zaisa ya nesanceta ko dan samun kwanciyar hankalinta, hakan" zaisa ya maida hankalinsa kaina.” Hannayensa ya sa akan kuncinta yace “shiyasa nace kishi kike.” Dan idanunta ga juya tace “inji wa?” Yace “gashinan kina abinda kika dade bakiyi ba.” "Murmushi tai tace “ka nemomai mata ya aura dan Allah, na tabbatar in akwai mace a kusa" dashi dole ta kama gabanta.” "“Korarta kikesanyi? Kiyi hakurin kwantar da ranki, Junaid naki ne ba wanda zai kwace miki shi.”" Tace “haka da na dauka amma yanzu nasan ba haka bane.” Murmushi yai sannan adan ja kuncinta yace “wannan mamar akwai neman fada.” ************* "Junaid ransa a bace ya shiga bangarensa, Azi ya bishi da sauri, Junaid ya kalleshi yace “wai kaji" abinda ake cewa? Azi yai kasa dakai yace “Tuba nake Yarima amma zancen nan ba inda baije ba.” Junaid yai shiru sannan yace “ina Binta?” "Binta? Nan Azi ya mike dan kiranta, Hari na zaune a waje suna hira Azi ya shigo, Hari ta kalleshi" yace “Binta fa?” Binta? Cikin mamaki tace “tabi yarima tun rana.” “Yarima? Yanzu kuma shiyake nemanta.” "Mikewa tai da sauri suka fito tare, Junaid na zaune suka shigo, kallan Hari yai yace “tana ina?”" Hari tace “ta bika ai.” Junaid yace “ni? Yaushe?” Tun rana. Mikewa yai da sauri tace “bansan waye a gabanta ba amma ba ita kadai ta fita ba.” Hankalinsa ne ya tashi yace “tun rana?” Tace “eh wlh tun rana.” "Da sauri Junaid ya fito Azi da Hari ma suka rufa mai baya, nan suka fito waje, Junaid yce “mu" "nemeta a hankali, kar hankalin wasu ya kawo kanmu.” Sukace to." "Nan suka fara nemanta sai dai duk inda sukabi babu alamunta ga guri kato, Junaid kam" "hankalinsa ya tashi ya nufi gun bishiyarnan sai dai ba ta gun, nan jikinsa ya kara sanyi, badai jin" abinda ke faruwa wani ya mata wani abun ba? "Kalaman Sarki ne ya fado mai, hankalinsa ne ya kara tashi, Hari dake ta nemanta itama itace ta" "zo wucewa ta bangaren Raga, kamar zata nufi gun sai ta juya tana tunanin me zai kawota gun, harta juya taji ana dan buga kofar kadan, kasancewar dare ne sai ta kara waigawa cikin dan" "fargaba, ji tai an kara bugawa kadan, a hankali ta nufi kofar gun, tace “Binta?”" "Daga ciki wacce ta gama galabaita ta kasa komai sai kokarin buga kofa da take da kyar, tace" “naaam.” "Da sauri Hari ta zari ichen da aka sa aka tare kofar, Binta ta gani a bakin kofa, da sauri ta riketa" tace “Binta? Me kike anan?” "Kallanta tai a galabaice tace “bansani ba nima, Hari ruwa ruwa. ”" "Hari ta taimaka ta dagata ta ririke hannunta, suka fara takawa a hankali, Hari tace “wani mara" imanin ne ya kulleki?” Binta cikin dauriya tace “Barira ce.” Da sauri ta kalleta tace “Barira?” "Kai ta daga mata alamar eh, Hari tace “karki fadama Yarima Barira ce.”" Kamar zata tambayeta dalili sai ta kasa saboda karfinta dake tafiya. "Suna shawo kwana Junaid na shawo kwana, da sauri ya karaso inda suke, kallan Binta yai wacce" "ta kalleshi itama tare da kokarin yin murmushi, ya kalli Hari yace “meya faru?”" Hari tace “watace ta kirata akan tazo injika shine ta kulleta.” Kallanta yai cikin tausayawa dan ya san shiya ja mata yace “muje ta kwanta.” "Nan suka karasa, suna tafe yana tunani kala kala a kansa har suka isa. Harira tace “bari na wace da ita can.”" "Kai ya daga alamar to, suka wuce." Shiru Junaid yai harsai da suka rufe kofa sannan ya juya ya shiga ciki. "Zama yai akan kujera tare da hada hannayensa, tabbas Hajjo ko Zeenatu ne suka aikata hakan," sannan dolene ya canza takunsa tunkafin Binta ta rasa ranta a dalilinsa. "Shiru yai yana tunani, ke din? Kalaman Sarki ne suka fadomai, kai ya girgiza da sauri yace “ba ita" "bace, wadancan biyu dai a cikinsu ne.”" Inhar yanaso ya kare Binta to lalai dole ya fahimci masarautar nan ya kuma san abinda ya dace yai. "Azi? Kiransa yai, wanda ke waje." "Shigowa yai ga zube a gabansa, Junaid ya kalleshi yace “Azi fadamin me ka sani a game da" masarautar nan?” Azi yai shiru kafin yace “bansan abubuwa ba saidai nasan kana tsakiyan makiyanka.” Junai ya kalleshi yace “nasan wannan amma me kake tunani a tattare da ita?” Azi yai shiru can yace “karka yadda da kowa.” Junaid yai murmushi yace “tashi kaje na yafe tambayar.” "Azi ya mike yai waje, Junaid ya kalleshi sannan ya mike ya shiga dakinsa........" Binta kam na shiga ta ci abinci ta sha ruwa dakyar tai sallah ta hau bacci. "Harira ta zuba mata ido tana kallanta, tana tausayinta sai dai ta tabbatar Azeema tanada hujjarta" "na kin yadda da ita, sai dai aganinta abin baikai haka ba, gwara tace ta tafi data nemi halaka ta." ****** *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* *Shafi Na Ashirin da Daya.* "Duk yanda Junaid yaso yai bacci ya kasa, wannan lamarin ya tsaya mai a rai, ance ya taho da" "mata, ance tanada ciki, sannan an kulleta." Kenan nan gaba baisan abinda za’a iya yima Binta ba? Kawai a dalilinsa. "Acan bangaren Binta itama sam ta tunda ta farka cikin dare ta kasa bacci, juyi kawai take tana" tunani metama mahaifiyar Junaid da zata sa a kulleta? Anya zamanta anan alkairi ne? Karfa ace ta zama wacce a dalilinta Junaid ya shiga wani hali. "Jitai kamar ana magana a waje mikewa tai a hankali ta leka windown dakin, Harira ce tsaye ga" "Azi a gefe, Azi yace “kiyi hakuri nasa kin taso.”" "Tace “ban mayi bacci ba dama, abinda ke damuna nasan shine ya hanaka bacci.”" Azi ya kalleta yace “waye ya kulleta?” Shiru tai kafin tace “Barira ce.” Sam baiyi mamaki ba sai dai yace “zance har gun Sarki inaga yaje akan Junaid ya taho da mace a cewar wasu ma tanada ciki.” "Jikin Binta ne ya fara rawa, muryar Harira taji tace “yanzu lokaci ne na Junaid ya cire yarinta da rashin damuwar dake ransa, inba haka ba haka zai zama wanda bashida ra’ayin kansa, dan a" hankali sai Gimbiya ta juyamai ra’ayinsa.” "Zubewa tai ta zauna, a hankali wasu zafaffan hawaye suka shiga zubo mata." ****** Me kake tunani? Ke mana Gimbiya ta "A hankali ta juyo da fuskarsa zata sumbaceshi, idanunta ta bude sannan ta kara maidasu ta rufe, hara budesu tai sannan a hankali ta mirgina akan gadan, saura kiris ta afka kasa ta danna kanta da pillow tare da yin ajiyar zuciya, meke damuna?" A hankali ta mike zaune sannan ta kalli kofa cikin gadara tace “Fure.” Jin shiru yasa ta sauko daga kan makeken gadan naga sannan ta bude kofa. "Fure ce keta kokarin nuna musu inda zasu ajiye abinci, jin bude kofa yasa ta juyo, ganin Zeena" yasa ta taho da sauri. Zeena tace “Fure zo.” "Fure ta bita suka shiga ciki, zama tai a kan gadonta mika mata kafarta da sauri ta fara matsa mata" "su, Zeena ta kalleta tace “Fure me kike tunani tsakanina da Yarima?”" Ba tare da wani dogon tunani ba tace “makiya?” "Kafa tasa ta hanbareta, Fure ta fadi, da sauri ta mike ta cigaba da tausar, Zeena ta hade fuska," Fure tace “Gimbiya badai kina tunanin wani abin bane bako?” Kamar me? Fure tace “bakomai dama a shirmenane nake tunani ko kina sanshi.” Kara bigeta tai da kafa tace “ni nake sanshi? Bama shi ba? Tashi ki ban gun banamasan tausar.” Da sauri Fure ta zube a kasa tace “tuba nake Gimbiya sai dai ina ganin in kinassn Junaid ai "komai mai sauki ne indai yana sanki, inkuwa bayayi ki fadawa Takawa.”" A kufule tace “kina tunanin zan auri wanda bai sona? Kuma uban wa yace miki ina sanshi? Tashi ki fita. "Ta zube tana bata hakuri, Zeena a zuciya tasa hannu ta finciketa tai waje da ita ta rufe kofarta," "zama tai dabas akan gado cikin kuluwa ta zauna agaban madubi, kanta ta kalla cikin takaici ta mike tai bandaki." ******** "Kasancewar kasa bacci dayai hakan yasashi yin bacci sosai, dan sai da rana ta fito ma ya farka, a" "zabure ya mike yai sallah sannan ya kara kwanciya, bacci ne ya sake daukarsa sai dai bai dade ba yaji motsin bayi na gyare gyare hakan ya sashi farkawa." "Fitowa yai ya shiga yai wanka sannan ya shirya ya fito, bangarensu Harira ya nufa, Azi na ganin ya" "fito ya ajiye ban ruwan da yakeyi ya nufoshi, duk da bayin dake binsa a baya. Junaid ya kalli Azi yace “zanga jikin Binta ne.”" Yace “ko a kirata?” Bari naje. "“to Yarima, dama dazu aka aiko kaje bangaren Gimbiya kuyi karin kumallo.”" To kawai yace yai ciki. "Harira najin an sanar da isowar Yarima gun yasa ta kalli Binta dake kwance tace “Binta, yarima" yazo.” Kallanta tai tace “Hari kice ina bacci dan Allah.” Cikin mamaki Hari tace “meyasa? Junaid ne fa?” Murmushi tai wanda hawaye suka taru a idanta tace “dan Allah.” "Harira ta kalleta sannan ta mike tai waje, gaida Junaid tai sannan tace mai tana bacci tare da cewa “in ta tashi tazo.”" "Junaid ya kurawa dakin ido sannan ya juya, Binta ce ta share kwallarta Hari ta shigo tace“Binta?”" Binta ta kalleta tace “taya yana Yarima zaizo nan? Ba gwara yace inzo ba? Hari bansan ya zanyi ba. ” "Kuka ne ya kunce mata, tausayinta ne ya kama Harira ta matso ta rungumeta, Binta tana kuka" tace “bankai matsayin da zan wargaza mai rayuwar daya dace da ita ba ” "Harira tai shiru tasan tabbas hakane, amma ya za’ayi? Junaid da Binta sun taso tun basusan kansu ba, taya zasu amshi wannan saban yanayin?????" ********* Junaid kam yasan idan Binta biyu dan tun asali ko rashin lafiya takeyi bata taba kaiwa wannan "lokacin tana bacci? Sai dai baisan dalilin sa shima nakin tilastawa sai ya ganta ba, yana fitowa" waje yai suka nufi nangaren Azeema. Azeema tana zaune akan kujerar ta tasha ado sosai kamar yadda ta saba tana zaune tana dan "kada dan yatsanta, Allah ne kadai yasan me take tunani a wannan lokacin, barira ce ta matso tace" “Gimbiya sun dauketa jiyan.” Ba tare da ta bude ido ba tace “iyanzu nasan ya fahimci nisanci da itane kadai kwanciyar "hankalinta, inba haka ba wayasan mezai sameta gaba.”" Barira tai murmushi tace “banaji tace nice na kulleta.” "Azeema tace “in ta fada kina tunanin shi zai yadda? Bayan yasan kina wajen wanzami lokacin? Kinga in ta fada alamace ta tana neman shiga tsakanina dashi, wanda har gwara tai shiru.”" "Sanarwar isowar Gimbiya Zeena ne yasa Azeema ta bude idanunta a hankali, Zeena kuma?" "Zeena ce ta shigo tasha kwalliya kai kace wani taro zata, alkyabar dake jikinta kalar sararin" "samaniya, Azeema ta zuba mata ido harta zo ta zauna, Fure ce ta ajiye kwanuka guda biyu." Zeena ta gaishe da Azeema sannan tace “Umma karama jiya nazo gaisheki akace bakida lafiya "shiyasa nasa a miki farfesu na kawo miki, nayi sa’a bakiyi karin kumallo ba.”" "Azeema ta kura mata ido, wanda haryasata yin kasa dakai? Murmushi tai sannan tace “nagode" "sosai, Allah ya saka da alkairi.”" "Zeena tace ameen, sannan ta mike tace bari naje." "Azeema bata tanka mata ba sai dai idanunta na kanta, yanda Zeena ke tafiya a hankali ne yasa ta fahimci batasan tafiya, har sai da Zeena taje bakin kofa sannan Azeema tace “ko zakici abinci damu? Duk da nasan ba lalai ”" Kafin ta karasa Zeena ta juyo ta kalleta tace “Ba wani abin?” Azeema tai dariya a kasan ranta tace me kike shirin yi? "Azeema tace “ba wani abin, dama Junaid ne zaizo in ba wani abin ki zauna.”" "Zeena ta zauna suka danyi shiru, sannan ta kalli Azeema tace“Umma karama naji ana zancen Ya" Junaid ko yazo da yarinya ko mata?” Azeema ta kalleta kamar bazata amsa ba sai tai murmushi kuma tace “wace mata ana zaune kalau? Yarinyace da ya taimaka daga can.” "A hankali tai dan ajiyar zuciya sannan ta kalli Azeema tana murmushi, Azeema cikin zargi tace" “Hajjo tasan kina nan?” "Zeena tace “a’a amma in na koma zan fada mata, dama dubaki nazoyi ”" "Sanarwar isowar Junaid akai, wanda yasa gaban Zeena faduwa wanda ita kanta batasan dalili ba." "Junaid ne ya shigo, kallan Zeena yai cikin mamaki, Azeema tai murmushi tace “karaso mana.”" "Junaid ya karasa ya zauna a dayan gefen, gaida Azeema yai sannan Zeena ce gaisheshi." "Kallanta yai sannan ya amsa, Azeema ce tace “ina Binta? Na dauka tare zaku taho?”" Yace “batadan jin dadi ne.” Azeema ta kalli Zeena tace “ashe jiya Zeenatu tazo.” “Eh kina bacci.” Murmushi tai sannan ta mike tace “fara cin abinci bari nazo.” "Ta mike ta shiga dakinta, tayi haka ne dan tanasan fahimtar meke kan Zeenatu." Zeenatu tana fita ta kalli Junaid tace “yaya na zubama?” "Kallanta yai bai tanka mata ba,tai shiru kafin tace “ zamuje yau din?” Ina?" Ta kalleshi . “ka manta? Nace zan kaika gun Hajiya Inna?” Baice komai ba hakan yasa tace “ anjima da yamma sai muje?” Kallanta yai yana tunanin itace? Itace ta kulle Binta? Yanda ya kalleta ne yasa cikin salo tace “ya Junaid.” “Kinsan Binta?” “Binta? Wacece?” Ido ya zuba mata ganin yanda fuskarta karara ta nuna alamar tambaya take yasa yace “shikenan.” "Ta bude baki zatai magana Azeema ta fito, kallansa tai bata ce komai ba." Azeema ce ta kalleta tace “ya naga baku zuba komai ba?” Nan Zeena tadan ja plate ta mikawa Junaid. ************ Mene? Zeena tana ina? Zubair yace “yanzu naganta ta nufi bangaren Azeema. Cikin zafi Hajjo tace “jiya mafa ance taje wai uban me ke kan yarinyar nan?” Zubair cikin hasala shima yace “anya Zeena ba akwai abinda ke ranta ba?” "Hajjo ta tuno kalamanta datai rannan, shiru tai tare da dunkule hannunta.”" Zubair yace “akwai ko?” Hajjo ta kalleshi tace “haukarta ce.” ******* *ZAFIN RANA* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* *NA Ayusher Muhd* *Shafi Na Ashirin da Biyu* "Azeema ta zauna sannan ta kalli Zeena wacce tai shiru ta kasa ko zuba abincin, Binta? Tunowa tai" da yanzu Azeema ta tambayeshi ina Binta? Itace? Itace yarinyar daya taho da ita? "Ganin Azeema na kallanta ne yasa tadan zuba abinci kadan a plate juya cokalin kawai takeyi," Fure ce ta shigo tace “Gimbiya ana nemanki.” "Wa? Ta fada tana kallanta, Azeema tace “kije ki gani.”" "Mikewa tai ta kalli Junaid wanda ko kallanta bai kuma yi ba, maida kallanta tai kan Azeema tace" “Umma karama na wuce.” "Azeema ta daga kai alamar to, Junaid ta kalla tace “Zeena zata wuce “to kawai yace ya cigaba da tunanin da yakeyi, kenan Hajjo ce?" "Haushi ne ya turnuketa ta juya ta fita, tana fita Azeema ta kalleshi tace “Junaid!”" Dagowa yai ya kalleta tace “baka huce da abinda ta maka bane?” Wace? Murmushi tai tace “shikenan.” Yana gama cin abincin ya kalleta yace “zanje bangaren Hajjo.” “Hajjo? Me zakaje yi?” “Gaisheta zan na fahimci tunda nazo banje ba.” "Azeema kamar zata sake magana sai taga harya mike ma, ganin haka yasa tace “sai ka dawo.”" "Juyawa yai ya fita, Azi ya kalla yace muje bangaren Hajjo.”" Zeena tana shiga bangaren Hajjo ta shiga jiki a sanyaye saboda gaba daya jikinta ya gama sanyi. Hajjo ce ta buga mata wata muguwar harara sannan tace“uban me kikaje yi bangaren Azeema?” Zama tai fuskarta duk ba dadi tace “Hajjo dan Allah ki kyale ni yanzu ni nanida karfin magana.” Hajjo ta kalleta a fusace tace “yau zanje na fadawa Mai Martaba ya hadaki aure da Sulaiman ba "tare da wani jiranki ba, tunda naga alama in aka barki Allah ne kadai yasan me zaki aikata.”" "Kallan Hajjo tai tace “Sulaiman? Wallahi indai kuka auramin shi sai dai ku gai gawata gidan, ni" mace ki barni da abinda ke damuna dan Allah. ” "Bata karasa ba ta mike tai cikin daki ranta a bace, Hajjo ta bita da kallo cikin takaici sannan tai kwafa, tace wallahi baki isa ba, ki rasa wanda zakiso sai dan da ya ke neman toshewa yayanki" gaba? "Tana zaune tana tunanin mafita taji ana sanarda isowar Junaid, tsantsar mamaki ne ya kamata" "amma ta daure ta nemi ya shigo, Junaid na shigowa ta saki fuska sosai tace “Junaid? Kaine da kanka?”" Junaid ya gaisheta sannan ya ja ya zauna. Tunani ta shigayi badai shima Zeenatun yake so ba? Junaid ne ya kalleta yace “a gafarceni tunda nazo bansamu nazo gaisheki ba.” Murmushi tai tace “ai bakada lokaci ne ni na sani kana ta fama da kokarin daidaita zamanka da mahaifiyarka.” Kallanta yai sannan yace “Eh da jiya naso zuwa to sai banga Binta ba hakan yasa muka shiga nemanta.” "Yai maganar yana kallan yanayinta, Murmushi tai tace “Binta? Ohhh wace kuka taho tare?” Yace “eh.” Yadan yi dariya kadan yace “wasu harcewa suke wai na taho da mata.”" "Hajjo tai dariya tace “kasan lamarin masarauta akwai gutsiri tsoma, amma ya Gimbiya taji? Suna" neman lalatawa danta suna?” "Junaid ya kalleta sannan yai murmushi, baice komai ba." Tace “irin wannan shi kesa a sa mutum yin abinda bai dace ba in mutum yaga ana neman lalata ma dansa mutuncinsa.” Junaid ya kalleta sannan yace “Yarima Zubair fa?” "Tace “yana bangarensa,dazu ya barnan, Junaid a kokarta a dinga kula da Gimbiya Azeema dan" ta shiga wani hali sanda baka nan.” Junaid ya kalleta sannan yace “Da a koda yaushe ya kamata yasan me zaiyiwa iyayensa.” "Wannan kalmar taba Hajjo haushi sai dai bata nuna ba tace “hakane, kanasan wani abu a" kawoma?” Yace “a’a zan wuce ma.” "Mikewa yai, jiyai an bude kofa, kallan inda yaji motsin yai, Zeena data fito dan ta wuce" "bangarenta ne ta zuba mai ido, jitai batasan dauke idanta daga kanshi." "Junaid na ganin itace ya maida idansa kan Hajjo yace “na wuce, A huta lafiya.”" Tace “to a gaishesu.” "Zeenatu tana kallansa har ya fita ko waigowa baiyi ba, jitai idanunta suna neman cikowa kawai ta" koma dakin ta rufe. "Junaid na tafe yana tunanin kalamanta, sannan ya hada da kalaman Mai martaba, yana tafe" "yana auna kalaman can da komai ya daidaita a kansa, yaja ya tsaya." Azi ya kalleshi yace “Yarima lafiya?” "Junaid ya kalleshi, sannan yace “mu koma bangarena.” “Ba zaka koma gun Gimbiya ba?”" Yace “anjima.” "Juyawa sukai ya wuce bangarensa, bai nemi Binta ba kawai ya shiga bangarensa ya zauna yana tunani, kenan Umma ce ta kulleta dan ta hukuntata akan abinda mutane ke zarginsa dashi? Kenan" batasan Binta kamar yadda take nunawa? Fitowa yai ya kalli wani bawa dake gefe yace “kiramin Binta.” Bawan ya amsa da to sannan ya juya. Tana zaune ta samu tai wanka tana shan kunu da kosai bawan ya sanar da ita Junaid na nemanta. Kallansa tai tace “to.” Yana juyawa ta kalli Hari sannan tace “Hari bari naje.” "Ajiye kofin tai sannan ta mike, Hari tace “sai kin dawo.” Binta tai murmushin yake ta fita." "Junaid na tsaye ya juya bayansa a cikin falan yana kallan window, yana kallanta sanda tazo ta" "wuce, hannunsa daya ba baya, sallama tai, ya amsa ba tare da ya juyo ba. Shigowa tai a hankali ta tsaya daga nesa dashi sosai tace “Yarima!”" Junaid bai juyo ba yace “Barira tazo nan jiya?” Kallansa tai kafin tace “a’a.” “Ya akai ke da bakida saurin yadda da mutane kikabi mutum ba tare da kin sanshi ba?” Shiru tai kafin Tace “cewa akai inje injika.” "Yanzu kam juyowa yai gaba dayanshi ya kalleta, tana tsaye tana kallanshi itama, a hankali ya fara" "takowa zuwa inda take, duk taku daya ji take kamar da bugun zuciyarta yakeyi, yauce rana ta farko a iya tarihinta dashi data taba ganinshi haka ba." "Daf da ita ya matso hartana iya jiyo numfashinsa, gabanta ne ya tsananta faduwa, dagowa tai ta" kalleshi. Yace “waye ya jaki?” "Da kyar ta hadiye yawun bakinta sannan tace “koma wanene ya Junaid baya riga ya wuce ba? Sannan laifi nai shiyasa aka hukuntani, dan Allah kabar maganarnan a inda take.”" "Ta fada tare da danyin taku daya zuwa baya, shima taku daya ya kara, ta kalleshi jikinta har rawa" yadan fara tace “Ya Junaid!” "Yanda tai maganar kamar mai shirin yin kuka, kansa ya juya sannan ya furzar da wata iska ya" "kalleta yanayin idanunsa ya canza sosai, wanda ya kara tsoratata, tace “Ya Junaid!”" "Bai tanka mata ba yanzun ma sai dai ya kara kallanta, bakinta na rawa muryarta na rawa tace" “Ya Junaid dan Allah!” "Taku daya yai baya sannan ya kara wani dayan, kallansa tai tace“idan harba da kwakwaran dalili" "ba dan Allah kar kazo bangaren su Harira domin ni, sannan na koma can da zama, sannan" kuma. ” "Shiru tai tana kallansa, ta daure saboda kukan dake neman kwace mata tace “dan Allah ka rage" "nemana, in kuma duk hakan ya gagara zan bar gidan nan.”" "Tana kaiwa nan ta juya da sauri tai waje, tana fita tai bayan bangarensa da gudu, ta tsuguna ta" "fashe da wani irin kuka mai taba zuciya, wannan shikadai ne abinda zata masa dan ta zauna kusa dashi, dan in har aka cigaba da yanda ake ta tabbatar wata ran ganinsa ma bazata tabayi ba, wanda a rayuwa bata tunanin zata iya kwana ta tashi bata ko sashi a idanta ba." "Kuka take sosai, ta toshe bakinta, gaba daya fuskarta tai jaa, kuka take har iya karfinta wanda duk" wani mai tausayi inyaga halin datake ciki zai tausaya mata. "Junaid kam tana fita ya runtse idanunsa shima bai zataba yaji hawaye sun gangaromai, hannu" "yasa y taba su, sannan ya kalli hannunsa, inhar mahaifiyarsa zata aikata hakan saboda kawai ya damu da Binta to lalai gaba baisan mezata aikata akan hakan ba." "Kansa ne yaji yana sarawa, ya dauka ganinta zaisa hankalinsa dana Binta ya kwanta me ke shirin" faruwa????? Tabbas dolene ya janye Binta daga jikinsa harsai yakai matsayin da zai kwaceta batare da fargaba "ko tunanin za’a mata wani abin ba, yau a wannan lokacin ya dau alkawarin tabbas shi Junaid sai ya ba Binta gatan da babu wace mace data taba samunsa, domin tun yana karami burinsa kenan, akoda yaushe yaganta cikin farinciki, yanzu me zai faru da Basu ganta ba jiya? Haka zatai ta zama" harta mutu kenan??????? ****** Ayusher ***** *ZAFIN RANA* ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ ♀* *23* "Azeema tana zaune tana jiran Junaid sai dai har dare ba alamarsa, Barira ta kalla bayan tayi" sallar isha’i tace “Barira Junaid haryanzu?” Barira ta sunkuyo tace “ko na je na kirashi?” Azeema tai saurin cewa “a’a da alama yana can da yarinyar nan.” Mikewa tai ta wuce dakinta ta kwanta zuciyarta duk ba dadi. Bata dade da kwanciya ba bacci yai gaba da ita. "Yanda yake nufota ne fuskarshi tana gumi, gudu take hana binta, hannunsa ta kalla taga jariri a rike, gudu take tana keta cikin dajin nan har takai karshe." "Juyowa tai cikin tashin hankali tana hakki, hannayenta ta hade tana neman gafara." Zubair ka tsaya kaji! Zubair ka. ” "A firgice ta farka, da sauri ta jawo bargonta ta gangame jikinta wanda yake rawa, kamar a fili tai" "gudu nan dan gaba daya jikinta ya jike da gumi, idanunta sun kada sunyi jaa sosai." "Fitilar kwai dake gefenta ta murda da sauri haske ya dan zagaye dakin, shiru tai hankalinta a tashe ta zauna akan gado ta hade kafafunta, tunanin wannan mafarki, ta tabbatar duk duniya ba wanda yasan wannan sirrin to meke faruwa?" "Shiru tai tana tunanin kalaman da Jakadiya ta fada mata, da sauri ta girgiza kanta alamar a’a." Da kyar ta samu bacci ya dauketa a xaunen. "A hankali ta bude idanunta, ganin gari yayi haske ne yasa ta kashe fitilar sannan ta mike ta shiga" bandaki. ********* "Fitowa tai bayan ta kimtsa, Barira da ragowar kuyangun ta nata faman gyara bangarensu." Azeema ta kalli Barira wacce suka zube suna gaisheta suna ganinta. Azeema tai murmushi tace “Barira kicewa Junaid anjima yazo muje ya gaida Hajiya Inna.” "Cikin mamaki Barira ta kalleta, tace “Gimbiya kinsan matar nan ba sanki take ba karta" wulakantaki a gaban Yarima.” Wani lalausan murmushi ta saka tace “ki sanar dashi.” Ta juya ta shiga ciki. Barira tai shiru kafin ta aika a sanar da Junaid. "Junaid kam wanda yau ma baisamu baccin kirki ba, yana zaune yana kokarin karatan wasu" littafai na tarihi da ya nemi Azi ya amso mai. "Nan Azi ga shigo ya sanar dashi sakon Azeema, yace “to.”" "Sai daya gama karatawa zuwa inda zai tsaya sannan ya mike ya shiga daki yai wanka ya shirya, a" ido inka ganshi bazaka taba kawo akwai abinda ke damunshi ba saboda babu yanayin komai a tattare dashi. "Karin Kumalo yai sannan suka fito shi da Azi, Azi sai binsa yake da kallo, duk da baisan yanda" sukai da Binta ba amma ya hasasu ganin yanda taci koka shima tunda ta tafi bai bar kowa ya shigo bangarensa ba sai shi daya kaima littafai. Junaid ne ya kalleshi yace “Azi sai yaushe za’a daina kallo na haka?” Azi yai kasa dakai yana dariya yace “ wai ka gani?” Junaid yace “ba dole ba? Kana neman sani na fadi kasa.” "A tare suka dan murmusa, can Junaid yace “Waccen gimbiyar tace Hajiya Inna batasan" Umma?” “Gimbiya Zeena?” Eh Azi ya danyi shiru kafin yace “bansani ba wallahi Yarima kaga ba’anan na zauna ba nima.” Junaid ya jinjina kai kawai baice komai ba. "Sun isa bangaren Azeema, ya shiga ciki, zama yai yana jira ta fito." "Barira ce ta fito ta zube tana gaisheshi ido ya zuba mata kamar bazai amsa ba, Barira ta kara" "gaisheshi gabanta na faduwa jitai ya amsa, a hankali ta saki wani ajiyar zuciya." Junaid ya kalleta yace “Ki sanar da Umma nazo.” "Mikewa tai da sauri ta nufi dakin Azeema, da ido Junaid ya bita kafin ya dauke idansa daga kanta." "Azeema wacce ta gama shiryawarta tsaf tasha kwalliya yanda ta saba, dan dama Azeema yar" kwalliyace sam baka ganinta ba kwalliya sai dai in bacci take. "Tana zaune tayi shiru tana tunani, dan yatsanta kawai take dan dagawa take saukewa tayi nisa" "cikin tunaninta har batasan sanda Barira ta shigo ba, sai da Barira ta matso kusa da ita tana cewa" “Gimbiya Yarima yaxo yana kilisarki.” "Kallanta tai sannan tai murmushi, mikewa tai ta kara daidaita zaman alkyabarta sannan tace" “muje.” "Tare suka fito Barira tana binta a baya, gana ganin Junaid ta saki wani lalausan murmushi na" "farinciki, Junaid." "Ta fada tana kallansa, Kallanta yai da fuskarsa wacce ita kanta ta kasa meke tattare da ita. Gaisheta yai, amsawa tai tace “jiya inata jiranka.”" Yace “eh dana dawo ne naji banasan fitowa.” "Murmushi tai tace “ka gaji da zirgazirga ne shiyasa, tunda ka dawo kake ta fama.” Kasa yai da kansa baice komai ba." Tace “muje?” Mikewa yai yace “eh.” "Tare suka fito tana nuna mai hanyoyi tare da dan bashi tarihin guraren sama sama, yana biye da" ita yana kuma jin tarihin harms tambayarta inda bai fahimta ba yakeyi har suka isa. "Bangaren Hajiya Inna shine daga can karshe karshen ginin, an kewaye mata bangarenta sosai," "Azeema suna kokarin shiga ta kalleshi tace “kakatka ce, kayi kokarin sakin jiki da ita.”" "Kai ya daga alamar to, sannan tace “Zubair mahaifinka shi kadaine yao tsawan rai a ‘ya’yanta maza, ta haifi maza guda hudu amma duk sun rasu kafin suyi aure shikadai ne har ya hau mulki sannan ya hayayyafa.”" Junaid cikin mamaki da tausayinta yace “ba ita bace mahaifiyar Sarki?” "Tace “AbdulSalam itace ta rikeshi tun yana karami, sai dai ba ita ta haifeshi ba.”" "Junaid ya jinjina kai, shiga sukai ciki, Jakadiya wacce ta sauka ta koma bangaren Hajiya Inna tana" "zaune a waje suna hira da wasu, tana ganin Azeema ta mike da sauri, dukansu suka hau gaishesu, Jakadiya ta kalli Azeema cikin mamaki, dan rabanta da bangaren nan ita kanta bazata iya tunawa ba." "Azeema tai gaba Junaid yabi bayanta, Hajiya inna na zaune tana bare goro Jakadiya ta shigo tana" sanar da ita zuwan Azeema. "Hajjiya Inna ta dago dayake bata gani sosai, ta kalli Jakadiya cikin muryar tsofafi tace “wace?”" Jakadiya ta kara sunkuyowa tace “Gimbiya Azeema.” "“Uban wayace ina nemanta? Karta kuskura ta shigomin nan dan koda wasa bana nemanta, na" dauka na fada mata ko mutuwa naj kartazo nan?” Jakadiya ta kalleta tace “Hajiya kidan saurara tare take da Junaid kar yaji.” Junaid? "Ta fada muryarta na rawa, Jakadiya tace “eh.”" "Azeema da Junaid da sukai shiru a waje saboda kalaman Hajiya Inna, Junaid ya kalli Azeema" wacce itama ta kalleshi tai murmushi tace “karka damu bakomai.” "Jakadiya ce tace su shigo, Junaid ya kalli Azeema sannan suka shiga ciki." Hajiya Inna ta mika hannunta tana cewa “Junaid!” "Matsawa yai gunta ya rike hannunta, kankame hannun sosai tai muryarta na rawa tace “Junaid! Junaid ashe da gaske sukeyi ka dawo.”" Ido yake kara kuramai? Ta zare hannunta daya tana shafa fuskarsa cikin farin ciki. Gaisheta yai t amsa tana cewa “ina ka shiga? Kakarka nata addu’ar ganinka kafin ta mutu?” "Azeema ce ta gaisheta, bata tanka mata ba ta cigaba da cewa “lale lale Junaid.”" "Azeema cikin sanyin murya takara gaisheta, ran Hajiya Inna a bace tace “tunda na barki kika shigo ai sai kimin shiru ko? Wallahi badan darajar Junaid ba zama a dakin nan bazaki sakeyi ba sai dai bayan raina.”" "Azeema tai kasa da kanta, Junaid wanda kalam Hajiya Inna suka mai zafi, balle daya kalli Azeema" yaga yanda itma kalaman suka tabata da alama. "Hajiya inna ce tace “Junaid barka barkan mu, yau Allah ya amsa addu’a ta.”" "Junaid ya kalleta yai murmushin yake, Azeema ce ta mike tace “kiyi hakuri Hajiya dama Junaid na kawo miki bari na koma.”" “Idan kina magana kamar mutuniyar arziki wannan mata Allah wadan bakin halin ki da "tsinanen san kai da san zuciya, yanzu kila in na tambayeki raban dakiyima Zubair addu’a ma kin manta, ki fita zai taho da kafarsa." "Azeema ta kalli Junaid wanda shima kallanta yakey, Murmushi tai mai ta daga mai kai alamar ba" komai sannan ta fita. Hajiya inna ta kalli Jakadiya tace “zubamin gishiri a kofar data fita.” Wannan kalma ta konama Junaid rai sai dai baice komai ba. Azeema na fitowa ta kalli Barira wacce idanta ya ciciko tace “meye hakan?” "Barira cikin konar rai tace “ji fa abinda ta miki, in da kara ai bai kamata ta miki hakan a gaban" Junaid ba.” Azeema tai murmushi a ranta tace hakan shine ya kamata da batai ba da banji dadi ba Amma a fili murmushi kawai tai ta fara tafiya ********** "Hajjo sam ta kasa kwantar da hankalinta, ganin yanda Zeena yau ko shigowa batai ba, kenan da" gaske san yaran nan take. Yamma nayi ta mike ta nufi bangaren mai martaba dan ta san lokacin dawowarsa daga fada ne.” "Takawa ya cire kaya kenan Zagi ya sanar da isowar Hajjo, jalabiya ya zura ya bada izinin ta shigo." "Hajjo ta shigo ta zauna, gaisheshi tai bai amsa ba yace “Hajjo lafiya? Banyi tunanin ganinki ba.”" Kallansa tai tace “me kake nufi da zaka cikama Junaid alkawari akan duk abinda yakeso?” Kallanta yai yace “akan me zan sanar dake?” Kallansa tai ranta ya fara baci tace “Naji bakada hujjar sanar dani amma meye matsayin Zubair a masarautar nan?” Kallanta yai cikin mamaki yace “Mekikesan ji?” "Tace “Ba abinda nake san ji sai dai nazone na tunama, Junaid ba jininka bane, Zubair ne danka" "wanda ka haifa, duk yanda kake tunanin san mutum baikai san daya kamata kayiwa danka ba.”" Ido ya zuba mata yana kallanta tace “sannan abu na biyu ka aurar da Zeena ga Sulaiman din nan dan hankalina ya kasa kwanciya da yanda ta fara maganar Junaid.” "Duk da yayi mamakin jin kalamanta amma bai tanka ba, tace “kardai ka manta nice matarka" "wacce nasoka tun bamuda matsayi, duk da ba sona kake ba ka auran amma a kalla inada hakki" akanka.” "Tana kaiwa nan ta mike tamai sallama ta fita, shiru yai yana kallanta, harta fita waje yanayin" "fuskarsa ne ya canza wanda yasani shiga tunanin abinda yake tunani, ban samo amsarba naji yace" “waya fada miki?” "Juyawa nai da sauri naga ba kowa agun, da wa yake? Abinda ya fadan kenan, na nuna kaina alamar ni? Lokacin na fahimci wai amsa yaba Hajjo wace ta dade da fita, to me yake nufi da waya" fada mata? Hmmmnmmmm ******** *ZAFIN RANA* ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ ♀* "Shiru mai martaba yai kafin yai gyaran murya alamar yanada magana, da sauri bafaden dake jikin" "kofa ya shigo, kallansa yai yace “A kiran Zeena.”" "Da sauri ya juya ya fita, Zeena dake keance akan gadonta ta rasa ina zata sa kanta, fitowa tai a" "fussce ta zauna, ta kalli Fure dake zaune agun tace“Fure bangaren Yarima nakesan kije ki kiramin Binta.”" Binta? Wacece hakan? "Fure tai tambayar, Zeenatu ta harareta tace“koma wacece meye damuwarki? Kedai ki kiramin ita, sannan ki kirata a boye karki bari Junaid ya ganki.”" Fure tace “Gimbiya taya zani bangarensa na kira wacce bansaniba sannan ba tare da ya ganni ba?” Ni Fure dan Allah kwakwalwarki tana aiki kuwa? Ke ni meyasa gaba daya bakida irin dabaru da fasaha ne? Wlh na kusa canzaki ki cigaba damin halin kifi.” "Fure ta juya da sauri tai waje, tsaki Azeema tai tace “bari inga yarinyar da har saboda ita yaje" gun Hajjo.” Fure na fita aka shigo neman Zeenatu inji mai martaba. "Mikewa tai jiki a sanyaye dan tasan maganar dai guda daya ce akan aure, shiryawa tai sannan ta" fito. Kallan kuyangarta tai tace “in Fure ta dawo kice su jirani.” Tace to sannan ta wuce. "Mai Martaba na zaune gabansa katan Littafi na fiqihu ne yana dubawa, Zeenatu tana zuwa bakin" kofar ta canza yanayin fuskarta a nutse ta shiga bayan ya bata izinin shiga. Zama tai daga gefe zama irin na ladabi. Abdulsalam ne ya kalleta yace “Mahaifiyarki tazo akan na aura miki Sulaiman.” Da sauri ta kalli Sarki tace “Ranka ya dade tuba nake amma Allah bana san shi.” Wani murmushi yai yace “ni kike kalla kice bakyasan zabina?” "Kallansa tai ta maida kanta kasa tace “Allah da kaima kanaso bazaka tambayi ra’ayi na ba," "zartar da auren kawai zakayi tunda Hajjo tama magana, amma kiran dakamin da tambayar daka" min ya nunamin bakaso.” Shiru yai yana kallanta kafin yai wani kalausan murmushi yace “to naji tunda bakyaso sannan banaso fadamin wa kikeso? Inbaki dashi kuwa na aura miki wanda yamin.” "Kallansa tai da sauri sannan ta maida kanta kasa, yace “baki dashi.”" Tace “akwai amma matsalar ba wanda zai yadda dani.” Wanene? "Shiru tai gabanta na wani irin faduwa, a hankali tace “Yarima.”" Me kikace?” A hankali tace “Yarima!” Ido ya kura mata sannan yace “Kina tunanin Azima da Hajjo zasu yadda?” "Ta kalleshi idanta ya ciciko tace “na sani, shiyasa nake tsoro.”" “Tashi kije.” "Da sauri ta kara kallansa, yace “kin fadi ra’ayinki sannan kinsan bazai yiwu ba, ko kina da wani abin cewa?”" Cikin sanyin jiki ta girgiza kai alamar a’a. Mikewa tai ta fito daga fadar. "Tana fita Abdulsalam ya mike ya shiga ciki, shiru yai yana tunani, abubuwa guda biyu suna mai" "yawo akai, me zai faru idan daga baya asiri ya bayyana?" Sai dai me? Yna tunanin ba abinda Zai faru tunda a lokacin Junaid yana auren Zeenatu in yai sa’a ma harda d’a. To amma in kuma asiri ya tuno kafin faruwar hakan fa? Ko kuma Junaid ya rufe idansa akan komai fa? In kuma abin ya shafi har Zeenatun fa? Wadannan dalilai sun sa gaba daya kansa kullewa. ******* "Zeenatu na fitowa ta nufi bangaren Junaid, wanda ita kanta batasan nan ta nufa ba sai data ganta" a kofar shiga. Da sauri tace “Fure me muke anan?” Da sauri wata kuyanga tace “Fure bata nan ai.” "Zeenatu ta kalli bangaren sannan tai ajiyar zuciya, samun kanta tai da juyawa." Gimbiya? "Abinda taji an fada kenan, juyawa tai cikin jin kunya, Azi ne Junaid na gefensa." Kallan Junaid tai a hankali tai dan yake tace “wucewa nazo yi nai.” "Junaid ya kalleta sannan yace “tanan?” Eh, naje bangaren Mai Martaba ne.” Oh!" Yace sannan ya nufi hanyar shiga. Ya Junaid? "Juyowa yai ya kalleta, tai murmushi tace “bamuje gun Hajiya Innan ba.”" Kallanta yai yadanyi wani tunani akasan ransa kadan kafin yace “zaki shigo?” "Shiru tai tana kallansa, yace “inbakyaso ki barshi.” Tace “tunda kai ka gayyacen ina zan ki zuwa.”" "Shiga yai tabi bayansa, zama tai tana kallan bangaren yanda aka gyara shi, murmushi tai tana" cewa “dole Hajjo taso aba Ya Zubair nan.” "A hankali tai maganar sai dai Junaid ya jita, kallanta yai bayan ya zauna yace “daga bangaren Hajiya Inna nake.”" Cikin mamaki tace “haba? Kai dawa?” Yace “Umma ce takaini.” Ido ta zaro tace “Umma karama? Garin ya?” Garin ya kuwa? Yai tambayar cikin bugar ciki. Zeena tai shiru kafin ta kalleshi tace “ Hajiya Inna ta haramtawa Umma karama zuwa bangarenta.” Junaid yace “meyasa? Bayan sirikarta ce?” Kallansa tai kamar zatai magana sai ta fasa. Can tace “Ya Junaid saboda haka kace nazo?” Yace “me? In saboda haka ne bazaki shigo ba?” Tace “bance ba amma a kalla nadanji haushi.” “Meya hadasu?” Kai ta girgza alamar rashin sani tace “kawai dai nasan batasanta sannan ta hanata shiga "bangarenta, ita da Mai martaba.”" Junaid ya kalleta yace “hardashi?” Eh shima baya zuwa. "Murmushi Junaid yadanyi kadan fuskarsa kunshe da tunani yace “shikenan, in kin gama gani" "bangaren sai ki wuce, zan shiga nai magrib.”" Mamaki ne ya kamata kafin ta tattaro abinda zata fada harya rufe kofa. Labanta ta cizs saboda takaici sannan ta mike ta bar bangaren nasa cikin takaici. "Idanunta ne taji suna kara cicikowa, kenan ita duk inda tai ba dadi, cikin jin haushi ta shiga" bangarenta. Wata yarinya ta gani a tsaye daga gefe kadan inka shiga. Kallanta tai a wulakance tace “uban me kike anan?” Binta ta kalleta tace “ance kina nemana ne.” Ni? Tai tambayar tana kallanta daga sama har kasa. Binta tace “haka waccen tace.” Ta nuna fure wacce ta taho da sauri. Binta wacce kafafunta harsun gaji da tsayuwa ta dan jingina. Fure ta karaso tace “Gimbiya itace .” "Da saure Zeenatu ta kara kallan Binta cikin mamaki, kece Binta?”" Eh nice. Batasan sanda tasa wata dariya ba wacce ni kaina na saki baki ina kallanta. A hankali ta fara zage Binta wacce ta nemi ta daidaita tsayuwarta. "Binta mamaki ya kamata, Zeenatu sai da tagama kallanta tsaf sannan tace “daga bangaren Ya" Junaid nake.” "Binta ta kalleta da sauri, Zeenatu tai murmushi tace “Ashe abinda ya faru dake kenan? Ayya kiyi" hakuri kinsan hausawa sunce babban goro sai magogin karfe.” Binta ta daure ta kalleta tace “me ya sameni?” "Zeenatu ta matso saitin kunnent tace “Ya Junaid ya fadamin komai, tundaga sands ya taimakeki har abinda ya faru kwanan nan.”" "Idanun Binta ne suka fara sauyawa, tace “mene?”" "Zeenatu ta shagwabe fuska tace “na tausaya miki, shima Ya Junaid yana tausayinki sosai.”" "Bakin Binta ne ya fara rawa, kuka na neman kwace mata, daurewa tai ta kalleta sannan ta" "sunkunya tace “tuba nake Gimbiya amma nasan ba abinda kikaji daga bakin Ya Junaid, sannan ko kinji ma nasan yayi maganar ne bada wani abin ba.”" "Zeenatu a zuciya ta kifa mata mari, Binta ta rike gun ta dago tace “menayi kuma?”" Zeenatu tace “tambaya kike? Sai yanzu ma na tuna ashe kece wannan ta rannan. Sannan yau ya zama rana ta karshe da zaki dinga maida min martani.” Tana kaiwa nan tai ciki. "Binta ta juya ta fita, tana fita tasa kuka, da gaske Ya Junaid ya fada mata komai? Kuka kawai" takeyi ta rasa ma me take tunani. ********** "Junaid bayan yayi sallah ne ya zauna akan sallaya yana tunani, ita da Mai martaba? Meyasa? Shiru yai yana tunani, kafin ya mike." "Waje ya fito yadan tsaya a baranda yana dan kallan kofar da zata sada ka da bangaren bayi, Binta" ko tana me? "Shiru yai tare da sakin ajiyar zuciya, ganin ba alamarta ne yasa ya juya kamar zai koma. Jin an bude kofa ne yasa ya juyo da sauri." "Binta ya gani tana tafe tana share hawaye, tsayawa tai daga bakin kofar itama ta zubamai ido," sun fi minti uku suna kallan juna kowa da abinda ke yawo a ransa kafin Junaid yace “Binta!” "Kallansa tai a hankali ta tako, sai dai bata isa inda yake ba tace “Yarima Barka da dare.” Ta juya zata wuce." "Shiru yai ya bita da kallo har ta shiga, meya sameta?" Umma ce? Abinda ya fado mai kenan. ****** Ayusher 24 *ZAFIN RANA* ...................... *H̝a̝ s̝ k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝ s̝ o̝ c̝ i̝a̝ t̝i̝o̝ n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ* *Wannan Littafin Na Saidawa ne ga Duk mai Bukatar siya ya tuntubi 07084161619 mungode* *25* Binta! "Tana kokarin rufe kofa taji ya kira sunanta, tsayawa tai cak" "zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, A hankali ta juyo ta kalleshi." "Murmushi ya sakar mata sannan yace "" magana nakeso muyi.""" "A hankali ta fara taka kafafunta zuwa inda yake, idanunta na kansa, tuntube tai saura kiris ta fadi, da sauri ya zabura yace Binta." Daidaita tsayuwarta tai ta kalleshi har ya sauko daga baranda din da yake. "Kallan juna sukai kawai suka sa dariya, yace ""har yanzu dai sai a dinga tafiya ana neman faduwa." "Ta karaso tace ""haryanzu dai kafin na fadi an gama" "razana.""" Murmushi suka sakeyi da tuno da yanda sukeyi acan. "Karasowa tai ya zauna a kasa ya zura kafafunsa kasan baranda din, kallansa tai sannan ta zauna daga gefe." "Ya kalleta cikin hasken farin wata yace ""daga ina?""" "Nadan fitane zagaye.""" Zagaye? Ya maimaita tare da yin sansanyan murmushi ganin indai zata fita dashi suke fita. "Kallanshi tai tace ""wacce magana?""" """Me kike tunani akan komawa bangaren Umma?"" Kallansa tai da sauri tace ""Naam?""" "Yace ""eh, ko bakyaso?""" "Shiru tai tana kallansa, kawar da kansa gefe yai, ganin haka yasa tace ""zan koma.""" "Shiru yai kafin yace ""Nagode.""" "Mikewa tai tace ""zan koma gobe in Allah ya kaimu."" Tafiya?" "Ya fada ganin ta mike tsaye, juyowa tai ta kalleshi a ranta tace kafi kowa sanin zamana a nan kusa dakai abinda zai haifar." A fili kam cewa tai na gaji ne. Ya fahimceta hakan yasa baice komai ba. Yana nan zaune har ta shiga ciki. "Mikewa yai ya shiga dakinsac zamanta acan shine kwanciyar hankalinsa ya tabbatar intana gunta ba'abinda ta isa ta mata, sannan hakan ne zai bashi damar kwatar" mata 'yancinta. ********** Binta na shiga ta sanar da Harira zata koma gobe "bangaren Azeeema, cikin tsananin mamaki Hari tace ""Binta hauka kike? Matar da tafi tsanarki kije ki gunta?" "Kallan Hari tai ta tuno da kawar da kansa dayai, tace" """akwai dalilinsa na yin hakan.""" Dalili? "Harira ta tambayeta, Binta ta kwanta tace ""eh.""" Shiru tai tana tunanin abinda ya faru tsakaninta da Zeena "yanzu, me Zeena take nufi? San Junaid take kenan ko me?" "Mikewa zaune tai da sauri ta kalli Harira tace ""Harira ya ake gane mutum na san wani?""" "Harira tace ""yanda kike san Junaid.""" "Ido ta zaro da sauri tace ""ni Ya Junaid ai. """ "Sai kuma tai shiru, Hari tace ""me?""" "Kwanciya ta kuma yi da sauri tace ""bacci nakeji.""" "Idanunta ta rufe tana tuno yanda Zeena ke magana, lalai" itakam tata ta kare dan ta tabbatar ba abinda Junaid zaiyi da ita yana ganin Zeenah. A haka har bacci ya dauketa. "Da safe Junaid ya nufi bangaren Azeema, tana zaune a" "falanta ta lumshe ido tana tunani, ga busar barewa datasa ake mata." Hannunta daya take dan kadawa wanda duk sands take tunani haka takeyi. "A hankali tace ""Barira an kawo rahoton danace?""" "Tace ""a'a Gimbiya amma nasan Waziri yana hanya.""" Sallamar Junaid ne yasa ta bude idanunta dan batai "tunanin jinsa ba.""" "Shigowa yai, tai saurin sallamar kuyangar dakeyin busar, tace ""Junaid!""" "Gaisheta yai sannan yace ""Tuba nake Umma jiya dana" "dawo bansamu shigowa ba.""" "Tace ""bakomai Junaid nasan kanada dalilinka.""" "Murmushi yai sannan ya kalleta cikin kulawa yace ""Umma" "wani abu ya hadaku da ita ne? hajiya Inna nake nufi.""" Kallansa tai itama sannan ta sallami kowa dake falan ta "kalleshi, tace ""Karkasa wannan abin a ranka dan nima ban bari ya dameni ba.""" "Tausayinta ne ya kamashi yace ""amma kin mata laifi ne?"" ""A'a batasona ne saboda tana jin haushi na auri" "Abdulsalam wanda ta rika bayan rasuwar Mahaifinka.""" Duk da bai gamsu na amma baice komai ba. "Shiru yai kafin ya daidaita zamansa yace ""Na umarci Binta" "ta dawo nan.""" "Kallansa tai da sauri tace ""nan?""" "Ta kalleshi cikin tsananin mamaki, dan bata taba tunanin" ko ita tace ba zai yadda da hakan. """Eh, sannan inasan sanin yanda yanayin masarautar take" "tun lokacin da suka gabata.""" "Azeema ta kalleshi cikin jin dadi tace ""ba matsala, zan sa Mahmud mijin Safiya wanda yake Hakimi ne shi ya sanar" "dakai komai.""" Muje? Ta tambayeshi. "Yace ""Eh amma akwai dalilin kiran ne?""" "Tace ""lokaci lokaci yakan kira mata da yaransa a tattauna.""" Junaid ya jinjina kai kawai. "Mikewa tai suka fito, a bakin kofar fita suka ga Binta wacce ke kokarin shigowa rike da ledar kayanta." "Da sauri ta rusuna ta gaisheta, Azeema ta kalleta tace ""Binta kin taho?""" Eh. "Shiru tai tana wani tunanin, kafin ta kalli Junaid tace ""Junaid me kake tunani in ta bimu?""" Ina? "Murmushi tai tace ""Su Barira ma suna zuwa dan taje itama bana ganin akwai matsala.""" "Junaid yai shiru duk da ya tabbatar akwai wani abin a ranta sai dai rashin sanin menene ya hanashi musawa. Barira ta kalla sannan tace ""Bari a ajiye kayan ku biyomu."" Nan suka shiga ciki." "Kayan kawai suka ajiye suka fito, Binta na tambayar Barira akan ina zasuje." "Barira ga shareta kamar ba da mutum take magana ba," hakan yasata yin shiru. Bangaren Mai Martaba Sarki Abdulsalam suka nufa. "Fadar sa aka bude musu kofa, Zagi ya sanar da isowarsu." Jakadiya na tsaye a bakin kofar tana musu barka da zuwa. "Hajjo, Zeena, Zubair da su Ramlatu da ragowar matan" sarki da yaransu sun hallara da alama sune sukazo karshe. "Hajjo ta hade fuska, Azeema ta zauna a inda aka ware" "dominta sannan Jakadiya ta nunawa Junaid inda zai zauna," zama yai su kuma su Binta da ragowa bayi suka koma gefe "suka tsafsaya, Binta tana tunanin me take anan?" Azeema kam kallanta tai kadan tace gwara ki fahimci Junaid ya miki nisa hakan ne yasa na kawoki. Zeena ce ta zubawa Junaid ido cikin jin dadi da mamaki halim da take neman tsintar kanta a ciki. "Gani tai ya dago ya kalli wani gun, idanuntanr suka kai kan" "Binta, wani irin kululun bakin ciki ne ya kamata." Sanar wa isowar Mai Martaba da Zagi yai ne yasa kowa ya daidaita. Abdulsalam ya shigo ya zauna tare da kallan su. Kowa an ajiye kayan marmari da abinsha a gabanshi. "Bayan an gaida Mai Martaba ne ya kalli Junaid yace ""Dafatan Junaid ka fara warewa da zaman nan?""" "Junaid yace ""Alhamdulila.""" "Andansyi shiru kafin Sarki yace sannan yace ""Bari mu fara gwada tambaya kamar yanda aka saba, dan a tattauna a" "kara rike sanin juna.""" """Idan akace za'a sai Sarki nawa kuke tunanin ya kamata a" "siye shi?""" "Hajjo ce ta kalleshi tace ""Rankanya dade wannan tambaya" "ta ina za'a nemo amsarta?""" "Sarki bai kalleta ba yace ""wannan tambaya inaso Zubair ya" "bani amsarta""" "Zubair ya kalleshi yaga yanda Sarki ya hada rai yace ""ta ina za'a sai sarki? Ai wannan sai dai bayi, idan kuma har akaje ga siyan sarki to lalai sai dai a kwashe duk tattalin arzikin" "garin a sai shi.""" "Wani kallo Sarki yamai yace ""idan aka kwashe arzikin kasar sai kuma ai rayuwa dame?""" "Zubair yai shiru, Ran AbdulSalam ya baci saboda haushin" "amsar daya bashi, kallan Zeena yai wacce itama taji haushin ansar.""" Zeena me kike tunani? "Kallansa tai tace ""indai za'a sai sarki to kenan ya zama ba" "sarki ba""" Yace haka ne indai har aka siye shi ai ya tashi daga "matsayinsa, Junaid kai fa me kake tunani?" A siyeshi a silai Silai? "Azeema ta kalleshi da sauri tace ""Junaid!""" "Nan kowa ya fara yan kananan maganganu, Zeena ce ta" kalleshi itama hankalinta a tashe. "Binta kam idanunta kawai ta runtse dan tasai halin Junaid duk abinda ke ransa fada zai, yanzu me ya kawo zancen" "silai? Karamin kudi?""" "Sarki wanda shi kansa ransa ya baci matuka ya dunkule hannunsa sannan ya dan murmusa yace ""me yasa kace" "haka?""" "Junaid yace ""A tunanin mutane dayawa Sukai ba wani kudi bane mai daraja sai dai a gun talaka wanda yake neman ci dasha dakyar silay tafi komai daraja a gunsa, kafin a samu wanda baisan darajar sulai daya ba za'a samu" "talakawan da suka san darajarta ashirin, hakan yasa Silai" "ta zama kudi mafi daraja a ciki kudi, sannan sai ka hada silai dayawa ne zaka samu kudi mai daraja da kake nema. Idan har za'a sai sarki to sai a siyeshi a abu mafi daraja" "wanda talaka da mai kudi sukafi sanin darajarsa.""" Yana kaiwa nan yai shiru bai kara tanka komai bs. "Ido Abdulsalam ya zubamai, tabbas koshi bai taba kawo hakan a ransa ba, wannan shi ake kira magana da hikima wanda ake neman Sarki da ita, tabbas dawowar Junaid nan" ba karamin matsala zai jawo masa ba nan gaba. "Azeema wacce dadi ya kamata ta kalli Abdulsalam," hannunsa ta kalla dan ta gama saninsa duk wani abu dayake tunani rabi tana ganewa daga kallansa. "Ganin hannunsa a dunkule yasa ta kalli fuskarsa, da sauri ya sake hannunsa sannan ya kalleta cikin nuna tsantssn jin dadinsa yace ""Masha Allah! Tabbas wannan shi ake kira" "magana cikin hikima.""" "Zeena ce ta kalleshi tace ""Mai Martaba ni kaina na tsorata" "jin Ya Junaid yace silai, sai dai jin bayaninsa yasa na" fahimci me yake nufi sannan na fahimci Silai yafi komai "daraja kamar yanda Sarki yafi mutanen gari.""" "Hajjo ce ta sa hannu ta bige Zeena dake gefenta, sannan tace ""amsoshi duka sunyi ma'ana kowane da nashi" "fahimtar.""" Azeema ta dau kofin dake gabanta ta kurbi ruwa. "Binta wacce tai shiru tana kallan Junaid wanda ya daure fuska sam ba alamar fara'a a tattare dashi, tabbas Junaid dinta jinin sarauta ne, wanda ita kuma take wacce" mahaifinta ma bayaso........ Zeenatu ce ta kalleta ganin yanda take kallan Junsid cikin "rauni yasa tace ""Binta!""" Kafin ma Binta ta amsa Junaid ya kalli Zeena. "A ranta tace au ashe zaka kalleni, Binta ce ta matso da" "sauri, Sunkuyowa tai Zeena ta mika mata kofinta tace ""dan daurayomin naga kamar kura.""" Binta ta kalli Junaid wanda ya dauke kai kamar baisan tana gun ba. "Sai dai gaba daya hankalinsa na kansu, Binta ga amsa tai" "waje, Azeema ta bita da kallo." "Zubair ne ya kalli Hajjo cikin kunar rai, alams tamai da" karya nuna jin haushinsa. "Sarki yai murmushi yace "" Junaid kayi tunanin abinda" "nace ka zaba?""" "Junaid yai kasa dakai yace ""zan sanar dakai Ranka ya" "dade.""" """Sirri ne kenan?""" "Zeena ta tambaya, bai ko kalleta ba sai dai Azeema datace" da alama..... ********** * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * "Nanma shiru yay yak'i tankawa, yakumak'i kallon kowa." "Binta ta dawo da kofin da zeena tabata ta d'aurayo, rissinawa tayi ta mik'a mata, d'agowar da" "zatayi suka had'a ido da Junaid, saurin janyewa tayi, shima ya basar." "Azeema da Idonta ke kallon duk motsinsu taji zuciyarta ta k'untata, amma saita had'iye fushinta" tamkar babu komai. "Sarki yacigaba da jeho tambayoyinsa ana bashi amsa, Junaid kam tundaga ta farko bai kuma" "tankawa ba, sai dai tsaf yake nazari akan amsar kowa da motsin kowa." "Bayan taron ya tashi kowa ya nufi sashensa, Azeema taso Junaid yakoma sashenta dan tanason jin" miya tanadi zaba bisa ga k'yautar sarki na abinda yakeso. ***************** "Tunda Junaid yadawo daga sashen mai martaba saiya kasa zama, sai safa da marwa yake a" "falonsa yana cud'anya wasu abubuwa daya danganci masarautar tasu, a yanzu mafita d'ayace dashi, nutsuwa wajen jin sirri da tushen masarautar tasu, haka kawai jikinshi na bashi ba dalilin dazaisa mahaifinsa ya kaishi can gefen gari ba tare da sanin mahaifiyarsa ba." Ta wannan hanyarne kawai zai samu amsar tambayarsa akan wanene yasa a fiddashi a masarautar zuwa ke6antaccen waje?. Ajiyar zuciya ya sauke da addu'ar samun kwarin gwiwa akan samun warwarar cud'ad'd'en al'amari da zuciyarsa ke hangowa gameda abubuwa masu yawan gaske. ***************** Suna isowa sashenta ta kalli zeena rai 6ace..... "“Hajjo nikam wannan kallon naki tsoro yake ban, nidai nasan banyi wata kato6ara a" "wannan taronba, banda abin arziki danai.”" "Hararta Hajjo tayi tana hura hanci, murya a cinkushe tace, “wani lokacin saina ringaji inama bani" "Na haifi Zubair ba, kwata-kwata k'wak'walwarsa bata ja yanda ya kamata, dolene na nemo" malami ya koyar dashi hikimar zance”. Dariya Zeena tayi sosai dukda kallon da hajjo ta watsa Mata bai hanata fad'in “To Hajjo ke da "kanki kin kirashi mai kwakwalwar kifi tayaya ko kin d'akko malami masanin hikima kan Yaya zai iya bud'ewa? Da dai kunyarda da shawarata kawai dayafi muku, danni inaji a jikina Yaya bazai mulki" masarautar nanb. ” "Hannu Hajjo ta kai mata, Zeena tai azamar matsawa da baya. “Nifa umma gaskiya nafad'a, idan" "baki haifi sairkiba ai kin haifi wadda zata haifa miki sarki, ki zauna kiyi tunani akan hakan?”." "“Lallai ashe ba Zubair kawai ne mai kwakwalwar kifiba? Kekam ai saita jakuna, shashasha kawai," "idanma barci kike ki farka, babu yanda za'ai jinina ya dunk'ulu dana Azeema”." "Baki Zeena ta ta6e ta mike tai hanyar d'akinta da k'unk'uni tana fad'in ”Ashe zaki mutu kuwa ayi," "Danni koza'a maida masarautarnan birnin sin saboda rikici saina mallaki ya Junaid matsayin mijina uban y'ay'ana, yau na tabbatar shikadai ne ya dace dani dan haka ba wanda ya isa ya hanani" mallakarsa.” "Hajjo najin k'unk'unin Zeena, amma batajin mitake fad'a, dan haka ta zuba tagumi tana binta" "da kallo. Takula inhar tayi wasa za'ayi sukuwar irganmun dokuna a masarautar nan batareda ta d'aurama nata sirdi ba. Kai ina ALLAH ya kikaye, koma mizai faru kam sai dai ya faru, sai Zubair yazama *SARKI!*." hummm to maji magani an binne tsohuwa da ranta *********************** "Gaba d'aya zama sashen Azeema bayama Binta dad'i, amma tayi alk'awarin jurewa" "kodan farin cikin Junaid. Yanzu haka buk'atar ganinsa takeyi, koda bazasuyi maganaba ta gansa tasami nutsuwa, dan talura lallai yamata nisa, ta k'ara fahimtar hakane bisa mizanin fahimtar gayyatar da azeema tamata zuwa taron jiya." "Da farko bata fahimtaba, saida suka dawo ta zauna tayi dogon nazari, ta umarci tabisune saboda a" "nuna mata iyakarta, murmushin takaici ta saki tana had'iye kukan daya fara taho Mata. Lallai dolene ta sake takunta, dan ta lura mahaifiyar Junaid kishi take da ita. Babbar magana, ina ita ina kishi da matar sarki, mahaifiyar Wanda tafiso aduk fad'in duniyarnan, insha ALLAH cikin ruwan sanyi zatabi matakan da mahaifiyar Junaid zata fahimci ba burinta rabata da d'antaba." "Sam bata iya ko fitowa, daga daki sai takar gida na baya, haka zata zauna tai shiru tana mamakin" "wannan rayuwa data tsinci kanta a ciki wanda bata taba kawowa ba, ada ta dauka samun inda iyayen Junaid suke shi yafi komai mahimmanci a gareta sai dai yanzu batasan me ke ma ranta ba. Dan wani sa’in takanji dama bai gansu ba......." In hakan yazo ranta sai tai saurin yin istigfari tare da fatan Allah ya kauda mata wannan mumunan abin da zuciyarta ke raya mata. ************** "Sai dayai kwana uku bai fita ko ina ba, ya zauna sosai yayi karatu akan abinda yake san fahimta." "Yau da wuri ya shirya, dan yanason zuwa sashen Umma akan maganarsu ta jiya Na" "sanin tarihin masarautar, dakuma yagama ji yana buk'atar ganawa da mai martaba akan za6in damar daya bashi." "Shiga yai ta alfarma, daka gansa kaga jinin sarauta na asali, dan akwanakin da yayi a masarautar" "komai nashi ya canja, ya canja d'abi'unsa sosai tamkar yanda ya lura mahaifiyarsa Na buk'ata. Shi kansa kuma ya gamsu da tsarin nata d'ari bisa d'ari." "Da mamaki yake bin kayan karin kumallo da aka shirya masa a falonsa, yay tsaye ya zuba musu" ido kamar yay gamo da abin kallo. Ganin yarasa amsa saiya kwala kiran Azi. Da hanzari Azi ya k'araso yana risinawa “Barka da safiya yarima”. "Kai Junaid ya jinjina masa, sannan yay masa nuni da shiryayyun kwanikan abincin batare da yayi" magana ba. Azi yad'an kuma risinawa yana murmushi “Ranka ya dad'e ai gimbiya ce takawo tare da kuyanginta”. “Gimbiya?” Junaid yafad'a cikin sigar rashin fahimta’. "Fahimtar hakan da Azi yayi saiya fad'ad'a murmushinsa“Ranka ya dade Gimbiya Zeena nake nufi," dazu aka aka kawo.” "Bak'aramin ware fararen idanunsa yayi akan Azi ba, yabud'e baki zaiyi magana saikuma yay shiru," ya kauda idonsa ga kwanikan yana fad'in “Muje sashen Ummana”. Da sauri Azi yace “Yarima Abincin fa?” Kallansa Junaid yai wanda yasa shi yin shiru. Kai Azi ya jinjina. ********* "Tunda suka fito bayi keta zubewa suna gaisheshi, iyakarsa d'aga musu hannu. Sun kusa shiga" "sashen Umma yace, “Har gulman ya ishesu?”." "Azi dabai fahimtaba yace, “Yarima gulma kuma?”." “Uhm” Yafad'a a tak'aice. "Murmushi Azi yayi, dan yanzu ya gane miyake nufi, kafin yabashi Amsa sun iso sashen Umma." Babu dad'ewa da sanar da isowarsa barira ta sanarmasa da izinin shiga inji Azeema. Yayi taku biyu zai shiga rumfarta idonsa ya sauka ga Binta dake hidimar gyaran falon. "Wani Abu yaji ya gangaro tun daga mak'oshinsa zuwa yatsun kafarsa, yaushe raban da ya" "ganga?amma saiya danne, yakuma basar tamkar bai gantaba." "Hakan yabama binta mamaki, sannan yayima barira dad'i. Kamar yanda sauran bayin suka zube" "suna gaisheshi haka itama binta tayi, hannu ya d'aga musu kawai yay gaba, hankalinsa duk yanakan binta daya lura yanayinsa ya tsoratar da ita." "Har cikin d'akin Azeema yashiga bisa jagorancin Barirah, Azeema na kishingid'e bisa dardumar" "tsakar d'akin, littafine da abin rubutu a hannunta." Zama yay d'an nesa da ita kad'an yana fad'in “Barka da safiya ummana” "Tai k'asaitaccen Murmushinta danjin yanda ya kira sunanta, hakan namata dad'i ainun, cikin" "lumshe idanu ta amsa da “barkan ka dai Junaid, ina fata katashi lafiya?”." “Alhmdllh”. "Zamanta ta gyara sosai tana kallonsa, saikuma ta d'auke kanta tana kiran barira." "Da sauri Barira ta shigo, batare da Azeema ta kalleta ba tace, “Yauma ahad'amin karin kumallo" tare da Junaid”. "“Angama ranki ya dad'e, amma a ina za'a shirya?”." Kallon Junaid Azeema tayi alamar jin ta bakinsa. Ya d'an murmusa sanann yamata alama da nan cikin d'aki. "Itama murmushin tayi, sannan ta kalli barira, nuni taimata da nan ta d'auke kanta." "Bayan fitar Barira Junaid ya gyara zamansa, kansa a k'asa yace, “Ummana idan abu nada daraja" bai kamata a daraja duk abinda ya dangancesa ba?”. "Shiru Azeema tayi tana kallonsa da juya maganarsa, saikuma tai murmushi cikeda k'asaita, tad'an" "sauke numfashi tana kuma kishingid'a “Gaskiyane Junaid, lallai za'a gyara”." "Baice komaiba sai d'an d'ago ido dayay ya kalleta, tai masa murmushi." Tsaf barira da kuyangi biyu suka kammala shirya abinci a gabansu. Bayan fitarsu Azeema ta kalli Junaid taimasa nuni da Bismillah. "Murmushi yayi yafara k'ok'arin zubawa, itadai tana kallonsa. A mamakinta koda yagama saiya" "matso gareta, fuskarsa d'auke da murmushi yace, ”A tsarin masarautar nan Ko inada hurumin cin abinci da matar sarki umman yarima Junaid?”." "Wani k'asaitaccen murmushi ta saki, wanda akan dad'e ba'a gansa a fuskarta ba, ta d'ora" "hannunta dayasha zobunan azurfa da lu'u-lu'u akan nasa, “Wannan shine yanayi da girmamawa mafi soyuwa ga matar sarki kuma Umman sarki insha ALLAH”." "Junaid yay murmushi mai sauti, Wanda ya bayyana fararen hak'oransa sosai." "Ahankali suka fara cin abincin cikin nutsuwa da tsintar kai a yanayin nishad'i, gimbiya Azeema" "najin lallai ta Isa kuma ta cancanta, kaso mafi yawa Na fargabar tazarar dake tsakaninta da d'anta ya ragu, harma tad'anji ta rage jin zafin Binta, balle tunda ya ajiyeta taga ko nemanta baiyi ba gashi yau yazo yana faranta mata rai wanda bata taba tsammanin samunshi a yanzu ba." Azeema ta kalli Barira tace “Wazirin ya fada miki?” "Tace “eh Gimbiya yace akwai Gimbiya Zainab a masarautar Zazzau, akwai Gimbiya Nafeesa a masarautar Gumel, akwai Gimbiya Kadijah a masarautar Kano.”" Azeema tai shiru tana tunani kafin tace “zansa a bincika mun su kafin nawa Mai Martaba maganar.” Barira cikin gulma tace “Mata zaki nemowa Junaid?” Azeema ta kalleta sai dai bata ce komai ba ta juya tana tunani. *********** "Tunda aka dawo daga kai masa abincin takasa zaune ta kasa tsaye, burinta da addu'arta shine ace" yaci dan ta tabbatar idan har yaci to ya fara saukowa kenan. Ganin lokaci yaja ta kwala kiran fure. "Jiki Na rawa Fure ta iso d'akin, ta risina tana fad'in “gani uwar d'akina”." "Wani kallo Zeena tamata, cikeda k'asaita tazauna bakin gadonta, “Fure! Inason kije sashen ya" Junaid ki bincikamin yaci abinda muka kai masa?”. "Fure ta had'iye yawu tana gyad'a kai, har zatayi magana Zeena ta katseta ta hanyar watsa mata" harara.... "“to mai kan kifi, halan zakice tayaya zaki sani? Lokaci kad'an yarage na canjaki fure, ko kad'an" baki dace da zama hadimata ba sam”. "“ALLAH ya huci zuciyarki uwar d'akina, a gafarceni gimbiya”." "Banza Zeena Tamata, ta d'auke kanta gefe kawai. Ganin haka sai Fure ta mik'e a sanyaye zuwa" sashen Yarima Junaid. ************* "Bayan sun kammala cin abincin su barira suka kwashe komai, Junaid ya kalli Azeema" saikuma ya duk'ar dakai. “Ummana yaushene zaizo?”. "Cikin nuna jin dad'inta da yanda hankakin Junaid yafara tasiri akan mulki ta amsa masa," "“Nan kusa zaka ganshi, sai dai kafin zuwansa ga tambaya?”." “Ina sauranki”. yafad'a batare da ya d'agoba. “Meka tanada zaka za6a bisa Umarnin mai martaba?”. "Murmushi yayi batare da ya kalleta ba, a ransa yace Umma za6ina bazai saki farin cikiba, dan naji" "a raina bashine burinki ba. Amma a fili sai ya fad'ad'a murmushinsa ”Ummana ina nan Ina nazari dai, kinsan yanzu nake fahimtar komai”." “Gaskiyane”. Ta fada cikin jin dadi. "Daga nan shiru ya biyo baya, shi duk hankalinsa nakan me binta takeyi yanzu? Amma ya kamata" Umma ta sa Binta aiki kamar Bakwa? Bayan ita ba baiwa bace? Ta ajiye aikin taci abinci? Kokuwa har yanzu tana can tana bautar? ************** "Sarki datun randa sukai taron nan amsar da Junaid ya bada ke damun zuciyarsa, sauke" numfashinsa yai tare da dunkule hannunsa. "Meyasa jikinshi ke bashi da matsala? lallai kasantuwar Junaid k'ark'ashin fadarsa babban kuskurene, sannan gangancine, danya lura yaron yana tattare da wata fik'ira dashi kansa baisan" "yana da ita d'inba, me zai faru idan komai ya fito? Ko kuma idan ya nemi amsar mulkin da yake" nasa? "Dolene yay azamar yima tufk'ar hanci, yau zai zauna da shamaki da wambai da waziri bisa" "shawarar daya yanke akan Junaid d'in, dan dolene yasaka Katanga a tsakaninsu." Azeema fa? "Wani sashen zuciyarsa ya ambata. Kansa ya dafe, lallai yanda yake haka Azeema take, musamman" "a yanzu da dukkan motsinta yake akan d'anta da makomarsa, tunda Junaid ya dawo ko gunsa batazuwa sai dai in shi ya aika tazo." Miye mafita to?. "Nace, “saiku nemo” ♀" **************** AYUSHER 26 **************** * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {27} Barira ce ta shigo ta durkusa tace “Gimbiya Mijin Gimbiya Safiya ya iso.” Junaid wanda ko mosti baiyi ba bashi kuma da alamar tankawa. Azeema cikin jin dadi tace “Barira akai Mahmud karamin falina na hutawa.” Da sauri tace to. "Junaid ta kalla, tace “Muje?” Ta fada tana mikewa." "Mikewa yai shima, a hankali ya kalli kofar da zata sadaka da bangaren dasu Binta suke, shiru yai" "kafin ya kalli Azeema wacce itama kallansa tai, ta fahimci me yake tunani. Muje Ummana!" "Yanda ya sake kiranta ne ya sa taji wani irin dadi ya kamata, kallansa tai cikin jin dadi sannan" suka nufi kofa ta baya. ************ "Azeema da kanta tayoma Junaid rakkiya k'aramin falonta Na hutawa, Wanda saika isa d'an gata" "agareta kake shigarsa, shikansa bai ma san da falan ba." "Cike da girmamawa Mahmud ya gaida Azeema, sannan suka gaisa da Junaid cikin girmama juna." "Mahmud cikin jin dadin ganin Junaid yace “Yarima barka da isowa, inata san zuwa dama.”" Junaid yace “bakomai.” Azeema ce takuma yima Mahmud bayani akan mai Junaid d'in ke buk'atar sani sannan ta fito "daga falan, Barira ta kalla tace “a kai musu kayan marmari.”" "Da sauri tace to, kallo daya zakama Azeema kasan hankalinta a kwance yake da alama zuwan" Junaid yau da yanda ya ke mata yasata jin wani dadi har ta kasa boyewa. "Mahmud da Junaid suka k'ara gaisawa, tareda jajantama juna dakuma murnar dawowarsa." "Daganan Mahmud yafara bashi labarin shud'ad'd'en tarihin masarautar, da sarakunan da suka" "gabata, da yanda kowa yay mulkinsa da tarihin daya ajiye har zuwa kan mahaifinsa da sarki Abdussalam na yanzu." "Junaid yacika da al'ajabi, tarihin ya k'ayatar dashi sosai." "Fuskar Mahmud d'auke da Murmushi yace, ""Yarima wanan shine masarautar a dunk'ule," "wad'annan litattafai ne dazaka kuma samun ilimi Na zamantakewa da dabarun mulki, dan sarakunan da suka shid'e sun k'aru da sirrika masu yawa a cikinsu, to lallai nasan kaima zaka k'arun""." "Junaid yad'an murmusa, ""lallai Na gode da gudunmawarka agareni, zankuma nazarcesu, idan ina" "buk'atar fad'ad'a ilimi Zan tuntu6eka""." """To Masha ALLAH""." Sun dan sake yin hira kafin suyi sallama. ************** "Azeema ta kalli barira dake durk'ushe gefenta tai d'an murmushi, ""Barira daga yau kar a sake" "saka binta aiki""." "Cike da mamaki barira tace, ""ranki ya dad'e miyasa?""." Azeema ta gyara zamanta cikeda k'asaita tana wani murmushin da ita kad'ai tasan fassarar "kayanta, ""karki damu da sanin dalili, kawai inason daraja duk abinda ya shafi Junaid”" "Barira ta jinjina kai cikeda mamaki, tasandai ba banzaba, akwai shirinda uwar d'akin nata keyi ta" "k'ark'ashin k'asa, dan tasan haka kawai Azeema bazata sauko ta nemi daraja Binta ba." Harzata mik'e Azeema ta dakatar da ita. """Inason ganin jakadiya""." Barira ta jinjina kai tare da amsawa da to. **************** "Yau sarki Abdussalam ya gagara fita fadanci, sai aiken yana buk'atar hutawa yay" "musu, sannan yabuk'aci ganin Shamaki da wambai da waziri." "Babu 6ata lokaci suka iso, bayan jakadiya ta nema musu Iso suka Shiga." Duk suka gaida sarki cikin girmamawa. "Sarki Abdussalam yay gyaran murya idonsa a Kansu, ""kunsan miyasa na aika a kiraku?”" "Wambai yace, ""ALLAH ya k'arama sarki lafiya bamu saniba, sai dai ganin yanda ka kiramu tabbas" akwai abinda ke faruwa.” Sarki Abdussalam ne yadan sauke ajiyar zuciya ya cigaba da fad'in “me kuke tunani a game da Junaid?” "Fuskarsu dauke da mamaki suka kalleshi, Junaid?" "Abdulsalam yace “duk d'inku kunsan minene ma'anar dawowarsa garemu, sannan kunsan" "makomar hakan, to yarage ruwanmu Neman mafita, domin yaron yawuce zatonmu, na rasa me yasa nakejin ba daidai ba, me kuke tunani zai faru in ya san abinda ya faru a baya? Wanda" idanunsa sun sa na fara tunanin dole mu san abinyi.” "Hankalinsu ne ya tashi, dukansu suka shiga nazari." Shamaki ne ya kalleshi cikin mamaki yace “ALLAH yabaka nasara mizai hana mu tuna baya "kawai?""." Da sauri Sarki Abdussalam ya kalleshi yace “Baya?” "Idanunsa ya zare da sauri yace “Bazai yiwu ba, kun manta wacece Azeema a gareni? bazanso" "aikata hakan ga jininta ba, anema wata mafitar.”" Shiru suka karayi. """Mafita d'ayace"" cewar Waziri wanda ya fada yana gyara zama." """Wacce kenan?"" Sarki Abdussalam yafad'a yana maida kallonsa gareshi." """kayi taron nad'ashi Matawalle ko Galadima, sannan kabashi auren y'arka Zeenatu, hakan zaisa" yai tunanin kafi kowa sanshi sannan yarka zata lura da duk al’amarinsa.” "Wani zazzafan huci Sarki ya sauke, ""shawarar k'arshe dama burinace, dukda ban yanke hukunciba," "amma jin kalamanka yasa ka k'aramin k'warin gwiwa, ta farko kuwa kasan dai galadima nada ransa da lafiya, zamu sakashi yin murabus ne ko me? Zubair kuma shike rik'e da sarautar matawalle""." "Wambai yay wata Y'ar dariya ""Ranka ya dad'e anzo dai-dai wajen kenan ai, dan inhar ka tu6e" "Yarima Zubair ka d'aura Junaid lallai kowa zaikuma girmama adalcin mulkinka, a lokacin kowa zai fahimci kanasan Junaid fiye da yanda kake san danka, uwa uba Gimbiya Azeema wacce zata kara" ganin girma da darajarka.” "Kai ya jinjina cikin gamsuwa, da alama. Kowa yayi na'am da hakan, nantake suka fahimci matsalar" "ta warware, suka cigaba da tsara abinda suke tunani." **************** "Fure dake zube gaban zeena a d'arare tace, ""ranki ya dad'e Azi hadimin yarima ya tabbatar" "min yaci abincin""." "Cikeda d'oki Zeena tace, ""da gaske?""." “Sosai kuwa ranki ya dad'e” """Kai fure baki ta6a sani farin ciki irin yauba, lallai kinata tukuycin albishir mai tsoka""." "Fure ta washe baki tace “godiya nake ranki ya dad'e, ALLAH ya mallakama yarima Junaid ke""." Zeena ta dan harareta tace “me kika sani?” Fure tai kasa dakai tana murmushi. "Sosai Zeena ke tsallen murna ita kad'ai a d'aki, jitake kamar anmata albishir da aljanna yau." "Haka ta fito ta gangaro bangaren Hajjo, Hajjo wacce ke kwance duk batajin dadi ta kalli Zeena," "kallo daya ta mata ta fahimci Zeena nacikin farin ciki, saidai bata tambayeta ba balle tasani saboda abinda ke damunta ya wuce wannan." "**************""" Tunda ya dawo sashensa yake cikin nazarin zamansu da Mahmud da yanda mahaifinsa ya "gudanar da mulkinsa zuwa sarki Abdussalam. Lallai lokacin dazai fito ainahinsa Na jinin sarauta yayi, yakamata kowa ya fahimci sarauta a jini take ba a ayyukaba." "Sabon shiri yasake, kafin ya aika Azi sashen mai martaba Neman ison ganinsa. Anyi sa'a shima mai" "Martaban yana muradin ganinsa, dan haka babu wani janjani yasamu izini." "A yanda Junaid ya fito dolene kowa ya kallesa, ya rikid'e ya canja gaba d'aya, saika rantse a" "madarautar ya girma, harira kanta galala tai tana kallonsa, lallai ta yarda mulki a jini yake ba'a ayyuka ba." "Shi kansa Zubair dake k'ok'arin shiga sashensa la6ewa yai yana kallon Junaid, gaba d'aya saiyaji ya" "raina ajinsa da girmansa, wai harma yaushe Junaid d'in yagama fahimtar shi jinin mulki ne? Jibifa yanda yake wani shak'ar iska da fesar da ita tamkar shine sarkin, lallai aikine babba agabansu, dan wannan yaron idan basu risinar dashiba to zai 6allo musu ruwa." Oho Yarima Junaid baisan yanaiba. "Itama Hajjo tuni labari yakai Mata, ba k'aramin girgiza tayiba dajin batun, zeena dake gefenta ta" "mik'e da hanzari tafice, saidai tana fitowa Junaid Na shigewa turakar mai martaba." "Takaici yasata cizon yatsa, takoma da alwashin jiran fitowarsa." **************** "Sarki Abdussalam dake kishingid'e ya zubama Junaid idanu, mamaki yake a ransa yaushe" "junaid d'in ya koma haka? Koda yake ba abin mamaki baneba, yasan wacece Azeema sarai, komai zata iya aikatawa akan d'anta domin mulkin nan, amma bai tdammaci hakan da wuriba....." "Gaisuwar Junaid ta katse tunanin mai martaba, ya amsa masa da kulawa. Shiru ne ya biyo baya," "kowa yana nazarin d'an uwansa, zuwa can mai martaba ya nisa yana gyara zamansa," """junaid akwai matsalane, Ka buk'aci ganina?""." "Murmushi junaid yayi, yad'an girgiza kansa, ""A'a Abba, dama za6in daka bani nazo fad'a maka""." Murmushi Abdulsalam yai yace “ina jinka me kakeso?” Ya boye damuwarsa dake kasan ransa. """Nayi farin ciki da hakan Junaid, amma kafin sannan gawani albishir"".Abdulsalam ya cigaba yana" kallansa. "Kallonsa Junaid yad'anyi, saikuma ya murmusa yana maida kansa k'asa." "Sarki Abdussalam bai fahimci murmushin Saba, ya danne ya Fara magana," "“Duba da wasu abubuwa danai na fahimci yakamata kayi aure, kai idan masarauta ne, hankalin" "kowa a kanka yake kana ganin matsalar data afkou wancen lokacin, hakan yasa yai tunani hadaka" aure da kanwarka Zeenatu.” “Zeenatu?” Junaid yafad'a yana kallon mai martaba fuskarsa dauke da matuk'ar mamaki. Shi kansa mai "martaba ya fahimci haka, dan haka ya gimtse fuska yana fad'in," “Umarnine Junaid dan dan Sarku matarsa ta farko dolene yabi umarnin wacce aka zaba masa.” Jinjina kai junaid yashiga yi yana wani irin murmushi “Sosai ka cancanci nabi Umarninka domin "matsayin mahaifi kake a gurina, naji na kar6a da hannu biyu""." "Sarki Abdussalam ya murmusa, dan aganinsa yasamu nasara a matakin farko. ""ALLAH yay maka" "albarka Junaid, ina sauraren za6inka.”" """Abba za6in nawa nima bamai wahala baneba, domin duk bisa bigire d'aya muke""." Bigire daya? "Gaban sarki Abdussalam ya fad'i, kardai mulkin?. Kafin ya nemo amsa maganar Junaid ya" katseshi...... """Inason izinin Auren yarinyar da muke tare acan, binta!...""" “Binta?” Sarki Abdussalam yafad'a a harzuk'e wanda yau ne karo ma farko da Junaid yaga yayi magana haka “Junaid maidamin murtani akan rashin kar6ar za6ina yasaka tunanin had'amin yarinya da Y'ar talakawa marar usul ko me? Ni nai tunanin taho maka da ita saboda ganin kana bukatar "kwanciyra hankali anan, yanzu kuma ka kawo zancen so?”" "Shiru junaid yai yak'i tankawa, yay kuma kicin-kicin da fuska babu alamar fara'a, danmmi za'a kira" "binta mara usili? To lallai inhar zai auri zeena sai dai da binta, inba hakaba kuma zai 6allo ruwa gaba d'aya kawai, saiya auri wadda basaso d'in da k'arfin mul......" """Dakai nake magana"". Sarki Abdussalam ya katse tunanin junaid." "“Dago ido junaid yay ya kallesa, fuskarsa babu alamar fara'a, hakan ba k'aramin razana sarki" "Abdussalam yayiba, dan ainahin marigayi sarki Zubair yagani a fuskar Junaid d'in, kasa cewa uffan" "yayi, saiya samu kansa da sassauta fushinsa, yace," """Nabaka lokaci kayi tunani, bani kad'aiba ko mahaifiyarka bazata yarda da za6inka ba, har gwara" ni zan iya hakura amma kai kasan Azeema bazata taba yadda ba.” "Junaid ya murmusa, ""Tuba nake Ranka ya dade ba binta kawai ba, ko Zeena bazata aminta ba," daga zuwana na shaida hakan.” "Yana gama fad'an hakan yamik'e ya fito cikeda kasaita da izza, wadda tasaka sarki Abdussalam" kasa d'auke ido daga kallonsa. Har yaushe Junaid d'in yay irin wannan canjawar?. "Junaid na fita ya tsaya a waje a hankalu ya juyo ya kalli bangaren Abdulsalam, bai taba tunanin" "shima xai zo mai da magana haka ba, juyawa yai cikin isa ya nufi bangarensa." ****************** "Jakadiya ta kwashi gaisuwa wajen Azeema kafin tace, ""Ranki ya dad'e gani""." """Na ganki ai"". Azeema tafad'a tare da zuba mata ido. Takuma gyara zamanta tana kallon jakafiya" dake gurfane. """Jakadiya inason bincike akan y'ay'an sarakunan k'asar zazzau, Gumel, kano""." """Angama ranki ya dad'e""." "Jakadiya na fita Azeema ta kalli barira, ""Naji ance jiya mai martaba yayi zama Na mussaman da" "waziri da wambai da shamaki""." """Eh lallai ranki ya dad'e anyi hakan, amma naji k'ishin-kishin akan auren gimbiya Zeena ne""." "Baki Azeema ta ta6e, saikuma tayi murmushi" Barira cikin san gulma tace “Gimbiya yanzu wace d'iyar sarkice a cikin ukunnan tadace da yarima "Junaid?""." Azeema ta dan harareta. "Dariyar farin ciki barira tayi, saboda tunowa da binta tace “ranki ya dad'e mu jirayi tarihin" "kowaccensu saimu d'ora a mizani, dan yarima yafi dacewa da d'iyar bajimin sarki mai ginannan" "tarihi""." """Wannan gaskiyane barira, shiyyasa nakeson kasancewa dake a komaina, ko mai martaba bazai" "San komaiba akai saina gama da shikansa junaid d'in""." """wannan shawara tayi ranki yadad'e""." ***************** """Uwar d'akina ga yariman can yafito daga sashen mai martaba, sai dai kuma ransa kamar a 6ace" kamar yanda na kula.” Kamar Zeena tana bama fure amsa saikuma ta fasa “A bace? Ko muje bangarensa? Ai yayanane ba wanda zaice wani abin.” “Amma ranki ya dad'e bak'ya ganin yawan zarya sashensa kamar zai ”saikuma tai shiru ta kasa k'arasawa saboda hararar da zeena ta watsa Mata. Tace “Gun Yayana zani kinada magana?” Fure ta zube tace “tuba nake Gimbiya.” "A falo suka iske hajjo da Ramlah suna magana sai dai da alama ana jinsu akai shiru, harzata" "wucesu hajjo ta dakatar da ita ""Ina zakije?""." "Baki ta turo, “zan d'an fita mik'e kafa mana""." Hajjo taja tsaki tana d'auke kanta. Zeena kuma tafice fure Na take mata baya. *************** "Gaba d'aya ran junaid a 6ace take, yayinda zuciyarsa kemasa wani sak'e-sak'e akan mai" "martaba. Ya tuna wadda akeson had'ashi aure da ita, yarinyar data tozartashi farkon shigowarsa masarautar, wadda batasan darajar d'an Adam ba, zai aminta da aurenta kawai domin yasamu damar kasancewa da kwatarwa Binta ‘yancinta, Ada ba son binta yake amatsayin masoyiyaba, amma ganin matsayinsa da nata ya kawo tazara a tsakaninsu yayi tunanin aurenta, hakanne kawai zai dai-daita matsayinsu tamkar yanda yake gani a tun farko. Yasan kuma babu Wanda zai amince masa da auren Binta kai tsaye, musamman mahaifiyarsa, amma idan ya jingina akan auren Zeena to lallai zai samu yanda yakeso, yanaji a zuciyarsa mai martaba da manufa yake son bashi auren" "Zeena, inhar kuma yaga bashida mafita dolene ya yarje masa akan auren binta." Ummana fa!?. Wani sashen zuciyarsa ya ambata. Kafin samun amsa sallamar Azi ta katse tunaninsa. Azi ya rissina yana sanar masa da neman iso daga Zeena. "Wani kallo ya watsama Azi, kafin yace, ""Bana bukatar hayaniya""." Azi ya jinjinamasa kai cike da girmamawa. "Takaici ya kama Zeena jin amsar da Junaid ya bayar abata, wannan wulak'anci har ina, takula" "yarima Junaid yacika tsauri da rik'o, yakamata ya yafe mata inhar akan laifin data aikatane bisa rashin sani, ita ta rasa meyasa take san ganinsa." Ranta a 6ace tabar sashen. *************** "Mamaki yakama Binta jin zancen da barira take Mata, wai gimbiya Azeema tace kar asake" sakata wani aiki. "Kodai Junaid ne yay magana? To amma jifa yanda ya watsar da ita d'azun, hakan bak'aramin k'ona" "ranta yayiba, dan har kuka tayi, ita gaba d'aya ya Junaid ya canja Mata, tamkar bashine abokin" nan nata dasuka tashi tare suka rayu tareba. """Ya ALLAH kabani ikon jurewa da wannan sabuwar rayuwa mai cike da rashin ya Junaid a cikinta""." Ta share hawayen da suka ziraro Mata. ************* "Mamaki sosai ya Kama gimbiya Azeema ganin yau kwanan junaid uku bai lek'ota ba, Anya kuwa" lafiya?. Kokuma nazarin littatafan tarihi da Mahmud ya bashine suka d'auke hankalinsa?. """Inaga hakane"". Tafad'a a fili tana murmushi da kauda zarginta na farko." "Sai mai martaba da shima a kwanaki ukunnan Sam bai nemeta ba, baki ta ta6e, dan hakan bai" "dameta sosai ba, ayanzu burin gyara rayuwar d'anta ne a gabanta, dan nan kusa take buk'atar dawowar mulki hannunsa, tunanin yanda zatai da Abdulsalam ne ya darsu a ranta, dolene ta san yanda zatai." "Nace, ""turk'ashi, wannanfa shine ga akuya ga kura ♀""." *************** Ayusher 27 *************** * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {28} "Bude idanunsa yai a hankali ya daurasu akan Azi dake durkushe a gefensa, Littafin dayake nazari" na hannunsa ya kulle. "Azi yai murmushi yace ""yauma bazaka fita bane?""" "Junaid ya kalleshi yace ""zuwa yamma.""" "Azi ya jinjina kai cikin gamsuwa sannan ya mike, haryaje kofa ya juyo ya kalli Junaid, Junaid ne ya" kalleshi kallo mai dauke da tambaya. "Azi ya kara rusunawa yace ""Binta fa ta zama 'ya, jiya dana ganta, da alama Gimbiya ta zareta" "daga gun bayi.""" "Kai Junaid ya jinjina bai ce komai ba, Azi wanda ya fahimci jin dadin Junaid ya fita daga falan." "Shiru Junaid yai a hankali kuma wani lalausan murmushi ya zagaye fuskarsa, baiyi niyyar fita ba" saboda yana jiran aike daga bangaren Mai Martaba sai dai jin haka yasa ya mike. "Ciki ya shiga ya fara shirin fita, harya gama shirya wa sai kuma ya koma ya zauna." ************ "Kallan Barira tai tace ""Anji daga gun Junaid?""" "Barira tace ""tuba nake ranki ya dade amma haryanzu ba labari.""" "Shiru Azeema tai, tace ""Binta fa?""" "Dazu wai zata fita, Azeema ta kalleta tana mata alamar ina?" "Kai Barira ta girgiza tace ""bansani ba Gimbiya.""" "Shiru Azeema tai tana dan kada hannunta, badai dan ta bata matsayin 'ya ba take neman" zagayewa ta dinga zuwa gun Junadi ba tare da saninta ba? ********** "Mikewa naga ya sake yi sannan ya fito daga cikin dakin nasa, da sauri Azi ya matso yace ""Yarima" "zaka fita ne?""" Kai Junaid ya daga cikin kasaita ba tare da ya amsa ba. Da sauri suka matso dan yima Junaid rakeyi. "Zeena wacce ta nufi bangaren Junaid ce ta tsaka cak, daga nesa wanda akala yakai taku goma" sha biyar tsakaninsu. Itama ja tai ta tsaya daga inda take. "Zeena ranta yakai matuka gun baci, tun daga sama ta kalleta zuwa kasa, da alama kenan ta fita" daga matsayin bayin da take? Cikin isa ta daga hannu tayima Binta alama da ta zo. Binta ta kalleta sannan ta karasa inda take. "Wani banzan kallo ta sake mata sannan tace ""daga ina?"" Binta ta kalleta tana tunanin wannan tambayar fa?" "Zeena ce ta katseta da cewa ""ina zaki kuma? A iya sanina kin bar bangaren Ya Junaid.""" "Binta ta dago ta kalleta sannan tace ""zanje gun Harira ne.""" """Harira? Wace kenan?""" "Shiru Binta tai ganin batasan me zata ce ba, Zeena jin bata tanka mata ba yasa tace ""banaji dai mace wacce tasan mutuncinta zata dinga zirga zirga bangaren namijin da batada alaka dashi ba.""" "Binta ita kanta batasan sanda ta kalleta ba, hatta Fure sai data guntae dariyar data taso mata." "Ganin yanda Binta ta kalleta ne ya harzako Zeena dan dama neman abinda zata mata takeyi," Binta bata nufa ba taji an wanketa da mari. "Kallanta tai cikin tsananin mamakin laifin datai, Zeena tace ""me? Zaki rama ne?""" "Binta tai shiru, ke yanzu in har kinada hankali ba tattarawa ya kamata kiyi ki dau kafafunki ki" koma mahaifarki ba? Binta yanzu kam ta fara zargin san shi Zeena takeyi. "Junaid wanda ya fito yana tsaye daga bayansu yanajin abinda ke faruwa, ransa yakai matuka gun" "baci duk da a fuskarsa bazaka gane ba, Binta ce ta dago zatai magana ta ga Junaid, ido ta kuramai ta kasa cewa komai." "A kufule Zeena ta juya dan taga meke faruwa, Junaid suka gani a tsaye yana kallansu." "Gaban Zeena ne ya fara dukan uku uku, wanda idanunta suka firfito waje, a hankali cikin kasaita" da takama ya fara taka kafafunsa zuwa inda suke. "Binta kam kallanshi kawai take gaba daya ya canza, ya sake kwarjini, dama haka Junaid yake ko" dan ya dawo inda ya dace dashi ne? "sauke idanunta tai daga kansa ganin ya nufo daf da inda suke, Zeena a rude tace ""Yaya.""" "Kallanta yai yace ""Zeena? Me kikeyi a nan?""" "Ta kalleshi cikin fargaba tace ""dama nayi tunani zuwa ne gunka.""" "Guna?""" "Kai ta daga,yace ""me kike anan to?""" Kallan Binta tai wacce ganin bai kalleta ba yasa gaba daya taji kafafunta sun fara rawa. Idan na kasa dake ya miki laifi me zai sa ki kaskantar da kanki a ciki mutane? "Mamaki ne ya kamata ta kalleshi da sauri, Binta kam gaba daya jitai kanta ya fara wani sarawa," "juyawa yai zuwa bangarensa, Zeena ta kalleta ta dafa kafadarta tace ""dan an sa saban kaya ba'a canza asali.""" "Tabi bayansa, Azi kam wannan lamari shi kanshi ya daure mai kai, meke faruwa?" "Suna shiga cikin falansa kallo kadai yama Azi, suka bar falan dukansu." "Yana tsaye dama bai zauna ba, ita kanta Zeena a tsaye take, cikin salo tace ""Ya Junaid.""" "Bai juye daga inda yake ba yace ""ke kika nemi hadin aure tsakani na dake?""" "Gabanta ne ya cigaba da faduwa, ta rasa me yasa yau take jin shakkar Junaid haka." Juyowa yai ya kalleta sai kuma taga ya saki wani murmushi wanda ya kara sata cikin wani yanayi. "A hankali ya tako zuwa inda take yace ""me? Bake bace?""" "Kallansa tai idanunta duk sunyi jaa, kai kace marinta akai, a hankali tace ""nice.""" "Murmushi ya sake yi yace ""kinasona da har kike tunanin zaki jure duk matsalar da zata fito ta" "bangaren Hajjo da Ummana?""" "Yawun bakinta ta hadiya sannan tace ""Eh.""" "Yadan jinjina kai a hankali yace "" hakan yayi, sai dai in har kinaso na aure nima sai kinbi sharadi na.""" Sharadi? "Ta fada a dan tsorace, yace ""eh sai dai in zan aureki tare da kawarki.""" Kawata? "Cikin mamaki tai tambayar, yace ""wacce kuke hira da ita a waje dazu, na tabbatar yanda kike yar" "sarki bazaki daga hankalinki akan hakan ba.""" "Rainin wayau, bayan yasan abinda sukai a waje harya tambayeta yanzu kuma yazo mata da wani" rainin hankali? Wai kawarta? Sannan me? Ya hadasu da wannan yar iskar da ba'a ma san tsatsonta ba? "Junaid ne ya kalleta yace ""kina so ki aureni wannan ce kadai hanya in kuma baki amince ba kowa" "yasha zamansa.""" Shiru gai tama rasa ta ina zata fara kamo abinda ya kamata. "Junaid yace ""ki sanar da Mahaifinki haka dan nasan zai kira ya tambayeki, in kuma baki amince" "ba kowa yasha zamansa.""" Yana kaiwa nan ya fita daga falan ya barta a tsaye kamar gunki. "Binta kam kasa ma shiga gun Hari tai tana tsaye a gun kamar wacce bata numfashi, abun daya" faru sai kara dawo mata yakeyi. "Ganin Azi ya fito yasa ta fahimci sune, da gudu tai kwana ta labe, sai dai kafin ta karasa kwanar" "Junaid ya hangota, tsoransa ma kartaje garin gudu ta fadi taji ciwo." "Haka suka zo ta saitin inda ta boye ya dan kalleta ta gefen ido ya basar, kiyi hakuri Binta idan har" banyi hakan ba bayanda za'ai na dawo dake gareni. Bangaren Azeema ya nufa wacce ganin Junaid baizo ba yasa tasa a kara kiran Jakadiya. "Suna zaune Jakadiya na mata bayani akan binciken da akai, Azeema kowacce aka nuna mata aka" mata bayani sai tadan kushe. Jakadiya tasa dariya tace “Gimbiya taya za’a samu wacce zata dace bayan duk wacce aka baki bata miki ba?” Azeema tai murmushi tace “bawai basumin bane Junaid dine kamar basu dace dashi ba.” "Barira ce tai dariya tace “A idanun Gimbiya, Junaid ne kadai ya cika yanda ya kamata .”" Azeema ta kalli Jakadiya tace “Me Takawa yake a ‘yan kwanakin nan?” "Jakadiya tace “nikaina bansan meke faruwa ba, da alama wani nazari yakeyi.”" Matsowa tai cikin gulma tana san sanar da ita har Junaid ya kira bayan sun zauna dasu Shammaki aka sanar da isowar Junaid. Da sauri ta suka tattare Barira ta nunawa Jakadiya hanyar baya ta fita da sauri. Azi ne ya kalli wacce tai ison ya sake mata alama dan ta sake sanarwa. "Barirace ta karaso da sauri ta bude kofar, sannan ta basu hanya." "Junaid ya shiga ciki, kallan Azeema yai wacce ta gyara zama kai kace ita kadaice dama a gun." Zama yai ya gaisheta cikin kulawa. "Kallansa tai cikin wani jin dadi tace “Barka da isowa Yarima, har ina tunanin aikawa kazo, ganin" kwana biyu banganka ba.” Junaid ne ya kalleta yace “Tuba nake Umma na.” "Wani dadi ne ya kamata, tace “Ya zanyi, ai ganinka ya wanke komai.”" Murmushi yai cikin jin dadi. "Barirace ta sunkuyo tace “Yarima, Gimbiya ta maida Binta matsayin ‘ya.”" Kallan Azeema yai sannan ya sunkuyo yace “tana godiya Ummana.” "Shikenan? Abinda yazo mata ranta kenan, ganin ba wani farin ciki a fuskarsa yanda ta zata." Sai dai hakan ya mata dadi ta wani bangaren. *************** "AbdulSalam ne yai shiru, yau ya gama tattare duk wani hukunci da zai dauka." "Shammaki ne ya kalleshi su biyu a cikin falan, yace “Ranka ya dade ka gama tunanin?”" "Abdulsalam yace “eh. Dole ne mubi abinda yakeso inhar munasan abinda mukeso ya samu," sannan inhar munaso mu binne abinda yake tattare da rayuwarmu.” "Kayi shawara mai kyau Ranka ya dade, kayi hakuri mu bashi abinda yakeso, ni inaga wahala ma" kadai ya isheta a gadan nan da batada kowa. Kai Abdulsalam ya jinjina yace “inka fita kasa a kira Zeena.” "Nan Shamaki yai sallama, a waje ya bada sakon Takawa sannan ya tafi." "Zeena wacce tunda ta shigo bangaren Hajjo ko kala batace ba, duk kuwa da maganar da Hajjo ta" mata bata iya tankawa ba. Zubair ne ya kalli Hajjo yace “Hajjo kin bincika mai Junaid suka tattauna da Mai Martaba?” Hajjo ta kalleshi tace “Zubair sau nawa zaka tambayeni ne? Menene matsalar ka ne nikam? Bantaba ganin ka cikin wannan yanayin ba.” Ya kalleta fuska a kumbure yace “Hajjo bakiga yaran nan bane shi yasa.” Tsaki taja tace“kaidai kayi kokarin bin karatun ds akema karka kuskura ka bari yaran nan ya sake wulakantani dan wlh bazan taba yadda ba.” Baki yadan kara kumburowa sai dai baice komai ba. Harara ta bugawa Zeena tace “Ke bansan iskamci kinshigo ko kala bakice ba.” Fure ce ta shigo da sallama ta zube tace “Gimbiya Mai Martaba yana nemanki.” Wani murmushin jin dadi Hajjo tai da alama Sarki ya yanke hukunci akan maganar Sulaiman datamai. Mikewa Zeena tai kamar mara rai ta nufi kofa. Hajjo ta sake wani murmushi jin dadi. Nace Zai zama kuka ♀ ******* Zeena ce dukufe a gaban Mai Martaba ya kalleta yace “Zeena!” Kallansa tai tace “Naam Abba.” Shiru Abdulsalam yai kafin yace “maganar Junaid namai magana.” Kallansa ta sakeyi sai dai batace komai ba dan ta riga tasan me zai karasa ce mata. Sai ji tai kuwa yana cewa “Yace inhar zai aureki sai dai ya hada da yarimyar daya taho da ita.” Shiru tai wanda hakan yasa Sarki yace “Zeena! In kinsan bazaki iya ba ki hakura ki auri Sulaiman.”Yai maganar cikin kakkausar murya dan ya fahimci inya mata lago lago zata lalata komai. Kallansa tai tace “a’a na amince.” “Kin tabbatar zakisa Hajjo ta yadda da abin nan?” Kanta tsaye tace “eh.” "Yace “jarki fadawa kowa maganar Binta, sannan Hajjon ma karki mata zancen ki da Junaid" harsai munyi magana dashi.” "Tace to, mikewa tak ta fito gaba daya jikinta ba karfi kai kace wacce ta tashi daga jinya ce........." Hmmm ♀ ******* Ayusher ♀ * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {29} "Zeena tana fita Abdulsalam yai shiru yana nazari, Junaid ya kamata yasa a kiramai ko Azeema?" Dan tabbas yana san al’amarin nan ya faru cikin gaggawa tunkafin Junaid ya gama fahimtar masarautar. Idanun Junaid ne suka fadi masa a lokacin daya mai zancen indai zai auri Zeena to lalai sai dai ya hada da Binta. "Bari ya shawo kan Azeema ya tabbatar ita bazata taba yadda da wata Binta ba, dole yai amfani da ita." A daren ranar sarki Abdussalam ya buk'aci ganin Azeema a matsayin wadda zata kwana a sashensa. Tunda yammaci jakadiya ta Isar mata da sak'on mai martaba. "Bata wani ja lokaci ba ta amsa kiransa itama, dan tanason jin wane zamane yayi dasu wambai" "kwana hud'u da suka wuce, sannan tana san tamai magana akan auran Junaid da takeso ayi." "Sai wajen tara Na dare ta kimtsa cikin shiri Na alfarma da baza k'amshi, ta d'ora had’ad’iyar" "alk'yabbarta, barira ce kawai tamata rakiya sashen mai martaba." Bayan sanar da zuwanta jakadiya tamata iso. Tana shigowa cikin turakar tasa ya mike a hankali ya tako zuwa inda take. Azeema ta kalleshi cikin kulawa tace “Takawa!” "Abdulsalam ya mika mata hannunta, hannu tasa ta rikoshi, ya jawota har jikin gadansa sannan" "ya zaunar da ita akan gado, dagowa tai ta kalleshi sannan tai murmushi." Zama yai kusa da ita shima sannan ya jawota jikinsa ya rungume. Murmushi ta sake yi sannan tace “AbdulSalam!” Bai saketa ba har sai daya biya bukatarsa. "Jawota yai jikinsa ya sake rungumeta, tadan tureshi kadan tace “Menene?”" Hannu yasa akan fuskarta yace “Me kike tunani in muka hada jinin mu aure?” Jinin mu? "Ta maimaita tana kallansa, kai ya daga mata yace “Zeena da Junaid nake nufi.”" Yanda take kallan kwayar idanunsa ne ya sashi sake cewa “menene?” Mikewa tai zaune da sauri tace “bangane Zeena da Junaid ba.” Shima zama yai sannan ya kamo hannayenta yace “badai na tunanin Azeema zataki hada jininta "da nawa, dan na tabbatar sirri na nata ne.”" Kallansa tai idanunta cike da tsoro tace “Abdulsalam?” Yace“me? Ba hakan bane? Na tabbatar duk abinda nai a baya kin sani sannan baki taba furtawa "wani mai numfashi ba a doron kasa ba, kinga hakan yasa nasan ni dake sirrinmu na juna ne kamar" yadda nima duk abinda ya shafi ki sirri nane.” Hannunta ta zare da sauri wanda gaba daya taji jikinta yana rawa. Bakinta na rawa tace “zan wuce bangarena.” "A daren nan? Ya fada yana kara rike hannunta, me kike tsoro? Bayan komai a tafin hannunki yake?" Ki kwanta kiyi bacci hankalinki a kwance. Yanda take kallansa yanzo kallo ne mai cika da shakka....... "Ya d'auke Kai yana wani murmushin k'asaita, yasan wacece Azeema sarai wajen rik'o da ra'ayin kai," amma ya tabbata a wannan ga6ar yamata kamun da bata Isa su6ucewa ba. "Itama komawa tai ta zauna zuciyarta na sake maimaita maganganunsa, dolene tayi hak'uri sai" "asuba ta koma sashenta tamkar yanda sukeyi, dan inhar takoma yanzu hakan zai d'auki hankalin wasu, duk yanda taso bacci ya dauketa kasawa tai." "Idan ita ta amince Junaid fa? Ko kad'an bataga ta inda junaid ya dace da Zeena ba, sannan tama" "Yaya jininta zai kasance waje d'aya dana hajjo? Dukma ba wannanba, hajia iya zama ta amincene? Kai, wai miyasa Abdussalam yay wannan tunaninma?...." Wannan tambaya da zuciyarta tai matane ya sakata juyawa ta kalli Sarki Abdussalam dake kwance shima yana kallonta. Murmushi yamata. Batareda ta maida masa murtani ba tace. “Kozan iya sanin dalilinka Na wannan had'in?” "Murmushi yakumayi, sannan yatashi zaune yana matsowa jikinta. “Azeema ki tsaida zuciyarki" "waje d'aya, kinsan har abada banzan cutar da jininki ba, auren wad'annan yaran shine Makullin sirrinmu, ko kina tunanin duk randa shi kansa Junaid ya san sirrinmu zai d'aga mana k'afane? Bayanann ki tuna inada d'a Zubair, ya girmi Junaid, atunaninki shi mahaifiyarsa batason yayi mulki? Had'in auren Junaid da Zeena itace hanya mafi sauk'i wajen dank'a masa mulki da maganin" tasowar duk wata k'ura da muka binne a baya”. "Ajiyar zuciya Azeema ta sauke, tad'an gamsu da jawabinsa, saidai gaskiya batason had'a zuri'a da" "hajjo, amma tasan matakin dazata d'auka, sannan tana a kan bakanta Na aura masa d'iyar mashahurin sarki." ****************** "Washe gari Azeema da kanta ta buk'aci ganin Junaid. Anutse yai shirinsa cikin kayan alfarma," Azi yai masa rakkiya tamkar kullum. Bayan an masa iso yasamu shiga har cikin k'uryar d'akinta. "A zaune ya isketa tayi shiru dan ko shigowar shi bataji ba tsabar ta shiga cikin tunani mai zurfi," "kallo d'aya zakai mata kuma ka fahimci tana tare da damuwa. Da sauri ya k'arasa gareta, “Umma lafiya kuwa?”." "Hannunta ta janye tana sauke ajiyar zuciya, ta kalli Barira dake tsaye a k'ofa. “bana buk'atar" "motsin kowacce hadima, kowa yaje sai nan da awa d'aya Ku dawo”." Barira ta jinjina kai da fad'in “angama ranki ya dad'e” juyawa tai ta fita zuciyarta na mamakin "minene matsalar uwar d'akin nasu, tunda tadawo sashen mai martaba da asubahi batada" walwala. "Azeema ta maida kallonta ga junaid dake durk'ushe gabanta, hannunsa ta Kama tana masa nuni" "daya zauna sosai. Bai musaba ya zauna, murya a raunane Yakuma mai-maita Mata tambayar d'azun." "Tad'an murmusa domin kauda damuwar fuskarta, “Ka kwantar da hankalinka Junaid, babu" "abinda ke damuna, yanzu natashi a barcine. Nakiraka ne muyi wata magana”." “ina saurarenki Umma” Abinda yace kenan duk da bai gamsu ba. “Junaid me kake tunani akan Zeena?” Duk da yasan me take nufi amma sai yai kamar bai sani ba yace “Zeena? Me nake tunani kamar ya?” Ta daure tace “Junaid zaka iya zaman aure da Zeena?” "Cikeda mamaki ya kalleta, ”Umma miyasa kikaimin wannan tambayar?”" “Saboda inason ka aureta”. "Y'ar zabura yai cikeda tsoro dan duk da yasan maganar amma bai kawo har an shawo kanta , ta" yaya? Kwana daya kacal? Tabbas akwai abin bincikawa a wannan lamari. Kallanta yai yace “Umma miya birgeki ga yarinyar data fara tozartani farkon shigowara "masarautarnan, ama bar wannan rashin sanine amma gaba daya yarinyar nan batada tarbiyyar" "data dace, meya birgeki dahar kike tunanin had'a jininta da naki?”" "Tambayar ta daki zuciyarta, amma saita danne, cikin dai-daita kanta tace, “Ka d'auki hakan" "matsayin kuskure Na rashin sani, sannan Zeena batada matsala matsalarta daya rashin uwa mai" tsawatar mata.” "Shiru Junaid yai yana nazarinta, lallai zuciyarsa takuma yarda akwai sirrin dake tsakanin sarki da" "mahaifiyarsa, to amma nami? Miyasa zai zargi mahaifiyarsa da kansa? Ya salam zuciya wannan k'aryane, ummana bazata aikata komai na son zuciya ba duk da bai gama saninta ba amma yana mata fatan hakan............" Tunaninsa ne ya katse saboda dafashin da tayi. Daidaita zamansa yai ya kalleta bayan ya canza yanayin fuskarsa. “Zan amince da auren Zeena amma da sharad'in in har zaki amince ku hadata da Binta.” Wata muguwar zabura tayi tana kallonsa cikeda tsananin mamaki. “Junaid kanada hankali kuwa?” Murmushi yai cikin wani yanayi mai wuyar fassara yace “Ummana lafiyar d'anki k'alau.” Bazai taba yiwu ba kai kasan bazan yadda ka auri Binta. Kallanta yai yace “Na yanke wannan shawaran ne ba dan komai ba sai zargin da nake akwai "manufar mai martaba na had'ani aure da Zeena, inhar y'ancinmu kike buk'atar mu k'wata, mulki yadawo gareni kamar yanda kike buri to lallai dolene na had'asu su biyun, inba hakaba zanbi tawata hanyar na bankad'o gaskiya, dan inada abubuwan da ban gansu dasu ba, inason sanin dalilin mahaifina na sakawa a maidani na rayu a ke6antaccen waje bayan yasan mahaifiyata nada" ranta. ” Kallansa tai tabbas Junaid jinin Zubair ne wanda ya dace da mulki sai dai in har yayo halin Zubair "tabbas ita kanta bazata tsira ba, hankalinta ne ya tashi ta kalleshi tace Junaid Na Neman k'ara Mata zafi akan Wanda sarki ya had'a Mata a daren jiya," "Daurewa tai tace “Amma Junaid hadin auren ba shi bane, yanzu na maida Binta ‘ya, zan samo" maka wata ka aura.” Ido ya kura mata yace “Me kikace a gaba da daraja abu mai daraja?” "Kallansa tai batace komai ba, yace“indai har bazaku amince da hadin auren da Binta ba to nima" bazan auri Zeena ba inyaso kowa yasha zamansa.” Ya fada fuska a hade. "Kallansa tai kanta taji ya fara sarawa, itakam sakayya ce take neman afkuwa da ita." "Mikewa yai yace “in kinyi nazari mayi magana, nabarki lafiya Ummana.”" "Shiru tai haryabar dakin, meyasa komai baya tafiya yanda takeso? Haryakai kofa tace" “shikenan!” "Da sauri ya juyo ya kalleta, murmushin yake ta kakaro tace “shikenan ka auresu, indai inaso in" daraja abu mai daraja dole naso abinda abin da kakeso.” "Jikinsa ne yai sanyi, ya tako a hankali zuwa inda take ya durkusa yace “nagode Ummana.”" Shiru tai batace komai ba... ****** "Binta kam gaba daya wani irin zazzabi ne takeji yana neman rufeta, tun abin da ya faru jiya, idanun Junaid take hangowa da yanda ya nuna bai damu da ita ba." "Wasu zafaffan kwala na dana sani ne ke zubo mata, da alama zamanta a gidan nan ya kare." ***** "Zeena kam abincin gabanta kawai take jujuyawa ta kasa ci, kallan Fure tai tace “Fure me kike" tunani a kan matsayina gun Ya Junaid?” Fure tai dariya tace “ai Yarima ya fara fuskartar kedin kece kika dace dashi ko baki ga abinda ya "faru jiya ba, kiga yadda ya wulakantata saboda ke.”" Kallanta Zeena tai a ranta tace “inafa wulakantata ya jani falo dai ya wulakantani san ransa.” "Saura Hajjo abinda ta fada kenan a ranta, mikewa tai tace “muje gun Hajjo.”" Da sauri Fure ta taso..... **** * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {30} ******************** "Ran Hajjo a 6ace ta kalli amintacciyar baiwarta. ""kina nufin jiya Azeema a turakar mai" "martaba ta kwana?""." """Wannan gaskiyane ranki ya dad'e, lamarin ya girgiza kowa, dan ansan dai kwanankine jiyan """ "Zeena dake zaune tana karyawa tai saurin fad'in ""To banda munafunci irinna bayi miya ruwanku?" "Shi Abba bashida damar kusanci da kowacce matarsa a lokacin daya so? Kunsan dalilin kwanan natane dazaku kawoma mutane tsirku""" Duk Harar da hajjo ke zubama Zeena batai shiruba saida takai aya. Sosai hankalin hajjo yakuma "tashi, dan dama labarin zuwan Zeena sashen mai martaba sau biyu dukya zomata." "Da sauri tace, ""inason a nemamin ison zuwa sashen mai martaba yanzunan""." """Angama ranki ya dad'e""." Babu dad'ewa da tafiyar baiwar tadawo da sak'on mai martaba yanada bak'i Na musamman. Dole hajjo ta hak'ura da zuwan. "Zeena ce ta daure bayan sun fita tace ""Hajjo.""" "Kare hade rai Hajjo tai ta kalleta tace ""ke kuma menene?""" Ganin yanayin Hajjo yasa ta kasa cewa komai. "Shikenan, dama cewa zanyi Ya Zubair ya fara karatun?" A kufule tace eh. Zeena tai shiru tana tunanin ta yanda zatai ta mata bayani. ********************* "Yinin yau gaba d'aya mafi yawan masarautar sunyisane acikin rashin dad'in rai, dan kowa da" tabon damuwarsa cikin zuciya. "Gimbiya Azeema, hajjo, Junaid, Zeena, Binta. Sai sarki daketa shirye-shiryen Neman mafita, dan" "kuwa yayi zama Na musamman da manyan fadawansa akan shirin auren Zeena da Junaid, da tu6e Zubair daga sarautar matawalle a nad'a Junaid." "Dukkan wani hukunci sun yankeshi akan auren Zeena da binta, Wanda za'a d'aurama Junaid arana" "d'aya, sannan amasa nad'in sarautar matawalle." "Fadawan dabasusan sirrin sarki Abdusslam ba mamaki yakamasu ainun, ganin ansaka bikin auren" "kusa, sannan zai tu6e d'ansa daga matsayinsa yabama Junaid rawanin bayan Zubair shine babba, shiya kamata afarama aure kafin Junaid. Basuda hurumin bin ba'asi dan haka sukai tsitt." Lalai Sarki yana da adalci. ****************** Da yammacin ranar Azeema ta nemi izinin ganin sarki Abdussalam. Kai tsaye yabada izinin shigowarta. "Kokad'an fuskarta babu walwala, sa6anin shi ta sarki dake a washe da farinciki. Koda ta zauna yai" k'ok'arin ta6ata saita janye jikinta. """Ba wannan ne yakawoniba Takawa.""" "Sarki ya dakata daga k'ok'arin ta6ata, sannan ya gyara zamansa, ""ina saurarenki""" """Na isarma Junaid da sak'onka, amma shima yazo da nasa sharad'in""." """Sharad'i kuma? Name kenan?""" """Inhar zai auri Zeena saidai ya hadasu da yarinyar da sukazo tare.""" Ta zayyane masa duk yanda sukai da Junaid. "Dukda shi Junaid yafara sanarma hakan saida zuciyarsa ta k'ara sosuwa, cikin danne yanayinsa" "yace, ""To Azeema mizai Hana mu kar6i nasa za6in, watakila akwai nasa hangen shima?""" """Wannan had'in baiminba, amma Zan amince dashi, daga baya Na d'au mataki""" """Mataki?!""" """Wane iri kenan?""" "Murmushin da tunjiya batayiba ta Saki, ta mik'e tsaye tana kallon sarki ""zakaji koma wanene anan" "gaba, dan bazan had'a zuri'a da y'ar da batada asaliba""" "Shima sarki abdussalam murmushin yayi, dan hakan yamasa dadi dari bisa d'ari. Kafin yabata" amsa harta fice. ******************** "Binta abin duniya duk ya isheta, gaba d'aya ganin Junaid yamata wahala, anbata y'ancin kanta" "amma an nisantata da yayanta, Wanda tasani tun a k'uruciya." "Shi kansa yamanta da ita gaba d'aya, hangensa ma da takeyi daga nesa yanzu ya gagareta, batada" "aiki saina kuka da zaman d'aki, ko wajen harira ma yanzu tabar zuwa tun randa Zeena ta mareta ya Junaid kuma yai halin ko in kuma da ita, ga zazzabi dake cin jikinta, abin haushi ba wanda ya damu da yanayin da take ciki." "Takanje wajen bishiyr kwanaki ta zauna taita tunani, kewar mahaifiyarta da Junaid na damunta," "wanda ayanzu haka datasan ina zata samo mahaifinta da babu abinda zai hanata guduwa garesa, wanda ya koresu ba tare da ya sake waiwayar su ba?" "Da ire-iren wad'annan tunanin take rayuwa yanzu, sune abokan hirarta a koyaushe, dan tasan" abokin hirrar nata dai yamata nisa gaba d'aya. Zeena da suka fito daga bangaren Hajiya Inna ta hango Binta a zaune ajikin bishiya kamar yadda ta saba zama wato jikin bishiya. "Tsayawa tai tana kallanta cikin takaici, da tuno abinda Junaid ya aikata mata akanta, sannan wai" da ita za'a hadasu zaman kishi? Lalai zata fuskanci wulakancin da har gwara ta hakura. A hankali ta tako zuwa inda Binta take wacce batama ganta ba tana zaune tana rubutu a kasa. "Fure ce tace ""uban me kikeyi anan kin tarewa Gimbiya hany?""" "Cikin mamaki Binta ta mike sannan ta matsa, duk hanyar can bata isheta ba sai tazo nan?" Zeena ce ta mata wani kallan banza sannan tasa kafa a inda Binta zata wuce ai kam Binta ta afka "kasa, da sauri ta dauke kafarta sannan ta girgiza kai cikin takaici tace ""kina mace amma bakya kallan hanya inkina tafiya.""" Taja dan karamin tsaki ta wuce. Binta dake yashe a kasa ta dago ta bita da kallo. "Fure ce ta kwashe da dariya tace ""Gimbiya!""" "Zeena ta hade rai tace ""menene?""" Da sauri tace bakomai. *********************** "Washe gari labarin auren yarima Junaid yafara zagaye cikin masarautar, sai dai babu" "wanda yasan wacece amaryar, sai kus-kus ake da hasashen y'ay'an manyan sarakuna dake da alak'a da masarautar." "Hakan yakuma tada hankalin hajjo, dan aganinta Zubair ya cancanci wannan auren gatan ba" "Junaid ba, gashi jiya tabuk'aci ganin mai martaba amma yak'i aminta su gana." Tarasa mi ake 6oye matane itakam. Gashi sarki yak'i cewa komai gameda auren Zeena da Sulaiman Mamakine ya kamata ganin Zeena ko kad'a bata damu da zancen auren na Junaid ba. Shiru tai tana tunani kafin tace ina Zeena? Tana ciki Hajjo. "Hajjo tace ""a kirata.""" "Zeena ce ta fito daga daki tana kwance tana hutawa, duk da dai haushi ke damunta ana zancen" "bikinta amma kwakwata Junaid ko nemanta bayayi, ita kuma tana san ganinsa amma kunya takeyi." "Hajjo ta zuba mata ido cikin zargi tace ""kinji Junaid wai zaiyi aure ko? Dazu Ramlah ke fadamun.""" "Zeena ta kalleta cikin waskewa tace ""Hmmm.""" "Ido Hajjo ta kara kura mata tace ""sai yaushe zaki fadamin me kukai keda Mahaifinki?""" "Zeena ta kalleta tace ""Hajjo!""" Hajjo tankankance ido tana kallanta. "Tasowa Zeena tai ta zo gabanta ta tsuguna ta riko hannunta, Hajjo kallanta kawai takeyi tace" """Hajjo ki barni na auri Ya Junaid dan Allah, ni banga namijin dayamin ba irinshi.""" "Hannunta Hajjo ta zare da sauri tace ""me kike nufi?""" "Zeena tai shiru kafin tace ""nice!""" Kece? Kece wa? "Da karfi ta fadi hakan wanda yasa hankalin Zeena ya tashi, Hajjo ta tureta ta fito daga falanta." Bangaren Azeema ta nufa cikin hanzari. Inba da dalili ba Hajjo bata taba zuwa bangaren kowa sai dai ta aika azo. Kafin Barira ta mata iso harta fada ciki. "Azeema dake zaune tana nazarin abubuwan dake faruwa kawai taga Hajjo a tsakiyar falan ta," "cikin mamaki ta kalleta tace ""Hajjo?""" "Hajjo cikin bacin rai tace ""wani munafurcin kuke shirin yi ke da Takawa?""" "Kallan gadara Azeema ta mata sannan tace ""koma me muke hadawa mijinki ne ai, bakya tunanin" "shi ya kamata ya sanar miki koma wani irin munafurci ne""" "Hajjo ta kara kufula tace ""kina tunanin hada Zeena da Junaid aure saboda ku amshi mulki kin" "dauka ban san me kike shirin yi ba?""" "Wani lalausan murmushi Azeema ta saki sannan tace ""sai Junaid ya auri Zeena ne zai amshi" "halak dinsa?""" Halak? "Cikin kufula Hajjo ta tambaya, Azeema tace ""ba Halak dinsa bane?""" Mene? "Hajjo ta fara huci, Azeema tai murmushi tace ""Ni yanzu banasan jan magana tsakanina dake a" "matsayin mu na sirikai.""" "Gaba daya ran Hajjo ya gama baci, takai bango makura, a zuciye ta juya tai waje." "Azeema tai tsaki tace ""ko wayake san yar taki?" ********* Bangaren Abdulsalam ta nufa a zuciye. "Yana zaune suna tattauna abinda suka tsara shi da Hakimi, Hajjo ta iso, Jakadiya da sauri ta" "matso tace ""Hajjo.""" "Daurewa tai tadan saita nutsuwarta, tace ""yimin iso.""" Da sauri Zagi ya fara sanar da isowarta. "Abdulsalam ya kalli Hakimi yace ""kaje zan nemi ka.""" Nan ya mike yai musu sallama. Hajjo ce ta shigo rai bace. Zama tai sannan ta kalleshi. "Gani tai fuskarsa a murtuke daurewa tai tace ""Yanzu abinda akamin an kyautamij?""" Name kenan? "Tace "" yanzu taya zaka hada auren Junaid da Zeena? Sannan bada sanina ba?""" """To yanzu kin sani ai? Sannan yarki bata sanar dake ba?""" "Kallansa tai rai a bace, yacigaba ""itace take sanshi kinsan yanda akai na shawo kansa ne? Ko kuwa tijara zakimin?""" Shiru tai tana kallanshi cikin takaici. "Yace ""idan har baki amince da auren nan ba to tabbas ko me yaje ya dawo bazan taba shiga" "zancen 'ya'yanki ba.""" Ya mike yai ciki ba tare da ta tofa kofa komai ba. Hajjo kamar tasa ihu yanzu haka zata bari komai ya faru ba tare da tayi wani abin. Haka ta fito jiki a sanyaye. ******* "Zan iya cewa babu wani farin ciki gaduk 6angarorin ma'auratan, idan kacire sarki kawai. Sai dai" kowa yana dannewa wajen 6oye k'in auren "A 6angaren Junaid kam yana farin cikin kusantowar binta gareshi, yayinda wani sashe na zuciyarsa" "yake takaicin auren Zeena, amma kokad'an baya nuna hakan, saima farin cikinsa dayake, ko baccinya kwanta wani irin dadi yakeji akan zai dawo da Binta kusa dashi. Ko yayarsa Safiyya datazo tana nuna takaicinta da duk aurarrakin nasa nuna mata yayi duk za6insane." "Hajiya Inna ma tayi fada sosai, sai dai data kira Junaid shi yace mata shi ya zabi hakan." Hakan yasa bata iya kara cewa komai ba....... "Zancen auren Junaid da Zeena yazo har kunan Binta, ranar tayi koka sannan ta san zamanta anan" "ya kare, dole zata tafi koda kuwa batasan inda zata nufa ba." *** *ZAFIN RANA* ...................... *H̝a̝ s̝ k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝ s̝ o̝ c̝ i̝a̝ t̝i̝o̝ n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ* {31} "Hajjo sai safa da marwa take a cikin dakinta, Zeena na zaune a kasa tana bin kafafunta da kallo." "Hajjo can ta juyo ta kalleta tace ""da wacece?""" "Zeena ta kalleta tace ""watace da suka taho tare, amma ya akai kika sani?""" "Cikin kufula Hajjo tace ""Banza shashasha, wannan wannan wlh kinfi Zubair dodadiyar kwakwalwa, banda hauka da jakanta har yaushe kika fara san Junaid da zaki yadda ya miki kishiya tun kafin ya aureki? Nasan dai a matsayinsa na yarima dole ne bazai zauna da mace daya ba amma a" "kalla ke ki shiga ki haihu tukunna mana.""" "Zeena tai shiru a ranta tace ""nima ce miki akai ina san" "hakan?""" "Hajjo kamar ta zuba mata duka takeji tace ""sa a kiran" "yarinyar na ganta.""" """Ki ganta kiyi me?""" Kin wuce ko sai na kifa miki mari? Zeena ta mike rai a bace tana 'yan kunkuninta. "Fure ta aika tace ""jeki kira Binta, karki bari Umma karama" "ta ganki.""" "Fure tace ""Gimbiya ina na isa shiga bangaren. """ "Kafarta ta saka ta taka tata kafar, yar kara Fure tai sannan tace ""Angama Gimbiya.""" Da sauri ta juya ta fita. Fure tayi sa'a taga kawarta wacce take aiki a bangarn Azeema nan ta turata ta kira Binta. Binta dake sa kaya ta fito da wanka da kyar saboda "zazzabin dake cikin ta ne ta kalleta sannan tace ""gatanan zuwa.""" Rigarta ta saka sannan suka fito tare. Hajjo tayi shiru tana tunanin munafurcin da aka kulla tsakanin Azeema da Sarki dan tasan wlh tabbas akwai dalilin dayasa Azeema ta yarda da hadin nan. "Shigowar Zeena ne yasa ta kalleta, Zeena tace ""gata a" "waje.""" Hajjo ta fito cikin falanta tasa Binta ta shigo. "A hankali Binta ta shigo ta zube kasa tana gaisheta, Hajjo bata amsa ba sai dai ta zuba mata ido tana kallanta kallan kurula, Binta kam gabanta sai faduwa yakeyi hakan yasa ta" kasa dagowa. Ke! "Hajjo ta kirata da haka, Binta ta dago a hankali, fadamin wanene mahaifinki?" "Binta a hankali cikin faduwar gaba tace "" tun ina karama" "ya koremu bansan inda yake ba.""" Mene? Binta ta kalleta ta kasa amsawa saboda hawaye dake neman zubo mata. Uwarki fa? "Zeena ta kalli Hajjo da sauri, Binta ce ta goge hawayenta" "tace ""ta rasu.""" Ha ha ha. ta rasu? Binta bakinta na rawa tace lalai ya nuna mana halin rashin "tarbiyya daya samu ta iyaye, ya rasa wanda zai hadaki kishi da ita sai wannan abar?""" Binta wacce kanta ke sarawa ta kasa gane me suke nufi. Zeena cikin jin haushi ta zuba mata ido tana harara. Fita daga nan. "Hajjo ta fada, Binta ta mike da kyar ta fito." "Da sauri Zeena tasha gabanta, ta kalleta tana huci tace ""kiyi gaggawar sanar da Ya Junaid bazaki aureshi ba, ko ki" "hada shirgin tsumokaranki ki bar gidan nan.""" Zan bar gidan nan in har Ya Junaid yace na........ "Marin da aka wanka mata ne yasa ta gigice, ta kalli Zeena a" ranta tace sau nawa kenan? "Zeena ta kara kifa mata wani, zata kara mata Hajjo ta ce" """Ke.""" "Hannunta ta sauke a zuciye, sannan ta dawo ciki." Binta a hankali ta bar bangaren kanta na cigaba da sarawa. Gun Hari ta nufa dan neman magani saboda azabar datakeji. *********** "Mikewa Junaid yai bayan ya gama nazarin da yakeyi a cikin kansa, daki ya shiga yai shiga irin ta alfarma, fitowa yai daga sashensa." "Azi da sauri ya taso yace ""Ranka ya dade zaka wani gurin" "ne?""" Eh ina san ganin Umma ne. "Da sauri yace ""To ranka ya dade.""" "Harira ce ta nufo inda yake da sauri, ta zube ta gaisheshi sannan tace ""Yarima!""" "Kallanta yai yace ""Hari ya akai?""" "Shiru tai sannan ta kalleshi tace ""Binta a gurina ta kwana" "jiya.""" Oh! "Harira tace ""sai dai yau dana tashi na ji jikinta da zafi sosai da alama ta dade bata jin dadi.""" "Hankalin Junaid ne ya tashi dan duk yanda yaso karya boye damuwarsa sai da abin yaci tura yace ""bangane ba?"" Tace "" tunda ta shigo take kuka shiyasa nima bansan" "abinda ya sameta ba, nadai san tace daga gun Hajjo take." Cikin hanzari ya nufi inda take. "Tana kwance cikin bargo tana rawar sanyi, kusa da ita yaje ya zauna, su kuma suka bar dakin." "Ido ya zuba mata zuciyarsa na tafasa da bacin rai, cikin dakewar zuci yace ""saura kadan Binta, saura kadan, na dau alkawarin rama duk wulakancin da aka miki, ki kara" "daurewa, mun kusa zuwa gurin.""" "Tana jin kalamansa sai dai ta kasa ko bude idanunta, sai hawaye da suka gangaro ta gefen idanta wanda ya sa ya" fahimci cewa idanta biyu. "Mikewa yai ya fito, ya kalli Azi yace ""bangaren Hajjo.""" "Da sauri Azi ya matso yace ""da kace. """ Kallan da Junaid yamai ne yasa shi yin shiru. "Hajjo na zaune ita da Zeena da Zubair da Ramlatu, sua mitar abinda ke faruwa." "Zeena dai tana jinsu amma ita tace sai Junaid, Zubair ne" "ya kalli Hajjo yace ""Hajjo nifa nasan Allah akwai abinda Abba yake shiryawa.""" "Hajjo ta kalleshi tace ""koma me yake mulki naka ne sai dai" bayan raina a kwace. "Isowar Junaid aka sanar cikin mamaki tace ""Junaid?""" "Zeena ce ta mike da sauri zatai hanyar kofa, Hajjo tace" """gidan ubanwa zaki?""" "Juyowa tai tace ""Yaya ne yazo ganina.""" Yazo ganinki? To ko ganinki yazo sai ki tashi kamar jela? Wai ni yaushe kika koma mara aji ne? Zeena ta dawo cikin bacin rai ta zauna. Junaid ne ya shigo. Sai daya kalli kowa a gun sannan ya zauna ya gaida Hajjo. "Hajjo ta amsa tace ""meya kawo sirikina nan?""" "Siriki? Ya maimaita hakan a ransa, amma a fili murmushi" "yai yace ""zuwanai nai wata sanarwa.""" "Sanarwa? Hajjo ta kalleshi fuska a sake, Allah yasa muji" alkairi to. Cikin salo na kasaita da aji ya dago ya kalleta tare da cewa """ ni a matsayin danki nake kema, inaso a koda yaushe a dinga daraja abin da yake mallakina.""" "Cikin rashin fahimta ta kalleshi, yace ""shikadai nazo sanarwa, dan ina tsoron abinda zai faru in aka cigaba da wulakanta min abu na.""" "Ya mike yai sallama ya fita, gaba daya Hajjo ta kasa gane" "me yake nufi, kallan Zubair tai tace ""me yake cewa?""" Zubair ya girgiza kai alamar baisani ba. "Zeena kam ido ta zubamai har ya fita, wani murmushi ne" "ya bayyana a fuskarta tace ""Hajjo dan Allah ya Junaid bai hadu dayawa ba?""" "Kobi takanta batai ba Hajjo ta kalli Ramlatu tace ""kinsan" "me yake cewa?""" "Ramlatu ta kalleta tace ""Hajjo magana fa ya yaba miki" "akan abinda kikace kinyiwa Binta.""" Shiru Hajjo tai ta tattaro kalamansa sannan ta fahimta. "Hucci ta fara yi kai kace kumurci, Ramlatu ta girgiza kai tace ""Hajjo sai dai kiyi hakuri amma Junaid yafi karfin" "Yarima Zubair."" Tuba nake da fadan haka." "Mikewa tai tana huci tai dakinta, da karfi ta bugo kofar" wanda sai daya razana su. "Bangaren Azeema ya nufa, tana zaune tana sanarda Safiya" "abubuwan da za'a bukata na biki, Junaid ya shigo." "Cikin nuna jin dadi ta kalleshi tace ""anjima nake tunanin a" "kiraka mu tattauna.""" "Kallanta yai yai dan murmushin yake sannan yace ""Umma na gode da kula da 'yar can da kikai, da amincewa da ita a" "matsayin surukarki da kikai.""" "Azeema jikinta yai sanyi, ji tai bata kyautawa Binta, jin" kalamansa yasa tasan tini yake mata a fakaici. Insha Allahu za'a gyara Junaid. Godiya nake Ummana. "Kallansa tai gaba daya sai jikinta yai sanyi, Safiyya tace ""Junaid tunda ta amince zaka aureta ai tayi kokari, ni kaina nayi mamakin hakan.""" "Junaid yai murmushi yace ""Ai Umma mai san abinda nake" "so ce ni na san hakan.""" Azeema tai shiru dana sani da jin haushin kanta ya kamata...... ********* Lokaci ya karato "A 6angarrn su Zeena kam itadai tana cikin murnarta, duk kuwa da tanajin zafin hadin zama da binta, ganin bintar ma ya gagareta gaba d'aya, dan hajjo gaba d'aya ta hanata zuwa sashen Azeema, amma hanata fita gaba d'aya, kullum tana sashensu Ana mata gyaran jiki irin Na y'an gatan Amare, shi kansa mai gayya mai aikin ya Junaida ganinsa" yamata wahala. **************** "Binta kam ta dawo bangaren Azeema, sai dai a yanzu taga" "canji sosai, dan Azeema da kanta ta sanar da ita auren da" za'a hadata da Junaid sannan ta nemi ta kular mata da danta bayan auransu. "Duk da a kasan ran Azeema bawai san Binta take ba sai dai a yanzu tasan ita kadaice mafitarta, dan tasan Zeena ta Hajjo ce dole ne ta kama Binta kafin danta ya zama dan" kallo a gareta. ******* "Da wannan aka shiga hidimar biki, ranar laraba akayi" "kamun daya k'ayatar ainun, Zeena kuma kawai akaimawa banda binta, hadalima bata lek'o wajenba." "Hakan yabama Junaid haushi, yarasa mikuma ake 6oyewa game da bintar, tunda sun aminta ya aureta shi baiga wani" abun 6oye-6oye ba kuma. Dukda mutanen dake cike da sashen Azeema haka yanemi ganinta. """Barira ki sanar masa zanzo sashensa cna damesa, dan" "babu ta inda zai iya shigowa nan""." """To ranki ya dad'e." Barira tazo ta sanarma Azi amsar Azeema. Shima yaje ya sanarma Junaid dake zaune a falonsa yana nazarin wani littafi "Ba tare da ya kalli Azi ba yace, ""babu damuwa""." Tashi Azi yai yafita. ************** "Bayan sallar isha'i Azeema ta iso sashen Junaid, a falo ta iskeshi kwance ido a lumshe, sai dai da alama ba barci" "yakeba, dan yana d'an kad'a k'afarsa." "Sallamarta ta sakashi bud'e idanunsa, sannan ya mik'e zaune sosai. Zama tayi kan babban tum-tum da aka" k'awata kwalliyar falon dasu. """Junaid lafiya kuwa ka buk'aci ganina?""." """Lafiya lau Ummana, barka da dare?""." """Barka dai, ya hidima?""." """Umma kuza'a tambaya ai, ni wace hidima nake?"" Yak'are" naganar da murmushi. Itama murmushin tamasa. "A nutse yafara magana ""Ummana wai Yaya tsarin bikin" "nan yake?""." """Ban fahimci tambayar takaba?""." "'Dan jimm yay yana tunani, saikuma ya sauke numfashi yana gyara zama, ""Ummana ina nufin yau kamu Zeena kawai Na gani, kina ganin bayan an d'aura auren mutane suka fahimci ba Zeena ce kawaiba bazasu kalli adalcin wannan masarautar a matsayin mai rauni ba? Hakan kuma tamkar rage darajane, duk mai mulki bazai yisaba saida talaka, Yaya muke tunani idan talakawan suka fahimci mun fifita kanmu sama da su? Anya bazasuji kamar bamu" "dace muzama masu mulkarsuba?""....." "Jin yayi shiru sai Azeema ta sauke ajiyar zuciya, lallai" "gaskiya Junaid ya fad'a, kuma tagane tayi kuskuren barin jama'a su fahimci sirrinta a wanan Karon...." """Anyi kuskure Junaid, amma namaka ank'awarin ganin" "gyara a safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu""." "Murmushi yamata yana kamo hannunta ""nagode Ummana mai share kukana da fahimtar abinda ya cancanta cikin" "sauk'i""." "Murmushi jin dad'in yabon nasa ta Saki, takai hannu taja" hanccinsa batareda tace komaiba. Sun d'an kuma tattauna abinda ya dace dasu kafin tamasa sallama ta koma. ********** "Bangarenshi aka gyara sosai saboda girmansa, daga ciki" aka tashi su Harira nan ma aka kara budashi. Babban shashin mai kunshe da manyan bangare da girma da tsari shine na Zeena. "Binta kuma aka bude bangaren su Hari aka kara girmanshi aka mata nata bangaren, su koma su hari aka maidasu can" baya. "Guri yayi kyau da tsari duk kuwa da cewa bangaren Zeena yafi kyau, amma Junaid ko damunsa hakan baiyi ba......." ********* Abdulsalam kam nata bashi shirin naba Junaid matsayin "Galadima, bayan anyi aure......." * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {32} "A daren ran da akai kamun Zeena, Azeema ta kira Binta tasa Barira tai mata gyaran jikin dan taji" kunya sosai da Junaid ya mata magana da kanshi. "Haka Barira da Safiya suka gyara Binta wacce gaba daya ta tabbatar rashin gata ne ya mata yawa," yanzu ace za’ai bikinta har yau Junaid baice mata komai ba? Tun randa yazo gunta tana kwance agun Harira har yau ganinsa ma sai dai daga nesa. "Haka dai take daurewa dan tasan duk duniya batada kowa banda Junaid, sannan kuma tasan ba" mantawa yai da ita ba tunda har zai aureta. ******** "Zeena na kwance ana murza mata hadin gyaran fata Hajjo ta shigo, kallanta tai tace “ni Zeena" kun taba zance da Junaid?” Gaban Zeena ne ya fadi ta kalleta tace “sau nawa kuma?” Hajjo tace “ni fa gaba daya gani nake kece kikesan abin nan ba shi ba.” "Zeena ta juyo tace “Hajjo ni dai ni nace naji na gani, ke makwan kiyi murna ma ‘yarki zatai" aure a inda kike amma sai kawo maganganu kikeyi.” Hajjo ta juya ta fita batace komai ba. Shiru tai a falo ta kalli Ramlatu tace “me kike gani?” Ramlatu tace “me zai hana kiyi taro na biki randa aka daura auren? Ki gayyaceshi mutane zasu ga "yana santa, hakan zaisa adaina yada cewar itace takeso, sannan inba damuwa ki gayyaci waccen" "kucakar, ki kaskantar da ita.”" "Hajjo ta jinjina kai cikin gamsuwa tace “Hakan yayi, yanzu ki fara shirye shirye, zan sa a kira" Shamaki na sanar dashi.” Da sauri tace to. ********** "A hankali jiki na rawa ta bude mayafin dake lulube agun, zube wa tai kasa da sauri jikinta na" "kakkarwa, a zabure ta bude idanunta dama tasan mafarki ne, a hankali ta kwantar da kanta jikin gado tare da sakin ajiyar zuciya." Jin ana kwankwasawa ne yasa tace “waye?” Ta miki jiki a sanyeye. Daga waje Barira tace “Gimbiya kin farka?” Azeema tace “eh.” "A hankali Barira ta bude kofar, sannan ta zube ta gaisheta tare da cewa “Gimbiya dama Hajjo ce tace “yau bayan an daura aure da yamma akwai taron data shirya.”" Azeema tace “taro?” Eh. Shiru tai tana nazari dan ta tabbatar akwai abinda yake a kasa. “Da wani abin ne?” Azeema ta tambaya ganin Barira bata mike ba. Tace wai harda Binta. Azeema tace “Hajjo me kike shiryawa?” ******* "Yau karfe 1 na rana aka dauka auren Junaid da Zeena, sannan aka daura auren Junaid da Binta." Akuma gun ne Sarki yai ma Junaid albishir na bashi sarautar Galadanci. Gaba daya ido aka zubo masa. "Junaid wanda yasha ado iya ado yana sanye da wata dakakiyar shadda fara, yasha babban riga da" "rawani, kana ganinsa kaga ango." Kallan Sarki yai yace “Nagode amma Mai Martaba wannan sarautar bata Zubair bace?” "Sarki yai murmushi yace “Tashi ce amma na fahimci yana bukatar hutu, kaine ya kamata ka" wakilceshi shi ya samu ya nutsu yai karatu.” Junaid yai kasa dakai yana nazarin wannan abin dake faruwa. "Zubair dake gefe ya cika ya batse sosai, kallo daya zaka mai kasan lalai an bakantamai rai." "Junaid ne ya daure ya dago ya kalli Sarki, fuskarsa bazaka taba ganene me yake cikin ransa ba." "Murmushi ya saki sannan ya kalli Zubair yace “Tuba nake Yarima, nayi laifi.”" "Zubair ya kalleshi, dan sam ba wanda yai tsammanin jin haka, kallan mutanen gun yai ya kasa" "danne bakin cikinsa, yace “bakomai.”" Yanda yai maganar ne yasa kowa ya fahimci ransa ya baci matuka. Junaid ya kalli Sarki yace “Ban isa bijirewa umarnin sarki ba sai dai inaso sarki ya duba rashin jin dadin hakan da Yarima Zubair yaji.” Wato dan ya nunawa mutane Zubair na bakin ciki shi yasa ya fara mai magana kenan? Nan Sarki ya kara tabbatar lalai Junaid inbaiyo wasa ba sai ya wargazasu. Daurewa yai ya kalli Zubair yana murmushi yace “Zubair!” Zubair yai kasa dakai da sauri yace “tuba nake ranka ya dade bawai ban amince bane.” To yanzu fa? Da sauri yace “Na amince Allah ya tayashi riko.” Junaid ya kalli Sarki kadan. "Fitowa sukai aka fara tayashi murna, sannan aka kunce rawaninsa aka mai wani na bashi" Galadima da akai. Nan aka shiga busa. Hajjo na ta bada umarnin taron da za’ai aka shigo mata da wannan bakin labarin. "Ranta yakai kololuwa gun bacci, har ta sabi alkyabba zata fita Zubair ya shigo." Cikin kumburim fuska tace “dan hauka kana zaune aka kwace mulkin ka aka ba waccen yaran?” Zubair kamar zaiyi kuka yace “ya zanyi Hajjo cikin mutane fa Abba ya sanar da hakan.” Hajjo ta fara hucci na takaici tace “haka zamu zauna har babban mulkin ma ya kwace kenan?” "Zubair yace “bazai taba yiwuwa ba wannan, yanzu ki barshi in ma munyi fadan mu za’awa" dariya.” Hajjo ranta ya kara bacci ta zauna tana nazari......... ********* "Kasancewar Azeema tasan abinda Abdulsalam yake shirin yi shiyasa ko mamaki batai ba, haka suka cigaba da hidima da mutane." Binta na can bangaren Junaid na da sanda yana yaro saboda gaba daya bangaren Azeema a ciki yake. Da yamma kowa ya fara shirin zuwa taron da Hajjo ta shirya. Binta ce ta kalli Safiya wacce ta mika mata kaya tace “muje ki shirya.” "Cikin mamaki Binta ta kalli kayan, Safiya tai murmushi tace “ke matar Junaid ce yanzu dan haka martabarshi itace taki.”" "Haka suka shiga daki da kanta Safiya ta shiryata, mutane sai gulma suke akan Junaid ya auri" "yarinyar dayazo da ita, wasu suce wacce take kwana a bangarensa da." "Ba karamin kyau Binta tai ba, dan ita kanta batasan tana da kyau haka ba sai yau." "Tayi kyau sosai, atamfashi ta saka mai kyau, sannan aka daura mata alkyabba ruwan kasa tayi kyau sosai da sosai, gashi tasha turaren wuta na tsugunno." "Safoya ta shigo ta sanarda Azeema akan angama shirya Binta, tace “to sai kum dawo.”" Cikin mamaki Safiya tace “bazaki ba?” "“Eh, banajin dadi.” Safiya tace to." Barira ta kalla tace “jeki duba ki ga ko Junaid ya shirya.” Nan Barira ta fita. "Junaid na zaune a kasan falansa yana nazarin bashi sarautar nan da akai, wajen bangarensa kuwa maroka ne keta kiraki, Azi ta samu tace “Yarima ya tafi?”" Ina kenan? Tace “taran da Hajjo zatai mana.” "“Oh, bansani ba bari na duba.”" Tace “to dan ita Binta har ta shirya.” "Azi ya shiga, ganin Junaid a zaune yasa yace “Yarima baka shirya ba?”" Junaid ya kalleshi yace “banajin zani.” Azi yace “to shikenan dan dama Barirace ke tambaya wai Binta ta shirya.” Binta? Ya tambaya cikin mamaki. Azi yace eh. Junaid yace “bari na shirya muje.” Murmushi Azi yai sannan yace to. "Daki ya shiga ya cire shaddar nan yasa wata shaddar, haka kawai ya jawo shadda mai ruwan kasa" ya saka. Yayi kyau sosai dan dama Junaid akwai zagi da haiba. "Cikin isa da takama ya fito daga bangarensa, maroka nata kirari." Dokin da Azi ya fito dashi yahau suka nufi gun taran. ********** "Katan gun taro na masarautar suka nufa, am gyarashi sosai, mutane sun cika agun, da alama har" an fara gabatar da shagalin. Isowar Junaid ne yasa aka bashi hanya kowa ya shiga kallansa. "Junaid ya sauko daga kan doki sannan ya nufi ciki, Azi da sauran hadimansa na take mai baya." "Zeena na zaune cikin shiga ta alfarmar gaske, wanda kudin da aka kashe gun shirya ta ma ba" kadan bane. "Tana zaune akan wata had’ad’iyar kujerar mulki, tayi kyau iya haduwa." Dauke kansa yai daga kanta sannan ya duba inda zsi hango Binta. Bai ganta ba hakan yasa ya fara sa kafa cikin gun yana dan amsa gaisuwar da ake mai. "Me zai gani? Daga kasan Zeena ya hango binta zaune kan tabarma, Safiya na tsaye itama ranta" da alama ya sosu. Hajjo wacce ta shirya wannan wulakancin ce takalleshi tace “barka da zuwa Ango.” Kallanta yai sannan yai murmushi yace “barka dai Hajjo.” "Kusa da Zeena ta nuna mai ya zauna, ya kalleta sannan ya kalli Zeena yace “Ayya Hajjo bayana" "ciwo yake banajin zama akan kujera, kasa nakeso.”" Kasa? Cikin mamaki ta tambayeshi a hankali. Yace “eh.” Kallan manyan mutanem data gayyata tai sannan tace “Junaid ka daure ka zauna akan kujera saboda mutane.” "Mutane? Ya za’ayi? Yanzu kuma naji ma zaman kasan bazan iya ba, komawa nake san yi.”" Ido Hajjo t zaro tace “komawa?” Yace”eh Hajjo ni na kawo kaina kuma inada ikon komawa.” Zeena wacce ta zuba musu ido tana san sanin me suke tattauna wa haka. Hajjo tace “ni matsayin mahaifiyarka nake kuma na umarceka daka wuce ka zauna.” Yace “to Hajjo zan zauna.” "Yana fadin haka ya fara takawa, murmushi Zeena ta saki cikin jin dadi, kallansa tai cikin so tana" jin wani dadh na ratsata. Har yakai jikin kujerar ta kawai ya karasa kan tabarmar da Binta ke kai ya zauna. "Ido aka zubamai, kowa ya saki baki, balle da akaga kayansu iri daya." "Zeena gaba daya jitai kanta ya kulle, Hajjo kam kasa ko motsi tai." A hankali Binta tace “yaya me kake anan?” Kusa da kunnenta ya matso cikin rada yace “na jure ganin ana wulakantaki ne dan ba yanda "zanyi, yanzu kuwa ke matata ce bazan iya jure ganin ana taba min ke ba, ko wanene kuwa.”" "Murmushi ta saki wanda gaba daya idan mutane na kansu, Safiya kam tama rasa me zatai, lalai" wato Azeema tasan akwai abinda zai faru shiyasa batazo ba. Tab * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {33} "Gaba daya Hajjo kallan mutanen gun ta shiga yi wanda suke gulma da zunden abinda ke faruwa," Zeena kam hawaye ne taji ya zubo mata ta zubawa Junaid ido wanda ko kallanta baiyi ba. Hajjo ta kalli Zeena wacce kana ganinta kasan tana cikin tsananin kunci. "Safiya ta daure ta kalli Junaid tace “ya isa haka nan, bari zan maida Binta ka zauna ku rabu lfy, ka gama wulakantasu wannan ma ya isa.”" "Binta ta kalleshi tace “ni zan koma yaya, kayi hakuri.”" "Mikewa tai Junaid yabita da kallo suka bar gun, Ramlatu ce tasa dariya tace “masha Allah, dama mun shirya haka ne dan kowa ya gane wacece Amaryar, yanzu tunda kun ganta shiyasa ta tafi," taran dama na Yarima Junaid ne da Gimbiya Zeena.” Junaid ya mike ya zaune kuda da Zeena fuskarsa a hade tam kai bakace shine dazu yake rada ba. "Zeena kam gaba daya komai ya fita a kanta, duk kwanakin data dauka tanw gyaran jikinta dan ta" "farantamai, a haka ta kare?" Junaid baiyo minti goma a zaune ba ya kalli Hajjo yace “in ba laifi zan koma.” Kallansa tai cikin kufula tace “banda wulakancin da ka mana wani kake neman sakewa?” Zeena ya kalla yace “baso kike mu tashi ba?” "Kallan Hajjo tai tace “Hajjo zamuyi magna ne, ku karasa.”" "Hajjo zata sake magana Zeena ta mike, Junaid ya mike suka bar gun a tare." Suna fita daga gun ta kalleshi idanunta a raunane tace “nagode da toxartani dakai a cikin mutane.” "Cikin kasaita ya kalleta kamar zaiyi magana kawai ya fara tafiya, da kallo ta bishi idanunta suka ciciko." Fure ce ta matso da sauri tace “Gimbiya karki bata kwalliyarki ” Waska mata mari tai cikin sauke jin haushi ta tace “kwalliyar uban me?” "Ta juya ta fara tafiya, dakinta ta shiga tana shiga ta rufe kofa cikin tsananin kunar rai." "Junaid kam bangaren Azeema ya wuce daga gun da yake, tana zaune cikin tsirarin mutanen da" "basu je ba, ana yi mai iso suka fara guda da kiranshi Ango kasha kamshi, kamshin ma har guda biyu." "Junaid ya gaishesu ya wuce ciki, Azeema ta mike ta bi bayansa." "Yana zaune a kasa a dakinta ta shiga, zama tai akan kujerar dake gabansa tace “harkun dawo?”" "Ido ya zuba mata bai ce komai ba, tace “menene?”" Shiru yai wanda ya da hankalinta yadan tashi sai gani tai ya saki murmushi yace “kawai ina mamakin meya hana Ummana zuwa gun taron nan ne.” "Kallansa tai tana nazarinsa, sannan tace “banadan jin dadi ne shi yasa.”" Kai ya jinjina a hankali cikin alamar gamsuwa yace “ayya! Na tabbatar Ummana bazataki zuwa gun ba haka kawai bayan tasan za’a wulakanta mata surukar ta wanda danta ke so ba.” "Gaban Azeema ne ya fadi, ta kalleshi sannan ta kakaro murmushi tai sai dai bata tofa komai ba." "Mikewa yai ya mata sallama ya fita, idanunta ta runtse." Junaid na fita yai kofar baya inda ta sadashi da inda Binta take zaune. "Tana kwance a daki, ya shiga falan, ganin bakowa ya bude kofar dakin a hankali, tana kwance idanunta na zubar da kwalla." "Tuno sanda suka isa gun tai, Ramlatu ta nuna mata tabarma akan ta zauna anan bayan ko bakin" gun kowa a kan kujera yake. "Junaid ne ya tako a hankali, jin motsi yasa tai saurin goge hawayenta ta dago dan ganin waye." "Junaid ne ya tsaya a inda yake kusa da gadan, ya sakar mata wani lallausan murmushi." Itama murmushin ta maidamai idanunta na kara neman ciko kwalla. "Karasowa yai a hankali jikin gadan ya zauna, kallansa tai tace “yaushe kazo?”" "Hannu yasa a hankali kan fuskarta yana dan murza hannun a hankali, sannan ya jawota jikinsa ya" rungume. "Shiru suka danyi a hankali yace “kiyi hakuri Binta, na kawoki inda ba’asan darajar ki ba, sai dai" daga yanzu bazan sake bari wani yacimin zarafinki ba.” "A hankali tace “bakomai Yaya, barina da akai na cigaba da zama kusa dakai ya isheni.”" "A hankali ya dagota yace “nagode Binta, a koda yaushe ina alfahari da kasancewarki tare dani.”" "Tace “nice da godiya yaya, ka ceci rayuwata dana mahaifiyata ka kuma kula dani kamar yar" gata.” "Murmushi ya sake mata cikin tausayinta ya sake rungumeta, kafin ya saketa yace “inaso ki san" "kome zai faru daga yanzu Junaid na dauke da Binta a cikin ransa, sannan kome Junaid yakeyi bazai" taba mantawa da ita ba.” Kai ta daga alamar fahimta sannan tace “to Ya Junaid.” Ni ynzu mijinki ne haka za’a cigaba da cemin Yaya? "Kasa dakai tai tana murmushin kunya, yace “ba’a san nazo nan ba zan wuce.”" Kai t daga alamar to sannan tace “Nagode Ya Junaid.” Sai kin iso. Kai tai da kanta cikin kunya "Mikewa yai ya fita, haryakai kofa ya sake juyowa ya kalleta sannan ya fita." Ta baya ya fita. ***** Hajjo cikin takaici ta nufi dakin Zeena ranta a bace matuka. Tana shiga tace “A haka kike sansa har kika nemi auransa bada amincewa ta ba?” "Zeena dake kwance ta mike zaune tace “Hajjo dan Allah ki barni da abinda ke damuna, duk ba ke" "kikaja ba, da baki gayyaceta ba hakan zai faru ne? Ko da baki sata a kasa ba hakan zai faru?”" “Wato laifin nawa ne kenan? Sanda na fada miki abinda zanyi ba dadi kikaji ba?” Zeena cikin masifa tace “to yanzu waye ya wulakanta?” Kin rufemin baki ko sai na fasashi? Waye yace kice kina san wanda baya sanki? Ai mace in tanada tunani gwara ta auri wanda bataso yake san akan ta auri wanda takeso baya santa.” "Zeena ta turo baki ta kwanta, kin tashi kin shirya ko sai ranki ya baci?" Zeena tana jinta batace komai ba dan bakin ciki. Hajjo cikin bacin rai ta fita. Dakinta ta shiga ta kalli Zubair dake jiranta tace “kai kuma ya akai?” "Yace “Hajjo gaskiya kima Abba magana ya bani wani mulkin, sam bazan iya zama banda komai ba." "Ka tashi ka bar nan ko sai ranka ya baci, ni wai meyasa gaba daya kuke nema ku kasheni da bakin" "ciki saboda waccen yaran? Kanwarka ta aureshi kai kuma ka bari ya kwace abinda yake naka, sannan yanzu kazo kana min wani zance daban?" Zubair ya mike ya fita rai a bace. Yana fita Hajjo ta da hannu akanta dake sarawa. ******** "Azeema da kanta ta shirya Binta dan tabbas taji kunyar abinda ta aikata, sannan ta fahimci Junaid" yasan da saninta. Safiya da Barira suka taimaka mata aka shiryata. "Sanye take cikin atamfa tayi kyau sosai, dan Azeema duk kayan lefen da sukai dinka mata su tai" saboda rashin kayan sawar ta. "Lefe ma haka aka kaima Zeena ukun na Binta, sai dai Junaid bai tanka ba." "Binta tayi kyau sosai, Azeema ta mika mata kofi cike da madara tace ta shanye." Binta ta shanye sannan Azeema ta kalleta tace “Binta!” Binta a hankali tace “Naam” "Azeem tace “kiyi hakuri abubuwan dana aikata miki, sannan inaso kisan zaman masarauta bazai taba yiwuwa da hali irin naki ba.”" "Kallanta Binta tai cikin rashin fahimta, Azeema tacigaba “dolene ki san kanki, ki kuma zama mai" san kanki.” "Bata gane me take nufi ba, Azeema tace “Duk sanda kikaga bazaki dauki abinda ake miki ba ki" "tuno kalaman nan lokacin zaki fahimta, sannan a kods yaushe ki zama mai amfani da damarki.”" "A hankali Binta tace“Nagode Gimbiya, nasan dalilinki na rashin sona wanda ko wanene bazai so" "wacce ba’a san iyayenta bama, sai dai a koda yaushe ina miki godiya a raina nakin korata da kikai, balle harkika barni na auri Yaya, nagode sosai.”" "Jikin Azeema ne ya kara sanyi, ta kalli su Safiya tace “in lokaci yayi ankai Zeena sai ku kaita.”" Tace “to.” ******** "“Kin zama matar Junaid daga wannan rana, dan haka a koda yaushe ki zama mai kama kai da kuma kula da mijinki, sannan duk sanda kika ga mijinki yayi abinda bai dace ba ki zama mai kokarin nuna masa.” Sarki ya kalleta bayan yazo nan a ransa yace “Allah yasa sadaukarwa da" auranku danai ya biya mun bukatata.” Zeena tai godiya sannan tai sallama suka fito. "Hajjo zamu wuce, abinda Zeena ke fada kenan a jikin kofar dakin Hajjo." Hajjo na jinta sai dai haushin abinda ya faru dazu ya hanata fitowa. Kanwar Hajjo tace “Zeena muje lokaci na wucewa kece Uwar gida ke za’a fara kaiwa.” Zeena ta gyara alkyabarta ta sauketa ta rufe fuskarta sannan suka riketa suka hau guda suka fito. "Mutane sun cika a gun ‘yan kai Amarya, sai busa ake ana guda tare da kirari." Haka suka nufi bangaren Junaid. Bangarenta wanda yasha gyara ta ko ina. Suka ajiyeta sannan sai datakai wajen awa daya aka kawo Binta nata bangaren dake gefe. "Junaid na zaune kan salaya yana tilawa, sai daya gama sannan ya rufe qur’anin yahau addu’oi" tare da fatan Allah ya bashi damar yin abinda ya dace a koda yaushe. Yan kai amarya kowa ya watse. Zeena ta kalli Fure tace “mikon madubi naga fuskata.” "Da sauri Fure ta miko mata, Zeena ta kalli fuskarta ta kara dan gyagyarawa sannan ta maids" fuskarta ta rufe. Binta kam sanin Safiya tace mata yau kwanan Zeena ne tunda itace Uwar gida yasa ta sauke alkyabar ta ta dauro alwala tai salla. Junaid ne ya kalli Azi wanda ke durkushe yana jiran Junaid ya nufi bangaren Gimbiya. Junaid ya tashi ganin wannan ne tuni na kusan biyar da Azi ke mai. "Junaid ya na mikewa Azi yace “Yauwa Yarima, an gaisheka.”" "Junaid bai tankashi ba suka fito, bangaren Binta ya kalla, harya juya sai kuma Azi yaga ya nufi can." Hankali a tashe Azi yace “Yarima yau kaine xakaje gun Gimbiya Zeena itace uwar gida.” Junaid ya kalleshi yace “na sani.” "Azi yai kasa dakai, bakin kofarta yaje kamar zai shiga sai kuma ya juga suka nufi sashen Zeena." Fure haryanzu bai iso ba? Fure tace “haryanzu Gimbiya.” Zeena haushi ya kamata tace “badai gun yarinyar can zaije ba ko?” Da sauri Fure tace inaaaa ai bazai yiwu ba. Isowar Junaid aka sanar wanda yasa Zeena jin dadi. Junaid na shigowa suka fita suka bar dakin dukansu. "Kallanta yai sannan ya karasa cikin dakin, zama yai akan kujera sannan ya gyara kafafunsa ya" kishingida Zeena dake zaune taji shiru hakan yasa tadan bude kanta. Tsananin mamaki ne yasa ta bude baki tana kallansa......... * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {34} "Cikin rashin fahimta Zeena ta kalleshi tace ""Ya Junaid?""" "Idanunsa na rufe bai bude ba yace ""Hmm.""" """Mekenan?""" "Ta fada fuska dauke da mamaki, juya baya yai ya fuskanci gefen kujera yace ""inkinyi sallah ki kwanta, ni bacci zanyi.""" "Idanu ta zaro cikin mamaki, sai dai a matsayinta na maje me aji batasan me zata sake cemai ba." "Gaba daya ta kasa ko mikewa daga inda take, tafi awa daya a haka kafin ta mike cikin takaici tai alwala tai sallah, kusa dashi taje ta zuba mai ido, shikam baccin sa yake sosai zuciya daya, bakinta ne ya shiga rawa cikin takaici ta juya ta kwanta." "Jin sanyin gari yasa taja bargo, kallansa tai hanayensa a hade, da alama shima sanyin yake ji" harararsa tai tace kai taji din. "Ta juya baya, sai dai sam ta kasa bacci, haka ta mike ta dau bargon ta rufamai ta luluba da zanin gadan." "Da safe bayan yai sallah ya zauna ya kasa yana nazari, tare da kallan Zeena wacce ke bacci." Zeena kam baccinta ta shara dan sai da rana ta fito. "Idanu ta bude cikin bacci, mamaki tai da idanunta suka sauka akan Junaid." "Yana zaune yana kallanta hannayensa a harde, da sauri ta mike zaune tace “Ya Junaid!”" "Idanunsa na kanta yace “ada bayan Jakadiya dake bangaren Marigayi, a cikin bayinshi akwai" wanda ya bar masarautar nan bayan rasuwarsa?” Kallansa tai cikin mamaki sannan tace “yaya ya daga tashi dai tambayar da ni kaina bansan ta ba?” "Ki tuno, kin tabaji anyi maganar wani wanda yabar masarautar nan bayan rasuwarsa." "Kallansa tai kafin tace “ni dai mutum biyu na tabaji, daya Allah yamai rasuwa.”" Dayan fa? "Tai dan shiru kafin tace “ban sani ba gaskiya, wasu sunce ya rasu wasu sunce yanada rai.”" Su waye sukace ya rasu su waye sukace yana da rai? "Kallansa tai cikin dan shakka, sannan tai shiru, mikewa yai a hankali yazo inda take kan gado, ya" "zauna, yace “wanene?”" "Kallansa tai a hankali sannan tace “nadaiji rannan Hajjo na umartan a nemo mata shi, sunanshi Sabisu, shine mai kula da sarki.”" Shiru yai kafin yace “Hajjo ta sameshi?” Kallansa Zeena tai tace “menene Ya Junaid?” Yace “kawai ina san sanin wadanda suka taimaki mahaifina ne.” "Sam bata yadda da wannan zancen ba, yanda ta dago ne yasa yace “menene?”" Shiru tai a ranta tana neman saita kwakwalwarta sannan tace “Bata sameshi ba a iya sanina kenan.” Mikewa yai sannan yace “nagode.” Har ya juya zai fita tace “idan na samoma shi me zan samu?” "Juyowa yai ya kalleta, itama kallansa takeyi tace “na tabbatar hanya ta sai tafi taka saboda baka" "dade anan ba, idan na samoma shi ni kuma me zan samu daga gareka?”" Wani rainanen murmushi ya saki yace “me kikeso?” "Shiru tai tare da dan motsa baki, yace “me? Kwana dani?”" "Kallansa tai zuciyar ta tayi matukar kuntata, idanunta ne suka ciciko tace “in naso haka laifi ne?" Meyasa yaya kake yabamin magana san ranka?” Kallanta yai sai dai baice komai ba ya juya zai fita. Daurewa tai tace “karka manta zamu gaida Umma karama.” Bai amsa mata ba yai fitarsa. Cikin takaici ta sa hannu ta cilar da filo din dake bayanta. Junaid kam yana fita ya kalli Azi yace “Azi ka nemomin wani sanisu a bangaren Marigayi yake.” Gaban Azi ne ya fadi ya kalleshi yace “Sabisu?” Junaid ya tsaya tare da kallan idansa yace kasanshi ne? Dasauri Azi yace “a’a” "Junaid yace “ka nemomin shi sannan inka san inda yake karka fadawa kowa ko shi kansa, ka sanar dani gun.”" Azi yace to. Bangaren Binta ya nufa. Tana ta gyara gadan data tashi daga bacci ya shiga. Jin motsin bude kofar dakin da take ne yasa ta juyo. Tsayawa yai a jikin kofar cikin wani irin farin ciki yace “Hajiya Binta me kikeyi?” Ya Junaid! "A hankali ya fara takowa yana zuwa yasa hannu ya rikota, kan gado ya zaunar da ita sannan ya" kwanta akan cinyarta tare da rufe idanunsa. "Shiru tai tare da saukar da kanta kasa, sai dai hakan ya kai fuskarta saitin nashi fuskar." "Shiru tai tana kallan fuskarsa, wani sansanyan murmushi ta saki tana kallan fuskarsa." Bai bude idanunsa ba sai jitai yace “irin wannan kure kallo? Ko so kike ki gano munina?” "Hannu tasa da sauri ta rufe fuskarta, kansa ya juyar saitin cikinta, yasa hannunsa yasa ya zagayo" dashi zuwa bayansa. "A hankali taja wani dan numfashi, ya. ”" Katseta yai da cewa “jina nake kamar a mafarki.” "Wani murmushi ta saki, tare da yin shiru, a hankali dan karamin bacci ya daukeshi, saboda" farkawar dayai da daddare yana kokarin gano abinda bashida masaniya a kanshi. "Hannu tasa a kansa tana shafa a hankali, can tace “nice nake ganin komai kamar a mafarki? Ban" "taba kawo wannan rana ba a tsayin rayuwata, ina mamaki abinda ke faruwa, a da na dauka a" "matsayin yaya na daukeka, sai dai tun daga sanda kabi bayan Gimbiya nasan zuciyata da biyu ta" daukeka. Kaine dai bansan ko haryanzu a matsayin kanwa nake na a gareka.” "Bata taba zata ba sai gani tai ya juyo ya kalleta, hannu yasa ya turata kan gadan tai baya ta" "kwanta, matsowa yai kusa da ita ta samanta yasa hannu a kan fuskarta yace “kinasan sani?”" "Hannu tasa ta rufe fuskarta, hannu yasa ya zare hannunta yace “shine abinda yake damunki?”" "Shiru tai sai dai tadan daga kai kadan, a hankali ya turo fuskarsa saitin tata, ya sumbaci goshints," ya sumbashi idanunta wanda ta lumshe su saboda wani shauki daya zo mata. "Kan hancinta ya sake sumbata sannan ya saukar da bakinsa kan nata, dan karamin sumba ya fara" mata sannan ya kalleta tare da kara kai bakinshi cikin nata. Me takeji? "Gaba daya jitai komai na jikinta ya kule, sai da ya gama sumbatarta sosai, sannan ya dago ya sa hannu ya dan kishingida ta gefenta ya kalleta yace “Ni tun sanda nasan kaina nasan ina sanki.” A hankali ta bude idanunta da gaba daya suka shanye, ta kalleshi, yace “gani ke ba da wannan" kika dauken ba yasa bantaba nuna miki ba. "Idanunta ne suke ciciko, tace “Ya Junaid nagode da kakesan wannan wacce batada gatan.”" Yatsansa ya saka akan lebanta sannan ya hade fuska sosai da sosai yace “meye hakan?” "Kallansa tai taga yanda ransa ya baci, mikewa yai ya zauna fuskarsa a hade." "Tanadaga kwance tasa hannu ta kamo rigarshi, dan jan rigar tai hakan ya sashi yai baya, tace" “na daina.” Kallanta yai yace “karki sake” Da sauri tace “to.” Jawota yai jikinsa ya rungume. "Baisan bacci ya daukeshi ba, ganin yanda yake bacci yasa ta zare jikinta a hankali ta fito ta rufe" kofar. "Harira ta gani a waje, ta bude mata, Harira ta kalli kuyangun tace “ku shiga da abincin.”" "Nan suka fara shiga da abincin, Binta ta kalleta, Harira tace “Azi yace yarima yana nan ko?”" Binta ta daga kai alamar eh. Nan suka ajiye suka fita. ********* Ta gama kwalliya duk da fuskarta kana kallo kasan ba ta farinciki duk kuwa da kasancewar ta Amarya. Kallan Fure tai wacce ke gyara mata kanta tace “Ki aika a cema Yarima na shirya.” Fure ta ajiye comb din ta fita. "Sai dai ba kowa a bangarensa sai bayinsa, nan suka sanar mata yana bangaren Binta." Mamaki ya kama Fure cikin jin haushi ta nufi bangaren Zeena ta sanar da ita. Zeena cikin mamaki tace “mene?” Fure tace “ancema wai bacci yake.” Bacin raine karara ya bayyana a fuskar Zeena ta mike a fusace tace kiramin Bintan. Binta tasa kaya kenan bayan tayi wanka tana jiran Junaid ya tashi suci abinci dan dama tun can ma tare suke ci. Harira ce ta shigo da sauri ta kalli Binta. Binta tace “Harira ashe kina nan.” Ana magana a waje.” "Binta ta fito, ganin Fure yasa tace “ya akai?”" Fure tace kizo. Ta juya. Zeena na zaune a falanta Binta ta shiga. "Kallanta tai cikin tsananin kishi, sannan ta daure bacin ranta tace “dama tambaya zanyi Ya" Junaid ya farka?” "Binta tai kalleta, Zeena tai murmushi tace “dazu yace zaije gunki ganin ke kadai kika kwana," sannan yace bacci yakeji nasan kila yadan kwanta ne.” "Binta tai shiru ta kasa magana, Zeena ta mike da kyar tace “zauna mana, kefa yanzu matar" "yarima ce, kiyi hakuri nima ba dadi nakeji ba.”" "Tadanyi kasa da murya tace kinsan maza da ranar daren farko, sai ana komawa baccin safe.”" * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {35} "Binta dake kasa tace ""bakomai nan ma ya isa.""" "Yanda tai maganar Gimbiya ta fahimci taji haushi, a ranta tace kiji yanda naji kema, sannan nasan bazai taba cemiki bai kwana dani ba shima." Wata zuciyarce tace inya fada fa? "Binta ce ta katseta da cewa ""zan sanar masa.""" Sannan ta nemi izinin tafiya. "Tana fita Zeena ta kumburo fuska cikin tsananin kishi, maganar daya yaba mata jiya ta tuno, wato daga cemai me zata samu shine zai fada mata haka?" ***** "Binta kam tana fita ta nufi bangarenta sam ta rasa me yasa take jinta duk ba dadi, a iya saninta dai Zeena matarsa ce yana kuma da hakkin yin duk abinda yaga dama da ita, to menene nata najin haushi?" "Turo kofar bangarenta tai, mamaki ne ya kamata dataga Junaid a zaune akan kujera." Kallanta hai yace “Daga ina?” Tace “naje gun Harira ne.” "Hannunsa ya miko mata, a hankali ta karaso ta rike hannunsa, jiti ya jawota ta zauna akan" "cinyarsa, yace “Binta!”" Naam! "Ya zuba mata idoyace “yanzu da da fa ba daya bane, kada ki kuskura ki bar wani ya rainaki, ke matar Junaid ce, ko gunsu Harira karki sake zuwa in kina nemanta ki aika tazo.”" "Tace to, yace “ni dai a iya sanina Binta da ko Junaid bai isa takata ya wuce ba amma tunda" "kikazo nan kin bari kowa ya rainaki, karki kuskura ki cigaba da bari ana rainaki, in ba haka ba nan" gaba baki isa ki gyara ba.” Dariya tadanyi tace “ko kaine?” Yace “eh ko nine kimin masifa yanda kika saba da in aka bata miki rai.” Dariya ta sakeyi sannan tace “Abinci.” Kallan Abincin yai yace “a bangaren Umma karama zamu karya.” Jikinta ne yai sanyi ta daga kai alamar to sannan ta mike daga kan cinyarsa tace “ana jiranka.” Mikewa yai yace “bari na shirya” "Ya fita, da kallo ta bishi sannan ta zauna abakin kujerar daya tashi cikin sanyin jiki." ********* "Junaid na fita ya wuce ya shirya, sanye yake cikin dakakiyar shadda kalar gajinare hula ya saka" sannan ya saka takalmi yayi kyau kwarai da gaske. Yana fitowa ya kalli Azi yace “ki kira Binta.” Azi ya kalleshi sai dai ganin yanda ya hade fuska yace “To Rankanya dade.” Nan ya kalli dayan bawan nasa yace “yima Zeenatu magana.” Nan shima ya jiya da sauri. Junaid ya karasa sa takalminsa sannan ya fito ragowar hadiman na biye dashi. "Binta dake zaune inda aka barta Azi ya sanar da ita sakon Junaid, cikin jin dadin hakan yasa ta mike da sauri ta shiga daki itama ta zura alkyabarta, kasancewar karta tsaya kwalliya ta bata ran Junaid yasa ta fito." "Zeena ce tsaye kusa dashi da alama magana sukeyi, kallan Zeena tai taga tasha uban kwalliya." Dan murmushi ta kakaro sannan ta nufo su. Agun Zeena da Junaid kuwa kallansa tai tace “bangane Binta muke jira ba?” Wani kallo ya mata yace “batada hakkin zuwa ne?” “Ba haka bane amma ai ” Yace “badai haryanzu a matsayin wacce batada matsayi a gidan nan kike kallanta ba?” "Ranta ne ya baci ta kalleshi, yace “karki manta kishiyarki ce matar Junaid, a ynzu in aka" "wulakanta matata kamar ni aka wulakanta, kuma ke ma kamar ke aka wulakanta.”" Shiru tai saboda tama rasa me zatace ta ina dan an wulakanta Binta aka wulakantata? Isowar Binta ne yasa t mata wani banzan kallo. Junaid wanda haryanzu fuskarsa a hade take yace “muje.” Haka suka taho suka nufi bangaren Azeema. "Kallan Zeena yai bayan sun dan yi tafiya mai dan tsayi jefi jefi suna daga hannu in an gaishesu," yace “ni Shamaki yaushe ya samu mukaminsa?” "Kara matsowa tai kusa dashi hakan yasa Binta tadan ware kadan da su, tace “sanda Abba ya" hau mulki.” Shamakin da fa? "Tace yayansa ne saukeshi akai, Junaid yace “Galadima fa?”" Tace tunda shine haryanzu kum ” "Baya tai tana neman faduwa, da sauri yasa hannu yariko hannunta." "Binta ta kalla wacce gaba daya takeji kamar an wareta, wacce ganin Zeena da Junaid a haka ya kara sa taji gaba daya komai ya tsaya mata." "Wani murmushin wulakanci ta watsama Binta, sannan ta dago." Junaid yace “Kina Gimbiya bakya ganin hanya.” Ya fada yana saketa. "Gyara tsayuwarta tai tana ‘yar dariya kadan, tace “tafiyarce bakaga yau wahala takemin ba?”" Cikin rashin fahimtar me take nufi ya maida kanshi kan Binta wacce ita ta fahimci me take san cewa. Junaid ne ya matsa kusa da ita yace “Binta!” Kallansa tai sannan tai murmushin yake tace “Naam.” "Muje, naga ne kin tsaya, kai ta daga alamar to." Haka suka isa bangaren Gimbiya Azeema wacce take ta jiransu. Da hanzari Barira ta karaso tace “sun iso Gimbiya.” Nan ta kara gyara zamanta tasa aka musu iso. Junaid ne ya fara shiga sai Zeena sannan Binta. Gaisheta suka fara yi ta amsa. "Kallan Zeena tai wacce take ta wani iyayi wai ta kasa zama daidai, sannan ta kalli Binta wacce tai" "shiru, ta kalli Junaid wanda kamar kullum yanzu fuskarsa daf take." Nan ta kalli abincin da aka jera sosai a gun tace “kuci abinci zan shiga ciki.” "Nan ta mike tai ciki, Zeena ta kalli Fure tace “Fure zubamin.”" "Fure ta taho da sauri, Junaid ya kalleta yace “ku bamu guri.”" "Nan kowa ya fita, cikin mamaki Zeena ta kalleshi, kallanta yai yace “ki zuba da kanki.”" In zuba? Ta fada tana nuna kanta. Dauke kai yai daga kanta yace “Binta bismillah.” Yanzu kam bazata kara bari a maidata ‘yar kallo ba. "Da sauri ta jawo plate ta zuba mai abinci, sannan ta zuba nata." "Spoon ya mika mata shima ya dauka, dariya yai yace “naki wayan shine aka cikamin?” Itama dariya tai tace “ya kamata kai kaci dayawa dan Allah nasan yunwa kake ji.”" "“Ahhhh na manta ashe kina gane in cikina ya rarake, lalai zanyi dabara yanda bazaki dinga" ganewa ba” Dan Kallan Zeena tai ta gefen ido wacce ta cika ta batse ko abincin ma ta kasa sawa. Kallan Junaid kawai take dama yana dariya haka? Binta ce ta kalleta tace “Gimbiya na zuba miki?” "Zeena tai shiru tana nazari kafin tace “basai kin zubamin ba, tunda ya Junaid yace nashi yamai" yawa bari muci tare.” "Cikin mamaki Junaid ya kalleta, Binta ta zuba mata ido itama." Junaid ya kalli Binta sannan ya nuna mata plate da idanunsa alamar t zuba nata ya dauke kai. Cikin kufula ta jawo plate ta zuba. Safiya wacce sanda sukazo tana hada kayanta taga Azeema ta shigo. "Kallanta tai tace “Umma ya kika shigo kika barsu, bayan kinsan mata biyu lokaci daya akwai" hidima?” Azeema ta zauna tare da cewa “hakan ne yasa na taso.” "Safiya tace “ni Binta nakeji, itada bata magana sosai, Zeena nasan haka zataita kunsa mata" haushi.” "Azeena ta gyara zamanta tace “intaga ana neman kwace mata miji ta kwaci kanta, zama ka" "fadawa mutum karya bari amai kaza da kaza bata lokaci ne, in taga mijinta na neman yin nisa da" ita ta mike.” Safiya tai dariya tace “Umma kenan komai naki sai kin hasaso kike aikata shi.” A falo kuwa haka kowa yai shiru kowa da abinda yake sakawa a ransa. "Zeena na jin haushin abinda Junaid ke mata, Binta na kishin yanda Zeena da Junaid ke maida ita" "yar kallo, Junaid kam tunanin Shamaki da Galadima yakeyi, kallan Zeena yai sannan yace “Waziri fa?”" Fuska ta hade tace “shima tun lokacin Marigayi.” Junaid yai shiru yana tunani. "Binta ce ta zuba ruwa ta ajiye kusa dashi, kallanta yai sannan ya sakar mata murmushi yace" “Nagode!” Itama murmushin ta maidamai tare da nunamai wata kwanon agun. Kallan robar yai sannan yace “a’a” Tace “kai Ya Junaid!” Yace “Allah karkici kin manta abinda ya saki?” Da sauri tace “na hakura ba sai ka fadaba.” "Zeena ta kalli kwanon dake cike da gwaza, sannan ta haraeta tare da tabe baki." *********** Sarki ne ya kalli Shamaki yace “ka gano inda Sabisun yake?” "Shamaki ya girgiza kai yace “haryanzu ranka ya dade, amma wai me yasa kake nemanshi" yanzu?” "Sarki yace “haka kawai nakejin hankalina ya kasa kwanciya, ni gaba daya yaran can gani nake" kamar kallan mu yake yana nazari akan mu.” Dariya Shamaki yai yace “karka damu Ranka ya dade na tabbatar yanzu da yke danka kuma sirikinka bazai kawo wannan a ransa bama.” Sarki ya jinjina kai alamar gamsuwa yace “haka nake fata.” ****** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {36} "A bangaren Azeema ya barsu, fitowa yai ya nufi bangaren Hajiya Inna." Daga baranda ya tsaya yana amsa gaisuwar Jakadiya. Junaid ya kalli Jakadiyar yace “Jakadiya ina san magana dake.” A tsorace ta kalleshi tace “To Yarima.” Fitowa tai tabi bayansa har bayan ginin Hajiya Inna. "Su biyu ne agun, ya kalleta yace “Jakadiya shekararki nawa kina aiki anan gidan?”" Dan murmushi tai tace “tun ina Yarinya nake anan.” Junaid ya kalleta yace “meyasa Hajiya Inna batasan Umma?” "Da sauri Jakadiya ta kalleshi, Junaid cikin yanayin maganarsa ta kasaita ya kalleta yace" "“tambayarki nake, dalilin zuwa na da kaina dan karma kiyi tunanin boyemin wani abu ne, zan iya shiga na tambayi Hajiya Innan da kaina.”" "Hankalin Jakadiya ne ya tashi, ta zube a kasa tace “Yarima!”" Junaid yace “menene dalili? Na tabbatar ba akan ta sake aure bane.” Shiru tai sai da Junaid yai gyaran murya alamar bacin rai. Da sauri tace “Yarima ka gafarceni amma Hajiya In "tace tun Marigayi nada rai Gimbiya da Sarki suna san juna, tace san mulki ne yasa Gimbiya taki" auran Sarkin yanzu ta zabi Sarki Zubair.” Junaid ya kalleta yace “dan tana sanshi ta auri yayansa menene na tsanar?” "Jakadiya gabanta ya sake faduwa, hankali a tashe ta kalli Junaid tace “wannan Hajiya Inna ce" kawai tasan dalilinta.” Ido Junaid ya zuba mata sannan a hankali yabar gun ba tare da yace komai ba. "Gaba daya kansa ne ya kulle, dan har bibiyu yake gani." "Dakewa yai harya isa bangarensa, a daki ya zauna yana tunani, in tana sansa kenan Hajiya Inna" tana zarginsu da kebencewa bayan anyi aure ko me? In haka take zargi kenan shima haihuwarsa "akwai ayar tambaya? Wani murmushin takaici yai yace “ta yaya? Ai da ba wanda zai kawo maganar aure na da Zeena a cikinsu, to menene?”" Sai can bayan Magrib Azi ya shigo yace “Yarima lokacin zuwa bangaren Binta yayi.” "Junaid ya kalleshi sannan ya mike jiki a sanyaye, Azi cikin mamaki ya kalleshi, ya dauka zumudi" "zai hana Junaid mantawa, meke faruwa?" ******* "Zagaye take tayi a cikin dakinta, gaba daya hankalinta nakan bangaren Binta dan ta tabbatar" "Junaid nacan tunda kwananta ne, zama tai a bakin gado ta harari kujerar daya kwanta daren jiya, mikewa tai zumbur ta sa mayafi ta fito falo." Fure da sauri ta taso tace “Gimbiya lafiya?” Zeena ta kalleta tace “Bangaren Maman Rabi zani.” "Ramlatu? Abinda ya fado ran Fure kenan, tace “Gimbiya me zakiyi acan?”" Wani banzan kallo ta mata tace “mu biyu zamu koma banasan kowa yasan inda muke.” Da sauri Fure tace to. Fitowa tai ta aiki kuyangin dake waje suka wuf suka fice. Ramlatu na zaune suna hira Fure ta shigo. "Zubewa tai ta gaisheta sannan ta mata alama data sallami mutanen dake gun, nan Ramlatu ta sallamesh." Kallan Fure tai tace “lafiya?” "Gani tai an bude labile kallan mai shigowa tai, mamaki ne ya kamata ganin Zeena." Da sauri ta mike tsaye tace “Gimbiya?” "Zeena ta karaso ta zauna sannan ta kalleta, sallamar Fure tai sannan ta maida hankalinta kan" Ramlatu tace “Ramlatu kun samo inda Sabisu yake?” Mamaki karara ne ya bayyana a fuskar Ramlatu tace “Sabisu?” Zeena ta hade fuska tace “kunsamo inda yake?” "Cikin mamaki tace “ai bangane bane, me zaki mai?”" Zeena tace “Zaki fadamin ko sai na fita na nufi bangaren Umma karama na fada mata kin amso magani?” Hankalin Ramlatu ne ya tashi a tsorace ta kalle Zeena tace “bamu sameshi ba amma munji labarin yana wani kauye wai Bukul.” Bukul? Zeena ta tambaya. Ramlatu tace “eh amma da alama Hajjo ta hakura dan bata sake sawa a nemeshi ba.” Zeena ta kalleta tace “kar wani mai numfashi yasan nazo gunki balle yasan maganar da mukai.” Ta mike ta fito. Suna isa bangarenta ta kalli Fure tace “da gari yadanyi haske kadan kije bangaren Binta kice Yarima ina bangarensa ina jiransa.” Kallan mamaki Fure ta mata sai dai batace komai ba sai to. "A can bangaren Junaid kuwa, bayan sunyi sallah tare ne akan sallaya ta kalleshi cikin kulawa" ganin yanda yai shiru yana dan nazari. "Hannu tasa a hankali ta kamo hannunsa, kallanta yai sannan yai murmushi." “Meke damunka Ya Junaid?” Wani sansanyan murmushi ya sakar mata yace “zuciyata ke sanar dani wani abin wanda kuma bansan kwakwalwata ta amince dashi.” "Hannunsa tadan murza kadan tace “in har bakasan amincewa dashi ko tsoron tabbatar da abinda kake zargi, ka hakura dashi mana.”" Kai ya girgiza mata alamar a’a yace “abu ne da dole sai nayi.” Kai ta daga alamar ta fahimta. Kallanta yai yace “shiyasa nake neman alfarma.” Alfarma? "Ta tambayeshi, yace “zaki iya jirana?”" "Kallan mamaki tamai na rashin fahimta, yace “zuciyata gaba daya bata nan gun, sannan ina" "tsoron abinda zan binciko wanda kila ya shafi tsatsona da rayuwata, zaki jira na gama abinda nake?" Banasan na shiga hakkin daya daga cikinkin ku.” Gaba daya jikinta ne yai sanyi duk da batasan me yake nufi ba amma tasan tabbas abinda yake tsoro yanada waya a ransa wanda har yasa yake tunani haka. "Kai ta daga alamar to hannu yasa ya jawota jikinsa ya rungume, tsoron abinda zuciyarsa take rayamai yakeyi." "Kwanciya ya fara yi ya jawota jikinsa ya rungume tsam, in har mahaifiyarsa nada wani tabo" baisan ya zaiyi rayuwarsa ba. Yanda ya matse binta ne yasa a hankali tace “Yaya!” Kallanta yai sannan ya sassauta rikon yace Yahkuri Binta.” "Murmushi tai ta dago kanta ta kalleshi, ganin yanayinsa ne yasa ta kwanta a kafadarsa cikin" tausayamai. A hankali bacci ya dauketa. Junaid kam kasa bacci yai sai can wajen dayan dare ya samu bacci ya daukeshi. Yana sallar asuba ya kalli Azi bayan sun fito daga masallaci zai mai magana kenan Hadimin sarki wanda ke jikinsa ya iso gun da suke. Junaid ya kalla bayan ya gaisheshi yace “Yarima Mai Martaba yace da rana ka shigo fada.” Junais yace to. "Yana tafiya ya kalli Azi yace “Azi inaso ka tafi neman Sabisu, karka bari kowa ya san abinda kakeyi.”" Da sauri Azi yace “to Yarima.” Daga nan ya fita. Junaid ya shiga bangaren Binta tana zaune kan sallaya tana wa Junaid addu’a da fatan dacewa. Zama yai a bayanta a hankali yasa kansa akan bayanta. Murmushi tai bayan ta kammala addu’arta a tare suka shafa sannan ta gaisheshi. Kallanta yai yace “Binta kin tashi lfy?” Cikin jin dadi tace “lafiya kalau Ya Junaid.” Murmushi yai yace “Da alama Bintata ta fara dawuwa.” Dariya tai tace “Da ina naje?” Yace “kin bari masarauta ta cinye rabinki.” Dariya ta sakeyi shima yana dariya yace “ba haka bane?” Zatai magana sukaji ana magana. Cikin mamaki ya kalleta ganin yanzu gari ya waye. Binta ta fito ta bude kofa. Fure ta gani cikin mamaki tace “lafiya?” Fure tace “Gimbiya ce tace acema Yarima tanada magana tana bangarensa.” "Tsayawa Binta tai cikin tsananin mamaki, Fure ta juya." "Binta jiki a sanyaye ta nufi ciki, kallan Junaid tai wanda yace “waye? Wai ya akai bakida hadimai" ne sai wata guda daya da na gani jiya?” Binta ta kalleshi tace “Gimbiya ce ke jiranka a bangarenka.” "Cikin mamaki ya kalleta, Gimbiya?" Tace eh. Yanda tai maganar kana gani kasan taji haushi. "Shiru yai yana tunani, ta samo wani abin ne? Kamar bazai tashi ba har Binta taji dadi sai taga" zumbur ya mike. Kallansa tai da sauri tace “ina zaka yaya?” Yace “bari naje zan dawo.” Mamaki ne ya kamata dako magana bai sake mata ba ya fita. "Kasa motsi tai a inda take, shiru tai tana tunani, yace bazai kwanta da ita ba bayan jiya ya kwana" "da Zeena, yanzu kuma ya tafi ya barta? Anya Ya Junaid dinta ne?" Junaid ne ya nufi bangarensa. Zeena na zaune a falo ya shiga. Zama yai daga kujerar dake kallan tata yace “ya akai?” Kallansa tai sannan ta dan lumshe ido tace “magana nakeso muyi.” Kallanta yake baice komai ba. Tace “na samo inda Sabisu yake.” Kallanta yai da sauri sai kuma yace “taya zaki san inda yake a yini daya?” Tace “Shikenan tunda baka yarda ba.” Ta mike zata fita. Hannu yasa da sauri ya riko hannunta. Cak ta tsaya ba tare da ta juyo ba yace “Yana ina?” A hankali ta juyo ta kalleshi tace “Yana Bukul.” "Mikewa yai da sauri, yace “inane Bukul?”" "Tace “bansani ba nima haka kawai akacemin, sai dai yanda nasamoma inda yake nima sai ka amince da abinda nake so.”" "Kallanta yai baice komai ba, tacigaba “Kamin alkawarin bani dama nima.”" Dama? Ta cigaba “Zuciyara zata hakura da rashin san da kakemin kafin aure amma bazata iya daukar kiyayyarka ba bayan aure. Kallanga yai baice komai ba. Shiru suka danyi. "Cikin jin haushin aikar Azi dayai, ya shiga tunanin abinyi." Kusa da shi ta kara matsowa tace “Meyasa kake nemanshi wai? Kai Da Hajjo bansan me kuke nema dashi ba.” Junaid ya kalleta yace “Inaji dole na fita da kaina.” ******* Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {37} "Kallansa tai hankali a tashe tace ""ina zaka?"" Ta fada tare da riko hannunsa." Kallanta yai ya kura mata ido yana nazari. "Gani tai ya saki wani dan siririn murmushi wanda ya bata tsoro, tace ""ya akai?""" """Ba sai naje da kaina ba, tunda bansan ya yake ba balle inda zan sameshi takamaimai."" Gaba" "daya batasan me yake nufi ba shi yasa ta kasa cewa komai, hannunsa ya zare cikin nata sannan ya fita." Kasa tsaidashi tai saboda tana tunanin abinda yake nufi a kanta. "Junaid na fita hadimansa suka biyo bayanshi, bangaren Azeema ya nufa." Tana daga kwance ana dan matsa mata kafarta. "Barirace ta shigo ta sanar da ita isowar Yarima, kallan Barira tai tace ""Junaid?""" """Eh Gimbiya.""" "Mikewa zaune tai ta sallamesu, Junaid ne ya shigo ya zauna a kasa." Sai daya gaisheta ta amsa tare da tambayan kwanan matansa. Suna lafiya ya fada yana kallanta. "Kallansa tai tace ""da wani abin ne?""" "Junaid yace ""matsalarku da Hajiya Inna, bakya tunanin ya kamata ki bata hakuri? Halin rayuwa" "shi ake dubawa.""" "Kallansa tai tace ""Junaid ko na bata bazata taba hakura ba, ta riga tasa abinda takeso a ranta.""" Abinda takeso? Ya tambayeta. "Dan zamanta ta gyara tace ""a'a kasan in mutum baya san wani kiris yake jira.""" """Amma da tana sanki ai.""" "Dan murmushi tai cikin waskewa tace ""hmm "" gani batasan cigaba da zancen yasa yace ""ko" "kinsan Sabisu?""" """Sabisu? Waye hakan?""" """Awwwww nagane shi bawan Mahaifinka, ya akai ka sanshi?""" "Dan kallanta yai yana nazari akanta kafin yace "" naji su Hajjo na nemanshi ne.""" "Hajjo? Tai tambayar cikin mamaki, idanu ta zaro da sauri, sannan ta sauke idanta kasa saboda" "karya gane, yace ""eh bandai san dalilinsu ba.""" "Yake tai tace ""Allah sarki.""" "Har ya mike yace ""naji yana wani kauye wai Bukul.""" "Mikewa yai ya mata sallama ya fita, yana fitowa Falo ya bi bayan kofar da kallo, yace ""Umma dan" "dan Allah ko menene karya zama akwai ki a ciki.""" "Tunda ya fito ta kasa ko motsi, meke faruwa?" "Fitowa yai ya koma bangarensa, bangaren Zeena ya fara shiga sai dai batanan, hakan yasa ya" wuce bangaren Binta yana nazari. "Binta na zaune a bakin gado duk abin duniya ya isheta, jin motsin yasa ta fito da sauri." Tana ganin Junaid ne taji wani dadi ya zo mata wanda har taji idanunta na neman kawo ruwa. "Mamaki ne ya kamashi, a hankali ya tako inda take, yana karasowa ta rungumeshi." """Ya akai?""" "Tace ""bakomai.""" "Dagota yai a hankali ya zubawa fuskarta ido, a hankali ya sumbaceta, sannan yace ""kinji haushi" "ne?""" "Cikin sanyin murya tace ""naji amma kadan""" "Murmushi yai yace ""wannan karan nayi laifi dafatan baza'a hukuntani ba.""" "Dariya ta dan yi tana neman dan matsawa daga jikinsa ya kara kankameta, tana kallansa tace" """bari naga wannan karan wani hukuncin za'ama.""" "Murmushi yai yace ""kenan laifin biyu nai tunda jiya nan na taho da safe kenan kowa namai" "laifi?""" "Fuska tadan hade, yace ""zan tafi Binta inada abinda zanyi, nazo ne na fada miki.""" "Jiki a sanyaye ta kalleshi tare da yin murmushin yake tace ""Uhm hmm.""" "A hankalinya zare ta daga jikinsa yace ""kici abinci, sannan zan nemi Harira ta kawo miki hadimai," "dan ita ta girma ne amma da ita ta dace dake.""" "Kai Binta ta daga alamar gamsuwa sannan tace ""to Ya Junaid.""" "Sake sumbatar kuncinta yai sannan ya juya ya fita, da kallo ta bishi." Yana shiga bangarensa yaga Zeena acan. Tsayawa yai yana kallanta cikin mamaki. "Tana ganinya shigo ta mike da sauri tace ""Ya Junaid me kake nufi? Wai me kake san ji gun Sabisu?""" "Kallanta yai yace ""kije ki sanar da Hajjo inda Sabisu yake, da alama itace take nemansa ba ni ba.""" "Kallan mamaki ta masa tace ""bangane ba.""" "Shiru yai yana san mata karin bayani sai dai inya tuna yar Hajjo ce sai yaji bazai iya ba, dan ya" tabbatar daga tayi subutar baki komai ya wargaje kenan. "Zeena ce ta kamo hannunsa tace ""menene?""" "Kallanta yai sannan yai murmushi yace ""bakomai kawai ina ganin ita take nemanshi bani ba.""" Shiru tai tana kallansa ta tabbatar akwai dalilinsa nayin haka. "Shikenan zan fada mata, kallanta yai a hankali yace ""nagode.""" "Dayake bata taba kawo jin hakan daga gareshi ba shiyasa kalmar ta shigeta dakyau, hannunsa ta" saki gaba daya jikinta yai sanyi. "Murmushi ya mata yace ""zaki iya sanar da ita yanzu?""" "Kai ta daga alamar eh, sannan tace ""nagode Ya Junaid.""" Dame? Kai ta girgiza alamar ba komai sannan ta fita. "Tana fita ta tsaya a waje, wani sanshi ne yake kara shigarta da darajashi." Tana kokarin wucewa sashinta taga Harira a bakin kofar Binta da alama abincin safe suka kawo mata. "Binta ce ta bude mata hakan yasa suka hada idanu, su Hari ne suka zube suna gaisheta." "Binta ce ta gaisheta, tana mamakin meyasa batabi ta can baya ba inda zata shiga bangarenta," amma sai data zagayo ta nan? "Zeena ce ta amsa cikin isa sannan ta wuce, Fure ce ta matso da sauri tace ""Gimbiya kina birgeni" "wato ki nuna mata daga can kike kenan.""" Wani kallo tama Fure batace komai ba har suka shiga bangarenta. Junaid kam zama yai a kan kujera tare da hade hannayensa yana fatan samun nasara akan abinda ya shirya. Shiru yai yana nazari........ ****** "Harira na shiga ta kalli Binta, tace ""Ranki ya dadw inasan magana dake inba damuwa.""" "Binta cikin dariya tace ""lalai Hari muje ciki.""" "Da sauri tace ""a'a nan ma yayi.""" Hadiman sun ajiye abincin sun fita sannan Hari ta kalleta. "Tace ""Kiyi hakuri da tambayar da zan miki.""" "Binta tace ""Hari ni ki daina min magana haka kimin magana kanki tsaye yanda muka saba.""" "Hari ta kalleta tace ""ba abinda ya faru daren jiya?""" "Kasancewar ta gane abinda take nufi yasa Binta tace ""eh.""" "Harira tace ""Gimbiya fa?""" "Binta tace ""bansani ba amma ta kirani tana sanar dani abu ya faru.""" "Harira ta kalleta tace ""Dama tun kafin aure naso na sanar dake amma bansamu dama ba" kasancewar kuna bangaren Gimbiya sai dai yau naga ya kamata ki sani. "Kada ki kuskura ki cigaba da sanyin nan da kike neman daurawa kanki, da can kinada sanyi amma abin bai kai haka ba, yanzu ba ke kadai bace agun Yarima, idan har kika cigaba da abinda kikeyi kina zaune wlh Junaid ganinsa ma sai ya gagareki.""" "Cikin mamaki ta kalleta tace ""bangane nida mijina ya gagaren gani ba.""" """Gidan sarauta kike bayan nan ku biyu ne sannan bayanan matarshi yar sarauta ce jinin mulki," "kina tunanin shakuwa da san da yake miki zai dawwama ne?""" "Binta tace ""Harira Ya Junaid ne fa?""" "Cikin dan zafi Harira tace ""ba namiji bane? Maza duk inda suke irinsu daya, idan har kika cigaba" "da wannan halin naki kina zaune sai kin rokama zai ganki, me kike mai anan? Banda ki zauna kullum kina kiransa? Kinsan matsalarsa? Kinsan burinsa? Kinsan abinda ke kasan ransa? Kinsan me yake tunani?""" """Taya zansan abinda bai fadamin ba?""" "Dole a matsayinki na matarsa wacce kuka taso tare sai kin mike kinji menene matsalarsa, na" "tabbatar shima yanasan sanar dake bayasan saki a damuwa ne.""" "Gaba daya jikin Binta ne yai sanyi, Harira tace ""anjima zan kawo miki hadiman da zasu kula" "dake.""" Tana kaiwa nan ta mata sallama ta mike. Shiru Binta tai tana nazarin kallamanta tabbas gaskiya Harira ta sanar da ita. ******** """Me kike anan? Haryaushe akai auren da zaki fara yawo?""" Hajjo ta tambayi Zeena dake zaune. "Zeena ta kalleta tace ""kefa Hajjo dadina dake rashin hakuri, sai kiji ai dame nazo miki ko?""" Hajjo ta hade fuska tace “menene?” “Sabisu!” Da sauri Hajjo ta kalleta tace “ya ya? Ke a ina ma kika sanshi?” "Ranar ina nan kuke labari da Ramlatu, na samo inda yake.”" Da sauri Hajjo ta matso tace “a ina yake?” “Bukul wani kauye ne.” Kallan mamaki Hajjo ta mata tace “ya akai kika sani?” "Shiru Hajjo tai tana kallanta, Zeena tace “menene?”" “Junaid kikaji yana nemanshi?” Zeena tai shiru badai Junaid abinda yakeso kenan ba? So yake ai zargin yana nemanshi? Kai ta girgiza sauri ganin abin bai bada ma’ana ba. Kallan Hajjo tai tace “koma menene ni ki fadamin meyasa kike nemanshi?” "Hajjo ta kalleta ta matso tace “Bincike nake san yi, so nake in samo abinda mahaifinki bai isa ya" hana Zubair mulki ba.” Baki ta tabe tace “wai ke haryanzu Hajjo batun ba Zubair mulki yana nan?” Wata muguwar harara Hajjo ta bata tace “tashi ki tafi gun mijinki da alama nan gaba komai naki ma gun mijinki zai koma.” Zeena ta mike ba musu ta masa sallama ta fita. Wani irin haushi ne ya kama Hajjo kafin tai maza tasa a kira mata Zubair dan yazo ya sa a nemo mata Sabisu. ********** Junaid ne ya shigo cikin fadar Zagi na mai kiran Lafiya. Junaid ya shigo sannan ya gaida mai martaba. Sarki cikin nuna jin dadinsa yace “Matawalle an shigo?” Junaid yace “Eh Ranka ya dade.” Nan su Shamaki da su Waziri da sauransu suka fara gaisheshi. Junaid ya amsa cikin isa da kasaita irin ta ‘ya’yan sarki. Sarki yai dan gyaran murya yace “Dama nasa kazo ne saboda a sanar dakai abubuwan da zaka dingayi a matsayinka ma matawalle.” Junaid yai dan kasa dakai cikin girmamawa yace “to Ranka ya dade.” Galadima ne ya kalli sarki yace “Ranka ya dade naga bai dade da aure ba da nauka za’a barshi ya dan huta zuwa sati biyu.” Junaid kam a ranshi yace ina za’a banni na huta ba’a san nasamu lokacin bincike? Haka sukai tattauna sannan suka taso. ********* "Azeema tayi shiru tanata zagaye a dakinta tana jiran Barira, can Barira ta shigo da sauri, ta yaye" "mayafinta tace “Gimbiya na sanar ma Gimbiya Safiya, tace ta sanar ma Mijinta yanzu zai wuce.”" Azeema ta jinjina kai cikin gamsuwa. ****** Hajjo ce ta kalli Zubair tace “ka tura kanin nawa?” Yace “eh Hajjo sai danaga tafiyarsa na shigo. ******* Junaid na kishingide a bangarensa idanunsa a lumshe a hankali naga ya sake yin wani sansanyan murmushi wanda nace hmmm ******Ayusher ****** * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {38} "Yau kwana biyu kenan da tafiyar Azi, gaba daya Mai Martaba yasa Junaid ya shiga hidima ta ko" ina. Yar yanzu ba wacce ya kwana da ita tsakanin Zeena da Binta. "Yau ya kasance ranar Zeena ne, yana zaune a bangarensa bayan ya kammala abubuwan daya kamata yai, shiru yai yana duba wasu takardu tare da fatan dawowar Azi a wannan rana." Tun safe yake jiran isowarsa amma haryanzu shiru. "Kamar da wasa yaji Azi yace ""Yarima nine!""" "Zamansa ya gyara yamai iso, Azi ya shigo ya zube a gabansa ya fara gaisheshi." "Junaid ya amsa sannan yace ""ya ya?""" Azi ya kalleshi ya danyi shiru. "Junaid yai dan murmushi yace ""bakomai, ko baka sameshi ba akwai masu kawoshi.""" "Kallansa yai cikin mamaki yace ""su wa?""" "Junaid yace ""inata nemanka ne dan ka samin ido ka dubamin bangaren Gimbiya da bangaren Hajjo, amma yanzu kaje ka huta zuwa dare tukun.""" "Azi yace ""na taho dashi ai.""" Ka taho dashi? Ya tambaya gabansa nadan faduwa kadan. "Azi yai kasa dakai yace ""Sabisu kanin mahaifina ne shiyasa kana fada nasan inda zan sameshi, yanzun ma dan baiyarda ya taho bane saboda yana tsoron abinda zai faru dashi, sai dana zauna" na shawo kansa tukunna tuba nake ranka ya dade.” Kallansa Junaid yai yace “Kanin mahaifinka?” Azi yai kasa dakai cikin daukan laifi. Junaid yace “yana ina yanzu?” "Yana can waje, a boye, bansan meke faruwa ba amma yace “baisan kowa ya ganshi.”" Junaid yace muje na shigo dashi dakaina.” "Fitowa sukai suka je inda Sabisu yake, Sabisu babban mutum ne dan a kalla zai kai shekaru 60," Junaid cikin girmamawa ya gaisheshi. Kallansa yai cikin jin dadin ganin Junaid yace “Yarima! Ashe zan ganka kafin lokaci na yayi?” Junaid ya kamo hannunshi yace “kayi hakuri duk da bansan meke faruwa ba amma nasan dalilin abinda ya faru ne ka bar masarautar nan.” "Shiru yai tare da sauke kansa kasa, Junaid ya kalli Azi yace “mu shiga.”" "Nan suka shiga Junaid na gaba, su Azi sun ba Sabisu kayan hadimai ya saka, haka suka shigo cikin" "dari, sunyi sa’s suka wuce bangaren Junaid." "Junaid ne yasa aka kawo mai abinci, sai dayaci sannan ya kalleshi yace “Baba kayi hakuri amma" na rasa meyasa nake da tambayoyi dayawa akaina game da masarautar nan.” Sabisu ya kalleshi yace “Yarima ya akai ka dawo?” Junaid ya bashi labari a takaici. Sabisu cikin jinjina kai yace “Alhamdulila da baka dawo ba sai daka mallaki hankalin kanka.” Junaid ya kalleshi duk da gabansa na faduwa saboda tsoron abinda zai tono amma yace “Sabisu kasan meyasa mahaifina ya kaini can wani gari? Ba da sanin mahaifiyata ba?” Sabisu yai shiru kafin ya kalleshi yace “Yarima!” "Junaid ya maida jankalinsa kansa yace “ka sanar dani, koma menene zan dauka.”" Ajiyar zuciya yai yace bakomai na sani ba sai dai zan sanar dakai abinda na sani. Junaid ya tattare hankalinsa kansa cikin danne damuwar dake ransa. Gimbiya ta dade tana neman haihuwar da namiji sai dai a duk sanda ta haihu cikin rashin sa’a sai ta haifi mace. Sannan abin ya dameta haka ma mai martaba saboda yasan irin san da Gimbiya kema Abdulsalam amma saboda burin zama matar sarki uwar sarki yasa ta ajiye komai ta aureshi. "Sarki Zubair na tsananin san Gimbiya, haka sukai ta fama amma duk sanda ta haihu sai dai ta haifi mace, daga bayama haihuwar ta tsaya, dan sai datai shekara hudu sannan ta sake samun ciki." Wannan cikin data samu yazo mata da matsala sabods tasha wahala akansa burin su kawai wannan karan a dace a samu d’a namiji. "Cikin yardar Allah Gimbiya ta haihu ta haifi d’anamiji, sai dai abin mamaki da tsoro yaran yazo ba lafiya, tunda aka haifeka bakai kuka ba sannan bakai bayan gida ba, bayan haka yanayin yanda kake numfashinka ba daidai yake fita ba." "Sai dai wannan rashin lafiya taka Azima ta sa an boyeta, dan inba ni da Mai martaba ba bawanda ya sani a iya sanina kenan." Sarki yasa an nemo masu magani cikin sirri amma abu yaki yiwuwa. "Duk an fara cire rai dakai, dan har ta fara hakura akan a sanar da mutane dan da alama bazakai rai ba." "Kwatsam wata rana Abdulsalam ya ziyarci Mai Martaba, tun daga sanda ya fito daga" bangarensa ” "Shiru yadanyi tare da dan share kwallarsa, Junaid wanda gaba daya yake jin kalaman Sabisu a" kwanyar kansa yace “inajinka.” "Sabisu ya cigaba “Tundaga wannan lokaci Sarki ya fara rashin lafiya, sai dai abin mamaki randa ya kwanta rashin lafiya ranar kai kashi, haka dai ya cigaba da daurewa sai dai mu munsan yanda yake jinya, yana jinya kai kuma kana samun sauki, ranar yana tashi daga bacci ya umarci a fara gini a filinsa dake cam wani kauye, tun daga nan kuma lamari sarki ya canza, kullum zaka sameshi shiru yana tunani." "Ciwon sa baya tashi sai dare, yasha wahala matuka sai dai da safe inka ganshi bazaka gane ba sai dai ramewa dayai." "Sarki ya hana matansa kwana a bangarensa sai dai adanyi hira sannan su koma. Ka samu lafiya sosai, hankalin kowa ya kwanta banda Sarki dake ta fama." "Akwai wata rana da ya zauna shi da Shamaki nada bana yanzu ba, tun daga wannan rana Sarki ya canza kwarai da gaske, ya fara janye jikinsa daga kan komai, sai ya zauna yai shiru yana tunani." "A lokacin kana shekara 7 ciwonsa ya tsananta, har Allah ya dau ransa.”" Shiru Junaid yai gaba daya ya kara sashi a duhu duk da dai ta wani bangaren ya dan warware "masa wasu abun, kenan shi dan Zubair ne da Gimbiya na gaskiya." Kallansa yai yace “bakasan me suka tattauna ba?” "Sabisu yace “bansani ba Yarima, sannan sai da mai martaba zai rasu ma Abdulsalam ya kira.”" "Azi, Junaid ya kirashi, da sauri ya shigo yace “ka kai Baba ya huta a bangarenku, kar ka bari wani" "yasan wanene shi, sannan inda dama ka zauna dashi.”" Azi yace “angama ranka ya dade.” "Tare suka fita Junaid yai shiru yana nazarin gaba daya a binda yake kwakwalwarsa, indanunsa ya" "rufe yanna tattara tunaninsa, yafi tsawon awa biyu a haka kafin a hankali naga ya bude idanunsa." Idansa ne naga yai jaaa sannan ya mike daga inda yake. Fitowa yai Hadimansa suka taso da sauri. Azi wanda ya zo gunsa ne ya matso yace “Yarima!” Junaid ya kalleshi yace “Dawo da shi dakina.” Dakinka?” "Azi ya tambaya, Junaid yace “eh yanzu.”" "Nan Azi ya juya da sauri, fuskar Junaid kadai xaka kalla kasan ba wasa a tattare dashi." "Ba a jima ba sai ga Azi ya dawo da Sabisu, nan suka shiga ciki, Junaid yace “ka zauna anan.”" Nan yace ina na isa zama a bangarenka? Junaid yace “ina tsoron abinda zai faru kana can ne.” "Sabisu ya jinjina kai, Junaid ne ya kalleshi cikin nazari yace “Akwai maganin da ka sani wanda" yake amfani da jinin wani?” Gaban Sabisu ne ya fadi ya kalli Junaid yace “me kake nufi Yarima?” "Junaid ya kalleshi yace “idan baka sani ba shikenan.” Ya juya, Sabisu ne yace “sai dai masu sidabaru.”" "Junaid ya kalleshi baice komai ba ya fito, bangaren Azeema ya wuce kai tsaye." Tana zaune cikin bacin rai tana tuno abinda sukai da Mahmud yanzu. tace “kana nufin Hajjo ta daukeshi kenan?” Mahmud yace bansani sai dai ina zuwa kauyen ance wani yazo wai Hajjo ce ta aikoshi.” "Azeema ta sauke ajiyar zuciyarta, me Hajjo take sanji?" Barira ce ta sanar da isowar Junaid hakan yasa ta gyara zamanta tare da daidaita tunaninta. Junaid ne ya shigo cikin dakinta. Cikin nuna farin ciki tace “Junaid.” "Zama yai sannan ya gaisheta, amsawa tai tace “kwana biyu banjika ba.”" "Kallanta yai ya kura mata ido, wanda har tadan sha jinin jikinta tace “Junaid!”" Sanda ina karami banda lafiya ya akai na fara samun sauki lokaci guda? Bayan alokacin an hakura da yin magani?” "Gaba daya jikin Azeema ne ya fara rawa, hannunta ta hade ta matsesu tana kokarin danne" fargabar kalamansa wanda bata taba tunanin ji ba. "“Zan fado kamar haka, Wata taga dan data jima tana nema yazo ba lafiya ga wanzamai da duk" "wasu masu magani sun kasa warkar dashi, hakan yasa ta nemi zuwa gun malaman tsubu, ta nemi wanda ta yarda dashi sukaje gun su biyu, bokan tsubu yace mata in tanaso danya ya warke to lalai sai ta sadaukar da jinin daya daga cikin iyayensa." Saboda tsoro da fargabar jin abinnan yasa ta dawo tare da hakura da abinda take nema. "Sai dai tasan wanda ta dauka bazai iya jurar ganinta cikin wani hali ba, hakan yasa ya koma ya nemi ai amfani da jinin mahaifin yaran, aiki ya fara ci daga sanda aka fara amfani da mahaifinsa." Haka rayuwar mahaifinsa ta karkare shikuma dan ya samu sauki.” "Idanunsa ya dago wanda sukai jaaaa sosai kai kace garwashi ne, yace “ Watan nan Umma ce, wanda ta yarda dashi Abdulsalam ne, sannan mahaifin Zubair ne.”" "Kafafunwanta ne suka shiga rawa hankalinta yayi kololuwar tashi, gaba daya ta kasa magana" "saboda gaba daya ta kasa daidaita tunaninta, bata taba tunanin wannan rana zatazo mata a duniyar nan ba." Junaid ya runtse ido wasu zafaffan kwalla ne suka zubo mai yace “kina tunanin abinda kikai kin cici danki ne saboda kina sansa? Ko kina tunanin abinda kikai Abdulsalam ya aikata ne saboda yana san danki? Ko kina tunanin Zubair be san me kuka aikata ba?” "Hankali a tashe ta sauko kasa, ta fara girgiza kai tace “Junaid Allah bansan komai ba, bani nace" "Abdulsalam ya koma ba, Allah bansan wannan abun ba.”" Hannunsa ta kamo ya kwace hannunsa yace “baki sani ba? Bayan kinsan Abdulsalam yana sanki? Sannan ke a naki tunanin Abdulsalam sabods ke kadai yai haka? Kina tunanin kece kikai amfani dashi?” "Kallan Junaid tai tana hawaye, kai ya girgizs mata yace “ko daya, kece akai amfani dake, kece" Abdulsalam yai amfani dake.” Me kake nufi Junaid?” "Mikewa yai cikin takaici yace “kiyi tunani dakanki, wannan abinda kika aikata bazan yafe miki ba," kina tunanin kuyi amfani da rayuwar mahaifina sannan kuyi tunanin zanyi rayuwar data dace? Saboda burinki nasan danki ya zama sarki?” Yanda yai maganar karshe kai kana ji kasan zuciyarsa ta gama raunana da bakinciki. Hawaye ne suka zubo mai yace “Daga ke har Abdulsalam da duk wani mai hsnnu aciki banaji zan iya yafe muku.” Kafin ta bude baki tai magana yabar dakin. "Yana fitowa yai bangarensa, duhu duhu ya shiga gani saboda kansa dake juyawa." "Hannu yasa ya rike bango da sauri kansa na wani irin sarawa, gaba daya baya gani sosai......" **** Ayusher **** * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {39} "Dakyar ya kai kansa ciki, yana neman faduwa Binta wacce ta fito ganin yanayinsa yasa ta matso da" "sauri, yana kokarin faduwa ta rikoshi da sauri, kallanta yai bakinsa ne ya shiga rawa, Yaya!" "Hannunta ya rike da karfi, ya nuna mata bangarenta." Rikeshi tai sosai suka shiga ciki. Tana rufe kofa ya zube ya zauna a kasa. Mamaki ne ya kamata tace “Ya Junaid!” "Dagowa yai ya kalleta kawai hawaye suka shiga gangaromai, gaba daya ya rasa ta ina ma zai fara." "Ganin yanda yake kuka ne hankalinta ya tashi karara, zama tai kusa dashi a hankali ta sa hannu" "kan fuskarsa, samun kanta tai da zubar da hawaye." Hannunsa yasa a kan hannunta cikin rawar baki ya kalleta yace “Binta. ” Kuka ne ya kwacekai wanda ya kara daga mata hankali sosai. "Kansa ya sa akan kafadarta yana kuka, itama hawaye kawai take tana shafar bayansa dan sam ta" kasa magana. "Ya dade a haka dan sunyi kusan awa daya a haka kafin ya share kwallarsa, dagowa yai ya kalleta" "tana hawaye, a hankali ya kakaro murmushi ya mata. Hannunsa ya daura kan fuskarta yace “kukan me kike?”" "Wasu hawayen ne suka gangaro tace “Nima bansani ba Yaya, zuciya ta na kuna ganin kana kuka," ban taba ganinka cikin irin wannan halin ba.” "Hannu yasa ya share mata hawayen sannan ya jawo kanta ya daura goshinta akan goshinsa," hakan yasa suna jin numfashin juna yace “Binta!” Hmm tace dan ta kasa amsawa. Yace “Bazan iya yafe musu ba dukansu.” "Suwa? Ta tambaya cikin sanyin murya, idanunsa ya runtse cikin kunar zuciya yana tuno abinda" ke faruwa. "Dago kanta tai ta rungumeshi, kasa magana tai sai kankameshi datai a jikinta." Idanunsa kawai ya rufe yana kara maimaita bazan yafe musu ba........ "Dagota yai kawai ya mike tsaye, kallansa tai tace “Yaya!”" "Murmushi yai yace “nagode Binta, samun ki kusa dani ba karamin karfi ya banni ba.”" "Kallansa take haryanzu batace komai ba, zan wuce." "Kai ta daga alamar to, ya juya ya wuceta zai fita." “Bazaka fadamin abinda ke damunka ba?” “Zan fada miki amma bayanzu ba.” Ya bude komar ya fita. "Da kallo ta bishi ta kasa tashi a gun, bata taba ganinsa yana kuka ba tunda take dashi, meya" sameshi? ******* "Bangarensa yaje, yai Sallah sannan ya ma Sabi’u sai da safe ya fito." "Bangaren Zeena suka nufa wacce tasha wanka cikin ruwan dayasha hadin turare, sannan ta turara" jikinta da turaren jiki. "Ba kwalloya tai na sai dai kamshin da take duk wanda ya ji sai ya yaba, ta taje kanta ta daureshi" da ribon. Abincin daren dake ajeye a gefe ta kalla sannan ta kalli Fure tace “Ya Junaid haryanzu?” jeFure ta sake fita sannan ta dawo tace “inaji yana hanya.” Kallan Fure tai tace “lekamin bangaren yarinyarcan ko yana can.” “Ah hb Gimbiya ai yasan kwanankine ya za’ai yaje can?” Wata harara ta buga mata tace “sau nawa nace ki dai fadamin abinda zanyi? Kinsan Allah kin kosa komawa gun Hajjo na canza ki.” Da sauri Fure tace “bari naje na dubo.” "Tana fita falo taji ana sanar da isowar Yarima, Junaid ne ya shigo ya wuce ciki." Zeena wacce dadi ya kamata ta mike tsaye tana jiranshi. "Yana shigowa ya kalleta, kallansa tai itama cikin jin dadi sannan ta kamo hannunsa tace“Yaya ka" iso?” Kallanta yai sannan yadanyi murmushi tare da kokarin zare hannunsa. Hannun ta sake rikewa sannan ta jashi zuwa inda aka jera abinci. Zama yai sannan ya kalleta. Kusa dashi ta zauna cikin salo da jan hankali ta zuba mai abincin sannan ta tura gabansa. "Shiru yai ya kurawa abincin ido yana nazari, spoon din ta dauka ta diba sannan ta nufi bakinshi" dashi. Kallan spoon din dake gabansa yai yana nazarin yaushe ma rabandayaci abinci yau? Karasa da spoon din tai daf da bakinsa hakan yasa ya kalleta sannan yasa hannu ya amshi spoon din yaci. "Murmushi tai sannan cikin jin dadi tace “Yaya da alama Hajjo bata sameshi ba, dazu Fure dana" aikata tace ran Hajjo a bace yake.” Kallanta yai sannan yace “ko?” "Kai ta daga tace “bansan ya akai ba, kuma Ramlatu ta tabbatar min yana can.”" Kallansa ta sakeyi tace “kana tunanin wani ya daukeshi?” Kila! Kawai yaci sannan ya ajiye spoon din ya mike yana kokarin zare hiramin daya yafa a kafarsa. "Mikewa tai a hankali tasa hannu a ta zagayo dashi ta cikinsa, ta kwantar da kanta a bayansa tace" “ Ya Junaid.” "Shiru yai baice komai ba, tace “ Ya Junaid!”" Juyowa yai ya kalleta ta sake zagayeshi ta bayansa hannu yasa zai zare hannunta ta sake hade hanayenta da kyau. Idanu ya kura mata yana tuno abinda akai domin sa? Anyi amfani dashi an salwantar da mahaifinsa. "Gaba daya yanayinsa ne ya canza, idanunsa ya runtse da karfi, sannan yace “kiyi hakuri Zeena" amma plz ki bani aran kwana uku.” Kwana uku? Ta tambaya cikin mamaki. "Hannunta ya zare sannan ya ajiye hiramin ya kwanta akan kujera yace “kwana biyu naki na binta daya kenan, kiyi hakuri.”" Shiru tai tana kallanshi cikin rashin jin dadin abinda ke faruwa. Daurewa tai ta matso tace “naji amma ka dawo gado mu kwana tare.” Hannunsa dake kan goshinsa ya sauke ya kalleta. Tace “bansan meya faru tsakaninka da Binta ba smms na tabbatar baka batta ta kwana ita kadai ba.” Ta dauka zaice wani abin sai gani tai ya mike ya kwanta akan gado. Haka zaka kwanta bakaci abincin bs? Idanunsa a lumshe yace “banajin ci.” Shiru tai tana kallansa....... ********* "Gaba daya Azeema ta kasa zaune ta kasa tsaye, tama rasa meke damunta, ji take kamar zatai" hauka. "Tayi kuka harta gaji, bata taba tunanin akwai wannan ranar da Junaid zai ji wannan kazamin al’" amarin data dauka ita kadai tasan sirrinta. Meyake nufi da Abdulsalam yayi amfani da ita? "Gsba daya kanta ya kasa nutsuwa, Bayan sallar magrib Barira ta shigota sanar da ita zuwan" Hajjo. Gaba daya batajin ganin kowa saboda abinda ke damunta sai dai ta tabbatar in taki ganin Hajjo zatai zargin wani abin. Haka ta fito gaba daya jiki a sanyeye sai dai tayi kokarin danne wa. Hajjo na zaune a falo Azeema ta shigo ta zauna. Hajjo ts zuba mata ido tace “Ina kika boye Sabisu?” Kallanta Azeema tai tace “mene?” Hajjo cikin gadara tace “badai sirri kuke boyewa ke da Abdulsalam ba?” Azeema ta daure tace“ke da kika dauke Sabisu shine kikazo dan ki sanar dani ko me? In kin kama sabisun me kike tunanin boyewa?” Kallanta Hajjo tai sannan tai dariya tace “mene?” Azeema ta daure itama tai dariya tace “inkin gams tambayoyin da zakimai kya aikon dashi. "Ta wuce ciki, Hajjo cikin kufula ta dau filo tai cilli dashi." ******** "Yana sallar asuba ya nufi bangaren Sarki dan kwana yai yana tunanin abinda zaiyi, yanzu kuwa ya" gama tattare nazarinsa. Sarki mamaki ne ya kamashi jin Junaid na neman iso da duku dukun safiyar nan. Junaid ne ya shigo ya gaisheshi sannan ya zauna. Sarki ya zauna yace “Junaid ya akai?” Kallansa Junaid yai batare da ya dauke idanunsa ba. Sarki cikin mamaki yace “Junaid!” “Me Marigayi ya sanar dakai lokacin da zai ce ka daukeni ka kaini kauyen nan?” Kallansa Sarki yai yace “me ya sanar dani? Ba abinda yacemin ka dauka yabar wasiyya ne?” "Junaid yai murmushi tare da sauke kansa kasa, kafin ya hade fuska tamau yace “ Ka dauka" abinda kuka aikata ba wanda zai sani har duniya ta nade?” Gaban Sarki ne yai wani mugun faduwa kallansa yai ya kasa cewa komai yana nazarin meya sani? ****** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {40} "Sarki yadan gyara nutsuwarsa yace ""Junaid wani shirman ka jiyu? Ina tunanin kai ka girmi aikata" "irin wadan nan shirmen.""" Shirme? "Sarki yace ""to nakasa gane me kake san cewa ne gaba daya.""" "Junaid ya kalleshi sannan yace ""ko mu bari anjima mu hadu a fada?""" "Abdulsalam cikin faduwar gaba yace ""mu hadu a fada ayi me?""" "Cikin zazzafan takaici da raunin zuciya ya kalleshi, idanun Junaid gaba daya suncanza sunyi jaa" "sosai, ya kalleshi bakinsa na rawa na bakin ciki yace ""bakaji kunyar kallan Umma dani ba? Baka taba kunyar halakar da mijinta da mahaifina ba sannan ka kallemu kamar ba komai?""" "Hankalin Sarki ne ya dugunzuma ya tashi ya daure yace ""nifa harayanxu. """ "Cikin zafin rai Junaid ya katseshi yace ""na hadu da Sabisu, ko haryanzu zaka cigaba da" "karyatawa?""" "Hankalin Sarki yanzu kam kiri kiri ya dugunzuma, yace ""Sabisu? Waye hakan?""" "Junaid cikin mamakin abinda yace yai dan murmushin takaici yace ""ta ina zaka sanshi dama?" "Kafin in sanar da mutane mugun abinda ka aikata kai gaggawar ajiye mulkin da ka kashe mahaifina duminsa, sannan ka jira hukuncin da ni saban sarki zan maka.""" "Sarki yanzu ya fahimci inda Junaid yasa gaba, kallansa yai yace ""komeya faru na tabbatar baka" "san mahaifiyarka bace sila? Sannan a dalilin ta cece ka ne akai wannan mumunan abin, shikanshi Zubair din daga baya yasan abinda ya faru.""" "Cikin tsananin raunin murya Junaid ya kalleshi yace ""Abba ya sani?""" "Abdulsalam yace ""ya san abinda mahaifiyarka ta sa ayi, hakan yasa ya daukeka ya bani na" "boyeka.""" "Ha ha ha. wata irin dariyar bacin rai Junaid yai yace ""a naka rashin fahimtar haka ka dauka?""" "Abdulsalam ya hade rai yace ""me kake san cewa?""" "Junaid ya kalleshi cikin zafin rai yace ""Ya baka nine yana san ganin iya kacin sanda zakai nadama," "sannan ya daukeni daga gunta ne dan ya nuna mata ta nustu ta fahimci halayenka, kana tunanin ya yarda da duk abinda ka fadamai ne?""" "Abdulsalam idanunsa ne suka fara canzawa ya turbune fuska yace "" ka shiga hankalinka Junaid," "duk sanda nakewa Azeema bais yafema danta ba in ya nemi shiga hurimina.""" "Junaid ya kalleshi yace ""ni nawa hurumin daka shiga fa?""" Huruminka? "Junaid cikin zafi yace ""mulkin naka ne? Ko kana tunanin badan Hajiya Inna ta rikeka ba har zaka" "samu damar kai kanka wannan matsayin?""" "Yanzu kam hucci kawai yakeyi, Junaid ya kalleshi yace ""kai gaggawar sauka daga kan mulkin nan," "kwana uku na baka, zanga da wani fuska zaka kalli mutane in sukasan tsubu kukai kuka halaka Sarki Zubair, daga kai har mukarabanka su Shamaki da Waziri da kuka hada baki.""" Juyawa yai ya fice. "Ya akai ya san komai yaran nan? Ya tabbatar Sabisu baisan ko rabin abinda ya faru ba, ya akai ya" sani? Azeema? Cikin hanzari ya mike ya nufi bangarenta. Tana kwance akan gado tsabar damuwa har dan zazzabi ne ya rufeta. "Tana kwance ya shigo, idanunta ta sauke kansa cikin zargi ta zuba mai ido." "Shigowa yai ya zauna kusa da ita, yace ""kin fadawa Junaid komai hankalinki ya kwanta?""" "Kallansa tai idanunta sun ciciko tace ""kenan amfani kai dani ka kashe sarki a matsayin ka ceceni" "saboda san da kake min?""" "Abdulsalam ya kauda kai, mikewa zaune tai cikin takaici tace ""yaune rana ta farko dana taba" "dana sani san da na maka a baya ina mugun dana sanin aurenka da nai, wadan nan sune babban kuskuren dana tafka a rayuwata, wanda bazan taba yafewa kaina ba.""" "Abdulsalam ya kalleta zuciyarsa na kuna yace ""saboda wa na aikata duk abin da na aikata? Ko" "kina tunanin saboda kaina nai? Duk abinda na aikata nayi ne saboda tsananin sanki da nake, ko kina tunanin zan iya cigaba da ganinki tare da Zubair ne? Sannan saboda wa na aikata abinda na aikata.""" "Ranta a bace ta sa hannu ta tureshi, tace ""karka kuskura kace saboda nine, a haukata da haka na" "dauka amma yanzu nasan babu ni a cikin tunaninka, kayi amfani da halin da nake ciki ne ka biya burin dake ranka.""" "Sarki ya kalleta yace ""koma menene yanzu bashida amfani, abinda ya faru ya faru, ki fadawa" "Junaid ya manta komai, yazo yana min kashedin na ajiye mulki nan da kwana uku, ke kinsan ba abu mai yiwuwa bane kinsan halina kinsan abinda zanyi da wanss bazan ba.""" "Ya juya ya fita, ihu ta kwalla tare da sa kanta cikin cinyarta." ****** "Hajjo ce ta kalli Zubair tace ""da sassafen nan?""" "Zubair yace ""da kaina na ganshi Hajjo, bansan me suka tattauna ba amma ransa a bace naga ya" "fito.""" "Hajjo tace aika a tambayo Zeena muji ko ta sani, kallanta yai yace ""wannan yanda take san Junaid" "zata fadi wani abu ne?""" "Hajjo cikin kuluwa tace ""aka mugani ko za'a dace """ "Junaid yana fitowa ya kalli bangaren Binta, ya kalli na Zeena, sannan ya kalli nashi sanda ya boye" "Sabisu, Binta yake san gani amma yana tsoron sata cikin wani hali, bangaren Zeena ya wuce. Sai" "yanzu tai sallah, tana kokarin kwanciya taga anbude kofa anshigo." "Cikin mamaki da jin dadinta kalli Junaid, bata taba kawowa zai dawo ba." Tunawa yai ashefa yar Abdulsalam ce ko? "Juyawa yai da sauri ta sako tace ""Ya Junaid.""" "Kallanta yai ta matso cikin jin dadi tace ""nagode daka dawo.""" Ya zataji in taji mugun halin babanta? Zeena ce ta kalleshi tace “Ya Junaid?” Kallanta yai yasan tabbas batada matsala duk rashin tarbiyya na gari ne ke damunta sai babbar "matsalarta isa data mata yawa da rashin hakuri, kallanta yai sannan ya wuce ya kwanta." Kaina kedan ciwo nake san kwantawa. Cikin jin dadi ta matsa kusa dashi ta kwanta sannan ta kankameshi. "Kamar zai tureta sai kuma ya fasa hannu yasa ya riketa, ajyar zuciya tai na jin dadi." "Tausayinta yake, yasan itama sai ta shiga wani hali." Bacci ne ya daukeshi dan dama baiyi bacci ba jiya. "Yana tashi yaga bata nan, ruwa yaji a toilet da alama wanka take, fitowa yai ya bar mangaren." Hadimans suka bi bayanshi. "Bangaren Binta ya kalla, kamar ya je kamar kar yaje, daurewa yai kawai ya kalli Hadiminsa yamai" alama. Nan suka sanar da zuwanshi. "Binta wacce tai wanka tana zaune tasa abincin safe a gaba tana jujuyawa, jin Junaid yasa ta tashi cikin hanzari ta bude." Yana shigowa ya kalleta yana dariya yace “ya ganki kinyi wani iri? Kamar mara lafiya?” "Shiru tai kawai tana kallansa, Ahhh tunda ba’a san ganins da alama bari na juya." Da sauri tace “a’a yaya.” Juyowa yai yana dariya yace “na sani ai.” Rungume ta yai yace “ina wannan zatace batasan ganins?” Tace “in nace fa?” Yace “hmm duk randa kika fada kinada kyauta.” Dagowa tai tace “ka tabbatar?” Yace “sosai.” Murmushi tai sannan tace “Yaya komai dai lafiya ko?” Kara rungumeta yai yace “komai zai zama lafiya insha Allah.” Murmushi tai sannan tace “Allah yasa.” "Kallanta yai yace “inata san na tambayeki, kin tabbatar bakyasan a aikama mahaifinki kinyi" aure?” Kai ta girgiza da sauri tace “in ma ya sani me zai min? Ka manta abinda ya mana?” Hannunta ya kama ya zaunar da ita gaban abincin sannan yadau cup din tea dinta ya kurba sannan ya mika mata. "Amsa tai ta kurba ba tare da ta musa ba, tsamen dake gabanta ya dauka ya kai bakinta, ba musu" ta bude bakin yasa mata sannan yace “zan tura Azi ya nemoshi.” Kallansa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa sai murmushi da tai kawai ba tare da tace komai ba. Gefen kanta ya shafa yace “yau Bintoto...” Ture hannun tai ta harareshi tace “Ya Junaid kasan banasan sunan ko?” Dariya yai yace “Bintalo...” Ajiye cup din tai tace bazan maci ba. Na tuba a yafemin. Dariya tai tace “sai ka fadi abin.” Yace ah to bari na shirya. Hanayenta ta hade tana jiransa. Dariya yai yace “Nana Fadima na tuba. ” Dariya yai sosai shikuma ya hade fuska. Tace “Ya Junaid dan sake.” Naki din. Ya fada cikin wasa....... Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {41} Kallan Azi yai yace “ka fita wajen gari ka yadamin jita jita cewar Sarki Abdulsalam ganin dawowar asalin dan Sarki Zubair yasa zaiyi Murabus ya ba asalin magajin sarki mulkinsa.” Azi ba tare da tambaya ba yace “To Yarima.” "Nan Ya fita da wasu hadiman Junaid, haka sukai ta yadawa tun daga cikin fada har wajen" masarauta. ******* "Sam Abdulsalam ya kasa zaune ya kasa tsaye, afa da marwa kawai yakeyi a cikin kilisarsa." Isowar su Shamaki ce yasa ya koma ya zauna. "Cikin tashin hankali suka shigo, Mai Martaba meke faruwa?" Abdulsalam ya kallesu yace “yaran nan ya san komai.” Galadima yace “taya za’ai ya sani abinda akai yana tsimma? Hatta wanda yai maganin fa mun ga bayansa.” "Abdulsalam yace “to kamar mai aljannu yaran nan hankali a kwance yazo ya sanar dani komai," Sabisun kansa baisan abinda ya faruba rabi da kwata in dai har ba aljanu ne dashi ba to ba yanda za’ai ya sani.” Waziri ne cikin nazari yace “ko dai Gimbiya ta fadamai abinda ta sani ne?” Taya zata fadi abinda tasan zai ja mata matsala? Shiru sukai suna tunanin abinyi. Jakadiya daga waje ta nemi iso cikin tashin hankali. Kallan juna sukai sannan sukace lafiya? Jakadiya ce ta shigo ta zube tace “Allah ya taimaki sarki yanzu labari ya karade ko ina akan wai zakai murabus.” Hankali a tashe suka kalli juna sannan a tare sukace “Murabus?” "Jakadiya tace “wai zaka maida sarauta inda take, tunda magajin sarki ya dawo.”" Cikin tsakanin tashin hankali sukace “magajin sarki? Junaid?” Jakadiya tace “ ka gafarce amma zance ya gama karade gari anata jinjinawa adalcinka.” Sallama tai ta fito. "Ba karamin tashin hankali bane ya bayyana a fuskokinsu, musammsn Abdulsalam wanda yakeji" duk duniya ba mai rabashi da kujerar mulkinsa. "Shamaki ne yace “yanzu ya zamuyi? Ya riga ya samu a karshen layin da babu mabula, yanzu" "inkace bazaka bashi ba mutane zasu fara zargin halayarka gaba daya mutane zasu bar bayanka," sannan inka bashi mu kuma gaba daya tamu ta kare.” Ran Galadima a bace yace “wai yaran nan ba sirikinka bane?” "Gaba daya hucci kawai Abdulsalam yake, yama rasa me zaice." ******** "Zeena na zaune Hajjo ta aiko tazo, tace “ace mata zanzo anjima." Kafafunta da ake gyara ma farce ta kara mikawa sannan ta kalli Fure tace “waccen matar mara galihu tana ina?” Fure tace “tana bangarenta ranki ya dade.” Baki Zeena ta tabe sannan tace “Yarima fa? Ta tambaya cikin alamar tambaya mai karfi. "Fure ta fita da sauri dan dubawa, bata dade ba ta dawo cikin jin dadi tace “bayacan Gimbiya.”" Dadi ne ya kama Zeena tai murmushin farin ciki. "Hadimar Hajjo ce ta shigo cikin tashin hankali tace “Gimbiya, Hajjo na nemanki cikin gaggawa.”" Zeena ta kalleta tace “kai!” Kamar zata sake magana sai kuma ta mike ta zura alkyabarta wace ke kara mata kyau suka fito. Mamaki ne ya kama Zeena ganin Hajjo a bakin kofa. Tana ganin Zeena ta ja hannunta suka shiga ciki. "Ramlatu, Zubair da kanin Hajjo Suna zaune a kilisar." Hajjo ta zaunar da ita a kasa a gabanta tace “fadamin dake a ka hada baki?” Zeena cikin rashin fahimta tace “aka hada baki a me?” "Bakin Hajjo ne ya fara kumbura, fuska ta turbune cikin kunar rai tace “uban waye ya isa yasa" Sarki murabus?wato ke dan hauka mijin da kwata kwata baki dade da aura ba shine yafi mahaifinki ko?” Zeena tace “nifa bansan me kike cewa ba.” "Ramlatu ce tace “nifa nafi tunanin Azeema ce, matarnan ba karamin shiri ta iya ba.”" "Hajjo cikin tsananin bacin rai ta kalli Zubair dake zaune kamar zaiyi kuka, tace “haka kawai an" "yada wai Sarki zaiyi murabus yaba asalin magaji mulki, inba Junaid ba wazai yadda wannan abin?”" "Zeena ta mike tace “ni wlh na dauka ma wani abin ne, to in an yada dama ba mulkinsa bane, tun" asali nashi ne dan yace yana san abinsa laifi ne?” "Hajjo ce ta mike ta daga hannu kamar zata kifa mata mari sai kuma ta tsaya tana hucci, Zeena" kam kyar take ba alamar tsoro tace “Wai Hajjo sai yaushe zaki daina tunanin ba ya Zubair mulkin nan? Bayan ke kanki kinsan bashi da abinda Sarki yake dashi? "Ran Hajjo ya kara kololuwa gun baci, Zubair ne yace “bani dashi kuma a hakan zan amshi" "hakkina, daga yau Hajjo karki kara kirana ki kira yarinyar nan.”" "Juyawa tai ta fita rai a bace, Hajjo cikin tsananin takaici ta bita da kallo." ****** Barira ta kalla tace “mene?” Barira ta kara sanar da ita tace “yanzu duk abinda yake yawo keman a masarautar nan.” "Komawa tai ta kwanta, saboda zazzabi da ciwon kai data kwana dashi, kallan Barira tai tace" "“Barira ki aika a kiran Junaid, kice a fadamai banda lafiya.”" "Nan Bari tace dakaina ma zani, ta fita." Junaid na zaune suna dan hirar da shida Sabisu yana bashi labarin Sarki Zubair aka sanar da isowar Barira. Sabisu ne ya shiga ciki sannan ya bata dama. Zubewa tai ta gaisheshi sannan ta sanar dashi aiken Gimbiya. Kallanta Junaid yai yace “Allah ya bata lfy.” Barira ta dan dago tace “Yarima rabanta da abinci tun jiya shima dakyar tasha kunu.” Kallanta Junaid yai yace “ki koma ki kula da ita tafi kowa sanin bazan zo ba.” "Barira ta bude baki zatai magana Junaid ya mata wani kallo, mikewa tai ta mai sallama ta fita." Jin yanda sukai da Junaid yasa Azeema tai murmushin takaici tace “nasan nima bazsi taba zuwa ba sai dai zuciyata na fatan zaizo din.” Barira tace “Gimbiya dukda bansan meke faruwa ba amma dan Allah kici abinci.” Tashi ki fita. Mikewa tai har zata fita sai Azeema tace “kiramin Binta.” Kallan ta tai da sauri tace “Binta?” Kai Azeema ta daga cikin azabar ciwon da kanta ke mata. "Binta tana zaune tanata gyara fuskarta, dan itama so take ta dinga fitowa das kamar Zeena." "Tayi kokari sosai dan tayi kyau, yanzu bata komai saboda jiya Harira ta kawo mata hadimai su" uku. Barira ce ta sanar da ita sakon Gimbiya. "Cikin jin dadi ta mike, kallan Barira tai tace “bari na aikama Yaya Mu tafi.”" "Nan ta tura aka sanar da Junaid, kamar ya hanata sai yaga inya hanata tabbas xatai xargin wani" abin. ****** Nan suka fito. Suna kokarin barin kofar Zeena na dawowa daga bangaren Hajjo. "Kallan Juna sukai ita da Binta, kafin Binta ta gaisheta, Zeena cikin isa ta amsa su kuma suka" wuce. Cikinta shiga. *** "Binta ta shiga cikin daki, Azeema na kwance, hannu Azeema ta mika mata alamar ta matso inda" "take, mamaki ne ya kama Binta ta kasa matsawa harsai da Barira tace “Binta ki karasa.”" Azeema dake zaune Binta na matsowa ta kama hannunta cikin dana sani da takaicin abinda ta aikata. Binta! Kallanta Binta tai cikin sanyi. Azeema tai murmushi tace “Junaid fa? Yana nan lfy?” Binta ta daga kai alamar eh. Barira ta kalla ta mata alamar ta fita. Nan ta juya ta rufo musu kofa tana mamakin meke damun Gimbiya? Yau ita ke yima Binta haka??? Nace daga baya kenan Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {42} "Gaba daya jikin binta ne yai sanyi, yanda Azeema ke rike da hannunta." Can tace “Mamanki kince ta rasu ko?” Kai Binta ta daga cikin sanyin jiki. Murmushi tai tace “kiyi hakuri ban dubi maraicinki na jaki a jiki ba.” Binta ta share kwallar da ta zubo mata. Babanki fa? "Tunda ya koremu bansake komawa ba, sai dai bayan na girma munganshi da yaya shima yayan ne ya kaini sai dai bamuyi magana ba.”" Dayan hannunta ta dan daura a saman hannunta data rike. "Binta ta kalleta tace “nice mai laifi, na san ko wanene dole yaki amincewa dani, balle dan sarki?”" "Kai Azeema ta girgiza tace “ko kadan san kai da dan zuciya ne irin nawa, a koda yaushe ina" "dauka nice nake tafiyar da rayuwata sai dai yanzu na fahimci duk rayuwata amfani ake dani, san" kai dana ke tunanin ina dashi na gane duk shi ya jamin wannan rayuwar dana sa kaina.” Binta bata san me take nufi ba hakan yass ta kslleta ganin yanda Azeema tai shiru cikin wani "yanayi, daurewa tai ta kalleta tace “karki damu da halin da nake ciki ni nasa kaina a ciki.”" *********** "Junaid ne ya kalli waje, ganin rana tadan fara sanyi ya kalli Azi yace “muje.”" "Nan suka fito, Junaid ya sa kaya wanda ko ranar bikinsa baiyi irin wannan kyan ba, Alkyabar dake" "jikinsa mai tsananin kyau ce tamai kyau sosai, yayi rawani wanda bayi yake yi ba in ba da dalili ba." "Tunda suka fito ake gaisheshi, har suka isa fadar sarki." Sarki wanda ke zaune cikin fada ya kalli manyan masu mukamai dukansu da suka iso akan abinda sukaji. "Turaki ne ya kalleshi yace “Dolene mu taso jin wannan babban al’amari, taya Ranka ya dade" zaka yanke wannan babban hukunci ba tare da munsan komai ba.” "Sarki ne ya kalleshi, Waziri ya dafa Shamaki wanda yaga yana neman yin magana, Shamaki cikin" "takaici ya kalli Galadima wanda shima ya cika ya batse, Sarki ne ya kalli Turaki bayan yayi murmushi yace “to mudai wannan magana. ”" Kafin ya karasa aka sanar da isowar Junaid. "Hankalin Abdulsalam a tashe sai dai baiko kalli kofa ba, isowar Matawalle Junaid ne yasa duk" kowa ya zubawa kofa ido. Junaid ya shigo sannan ya gaisuwa ya ja ya zauna. Sarki ne ya kalleshi yace “Matawalle kaima ka fito?” Junaid yai murmushi yace “munzo ban hakuri ne akan abinda kake neman aikatawa.” Kallanshi Sarki yai a ransa yace “me kuma kake shirin yi?” Junaid ya sunkuyar dakai yace “Tuba nake ranka ya dade amma ina ganin hukunci da umarninka na ajiye mulkin nan yayi tsauri.” "Kallansa sukai da sarki dasu Shamaki, gaba daya shamaki da Galadima sun bude baki, Junaid ya" dan kara dagowa yace “kace haka kama Marigayi Sarki Zubair alkawari amma ina ganin a sake dubawa.” Gaba daya kasa magana sukai saboda tsananin mamakin wannan dabaibaiyo daya faru. "Turaki ya kalli Sarki yace “Amincin Allah ya tabbata a gareka, ashe alkawari kukai da sarki?”" Nan ragowar na fada suka fara jinjina ma imani da adalci irin na Sarki.” "Wale ne ya kalli Sarki yace “gaskiya Sarki Allah yasa ka gama da duniya lafiya, ba karamin" "mamaki mukai ba da jin wannan abun, da ranmu ya baci amma jin dalilinka yasa mun fahimci" abinda kake nufi.” Allah ya sa haka ne mafi alkairi. Nan kowa yace Ameen "Gaba daya kwakwalwar Abdulsalam ta kulle, kallan Junaid ya shiga yi, Junaid yai murmushi" sannan ya kallesu yace “ku ba Sarki hakuri taya zan hau mulki bayan da karfinsa?” Turaki ne ya kalli Sarki yace “Takawa kaji abinda yace? Sai dai nasan alkawarin sarakuna ba’a ajiye shi.” "Da kyar Sarki ya daidaita nutsuwar sa sannan yace “To ka gani, dole dai ayi abinda ya dace.”" Junaid ne ya sake yin kasa dakai yace “ku ba Takawa hakuri ba jibi na ya bari sai nan da shekara.” Jibi? A tare suka fadq harshi sarkin dai baisan ya fadi hakan ba. "Kallansa sukai jin muryarsa, murmushi yai yace “Jibin dai.”" Turaki yace “Allah ya kara ma yawan rai.” Sarki ne ya kallesu yace “kaina nadan ciwo ina san shiga ciki.” Nan suka kara gaisheshi ya fita. Waziri dasu Shamaki suka fita suma. Junaid ya tsaya suna ta gagaisawa dasu kafin ya fito. Yana sa takalminsa ana sanar dashi Sarki na nemansa. Bai musa ba ya nufi bangarensa kai tsaye. "Sarki na tsaye ya juya baya gaba daya hankalinsa ya kai kolokuwa gun tashi, idanunsa sunyi jaaa" alamar tashin hankali. Junaid ne ya shigo ya zauna zaman cin abinci a kasa sannan ya daura hannayensa a kan cinyarsa baice komai ba. Juyowa yai ya kalleshi Junaid na zaune yana kallansa shima. Cikin tsananin bacin rai Sarki ya kalleshi yace “me kake shirin yi?” Junaid ne ya kalleshi yace “kai me kake shirin yi?” Baki Abdulsalam ya bude yace “ni kake fadawa magana haka kanka tsaye?” Ya kake so nawa makiyina magana? "Makiyi? Abdulsalam ya maimaita cikin jin haushi, Junaid na fada maka duk abinda ya faru akan" mahaifiyarka ne ko? Ko duk ba akanka aka aikata ba?” Wani murmushi yai yace “ita kenan itace zata yadda akanta ka aikata amma ni dakai munsan ba a kanta ka aikata ba.” Hura hanci yai yace “Kasan ka kiyayeni?” Junaid yai murmushi yace “duk abinda zaka aikata min inaso ka tuna abu biyu na farko kowa "yasan ni zaka ba mulki jibi dan haka duk abinda ya sameni cikin dayan biyu ne ko kai ko Zubair danka ne, to sai dai matsalar na riga na sanarwa yarka duk abinda ya saman kaine, kaga shaidarta" ta isa komai naka ya wargaje.” "Gaba daya Abdulsalam ya gama shan jinin jikinsa, ya kalli Junaid yace “to ka fito ka sanar da" duniya laifin nawa mana.” "Junaid yai dan dariya yace “ karka damu komai da lokacinsa, sannan ina duba darajar yarka ko" "nace wacce ka bani ita saboda kana san boye laifinka ne, hakan yasa bazan fada ba, sai dai wannan shine kashaidi na karshe da zan ma, daga gobe ka tattara ka koma inda aka ajiyeni na zauna ko kuma ka nemi wani gidan ka zauna inba haka ba duk abinda ya biyo baya karkaga laifina," inada shaidu da zan lalata ma suna cikin mintina kadan wanda fita ma gagararka xatai.” "Mikewa yai zai fita, ita Azeemar fa? Badai kana tunanin ajiyeta anan ba?" Junaid bai kalleshi ba yace “duk wani mai laifi sai ya amshi laifinsa ko itace kuwa.” Ya juya ya fita abinsa. Yana fita Abdulsalam ya saki wani kara tare da zama a kan gado cikin tsananin bacin ran da tunda yazo duniya bai taba fuskan tarshi ba. ***** Zeena ce ta kalli Fure tace “da gaske hakan ake yadawa?” Fure tace “yanzu ma jinai ance wai jibi Sarki zaiyi murabus.” Shiru tai tana nazari meke faruwa Ya Junaid? Hajjo kam cikin kumburin baki ta sabi alkyabarta ita da Zubair suka nufo bangaren Sarki sai dai an sanar dasu bazai gansu ba. Wannan abu ya kara koma mata rai matuka wanda takeji ko zata kwana a wajen nan bazata tafi ba sai ta ganshi.... **** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {42} "Gaba daya jikin binta ne yai sanyi, yanda Azeema ke rike da hannunta." Can tace “Mamanki kince ta rasu ko?” Kai Binta ta daga cikin sanyin jiki. Murmushi tai tace “kiyi hakuri ban dubi maraicinki na jaki a jiki ba.” Binta ta share kwallar da ta zubo mata. Babanki fa? "Tunda ya koremu bansake komawa ba, sai dai bayan na girma munganshi da yaya shima yayan ne ya kaini sai dai bamuyi magana ba.”" Dayan hannunta ta dan daura a saman hannunta data rike. "Binta ta kalleta tace “nice mai laifi, na san ko wanene dole yaki amincewa dani, balle dan sarki?”" "Kai Azeema ta girgiza tace “ko kadan san kai da dan zuciya ne irin nawa, a koda yaushe ina" "dauka nice nake tafiyar da rayuwata sai dai yanzu na fahimci duk rayuwata amfani ake dani, san" kai dana ke tunanin ina dashi na gane duk shi ya jamin wannan rayuwar dana sa kaina.” Binta bata san me take nufi ba hakan yass ta kslleta ganin yanda Azeema tai shiru cikin wani "yanayi, daurewa tai ta kalleta tace “karki damu da halin da nake ciki ni nasa kaina a ciki.”" *********** "Junaid ne ya kalli waje, ganin rana tadan fara sanyi ya kalli Azi yace “muje.”" "Nan suka fito, Junaid ya sa kaya wanda ko ranar bikinsa baiyi irin wannan kyan ba, Alkyabar dake" "jikinsa mai tsananin kyau ce tamai kyau sosai, yayi rawani wanda bayi yake yi ba in ba da dalili ba." "Tunda suka fito ake gaisheshi, har suka isa fadar sarki." Sarki wanda ke zaune cikin fada ya kalli manyan masu mukamai dukansu da suka iso akan abinda sukaji. "Turaki ne ya kalleshi yace “Dolene mu taso jin wannan babban al’amari, taya Ranka ya dade" zaka yanke wannan babban hukunci ba tare da munsan komai ba.” "Sarki ne ya kalleshi, Waziri ya dafa Shamaki wanda yaga yana neman yin magana, Shamaki cikin" "takaici ya kalli Galadima wanda shima ya cika ya batse, Sarki ne ya kalli Turaki bayan yayi murmushi yace “to mudai wannan magana. ”" Kafin ya karasa aka sanar da isowar Junaid. "Hankalin Abdulsalam a tashe sai dai baiko kalli kofa ba, isowar Matawalle Junaid ne yasa duk" kowa ya zubawa kofa ido. Junaid ya shigo sannan ya gaisuwa ya ja ya zauna. Sarki ne ya kalleshi yace “Matawalle kaima ka fito?” Junaid yai murmushi yace “munzo ban hakuri ne akan abinda kake neman aikatawa.” Kallanshi Sarki yai a ransa yace “me kuma kake shirin yi?” Junaid ya sunkuyar dakai yace “Tuba nake ranka ya dade amma ina ganin hukunci da umarninka na ajiye mulkin nan yayi tsauri.” "Kallansa sukai da sarki dasu Shamaki, gaba daya shamaki da Galadima sun bude baki, Junaid ya" dan kara dagowa yace “kace haka kama Marigayi Sarki Zubair alkawari amma ina ganin a sake dubawa.” Gaba daya kasa magana sukai saboda tsananin mamakin wannan dabaibaiyo daya faru. "Turaki ya kalli Sarki yace “Amincin Allah ya tabbata a gareka, ashe alkawari kukai da sarki?”" Nan ragowar na fada suka fara jinjina ma imani da adalci irin na Sarki.” "Wale ne ya kalli Sarki yace “gaskiya Sarki Allah yasa ka gama da duniya lafiya, ba karamin" "mamaki mukai ba da jin wannan abun, da ranmu ya baci amma jin dalilinka yasa mun fahimci" abinda kake nufi.” Allah ya sa haka ne mafi alkairi. Nan kowa yace Ameen "Gaba daya kwakwalwar Abdulsalam ta kulle, kallan Junaid ya shiga yi, Junaid yai murmushi" sannan ya kallesu yace “ku ba Sarki hakuri taya zan hau mulki bayan da karfinsa?” Turaki ne ya kalli Sarki yace “Takawa kaji abinda yace? Sai dai nasan alkawarin sarakuna ba’a ajiye shi.” "Da kyar Sarki ya daidaita nutsuwar sa sannan yace “To ka gani, dole dai ayi abinda ya dace.”" Junaid ne ya sake yin kasa dakai yace “ku ba Takawa hakuri ba jibi na ya bari sai nan da shekara.” Jibi? A tare suka fadq harshi sarkin dai baisan ya fadi hakan ba. "Kallansa sukai jin muryarsa, murmushi yai yace “Jibin dai.”" Turaki yace “Allah ya kara ma yawan rai.” Sarki ne ya kallesu yace “kaina nadan ciwo ina san shiga ciki.” Nan suka kara gaisheshi ya fita. Waziri dasu Shamaki suka fita suma. Junaid ya tsaya suna ta gagaisawa dasu kafin ya fito. Yana sa takalminsa ana sanar dashi Sarki na nemansa. Bai musa ba ya nufi bangarensa kai tsaye. "Sarki na tsaye ya juya baya gaba daya hankalinsa ya kai kolokuwa gun tashi, idanunsa sunyi jaaa" alamar tashin hankali. Junaid ne ya shigo ya zauna zaman cin abinci a kasa sannan ya daura hannayensa a kan cinyarsa baice komai ba. Juyowa yai ya kalleshi Junaid na zaune yana kallansa shima. Cikin tsananin bacin rai Sarki ya kalleshi yace “me kake shirin yi?” Junaid ne ya kalleshi yace “kai me kake shirin yi?” Baki Abdulsalam ya bude yace “ni kake fadawa magana haka kanka tsaye?” Ya kake so nawa makiyina magana? "Makiyi? Abdulsalam ya maimaita cikin jin haushi, Junaid na fada maka duk abinda ya faru akan" mahaifiyarka ne ko? Ko duk ba akanka aka aikata ba?” Wani murmushi yai yace “ita kenan itace zata yadda akanta ka aikata amma ni dakai munsan ba a kanta ka aikata ba.” Hura hanci yai yace “Kasan ka kiyayeni?” Junaid yai murmushi yace “duk abinda zaka aikata min inaso ka tuna abu biyu na farko kowa "yasan ni zaka ba mulki jibi dan haka duk abinda ya sameni cikin dayan biyu ne ko kai ko Zubair danka ne, to sai dai matsalar na riga na sanarwa yarka duk abinda ya saman kaine, kaga shaidarta" ta isa komai naka ya wargaje.” "Gaba daya Abdulsalam ya gama shan jinin jikinsa, ya kalli Junaid yace “to ka fito ka sanar da" duniya laifin nawa mana.” "Junaid yai dan dariya yace “ karka damu komai da lokacinsa, sannan ina duba darajar yarka ko" "nace wacce ka bani ita saboda kana san boye laifinka ne, hakan yasa bazan fada ba, sai dai wannan shine kashaidi na karshe da zan ma, daga gobe ka tattara ka koma inda aka ajiyeni na zauna ko kuma ka nemi wani gidan ka zauna inba haka ba duk abinda ya biyo baya karkaga laifina," inada shaidu da zan lalata ma suna cikin mintina kadan wanda fita ma gagararka xatai.” "Mikewa yai zai fita, ita Azeemar fa? Badai kana tunanin ajiyeta anan ba?" Junaid bai kalleshi ba yace “duk wani mai laifi sai ya amshi laifinsa ko itace kuwa.” Ya juya ya fita abinsa. Yana fita Abdulsalam ya saki wani kara tare da zama a kan gado cikin tsananin bacin ran da tunda yazo duniya bai taba fuskan tarshi ba. ***** Zeena ce ta kalli Fure tace “da gaske hakan ake yadawa?” Fure tace “yanzu ma jinai ance wai jibi Sarki zaiyi murabus.” Shiru tai tana nazari meke faruwa Ya Junaid? Hajjo kam cikin kumburin baki ta sabi alkyabarta ita da Zubair suka nufo bangaren Sarki sai dai an sanar dasu bazai gansu ba. Wannan abu ya kara koma mata rai matuka wanda takeji ko zata kwana a wajen nan bazata tafi ba sai ta ganshi.... **** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {43} "Binta tana dawowa daga bangarenta taga Fure a bakin kofar sashenta, da sauri fa karasa." "Fure na ganinta ta azamo itama ta gaisheta. Binta ce ta kalleta tace ""lafiya?""" "Fure tace ""Gimbiya ke san ganinki.""" Ba ta kawo komai ba ta bi bayanta suka nufi sashen Zeena. "Tana zaune a kilisarta Binta ta shigo, sai data gaisheta sannan Zeena ta sallami yan falan, kallan" "Binta tai sannan tace ""Yarima ya fada miki wani abu ne?""" "Kallan ta Binta tai cikin rashin fahimta tace ""kamar me kenan?""" "Zeena cikin isa tace ""koma menene abinda dai ya shafeshi a wannan lokacin.""" "Cikin mamaki Binta tace ""banji komai ba sai dai in ke bansan ko kinji wani abin ba."" Ta fada cikin" dakewa. "Mamaki ne ya kama Zeena yanda ta maida mata magana, sai dai yanzu ita duk ba wannan bane" a gabanta. "Kallanta tai tace ""Yace yana da abubuwan da yake so ya kammala a kwana uku, yau ne karshen kwana na farko, saura kwana biyu kenan, shi yasa nake san ji ko ya fada miki sama da haka.""" "Basuyi wannan maganar da Ya Junaid ba, kenan ita yake fadawa matsalarsa? Daurewa tai ta" "kalleta tace ""nima abinda yacemin kenan, sai dai ya kara abu daya.""" Zeena ta kalleta tace mene? "Shiru binta tai tana tuno abinda zata ce can tace ""Yana san muyi hakuri har saikomai ya kammala sai nan zai samu nutsuwar fuskantar matanshi.""" Zeena ta kalleta rai a bace kenan magana take fada mata akan karyai datai ya kwana da ita? "Binta ce ta kalleta tace ""Gimbiya bada wani abin ma fada ba ina fada miki abinda na sani ne.""" "Zeena ta daure tadan daga girarta kadan kafin tace ""kinsan zancen Sarkin yanzu zaiyi murabus ya" "ba Junaid mulki?""" "Mamaki me karara ya bayyana a fuskar Binta, wanda kallo daya xaka mata kasan tana cikin tsananin mamaki, kafin Zeena tace ""kinsan kuma murabus din jibi ne?""" "Binta tace ""bashida lafiya ne?""" "Zeena tace ""a'a lafiyar Abba kalau shiyasa na kiraki dan naji, ko kinji wani abin ne.""" "Dana sani Binta tai da yimata wancan zancen, kanta tai kasa dashi tace ""kiyi hakuri Gimbiya" "bansan manufarki ba.""" "Kai Zeena ta girgiza alamar bakomai tace ""nina fara sannan ba laifi bane in kin rama, haka ake" "san matar dan sarki bawai kiyi ta bari ana taka ki ba, gaba daya ni na rasa yanda zanyi nasan abinda ke faruwa, shi yasa na ajiye girmana da matsayina na tambayeki.""" "Binta tace ""Kina ganin akwai dalilin sa na yin hakan kenan?""" Shiru Zeena tai dan gaba daya tunda taji jibi xa'ai abin ko nutsuwa ta kasayo gaba daya. Ta tabbatar da abinda ke faruwa amma batasan menene ba. "Kallan Binta tai tace “shikenan jeki kawai, Binta cikin damuwa tai sallama ta fita." Fitowa tai ta kalli Fure tace “haryanzu baya bangarensa? Tace eh. Kallan Fure tai tace “ina san zuwa gun Ramlatu.” Fure tace “dare yayi Gimbiya.” Zeena tai shiru cikin tsananin damuwa. ***** Binta na fita bangaren Junaid taje sai dai Azi yace mata bayanan tun yamma ya fita. Shiru tai kafin ta kalli duhun da garin yai bari tai sallah in bai dawo ba ta fita. Bangrenta ta nufa ta wuce daki. "Ba karamin tsoro taji ba ganin mutum lulube da bargo, wutar dakin a kashe." "Tsayawa tai kafin ta nufi gun a hankali, Junaid ne kwance a kan gado ya dukunkune da bargo." Kusa dashi taje da sauri ta zauna a gabansa tace “Ya Junaid?” Idanunsa ya bude a hankali ya kalleta sannan yai dan murmushi yace “Bintalo ta dawo?” "Hankali a tashe tasa hannu akansa, hannunta ya rike yace “lafiya ta kalau.”" Ajiyar zuciya tai murmushi ya sakeyi sannan ya kalli idanunta wadanda suka ciciko tana neman kuka yace “karki fara lafiyata kalau.” "Kallansa tai ta kasa magana, mikewa yai ya zauna sannan yasa hannu ya jawota kan cinyarsa ya" rungumeta sannan ya fita da wata iska daga bakinsa. Cikin raunin murya tace “Ya Junaid lafiya dai ko?” "Lafiya kalau, me Umma tace miki?" "Dan juyo da kanta kadan tai ta kalleshi tace “hskiri ta bani, ni duk kunya ma ta kamani.”" "Shiru yai baice komai ba, ta kara cewa “Amma yaya Umma fa ba lafiya kuma naga bakaje ba.”" Kara rungumeta yai yace “ke kinjemin ai.” Tace “taya zanje ma bayan nasan tana san ganin danta.” "Bakinta yakaiwa sumba sannan ya kalli idanunta dake lumshe ya sumbacesu, cikin rada yace" “kinyi sallah ne?” "Idanunta ta bude tana murmushi, tare sukai sallah ya dade yana addu’oi dan har ta jingina da" bango. "Junaid ya kalleta sannan ya sa hannu ya kwantar da kanta akan cinyarsa, yatsarsa yasa yana" shafa girarta yace “me kika jiyo a waje?” "Kallansa tai tace banji komai ba amma naji yanzu agun Gimbiya, meke faruwa da zancen" murabus? Zeenah? "Eh yanzu ta kirani take tambayata ko naji wani abu, da alama tana cikin damuwa." Shiru yadanyi tare da dakatawa da dan shafa girarta da yakeyi cikin wata murya yace “Binta!” "Naam ta fada a hankali, yace “duk abinda Zeena zata miki kiyi hakuri, batada halayen banza" "rashin tarbiya mai kyau da ganin ta isa ne yasa take abubuwan da take, amma in kika santa a" hankali zaki fahimci ba haka take ba.” Kallansa tai duk tadanji zafi wanda kishi ne kowa yanadashi amma murmushi tai tace “insha "Allah, sai dai ina ganin ka fada mata ko hankalinta zai kwanta, tunda harya kirani ta kaskantar da" kanta alama ne na ta matsu. Ba musu yace “Shawararki tayi bari naje yanzu.” "Mikewa tai jiki a sanyaye tana ganinsa ya fita, shiru tadanyi tana tunani dan harga Allah batasan" daga fada zaice zaije yanzu ba. Bangaren Zeena ya nufa tana zaune sai dai gaba daya ta rasa abinda ke mata dadi balle tanaso dare ya kara rufawa ta nufi gun Ramlatu. Jin sanarwar isowar Junaid ne yasa ta mike zunbur. Junaid ya shigo ta gaisheshi cikin mamaki tace “Ya Junaid.” Zama yai sannan ya kalleta yace “Tunanin me kike?” Kallansa tai sannan ta karaso ta zauna tace “bakomai.” Binta tace kina cikin damuwa. Binta? "Ya kalleta tare da daga kai, kallansa tai tace “Ya Junaid akwai abinda ya faru tsakaninka da Abba ne dan Allah?”" "Junaid daya zuba mata ido baice komai ba, ta daure tai murmushi tace “nasan ba lalai ka" "fadamin ba, amma ni nasan haka kawai Abba bazai taba yadda yai murabus ba.”" "Idanunsa ya dago ya kara kallanta sannan yace “komenene tsakaninmu ne, kar kiyi bincike kar" kuma kiso sani.” "Yadan yi shiru kafin yace “wannan umarnine miji yake ba matarsa, in lokaci yayi komai zaki sani.”" "Kallansa tai cikin dakiya duk da rauni da zuciyarta tai sai dai ta daga kai, dan tana san Junaid" matuka. Junaid ya kalleta a ransa yace wannan taimakon kadai zan iya miki a wannan lokacin. Kafadarta ya dafa yace “ki taimaka.” Kai ta daga cikin sanyin jiki. Sai da safe ya fada sannan ya fita. ******* "Gaba daya Abdulsalam ya kasa sukuni, balle zance yazo mai har magana ta fara fita wasu garuruwa." "Sam ya rasa abinda ke mai ciwo, Azeema!" Ita kadaice zata sa Junaid ya bar abinda yakeyi. Kallan Hadiminsa yai yace “yi maza ka kiramin Azeema.” Yana fita Hajjo wacce ta gaji da tsayuwa tace “ina zaka?” Yace “Takawa ne yace na kira Gimbiya.” Cikin kumburi da bacin rai Hajjo ta dannu cikin turakar Takawa. Juyowa yai cikin mamaki dan yasan har baici ace tazo ba. Kallanta yai yace “Hajjo? Me kike anan?” Cikin masifa tace “koma menake ba damuwarka bace me kake nufi da ni? Wlh sai dai a mutu ai rai amma duk duniya ba wanda ya ksa kwacema Zubair sarautarsa.” Cikin kuluwa yace “naji jeki dan Allah.” Wai me ka daukeni....... Tsawa ya daka mata yace “jeki nace ko?” Kallansa tai tana hakkin bakin ciki kamar zatai magana ta fita rai a bace. ****** Gimbiya yana jiranki fa. Kallan Barira tai tace “banace ace bazanzo ba?” Barira cikin mamaki tace “Gimbiya.” Azeema ta kalleta tace “fita ki kuma rufemin kofar dakina.” Nan ya juya ya fita....... ****** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {44} Bazata zo ba? "Dan aiken ya zube a kasa yace ""tuba nake Ranka ya dade, hukuncina mai karfi ne.""" "Abdulsalam hankalinshi ne ya kara tashi, har ya yi hanyar kofa zaije gunta sai kuma ya dawo," "zama yai tare da hade hannayensa yana tunani, rana a zaune ya kwana dan duk yanda yaso yai bacci kasa wa yai." "Junaid kam baccinsa yai karfe hudu ya bude idanunsa tare da kallan Binta, shawarar daya yanke" "jiya kafin yai bacci ya sake tunowa, tabbas wannan shawarar itace ta dace a wannan lokacin." "A hankali ya zare jikinsa ya gyara mata kwanciya, kallan fuskarta yai cikin jin dadi sannan ya" sumbaceta ya sakko. "Bangarensa ya nufa ya kimtsa suka fito massalaci shi da Azi, bayan sunyi sallah ne ya zauna yai" "karatu sosai har sai da gari yai haske,ya kalli Azi yace “ka dubo gidan Wazirin?”" Cikin rada yace “eh.” "Tare suka fito suka nufi hanyar waje, masu kula da kofa basu kawo komai ba saboda jalabiya ce a" jikin Junaid sannan ya sa hula dan kar a ganeshi. "Gidan Waziri suka nufa kai tsaye, Waziri na soro inda ya maidashi karamar fadarsa." Yana zaune yana jiran kummalo. "Bafaden sa ne ya shigo ya sanar dashi yayi baki, Waziri cikin mamaki yace “da safen nan?”" Kallan kofar yai bayan ya musu izinin shigowa. Zumbur ya tashi tsaye cike da al’ajabi yace “Yarima!” "Junaid ya zare hularsa sannan ya kalleshi, hankali a tashe ya fara kokarin shimfida katuwar" "dadduma akan wata daddumar, yama kasa sawa ayi." Junaid dake tsaye ne yace “nan ma ya isa.” Ya nunamai asalin daddumar dake shimfide. "Duk ya rasa me zaiyi, Junaid ya zauna sannan Waziri ya gaisheshi." "Kallansa Junaid yai ya mai alama daya sallami bafaden, nan Waziri ya sallameshi." Azi ya fita ya rufo musu kofa tare da tsayawa a jikin kofar. Waziri ne ya kalli Junaid yace “Yarima!” Junaid ya dan kalleshi cikin tsananin kasaita da mulki yace “Zuwa nai nama gargadi da kuma Kashaidi.” "Waziri ya kalleshi gabansa na faduwa, murmushi Junaid yai yace “ka saki jikinka bawai neman" magana nazo ba nazone na nunama hanyar da kuke nema mai bulewa.” "Kallansa Waziri yai a tsorace, Junaid ya kalleshi yace “idan har kunaso na yafe muku laifinku na" "hada baki gun halakar da mahaifina da kukai, na yafe muku na cigaba da rayuwar da kuke buri" bayan rasuwarsa to dole kubi abinda zan sanar dakai a wannan lokacin.” Yawo Waziri ya hadiya cikin tsananin fargaba kenan yasan hadda su? Junaid yace “kayi gaggawar sanar da ‘yan uwanka su Shamaki dasu Galadima idan har suna san su da ‘ya’yansu su tsira to tabbas sai kunbi abinda nakeso.” Waziri ya daure yace “me zamubi?” Dukanku kar wanda ya sake zuwa gun Sarki Abdulsalam.” Da sauri ya dago ya kalleshi yace “bangane ba Yarima!” "Junaid yace “duk cikinku nasan kafi kowa fahimta shiyasa nazo gunka, maganar daya ce koya" "aiko kuje kusan karyar da zakumai karkuje, in kuma har naji labari ko naga daya daga cikinku yaje" kiran Sarki daga yau zuwa gobe to lalai daga ku har zuri’arku ku shirya fuskantar babban hukunci.” "Waziri yai shiru yana mamakin wannan yaran wanda sanda ya dawo yaro kamar bashida ilimi," daurewa yai yace “in mukai fa?” Yace “in kukai abinda nace zan barku a matsayinku sannan zan yafe muku.” Kallan zargi waziri yama Junaid dan bai yadda da wannan maganar ba. Junaid ya kalleshi yace “Ruwanka ne ka yadda ruwanka ne kaki yadda sanda karkai tunanin nazo "nan a san rai nane bayan nasan laifin da kuka aikata, zansa ido inga abinda zakai.”" Yana kaiwa nan ya mike ya fito bai jira ko Waziri ya tattaro tunaninsa ba. Yana fita waziri ya zauna yai shiru. ******** Ana kawoma Abdulsalam karin kummalo ya kalli Jakadiya dake basu umarnin inda xasu ajiye yace “Jakadiya a aika a kiran Waziri.” "Da sauri tace to, kallo daya zakama Sarki kasan yana cikin wani hali ko dan yanda yanayinsa gaba" daya ya canza. "Sam ya kasa cin abinci har dan aiken ya dawo, sanar dashi yai wai Waziri baya gida, nan ya aika a" "kira Shamaki, sai dai shima akacemai wai Shamaki bashida lafiya, bai hakura badai ya aika a kiramai Galadima, nan ma aka dawo akacemai wai ya je ganin gona." "Nan ya fahimci zuwa ne basa sanyi wanda hakan ya kara daga mai hankali, dan har tsoronsa ya" "fito karara dama yana tunanin in su Waziri suka bi bayansa tabbas zai samo mafita, wato suma sun yada shi kenan ko me?" Hankali a tashe yace “Akira Azeema.” "Kallansa dan aiken yai yace to, haka nan ya dawo ya sanar dashi wai tana bacci." "Gaba daya Abdulsalam ya fara neman zaucewa, yace “banda kowa kenan ko me?”" Dan aiken yace “ko na kira Hajjo?” Hajjo? Me zatamin wannan? "Tausayinshi ne ya kamashi ya mike zai fita, Abdulsalam yace “kiramin hajjo.”" "Nan ya fita, Hajjo na zaune ranta duk a dagule, ga Zubair a gefenta, nan aiken Sarki yazo mata." Mamaki ne ya kamata da sauri ta mike ta zura alkyaba dinta ta fito. Sarki sai safa da marwa yake a daki haryanzu ko abincin da aka jera mai bai kalla ba. "Hajjo ce ta shigo, mamaki ne ya kamata yanda ta ganshi duk a rikice." Tace “Takawa mai ya sameka?” "Abdulsalam ya juyo da sauri, hannunta ya kamo ya zAunar da ita, kallanta yai yace “Hajjo ki" "taimakamin, gaba daya na rasa yanda zan shawo kan matsalar dake gabana.”" Matsala? Kai da kake neman ba Dan Azeema mulki saboda soyayya wace matsala ce dakai? Abdulsalam ya kalleta yace “ke yanzu a yanda nake din nan kina tunanin har zan iya ba ko dana na cikina ne mulki balle dan da ba nawa ba?” Cikin rashin fahimta Hajjo tace “bangane ba?” "Kallanta yai yace “Junaid ne duk ya shirya wannan abin, kuma a gobe yake so ya kwace mulkin" "nan, sam na rasa yanda zan shawowa matsalar.”" Wata dariyar rashin yadda tai tace “har Junaid yakai girman da zai saka kai abunda bakai niyya ba?” "Abdulsalam yai shiru, kallan zargi tamai tace “ko yasan wani sirrinka ne?”" Kallanta yai yace “kema kinsan sirrin nawa ai.” Tace ni? Ta tambayeshi cikin rashin fahimta. Kallanta yai yace “Yayana Zubair.” Baki ta hangame ta bude tace “da gaske kana da hannu a ciki? Amma sanda na tambayeka kacemin bakada hannu harda min fada.” "Shiru yai, can yace yanzu duk ba wannan bane matsala yanda zan kwaci mulkina na koreshi ko" na halakashi nake nema.” Mijin yar taka? Kallanta yai yace “da dan me na bashi ita? Ai dan kome ya faru ya yafemin ne a matsayin mahaifints.” Hajjo ta kalleshi tace “da can bakasan dani ba sai data keabe muku kai da matarka ta so? Sannan yanzu bani ba neman ruguza rayuwar yarka kake?” "Yace “shawara na kiraki muyi, kinsan dai in komai yai daidai Zubair danki ne zai gajeni wannan" alkawari na miki.” Kallansa tai tace ka tabbatar? Da sauri yace eh Tace ka kwace yar ka kace sai ya hakura da abinda yake shirin yi zaka mai data. "Wani kallan takaici ya mata dama can shiyasa bai san yin shawara da ita gaba daya bata da lissafi," a kufule yace “dama can santa yakeyi? Da har in muka dauketa xai bar abinda yake?” "Tace “eh mana, ka bari na gwada ka gani, ai namiji ba sai yana san mace kadai ba da zaran ya" "dandana zumarta magana ta kare, nasan yanda na shirya ‘yata.”" Cikin takaici yace “to jeki.” Mikewa tai tace “zan aiwatar yanzu zakaji sakamako mai kyau.” Haushi yasa ma bai kulata ba. "Jakadiya ce ta shigo da sauri bayan fitar Hajjo ta zube tace “Takawa, sarkin Zazzau da sarkin" Kano sun aiko tayaka murnar ba surukinka mulki da zakai.” Idanu ya zaro yace “mene?” Jakadiya tace yanzu dakarun dake kula da kofar gari suka aiko a sanar yanzu zasu shigo kofar garin. Jikinsa ne ya kaure da rawa. Wannan yaro anyi tsinane ****** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {45} Hajjo ta fito daga bangaren mai martaba kai tsaye ta nufi bangaren Zeena. "Zeena na zaune ta gama cin abinci kenan, haka kawai tun jiya takejin dadi, a kalla tasan Junaid ya" "damu da ita, a hankali takai hannunta kan kafadarta inda ya dafa ta jiya, wani lalausan murmushi ta sake cikin jin dadi." "Fure ce ta kalleta tace ""Gimbiya kalau dai ko?""" "Kallanta Zeena tai, Fure tace ""naga kina dariya ne kamar "" sai kuma tai shiru." "Zeena ta kalleta cikin takaici, tace ""wlh fure na kusa koraki gun Hajjo can kika fi dacewa ba nan" "ba, wato nice mahaukaciya kenan?""" "Da sauri Fure tace ""Gimbiya ba haka nake nufi ba wlh.""" Zeena tace ko? Da sauri tace eh. "Alama ta mata data matso, da sauri ta matsa kusa da ita da jan gwiwa." Zeena ta daga hannu da sauri Fure ta runtse ido tana jiran saukar mari. "Jin shiru yasa ta bude ido daya kafin ta bude dayan idan, Zeena tace ""nama fasa aikaki gun Hajjo" "hada kayanki ki koma gun Binta, can itace zata iya da haukarki.""" "Fure tace ""tuba nake Gimbiya wlh bazan iya zaka gun kowa ba in bake ba.""" "Hannu ta kara dagawa, da sauri Fure da sake rufe ido, Zeena tasa hannu ta dungure mata kai tai" "baya, tace ""tashi kije can waje cikin rana ki tsaya, nama fahimci duka da hannu batawa kaina lokaci ne.""" "Fure tace ""Haba Gimbiyata, kin manta yau kwananki ne? Ai yanzu zamu fara shirin kwana.""" "Murmushi Zeena tai tace ""kin wanke kanki, me zamu shiryama Ya Junaid yau?""" Fure zatai magana Hajjo ta banko kofa. "Baki a sake Zeena ta kalleta, Hajjo tace ""tashi.""" Tashi? Wa? Ni? "Hajjo tace ""a'a ni.""" "Zeena tace ""meya kawoki dakin sirikinki? Bayan ko gaisheki baizo ba tukun?""" "A kufule tace ""suruku, kin tashi kin fito mun tafi ko sai na sa an ja ki?""" "Zeena fuskarta dauke da mamaki tace ""wai ni za'a dauka ko kuwa wata? Na tabbatar kinsan halina" "da abinda zanyi da wanda bazan ba.""" "Hajjo tace ""yau kuwa dole kiyi abinda nakeso, kin tashi mun tafi ko sai na ci mutuncinki, aure ne" "na raba ya kawo miki takardarki, ya dau uwarsa da matarsa su koma kauye.""" "Da fuskarta alamar mamaki ta fara nunawa kafin ta sa dariya tace ""lalai Hajjo ni yau Allah yasa" "lfy kike?""" "Kin wuce ko kuwa?""" "Gyara zamanta tai ta kalli Fure tace ""dubo in Ya Junaid na nan kece mai Hajjo tazo zasu gaisa.""" "Fure data tsaya a kofa tun zuwa Hajjo tai waje da sauri, Hajjo tace ""uban wa yace ina nemanshi?" "Balle har mu gaisa?""" Zeena bata ce mata komai ba sai kallan gefe ma datai. ****** "Binta ce ta gaisheda Sabisu cikin sha'awa ya kalleta yace ""Masha Allah kece matar Yariman?""" "Binta ta kalli Junaid cikin kunya sannan tai kasa dakai.""" "Sabisu yace ""kai lalai Yarima kayi sa'a na tabbatar da Sarki nadarai da ya kasance mai alfahari da" "zabinka.""" "Junaid ne ya kalli Binta wace ganin bai dawo yaci abincin safe ba yasa ta bi bayansa yace ""nayi" "laifi amim afuwa.""" "Dan kallansa tai ta kasan ido tamai alama da zata wuce, dan wata kunyace ta rufeta datasan" akwai babban mutum a can da bazata taso ba. "Junaid yace ""Baba tun kafin inyi laifim da za'a dakeni bari naje.""" "Dariya sosai Sabisu yai yace ""waya isa tabaka Yarima? Ko 'yarnan?""" "Binta tace ""zolayarsa ne wlh.""" Da sauri ta mike cikin kunya ta fita. "Dariya Junaid yai, Sabisu cikin sha'awa ya kalleta sannan ya kalleshi." "Junaid ne ya canza yanayin fuskarsa yace ""Baba kana tunanin abokin naka zai kai takardar" "wasikar Gayyatar?""" "Sabisu yace ""ai inaji yanzu ma ya kai, amma me kake nufi da aika takardar gayyata dakai?""" "Junaid yai wani murmushi sannan yace ""daga jiya zuwa yau kana tunanin ya isa masarauta" "nawa?""" "Sabisu yace ""matsalar dansa ne ba shi din bane, amma shi a lokacin Sarki Zubair in aka aikeshi kai" "sako kwana daya yakeyi ya je masarauta hudu.""" "Junaid cikin jinjina yace ""masha Allah, to d'an nasa musamai ran daga jiya zuwa yau yaje uku" "kenan?""" "Sabisu yace ""eh.""" "Azi dake bakin kofa yana neman izini ne Junaid yace ""shigo.""" "Nan Azi ya shigo ya gaisheshi, sannan yace ""Yarima ance Masarauta biyu na kano da Zazzau sun aiko da sako kyaututuka da taya murnar Murabus din sannan da jinjinama Sarki, wasikar yanzu za'a shiga da ita fada.""" "Junaid ya kalli Azi yace ""Alhamdulila komai na tafiya yanda ya dace.""" "Kallansu yai yace ""bari naje na dawo.""" Mikewa yai ya nufi bangaren Binta. Tana zaune akan kujera ta cika ta batse ya tura kofar tare da dan gyara kafadarsa. "Kauda kanta gefe tai cikin nuna alamar fushi, zama yai kusa da ita sannan yadan bige kafadarta" da kafadarsa. "Kara kauda kai tai, turata yai daga inda take ta matsa ya kara turata, mikewa tai zata bai gun, da" "sauri ya maida ita ta zauna yace ""Bintalo na tuba.""" Kara hade fuska tai. """Laaaa har na tuno wata rana, muna zaune a waje ana hira cikin hasken farin wata, wata ta. """ "Da sauri ta toshe mai baki tace ""Na hakura ya isa ba sai ka fadi me nai ba.""" Yana dariya yana kokarin yin magana bakin nasa a rufe. "Dan cizo ya mata a tafin hannun nata, sakeshi tai tana cewa ""yaya Allah na hakura.""" "Yace ""inaaa ai sai na karasa.""" Batasan sanda ta sake rufe bai baki ba ta daddane shi da jikinta tana girgiza mai kai. Idanunta yake kallo yana dariya sannan ya daga kai alamar ya daina. "Sakeshi tai tare da cewa ""Allah Yaya gaskiya ka gama dani, ka gama sanin komai nawa ina yarinya" "nasan haka zakai ta zolaya ta.""" Dariya yai zai sake magana sukaji ana magana a waje. Baiwarta ce ta shigo ta sanar da ita sakon Fure. "Junaid ne ya kalleta fuskarshi dauke da mamaki, kallan Binta yai yace ""bari na dawo yanzu.""" "Bangaren Zeena ya nufa, Hadimansa na biye dashi." "Yana kokarin shiga yana Hajjo rike da Hannun Zeena ita kuma tana zaune, ta rike kujera da daya hannun." Hajjo ko da ganin Junaid bai sa ta bar abinda take ba. Zeena na ganin Junaid ta warce hannunta da karfi ta nufi kusa da Junaid ta tsaya a bayansa tare da rike rigarsa ta baya. Hajjo ya kalla alamar karin bayani. "Fuskar Hajjo a turbune tace ""ka gaida ni ne?""" "Junaid yace ""jira nake ki zauna.""" "Haushi ya kamata tace ""ba zama nazo ba tafiya da yar Abdulsalam zanyi tunda bakaga darajar yarsa ba kake neman wulakantashi.""" "Kallansa Zeena tai cikin rashin fahimtar kalaman Hajjo, Junaid ne ya kalleta yace ""babu" "wulakantace a duniya sai wanda ya wulakanta kansa, sannan duk wanda ya wulakanta mutum da saninsa to lalai cikin dayam biyu ne kodai wanda aka wulakanta baisan kanshi ba ko kuma bashida daraja.""" "Hajjo ta cika da bacin rai tace ""bamu 'yarmu.""" "Junaid ya kalleta yace ""gatanan in zata biki.""" "Da sauri Zeena tace ""Ya Junaid?""" "Sannan ta kalli Hajjo tace ""ba inda zani.""" "Junaid Hajjo ta kalla tace ""bata takardarta, na tabbatar inka saketa dole ta tafi.""" """Takarda?""" "Hankali Zeena ne ya tashi tace ""Hajjo baki da. """ Kallan da Junaid ya mata ne yasa tai shiru ranta yayi matukar baci. "Junaid yace ""wannan kuma banga mai sani inyi abinda banyi niyya ba.""" "Sannan ya sake kallanta yace ""ki huta lafiya.""" Ya juya ya fita. Hajjo kam kiris take jira ta fashe da alama. ******* "Isowar masu aiken sarakunan nan ba karamin hargitsa kwakwalwar Abdulsalam akai ba, yana" "makale a kasa a lungun gado kamar zautace yana cewa ""a'a ba wanda ya isa ya kwacen mulki.""" Nace sai mugani ai * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {46} "Gaba daya Azeema banda kwanciya a daki ba abinda takeyi, zazzabin ya barta amma abinda ke" "zuciyarta ya kasa sakinta, a duk sanda ta tuno abinda ya faru sai taji kwalla na neman kawo mata, ba shakka tasan tama Zubair babban laifi amma inta tuna ta bada kofa anyi amfani da ita ne sannan yanzu hankalinta ya kaimata ai shi Abdulsalam din shine ya kaita gun mai maganin, kenan dama ya gama shirinsa?" Duk sanda ta tuno hakan wani hawaye ne ke zubo mata. "Barira kam ta rasa abinda ke mata dadi, gashi Azeema tace karta sanar da ko Safiyah." Inta gaji da kwanciyar ta mike tai tasbihi da hailala. ******* Gaba daya shi kadai ne a cikin tangamemen kilisarsa yana zaune a lungu hankalinsa a tashe. "Jakadiya ce ta sake shigowa tace ""Takawa ana jiranka a fada.""" "Abdulsalam ya kalleta hankalinsa a tashe, sannan yace ""to.""" Da kyar ya daure hadimansa suka shigo suka tayashi shiryawa. Junaid yana zaune falan Binta amma gaba daya hankalinsa nakan Azi akan ya dawo ya sanar dashi ko Sarki ya shiga fada. "Binta ce ta fito daga daki ta kalleshi tace ""Yaya!""" "Kallanta yai yace ""zuwan zakiyi?""" "Tace ""tunda kai bazaka ba gwara ni naje, dan Allah yaya kazo muje Allah Umma batada lfy.""" "Yanda ya kalleta tasan bazashi ba, fuska ta hade tace ""shikenan.""" "Ta fita, murmushi yai tare da kara jiran Azi." Binta ko minti biyar da fita batai ba Azi ya dawo. Junaid na ganinshi ya mike yace “ya?” Azi yace ya fito daga sashensa. Nan Junaid yace muje. Tare suka fito hadiman sa suka bi bayansa suna tafe ya kalla Azi yace “Zeena fa? Tabi Hajjon?” Yace “a’a tana bangarenta.” Su Waziri fa? Sun iso yarima. Junaid ya jinjina kai sannan yace “Zubair fa?” Haddashi? Junaid yadan kalleshi kadan yace “haddashi.” Nan Azi ya amsa aike sannan ya juya. Junaid fada ya wuce daga nan kai tsaye. "A fada kuwa Sarki na zaune bayan ya amsa gaisuwa ne, kallan Waziri yai wanda kansa ke kasa, ya" "kalli Shamaki shima kansa na kasa, ya kuma kalli Galadima." "Daurewa yai yace “banyi tsammanin taran gaggawa haka ba, Allah yasa komai dai lafiya.”" Turaki cikin mamaki yace “Ranka ya dade ai mu sako aka iso mana dashi akan kana neman nemanmu a fada.” "Nan kowa ya amsa da hakan ne, Sarki yai shiru kenan Junaid ne? Uban me yake nema dashi?" "Zagi ne ya sanar da isowar Wakilan da aka turo, Sarki ya basu izini cikin dakewa, duk da yanda" gabansa ke faduwa. Suna shigowa Zagi ya sanar da isowar Junaid. Ba Sarki ba hatta su Waziri sai da gabansu ya fadi. "Junaid ne ya shigo cikin isa da takamarsa, ya gaida sarki sannan ya zauna." "Wakilai suka kalli Junaid sannan suka kalli Sarki, wakilin sarkin kano ne yace “wannan sako ne" "daga mai martaba sarkin Kano, tabbas yana kara jinjina maka yace mu tafin masa da ranar yin" nadin shi da kansa zaizo.” "Sarkin Zazzau ma abu daya ya fada, ajiye kayan kyautar da suka kawoma Junaid sukai sannan suka" gaisheshi. Gaba daya Abdulsalam ya kara rikicewa kafafunsa kawai yake matsewa ta cikin kayansa. "Junaid ya amsa tare da yin godiya, sai da suka fita, Turaki yace “ai Sarki wannan lamari kowa" "yana bashi mamaki, duk da muma ba san murabus dinka muke ba amma in muka tuna namijin" kokarin dakai gun yanke wannan hukunci sai musan bakuda bakin magana.” "Nan kowa ya fara tofa albarkacin bakinsa, Abdulsalam ji yake kamar ya saki wani ihu a gun da" yake. Junaid ne ya kalleshi cikin mamaki yace “Takawa ina tafe ina fatan Allah yasa ba abinda kake shirin fada yasa ka taramu ba?” Abdulsalam ya kalleshi me yake shirin yi? "Zubair ne ya shigo ya zauna, Turaki yace “Mai Martaba badai ?”" Sai yai shiru suna kallan Juna. Wale yace “Takawa bai kamata ayi abu cikin gaggawa ba.” "Junaid yace “sosai ma kuwa, komai ayishi a hankali, dan Allah ka janye alkawarin nan naka na" yau zaka ajiye mulkin nan.” "Bai san sanda ya bude baki ba, Waziri cikin tsoron Junaid ya kalli Sarki anya wannan zai barsu" suma kuwa? Turaki yace “au yau? Indai Alkawari yai ba yanda zamuyi.” Junaid ya kalli Abdulsalam sannan ya kalli Zubair wanda ya kumbura fam. "Abdulsalam idanunsa ne suka canza kala, ya daure ya kallesu yanzu kam yasan bashida wata" "mafita, inba so yake komai ya fito ba, an gama daureshi ta ko ina." "Wale ne yace “da alama Sarki sauri yake ya baka mulki a matsayinka na sirikinsa kuma dansa," yafisan yai jika yana gefe.” Dariya sukai dukansu wanda dariyar ta kasance kamar arsashi ne ya dira a zuciyarsa. "Zubair ya kalla wanda ya gama bata rai, Junaid ya kalla wanda ya kalleshi shima." Mamaki me ya kamashi dayaji yace “to Mai Martaba.” "Kafin ya fara tunanin me zaiyi kawai yaga ya taso yazo inda yake ya tsuguna, ya dukufo kusa da" kunnensa. "Yace “idan har baka sauka ba a wannan lokacin yanzu kuma, duk abinda ya biyo baya a wannan" "lokacin karkaga laifin kowa sai naka, ga danka ga fadawan ka nan, kowa yaga mumunan halinka da" "kake boyewa a cikin fara’arka, sannan kar ka manta ina da shaidar laifukanka, kana batamin rai komai xai tarwatse a gun nan.”" Murmushi yai bayan ya dago ya daga kai alamar to sannan ya juya ya zauna. Waziri dasu Shamaki ba shakka tsananin tsoron Junaid ya gama kamasu. "Sarki ya daure yai gyaran murya, da kyar ya samu ya daidaita muryar sa dake rawa yace “abu" "dai da kukaji haka yake, ina faran zaku bani hadin kai, nima na samu na huta, dama can asalin mulkin nan na shi ne, na rikemai ne saboda mahaifinsa ne wato yayana ya sani, sai dai yanzu" "Junaid ya girma yayi aure, na tabbatar ku kanku yanzu kunsan Junaid ya cancanci kujerarsa.”" "Zubair kara habaka yai, cikin bacin rai matuka." Sukam yan fada kowa ya gamsu da maganar Abdulsalam. "Yau zan ajiye mulkin nan, a wannan lokacin ina fatan xaku ba shi hadin kai, na tabbatar xai yi" abinda ni da mahaifinsa bamuyi ba.” Wale yai dan murmushi yace “tabbas Takawa samun irinka a duniya sai an tona.” "Junaid ya rusuna sosai yace “Ina godiya Takawa, na gode daka zabeni sama da jininka, wannan" hallarci naka tabbas abin dubawa ne.” "Kallan Shamaki yai yace “a dako sandar mulki a da kamai, inyaso ragowar abin Sarauta sai ranar" da za’ai nadin sai a bashi.” "Nan Shamaki ya juya ya fita, Waziri ya kalli Sarki wanda yasan Allah ne kadai yasan halin da yake" ciki a wannan lokacin. ******** "Haka Binta ta zauna sai dataga Azeema taci abinci sosai, sannan sukafara hira sama sama duk da" rabin hira Binta ce ke bata labarin tasowarsu da abubuwan daya faru a shekarun. Azeema nata murmushin jin dadi tare da kunyar abinda ta aikata. ********* Hajjo dake zauna cikin bacin rai ta kalli Ramlatu tace “ya kike ganin zanyi in kamo yarinyarcan?” Ramlatu tace “ai Gimbiya ce in ta dage a abu ba mai hanata.” Hajjo a kufule tace “duk ni na barta haka yanzu ga abinda take neman jawomin ai.” Sanar da isowar Jakadiya da akai ne yasa Hajjo cikin mamaki ta kalli kofa. Jakadiya cikin haki da alama gudu tai ta shigo ta zube a gabanta tace “Hajjo Hajjo.” Hajjo ta kalleta rai a bace tace “meye kuma?” Jakadiya tace “Sarki ya ajiye mulkinsa.” Mene? Ta tambaya cikin rashin fahimta. "Jakadiya tace “an dako sandar mulki yanzu an shiga da ita fada, bansan meke faruwa ba.”" Hajjo tace “yauwa Abdulsalam gwara kaga Zubair mulkin kafin wacen mara mutuncin ya aikata "mana tsiya, ashe shi yasa aka kira Zubair dazu?”" Cikin wata dariyar farin ciki ta tambayi Ramlatu. "Dariya sosai Hajjo take cikin jin dadi tana jin jina kai, Ramlatu sai kara wasa mata kai take." tab **** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {47} Hajjo cikin tsananin murna ta mike ta fito daga sasshenta Ramlatu na bi mata baya cikin tsananin farin ciki. "Daga dan nesa kadan taga kamar Zeena da tata tawagar, baki ta tabe tace “naga bakin ki yanzu" mai zaice.” "Hajjo tai gaba ba tare da ta kara ko kallan Zeena ba, Zeena wacce yanzu taji abinda ke faruwa ta" "taso dan san ganin Hajjo da halin da take ciki ta tsaya daga inda take, fuskarta dauke da mamaki, dan bata taba tunanin ganin Hajjo haka ba." "Kallan Fure tai tace “da alama Hajjo lafiyanta kalau, mu koma tun kafin wani abu ya faru muna" waje.” "Nan Fure ta amsa dato, haka suka juya Zeenatu na tafe da tsananin mamakin abubuwa biyu, na" "farko murabus din da gaba daya bata taba tunani ba, sannan da ganin Hajjo hankali a kwance." Hajjo tana tsakiyar masarauta inda tafiya kadan ne zai hadasu da Fada sukaji masu kirari da busa "sun fara, sam duk yanda masu kirari Ke magana bataji saboda tsabar zumudi." "Ramlatu wacce yanzu kunnanta sukaji Junaid akema kirarin, yasa a tsorace ta matso kusa da Hajjo." Hajjo ta tsaya ganin yanda tadan tare gefen tafiyarta kadan. Hajjo tace “ya akai?” Ramlatu a tsorace tace “Hajjo ina tunanin mu koma daga nan.” "Mu koma ina? Ai dole muje godiya, Ramlatu a tsorace take kallanta sannan tace “tuba nake" Hajjo amma dakin danji me masu kirarin nan suke cewa.” "Kallan banza ta mata sannan tace “ina nake da lokacin jin wannan shirman, me suke cewa?”" Ramlatu dai tai shiru kafin tace “mu koma mu kira Yarima Zubair din yazo da kansa.” Hajjo tai shiru kafin tace “bai kamata muje godiyar ba?” Ramlatu tace “eh gwara mu jirashi.” Shiru tai kafin tace “to.” "Juyawa tai suka koma, fuskarnan tata wasai da farinciki, kallan hanya tai tace “waccen yar rainin" hankalin ta juya ne?” "Ramlatu da batama jita ba tana tunanin yanda zata zame ta gudu, Hajjo ta kalleta tace “me kike" tunani?” Ramlatu tace “inaji tsabar murna ce tasa kaina ciwo ina tunanin komawa bangarena kafin Yariman ya dawo.” Hajjo tace “shikenan.” "Nan tai wuf ta gudu da hadimanta, Hajjo tana tafe tana farin ciki, daga sama sama taji kamar sun" "kira Junaid, sai kuma taji Zubair." Baki ta tabe tace “wato yayan Junaid? Ni da sunbi ta tawa ko sunanansa basa kiraba.” "Tasa kafa zata shiga bangarenta taga Hadimanta ragowar data bari sun hada kai suna magana," suna ganinta sukai shiru. Wucewa ciki tai ta zauna. Batafi minti goma da zama ba sai ka bawan Zubair wanda yafi kusanci dashi ya nemi izini ya shigo. Hajjo cikin zumudi tace “Aram ya akai? Ina Ranka ya dade din?” Kallanta yai yace “Hajjo! ki taimaka ki aika a kira Yarima kafin wani abu ya sameshi.” Me zai sameshi? Ta tambaya cikin mamaki. "Aram yace “Hajjo gaba daya ba wanda yake bi takan Yarima murna kawai suke taya Junaid ba wands ya damu da halin da yake ciki, gashi ba damar ya taso kar a dauka bakin ciki yake.”" Bakin ciki? Ta tambaya hankali a tashe. Yace “bakiji Sarki ya ba Junaid mulkin na?” A zabure ta mike tsaye tace “yaba Yarima me?” "Aram yace “yanzu kam ai kowa yasan abinda ke faruwa, tunda gashi anata busa ana kirarin ana" sanarwa.” Gaba daya hankalinta ne ya tashi tace “inji wa? Inki ubanwa yace ya isa ya ba Junaid mulki ba Zubair ba?” Hajjo gaba daya ta rikice hankalinta a tashe take magana........ ***** Zeena sai sintiri take a sashenta kafin ta kalli Fure tace “hankalina ya kasa kwanciya Fure dubomin Binta.” "Nan Fure tai waje, bata dade ba ta dawo tace “tana bangaren Gimbiya Azeema.”" Zeena tace “tashi muje gun Umman.” Nan suka fito. Ramlatu tana gudu ta nufi bangaren Azeema. "Gimbiya na zaune suna hira da Binta, dan Binta yanzu ta sata ta fito falan ta, Barira sai dadi" takeji. "Suna cikin hira ne aka fara bushe bushe, Azeema ta kalli Barira tace “Bari duba ki gani meke" faruwa? Wannan busar busace ta Sarki.” "Nan Fure ta fita, bata dade ba ta dawo ta sanar da Azeema ai wai sarki me yai murabus yaba" Junaid mulki. Fuskarta dauke da tsananin mamaki tace “AbdulSalam din?” Barira tace “eh.” "Shiru Azeema tai dan tasan tabbas ba abinda zai sa Abdulsalam yabar mulkim nan da yake so, sai" dai ta tabbatar Junaid ne yasashi dole saboda abinda ya aikata. Muryar Binta ce ta katseta datace “Haba Bari sai kace wasa ta ya za’ai murabus ba wanda ya sani.” "Barira tace “shine abin mamakin, gun a cike yake dam da alama an shirya dama”" "Azeema tai shiru idanunta suka ciciko,babban burinta ada bai wuce Junaid ya samu mulki ba" amma batasan meyasa yanzu gaba daya zuciyarta a cike take da tsanar kanta. "Shigowar Ramlatu ce yasa ta hade fuska, Ramlatu ta zauna ta gaisheta." Azeema ta kalleta bayan ta amsa tace “lafiya?” "“Dama nazo wucewa nace bari nazo na gaisheki, na dade banzo na gaidake ba.”" Azeema ta dauke kai ko tanka mata batai ba. Ramlatu tai dariya tace “Matar Yarima ce?” "Barira tace eh, Binta ce ta gaisheta." “Ina Gimbiya Zeena? Allah yasa bata wahalar dake kinsam yarinyar nan Hajjo duk ta gama sangartata.” "Binta cikin mamaki ta kalleta, dan ita ko saninta batai ba kafin tace “ba abinda take min.”" Ramlatu tai dariya tace “ko dayake yanzu farko ne na tabbatar ” “Ya isa haka nan” abinda Azeema tace mata kenan. "Jiki a sanyaye tai shiru, Azeema tace “inkina gama gaisuwar zaki iya tafiya.”" "Ramlatu wacce taji haushin haka ta mike tana dariya tace “ba laifi, bari na wuce.”" Tana kokarin fita ana sanar da isowar Zeena. Idanu ta zaro kafin ta dan kauda kai. Azeema ta kalleta sannan tama Barira alamar ta bata izini. "Nan Zeena ta shigo, tsayawa tai cikin mamaki ta kalli Ramlatu wacce yanzun nan fa taganta da" "Hajjo, Ramlatu tai saurin kallanta kafin tace “nazo wucewa ne shine na shigo mu gaisa, naga mun dade bamu ko gaisa ba.”" Zeena tai wani murmushin takaici tace “ko? Wucewar ce naganki yanzu da Hajjo?” Ramlatu tai kasa dakai tace “eh zan wuce bangarenane.” "Zeena ta jinjina kai tace “haka akeso ki bar layin da zai sadaki da bangarenki kiyi zagaye, kin" kyauta da kika zo gaidata.” "Ramlatu tai kasa dakai, nan tai sum sum ta fice." "Zama Zeena tai ta gaida Azeema, Binta kuma ta gaisheta." Kallan Azeema tai tace “Umma Karama dan Allah kinsan meke faruwa? Gaba daya na kasa "samun nutsuwa, na tabbatar akwai wani abu dake faruwa, duk da Ya Junaid yace kar nai bincike" kar na tambaya amma sam hankalina ya kasa nutsuwa.” Idanun Azeema ne a dan ciciko tace “kibi abinda mijinki yace sannan dake da Binta ku tashi ku "koma bangarenku, kar wanda ya sake zuwa nan bangaren har sai Junaid yamin hukunci na.”" "Kallanta sukai a tare, Binta tace “hukunci?”" "Murmushi Azeema tai tace “duk mai laifi dole ne a hukuntashi, kada wanda yasa baki akan" "abinda ke faruwa, ku tashi ku koma bangarenku.”" Jiki a sanyaye suka tashi suka fito. Binta suna fitowa ta kalli Zeena tace “meke faruwa Gimbiya? Ance murabus yanzu Umma tace hukunci.” Zeena tai shiru kafin ta kalli Binta idanunta sun dan ciciko tace “kenan Umma da Abbana sunma Junaid laifi.” Laifi? Binta Shiru tai tana tunanin kalaman Junaid na rannan. Zeena ta kalleta tace “wani irin laifi kike tunani?” Binta ta girgiza kai tace “bansani ba.” Shiru sukai a haka suka koma. ********* Hajiya inna ta fito daga dakinta dakyar cikin farinciki ta zauna a waje tace “yau ko yanzu na muti Jakadiya hankalina a kwance zan tafi.” "Jakadiya cikin jin dadi tace “Barka Hajiya inna, wannan lamari yayi dadi.”" Junaid! Hajiya Inna ta fada cikin jin dadi...... ****** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {48} "Fure ce ta shigo da sauri, ta kallai Zeena wacce ta zuba mata ido itama." Fure tace “Gimbiya baki daga cikin gida sunzo tayaki murna.” “Murna? Ai sa bari sai gobe ko?” Dan tsaki tai sannan ta kalli Fure tace “ke kuma meye?” Dan yanda taga Fure ta zuba mata ido. Fure ce ta kalleta cikin mamaki tace “Gimbiya yaushe kuka zama kawaye?” Harara ta maka mata tace “haka kawayen suke? Tashi ki shigo dasu.” "Nan ta fita, matan kanen Abdulsalam ne da kuma yan uwa dake zaune anan." ******** Binta tana fitowa ta kali Hadimarta tace “Rali kira min Harira dan Allah.” Raliya tai dariya tace “Ranki ya dade in kina san abu ki baku umarni kawai.” Binta tai murmushi sannan ta shiga ciki itama hankalinta duk a dagule. "Harira ce ta shigo ta gaisheta sannan ta zauna, Binta ta sauko kasa kusa da ita tace “Harira kinji" abinda ke faruwa?” Harira tace “naji sai dai sam na kasa gane meke faruwa.” "Shiru Harira tai tana kallan Binta tace “Karki damu, Yarima yasan me yakeyi duk abinda kikaga" ya aikata da dalilinsa.” Binta tace “na sani sosai sai dai ina tsoron yana cutar da kansa ne.” Fuskarta dauke da mamaki tace “kamar ya?” Binta tai shiru dan batasan fadar abinda ke tsakaninta da mijinta duk kankantarsa kuwa. Harira tai murmushi tace “ki kwantar da hankalinki insha Allah ba komai.” Kai ta daga a hankali sannan Harira ta mata sallama ta fita. Tanajin yanda ake magana da guda daga bangaren Zeena ita kuma bako mutum daya a "bangarenta, mikewa tai ta shiga ciki tana tunanin hukuncin da Junaid ke dauka." ********** Sai yamma kowa ya watse Junaid ya tunkari bangaren Sarki. "Abdulsalam najin Zagi na sanar da isowar Junaid yaji gabansa ya fadi, sam shi ko sunansa" bayasan yaji an fada. Junaid ne ya shigo ya zauna sannan ya kalleshi. Abdulsalam wanda a yan kwanakin nan har ya rame ya canza ne ya kalleshi. Junaid ya kalleshi sannan ya saki wani irin murmushi yace “kayi kokari sai dai saura abu daya.” "Kallansa Abdulsalam yai zuciyarsa na tafasa, tari ne ya dan kwace mai yana kallan Junaid." Junaid yace “ a randa akai taron nadi a ranar nakeso ka dau matarka Hajjo ka bar masarautarnan.” Da sauri Abdulsalam yace “muje ina?” Kafada Junaid ya daga yace “wannan kuma banaji ya dameni.” "Gaba daya Abdulsalam ya rasa me zaice, daurewa yai yasan in ya sake bari yanzu ma galaba" Junaid zaici a kansa yace “Ragowar matana da kuma Azeema fa?” Kallansa Junaid yai yace “baka taba jin kunyar zama da matar yayanka wacce kai ajalinsa ba?” Abdulsalam yace “ni na kasheshi da hanuna?” Kaikai ajalinsa. Ita kuma Azeemar fa? Tanada laifi babba dan haka yanda na ma hukunci itama haka zan mata.” Abdulsalam rai a bace yace “na ajiye mulki yanda kakeso amma duk duniya ba mai rabani da "Azeema, in har zan bar nan gidan to lalai sai dai na tafi da ita.”" "Junaid ya kalleshi, Abdulsalam yace “in komai ya fito ai ba ni kadai zata kwabe wa ba.”" Junaid yai shiru yana nazari akansa kafin ya mai sallama ya fita. ******** "Bangarensa ya nufa? Yana tafe ana mai buda yana kan doki, mutane na biye dashi, har ya isa" bangarensa. "A bakin kofar shiga daga ciki mata ne a cike suna jiransa, Yana shigowa suka fara tayashi murna," yana amsawa. Jakadiya tada wanda har da ita a ciki tace “Yarima au Sarki zance barka da sauka Takawa!” Junaid ya daga kai sannan yai ciki. "Zeena wacce ta gama daukan kwalliyarta, tana jiran su fita taje gun Junaid." Azi Junaid ya kalla yace “Sabisu na nan ne?” Azi yace “dazu da kana fada ya fita wai dan kokari zai ga gari.” Murmushi Junaid yai suka nufi ciki. ***** "Zubair wanda yake tafe Arim na rike dashi, da kyar suka karasa bangaren Hajjo saboda yanda" gaba daya bakin ciki da takaici suka gama galabaitashi. A kasa daram yaga Hajjo ta baje ta zauna a kasa hankalinta a tsananin tashe. "Kallanta yai bayan ya shigo ya zauna a gabanta, wasu zafaffan hawaye ne suka zubo mai yace" “anya Hajjo ni dan Abba ne? Ace yana mahaifina amma gaba daya bai damu dani ba baya sona?” Hajjo wacce tashin hankalinta ya ninka na Zubair ta kalleshi hankalinta a tashe tace “Zubair gaba "daya yau ina tunanin kafin dare zan karasa lahira, banaji zan iya rayuwa a haka, ta yaya ma hakan" zai faru?” "Ta fada kanta na wani irin sarawa, tana rike shi." "Zubair yace “Goggo ki tashi kije gun Abba dan Allah, wlh ni kam bazan taba yadda ba.”" Ranta a bace ta mike ta shiga dakinta ta kwanta. Zubair cikin takaici ya mike ya nufi bangarensa. ******** "Kallan Harira yai wacce yasa tazo yace “ki sa a hada mana abinci duka a nan, ki sanar dasu suzo" nan.” Harira tace “To Ranka ya dade.” "Bayan sallar isha’i kuwa Zeena da Binta suka nufi bangaren Junaid, yauma Binta ta yi kwalliya" "sosai, dukansu sai kamshi sukeyi." Junaid ya sallami kowa a bangarensa dan yanzu saboda komai ya kusa kammala Sabisu ya koma bangarensu Azi. "Binta ce ta fara isowa, Junaid na ganinta ya saki wani murmushin jin dadi, tun dazu yake san" ganin fuskar nan.” "Binta ta kalleshi, hannayensa ya bude alamar tazo, murmushi tai a hankali sannan ta zo ta zauna" "kusa dashi bata rungumenshin ba, kallanta yai ya dan turo baki kadan tare da kauda kansa gefe." "Jiyai ta sumbaceshi a kuncinsa, juyowa yai ya kalleta yace “wannan cin hanci ne?”" Murmushi tai ta dan matso saitin kunnensa tace “in na rungumeka uwar gida ta shigo ince me?” Hannu yasa kamar mai nazari sannan yace “itama in tazo sai ta rungumeni.” Wata harara ta galla mai tace “da cewa nai bazata rungume kan ba?” Yace “ba haka kila ce ba?” Haushi ya kamata tace “Allah zan rama.” Ta fada tare da hade rai. "Sanar da isowar Zeena ne yasa ya kalli kofa, shigowa tai cikin shiga ta isa da matsayi." "Tayi kyau sosai, gefen damanshi ta zauna sannan ta gaisheshi." Amsawa yai fuskarsa a sake. Shiru suka danyi kafin ya kalli Zeena wacce gaba daya hankalinta da tunaninta rabi makan tasan abinda ke faruwa. "Hannunta ya kamo ya rike, da sauri ta kalleshi cikin sanyin murya yace “Zeena!”" "Jikinta ne gaba daya yai sanyi sai idanu data zuba mai, Junaid yace “Ga Binta nan, inaso ki kula" "da ita, kece uwar gida sannan matsayinki a masarautarnan mai karfi ne, yanzu komai na rayuwa zai canza, bakoda yaushe zan samu damar kula daku ba dan haka ina rokonki da ki ajiye duk wani halaye naki da kikasan basu da kyau, ke yanzu uwa ce ga mutane dayawa dolene ki zama abin koyi" "ga mutane, bazan yadda da sakarci da cin zarafi ba kamar yadda kika saba a baya.”" Hawaye ne suka zubo mata ta daga kai alamar to. "Junaid ya saketa sannan ya kalli Binta wacce gaba daya jikinta yai sanyi, yace “Binta!” Kallansa" "tai ya rike hannunta yace “kece karama, banasan wani abu daya danganci rashin kunya ko wani batanci daga gareki, duk da nasan halayenki sai dai inaso ki kiyayi kanki daga biyewa mutanen da" zasu kawo miki gulma da kuma hadaku da mutane.” A hankali Binta ta daga kai alamar fahimta. Murmushi Junaid yai sannan yace “muci abinci?” Zeena ce ta kalleshi tace “Abba yama laifi ko?” "Yanda tai tambayar ne yasa ya kalleta, saboda tambaya ce da aka yishi cikin shakkar amsar da" zataji.” "Yanda take kallansa yasa yasan a tsorace take yace “karkisa irin wadan nan abin a ranki," "Abdulsalam mahaifinki ne ki daukeshi a fuskar da kika sanshi, nima zan daukeshi a fuskar dana" sanshi.” Kallanta yai sannan ya kalli Binta yace “Bismillah!” *** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {49} Kasancewar ranan kwanan Zeena ne bayan sun gama cin abinci Binta ta musu sallama ta nufi sashenta. "Zeena tasa su Fure suka kwashe kwanuka, kallan Junaid tai wanda yasashi kallanta yace “me" kike san cewa?” Tambaya nake sanyi kuma bansan ta yanda zanyi ba? Kasan haka na taso magana ina fadarta ne "daga raina, sai dai yanzu nasan dole ne na dinga sanin abinda zan fada kafin ya fito daga bakina.”" Cikin jin dadin kalamanta yace “menene?” Idanunsa ta kalla wanda ke mata kwarjini ga so da take masa har cikin jikinta tace “ Hajjo ” "ta kasa kuma karasawa sai kasa da idanunta datai, jitai kwalla tana neman zubo mata, haka kawai" jikinta ke bata laifin Abba mai karfi ne tunda har ya iya ajiye mulkinsa saboda shi. Idanunta a runtse tana kokarin maida kwallarta ne taji hannunsa akan fuskarta gaba daya jikinta "ne ya amsa, a hankali ya dagota ta kalleshi, da kyar ta kakaro murmushi ta mai wanda suka kara bayyana kwallarta dake neman zubowa, yanda ya zuba mata ido ne yasa kwallar suka gangaro a kan hannunsa." "Idanunsa ya lumshe sannan ya sake kallanta, murmushi ta sake yi na dauriya tace “Yaya na sani" "ni mai laifi ce, ma taso ba ruwana da halin da wani zai shiga a dalilina, wannan banzan halin nawa ya ja mutane dayawa sun shiga wani hali ciki hadda kai, banda bakin da zan nemi ka saukaka ma" mahaifiyata da mahaifina. ” "Wasu kwalla ne suka sake gangarowa akan hannunsa, wannan lokacin shine karo na farko dayaji" "Zeena har ransa, ya aureta ne saboda burinsa ma auran Binta, san Binta a jininsa yake tun baisan kanta ba take da babban matsayi mai karfi a ransa, sai dai a wannan lokacin ya fahimci Zeena ta samu guri a ransa, dan tabbas tausayinta yakeji sosai, ya sani yanzu shi kadai ne da ita, dole ko dan haka ya boye abinda mahaifinta ya aikata in ba haka ba mutane ma kinta itama zasuyi." "Hannu ta dago tana neman share hawayenta, hannunta ya rike da daya hannunsa, jitai zuciyarta" "na kara raunana, kallansa tai tana san sake magana kuka ya kwace mata." "Jawota jikinsa yai ya rungumeta, sai datai kuka sosai sannan ta daina, ba tare da yace mata" "komai ba, sai data gama sannan yace mata “Karki damu komai zaizo da sauki insha Allah, sannan in har kika canza halayenki komai naki zai canza, kada ki manta na fadamiki kece ido na nacikin" "gida, dole ne ki dinga sanin abinda zaki dinga yi daga wannan lokacin.”" Kai ta daga tana kwance a jikinsa tace “insha Allah bazan taba baka kunya ba.” "Murmushi yai, dagowa tai a hankali ta kalleshi sannan itama tai murmushi tace “nagode da ka" bani dama.” "Mikewa yai sannan ya mika mata hannunsa, wani irin dadi ne ya kamata ta mika masa nata" hannun cikin wani irin jin dadi da ita kadai tasan yanda takeji. "Hannunta ya kama suka shiga daki, a bakin gadan ta zauna cikin kunya, tana cewa “yau na fara" shigowa dakinka.” "A hankalinya taka zuwa inda take ya zauna a gefenta, hannunsa dataji ta ratsin cikinta ne yasa ta" dan rike numfashinta tare da saukeshi a hankali. Kansa ya sako ta kafadarta yace “garin ya ya?” "Gaba daya ta kasa magana saboda wani irin yanayi data tsinci kanta a ciki, dan juyowa tai ta" "kalleshi, hannu yasa yai baya da ita a hankali ta kwanta akan gadon, idanunta na lumshe sai gabanta dake wani irin faduwa." Bakinsa ya sa a cikin nata................ ********** Washegari! "Cikin tsananin kunya ta tashi, bakowa a dakin hakan yasa ta dinga tuno abinda ya faru jiya tana" "dariya tare da rufe fuskarta, da alama da sukai sallar asuba tare ta koma bacci lokacin ne ya fita." "Mikewa tai zuciya daya, jin zafin datai ya ratsa ta ne yasa cikin kunya ta koma ta kwanta." Junaid kam bayan ya gama karatunsa yana ganin gari yayi haske ya mike ya nufi bangaren Azeema. "Gaba daya ba kowa a hanyar dan duku dukun safiya ne, ita kanta Azeemar tayi sallah kenan" "tadan kishingida a inda ta kwanta din, barira ce ta leko ta sanar da ita isowar Junaid." "Mamaki ne ya kamata matuka, jitai baccin idanta ya ware ta kalleta tace “ya shigo.”" "Da sauri ta gyara zamanta, gabanta na faduwa." "Junaid ya shigo ya zauna sannan ya gaisheta, kallansa tai cikin wani irin yanayi mai wuyar" fassarawa tace “Junaid!” "Kallanta yai bai amsa ba, murmushi tai tace “banyi tsammanin ganinka ba.”" "Fuskarsa a hade take babu alamar fara’a a tattare dashi, kallanta yai yace “nazo ne na sanar" dake abubuwa guda biyu.” Jikinta a sanyaye ta kalleshi tace “inaji!” "Nasan kinsan abinda ya faru kin kuma san jiya Sarki ya ajiye mulkinsa, daga yau har zuwa sanda" "xa’ai nadi bazan sake cewa komai ba, sai dai ina so kisan daga wannan lokacin zan yanke hukunci akan abinda kika aikata a dalilin san zuciyarki." Azeema ta daga kai cikin dana sani tace “nagode Junaid.” Bai amsa ba yace “mijinki nace ya bar masarautar nan shida matarsa yace sai dake zai tafi.” Fuskarta ta hade tace “ni?” "Junaid ya mata kallan eh, haushi ne ya kara rufeta tace “zan dau matakin wannan, ma tabbatar" "wannan me kadai abinda zan iya na taimakeka, ko da kuwa hakan ya kasance na bi shi ne to lalai" zan tafi dashi dan samun sauki da kwanciyar hankali a masarautar nan.” Kallanta yai yace “Ta yaya kika bari san zuciya ya rufe miki ido? Kinsan yanda nake ji a duk sanda "na sa abinci a bakina? Ina tuna ina ci ne a maimakon mahaifina, ko me nakeyi abinda nake tunani" "kenan, taya a cikin mutanen duk duniya ace ke? Ta ya. ”" Idanunsa ya runtse cikin takaici. "Azeema ta share ta kasa cewa komai, idanunsa ya bude yace “ina sauraran yanda zaki sa ya bar" masarautar nan.” "Kallansa tai cikin wani yanayi, mikewa yai ya mata sallama ya fita." "Da kallo ta bishi har ya fita, tace “Abban Zubair da ace kana da rai na tabbatar da sai kafi kowa" "alfahari da yanda danka yake, wannan shine halin cikaken Sarki, karya kuskura ya karaya kar kuma" ya ragawa duk wani mai laifi koda kuwa mahaifiyarsa ce.” Murmushi tai tana mai jin haushin kanta. ****** Dare........ Junaid wanda ya dawo daga fada sunyi karamin zama akan wata shari’a wacce yau ya fara aikinsa. "Daga nan sukai sallah ya taho, kallan bangaren Binta yai sannan yai murmushi yace “Azi bari na" dan lekata.” Azi ya matso yace “Ranka ya dade zatazo anjima ai.” “Cewa nai bazata zo ba?” Ya tambaya yana san jin me Azi zai sake cewa. Da sauri Azi yace “gwara mu leka kam kafin tazo.” Bai amsa mai ba ya nufi bangarenta. ****** "Binta na zaune tana gyara jikinta, yau tun safe ita da Hari suke hidimar gyara jikinta, ita har" kunya ce ta isheta ganin yanda ake ta hidima. "Harira ta tafi ita kadaice a daki tana tufke gashin kanta, jin bude kofa yasa ba tare da ta juyo ba" tace Hari kin dawo mu tafi? "Jin shiru ne yasa ta juyo, Junaid ne ya kalleta tare da harde hannunsa a baya ya fara takowa a" "hankali yana kallan dakin, yace “baki ganni bane?”" Binta wacce bakinta ke bude ta kalleshi tace “Ya j. au Takawa mai kake anan?” Hade fuska yai yace “me? Bakya nemana anan?” Mikewa tai da sauri tazo kusa dashi sannan ta wuceshi zuwa kofa ta tura kofar ta rufe ta dawo gabansa a hankali tace “Yaya ka manta yanzu kai Sarki ne?” Cikin irin radar nan tai maganar shima cikin rada yace “sai akace Sarki karyazo yaga matarsa?” Tace “ba’a ce ba tunda nima yanzu zanje.” Murmushi yai cikin rada ya sake cewa “in koma kenan?” Ya fada yana nuna kofa. "Kai ta daga alamar eh, harararta yai ya hade fuska ya juya, dariyarta ta guntse harya fita sannan" ta kara shafa humra. "Yana fita Harira na isowa, nan suka fita." Junaid rai a bace ya koma bangarensa yana zama ya harde hannunsa ya kalli Azi yace “daga yau "ko nace zani lekota kacemin na tuna, daga ka fadi haka zan gane.”" Dariya Azi ya dane yace “to Yarima.” "Jin sanar da isowar Binta da akai ne yasa ya mike ya shiga daki, Azi yai dariya ya rasa me yasa" Junaid ke komawa yaro inda akai Binta ne. Binta ce ta shigo ta kalli Azi tace “yana ina?” Daki Azi ya nuna mata yana murmushi tare da jan kofa ya fita. "Tura kofar tai ta leka, ganin ba kowa yasa ta bude sosai ta shiga tana kallan dakin." Daga gefe ta ganshi a zaune akan kujera ya harde kafafunsa. Murmushi tai sannan ta nufi gun tace “Ranka ya dade ashe nan ka boya.” "Hade fuska yai yana kara kallan Littafin daya dauka wanda bude wa kawai yai, zama tai ta" "kalleshi sannan ta kalli littafin, dariya tai tare da zuwa kusa da kunnensa tace “a juye littafin yake.”" Kallan littafin yai da sauri sannan ya hade fuska yace “a haka nake san karantawa.” Dariya ta sa tace “Hmmm na manta ashe ana iya yi a haka.” "Harararta yai, hannu tasa ta riko hannunsa tace “Ya Junaid!”" "Kamshin da take ne yasa ya dan lumshe ido, kallanta yai tace “nice fa Bintalo!”" Dariya yasa yace “Bintalo?” Tace “tunda nasan shikadai zai saka dariya ba dole na fada ba.” Dariya ya sakeyi sannan ya kalleta. "Kallansa tai itama ta sakar mai murmushi, hannu yasa ya jawota jikinsa, kan cinyarsa ta zauna" tadan sauke idanunta kasa. Dagosu tai ta zubamai tace “Yau zanta cewa Ya Junaid saboda yaune rana ta karshe da zan kiraka haka.” "Junaid ya kalleta yace “ban yadda ba, na fisan in muna tare mu biyu ki fadi hakan.”" Kai ta daga cikin amincewa sannan ta sake murmushi. A hankali ya sa hannu ya matso da fuskarta ya sa bakinsa cikin nata......... ******** "Shiri ake sosai na nadin sarauta, sai dai duk wannan shirin Zeena da Binta ke yinshi, Hajjo na" "kwance ciwon bakin ciki ya kamata, komai nata masifa ne, sau uku Zeena na zuwa tana cewa ta koma batasan ganinta, Zubair kam gaba daya ya zama sauna, shikenan da yawo a gari yana neman abin da zai daukemai kewa ya rage mai bakin ciki." "Azeema kam ita ke aikawa Binta tazo ta nuna mata abinda zatai, duk wani abin masaruta ta koya" mata sannan ta nuna mata yanda xata zauna da mutane ba tare da ta bari sun cuce ta ba. Sosai Binta ta ke daukan darasi take kara sanin yanda al’amura ke tafiya. "Sarki kam gaba daya abin duniya ya isarsa, duk ya rame ya jeme a yan kwanakin nan, haka ya" koma daya bangaren aka hau gyarana Junaid bangarensa. Zeena sau uku shima tana neman iso a gunsa yana maidata wannan abu ya dameta sai dai data fadawa Junaid yace “karta damu zai sa tagansu.” Azeema yau da kanta ta nufi bangaren Abdulsalam. "Yana zaune a kasa akan dadduma, duk abin duniya ya dameshi yaji isowarta." "Da sauri ya mike ya taho jikin kofa, tana shigowa ya rumgumeta, Azeema!" "Abinda ya fada kenan cikin tsananin farin ciki yace “ban taba tunanin zaki zo ganina ba, nagode" sosai Azeema nasan kema bazaki iya rayuwa ba ni ba.” "Dan matsar dashi tai daga jikinta sannan ta kalleshi, kallanta yai sannan ya jawota ya zaunar" "sannan shima ya zauna, Yace “Azeema!”" Kallansa tai sannan tace “yaushe zaka bar masarautar nan?” Fuskarsa ya canza ya gumtseta yace “bangane ba?” Tace “sai yaushe zaka daina wannan abin daka daurawa kanka? Har yanzu bakai dana sanin abinda ka aikata bane? Na tabbatar da kayi ba sai na tako na ma magana ba da kanka zaka ce zaka tafi.” “Zan tafi amma sai dai in har zaki bini.” Wani murmushin takaici tai tace “in bika in ma me? In bika na ma kallan cutar dani dakai ko na bika na ma kallan makiyi?” Fuskarsa sosai ya canza yace “ko zan mutu sai dai na mutu dake amma wlh bazan daga kafa na "bar nan ba sai dake, inko ba haka ba na mutu a cikin dakin nan.”" Kallansa tai tace mene?” "Yace “nayi rantsuwa kin kuma jini, in har kinaso na bar masarautar nan da Junaid to ki hada" kayanki a gobe ma zan barta in dai zaki bini.” "Kallansa kawai take, tari ne ya kwace mata wanda take ta fama dashi, da sauri ya riketa yana" cewa “baki da lafiya ne?” "Ture hannunsa tai tana kallansa, yace “Azeema mu tafi tare na rokeki da Allah, bani da lafiya ni" "kadai nasan jikina na tabbatar bazan dade a duniyan nan ba, ki taimaka ki bini na mutu kusa" dake.” "Kallansa kawai takeyi, yace “Azeema ki taimakamin dan Allah.”" ***** Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {50} "Junaid dake durkushe gabanta ta kalla, tamai murmushi jin dadi sannan ta kamo hanunsa ta rike." Kallanta yai cikin tausayawa yace “Hajiya Inna!” Cikin maganar tsofafi masu shan wahala ta kalleshi tace “Bazan bar godewa Allah ba dayasa kai "dan Zubair ne ba, ina kaico da lokacin da zuciyata ta rayamun Azeema amanar Zubair taci ita da" "Abdulsalam aka sameka, saboda hankalina ya tashi sanda naje duba d’ana naga halin da yake ciki sannan na taho ina tafe ina tausayinsa kawai na hango Abdulsalam ya nufi ta baya, ina ta binsa" "saboda ina san naji halin da Zubair yake ciki ne naganshi ya nufi kango, abin mamaki naga" "Azeema a cikin kangon, wannan lamari yasa na fara kawo shirme a raina sai dai kafin Zubair ya rasu ya fadamin ba haka bane, Duk ‘ya’yan Azeema nashi me, wannan ne yasa na cire hakan a raina sai dai na san tabbas da wani abin a kasa." "Kwatsam sai gashi yana rasuwa ta auri Abdulsalam, tun daga wannan lokaci ne gaba daya na canza musu, nan na kira Abdulsalam ina mai magana akan auran dayai ban sani ba sai cemin yai ai dama can shi da Azeema ke san juna na aurama Zubair saboda d’a nane, sannan ya daukemin" kai.” "Kallan Junaid tai saboda wahalar datasha gun magana, tace “tundaga lokacin na yanke" tsakanina da Azeema da kuma Abdulsalam!” Junaid ya kalleta sannan yadan yi murmushi mai tattare da tausayinta yace “kiyi hakuri Hajiya ki "yafe musu, sannan Marigayi ne yasa a kaini can ba shi bane.”" "Kallansa tai duk da idanunta basa Kai ta daga tace “nayafe musu Junaid banda wani buri a yanzu," "balle nasan dakyar ko gobe in zan kai, nagodema Allah dayasa zanga wannan rana.”" Kallanta yai cikin tausayi yace “zaki kai insha Allah.” Haka ya zauna a gunta kafin ya fito. ******** "Bangarensa ya koma saboda shirin yana shiga yaga masu shiryashi sun hallara, gaba daya" "masarautar cike take taf ta ko ina, shiyasa yai shigar burtu dan zuwa gun Hajiya Inna." Shiryashi aka farayi. "Daga can cikin gida kuwa Binta da Zeena hidima suke ta ko ina, Azeema ma ta zake sosai tana" hidima dan ta gama tsara abinda zata aiwatar a daren yau. "Sarkin kano bai samu zuwa ba sai dai ya turo babban dansa ya wakilceshi, Sarkin Zazzau ma" "turowa yai, hidima sosai sukeyi, ta ko ina mutane ke hada hadarsu." Zeena ce ta kalli Fure tace “kin aikama Hajjo kayan?” Fure ta kalleta jiki a sanyaye tace “tace ma dawo miki dasu.” Kallan kayan tai da bata kula dasu ba da sannan tai yake tace kawo na kai mata dakaina. "Haka nan suka cigaba da hidima, sosai Binta da Zeena sukai kyau sosai, kayan iri daya ne sai dai" kowa kalarsa daban. "Binta da yake ba fara bace sai ta saka sky blue, ita kuma Zeena wace ke fara sosai saboda" "Abdulsalam tayo ta saka kalar Orange, sunyi kyau sosai." "Safiya uwar hidima ita da mijinta Mahmud ta ko ina hidima sukeyi, an gama shirya Junaid tsaf" sannan suka nufi fada danyin nadi. "Haka aka sha shagali wanda ya kwanta a zuciyar wadanda ke farin ciki, wadanda ke bakin ciki" kuma ya bar musu babban tabo wanda bazai iya warkewa ba. "Junaid kam yayi kyau har bansan ta yanda zan muku bayani ba, yo abinka da mai taro lol" "Haka akai taro aka gama, a kuma daren ranar ne bayan yayi sallar isha’i a saban sashensa yana" "mike saboda gajiyar dayai, tunani yake a kira masa Binta tadan taimaka ta bugamai bayansa," "gefensa Azi ne wanda ya kira, ya kalleshi yace “Sabisu ya wuce din?”" Azi yace “ya tafi ranka ya dade” Junaid ya kalleshi yace “Inasan kai tafiya zuwa kauyen nan.” Kallansa Azi yai yace “wani abin za’ai?” Junaid ne ya kalleshi yace “Azi girma ya dan fara kamaka kamar ya kamata daga wannan aiken ka kuma yi aure ka zauna da iyalinka.” Azi cikin kunya yace “ni ka barni a haka Takawa hakan nan kula dakai yafi komai a gareni.” Junaid yace “a’a in ka dawo zan nemo ma mata da kaina inkai aure sai ka ajiyeta anan cikin masarauta.” "Zubewa Azi yai gaba daya ya rasa ta inda zaiyi magana,ya dago yace “ina godiya Takawa Allah ya" karemin kai a koda yaushe.” "Junaid yace “Ameen, ka shirya ka nemomin mahaifin Binta ka taho dashi.”" Azi ya kalleshi yace “nan?” "Junaid ya daga kai, da sauri Azi yace “angama ranka ya dade.”" "Zagi ne ya fara sanar da isowar Azeema, nan Azi yai sallama ya fita." "Azeema ce ta shigo bayan an mata iso, Junaid ne ya kalleta har ta shigo, sannan ta zauna," kallanta yai yace “Umma?” "Kallansa tai tana murmushi sannan ta ajiye abinda ke hannunta, kaya ne na sarki wanda kana" "kallo zakasan kaya ne wanda Sarki kadai ke da damar sashi, kallanta yai sannan ya kara kallan kaya." Murmushi tai tace “zaka tashi na gwada ma?” "Jiki a sanyaye ya mike, da kanta ta taimaka mai ya saka, ganin yayi mai cif cif ne ya sata yin dariya" "mai hade da hawaye tace “Alhamdulila, na dauka sai mun sake yi.”" "Gaba daya jikinsa ne yai sanyi ya kalleta, kallansa tai tana dariya sannan tace “nagode daka" amshi kyautata.” “Taya zanki amsa?” "Furucin da taji ya fito daga bakinsa kenan, kallansa tai jiki a sanyaye, murmushi ya mata yace" “barina kika yanke shawarar yi?” Idanunta ta zaro ta kalleshi jikinta ya sake yin sanyi a hankali tace “ya akai ka sani?” "Nuna mata yai ta zauna sannan shima ya zauna, kallansa tai yace “taya bazan gane ba? Bayan" kina nufin kin kawomin rigar sallama.” A hankali ta sa hannu a kan fuskarsa tace “Junaid dina ya girma.” Ta fada tana kokarin maida kwallarta. Sauke hannunta tai tadan ja hancinta tace “Abdulsalam bashi da lafiya.” Na sani! Kallansa tai tace “yaushe?” "Murmushi yai yace “jiya, ya kirani.”" Yace me? Ta tambaya cikin sanyin murya. Shiru yai yana tunowa. Kallansa tai tana nazarin abinda yake tunani. "Jiya ya kasance kwanan Zeena ne, bai kuma dawo saban bangarensa ba yana kwance a daki" hadimin Abdulsalam ya zo da sakon san ganinsa da Abdulsalam yake. "Junaid ya mike zai fita, da sauri Zeena ta rike rigarsa tace “Yaya inzo muje?”" Murmushi ya mata sannan ya dafata yace “yanzu zan dawo.” Kallansa tai jiki a sanyaye ya fita. Abdulsalam na zaune a bangarensa Junaid ya shiga. Zama yai Abdulsalam ya zuba ruwa a kofuna guda biyu dake gabansa sannan ya tura ma Junaid kusa dashi. "Kallansa Junaid yai sannan ya kalli kofunan, Abdulsalam yace “daya ruwa ne kamar yanda kaka" "na zuba shi, dayan kuma akwai guba a cikin kofin kafin na zuba ruwan.”" "Kallansa Junaid yai, Abdulsalam yace “ka dau daya nima na dau daya, idan har ka dau ruwa to" "tabbas zan mutu a cikin dakin nan, kaga shikenan sai a ce kai ne ka kasheni, idan kuma ka dau gubar kaga shikenan daga wannan gun kowa zai san nine na kasheka nima hukuncina kisa ne zai" biyo.” Junaid wanda ke kallansa ne yai wani murmushi sannan yace “to sai akace kuma dole nasha ruwan?” Abdulsalam yace “dole ne domin inba haka ba zan shanye duka ruwan kaga duk abinda ya biyo baya kaine.” "Shiru Junaid yai tare da kuramai ido, Abdulsalam ya kalleshi, Junaid yace “baka da lafiya ne?”" "Kauda kai Abdulsalam yai, yana juyowa yaga Junaid ya dau ruwan ya juyeshi a daya cup din" sannan ya shanye. Ido Abdulsalam ya zaro yace “bakada hankali ne?” Junaid ya ajiye cup din sannan ya kalleshi yace “me yasa ka kirani? Nasan ba wai kirana kai dan kawai kai wannan wasan ba?” Kallansa Yai sannan yai murmushi yace “ya akai kasan bakomai?” Junaid yace “menene abin wahala a cik? Ta ina zaka samu guba a inda ni nasa a killaceka? Sannan koma ka samu taya zaka sakama mijin yarka? Sannan inka kasheni da wani ido zaka fito? Sannan babban damuwarka shine Umma ta tsaneka.” "Hannu yasa yana murza idanunsa, sannan ya kalleshi yace “na fadi”" Ya akai? Abdulsalam yaga ya mike ya sanya gwiwowinsa a kasa. Da sauri Junaid ya kalleshi yace “lafiya?” Abdulsalam ya kalli Junaid tari ne yadan kwace mai kafin ya tsagaita yace “ Junaid na san "laifina bazai musaltu ba? Sai dai bazanji kunyar tambayarka alfarka guda uku ba, ka dubi girman Allah ka yafemin? Nasan abinda nai har abada bazan taba samun sassauci ba, laifi ne babba wanda na aikatawa Allah, sai dai zan karasa rayuwata agun neman yafiya gun Allah, nasan hukuncina a musulunce mai karfi ne, sai dai ina nemi alfarma kasa a kulleni a gidan daka zauna" har karshen rayuwata.” "Junaid ne ya kalleshi, Abdulsalam ya kalleshi yace “Sannan abu na biyu ga amanar Zeena da" "Zubair nan, dan Allah ka kula dasu Junaid, laifina karya shafesu basusan abinda akeyi ba.”" "Junaid ne ya hadiya yawon bakinsa, yana kokarin danne raunin da zuciyarsa ke neman yi." "Abdulsalam yace “sai na karshe, ka taimaka ka barni na tafi da Azeema.”" Kallan Junaid yai gaba daya dana sani na damunsa. Junaid me ya kalleshi yace “na farko dana biyu na yadda dasu sai dai na uku banida hakki akai.” "Kallan Azeema yai ya tuno yanda ya fito ya bashi yana hawaye, Azeema tai murmushi tace" “shikenan.” Ta daure tace “Na fahimci nima zamana anan bazai dada ma komai ba sai bakin ciki. Na "tabbatar duk sanda ka tuno abinda ya faro sai ka tsaneni, duk kuma sanda ka ganni sai abin ya dawoma, hakan yasa zan bishi, sai dai ina so kamana hukuncin daya dace damu, duk abinda ka" yanke zan zama mai bi.” Tana kaiwa nan ta mai sallama ta mike. Kallanta yai yace “Umma!” Juyowa tai ta kalleshi da raunana idanunta. Yace “bari a kirashi.” Kallansa tai sannan ta dawo ta zauna tace “yanzu?” Azi ya kira yace a kira Sarki. Hannu yasa a kansa sannan ya rufe idanunsa. Gaba day jikin Azeema ne yai sanyi zuciyarta na bugawa da karfi da karfi. Bazata taba yafema Abdulsalam ba sai dai in ta duba ta wani bangaren gani take komai ya faru ne "saboda ita, ta tabbatar da badan saboda ita ba da duk hakan bazata faru ba." * Ayusher * ZAFIN RANA * ...................... *H̝a̝sk̝ e̝ ̝ W̝ r̝it̝ e̝ ̝r̝s̝ A̝ss̝ o̝ ̝ci̝ a̝ ̝ti̝ o̝ ̝n̝* *Wattpad :-AyusherMohd* *ŋą Ä̤ ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ * {51} "Abdulsalam ne ya shigo gaba daya jikinsa ya kara rarakewa duk ya rame, zama yai Junaid har" yanzu bai bude idanunsa ba. Can sai ga Hajjo wacce yasa itama a kirata daga baya. "Ajiyar zuciya yai sannan ya bude idanunsa a hankali, kallan Abdulsalam yai sannan ya kalli" "Azeema yace ""daga wannan lokacin na haramtawa Azeema da Abdulsalam shigowa cikin gari, zasu koma kauyen dana nemi su zauna, a kuma can zasu cigaba da rayuwa har karshen ransu, sannan dole su zasu nemi abinda zasu ci su sha, hadima daya da hadimi daya na amince su tafi dasu, sannan idan har Hajjo ta nemi ta bisu itama da hadima daya zata tafi, in kuma mijinta ya nemi zamanta anan ko kuma yana neman sauwake mata? zata koma can karshen ginin kewaye, gefen da Hajiya Inna take ta zauna, sannan itama gudun fitina mai tasowa zata bar shiga duk wani" "sabga data shafi cikin masarauta.""" "Kallan Hajjo yai sannan yace ""sannan Zubair zan nadashi Hakkimi zai bar cikin masarautar nan ya" "koma Hakimin garin da na bashi.""" "Maida idanunsa yai yadan lumshe sannan ya sake budesu yace ""inaso a cikin gurin nan maganar" "abinda kuka aikata ta tsaya, wannan ne kadai abinda xan iya muku." "Abdulsalam ya kalla yace ""kafin ka tafi gobe kaga nemi ganin 'yarka.""" "Da sauri yace ""to""" "Yana kaiwa nan yace ""nagama magana.""" "Abdulsalam ya sake zubewa yana godiya, Azeema kam hawaye ne ya zubo mata saboda harta" "fara rashin dan nata, ita kuma kaddararta kenan, bata taso da shi ba yanzu kuma shn hadu gashi zasu sake rabuwa." "Kwallarta ta share sannan ta mike ta fita, Abdulsalam yabi bayanta da sauri har yana tuntube." "Hajjo Junaid ya kalla wacce ta sauke kanta kasa ko tofa kalma daya batai ba, kallanta yai, kallansa" "tai ta daure tace ""Zubair laifin me yai?""" "Kallanta yai yace ba laifin dayai sai dai zamanshi kusa dake zaisa ki sashi, in ba abinda zakice zan" "shiga ciki, sannan kema kiga yarki ta damu." Ya wuce ciki. "Haka tafito gaba daya danta a bace, yanzu kam ba yanda ta iya inba so take a turata kauye ba" "bayan ba ita ya kar zomon ba, rataya aka bata, bataga abinda zaisa tabishi wani kauye ba." ^**** "Abdulsalam ne yabi Azeema da sauri, hannunta ya kamo yace ""Azeema nagode sosai """ "Tari ne ya kwace mai, kallansa tai tace ""karkai tunanin zan bika ne saboda soyayya ko kiyayya," "zan bika ne saboda ma kare mutunci da darajar d'ana.""" "Kai ya daga da sauri yace ""koma menene nidai nagode Azeema ke kadai nake bukata a" "rayuwata.""" "Hajjo wacce ta taho tana jin karshen kalamansa ta tabe baki tace ""sai ka dauki abinka.""" "Kallansa tai bayan ta karaso tace ""kasan dai ni ina nan ko?""" "Yace ""nasani.""" "Ta maka mai harara ta harari Azeema ta wuce, dan inba su ba da duk wannan abin bakin cikin bazai sameta ba, taga samu taga rashi." ******* Washe gari a fada. "Junaid yai gyaran murya wanda yasa kowa sake nutsuwa, kallansu yai dukansu sannan yace" """inada muhimmiyar sanarwa, da farko dai Sarki Abdulsalam da matarsa Gimbiya Azeema zasu bar masarautar nan sakamakon izinin hutawa da sukesan yi, abu na biyu kuma Waziri, Shamaki da Galadima.""" "Da sauri suka kalleshi gabansu na faduwa, suma ina neman kowa ya kawo sunan dansa wanda" "zai gajeshi, ya zauna ya huta a gida, lafiyarku itace anin dubawa.""" """Sannan abu na uku Zubair!""" "Zubair wanda dama yasan menene saboda Hajjo ta fadamai, Junaid yace ""na nadaka Hakimin" "Gabas!""" "Da sauri mai kiran lafiya ya fara yima sarki kiraki, su Waziri kuwa yanda kasan an musu duka" "haka sukaji abin.""" Da wannan aka shiga wata hidimar. "Yana fitowa ya hadu da Azi ya dawo, Azi aya kalla yamai alama da ido akan an sameshi?" Azi ya daga kai alamar eh. "Bangarensa suka nufa daga gefen kofa yaga mutumin dake tsaye duk kayan jikinsa a kode," kafarsa wani sidaden silifas ne. Junaid ya kalleshi da sauri ya zube kasa yana kwasar gaisuwa. Junaid ya kalleshi sannan ya nemi ya shigo ciki. "Da bakin kofa ya tsuguna gaba daya ya rude, sai da Junaid ya nutsu sannan ya kalleshi yace" """kaine Malam Kasim?""" "Da sauri yace ""eh.""" "Junaid ya kalleshi cikin takaici yace ""ka taba tunanin inda yarka take? Ko a wace irin rayuwa" "take?""" 'Yata? "Ran Junaid ne ya kara baci, da sauri Kasim ya kalli Junaid yace ""Binta?""" "Junaid ne ya kalleshi, da sauri ya sake zubewa yace ""Binta? Tanada rai?""" "Junaid yace ""ka taba dana sanin abinda ka aikata?""" "Kuka Kasim ya saka yace ""a koda yaushe cikin dana sani nake, san zuciya yasa na wulakanta yar" "yarinyar da take marainiya.""" Marainiya? "Kasim yana kuka yace ""Yarinyar mutumin daya taimakeni na zauna a garin ne, babban mutum ne" "malami yana zaune da matarsa lokacin da mukazo garin, sai dai yana fama da lalurar ciwon daji, a koda yaushe yana zaune saboda kafafunsa, matarsa nada ciki ya rasu, haka almajiransa kowa ya shiga kokarin auranta dan ya biya hallarcin malam, harnima na shiga ciki, sai dai bansan dalilin Hafsa na zabata ba, nazo kuma ganin na samu dukiyar daya bari nai aure har na koresu.""" "Sake zubewa yai yana wani irin kuka, ran Junaid yakai matuka gun baci yace ""wannan wani irin" "mugun hali ne? Bayan cutar da mahaifiyarta dakai sannan ka sawa yarinyar kiyayar mahaifi?""" "Kasimu yana kuka yana neman yafiya, Ran Junaid s bace yasa Azi ya sa a kulleshi." Ba karamin bacin rai bane ya bayyana a fuskarsa. **** "Abdulsalam da Azeema haka suka bar masarauta bayan kwana biyu da hawan Junaid mulki," "Zeena da Binta sunsha kuka sosai dan Binta tunda Abdulsalam ya kirata yake neman yafiyarta take kuka, dakyar Junaid ya lalabata ta bari." "Binta kam tasha kuka sosai jin Azeema zata tafi, Sai dai tafi tausayin Junaid dan tasan shikadai" yasan me yakeji zai rabu da mahaifiyar da ya samu bayan shekaru masu yawa yanzu gashi zai sake rabuwa da ita. ***** "Hajjo haka Zeena ta taimaka mata ta koma can gefen Hajiya Inna, Junaid yasa aka gyara bangaren biyu, Zeena ta koma bangaren Hajjo ita kuma Binta ta koma na Azeema." "Da wannan Fada ta samu nutsuwa wanda kowa hankalinsa ya kwanta, sai dai Junaid a koda" yaushe yana rashin mahaifiyarsa wacce yaso ya kasance da ita sai dai ba yanda ya iya da kaddarar da Allah ya dora musu. Ba'a dade ba akai rashin Hajiya Inna Allah ya jikanta Ameen ^*********** Bayan watani........ Kwance yake ya juya baya tana matsamai bayansa yana lumshe idanunsa kamar mai shirin bacci. "Can tace ""Ya Junaid?""" Hmmmm Bacci? Uhm uhm! "Murmushi tai tace ""ka juyo in ganka tunda ka hau mulkin nan ganinka ma wahala yake mana.""" "Juyowa yai gaba dayansa ya kalleta, idanunsa yana dan lumshe su yana budesu yana saitinta" "yace ""Binta Allah bacci."" Yai maganar cikin shagwaba" "Juya mai baya tai tace ""ai bacci lafiya.""" "Murmushi yai sannan ya matso ya rungumeta ta baya a hankali ya sa hannunsa cikin rigarta," "idanunta tadan lumshe, hannunta tasa ta rike hannunsa dake kokarin zare mata bra.""" Ya akai? "Juyowa tai tace ""Yaya Allah Bacci!"" Tai maganar yanda yai dazu, dariya ya saka sosai, sannan yasa" "hannu ya cakulota bayan ta juya, da sauri ta juyo tana dariya, tana cewa Yaya bari!!!!" "Ganin yaki bari ta fara ramawa itama, dariya sosai sukai sannan suka kalli juna suna dan numfashi, kan bakinsa ta matso ta sumbaceshi sannan ta koma tana neman kwanciya, hannu yasa ya riko wuyanta sannan ya dawo da bakinta kan nasa, cikin salo da suke sumbatar juna, a hankali yasa hannu ya zare rigarta yana cirewa yana aika mata da sako zuwa bakinta..........." "Bayan sunyi wanka ne ta kalleshi ta hade fuska tace ""sai yaushe zaka fadamin yanda kukai da" "Babana?""" "Idanunsa ya bude yace ""naam?""" "Ta kwanta itama tana fuskantarsa tace ""Ya kukai?""" "Bakinsa yadan motsa sannan ya jawota ya rungume nan ya sanar da ita, hawayen dake zubo" "mata ne sukaki daina zuba, dagota yai yana kallanta." Itama kallansa take tana kuka............. "Rungumeta yai yace ""ki mai addu'a daga shi har Umma abinda suke bukata kenan daga garemu""" "A ransa yace dake da Zeena da alama Allah ya dauramin nauyin zama komai naku, ina rokon Allah" ya bani ikon kula daku. "Hannu yasa akan cikinta yace ""sai yaushe zai fito ne wai? Naga na Zeena harya fito.""" Idanunta dasukai jaa ta dago ta kalleshi tasan so yake yasata dariya........ ******** Bayan shekara daya. "A wannan lokaci ansamu canji dayawa, Zeena ta haifi danta namiji aka saka mai sunan mahaifin" "Junaid Zubair, sai ake kiransa da Baba karami, Binta kuma ta haifi mace aka sa mata sunan mahaifiyarta Hafsa." "Baba karami yaba Hafsa wata daya, kusan koda yaushe suna bangaren Hajjo wacce zaman kadaici" "yake neman halakata, shiyasa ana haifarsu ta nemi a dinga kawosu." "Ramlatu kam ta zama yar sai a hankali, an tasheta itama daga inda take tabar cikin masarauta." "Junaid ya samawa Azi mata aka auramai suke zaune a nan masarauta, Harira ma tayi aurenta." "Yau sun tashi ana ta shiri saboda kasancewar yau ranar sallah karama ce, tun safe ake ta hada" "hada a fada, Zeena ce ta kalli Fure tace ""Zanje na dawo.""" "Da sauri Fure ta taso, Zeena tace ""ki zauna ni kadai zani.""" "Nan ta fito ta nufi hanyar bangaren Junaid, yana zaune yana duba littafin dake gabansa Zeena ta" shigo. "Kallanta yai yace ""Zeena?""" "Zama tai kusa dashi tace ""me kake gani game da yau?""" "Yau? Ya tambaya, tace ""maganar da mukai""" "Yanayin fuskarsa ne ya canza yace ""kina ganin yaune kuma ya dace?""" "Tace ""naga yanzu kowa na hidimar shiryawa, sannan hankalin kowa baya fada har dai zuwa" "yamma idan za'ai hawa.""" "Yanzu ya fahimci manufarta yace ""na gane, zamuje taren?""" "Idanunta ne suka dan canza ta girgiza kai tace ""kaje kai kadai yaya ni zan zauna anan harka dawo" "saboda kauda kokonto.""" "Murmushi ya saki cikin jin dadi, sannan ya rungumeta yace ""nagode Gimbiya.""" "Fita yai ta kofar baya bayan ya kira Azi, suna fita Azi ya zagaya ya fita da mota Junaid ya hau suka" nufi kauyen. "Azeema na zaune tana tsince shinkafa, gefenta kuma Barira ce tana fifita ruwan dake kan wuta," "Abdulsalam dake cikin dake a kwance rai a hannun Allah ne ya fara tari, mikewa tai ta shiga dakim, tari yake sosai hadda amai, ta rikeshi ya gama sannan aka gyara gun, duk sun canza in ka gansu abin tausai, dan ma Azeema ta taho da kadararta da kayanta su suka saida suka yar gona suna noma." "Sai daya kwanta ya kamo hannunta yana lumshe idanunsa, yau kam tun safe yake kwara amai" tsoron halin nan da yake ciki take gashi yasha magani amma abin karuwa yake. Gimbiya! Yanda Barira ta kira sunan ta a razane ne yasa ta sakeshi ta fito. "Daga bakin kofa ya tsaya gaba daya jikinta ya hau rawa, Junaid wanda ke tsaye ne ya mata" murmushi. Shigowa yai ya zauna kusa da Abdulsalam. "Kallansa yai sannan ya kalleta yace ""jikin ne?""" "Jin muryar ne yasa Abdulsalam ya bude idanunsa, yana ganin Junaid ya fara kokarin mikewa sai" amai. Junaid ya maidashi ya kwanta sannan ya kalleta. "Abdulsalam ya kamo hannun Junaid yace ""Junaid ka yafemi """ "Amai ya shiga kara yi kai kace kayan cikinsa zai amayar, nan hankalinsu ya tashi, Junaid ya rikeshi" "yace ""na yafema kai shiru ka kwanta.""" "Sai dai ina, jikin ne ya sake rikicewa anan rai yai halinsa." "Bakaramar firgita Junaid yai ba ganin baya numfashi, hankalinsa ya tashi matuka." "Azeema kam kasa ko kuka tai, haka Junaid suka mai sallah suka kaishi, nan ya nemi su koma da" "Azeema amma tace anan take san zama, dole ya taho ya barta." "Tunda ya shiga moga idanunsa sukai jaaa sosai, tausayin Zeena da Binta su kara kamashi, dole ne" "ya zamar musu uba, yana fatan Allah ya tayashi rekesu cikin adalci." "A haka ya isa akai hawa, sai daga baya akaji rasuwar sa......" Allah ya mana mai kyau Ameeeeeen **** Ayusher Ina mika godiya gareku gaba daya wadanda suka sai littafin nan nagode da karamci da kuma "kauna, kura kuran dake cikin littafin nan Allah ya yafe min su, wanda na fada daidai kuma Allah ya bani ladansu." "Muna nan haryanzu a tare tunda bamu karasa A GIDANA ba. mu cigaba daga can muji Goggo," "Adamu, Zainab da Khalid da kuma Razy " Love you soooo much Onelove❣️