[11/07, 9:43 AM] +234 906 548 4591: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ _*'KIRKIRARRAN LABARI NE, BA'AYI DAN ACI ZARAFIN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAI-DAI DA YANAYI NA RAYUWARSA TO A RASHIN SANI NE!*_ ~~~~~~~ _Pegen farko naki ne_ *_Ummi 'yar bare bari na gaisheki kanuri kina 'kamshi ina binki da humra 'yar dakina Allah ya bar 'kauna ta dan Allah!_* ~~~~~~~~ _Bisimillahi_ Free Pege *1* *'DORAYI* Wani rugujajan gida na hango na jar 'kasa duk katangar gidan ta zaizaye ta dur'kushe ta zama 'yar 'karama saboda tsabar wahala 'kofar gidan hanhai!! yake masu wucewa ma suna kallon cikin gidan .....Wani tattararran buhu na hango wata budurwa ta saki tana fad'in"Haba wannan wace irin masifa ce ace kullum gida a bud'e saboda tsabar mutunci duk kuna zaune a rasa wanda zai sakaya 'kofar ko kishin kanku ba kwayi meye amfanin talauci Allah ubangiji kayi mana katangar 'karfe dashi." "A'a aunty Wasila kyalemu mu sake mu sha iska yo wannan gidan in ba abude shi ba me za'ayi masa gida a ru'be da jar 'kasa ai wallahi ko ta halin 'Kaka sai nayi kudi in huce takaici nayi dakace dana fito ta tsatson babanmu duk shine ya cuce mu aikin banza kawai." Ta 'karasa maganar tana jan dogon tsaki! Uwani dake sunkuye a bakin rijiya tana wanki tace"Kya fad'a Rashida ni kaina da kace nakeyi da auran babanku gashi ya mutu ya barni da wahala da 'kailulu kafin zuwansa gidanmu akwai manyan mutanan da suka fito zasu aureni nace shi nake so saboda naga fari kyakkyawa sai da tafiya tayi nisa a tsakaninmu na gane kyau bashi bane kawai ka auri mai kudi ka huce bakin cikin duniya." Rashi da turo daurin dankwali gaba tace"Ai wallahi Uwani nayi alkawarin sai nayi auran kece raini dan ba zan auri 'karamin mutun ba sai na za'ba na durje sannan dan wannan kyawun nawa ba zai tashi a banza ba." Uwani tace"Yawwa 'yar gari kiyi komai ba komai nice Uwarku nice Ubanku babu shegen da ya isa ya sanya ido a kanku tunda babu wanda yake taimaka mana to kuwa banga dalilin da zai sanya ace dole sai kunyi aure ba ko wacce tayi abunda take so kwalliya kuwa ko wace iri ce kuyi ku futa ku samo manyan maza masu abun hannu ni kaina wannan kyawun da Allah ya baku bana so ya tashi a banza a wofi." Wasila dake tsaye tana sauraransu tace"Yanzu dai Uwani idan na fahimce ki kina so kice mu tafi yawon karuwanci ko."? Uwani tace"To meye idan karuwanci kukayi? ai halak dinku kuke nema da kuje ku dauki na wani gwara ku mika jikinku a biya bukata sai me waye zai gani abunda ba fitowa yake a saman goshi ba." Wasila tace"To sai dai in Rashida amma ni na fad'i miki kome zakiyi wallahi bazan zubda daraja ta da mutunci na ba, na yarda zanyi ko wace irin sana'a ce amma banda karuwanci." Uwani tace"Kece babba kuma kece mara wayo yo mara wayo mana duk wata sana'ar da zakiyi a yanzu ba takai ta karuwanci ba itace yanzu yanzu zaki mi'ka kiji dumus! a hannunki yanzu sai kiga kina murza sitiyarin mota yanda kike da zubi ai nasan manyan mutane da sarai ne za suyi karakaina a kanki." Wasila ta harari mahaifiyar tata tace"Wallahi Uwani kinji kunya kwarai komai hud'ubarki ba zanyi wannan sana'a ba ina da ilimi dai-dai gwargwado sannan kuma ni babu abunda na tsana a duniya irin iskanci, wallahi da in mi'ka kaina gurin wani gardi gwara na kwana banci ba, Sana'a kam nace zanyi ko wace iri ce banda karuwanci." Rashida tace"Wallahi aunty Wasila baki da wayo kin fini fa zubin jiki mai kyau da daukar hankali wallahi kina fad'awa wannan harkar maza zasuyi caaaa! a kanki shikkenan mu da talauci munyi hannun riga." Ashar! ta lailaya mata tace''Kika sake mun irin wannan maganar sai ranki ya 'baci! kema bana fata kiyi wannan sana'a in dai kudi ne ku bari ku gani ku dai ku taya ni da addua." Uwani na shanya kayan wankau din mutane tace"To shikkenan muna zuba ido mu gani a 'kasa uwar tsari yau ki shigo mana da gassasun kaji da lemo nan zamu gane kin zama "yar kasuwa." Wasila tace"Uwani dan girman Allah da Annabi kar kuje yawon bin gidajan jama'a sannan kar ki tura Rashida tayi wannan sana'a wallahi bata dace damu ba a matsayinki na mahaifiyarmu ki kare mana martabarmu insha Allahu yau zan fita a sa'a za'a dace." Uwani tace"To tunda kince haka shikkenan Cin mu da shan mu duk ya rataya a wuyan ki." Tace"Eh naji insha Allahu Allah zai bani ikon d'aukar nauyinku." Har ta d'aga buhun zata futa sai ta dawo tana kallon mahaifiyar tasu tace"Ko na futa dan Allah karku daga buhun nan ku barshi a haka yafi mutunci." Uwani tace"Shikkenan Allah yq bada sa'a." Wasila ta amsa da "ameeen" tasa kai ta fice daga gidan. _Muje zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [11/07, 9:44 AM] +234 906 548 4591: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege2* Wasila na fita ta nufi gidansu Hadiza 'Yar camas! 'kawarta ce sosai amma kuma halinsu ya bambamta! Camas! tana bin maza kuma tana d'an ta'ba shaye shaye sa'banin Wasila da bata shan komai na maye sannan kuma bata bin maza kawai dai ku barta da tsiwa da rashin kunyarta. Camas! na zauna a tsakar gidansu suna hira jefi jefi da mamanta Wasila tayi sallama ta shiga gidan Mahaifiyar Camas mai suna Asabe ta amsa tana fad'in"Wasila kece a gidan." ? Tace"E wallahi ina wuni." Suka gaisa a mutunce har Asabe na tambayarta Uwani tace"Tana nan lafiya. Camas! Tace"Ke 'yar iska ina zuwa kuma nagan ki da mayafi yau ina hijab din."? Wasila tace"Dauko mayafinki muje." Camas ta mike a hanzarce ta shiga dakinta ta dauko wani karamin mayafi ta yafa suka fita Asabe ta bisu da kallo tana girgiza kai al'amarin na 'yar tata sai addua dan a zahiri ma gwara Wasila kanta komai ma Hadiza ya lalace har karatu duk ta watsar gwara Wasila nayin asha ruwan tsintsaye gurin zuwa makarantar. Sai da suka kusa futa daga layin sannan Wasila tace"Ke Camas! yau fa a shirye nake wallahi! Gidan gwammanti zamu je yanzu." Camas! tace"Kai! Wasila me zamuyi a gidan gwamnati kuma."? Wasila tace"Muje kawai ina so in fara harkar Siyasa ne." Camas! tace"Harkar Siyasa kuma lallai Wasila kina so ki jefa rayuwarki a rud'ani Siyasa masifa ce duk ga sana'oi nan da zakiyi ki rufawa kanki asiri sai kice siyasa za kiyi."! "Kinga Camas! idan zakije to ni bana son wata doguwar magana anan gurin harkar Siyasar ma idan ta kar'beka sai kaga ka samu kudi sannan kuma duniya ta san da zamanka." Camas! tace"Kuma fa hakane wallahi hausawa nacewa matsoraci baya zama gwani kawai mu afka ba'asan inda rana zata fad'i ba.'' Wasila tace"Ashe kin gane 'kawata." Bakin titi suka fito suka samu a dai-dai ta sahu kai tsaye sukace ya kaisu gidan gwamna. Mai d'an sahu ya kallesu da mamaki sosai a tare dashi gidan gwamnati to me zai kai wad'annan yaran can? bashi da mai bashi amsa kawai ya ja babur din sukayi gaba.....Yanda suke hirar ne ya fahimci inda suka dosa yace''Yaya na ni dai shawarar da zan baku shine ko zakuyi wannan harkar dan Allah ku tsare mutuncin ku kar ku ku watsar da martabar da Allah yayi muku." Wasila tace"Insha Allahu baba zamu kiyaye." Yace."To nagode da kuka dauki magana ta." Ana kiran sallahr magariba ya sauke su a bakin titi Wasila ta ciro dari biyu a bayan condem din wayarta ta bashi yace."Ai saura dari dari uku ne kudin." "Haba Baba kayi hakuri da wannan d'in ita kenan muka baka ka gani ko na dawowa ma bamu dashi." Yace"Shikkenan." Babur din yaja ya barsu a gurin. Camas tace"Shiyasa sam bana son shiga babur! din dattijai duk 'yan buri ne gwara in shiga na samari masu tara suma su kunna maka kad'e kad'e in ta kama ma suce ka bar kudinki." Wasila hankalinta na kan wata mota dake kokarin shiga rukunin gidan gwamna tace"Wallahi haka maganarki take Yawwa kinga wata mota zata shiga bari na tsayar da ita sai ta hau d'agawa mai motar hannu. A hankali motar ta tsaya inda take kana gilashin motar ya sauka a hankali mamalakin motar ya bayyana.....Wani 'kosashen mutun ne bayan motar a hakimce kana ganinsa kasan yaci ya tada kai da nera yana hada ido da Wasila ya had'iya wani yawu zuba mata ido yayi har suka 'karaso gurin.........Manya manyan idanunta ta juya kana ta dafa motar da hannunta guda ta lankwasar da mirya ta tace"Barka da wuni yallabai ya gida ya fama da jama'a."? Alhaji Ma'aruf ya amsa yana washe baki sosai yace."Lafiya 'yan mata jama'a kuma ku za'a tambaye." Ta saki wani shu'umin murmushi tace"Yallabai kenan, Dama muna neman wata alfarma ne." Yace."Ko wace alfarma ce ku fad'eta mutukar ta shafi gidan gwamnati to zanyi kokarin ganin kun sameta." "Yawwa Yallabai muna so mu fara harkar siyasa ne shiyasa muka dacewar muzo muyi tambaya akai." Alhaji Ma'aruf yayi mirmushi hade da shafa sajensa ya dan tura hular sa 'keya yace"To ai kaya ne suka tsinke a gindin kaba, babu matsala ku shigo mota muje zan shiga gurin mai girma Governor idan na fito sai muje daku guest hause dina in yaso sai muyi maganar. Ba tare da wata fargaba ba suka bude mota suka shiga suka zauna dravar yaja motar suka bar gurin. *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege3* Kunnanshi ma'kale da waya ya fito daga bedroom din shi ya zauna daya daga cikin shirga shirga kujerun dake palon ya wani d'ora kafa d'aya kan d'aya yana masifa!....."Khalifa wad'annan mutanan fa babu Allah a tare dasu ni wallahi tuntuni na dawo daga rakiyarsu shin wai mulki hauka ne!? duk wannan kashe kashen da akeyi da sace sacen yara kananun mun san daga ina ne kawai saboda ana jin tsoronsu sai ayi shiru to wallahi daga yau na shirya d'amarar ya'ki! dasu mulki suke so nima shi nake so Allah ya bawa mai rabo sa'a haba! wannan al'amarin ya ishi talakawa wuya tayi wuya mutane sai mutuwa sukeyi gobe ka fito da wuri zamu fara yawon kamfen insha Allah." Khalifa dake daya bangaran yace."Insha Allahu zan fito da wuri amma yana da kyau ka tanadi matakan tsaro kafin fitar tamu.'' Yace."Kar ka damu da wannan insha Allah Allah zai karemu tunda domunshi muke." Sallama sukayi da juna ya kashe wayar tare da ajiyeta saman tevur din dake gabanshi.....Zuba masa ido nayi ina kallo wai! Allah yayi hallita a gurin kyakkyawa ne ajin farko fari gaggausa yana da dogon hanci da manya ido da gashin gira kewayayyiyar fuskarsa na dauke da sisirin sajensa wanda yasha gyara ya zauna das ya kawata fuskar tashi......Ya wuce ka kirashi yaro gaskiyar magana kenan domin idan ka tsaya ka kalleshi da kyau zaka fahimci shekaru sun d'an tura masa a 'kalla yanzu shekarunsa ar'bain da biyu zuwa da uku........ *Ahamad Musa (Ba iya ka!)* ainin sunansa kenan Matashin saurayi mai jini a jiki mai tashen kudi wanda bai san iya adadinsu ba, shi ya sanya jama'ar gari suke kiranshi da wannan suna *Ba Iya ka!* shima ya samo shi gurin mahaifinsa *Alhaji Musa (Ba iya ka)* wanda ya shahara yayi shura a zamaninsa Allah ka ji'kan maza. Ahamad kawai ya haifa shima kuma kafin ya haifeshi din sai da ya futar da rai! da haihuwa lokacin duk girma ya baibayeshi ya auri wata 'yar filani ashe rabon a jikinta yake haduwarta ta farko ta dauki ciki.......Farin cikin da ya shiga a lokacin Allah yayi yawa dashi ya dinga sadake sadake yana kai mutane saudiya suyi wa matarshi addua Allah ya sauketa lafiya. Allah babu yanda baya tsara lamarinsa gurin haihuwar Ahamad mahaifyarsa ta rasu sosai iyalin Alhaji Musa sukaji mutuwar daga bisani suka barwa Allah lamarinsa.....Sai suka dawo kan Ahamad suka dinga nuna masa so da kulawa mussaman mahaifinshi Allah ya jarrabeshi da kaunar yaron nashi ashe ba zasu dade da juna ba Allah ya dauki rayuwar Alhaji Musa....Mutuwar da ta girgixa zu'katan al'ummar gari suka dinga kuka da fadin"Bango majin ginar talakawa ya fad'i!! Jama'a sukayi dafifi a harabar gidan suna masa addua da fatan Allah ya kai rahama kabarinsa. Tunda Ahamad ya taso yaga yanda mahaifin shi ke taimakon al'umma sai ya dora a inda ya tsaya tun yana dan shekara ashirin a duniya sunanshi ya 'bace a gari mutukar baka kira *(Ba iya ka)* ba to babu in zaka kwana kana kiran Ahamad babu wanda zai gane wanda kake nufi.... Ahamad jama'ar gari ne suka kwadaita masa sha'awar mulki da sam ba tsarinsa bane ya fiso yayi harkokinsa to shima kuma da ya zauna yayi nazarin yanda al'amuran siyasar ya ta'bar'bare sai kawai yayi sha'awar fantsama kansa a harkar domin ya taimaki al'ummar da suke galabaita a jahar mussaman talakawa sune dama abun tausayi. Kallo guda za kayi masa ka gane yana da fuskar Salihai! a zahirinsa kenan a bad'insa kuwa mutum ne shi mara hakuri kuma sam baya barin ta kwana kamar zawo yake mutukar kayi masa abu idan bai rama ba sam baya jin dad'i....bayan wannan halin nasa bai da wani mummunar hali dama ance adan adam tara yake bai cika goma ba Ahamad nada tausayi da taimako sai nace muku ma duk rabin neman kudinsa yanayi ne kan jama'ar gari marasa galihu da na kasassu gami da marayu.......Dalili kuwa bashi da nauyin kowa a kanshi tunda shi ba aurene dashi ba ballanta ayi maganar yara, Jama'ar gari duk sun dauka yana da aure da iyali shiyasa duk adduarsu a kan iyalinsa take 'karewa sai dai kawai amsa da "ameeen" Nasan zakuyi mamakin namiji kamar Ahamad mai jini a jika sannan uwa uba kudi! ga kyau da kwarjini da haiba da yake dasu amma me yasa bai aure ba? Yana zaune hakane ba wai dan bashi da lafiya ba ko kuma rashin matar aure akwai 'yan mata bila adadin dan ba zasu lissafu ba, kawai duk cikinsu bai ga wacce ta kwanta masa a ransa bane ya ajiye maganar aure a gefe saboda yasan cewa lokaci ne idan Allah ya kawo masa matar lokaci guda za'ayi a gama. 'Daya daga cikin masu tsaronshi ne ya shigo palon....Ya d'aga kanshi yana kallonshi A nutse yace."Ya akayi."? Garba yace."Kana da bakuwa tana dakin 'baki mun sauketa." Jim! yayi yana nazari wace 'bakuwa yayi kuma yanzu karfe goma na dare! Ko da yake ai tunda ya fara wannan harkar kuma yayi ta ganin jama'a ya mike a nutse Garba ya bashi hanya ya wuce kana ya take bayanshi. *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege5* Yana tsaye a inda yake Garba ya shigo ya sanya masa ido har ya 'karaso inda yake tsaye.....Kai a 'kasa Garba yace."Sir tayi nisa da layi sosai amma fa ina zargin wani dan gane da wannan yarinyar." Ido ya sanya masa a nutse yace."Kamar name kenan." Garba ya 'kara risinar da kanshi a kasa yace."Anya kuwa ba turo ta akayi ba kuwa kasan fa mutanan babu abunda ba zasu iya ba." Murmushi yayi yace."Garba idan ma turo ta sukayi tayi min sharri ko abu makancin wannan to insha Allahu ba zasu samu nasara ba ni nafi karfinsu tunda bana nufin su da sharri sai alkairi harkata ta siyasa kuma yanzu na fara babu gudu babu ja da baya ni dasu Allah ya bawa mai rabo sa'a." Garba yace."Ka gama magana Yallabai Allah ya baka nasara kan dukanin abunda kasa a gaba." Ya amsa da "ameeen.'' Ya juya cikin yanayin tafiyarshi ta gwazan maza, Garba ya take masa baya. Wasila na fita daga Estate din ta hango motar Alhaji Ma'aruf a can tsallake a fake.....ranta duk a bace ta karasa bakin motar.....'Dan kwankwasa jikin motar tayi Camas! da Alhaji Ma'aruf suka firgita sukayi saurin sakin junansu suna gyarawa Ido jawur! ya bude mata motar yana fad'in" Ya akayi *'Yar gaske* Allah yasa kin aiwatar da komai." Rai a 'bace tace" Wallahi ya'ki bada had'in kai d'an iska kawai yasa na fitar da tsaraicina amma kallo ban isheshi ba." Alhaji Ma'aruf yace."Kai! wannan d'an iskan mutumin taurin kanshi yayi yawa wallahi yanzu duk cikar ki da batsewar ki bai sanya yaji sha'awarki ba? anya ma kuwa yana da lafiya? duk mutum mai lafiya dai ya ganki sai yaji sha'awa ta kamashi." Ya 'karashe maganar yana bin jikinta da kallo. Wasila ganin yana mata kallon iskanci yasa ta dan ja tsaki kadan ta mika hannu tana jan hijab dinta wanda Camas! take kwance a kai! Kallo guda tayi mata ta gane abunda ke faruwa wato bayan futar ta ayarsu suka she'ke! Allah ya kyauta. Hijab dinta ta sanya tace"Alhaji kaimu gida dare nayi sai dai kuma mu sauya wata dubarar na gane guy sai an bude masa wuta dan a tsaye yake kuma wallahi kuka bari ya hau kan kujerar mulki sai kashin ku ya bushe duk sai ya kame ku. Alhaji Ma'aruf ya kunna motarshi yana goge gumi yace."Maganar ki gaskiya ce *'Yar gaske* shiyasa muke 'kokarin muga mun kassarashi tun kafin ya cimmana amma babu damuwa zamu shirya masa wani sharrin." Suna tafiya suna zan can Ahamad dashi da taurinka kansa Alhaji Ma'aruf na fada musu yanda suke dauki ba dad'i a kan suga bayanshi amma abun yaci tura yace shi har jinin kad'angare ya sha duk saboda yaga bayan Ahamd amma asirin bai kar'beshi ba a lokacin ma so yayi ya dawo kansa sai da bokan da ya kulla asirin ya warware tukkuna ya samu lafiya. Wasila tace"Ka rabu dashi Alhaji duk ku daina wahalar da kanku da kudinku da yawon bin malamai a kanshi sharrina ma kad'ai ya isheshi sai nayi fata-fata da rayuwarshi." Alhaji Ma'aruf yaji dadi maganar ta yace.''Mu kuma munyi miki alkawarin baki dadin duniya *Yar gaske* zaki fantama sosai da kudi sai dai ki bawa wasu." Da jin wannan magana tashi sai Wasila ta sake daukar aniyar babu gudu babu ja da baya a kan Ahmadu Musa *(Ba iyak ka)* har sai taga abunda ya turewa buzu nadi. 'Karfe goma sha biyu saura na dare ya ajiyesu a kofar gidansu Ledoji cike da kayan dadi ya bawa Wasila rafar kudi ta dubu dari camas ya bata dubu hamsin sukayi sallama da juna kan cewar zasu fito da wurwuri domi zuwa yawon kamfen........ 'Yar 'kofar da suke karawa Wasila ta tura firgigit Uwani ta mike zaune dama ba baccin take ba tana zaune tana dakon dawowar 'yar tata. Wasila ta mayar da 'kofar ta kare gidan kana ta saki buhun dake sakale suka shiga cikin gidan suna ihu! kamar ba dare ba. Uwani da Rashida suka fito a guje! Wasila ta farke rafar kudin dake hannunta ta soma mannawa Uwani a saman goshi.....Uwani na ganin Sabbin 'yan dubu-dubu na watsi a a tsakar gida sai ta fasa ihu! ta rungume! 'yar tata suka kama rawa wata lafiyayyar gud'a ta dinga rangadawa tana sakarwa 'yar tata kirari......Ita kuwa Rashida kudin take bi tana tsince tana ta faman kyalkyala Dariya sai kace mahaukaciya. Sai da suka gama murnarsu sannan suka dauki ledojinsu suka shige ru'babbiyar rumfarsu da ta kusa ruftawa Rasida ta samo katon faranti suka baje wasu 'kosassan kaji guda shida wanda komai zulamar mutum bai iya cinye guda saboda girmansu ga had'ddaun lemuka masu sanyi nan suka baje suka dinga yagar kaza suna yi mata cin ala tsine uwar me karya, wai! yaushe rabon duniya da ayya raye."!! Uwani ta fada tana shigowa dakin bayan taje ta wanko hannunta........Wasila tace"Yanzu dai mu kwanta muyi bacci dare yayi sai gobe in yaso sai kuji labarin abunda yake faruwa. Uwani tace"Ki d'an gutsira min wani abu mana na kwana dasu a karkashin filona anya ma kuwa yau zan iya bacci oh! duniya kenan." Wasila tace"Uwani kwanta kiyi bacci harda munsharri ai insha Allahu mu da talauci munyi hannun riga." Uwani ta dinga wata mahaukaciyar dariya tana fad'in"Ai dama ni nasan jari na haifa ke ba 'karamar mace bace idan ba'aso ki dan komai ba a so ki dan 'kirar jikinki ita kuma Rashida wannan farar fatar tata itace jarina." Wasila tace"Uwani nifa ba karuwanci naje nayi ba sana'a muka fita mukayi ko ba haka ba Camas!." Tafada tana kallon Camas! dake irga kudinta. Camas tace"Kwarai kuwa sana'ar mukaje mukayi ta siyasa gobe zamu fita da wurwuri shiyasa ma ban wuce gida ba." Uwani tace"Kai amma wannan sana'a ta karbeku wallahi Allah ya bada sa'a ya taimake ku." Suka amsa da "ameen." Sannan ko wacce ta gyara shimfida ta yada ha'karkari ta kwanta ana jira kuma gari ya waye a fita *Sana'a* _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/11, 9:41 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free pege4* Cikin takun girma gami da 'kasaita ya shiga d'akin, lokaci guda 'kamshin turaransa ya karad'e hancinta, ta d'ago shanyayyun idananunta ta zubasu a kansa, tun kafin ya 'karaso inda take zaune ya 'kare mata kalau black beauty mara tsayi sosai da cikar kirji dauke kansa yayi daga kanta ya had'e fuska sosai wannan bakuwar tashi ba ta arziki bace duba da yanayin suturar dake cikinta. Tana sanye da wata matsatstsiyar t_shart da dogon wandon jins wanda ya fitar mata da zahirin hallitarta ta sanya karamin hijab wanda ko kirjinta bai rufe ba tsakiyar kanta yayi tozo da tsayi da alama tana da gashi sosai tunda ga alamunsa nan ya nuna saman goshinta. Hannunsa cikin aljuhu ya isa inda take, ta mike tsaye da sauri tana marmar da shegun idanunta masu rikita lissafin da namiji......Ya kura ma jikinta kallo tayi sosai dan bai hango makusa a tattare da ita ba ta cika har ta batse kuma tana da abubuwan da yake bala'in so a jikin 'ya mace sai dai kash! ba wannan ne a gabansa ba abunda ke gabansa a halin yanzu shine ya za'ayi talakawa su samu walwala da farin ciki. Fuskarshi ya sake tamkewa tamau! yace."Baiwar Allah daga ina? ance dani nayi bakuwa na dauka ta arziki ce sai a ka samu akasi." Wasila taji ciwon maganarshi kasancewar ta macen da bata daukar raini mussaman ga da namiji basarwa tayi ta matsa kusa dashi cikin salon janye hankali tace"Daga duniya na fito nazo ne in d'ebe maka kewa nasan namiji lafiyayye kamar ka na bukatar lafiyayyar mace ka mata. Tsawa ya buga mata yana nuna ta da hannu"Ke! cikin gidana kika shigo kina min wannan maganar? ashe dama zargin da nake miki gaske ne okey get out from my house. "! Maimakon ta fita sai ta durfafeshi tana so ta rungumeshi, ya kai mata wani wawan mari! yana ya tsine fuska sai karkad'e jikinsa yake kamar wanda ya ra'bi motar daukar kashi.....Ya mutsa fuska yake yana korar shaid'an, yace." Za kici Ubanki yanzu yanzu zan sanya a xane miki jiki har gida zaki shigo ki kawo min iskanci ni ba'irinku bane." Fita yayi yana 'kwalawa Garba kira. Wasila ta dauke hannunta dake fuskarta gaskiya yana da taurin kai ta lura ba zai bari ha'kansu ya cimma ba ruwa ba d'an iska kawai tayi irin wannan shigar ya dinga kauda kai yana ya tsine fuska anya ma kuwa lafiyayye ne? bata da mai bata amsa sai tayi maxa ta dauki jakarta zata futa suka buga karo dashi yazo zai shigo kirjinta ya daki kirjinsa yayi saurin ja gefe guda yana kallonta sai wani gumi yake kamar wanda yayi tsere. A ya tsine ta kalleshi tace"Na d'auka ai lafiyayyan namiji ne ashe hotiho ne har kana zagina 'kato da kai baka kunyar zagi anzo a jiyar da kai dad'i kana gudu Allah ya kyauta kaje ka nemi magani." Wata sha'ka ya kai mata ya matse ta a jikin bango (garo) ta dinga kakari idanunta sunyi jajawur!!! Cikin kaushin murya yace."Idan za'a had'a min iri-irin irinki guda dari duk zan gama musu aiki ba tare da nagaji ba, 'karyar iskanci kike yarinya da ina da bukatar mace a yanzu dana fatattaka ki kuma in kwana lafiya 'yar iska mara galihu." Hannu tasa tana 'kokarin 'bam'bare hannunsa dake sha'ke da wuyanta duk ta muzanta sai kyarmar jiki take tana cizan le'banta.....Sai da ya gama galabaitar da isa sannan ya saketa aikuwa ba tayi wata-wata ba ta kai hanni gabanshi zata d'amka! yayi gaggawar ri'ke hannunta yana kallonta da mamaki a tare dashi. Sun jima suna kallon juna ita dashi mugun mamakin 'karfin halin yarinyar yake wato shammatarsa take so tayi ta nakasta shi....Ido jawur! tace"Sake min hannuna."! Ya 'kara rike hannun tamau! yana sakin wani killer smile yace"Kina so ki ta'ba ne."? Wasila tayi tsuru-tsuru tana kallonsa sam ba tayi tsammanin guy zai samu galaba a kanta ba. "Wannan kayan aikin da kike gani yafi 'karfin irinku 'yan iska! na kamilar mace ne mai addani ba irinki mai yawon ta zubar ba." A fusace! ta fuzge! hannunta ta watsa masa kallon raini fuuuuu!! ta kama hanyar fita......Taku uku yayi ya cimmata tare kofa yayi yana me bin jikinta da wani shu'umin kallo. "Sosai kikayi babu wata makusa a jikinki duk inda 'yan mace ta kai kin kai yarinya sai dai sam baki burgeni ba idan ma turo ki akayi to sai kije ki sake sabon shiri ki sani Ahamad ya wuce tunaninki." Yana 'kare maganarshi ya 'kwalawa Garba kira. Ya shigo da sauri yana fadin "Yalla'bai! gani.'' Yace." Maza rakata da bulala idan tayi gardama ka zane 'kafafunta." Garba Ya kalleta, "Wuce muje." Yafada cikin bin umarnin Ubangidansa. Wasila kamar ta hadiye zuciya ta mace tunda take a rayuwa ba'a ta'ba tozarta irin yau ba lallai guy bashi da mutunci amma babu komai sun d'aura idan kere na yawo zabo na yawo watarana za'a had'u. Kallon uku shaura kwata tayi masa kana ta gyada kai ta wuce shi.....Garba ya bita a baya da zabgegiyar bulalarsa....Harbar gidan ya fito ya tsanya tare da zuba hannuwansa cikin aljuhu yana kallo Garba ya tasa 'keyarta har bakin gate yanayi yana caud'a bulala a 'kasa kamar zai daketa hakan ya sake kular da ita ta sake 'kullatar guy girgiza kai kurrum take tabbas maganar da chamas! tayi gaskiya ne babu abunda yake cikin harkar Siyasa sai tozarci da wulakanci, Garba na ganin tayi nisa da layin sai ya juya ya koma cikin gidan. _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/12, 8:39 AM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege5* Yana tsaye a inda yake Garba ya shigo ya sanya masa ido har ya 'karaso inda yake tsaye.....Kai a 'kasa Garba yace."Sir tayi nisa da layi sosai amma fa ina zargin wani dan gane da wannan yarinyar." Ido ya sanya masa a nutse yace."Kamar name kenan." Garba ya 'kara risinar da kanshi a kasa yace."Anya kuwa ba turo ta akayi ba kuwa kasan fa mutanan babu abunda ba zasu iya ba." Murmushi yayi yace."Garba idan ma turo ta sukayi tayi min sharri ko abu makancin wannan to insha Allahu ba zasu samu nasara ba ni nafi karfinsu tunda bana nufin su da sharri sai alkairi harkata ta siyasa kuma yanzu na fara babu gudu babu ja da baya ni dasu Allah ya bawa mai rabo sa'a." Garba yace."Ka gama magana Yallabai Allah ya baka nasara kan dukanin abunda kasa a gaba." Ya amsa da "ameeen.'' Ya juya cikin yanayin tafiyarshi ta gwazan maza, Garba ya take masa baya. Wasila na fita daga Estate din ta hango motar Alhaji Ma'aruf a can tsallake a fake.....ranta duk a bace ta karasa bakin motar.....'Dan kwankwasa jikin motar tayi Camas! da Alhaji Ma'aruf suka firgita sukayi saurin sakin junansu suna gyarawa Ido jawur! ya bude mata motar yana fad'in" Ya akayi *'Yar gaske* Allah yasa kin aiwatar da komai." Rai a 'bace tace" Wallahi ya'ki bada had'in kai d'an iska kawai yasa na fitar da tsaraicina amma kallo ban isheshi ba." Alhaji Ma'aruf yace."Kai! wannan d'an iskan mutumin taurin kanshi yayi yawa wallahi yanzu duk cikar ki da batsewar ki bai sanya yaji sha'awarki ba? anya ma kuwa yana da lafiya? duk mutum mai lafiya dai ya ganki sai yaji sha'awa ta kamashi." Ya 'karashe maganar yana bin jikinta da kallo. Wasila ganin yana mata kallon iskanci yasa ta dan ja tsaki kadan ta mika hannu tana jan hijab dinta wanda Camas! take kwance a kai! Kallo guda tayi mata ta gane abunda ke faruwa wato bayan futar ta ayarsu suka she'ke! Allah ya kyauta. Hijab dinta ta sanya tace"Alhaji kaimu gida dare nayi sai dai kuma mu sauya wata dubarar na gane guy sai an bude masa wuta dan a tsaye yake kuma wallahi kuka bari ya hau kan kujerar mulki sai kashin ku ya bushe duk sai ya kame ku. Alhaji Ma'aruf ya kunna motarshi yana goge gumi yace."Maganar ki gaskiya ce *'Yar gaske* shiyasa muke 'kokarin muga mun kassarashi tun kafin ya cimmana amma babu damuwa zamu shirya masa wani sharrin." Suna tafiya suna zan can Ahamad dashi da taurinka kansa Alhaji Ma'aruf na fada musu yanda suke dauki ba dad'i a kan suga bayanshi amma abun yaci tura yace shi har jinin kad'angare ya sha duk saboda yaga bayan Ahamd amma asirin bai kar'beshi ba a lokacin ma so yayi ya dawo kansa sai da bokan da ya kulla asirin ya warware tukkuna ya samu lafiya. Wasila tace"Ka rabu dashi Alhaji duk ku daina wahalar da kanku da kudinku da yawon bin malamai a kanshi sharrina ma kad'ai ya isheshi sai nayi fata-fata da rayuwarshi." Alhaji Ma'aruf yaji dadi maganar ta yace.''Mu kuma munyi miki alkawarin baki dadin duniya *Yar gaske* zaki fantama sosai da kudi sai dai ki bawa wasu." Da jin wannan magana tashi sai Wasila ta sake daukar aniyar babu gudu babu ja da baya a kan Ahmadu Musa *(Ba iyak ka)* har sai taga abunda ya turewa buzu nadi. 'Karfe goma sha biyu saura na dare ya ajiyesu a kofar gidansu Ledoji cike da kayan dadi ya bawa Wasila rafar kudi ta dubu dari camas ya bata dubu hamsin sukayi sallama da juna kan cewar zasu fito da wurwuri domi zuwa yawon kamfen........ 'Yar 'kofar da suke karawa Wasila ta tura firgigit Uwani ta mike zaune dama ba baccin take ba tana zaune tana dakon dawowar 'yar tata. Wasila ta mayar da 'kofar ta kare gidan kana ta saki buhun dake sakale suka shiga cikin gidan suna ihu! kamar ba dare ba. Uwani da Rashida suka fito a guje! Wasila ta farke rafar kudin dake hannunta ta soma mannawa Uwani a saman goshi.....Uwani na ganin Sabbin 'yan dubu-dubu na watsi a a tsakar gida sai ta fasa ihu! ta rungume! 'yar tata suka kama rawa wata lafiyayyar gud'a ta dinga rangadawa tana sakarwa 'yar tata kirari......Ita kuwa Rashida kudin take bi tana tsince tana ta faman kyalkyala Dariya sai kace mahaukaciya. Sai da suka gama murnarsu sannan suka dauki ledojinsu suka shige ru'babbiyar rumfarsu da ta kusa ruftawa Rasida ta samo katon faranti suka baje wasu 'kosassan kaji guda shida wanda komai zulamar mutum bai iya cinye guda saboda girmansu ga had'ddaun lemuka masu sanyi nan suka baje suka dinga yagar kaza suna yi mata cin ala tsine uwar me karya, wai! yaushe rabon duniya da ayya raye."!! Uwani ta fada tana shigowa dakin bayan taje ta wanko hannunta........Wasila tace"Yanzu dai mu kwanta muyi bacci dare yayi sai gobe in yaso sai kuji labarin abunda yake faruwa. Uwani tace"Ki d'an gutsira min wani abu mana na kwana dasu a karkashin filona anya ma kuwa yau zan iya bacci oh! duniya kenan." Wasila tace"Uwani kwanta kiyi bacci harda munsharri ai insha Allahu mu da talauci munyi hannun riga." Uwani ta dinga wata mahaukaciyar dariya tana fad'in"Ai dama ni nasan jari na haifa ke ba 'karamar mace bace idan ba'aso ki dan komai ba a so ki dan 'kirar jikinki ita kuma Rashida wannan farar fatar tata itace jarina." Wasila tace"Uwani nifa ba karuwanci naje nayi ba sana'a muka fita mukayi ko ba haka ba Camas!." Tafada tana kallon Camas! dake irga kudinta. Camas tace"Kwarai kuwa sana'ar mukaje mukayi ta siyasa gobe zamu fita da wurwuri shiyasa ma ban wuce gida ba." Uwani tace"Kai amma wannan sana'a ta karbeku wallahi Allah ya bada sa'a ya taimake ku." Suka amsa da "ameen." Sannan ko wacce ta gyara shimfida ta yada ha'karkari ta kwanta ana jira kuma gari ya waye a fita *Sana'a* _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/13, 1:07 AM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange *Free Pege6* Da safe suka tashi da wurwuri sukayi wanka tsaf suka shirya tuni Uwani ta ta fasa musu shayi Rashida ta siyo su madara da milo da bread har da su kwai Uwani ta soya musu yau karin kullamo sukayi rigijib suka karasa cinye sauran kajinsu na jiya....Wasila ta kalli Camas! dake gyara daurin dankwali tace"Ya kamata kije gida mamanku ta ganki kafin mu tafi ko." Camas! tace"Ke kin san idan na shiga gida yanzu babanmu nanan ba zai bari na sake fita ba kawai ki kyalesu idan na dawo ma had'u." Tace"Shikkenan ke Rashida zan bada dubu talatin ayi aikin gidanan a sanya kokafi data waje data bandaki saboda bana so in doso layin nan wallahi in hango ku kamar tumaki a akurki wai sunan kuna cikin gida a zaune amma jama'ar dake waje na ganinku wannan gidan ai sunansa kango ba gida ba. Uwani tace"Naji kinyi maganar dubu talatin duk a aikin gidan anya kuwa basuyi yawa ba." Tace"Na fiso ayi komai da inganci a sa kofofi masu kyau insha Allah yau ma idan mun fita zamu samo kudi.' Uwani tace"To Allah yasa." Wasila ta irga dubu talatin da biyar ta bawasu Uwani talatin na gyaran gida biyar kuma tace su dan auno kwanan shinkafa suyi cefane kafin ta dawo.......Haka sukayi musu sallama suka kama hanya suka tafi can guest house din Alhaji Ma'aruf dake a can yace su had'u. Suna shiga harabar gurin suka wasu gugun matasa rukuni rukuni! amma 'yan daba da shaye-shaye sunfi yawa.....Alhaji Ma'aruf da wani mutumi suna tsaye a kansu suna magana dasu. Kai tsaye can suka nufa Alhaji Ma'aruf na ganinsu ya washe baki ya kalli Alhaji Tasi'u "Yawwa kaga 'yan halak! ko yanzu yanzu mu ka gama zancensu ashe suna tafe. Wasila tace" Aikuwa dai muna hanya wallahi kun san matsalar abun hawa sai a hankali." Alhaji Tasi'u ya kalli abokinsa yana nuna Wasila da bakinsa yace"Ko baka fada mun ba na gane wannan ce *Wasila 'Yar gaske!"* Yace."Kwarai kuwa Alhaji kayi mamakin ganinta 'yar karama ko." Yace."Dai-dai kenan duk da kankantar ta nasan zata bamu gudumawar da muke bukata daga gareta Wasila naji kina maganar abun hawa da sauransu ki kwantar da hankalinki zan siya miki mota ta kece raini ke dai kawai ki bamu goyon baya domin zamuyi amfani dake domin cimma manufarmu.'' A dake! tace"Kar ka damu Alhaji a shirye nake wallahi domin harkar na shigo gadan gadan duk inda nasan zan samu nan zan nufa in zaku sakar min kudi magana ta 'kare." Alhaji Ma'aruf da Alhaji Tasi'u suka fashe da dariya suna tafawa, Sai bayan sun tsaigata da dariyar ne Alhaji Tasi'u yace."Kunga wad'ancan mutanan dake zazzaune ko."? Suka ce."Eh." yace."To zaku fita dasu yawon kamfen saboda mun samu labarin *Ahamadu (Ba iya ka)* zai fita zagaye gari domin yad'a munufarsa a kan talakawa to muna so duk inda suka shiga suna yad'a manufarsu su shi ku soke! ku watsa jama'a akwai kayan aiki a tare dasu Lauje karkuji komai kuyi aiki sosai mune muke da mulki a hannunmu babu wani abu da zai same ku." Wasila tace"Kar ka damu alhaji nayi maka al'kawari bakin rai bakin fama." Alhaji Ma'aruf ya kalli Camas yana lumshe mata ido yace."Kefa baki ce komai ba." Tace"Haba karfa ku damu nima na dauki alkawari insha Allah sai mun rusa shirin *Ba iya ka."* Alhaji Tasiu ya nunawa matasan nan su Wasila yace sune abokanan tafiyarsu su kula dasu a matsayinsu na mata, har bakin mota suka rakasu suka shishhiga a'kalla sai da suka cika motaci hud'u irin na haya saboda yawansu sun kai su ashirin da wani abun....Kai tsaye suka dauki titin da zai futar da mutun cikin gari. Cikin shadda fara kal ya fito yana daura agogon silvar a hannunshi hularshi ya kar'ba daga hannun Garba ya d'ora a kanshi *Ba kano* zallah yayi kyau har ya gaji ya zaune gefan gujera yana sanya safa Garba ya gama goge masa takalminsa sawu ciki ya mika masa ya sanya a kafafunsa yana mikewa Khalifa babban amininsa ya shigo shima yana sanya da manyan kaya shi harda babbar riga cikin kamala da mutumta juna suka gaisa kai kana ganin mu'amularsu zaka gane masu ilimi ne suna kuma aiki dashi........suna fita harabar gidan suka tadda matasa sun kai su goma duk suna jiran fitowarsa....Aikuwa ya dinga amsa gaisuwarsu yana daga musu hannu su kuma sun rud'e da fad'in" Sai kayi Ko garin ba kowa mu muna tare da kai kane za'bin talakawa, Kano sai *Dan Musa."* Ahamad ya d'aga dukanin hannuwasa biyu sama da 'karfi yace." *CPC."!* Suka amsa da *"Sa'a!!!"* Yace."Sa'a ta mai rabo ce." Sukace "Kaine kake da Sa'a mai Sa'a." Ya saki murmushi da fad'in "Allah ya bawa mai rabo Sa'a." Suka amsa da "ameeen."!!!" Da sauri Garba ya bude masa bayan wata had'addiyar mota ya shiga Khalifa yabi bayanshi Garba da Dan uwanshi Hadi suka shiga sai direba ya shiga mazauninsa.....Kafin kice kwabo kin nemi jama'ar gurin nan kin rasa duk sun shisshige motocin dake fake a gurin domin su raka dan takararsu yad'a munufarshi.....Kai tsaye titin da zai sadaka da wata unguwa a cikin gari suka nufa mai suna *Jakara* nan yake so ya fara zuwa saboda yanda yake jin labarin unguwar babu kyau ga ta'bar'barewar al'amura da yawa tarbiyar yara matasa ta lalace babu sana'ar yi sai jagaliya da harkar gwan-gwan da sauransu yana so ya fara zuwa unguwar ya yad'a munfarashi kafin ya shiga sauran unguwanni. A kan idonsu motocinsu suka dinga parking, dake duk rabin unguwar Jakara kasuwa ce kafin kice kwabo guri ya hargitse da kaya-kaya jin cewar ga d'an takarar gwamna nan yazo yad'a munufarshi masoya *Ahamdu Musa Ba Iya ka* suka dinga turereniya domin suje su daga masa hannu.....Matasan nan suka fito da tarin pastocinsa suka fara aikin mannawa a bango da shagunan mutane gefan titi suka dinga bi suna mannawa guri ya cika ma'kil! Khalifa ya bude masa samar mota ya fito da jikinsa ya daga hannuwansa biyu yana fad'in" *CPC."!* Sai gurin ya rud'e! da fad'in" *Sa'a!!!!!* Su Wasila suka keto gurin da motocinsu a guje!!!! A take mutane suka watse kowa na ceton ransa.....Parking din motocin sukayi suka fito a fusace! ko wanne da makami a hannunsa.....A sai guri ya hargitse ihu!! kawai kakaji da gudu radadada!!!!! Hankalin Ahamad ya tashi sosai gashi Police guda biyu kacal ya dauka kuma suma al'amarin yafi 'karfinsu domin 'yan daban gidan gwamnati suna da muggan makamai!! Ya ware murya sosai yana fad'in"Kowa yayi takansa ya tsira da rashi."!!!! Wani *Dan daba* ya 'bullo daga wata hanya dake da maraba da wata katuwar kwata hannunsa rike da wata shar'be'biyar addah! sai kartar ta yake a 'kas! yana sakin wani uban ihu! da fad'in" *Sai kayi ko garin ba kowa."* Eh! yane! mu za'a kawo wa raini a unguwar tamu! ashe yau sai an zubar da jini wallah!!!! Huhhhhhh! ya kurma wani uban ihu! yayi kan 'Yan daban Gidan gwamnati yana sararsu ta ko'ina!!! Wasila dake can aikin Ya'bawa Fastocin Ahamad kwata da 'bakin mai!! ta hango abunda ke faruwa Abokanan tafiyar ta sun suna shigewa mota saboda *'Kumd'um!* dan daban nan ya soma fitarwa da wasu jini sai suka razana suka soma shiga mota.....Da gudu tazo shiga mota *'Kumdum'* ya fuzgo hijab din jikinta ta dawo baya 'Kara ta 'kwallara! ganin yana 'kokarin kai mata sara da 'katuwar addar dake hannunsa ta rintse ido gabanta na buguwa fat! fat! fat! shikkenan ta mutu!!! Shiru taji gurin yayi ta bude idonta a hankali tana bin mutanan gurin da kallo......Shi ta gani tsaye a gabanta hannuwansa cikin aljihu yana mata wani mummunan kallo still ga *'Kumdum* rike da shar'bebiyar addarsa a hannu.!! Kallon juna suke ita dashi! tsaf! ya gane yarinyar nan ce da shigo masa gida jiya tabbas ga maganar Garba ta fito ashe da wata manufa ta ziyarceshi ya gode Allah da bai sanya masa kwad'ayin mata ba da badan hakaba da tuni bukatarsu ta biya a kansa. Ya kalli 'Kumdum dake zare ido yana ciccije baki!!! Yace."Rabu da ita kar kayi mata rauni ko ka zubar mata da jini! taci albarkacin sunan mace da ta amsa mace duk inda akasanta mai daraja ce da kame kai Astagafurullah wannan yarinyar ta 'batawa mata sunansu idan ka daketa ko ka zubar mata da jini duk a banza tunda na lura da akwai bakin iyaye a kanta so ka kyaleta taji da abunda ke damunta zamu dai cigaba da yi mata addua idan mai shiryuwa ce kuma insha Allahu muka samu mulki a hannunmu duk zamu tattara ire irensu mu samu mu had'asu da mazaje dai-dai dasu muyi musu aure babu shakka za'a samu sassaucin wasu abubuwan." 'Kumdum! ya saki hijab d'in Wasila dake damke! a hannunsa yana fad'in"Eh! Yanda kace haka zakayi mahadi mai dogon xamani insha Allahu kano ta kace ko ana ha! maza ha! mata sai ka tuge! wancan wawan! da bai iya komai ba sai hauka.''!!!!!! Jama'ar dake gurin suka sa ihu! da fadin""Maganarka haka take 'Kumdum Kano ta d'an Musa ce ko ana so ko ba'a so sai yayi."""!!! Wannan damar da Wasila ta samu ya sanya tayi wuf! ta bar gurin can inda motocinsu suke ta nufa ta tarar duk an ragargaza gilashin motocin Camas! ta bude motar ta shiga da sauri wani matashi ya daki motar da kafarsa yana musu ihu!!! Sai da suka yi nisa da gurin sai suka saki wa'kar gwamnan dake ci a yanzu Mai taken *Munyi muku fintinkau!!!!!! Kano sai kallo daga nesa mai raba gardama yazo Enginer Lawan Rabo, duk wanda zai ja dakai shine wawa!!!!!* Wasila ta fito da jikinta ta saman mota tana watsawa Ahamad da'kuwa! da dukanin hannunta tana sake fad'id" *Wanda zai ja da Engener Lawan Rabo shine wawa!!* Ahamad yana kallon sanda take watsa masa hannayenta da sunan da'kuwa! *{Zagi!}* ransa ya 'baci sosai lallai yarinyar nan bata da kirki ya lura yar adawa ce mutuka dole ne ya sanya ayi masa bunkice akanta domin abun nata ya wuce gona da iri. Mota ya shiga tare da jama'arshi jama'ar gurin sai daga masa hannu suke suna masa fatan alkairi yana amsa musu cikin sakin fuska amma in zaka tona zuciyarsa a lokacin zaka tarar tayi ba'kikkirin sakamakon zagin da Wasila tayi masa wanda ba kowa ne zai fahinta ba sai shi wanda akayi dominsa. _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/13, 4:15 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko Orange_ *Free Pege7* Wani irin gudu motocinsu sukeyi kan kwalta, suna sakin ihu!Wa'kar injiniya Lawan Rabo ta tashi a motocinsu jama'ar gari suma suka dinga ihu! da fad'in "Ba mayi!!! insha Allahu kano ta d'an Musa ce! su dinga jifan motocinsu da duwatsu suna ihu!!! Su Wasila da kyar suka sha amma dai hakan yayi musu dadi tunda dai sun rusa shirin *Ahamadu* sun hanashi aiwatar da nufinsa wannan ya nuna musu suke da nasara a kanshi. Khalifa ya kalli fuskarshi ya ganta a murtuke! yasan ranshi a 'bace yake gyaran murya yayi yace." Wai wannan cin maganin da kakeyi na menene dole fa ka fuskanci irin wannan 'kalubalan al'amarin siyasa sai addua komai mutuncinka sai ya zube kauda kanka kawai zakayi. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya d'an gyara zamanshi yace."Khalifa sam abunda mutanan suka turo ayi mun bai dameni ba saboda nasan sunyi abunda yafi wannan......Shin wai baka ganin zagin da yarinyar tayi min ne."!? Khalifa ya dan gyara zaman hularshi yana sakin murmushi a hankali yace."Duk akan idona al'amarin ya faru sosai nayi mamakin tsaurin idonta na fahimci kuma harkar takeyi da gaske so kar ka damu da wannan Siyasa ce a gabanka ma sai a zage ka a jefe ka kai dai tunda kace za kayi to sai ka daura d'amara! "No!!! Karya ne wallahi." Yafada a zafafe! ya kalli Khalifan da jajayen idanunsa da suka rine da 'bacin rai! yace."Khalifa Siyasa ba hauka bace kamar ni wannan yarinyar gantafalfala ta zageni! kai kanka kasan halina bana ya fiya mutukar mutum ya shiga gonata ban hanata tayi min komai ba na yarda siyasar 'kasa ce amma banda zagi sai na ci mutuncinta wallahi."!!! "Clm dwon mana ka nutsu fa ba'a saurin yankw hukunci da gaggawa ka kyaleta kawai idan ta sake sai ka dauki mataki a kanta amma yanzu kana yi mata wani abu zasu 'kulla maka wani sharrin kasan halin su dai." Ya rintse ido yana sake hango lokacin da take watsa masa hannuwanta da sunan zagi! Ya bude ido yana sauke numfashi idan fa bai rama abunda yarinyar tayi masa zuciyarsa zata iya tarwatsewa mutum ne shi mai bala'in kishin kansa da 'kaunar iyayensa ya tsani na 'kasa dashi ya raina shi ko ya zageshi baya daukar irin wannan rainin shiyasa yanzu hankalinsa ya tashi mutuka duba da yanda yarinya 'kankanuwa wacce bata wuce 'yar cikinsa ba ta zageshi dole yayi bunkice a kanta. Khalifa ya dinga tausarsa da kalamai masu sanyi yana nuna masa haka lamarin siyasa yake dole fa sai ya kauda kansa ga dukanin abunda 'yan adawa zasuyi masa idan ba hakaba kuwa zai 'bata rawarsa da tsalle kawai ya share yarinyar ya bari kawai duk sanda ta sake to suma baza su kyale ba. Garba Da Hadi suka ce "Sir da ka bari wannan 'dan daban ya koya mata hankali wallahi yarinyar bata da mutunci ko kadan muma munga abunda tayi maka wallahi munyi rantsuwar duk sanda ta sake maimaita abunda tayi sai munyi mata tsirara sai mun tujara ta a gari karyar iskanci takeyi. Ajiyar zuciya ya sauke ya dan ji sanyi cikin ranshi Yace." Na rabu da ita saboda maganganunku ammafa ku sani duk sanda ta sake kwatanta zagina wallahi ranar sai ta raina kanta sai tayi nadamar zuwanta duniya babu ruwana." Khalifa yace."Yawwa mai girma Governor haka ake son shugaba da daukar shawara insha Allahu kai ke da nasara a kansu" Hannu ya bashi suka rike suna sakin dariya Ahamadu yace." *CPC."* gabad'anyansu suka amsa da *"Sa'a!* Ya sake fadin." *CPC."* Suka amsa da *"Sa'a."!* Yace." Mulki na Allah ne."! suka amsa da fad'in "Insha Allahu kai Allah zai bawa." Ya amsa da "Allah ya bamu Sa'a." Suma suka amsa da "ameen." Wasu Wasila kuwa kai tsaye gidan Governor suka nufa domin su alhaji Ma'aruf nacan gidan suna meeting sai sukace su samesu a can, suka samu wata katuwar rumfa suka zazzauna kamar wasu almajirai suna jiran fitowarsu.....Can sai gasu sun fito daga wani dakin wanda yake nuna alamun dakin taro ne sun kai su goma wannan yana wane wannan sun sha lafiyayyun shaddodi sai motsi takeyi tana she'ki masu Cot a cikinsu kad'an ne......Kai tsaye rumfar dasu Wasilar suke suka nufa ta ganinsu sun doso gurinsu sai ta mike da saurin gaske ganin harda Governor ya sanya ta fara masa kirari da bambad'anci! dama Wasila akwai shegen za'kin murya tsiya Governor tun kafin su karaso yake murmushi babu shakka wannan yarinyar za'aje da ita irin wannan washi haka!!!! Gabadayansu suka mike tsaye ganin sun iso gurin Lauje dake jin haushin abunda Wasila takeyi ya buga mata tsawa da fad'in"Ai sai ki saurara haka domin mai girma governor ya iso ki bamu damar magana." Wasila tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya. Gaisuwa suka mike garesu suka amsa sosai Alhaji Ma'aruf ya kalli Lauje yace."Kaine wakilin tafiyar ya akayi alamu na nuna mana cewa akwai nasara a tafiyar." Kafin Lauje yace komai Wasila tayi karaf! tace"Alhamdullihi muke da nasara insha Allah domin tun zuwanmu gurin muka watsa shirinsu muka tashi hankalinsa dana jama'arsa ni da kaina na dinga bin pastes dinsa da suke mannawa ina yagewa ina watsa masa ruwan kwata da bakin mai! da 'kyar! nasha a hannun wani d'an daba."! Governor Ya kallesu yana fad'in"Da gaske maganar haka take."? Duk suka amsa da "Hakane ranka ya dad'e."! Lauje yaji tamkar yaje ya sha'ke wuyan Wasila shin wai me take nufi ne? yarinyar fa ta za'ke da yawa anya ba sai ya taka mata burki ba kuwa." Governor Ya kalli Wasila yana murmushi Yace."Dama tun kafin na ganki na samu labarinki gurinsu Alhaji Ma'aruf gaskiya ne *'Yar gaske!* kin cancanci ayi miki komai zamu zauna dake insha Allahu ki fada mun dukanin bukatunki." Wasila aka saki murmushi ana gyara tsayuwa farin ciki duk ya isheta tace"Godiya nake mahadi mai dogon zamani governor da ba ta'bayin irinshi ba ba za'ayi ba insha Allah." tana gama maganarta Ta koma ta zauna inda take kana ganinta zaka gane tana cikin farin ciki babu shakka bukatarta ta kusa biya sun kusa yin hannun riga da talauci. Alhaji Tasi'u ya kalli Lauje dake faman cin kunu babu shakka katsalandan din da Wasila ke masa akan harkarsa ya isa har yaushe ta shigo harkar da zata dinga za'kewa da za'kalewa kan komai kafin zuwanta shine yake jagoranta al'amura da suka shafi harkar jagaliya amma ya lura yarinyar idanunta kar suke zata iya komai bayan haka kuma macace dole tafi shi samu power a kanshi Yace."Duk wasu bayanai munji su daga bakin *'Yar gaske!* kuma kun tabbatar da maganarta babu shakka munji dadin kasancewarta a wannan tafiya tamu, domin ta nuna mana ita jaruma ce kuma mai alkawari zata iya fansar da ranta a kan wannan harkar Kai Lauje daga yau Wasila *'Yar gaske* itace shugaba a wannan tafiya taku abunda tace muku shi zakuyi kai kuma in yaso sai ka zama mai take mata baya. Lauje wani irin gumi! ya shiga yanko masa kai!!! 'Karya ma kenan! wannan afiruwar yarinyar itace za'ace zata jagorance shi aikuwa da sake!!! wallahi ba zai yarda ba. Cikin ranshi yake wannan zantukan amma a fili sai yace."Gaskiya ne Yallabai dukaninmu mun yaba bajintar yarinyar dan haka zamu bata hadin kai dari bisa dari mu dai fatanmu mulki ya cigaba da dawwama a hannunmu." Governor Ya kalli Alhaji Ma'aruf yace."Ayiwa *'Yar gaske* kyauta ta mussaman Kafin mu zauna da ita.....Lauje da sauran yara suma ayi musu kyauta dai-dai gwargwado ai sun faranta min rai mutuka." Aikuwa Alhaji Ma'aruf ya d'auko daurarrun kudi 'yan dubu dubu sabbi fil fil ya mikawa Wasila dauri hud'u....Kana ya mikawa su Lauje dauri hud'u kwatankwacin na Wasilan Ita kuma Camas aka bata dauri d'aya.....Wannan al'amari yayi masifar 'batawa su Lauje rai!! lokaci guda sukaji sunyi masifar tsanar Wasila daga zuwanta zata zo ta kar'be musu fada lallai da sake sai sun dauki 'kwakkwaran mataki a kanta. Wannan karon da wuri suka koma gida wajejan karfe biyar da rabi tunda suka doso layin Wasila ke sakin murmushi ta hango gidansu da 'kofa lafiyayya sannan an d'an kwaskware wasu guraran da suka ruguje hakan yayi mata dadi sosai babu abunda ta tsana irin taga ana hango mahaifiyarta da kanwarta a waje.....Gidan sai 'kamshi yakeyi Uwani an dage ana ta soya miyar dage dage Rashida kuma na gefe tana yanka salak gefe guda kifi ne manya manya (sukunbiya) an soya cikin kwalanda za'a sa a miya....Uwani ta amsa sallamarsu tana washe baki Rashida ta gyara tabarmar da take zaune tana fadin "Aunty Wasila yau da wuri kuka dawo Allah yasa dai an samo wasu kudin.....Wasila ta cire hijab din jikinta ta ta shiga zazzage kudin da suke cikin jakarta......Uwani ta razana! ganin uban kudi gaban Wasila sun tassama dubu dari biyar! Sai kawai ta dora hannunta a saman hancinta ta dinga rangwada bud'a yi takeyi kamar zata tsine hancinta. Sai da tayi mai isarta sannan ta iso inda suke zaune Rashida sai faman irga kudin take tana ihu!! " Kai jama'a! ashe dai zanga wannan rana ni Uwani, ashe idona zai ta'ba ganin irin wadannan uban kudade masu yawa lallai wannan sana'a tafi irin wacce nakw cewa kiyi 'yata Wasila ina alfaharin haifarki Allah yayi miki albarka Wasila." Uwani ta gigice sai sambatu takeyi Camas da Rashida sai dariya suke mata....Wasila kam mikewa tayi jikinta duk ya mutu duk sanda ta tuni artabunsu da *'Kumdum!* sai gabanta ya yanke ya fad'i shikkenan fa idan da da tsautsayi da karar kwana da tuni ta zama tarihi domin ta lura babu imani a cikin zuciyar dan daban ta wani gefan kuma guy nan ya taimake ta dan sai yanzu take nadamar zagin da tayi masa kuma ta lura ya gani ya kuma ji rashin dad'i, sosai abun yake dan ta'ba zuciyarta babban mutum ne da shekarunsa suka wuce tayi masa haka domin zuwanta gidanshi na farko bata tantance kamaninsa da shekarunsa ba sai ganin da tayi masa a dazu.....Ganin zuciyarta na damunta ya sanya ta tattara ta watsar da al'amarin babu wani abunda zai faru dan ta zageshi ai Siyasar 'kasa ce kowa yana da 'yancin yin abunda yake so ga wanda baya so....Wanka tayi ta fito ta tarar Camas ta tafi gida ta kalli Rashida dake zuba musu abinci tace"Idan anjima zamuje Sto muyi siyayya dukanin abunda bamu dashi walau naci dana sha da daurawa." Rashida tace"Shikkenan bari nima nayi wankan sai muci abinci mu tafi." Uwani kam sai faman juya miya takeyi tana murmushi Ah!! Allah maiyin yanda akeso dare daya Allah kanyi bature Arziki ya sakko musu lallai babu abunda yafi haihuwa rana a duniya shiyasa masu karin magana ke cewa ko kana gudu haifi ka jefar ita dai gashi haihuwa tayi mata rana. _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/13, 10:52 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege 8* Suna idar da sallahr magariba suka fito har Uwani domin tace itama zata bisu kasuwar suka sanyawa kofar gidan katon kwado kana suka fito titi domin samun abun hawa, suna tsayawa wani mai d'an sahu ya tsaya gabansu Wasila tace" Al'Ikilas zaka kaimu." Yace."An gama hajiya nawa zaku bayar."? A ya tsine tace"Muje dan Allah bana son harkar fatara ko nawa ne kudinka zan baka." Me dan sahu yace."A'a hajiya daga magana karfa ki zageni dan wallahi kika zageni ba yarda zanyi ba." Rashida tace"Kai dan Allah muje kana jan duguwar magana ai laifinka ne meye na tambayar nawa zamu bayar mu ba mutsiyata bane." Yace."Bana son in dauke ku ne bamu daddale daku ba sai kunzo sauka ku kawo min kauli da ba'adi shiyasa nake so naji nawa ne kudina." Wasila taja tsaki! tana kokarin shiga babur dole ne ta siyi sutturu masu tsada saboda ta lura suma 'yan a dai-da ta basu da kirki daga sunga mace da kod'addiyar atamfa sai su hau wulakanci in kuwa suka ga mace da dankareran lesi da gwala gwalai har rubibin daukarta sukeyi saboda sun san ko nawa sukace ta basu zata basu. Wasila har waya take so ta sauya sai dai kuma abun yayi yawa dole gobe ma su sake fita dan yau kayan kwalliya zasu siyo da atampopi da mayafai da takalma, har bakin super Sto din ya ajiyasu ta dauko dubu daya dal ta mika masa baiyi tsammanin haka daga gareta ba ya dauka zaiga ta fito da dukukkunanniyar dari biyu canji yake kokarin dauko mata tace''Rike na barka maka." Ya sako baki yana kallonsu sun juya suna tafiya, kai! ammafa yayi mamakin lamarin nan ashe arziki ne yake binsa yana basarwa duka kudinsa dari uku ne gashi ya tashi da dari bakwai sun isheshi karin kummalo da safe dan haka sai kawai ya nufi gida ya tashi daga aiki sai kuma gobe. Su Wasila kuwa zagaye Store din suke suna so suga iyakarsa sun kasa babban store ne da sai wane da wane ke zuwa gurin duk abunda ke cikin gurin ba na yarwa komai kudi ne Wasila suka dauki atampopi kusan kala bakwai suka d'ibi lesuka da mayafai sannan suka nufi gurin kayan make up nan ma ta dinga hada kayan kwalliya so take ta dawo babbar mace ta dinga cin kwalliya dama can ita bata yarda da karamar shiga ba, Can bagaran turirrika ta nufa su Uwani da Rashida suka tsaya gurin gwala-gwala sai 'kyauyanci sukeyi..........Yana kai hannunsa kan wani kwallin turare itama ta kai nata hannun ya sauka akan nashi. Da sauri ta dauke hannunta tana kallon zatinsa gaggausa mutum ta gani tsaye a kanta yayi mata rumfa kasancewar ta mace mara tsayi sosai.....Sai ta daga kanta tana kallon fuskarta a lokaci guda taji wani irin miyau! ya tsinke mata a baki ganin wanda yake tsaye kusa da ita. *Ahamdu* Da sauri tayi 'kasa da kanta tana adduar Allah yasa bai gane ta....'Kokarin wucewa takeyi taji yo muryarshi na fad'in"Zo ki dauki turaranki na samu wani." Gaba tayi ba tare da ta amsa masa ba, suka hadu da Garba wanda yake kokarin isa inda ubangidansa ke tsaye.....Sarai! Garba ya ganeta sosai dan har waiwayenta yakeyi Ahamdu yace."Kai! kula dallah! kallon me kakeyi ne." Da sauri yacs."Sir baka gane waccan yarinyar ba."? Tsaki yaja yana d'an ya tsine fuska yace."Meye ya dame ni da ita da zan tsaya tantance wacece."? Garba yace."Sorry sir yarinyar nan ce fa ta d'azu." Ya zare gilashin dake fuskarshi yana kallon Garba da mamaki yace."Da gaske."? Garba yace."Wallahi itace sir wai baka gane yanayinta bane ai naga a furgice ta bar gurin nan." Murmushi yayi kawai ya mai da gilashinsa, ashe ita ta ganeshi shiyasa tayi gaggawar barin gurin yanzu ya gane Jagaliyarta ta 'karya ce tunda bata iya tsayuwa a gabanshi ta mai da masa da martani.... Suna tsaye a gurin biyan kud'i ya 'karaso gurin sai taga ana bashi girma duk ma'aikatan gurin na kiranshi da Sir tayi 'kasa da kanta tana jinsa na magana cikin had'addan turancinsa da babu tangarda a ciki duk sai ta raina kanta gaskiya ilimi yayi addua takeyi Allah yasa kar ya waiwayo ya kallesu..........Ya kalli Manager gurin da Hausa yace."Cikin wannan satin Salim zaije saudia wani na'uin turare da babu a gurin nan sa ka rubuta masa gudun mantuwa.'' Yace."Insha Allahu." Wucewa yayi ba tare da yayi kuskuran kallon inda suke tsaye ba, suna fita Uwani tace"Oh wannan turanci sai kace wani ba amuruke da alama dai shine shugaban gurin.....Manager da ba hausa yake ji sosai ba ya d'aga mata kai alamar Eh......Rashida tace"Gaskiya aunty Wasila mutumin nan yayi wallahi kun dace dake dashi dama yace yana sonki." Wata harara ta watsa mata "Dallah kwaso kayayyakin mu wuce kin tsaya kina shashanci dare yayi." Rashida ta dauki manya manya ledoji guda biyu Uwani ma ta dauka itama ta dauka haka suka fita hannunsu ni'ki ni'ki da kaya su ba mota ba, sai da suka fito ne ma suka fahimci dare yayi sosai dan goma ma ta gota.....Da kyar! suka samu mai babur ganinsu da kaya ya sanya ya lafta musu kudi wai dubu biyu Wasila tace"Muje zan baka." aikuwa da sauri yaja babur din suka dauki hanya. Sai da suka zo dai-dai titin makarantar legal tayar a dai-dai tar tayi faci!!! Tofa ga dare gashi babu masu faci a kurkusa ga gurin tsit! sai kukan tsintsaye....Uwani ta fito tana salati da sallami motocin gida jefi jefi ne suke wucewa suma kuma da gudu suke wucewa saboda sun samu arhar titi babu go solow, Wasila ta fito daga babur din tana fad'in"Yanzu ya za'ayi? kai innalilihi gaskiya banji dad'i ba wallahi." Mai babur yace."Ni wallahi na rasa ma ya zanyi dana sani nake wallahi dan idan ban samu wanda zaiyi min faci ba dole in bar babur din a gurin.......Wasila tace"To mu kuma muyi yaya kenan."? Yace."Hajiya dan Allah ki kyaleni naji da abunda ya dame ni ai kuna da kafafu ku karasa mana a kafa." Rashida tace"Ka duba tazarar dake tsakanin nan da dorayi fa akwai sauran tafiya gaskiya mu dai kasan yanda zakayi damu." Haushi yasa mai babur din fad'in"Ai sai ku kwana a gurin ni kunga tafiya ta." Ya zare key dinsa daga jikin babur din ya dauki hanya ya barsu a tsaye a gurin.......Sai da suka daina hangoshi sannan suka tabbatar da cewar da gaske ya tafi din Wasila tace"Ai sai ku dauki kayan muma mu daura damarar tafiya da kafafunmu dan babu wani alamun babur a kan titin nan." Suka d'addauki ledoji suka saici hanya suna tafiya fakam fakam! ga nauyin kaya ga gajiya sunyi masifar galabaita......Sunyi nisa d a tafiya sosai suka hango ana haske su da touch Dukaninsu sun razana! ganin wasu tsagerun matasa sun durfafo inda suke "Kai! matanan daga ina kuke ne."? Uwani tace" Ku bamu hanya mu wuce munyi dare zamu koma gid.....ai kafin ta rufe bakinta na kusa da ita ya wafci ledar hannunta yana zazzagewa.....Wasila tace"Kai meye haka kuk.....Ita taji ya fizgo jakarta dake rataye a kafad'a ya zazzage a kasa uban kudi suka watse a gurin....Ihu!! suka zumduma! suna fad'in Kai!! ashe yau mun fito a sa'a Kwashe mana su mana jeka bunciki jikinsu kaga ko da akwai sauran wasu idan da gold a jikinsu ka ciro." Babban cikinsu ne ke wannan maganar....."Kar ka kuskura ka ta'bani wallahi hannunka ya sauka a jikina sai nayi maka illah."!! kamar mahaukaciya take maganar....babban cikinsu ya taso yana haskata da touch "Wow!! yafada yana lasar le'be." Baby wannan jikinki naki ai bana banza bane ke kanki kin san sai an mora da har kike maganar zakiyi wa yarona illah to kafin kiyi masa ni bari nayi fara miki." Yana kai hannunsa jikinta ta gaura masa wani lafiyyan mari!!!! Ya kurma wani ihu! "Ni kika mara!? kanta yayi ta goce a guje tayi kan titi yabi ta hijab dinta ya take da kafafunsa tayi dubarar zare hijab din ta mike a sukwane ta sake ranta a na kare gashin kanta duk ya warware ya zubo mata a fuska da kafada......... tana tsallaka titi taga haske fitilar mota ta doso, tun kafin ta karaso take daga hannunta sama......Yace." Garba rage gudun motar nan babu lafiya waccan kamar yarinya mace Allah yasa ba fyade za'ayi mata ba." Garba yace."Ai kuwa sir ga dukanin alamu hakad'in n.... ai kafin Garba ya rufe baki Goga ya iske inda Wasila take suka hargitse da kokawa......Da sauri yace."Subahannahi Garba kashe mota." Garba ya kashe mota da sauri ya bude motar ya fito wanda yayi dai-dai da lokacin da Wasila ta samu nasarar kwatar kanta daga Hannun Goga, a jigace! ta iske! inda yake tsaye ta afka kansa ba tare da ta sani ba, yayi saurin dafe bayanta da hannunshi guda yana kallon Goga ya dumfaro gurin......Yana isowa ya kai masa 'kwakkwaran naushi! da hannunsa guda ba tare da 'bata lokaci ba Goga ya zube a gurin hancinsa na zubar da jini *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege 9* Yaran Goga na hango ogansu a kwance a 'kas yana matagugu! sai suka ranta a ana kare ko wannesu na neman mafaka a tunaninsu jami'an tsaro ne sukayi basaja, a gurin......Uwani da Rashida suka iso gurin hankalinsu a tashe Uwani fadi take"Shegu tsinannu 'yan iska kawai mu samu kudinmu da 'kyar! su biyo dare su 'kwace ai gaskiya 'barawo baiyi ba." Ahamad ya d'an ja jikinsa kadan ganin ta daina rawar jikin da takeyi ya dan tsira mata ido fuskatara na kallon 'kasa ta kasa dago kanta har yanzu da akwai furgice a tare da ita sosai ta tsorata da goga a duniya babu abunda takeji dashi kamar budurcinta Rashida ta 'karaso inda take tsaye tana mika mata hijab dinta ta kar'ba ta zura Uwani tace"Amma dai babu abunda yayi miki ko." Daga kai kawai tayi tana goge fuskarta 'kamshin turaran da mutumin yake yi shine ya dabbeta tana ji kuma kamar tasan me irinshi Muryarsa ce ta daki dodon kunnata wanda yasa tayi saurin dagowa sai taga ya juya yana tafiya bayanshi kawai ta kalla ta gane shi! *Ahamdu* ne Garba yace."Yallabai yace."Ku shigo motar sai mu aje ku a gida amma yana da kyau ku daina tafiya irin wannan ku kai dare kasancewarku mata akwai 'bata gari a ko ina zasu cutar daku." Wasila ta dago kanta tana kallon Garba ya kalleta da mamaki! sai yanzu ya ganesu sune ashe!? to anya ma kuwa Yallabai din ya gane su.....Uwani ta hau daukar kaya ta nufi motar Garba yace."dan dakata tukkuna." Motar ya nufa ya tarar dashi a kishingide idanunsa a lumshe wata iriyar kasala ce ta dabaibaye shi sakamakon rungumar da yarinyar tayi masa duk ta gwaggoga nasa nonowanta a kirjinsa tsigar jikinsa sai wani irin mikewa takeyi sanyi sanyi ma yake ji burinsa ya isa gida ya kwanta ko samu sauki......"Sir." Garba ya kira sunanshi yana runkufar da kansa ya bude lumsassun idanunsa yana kallonsa yace." Shin ka gane ta kuwa? naji kace su shigo mota yarinyar nan ce fa mara kunya wacce ta zage ka dazu gurin kamfen." Ya tsirawa Garba ido yana kallonshi da mamaki a tare dashi.....Garba yace."ai da kana gurin kasa dago fuska tayi saboda itama tasan bata kyauta sai bayan ka bar gurin ne ta dago fuskarta nan na ganeta.......Jim! na minti biyu kafin yace."Kyaleta kawai shigo dasu muje dare nayi taci albarkacin abokanan tafiyarta." Garba baiyi tsammanin hakaba saboda yasan halin Ogan nashi baya barin bashi babu shakka yarinyar nan na samu dama a gurinshi..........Wasila kam masifa ta hau yiwa su Uwani wai lallai sai sun shiga motar tunda Allah yasa zai tamaike su ita kuma kunya tasa tace dole su dauki kayansu su karasa da kafa ai sun kusa isa gida babu yanda zasuyi da ita suka dauki ledojin suka hau tafiya fakam! fakam!!! Garba ya cimmusu yana fad'in"Yallabai yace."Ku shigo muje ku kawo kayan." Ya hau kar'bar na hannun Rashida ta sakar masa dan dama ita ta riga ta gaji tsoron masifar wasila takeji Uwani ta kalli Wasila dake cigaba da tafiya tace"Haba Wasila ki tsaya mana a taimaka mana kinsan fa kafin muje gida mun galabaita gashi kin san inada ciwon kirji idan ya tayar min kamar zan mutu. Tace"Tunda dai kun nace sai mun shiga muje amma meye saura anan mun kusa zuwa 'yan babura fa." Rashida tace"Eh duk da haka dai aunty Wasila ai ragi ragi ne." Shiru tayi musu suka kawai tabi bayansu a zahirin gaskiya bata son shiga motar dan dai kawai sun nace ne! Yana hango zuwansu gurin ya fito daga bayan motar ya bude gaban motar ya zauna gilashinsa ya gyara, ya tamke fuskarsa yayi dakacen hada jiki da ita ko da yake ai itace ta rungumeshi........Yana da tausayi sosai mussaman kan 'yaya mata shine dalilin ma da ya sanya ya tsaya amma da yasan yarinyar nan ce mara kunya babu abinda zai sanya ya tsaya ya 'bata lokacinsa Hanyar biri daban ta mota daban. Suna shiga motar sanyi Ac da kamshi ya bakunce su, Uwani ce a farko sai Rashida Wasila ta zama karshen shiga motar sai dauke kai takeyi bata so su hada ido dashi gashi sun zauna a site daya tana kallon fuskarshi ta mirror ya hade rai! sai itama ta hade nata ran! tayi kasa da kanta, ita sam wannan taimakon baiyi mata ba saboda babban abun kunya ne guy nan yaje yaga makwancinta duk da haka dai ba zata bari su shiga ciki ba a bakin titi zasu sauka. Jin surutun da su Rashida yayi yawa yana nema ya karasa wata damuwar bayan wacce yake ciki......Sai ya sanya hannunshi ya kunna redio karatun alkur'ani ya soma a tashi daga bakin *Ahamd Sulaiman* Duk da haka dai su Uwani basuyi shiru ba sai surutu suke suna ta zancan 'barayin da suka tare su. Gyaran murya yayi sai suka yi shiru suna kallonsa....Wasila ta dan ja tsaki kadan tace"Dan Allah kuyi shiru idan munje gida kwayi maganar haba." Shiru sukayi basu sake cewa komai ba motar ta cigaba da tafiya. A hankali ya dago idanunsa dake sakaye da gilas yana kare mata kallo ko da wasa baza kace ita yake kallo ba saboda yanda yake wani basarwa.......Yarinyar nada kyau! sosai sai dai bata da kunya ko kad'an! shi kuwa baya shiri da mara kunya marasa ganin girman na gaba dashi. Dai-dai bakin titin 'yan babura Wasila tace"Ajiye mu anan ba sai ka shiga damu zamu karasa da kafafunmu. Uwani tace"Haba 'yar nan ki bari mana a karasa damu mana mutumin nan fa taimakon yake yi kar ki katse masa hanzari." Dan Allah aunty Wasila ki bari a karasa damu." Rashida ta fadi maganar tana karyar da kai.....Sai magiya take mata kamar zatayi kuka." Yace."Garba shiga da motar nan ka kaisu har kofar gidansu kar ka dakata maganar ta." Yace."Angama Yallaba.'! Uwani tace"Mungode sosai Allah yayi albarka alhaji Allah yasa a gama lafiya, Allah ya raya zuria." Ya amsa da "ameen." yana duba wayarshi....Wasila kam! sai shan kunu takeyi sam bata so haka ba dan dai kawai sunfi karfinta ne. Wani tsukakken layin suka shiga motar ta dinga gwajab gwajab!! tana cijewa......Ya dan gyara zamanshi yana duba yanayin ungywar kai da gani kasan unguwace ta marasa galihu gidaje kananu babu tsayin katangar arziki ga kwatoci duk sunbi hanya abun babu kyan gani sam unguwar bata yi masa ba, bai shiga mamaki ba sai da yaji muryata na fad'in"Tsaya anan ga gidanan ai." Yabi gidan da kallo yana mamaki! wai sunan angyara ansa kofa da lokacin buhu ne abun sai ya bashi mamaki dan adam ke rayuwa cikin wannan gidan rubabbe lokacin damuna mutum na cike da fargaba da alhini kar ya rikito masa amma su haka suke kwanciya hankalinsu kwance......Tausayi suka bashi yanzu ya gane abunda ya sanya yarinyar famtsama harkar Jagaliya talauci masifa ne! da'alama kuma su kadai suke rayuwa a gidan.....Tunaninsa ne ya katse lokacin da ya hangota tana bude gidan...Uwani da Rashida sai faman godiya suke masa, Ya bude wani guri a cikin motar kudi ya dauko a daure a kyaure! ya mika ma Uwani ta karba hannunta na rawa gwiwa kasa ta zube tana godiya yace."Tashi dan Allah kamar hakan bai dace ba nayi niyya ne na baku amma akwai 'yar shawarar da zan baku idan babu damuwa." Tace"To Alhaji Yace."Ki hana 'kanwarki harkar Jagaliya sam bai dace da 'ya mace ba ni zan taimake ku sannan idan kun samu mijin aure kuyi aure ni zan dauki nauyin komai naku." Sai Uwani ta fashe da kuka tana fadin "Alhaji labarinmu mai tsayi ne Wasila kuma ba kanwata bace babbar 'yata ce sai Rashida su kadai na haifa marayu ne babansu ya mutu tun kafin suyi wayon haka sannan duk dangi sun guje mu saboda bamu dashi mune muke ciyar da kanmu kaga kuwa har jagajiya ai sana'a ce bazan iya hanata ba tunda gashi ta rufa mana asiri." Yayi shiru yana sauraronta tausayinta yaji ashe itace mahaifiyar yaran shi ya dauka yarsu ce, Ganinta tana kuka ya sanya yace." amma al'amarin akwai hadari a ciki tunda kun daukeshi a matsayin sana'a Allah ya taimaka." Uwani ta amsa da "ameen tana sake godiyar kudin da ya basu....Ahamad ya bawa Garba Umarnin tafiya Garba yaja motar suka bar gurin Wasila kuwa ta jima da shiga gida sai haushin tsayuwar su Uwani takeyi a waje Allah yasa dai ba ro'konsa suka tsayi ba tasan halin masifar kwadayi da roko na mahaifiyar tata. *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko oragne_ *Free Pege10* Suna shiga cikin gidan Wasila ta rufe su da masifa,"Haba Uwani nifa bana son 'karanta bisabillahi yanzu minti na nawa da shigowa cikin gidanan kuna can kuna maula da zubda mutunci dama tunda naji shiru nace to kun tsaya roko wane irin rayuwa ce ban saka kaina ba a akanku amma duk da haka sai kun watsa min kasa a ido idan kuka ce haka zaku dinga yi to wallahi zan barku da halinku ko na samu kudi in boye kaya na." "Haba 'Yar nan, mutumin nan ya cancani a tsaya ayi masa godiya ba don komai ba sai dan taimakon da yayi mana a wannan zamanin ba ko wane mai kudi ne zai tsaya ya taimaki talaka ba yanzu idan da badan yazo gurin ba da me kike tunani zai faru tsakanin da 'barayin nan nasan wallahi sai sunyi mana tas! wannan budurcin naki da kike tattalawa su keta shi da wagari ya waya ai dole a tsaya ayi masa godiya ba abunda kike tunani ne ya tsayar damu a gurinsa shine dai yayi niyya ya bamu kudi kingasu ma." Ta mika mata daurarrun kudin dake hannunta, Wani banzan kallo tayi wa kudin kafin tace"Yanda ya baku kudin to ku ajiye ko lissafawa bance ayi ba ni ina da a'kida idan ina son mutum a siyasance ina sonsa idan bana son mutum bana sonsa dan haka banga abunda kudinsa zasuyi min ba tunda dai ina dasu." Uwani da Rashida suka saki baki suna kallonta da mamaki! wannan kudin masu tarin yawa zasu aje to akan me? ai su ba 'yan siyasa bane kuma ai ba ita ya bawa kudin ba su ya baiwa ballanta tace. Wasila tace"Ko kuna so dai inyi muku bayani dalla dallah akan mutumin nan domin naga kudinsa duk ya furgitaku." Uwani tace"To ai kece naji kina wata magana a wannan zamanin ayi maka kyautar kudi ka mayar gaskiya abin da kamar wahala." "Uwani wannan guy fa shine dan takarar Governor a yanzu dashi suke fafatawa da Governor mai ci a yanzu kuma duk kudin da kikaga na samu ta bangaran harkar siyasar nan to ta dalilinsa ne dan akanshi muke jagaliyarmu saboda haka duk ranar da mai girma governor yasan da cewar ina bangare biyu a wannan harkar to yan kudin da nake samu zai hanani dazu fa cewa yayi zai zauna dani na fada masa dukanin bukatuna sannan kuma ya sauke mukamin wani a dora ni a kai nan gaba kadan ina ganin zan zama 'kusa a harkar dan haka banga amfanin da wad'annan 'yan kudin zasuyi mana gobe insha Allah kafin mu isa government house zan kai masa kudinsa har gida bama bukata." Uwani tace"Kuma fa hakane maganarki Wasila duk ranar da governor ya gane baki da a'kida to kashinmu ya bushe gwara ki tsaya a bigire guda mussaman yanzu sune ludayin su yake kan dawo zamu kwashi roman da mukarad'iya gwara mu tsaya da kafafunmu kafin ya sauka. Wasila tace"Ashe kin gane abunda nake nufi dan haka bani kudin na ajiyesu taimakon da yayi mana kuwa shine yayi niyya 'yan kudinsa baza su sanya ni na sauka daga a'kida ta ba." Uwani ta mika mata kudin ba dan ranta yaso ba sai dan ba yarda zatayi da 'yar tata. ****** Tunda suka doso layin suke ganin cincirindon mutane wasu na shiga wasu na fita ga 'katon gate din da ya zama security ga estate din a bude jama'a sunja dogon layi sai kar'bar tallafi sukeyi layin mata daban na maza daban.....Camas! tace"Kawata me yake faruwa ne naga mutane sunja layi." Wasila ta gyara ni'kab din dake sakeye da fuskarta tace"Zai wuce kamfen yake domin yaudarar al'umma amma dai bari mu tambayi wannan matar." "Baiwar Allah dan Allah me akeyi anan gurin."? Matar ta tsaya tana washe baki tace" Tallafi mai girma Governor mu na gobe yake raba mana mata dubu goma maza dubu ashirin." Wasila tace"Ke kin samu kenan."? Cike da farin ciki matar tace"Na samu mana gasu ma nasa a cikin jakata, zuwa zanyi na siyo gyada buhu biyu mu dinga soyawa da yara na kafin muga abunda Allah Zaiyi." Wasila tayi murmushi tana jan tsaki tace"Kin san wani abu."? matar ta girgiza kai...."Zan baki baki dubu ashirin yanzu kije ki watsa masa kudinsa kice baki so kudinsa basu isa su siyi 'kuri'arki ba mulki kuma sai dai yaga anayi." Matar tabi Wasila da kallon mamaki.! Wasila tace"Ko dai kudin da na fada sunyi miki kadan ne to na kara miki talatin akai sun zama hamsin nasan dai zasu isheki kija jarin ko wace sana'a ce." Matar tace"Bana son roman baka yarinya in fara gani a'kas! tukkuna." Wasila ta zaro jakarta dake rataye a kafada ta lissafa kudi dubu hamsin cif tace kin gansu a hannuna kina aiwatar da aikin dana saki zan baki su. Laraba na ganin kudi dumus a hannun Wasila sai ta gigice! tace"To yanzu ya za'ayi na shiga gurinan akwai 'yan sanda sosai a gurin kuma suna ganin shige da ficen jama'a kana suna gane wanda ya fita da wanda ya shiga kuma kina ganin idan na aikata hakan ba za'ayi min komai ba." Wasila tace"Karki damu malama muje tare zamu sanyaki a tsakiya ba zasu gane ki ba." Laraba tace."To ku muje." Kai tsaye suka durfafi kofar shiga gurin jami'an tsaron dake tsaye a gurin sukace su tsaya wani abu suka kara a jikinsu minti biyu sukace su wuce ciki.......Wasila da Camas! suka kama layi kamar gaske! Laraba kuma ta mike hanya dan isa inda yake tsaye..........Tana zuwa ta watsa masa kudinsa a jikinsa da karfi tace." *Bama so bama yi! wa 'yan nan 'yan kud'in naka basu isa su siyi kuri'armu bamu ba!.* Ai sai gurin ya kaure da hayaniya Garba da Hadi sukayo kan laraba Ahamad dake tsaye cikin dumbun mamaki ya hanasu dukanta, su kansu Police din dake tsaye a gurin Sunyi mamakin matar amma ya hana a ta'bata komeye dalili oho." Ya Kalli Garba a nutse yace."Zo ka tsaya ka cigaba da raba musu." Garba ya tsaya inda yake shi kuma ya kalli Laraba dake tsaye jikinta yayi sanyi kalau yace."Baiwar Allah bance dole ki za'be ni a matsayin d'antakarar ki ba wannan kudin da nake raba muku duk karshen wata inayi ne saboda Allah ba da wata manufa fa ra'ayinki ne ki za'be ni ko ki za'bi abokin gamayya ta ni nasan ba zai iya siyan 'yanci ki ba nafi so duk wanda zai za'beni ya za'beni saboda Allah da kishin kansa da kuma 'kasarsa...." Laraba ta fashe da kuka tana fad'in"Kagafarce ni yallabai! wallahi bayin kaina bane roman baka akayi min wata yarinya ce yanzu tayi min alkawarin zata bani dubu hamsin idan na aikata maka haka yanzu kuma wad'annan maganganun da kayi sunyi bala'in kashe min jiki don girman Allah ka gafarce ni." Ahamd ya sauke ajiyar zuciya shi sam baiji zafin matar ta saboda yasan irinsu siyansu ake da 'yan kud'i kad'an! saboda an san shi talaka bukatarshi kudi ko ta halilin kakane zai iya siyar da 'yanci akan sabulu ko omo ko sukari. Yace."Yanzu zaki iya nuna min inda yarinyar take."? tace"Kwarai kuwa Yallabai ai gatacan ma ta kama layi." Ahamd ya goya hannunsa a baya suka mike dogon layin dake jere da mata har suka inda su Wasila suke....."Gata nan Yallabai."! Laraba ta nuna Wasila dake tsaye fuskarta da ni'kabi.....Zatin ta kawai ya kalla ya gane ta ya d'an tsirawa idanunta kallo dake ni'kab itama ta sama ido suna kallon juna.....Ya d'an juya a nutse ya kira police yana karaso yace."Zura mata ankwa ka kai min ita cikin gida." Camas! tace"Innallihi wa'ina ilahi raji'un! Jama'a me mukayi baiwar Allah me tayi miki zakice itace haka kawai dan sharri! Yalla'bai wallahi ba ita bace hasali ma mu yanzu muka shigo gurin kuma ai ba ita kadai ce mai niqab ba a gurin." Ahamdu ko sauraranta baiyi ba ya bar gurin. Camas! ta dinga ihu! tana zagin Laraba Wasila ta dinga turjewa tana fad'in''Me nayi muku wannan sharri tayi min bani bace wallahi Police din yace."Wallahi idan bakiyi shiru ba zan fuxge wannan niqab din dake fuskarki in yaso kowa ya ganki munafuka kawai." Jin abinda Police din yace ne sai ta daina turjewa saboda bata so ya cire mata niqab jama'a su ganta akwai tozarci sai kawai ta hau fuffukar 'karya da fad'in"Ai gaskiya daya ce kuma wanda ya zalinci wani Allah yana gani haka kawai saboda rashin adalci za'a sanya min ankwa sai kace 'barauniya ko kuma wacce tayi kisan kai!! kuma a haka ake cewa za' a iya mulki wannan ba adalci bane wallahi duk wanda ya shiga hurima na barshi da Allah."!!! Dan sanda kuwa ya tasa 'keyar ta tana tafiya tana surutai da farfad'ar bakake maganganu masu harshen damo wanda wanda ake dominsa ya sani masu hankali ma a gurin sun gane da wanda takeyi....Angizata yayi cikin gate din yayi ya mayar da 'kofa ya rufe......Ta waiwaya bayanta babu kowa har masu gadi duk suna waje gefen bainci masu gadi ta zauna gabanta na fad'uwa sai yanzu jikinta yayi sanyi da al'amarin, dole ta cire tsoro da shakku a kan abunda zai faru ita dashi tayi al'kawarin ba zai ta'ba samun nasara a kanta ba.......Can ta hango shi ya fito daga wata iriyar kofa ta gilas ya durfafo inda take zaune gabanta ya dinga duka yana daka! mussaman ganin yanda fuskarsa take had'e tamkar hadarin da ya daf da zubar da ruwa. *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ _*Babu mahalu'kin da ya isa yayiwa mutum abunda Allah bai masa ba, bama nema gurin kowa! gurin Allah muke nema Allah ka yi mana ba dan mu ba*👏🏻_ ~~~~~~~~~~~~~~ *Page d'in naku ne* _HAUWA S ZARIA_ *(Mmn Uswan)*🌺 _MAMAN MAMY_ *(Shalele)*🌺 *Free Pege11* Ganin ya kusa isowa inda takene ya sanya tayi maza ta yi 'kasa da kanta gani tayi ya kara wani kwarjini da kamala adduar neman rinjaye ta soma sai dai duk wacce ta dauka sai ta subce ta kamo waccen ma ta subce duk sakamakon tsayuwarshi a kanta ga masifar kamshinsa ya rikirkita mata lissafi. "Cire wannan ba'kin abun na fuskarki." Yafad'a cikin wata iriyar murya.....Ta dago kanta tana kallonshi, "Kamar yaya na cir.....Kafin ta 'karasa ya fuzge niqab! din ya jefar, tayi saurin kauda kanta gefe. Hannu ya mika yayi kamar zai juyo da fuskarta sai ya fasa yace." Juyo ki kalleni ina son muyi magana dake." Sai da ta dai-dai ta nutsuwarta tukkuna ta juyo tana kallonshi........Sun kai kimanin minti uku suna kallon juna kafin ta dauke kanta tana wani ya mutse fuska. Gyaran mirya yayi a nutse yace."Ina so ki fad'amin nawa aka biya ki kika tsunduma kanki a wannan harka ta jagaliya ki fada mun ko nawa suka baki ni nayi miki al'kawari zan nin ka miki abunda suka baki ko sukayi miki alkawarin mutukar zaki dawo kiyi harkar ta siyasa mai kyau, da tsari! Ta mike tana karkad'e hijab d'inta ta kalleshi ido da ido tace"Ni! bana jagaliya siyasa nake tsaftacciya kuma kai baka da kudin da zaka iya biya na kan wannan harkar." Murmushi ya saki yace."Kina bani tausayi yarinya baki san waye Ahamdu ba ko."? Tace"Saninka ba zai amfana min da komai ba tunda nasan anayi siyasa ne da ra'ayi ni bana ra'ayinka kuma baka isa kasa ni na sauka daga a'kida ta ba.'' "God."! yafada yana tafa hannunsa ya kalleta da kwantaccen murmushi a fuskarshi yace." Gaskiya kin burgeni yarinya kuma ana siyance ana son mutum mai a'kida ni kaina idan da zan samu abokin tafiya irinki da naji dadin harkar ammafa ni yanda na dauka kin tsunduma kanki wannan harka ne domin cimma wata manufa taki. "Kwarai kuwa akwai manufofi da nake dasu akan wannan harkar wanda ni kadai na barwa kaina su ina so kuma Allah ya cika min burika na." "Masha Allah shin meye sane kuka daura tuntuninku akaina kuka tsawwala min sai kace ni kadai ne dan takarar Governor dake takara da governor ku me yasa duk inda nake kuna bibiyata da al'amurana saboda tsabar bin diddigi irin naki har gida kike biyo ni kina kokarin ci min mutunci shin wai me kuka dauki wannan harkar ne."!? Wasila tayi shiru yace." Siyasa ba hauka bace! wad'anda suka san abunda sukeyi sunayi ne kan tsari amma ke naga kina so ki wuce gona da iri saboda talauci yayi miki katutu shiyasa kike ganin zaki iya zagin mutum kamar ni wanda yake da shekarun da suka nunka naki sau uku, okey nasan babu abunda ke damunki sai jahilci da rashin mafad'i to wannan shine lest winning na 'karshe kada! na sake ganin wad'annan kafafun naki a gidana duk ranar da kika sake kuskuran shigo min gida to a ranar ki kwana da shirin wad'anann kafafun naki ba naki bane dan sai na sanya an ragargaje su! in yaso sai naga kafafun yawon *Banga* ban hanaki ki zageni ba ko ki jefe ni kije kiyi tayi idan kin cimma burinki nasan zaki bari gidana dai ban lamunce in sake ganin kafafunki a ciki ba." Maganganunsa sunyi mata zafi sosai! ta kalleshi tana girgiza kai *"Jagaliya da Banga* yanzu na fara." Tana fadin wannan magana sai tw zuge jakarta ta zaro kudinshi na jiya ta jefa masa "Wannan kudin da ka bawa Mamana da kanwata basu ishemu kallo ba saboda aban bamu wanda yaf.......... Taji saukar Wani bahagon mari a kumatunta! A razane! ta dafe fuska idanunta yayi jawur! Ya dam'ki! wuyanta ya sha'ke cikin hijab.....Ta dinga kyarma! tana kyafta ido!! Ganin idanunta sun soma shagid'ewa ne ya sanya ya saketa sai ta fad'i a gurin ragwajab! tana kakari! tare da rike ma'kogwaronta! kanta 'kas!! ya tsugana dai-d'ai kafafunta, A kausashe yace." Har yanzu baki san waye Ahamadu ba ko! ni zaki jefa da kudi! ke! wai shin ma dame kike takama ne.''!!! Wasila tayi shiru bakinta ya mutu har yanzu ma'kogwaronta suya yake mata wai! sauran kadan ta bakunci lahira......"Wallahi wallahi duk ranar da kika sake gangancin aikata min abu makamancin wannan sai kin raina kanki in yaso su wad'anda suke daure miki gindi su same ni da kansu ni bana tsoron kowa kije ki fada musu basu isa nayi dake ba su zasu zo da kansu mu fafata! mahaukata kawai wadanda suka dauki mulki wata tsiya kije ki fad'a musu ni *Ahamadu* ina jiransu suzo da kansu sa'ko na baki duk ranar da suka sake turo ki to zan huce fushina a kanki Tausayi da jin kai ya sanya nake kyaleki kina min abunda kike so kuma ina baki damarki a siyance okey tunda ke d'in dabbace! mara kishin kanta zan fara cin ubanki idan kin soma ji a jikinki sai kije ki gyara *BANGAR SIYASAR KI* Tashi! maza ki kwashe min wannan kudin da kika watsar a kas! dubban mutane nacan suna nema ke kin samu kina zubarwa saboda kina da masu baki....Ki shirya min kudina tsaf! a cikin kyaure kamar yanda suke tunda bakwa so akwai dubunku masu so." Wasila ta yunkura ta tashi tsaye idanunta yayi jawur!!! Gefan hijab dinta tasa ta goge gomin goshinta ta ratse shi zata wuce!!! Tare ta yayi da kirjinsa ta dannata a jikin bango (garo) Sai ya zamana ma nuffashi da kyar take futarwa Gaggausan mutum irin wannan ya sanya mata nauyinsa ai sai Allah...."Ni zaki nunawa zafin kai ko."!? Yafada yana sake matse ta a jikin bango.....Kanta tasa ta daki kirjinsa dashi Yace."Idan kukan jini zakiyi anan gurin sai dai kiyi sai naga karshen tashen balagarki kiyi abinda nace kawai shine mafitarki." Cikin 'kunar rai! tace"Ka matsa daga jikina ka matseni a bango domin ka cimma wata manufa taka akaina to Allah ya isa kudi kuma zan tsince dan karan kaina ba dan wani ba." Ya matsa daga jikinta yana ya mutse fuska.......Bani da wata manufa da zan cimma akanki saboda na had'u mata iri iri wad'anda suks fiki komai kazama dake mai zanji a jikinki da kike wannan maganar." Shiru tayi masa ba tace komai ba ta hade masa kudinsa ya sanya hannu ya karba da hannu ya nuna mata 'kofa "Fice min a gida wannan shine karo na biyu idan kika kuskura kika sake shigo min gida to kin san abunda zai biyo baya." Hijab! d'inta ta buge! tayi masa wani irin kallo mai nuna alamun akwai sauran kalubale tayi kwafa ta juya tana tafiya da sauri sauri!!! Hannuwa ya zuba cikin aljihu yana kallo ta tsaya ta daura niqab dinta kana ta murda kofa zata futa......Dake a kulle take daga waje, Hadi yazo da sauri ya bude mata ta fice da sauri tamkar zata tureshi.....Can ta hango Camas tsaye jikin wata bishiya ta nufe ta da saurin gaske sam! bata damu da kallon da mutanan dake gurin suke mata ba, saboda babbar dama ce ta samu domin cimma manufofinta a kansa.....Suna fita suka samu babur kai tsaye government house suka nufa. *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege12* Sai da sukayi nisa sosai Wasila ta cire niqab din fuskarta tana goge fuska Camas tace"Ammafa matar nan taso ta saka ki a bala'i wallahi dan naga guy ranshi ya 'baci sosai ni na dauka ma zan ga kin fito da fasashen baki! wallahi." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Bai fasa min baki ba amma ya mareni ya sha'ke min ma'kogwaro har na soma jiyo 'kamshin mutuwa! ammafa bai daki banza sai na kulla masa sharri nifa naji dadi da hakan ta faru wani plan zan shirya a kanshi ke dai kawai mu bar maganar sai munje gida tukkuna." Camas tace"Shiyasa naga kin fito a furgice! gaskiya Wasila akwai ki da jarumta wallahi da nice da tuni na karaya da wannan harkar akwai hadari a cikinta......"Camas idan kinga na daina banga to na cimma manufofina ne kawai ke dai ki cigaba da take mun baya insha Allahu wannan plan din da zan shirya shine zai janyo min arziki na har abadah." Camas tace"Allah yasa kawata kice dai mun kusa daina yawo a babur din haya zamu mallaki motar kanmu." Murmushi tayi har fararan hakoranta suka bayyana tace"Ke dai lokaci Camas! Allah dai ya taimake mu." Camas! ta amsa da "ameen" kana suka cigaba da wata hirar. Koda suka isa government house din Governor da sauran mukarrabansa suna dakin meeting sai da sukayi xaman awa biyu tukkuna suka fito lokacin har magariba tayi duhu ya shigo a gurguje suka gaisa kana Wasila ta fada musu abunda ya faru a gidan Ahamadu tace....Wannan damar tamu itace zata rusa duk wani shirinsa a gaban bainar jama'a al'amarin ya faru saboda haka da kaina zan shiga gidan redio in watsa maganar nasan wad'anda abun ya faru a gabansu zasu gazgata kaga da kanan shikkenan magana ta kare." Governor Lawan Rabo yace."Mutukar wannan magana taki ta rusa shirin Ahamdu to ni Lawan Rabo nayi miki al'kawarin baki kud'in da zasu gigitaki! zan baki mamaki 'Yar gaske in har wannan plan din da kika shirya kan Ahamdu ya sanya ya janye kudirinsa na zama dan takarar governor a jam'iyyar *CPC."* "Kar ka damu mai girma governor insha Allahu magana ta 'kare kujerar mulki kam kaine zaka cigaba da zama a kanta." Tafada cikin karfafawa kanta gwiwa kuma tana sanya ran insha Allah bukatarta zata biya. Basu dawo gida ba sai kusan karfe goma na dare dan daukarsu sukayi a mota suka nufi wani kayataccen hotel sukayi ciye ciye kana sukayo guzirin wasu, har bakin layi Alhaji Tasiu ya kawo su yana so ya fadawa Wasila munufarshi a kanta ya kasa wani irin kwarjini take masa shiyasa har ya yanzu ya kasa tunkararta yana kallon yanda abokansa ke shakawata da mata sam baya sha'awa amma yanzu ganin Wasila ya sanya yaji yana sha'awarta kuma ya daura aniya a kanta insha Allahu sai ya dandani zumarta yaji ya take....Dama tuntuni Alhaji ma'aruf ke kwadaita masa harkar yana basarwa sai yanzu kuma yaji yana sha'awar yi da Wasila *'Yar gaske!* **** Bayan mako biyu da faruwan al'amarin Ahamd ya sake fita kamfen dashi da mutanansa alhamdullahi anyi an kare lafiya dan har gidajen redio sai da suka sanyo muryarsa yanda take jawabi da irin ayukan da zaiyi idan Allah ya bashi gwamnati a hannunsa.....Ahamdu yaga masoya ta ko wane bangare dan gurin cika yayi ma'kil! da jama'a 'yan nahiyar birget da kwana hudu, babban abunda zai baka mamaki! shine yanda mata da maza manya da yara suke fitowa suna turmutsutsu da fad'in "Se jam'iyar *CPC* sauyi muke so da *Ahamdu dan Musa* insha Allahu kano takace." Wasila na zaune kan tabarma anci kwalliya da wani uban les kunnanta da wuyanta gold ne sai sheki yake yi kawai taji muryarsa na jawabi yanda zai kula da gari da ayyukan da zaiyi mutukar Allah ya bashi iko, ta karo murya tana sauraran jawabin nasa da ba'aji sosai sakamakon hayaniyar da tayi yawa, mamaki take ya akayi har ya fita yayi wannan kamfen din basu sani ba.....Cizan lebe tayi ta dauki tafkekiyar wayarta mai tsadar gaske, Alhaji Tasiu ta kira ya daga wayar da sauri tace"Yallabai ka kunna redio kaji abunda ke faruwa mutuminka ya fita kamfen sai alkawarin karya yakeyi jama'ar gari na yi masa ihu.'' Alhaji Tasiu ya kunna redion wayarshi yana saurara......Kiranta ya sakeyi a waya bayan ya gama saurara yace."Yanzu meye matakin dauka." Kwafa tayi tace"Bari bayan sallahr isha'i kazo ka dauke mu muje gidan redion *Salama* zan musu magana idan Allah ya kaimu gobe su sanar da cewar za'a hira dani *Wasila 'Yar gaske* a filin mu Siyasa." Yace." Hakan yayi dai-dai 'Yar gaske insha Allahu zan shigo da wuri sai muje ammafa nima ina da wata bukata da nake nema a tare da ke." Yafada yana wani kashe murya.....Tuntuni ta riga ta gama gane inda ya dosa kawai tana basar dashi ta fahimci yanda yake kulafucinta bai san me cin wannan budurcin nata ba sai ya shirya ji takeyi dashi domin tasan shine darajarta ta gama yawace yawacen ta dawo tilas tasan zatayi aure kuma shine mutuncinta shiyasa take tattala abinta domin ta mika shi ga namijin da yayi nasarar auranta......Amsa masa tayi kawai da shikkenan sai kazo d'in." Alhaji Tasiu ya kashe waya yana me cike da nishadi zai biya bukatarshi gurin Wasila.....A waya ta kira Camas! tace bayan sallahar isha'i ta fito zasuje inguwa. Aikuwa Camas! na idar da sallah tayi kwalliya tayiwa mahaifiyata sallama ta nufi gidan su Wasila mahaifinta na zaune kan tabarma yana shan iska yana kallon fitarta baice komai ba wanda inda dane da tuni ya korata gida amma dake yanzu ta toshe masa baki da kudi shiru kakeji wai malam yaci shirwa. Cikin wata dan'kareriyar mota Alhaji Tasi'u yazo daukarsu Wasila matasan unguwa suka dinga zind'en Wasila da Camas! cewar ba harkar siyasa kadai suka tsaya ba harda karuwanci ganin irin manya motocin dake zuwa daukarsu, ganin irin shigar da Wasila tayi ta fito dashi ya sanya suka sake gazgata zatonsu a kanta tana sanye da wani material roba roba anyi mata wani irin dinki riga da siket ne sun matseta ga wuyan rigar daga baya a fafake! daga gaba kuma anfutar da gidan nono ya matseta sosai Wasila akwai hips da brest duk sun fito sun das duk lafiyayyan namijn da ya kalleta a lokacin sai ya d'arsa wani abun a ranshi gashi ta kawo wani siririn mayafi ta rataya a kafadarta hannunta sakale da jakarta mahadin takalminta kana kallonta zaka gane ta soma wankuwa idanunta sun bude tar! tar! sai taunar cingum takeyi.....Alhaji Tasiu yaji jijiyarsa ta mike ganin tsarin jikin Wasila ashe cika da 'kasaitar yarinyar ya kai haka babu shakka dole xaiyi mata kwance kwance ya dandana zumarta. Gaban mota ta shiga ta zauna camas ta zauna a baya Kana Alhaji Tasi'u As na gomna ya tuka motar suka fuce daga layin yara na jifan motar da fad'in"Ba mayi! Kano ta d'an Musa ce wallahi.....Alhaji Tasiu yace."Na lura jama'ar unguwar nan taku basayin wannan gwamnatin tamu shin bakya musu hasafi ne kin san fa dole ki sake musu kudi sosai saboda ranar za'be! su fito su mara miki baya. Wasila ta sauke ajiyar zuciya tace"Na rasa abunda mutumin nan yake bawa mutanan jahar nan wallahi in kaga yanda jama'a ke sonsa sai ka rike baki ni kaina wani sa'in idan na fito jifana sukeyi sai nayi da gaske tukkuna." Alhaji Tasiu yace."Ai yana da masoya gaskiya dalili kenan da muke so mu dakusar da duk wani shirinsa muna so mu kashe masa gwiwa kan harkar yaji kwata kwata ta fita daga ranshi." Wasila tace."Kar ka damu insha Allahu bukatarmu zata biya a kanshi. Alhaji Tasiu ya biya tashar redio *Salama* kudi masu kauri yace."Tun yanzu su soma watsa wa cewar zasuyi hira da *Wasila 'Yar gaske* Yar partyn Lawan Rabo governor mai ci a yanzu." aikuwa kafin ma su bar cikin gidan redion sun soma sanarwa kan zasu hira da Wasila 'Yar gaske a filinsu na Siyasarmu da misalin karfe takwas na dare." Tun a cikin mota Alhaji Tasiu ke yi mata wani irin kallo yana lumshe ido tana hankalce dashi kawai tana basarwa ne babu zato taji saukar hannunsa kan cinyarta....kici kici tayi da fuska tace"Meye haka kuma kar ka kara kuskuran ta'ba jikina duk mutumcin da muke da kai naga zaka keta min martaba ta mutuntaka to zamu raba hanya." As ya soma yake yana sosa kai yace."Har yanzu baki gane inda na dosa ba kenan *Yar gaske* ki taimaka min rana daya ki mallaka min kanki." Ta watsa masa wani irin kallo, kankance ido tayi tace"As ina ganin girmanka da mutuncinka muyi harkar data hadamu da kai wato siyasa ni ba yar iska bace bana kuma shiri da mazinaci saboda haka kada ka kara yi min magana irin wannan duk ranar da ka sake to kam zan fadawa mai girma governor yayi min tsakani dakai ka kyaleni nayi sana'a ta kaje ka nemi 'yar iska kuyi iskancinku amma ni ba wannan na fito ba." As yaji ciwon magangunta Wasila butuluce meye bai yi mata ba a rayuwa da girmansa da komai take fada masa irin wannan maganar.....Shiru yayi bai sake tankawa ba Ita taci kunu tana tauna cingum dinta jefi jefi tana amsa waya Camas na baya da tata wayar a hannu tana chating duk tana jin abunda sukeyi tana ganin idan da itace Wasila da gudu zata amince wallahi ai duk sana'a ce a wannan zamanin samun irinsu As zaiyi wuya kuma ta fahimci mutumin bashi da mugunta iya kudi yana sakar musu ya kaisu su dungo siyayya harda ta banza ya biya kudin kuma ya basu wasu ita kam idan ya nemeta zata amince masa da gudu. **** Washe gari gidan redion *Salama* suna bude tasharsu da abunda suka fara kenan "Jama'ar gari da misalin karfe takwas da rabi na dare zamuyi hira da Hajiya Wasila 'Yar gaske a filinmu na Siyasa kowa ya kasance da redionsa a kusa dashi a dai-dai wannan lokaci domin yaji abunda yake tafe da wannan shahararriyar 'yar siyasar." Gari ya dauka kowa na jiran lokaci......Labari ya iske Ahamdu ta bakin abokinshi Khalifa wanda yake mara masa baya ga dukanin harkokinsa tare sukeyi kuma shine a matsayin mataimakin shi idan Allah ya basu mulki a hannunsu.........Sam bai wani damu ba da jin wai zai ai hira da yarinyar a tashar redio ta *Salama* yasan dai zancan gizo baya wuce na 'koki shirme ne zasuyi tayi har su gaji su daina, Khalifa kuwa yasha jinin jikinsa jiran lokaci kawai yake yi. *** Karfe takwas da rabi an soma gudanar da shirin *Siyasarmu* Jama'ar gari na makale da redionsu da wayoyinsu. Mai gabatarwa ya fara magana kamar haka.... "Jama'a yau filin namu na da babbar bakuwa Hajiya Wasila 'Yar gaske wanda tun kafin zuwan wannan lokacin muke ta sanar daku cewar zata shigo cikin shirin Siyasarmu domin ta warware mana zare da a bawa kan wata kullalan kulli dake faruwa a wannan jahar wanda jama'ar gari basu sanshi ba yau dai tace bari ta shigo wannan fili ta fasa 'kwan! kowa yaji ya san abunda ke faruwa 'yan takarkarin da suke gwabzawa guda biyu, masha Allah *'Yar gaske!* filin Siyasarmu ya shirya tsaf hakanan masu sauraro suma sun shirya suna sauraranki." *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *YABON GWANI YA ZAMA DOLE* 🕺🕺🕺🕺🕺🕺🕺 *PEGE DIN YAU KACOKAN! NAKI NE UWAR ARZIKI MACE MAI FARAR ANIYA DA FARAR ZUCIYA KINYI MIN KINA KAN YI MOMYNA FATIMA MUSA NIJAR ALHERIN ALLAH YAZO INDA KIKE DAKE DA ZURIARKI BANTA'BA MU'AMULA DA MUTUM IRINKI BA BANI DA BAKIN GODIYA A GURINKI MOMY ADDUA CE A TSAKANINA DAKE UBANGIJI ALLAH YA DUBA 'KARSHEN KI YASA KI GAMA LAFIYA ALLAH ABUNDA KIKEYI MIN ALLAH YAYI MIKI MOMY BAZAN TA'BA MANTAWA DAKE BA DOMIN KINYI MIN ABUNDA BAZAN MANTA DASHI BA NAGODE NAGODE NAGODE ALLAH YA AMFANI ZURIA👏🏻* ~~~~~~~~~~~~~ *Free Pege13* Cikin zazza'kar muryata tayi sallama har da addua kamar wacce za tayi abun arziki...."Bisimillahi rahamanir rahim rabi sharali sadari wayasirli amri wa'alal u'kudatun millisani yaf'kahu 'kauli ameen ya Allah, to jama'a assalamu alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu kamar yanda mai gabatarwa ya fada musu suna hakane nice Wasila 'Yar gaske 'yar partyn mai girma Governor Lawan Rabo governor da ba za'a ta'bayin irinshi ba insha Allah to a yau dai na shigo wannan filin ne domin nayi tankade da rairaye kana kuma na fed'e muku biri har hutsiyarsa, to jama'a hausawa nacewa yabon gwani ya zama dole dan haka kafin in fara cewa komai zan yabi maigirma Governor na saboda ya cancanta a yabe shi duba da irin dumbin ayyukan da yake a wannan jahar tamu......*A dad'e anayi sai gaskiya Engineer Turmi kake sha sassaka! Gugan 'karfe sha kwarafniya! kayi mun gani jama'ar gari sun gani sun shaida! mun shaida! A daka a bari dole uwar na'ki! ayi ayi a hakura kai d'in dai kaine duk inda akaje aka dawo sai kai!!! Engineer ma'kiyan ka! sai da su mutu domin ka riga kayi musu nisa sai dai kallo daga nesa! mu dai kaine gwaninmu kai muka za'ba jama'ar gari kai suka za'ba kawai dai 'yan adawa nayi musu romon baka da kuma al'kawaririkan 'karya! tare basu tsohiyar hanci domin a siyi kuri'arsu mu mun yarda da kanmu ba sai munyi kamfen ba insha Allahu babu canji da yardar Allah sai mun maimaita 4+4 Ba sauyi insha Allahu." Ta kare maganar tana sauke nuffashi, Mai gabatarwa yace."Hajiya Wasila wannan yabon da kikeyi fa ni sai nake gani kamar kune kukeyi irinshi dan tuntuni jama'ar wannan jahar tamu suka dawo da rakiyar wannan gwamnati a cewarsu har yanxu basu gani a 'kas ba ance za'ayi mugudanar ruwa kana za'a saki wutar lantarki za'a biyawa yara kudin makaranta za'a gina sabbin makaranta da asibitoci da dai duk ayyukan da mai girma governor ya fada zaiyi kafin hawansa kujerar mulki shuru kakeji malam yaci shirwa wasu ayyukan idan an fara gadan gadan sai ajiye a shiga wata sabagar gashi yanzu har kunci shekaru uku akan wannan kujera babu wani sauyi da suka gani shiyasa suke ganin gwara su nemawa kansu mafita tun kafin dare yayi musu." Wata siririyar dariya ta saki tace"Haba d'an jarida kasa kunne kaji da kyau!! Wallahi wannan gwamnatin ayyukanta daban suke dana sauran gomnonin da suka gabata haba Alaji ka duba babbar gadar da mukayi wacce ta fara tun daga farkon titi gwaron dutse bata tsaya ba sai da takai unguwar na'ibawa, wannan katuwar kwatar ta jakara mun rufe ta ruf! idan ana ruwa mutane hankalinsu akwance duk wannan fargabar da suke a da sun daina sai ka fada min wace gwamnati ce tayi wannan aiki."? ''To ai ba anan take ba 'Yar gaske sufa jama'ar gari suna magane akan al'kawarrikan da kuka dauka baku cika ko daya ba ba wai gada da aikin katuwar kwata ne ya damesu ba burinsu kawai suga ruwa da wuta kana kuma 'yayansu su samu ingantaccan ilimi har yanzu fa akwai makarantun da suke zama kan buhu babu banci da sauran abubuwan amfani kuma kafin hawanku wannan kujera kunyi alkawarin kan zaku inganta ilimin yara kana kuma kuyi karin albashi ga ma'aikata." "Humm! ai kaji gareje irin na mutane jama'a basa tsayawa suyi aiki da lura wannan gwamnati fa kafin hawanmu akwai abubuwan da muka tarar akai akwai tarin bashishshika da gwamna na baya ya bari bai biya ba tilas! mu muka biya wanda har yanzu ba'a karasa ba haba jama'ar gari ku kwantar da hankalinku kamar tsumma a randa insha Allahu dukanin abunda mai girma gwamna ya ambata zaiyi to zaiyi ku dai kawai ku mara masa baya a za'be na gaba ya maimaita insha Allahu zakuyi mamakin aikin da zaiyi muku kano zata koma tamkar kasar waje saboda yanda za'a gyarata da titina da makarantu da asibitoci da sauransu." " 'Yar gaske na tabbata jama'ar gari na sauraranki da duk bayanai da kikeyi to amma inda gizo ke sakar anan shine! sufa a halin yanzu duk wata magana da zaku fito ku fad'a a yanzu ba zasu dauketa da muhimanci ba saboda zuciyarsu ta riga ta gama makancewa da kaunar wannan d'an tahalikin mutumin wato *Ahamadu Musu* wanda suke masa inkiya da *(Ba'iya ka!)* shine nima nake ganin gwara kawai ku hakura ku bar masa tunda a zahiri kamar yafi ku mutane a wannan tafiyar." Dariya ta saki harda tafa hannu "Oh! mutane kenan!? Ni wallahi ma abun mamaki yake bani idan naji suna kiran wannan mutumi da sunan dan takarar gwamna banta'ba jin inda *Gwauro* yayi mulki ba babban mutumin dan kimanin shekaru ar'abain da biyar yana zaune banu aure ai dole a bunkice shi.....To jama'a yau dai bari na fad'a muku abunda baku sani ba akan wannnan mutumi da kuka nace ya zama shugabanku.....Ahamdu dai tunda yake bai ta'ba aure ba duk wani mai shakku yaje yayi bunkice akai, yana zaune a gidanshi yaci karansa babu babbaka ya kawo duk macen da yake so yayi mu'amula da ita tamakar matarshi....Jama'a ni Wasilatu 'Yar gaske zancen dai da nake muku nima ya auna ni a gidanshi Allah ne ya tseratar dani nasan mutanan da suka je gidanshi kar'bar tallafin da yakeyi duk karshen wata sun gani lokacin da ya sanya aka daura min ankwa babu ji babu gani ya sanya aka shiga dani ciki gidanshi a kulle da kwado..... dan jaridar ya katseta da fadin" To Yar gaske ya akayi kikeje gidanshi bayan kowa yasan ke ba 'yar bangaranshi bace shin ko zaki fadawa masu sauraranki dalili."? Shiri fa ya dauki zafi!! Zama ta gyara tace"Eh tabbas jama'a zasu zargi haka to abunda ya kaine gidanshi shine sati biyu da suka wuce yazo har kofar gidanmu da niyyar yaudarar kanwata sai ni kuma Allah ya nuna min shi ya dauki makudan kudi ya bata nice nan na hanata ta'ba kudin washe gari na nufi gidanshi domin na bashi kayanshi sai na tarar yana rabawa jama'ar gari kudi......Kafin nayi aune! kawai na ganshi tare da wata mata a kaina tana nuna masa ni wai nice! 'kawata Camas! da muke tafiya tare ta shiga rudani a gaban mutane ba tare da yayi wani bunkice ba ya kira police yasa aka buga min ankwa aka tasa 'keya ta cikin gidanshi a kulle to wannan damar ya samu yaso ya biya bukatarshi a kaina sai Allah ya kare ni." Dan Jaridar maganar tasha masa kai sosai.....Ashe bashi kadai ba harda jama'ar gari dake sauran shirin kafin kice kwabo zantuka sun soma tashi a garin wanda tun kafin a rufe shirin gari ya hargitse da hayaniya kowa na fadin albarkacin bakinsa kan Ahamdu ashe dama bashi da aure Gaskiya magana ta fito kan zargin da mutane ke masa gurin bada kudin da yake a cikin gidansa yana lalata da 'yayan mutane, sai wad'anda akayi abun a gabansu suka fara gazgatawa har suna bada larabi zance fa yayi tsanani a gari anata kace!kace! masu tsinewa Ahamadu sunfi yawa kan wadanda suka karyata maganar. Wani irin gumi yake tsiyayarwa a jikinsa ita kanta rigar dake jikinsa sai da ta jike saboda tsananin tashin hankali ashe dama alkairi yana zama sharri! bai ta'ba nadamar zamanshi a haka ba sai yanzu shin wai yama akayi yarinyar nan tasan bashi da aure.....Shine taje ta kwancewa zani a kasuwa tilas masu karamin tunani su gazgata maganarta, Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! bai ta'ba tunanin al'amarin siyasa ya kai hakaba amma kuma wannan siyasar da sukeyi kamar ta sa'bawa dokar 'kasa 'kazafi! babu shi a siyance. *Humm! Ahamdu kenan har yanzu baka san meye Siyasa ba.!* Garba da Hadi suka fusata sosai Suka mike cikin zafin nama zasu fita Khalifa ya dakatar dasu da fad'in"Ina zakuje a wannan halin."? Garba Yace."Yallabai yarinyar nan yau sai tayi nadamar uwarta bata haifeta ba mu za tayiwa 'kazafi! banta'ba ganin butulu irinta ba, wallahi da ba don Yallabai yace tun farko a kyaleta da yanzu na zubar mata da hakora da tuni tana kwance tana jinyar kanta dan sai nayi mugun sa'ba mata kammani."! Khalifa yace."Ku dawo ku zauna ku samu nutsuwa." Suka koma suka zauna suna huci! yanda suka fusata niyyarsu subi Wasila gidan redion tana fitowa suci ubanta sai kuma aka katse musu hanzari.....Khalifa yaje ya zauna kusa dashi ya sanya hannu ya dafa kafad'arshi a hankali yace."Siyasa ce f........! katse shi yayi ta hanyar d'aga masa hannu Khalifa ya tsira masa ido ganin yanda duk ya wani burkice har yanzu yana digar da gumi kamar dakin babu Ac 'yan ya tsunsa biyu ya d'ora saman fatar le'bunansa ya tsurawa guri daya ido yana girgid'a kansa. MYSON, NAJIB SA'ID* Tare da kai da *LAWAN RANO* Nagode kwarai da kulawar ku akan wannan book din Allah ya 'kara kauna ya baku mata na gari👏🏻 ~~~~~~~~~~~~~~~~ *Free Pege14* To ganin Malam mai allo ya nufi masallaci yasa suma suka daura alwala domin gabatar da tasu sallahar kafin ya shigo gidan su tattauna abunda yake faruwa, suna zaune kan tabarma ya shigo bakinsa da sallama kamilin mutum ne wanda karatun al'kur'ani ya ratsa shi fari tas dashi kana ganinshi kaga bafulatani usul......Bitan! ta gyara masa tabarma ya zauna yana fad'in"Ashe bakuwa mukayi a gidan Hajara kece kike tafe."? Ta amsa da "Eh wallahi malam tun kusan azuhur nake gidanan Bitan tace min kana tsangaya tare da yan makaranta malam ya gida ya damuna dafatan duk mun same ku lafiya."? Ya aje carbin hannunsa a gefe ya amsa da fadin" Lafiya lau Haraja ya yara ya mai gidan naki."? Duk sunan lafiya kalau wallahi ai yace ma a gaishe ku da kyau."! To masha Allah muna amsawa amma dai za kiyi mana kwana biyu kafin ki koma." Murmushi tayi "A'a malam gobe nake sanya ran komawa dama muhimaniyar maganace ta taso wanda shi mai gidan nawa ne ma yace lallai nazo na shaida maka abunda ke da akwai." To Allah yasa alkairi Hajara ina sauranki." Malam mai allo ya gyara zamanshi yana fuskantar Hajara wacce ta soma warware masa abunda ke faruwa ga iyalin Dan uwanshi Yahuza mai rasuwa.........Ta kara da cewa"Malam yana da kyau ku sanya ido sosai kan wannan yarinyar domin a gaskiyar magana abun da takeyi ya soma wuce gona da iri watarana zata dauko muku abin kunya ko kuma taje ta zagi wani babban mutumin da zai daureku gabadaya yau da al'amarin ma a kanta zai tsaya da sauki wani abun idan ta dauko to ku da bakuji ba baku gani ba sai ta shafeku wannan shine dalilin da ya sanya nace to bari nazo na fada muku halin da ake ciki." Malam mai allo yayi shiru yana jimanta al'amarin, to har yausha hakan ta faru basu sani basu sani ba ko da yake hakan zata iya kasancewa tunda bayan rasuwar Yahuza rigima suka dinga tafkawa da Uwani mahaifiyar yaran kan dole sai an raba gado an bata na yaranta shi kuma yace ko za'a raba gado to ba za'a bata na yara saboda ita mace ce su kuma yaran lokacin suna yara kananu za dai a siyar da gona a raba kudi kaso biyu shi ya dauki kashi daya sauran kuma ya zama magada wato Wasila da Rashida kenan in yaso ita sai a fitar da ita na tuminin takaba kamar yanda addini ya shara'anta.....Nan ma sai ta tada ballin masifa taje 'yan uwanta suka zugota tazo tana yiwa su malam rashin kunya wanda hakan ya janyo sukayi mata fatata fatata! sannan suka kwace su Wasila daga hannunta, kwana biyu da faruwan lamarin Wasila dake tana da wayo a lokacin ta kai kimanin shekaru goma sha biyu sai ta fakaici malam din ya tafi tsangaya ra rike hannun kanwarta suka gudu da malam ya dawo ya samu labari yace."Suje idan shine sai sun tako da kafafunsa sun neme shi, to hakance ta kasance koda su Wasila suka koma gaban mahaifiyarsu sai wahala tayi tsanani a garesu da kyar suke ci daya a rana Wasila itace yawon bin gidajen amare tana musu wanke wanke da raino da share share su bata kudi da abinci ita kuma Uwani itace aikin wankau da dakau da sauransu.....Wasila ta yanke shawarar tun karar wan mahaifin nasu domin su bashi hakuri suka shirya tsaf suka nufi Garin nasu Garko!! Malam ya dinga musu fad'a sosai yace."Duk tsiya dai nine mahaifinku tunda babu ubanku kuna bin shawarar mahaifiyarku kuna bijere ma dangin ubanku to ko auranku ake nema gurinmu zaku zo gwara ku nutsu kuyi hankali ku zauna tare damu zaman ku cikin wannan gida ku kadai bai dace ba saboda haka na yanke shawarar zan baku daki daga ku zauna har Allah yasa ku samu mijin aure ita kuma Uwani ta tafi gidansu itama bata wuce aure ba idan ta samu miji tayi aure....Da jin wannan magana ta malam mai allo sai su Wasila suka yanke sgawarar guduwa domin a ganinsu yanda suka saba da zaman birni zasu cutu a kauye....Washe gari Uwani ta tasa kan 'Yayanta da asuba suka gudu....Wannan abu da sukayi ya batawa malam mai allo rai tun daga lokacin ya dauke hannunsa daga kansu idan ma sauran 'yan uwa suka kawo masa maganarsu sai ya koresu yace kar wanda ya sake kawo masa maganar wadannan yaran marasa kunya suje duniya ce zata koya musu hankali. *Wannan kenan* Malam mai allo ya kalli Hajara yana girgiza kansa yace."Hakika naji dadi da kukayi gaggawa zuwa ku sanar dani wannan al'amari dake faruwa, wannan rashin tarbiyar ne yasa tuntuni na hana Yahuza tafiya maraya da zama saboda nasan tilas a haifi da mara ido a lokacin ya rufe ido yaki sauraran kowa shi dai kawai ya tafi burni ya nemi kudi karin abun kuma ya hadu da mata mara kamun kai ya aure ai asalin lalacewar yaran daga mahaifiyarsu ne da ta basu tarbiya da duk haka bata faruwa ba mu kanmu Uwani bata ganin girmanmu ballanta tana nuna musu muhimancimu a gurinmu, amma babu komai insha Allahu gobe tare zamu tafi kome za'ayi kafata kafar yaran nan dan bazan bari su lalace ba ace muna kallo nan zan kawo su duk in aurar dasu kowa ya huta." Hajara tace"Wannan shawara taka itace abun dubawa Allah ya tabbatar mana da alkairi." suka amsa da "ameen" gaba d'ayansu. To kamar dai yanda malam mai allo ya fad'a hakane ya kasance da wurwuri yayi sallama da 'yan uwa ya fad'a musu abunda ke faruwa suma suka bada goyon bayan kan hukumcin da ya yanke, kana suka hadawa Haraja sha tara ta arziki suka bita da godiya da fatan sauka gida lafiya. Uwani da Rashida kadai ne a gidan sunci kwalliya har sun gaji kamar wanda zasuje gidan buki ga cefane nan kayan miya da nama cikin takarda za'ayi miya gida sai kamshi yake yi....Amina na kwance a tabarma tana danna katuwar waya Uwani na kicin tana aiki Malam mai allo yayi sallama a kofar gidan.....Gaba d'ayansu sai da gabansu ya fadi! Uwani ta fito daga kicin da ludayi a hannunta tana fad'in"Ke Rashida muryar wa nakeji kamar ta wannan masifaffan tsohon."! Rashida tace"Wallahi nima irib muryarshi naj......Kafin ta karasa muryarsa ta sake karad'e gidan "Salamu alaikum."!! Uwani ta amsa da karfi tana fad'in" Waye wai yake rangwada mana sallama kamar munci bashi." Malam mai allo ya girgiza kansa jin muryar Uwani radau! yasan zata aika tunda dama ba kunya gareta ba......"Nine malam mai allo na Garko."! Yafada yana dafe kyauran kofar gidan. "Ayyo koda naji wannan sallama haka to ana zuwa." Uwani tafada tana jan karamin tsaki." Ta kalli Hajara "Ai sai ki tashi kije kece tilas dinsa ni kuwa yace zai min wannan wa'azin sai dai mu kwashi 'yan kallo ni dashi a unguwar nan." Jiki a sanyaye Rashida ta mike ta dauki yalolon mayafinta dake kan igiya ta yafa, duk rashin kunyarsu suna shakkar malam mai allo dan baya musu da sauki.........Tana fitowa ta durkusa tana gaisheshi bai amsa ba sai kare mata kallo yake ganin irin dinki dake jikinta atamfa ce duk an kacalcalata saman nonowanta duk a waje......Girgiza kansa yayi yace"Rashida kece kika dawo kamar ba d'iyan musulmai ba wannan shigar ta jikinki ta sabawa sharia meye abun burgewa anan.? to babu komai duk magana ta kare kiyi maza ki kirawo min daya marakunyar yanzu yanzu zan tasa ku a gaba mu wuce garko saboda na samu labarin ashararanci da kukeyi a gari mahaifiyarku na daure muku gindi kuna yiwa manya mutane rashin kunya wai Wasila ce take siyasa tana gogayya da maza saboda kasa ta rufe idon ubanku shiyasa annabi yace ka zabawa 'yayanka mace tagari duk dan gudun faruwar irin wannan, mu ba'a son ranmu dan uwanmu ya auri mahaifiyarku ba saboda sam bata da tarbiya gashi kuma kun dauko irin nata halin to kome zakuyi sai da kuyi amma tilas ku koma can Garko da zama idan Allah ya kawo muku miji kuyi aur......"Babu wanda ya isa ya rabani da 'yayana wallahi akan wannan sai in maka mutum a kotu."!!!!Uwani ce ke fadar wannan maganar ashe tana la'be tana jinsu......"Haka kawai zaka zo har gida kana zagina malam ka rike mutuncinka da girman ka ada can ma ban yarda ba ballanta yanzu da nasan ina da 'kumbar susa a hannuna dan haka ni banga wanda ya isa ya rabani da 'yayana ba." Malam mai allo yace."Uwani rashin kunya za kiyi min."? Wannan ba rashin kunya bace gaskiya ce, sai da yarana suka girma suka zama mutane inacin ganiyarsu sannan za'a lalla'bo kawai saboda an samu labarin mun faso gari ace ga zance ga magana kafad'i idan kana bukatae wani abu yanzu yanzu sai na kira Wasila tayi maka hasafi ba wai kace zaka tafar min da 'yaya kauye ba." Malam mai allo 'kwalla ta taru a kwarmin idonsa yace."Baku da kudin da zaku bani Uwani kuma kinyi min abunda yafi haka dan kin zageni a yanzu ba wani abun bane ni dai na gama yanke hukunci ke Rashida idan na isa daku maza jeki had'o kayanku muka kama hanya mu tafi.". Rashida ta mike ta shiga cikin gidan tana kuka wayarta ta dauka ta kira Wasila ta fada mata abunda ke faruwa.....Wasila tace''Kome zaiyi kar ku sake ku bishi ku kyaleshi a soro idan ya gaji da tsayuwa ya gaji ya tafi masifaffan tsoho kawai." Uwani kuwa taja tunga ta tare bakin kofa ta rantse babu inda zai tafar mata da 'yaya......Suka dinga tafka rigima da Malam mai allo Uwani ta dinga yi masa rashin kunya kamar ba wan mijinta ba har hankulan mutane ya fara dawowa kansu mutane suka fara taruwa a'lamarin yayi wa malam ciwo a ranshi sai ya fito waje ya tsaya yana tsumayin fitowar Rashida ganin ya fita daga gidan sau kawai Uwani ta rufe kofar gidan ta zura sakata ta koma ciki tana surutai "Idan ka kaji da tsayuwa ka tafi tsoho mai nacin tsiya kawai..........Garba dake can gefe suna magana da wani mutumi ya nuna masa malam mai allo dake bin kofar gidan da kallo yana mamakin rashin kirkin Uwani wato shi suka rufewa kofa, sai ya sanya gefan babbar rigarsa yana goge gumin saman goshinsa.....Garba ya karaso inda yake hannu ya mika masa suka gaisa yace." Aramma idan ba zaka damu ba ina so mu tattauna wata magana da kai." Malam mai allo dake neman wanda zai rarrashe shi kan abunda su Uwani sukayi masa yace."Babu komai yaro ina sauraranka." Garba yace."Muje mota arrama." Malam mai allo baiyi shakkun bin Garba ba saboda lokaci guda yaji ya aminta dashi suka nufi inda yayi parking din motar a tare. _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/18, 2:01 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *PEGE 'DIN YAU NAKI NE* *Real Eshaa🌺* Marubuciyar book d'in. *NAGA RAYUWA* Fatan alkairi har karshen rayuwa aysha Allah ya kawo miji nagari wanda zai rike min ke tsakani da Allah👏🏻 ~~~~~~~ *Free Pege15* Cikin nutsuwa Garba yace."Aramma alamu sun nuna kamar kana da ala'ka da masu wancan gidan, dan Allah idan babu damuwa ina so in san wani abu dangane da wata yarinya a gidan mai suna Wasila." Malam mai allo yace."Ni a matsayin mahaifi nake a gurin Wasila da kanwarta Rashida Yahuza mahaifin yaran kanina ne ciki daya muka fito kuma mu 'yan asalin garin garko ne Yahuza yazo kano neman kudi tun yana saurayi sai ya sai gida yayi aure tare da wannan matar wacce ta kasance a matsayin mahaifiyar su Wasila da Rashida......Garba ya katse shi ta hanyar fadin"Alhamdullhi dama abunda nake so naji kenan ashe faduwa tazo dai-dai da zama malam idan babu damuwa zamuje can gidan ubangidana wanda shine ya sanya ni nayi masa bunkice akan asalin iyayen yarinyar to kuma sai nayi katarin had'uwa da kai, kar kadamu arrama idan mun isa sai kayi masa cikakken bayani akan yarinyar." Malam yace."Yaro ina fata dai ba laifi yarinyar tayi ba domin nima abunda ya taso ni kenan saboda na samu labarin cewar tana cin mutuncin manyan mutane a gari tana fakaicewa da siyasa wannan shine dalilin zuwa na garin." Garba yace."Kar ka damu arrama alheri ne insha Allahu muje koma meye zakaji daga bakin mai gidana." Malam yayi shiru yana nazari yana tsoro kar daga zuwan sa ya shiga masifar yarinyar nan tasa a daure shi baiji ba bai gani ba....Girgiza kai yayi yace."Babu damuwa samari muje kawai Allah yasa alheri ne." Garba ya kunna motar yaja suka futa daga cikin unguwar. Suna tare da Khalifa a harbar gidanshi suna hutawa motar su Garba ta shigo cikin gidan.....Can parking spece ya nufa yayi parking din motar ya fito ya budewa malam mota yana fitowa Idanun Ahamdu suka sauka a kanshi A fuzge yaga suna kama da yarinyar babu tamtama wani nata ne amma babu shakka Garba ya iya aiki bai dauka futa ta farko za'a samu nasara ba to amma yanda yaga kamilin mutum sai yasha jinin jikinsa anya wannan kudi zasu rud'ashi ko dai ya sauya wata hanyar ne dan baiga alamar zalama ta kudi a idon dattijon ba......A nutse ya mike yana masa barka da zuwa dake suna zaune a wata rumfa wacce aka kewaye ta da wasu kujeru masu kyau tsakiyar kujerun katon teble ne da lemuka akai kana ganin gurin kasan na hutawa ne....Malam mai allo ya zauna nutse suka gaisa cikin girmama juna......Garba yace."Yallabai Allah ya takaita mana wahala ina zuwa unguwar nayi katari da wannan bawan Allahn shine yake shaida min shi din shine mahaifin Wasila shima zuwanshi kenan garin to anan na nemi alfarma a gurinshi kan yazo kana son magana dashi." Cikin girmamawa Ahamadu yace."Alhamdullahi naji dadi da hakan ta faru dama ni nafi so nayi magana baki da baki da mahaifin yarinyar dan haka Garba kana iya tafiya babu damuwa." Garba ya bar gurin yana godiya....Ahamadu ya sake mikewa Malam hannu suka sake gaisawa Yace."Malam kan maganar wannan yarinya ne Wasila.'' Malam mai allo ya kalli Ahamadu ganin nutsuwa da kuma a kamala a tattare dashi ya sanya hankalinsa ya kwanta yace."Alhaji ina fatan dai yarinyar nan ba wani laifi tayi muku ba dan wallahi dukkanin abunda takeyi bamu sani ba tunda bama tare dasu labarin abunda takeyi ne ya iskemu hakan ya sanya hankalinmu tashi, muka yanke shawarar zuwa domun mu tattara su mu koma can inda muke da zama dama kuma zamansu hakan bai dace ba a matsayinsu na 'yaya mata komeye zai iya faruwa da rayuwarsu. Khalifa yace."Kwarai kuwa malam muma abunda muka hango kenan ya sanya muka sa ayi mana bunkice akan asalin yarinyar sai kuma Allah ya takaita mana lokaci guda kazo gari ashe ma ba a kurkusa kuke ba." Malam yace." Mu 'yan karamar hukumar Garko ne Yahuza mahaifin yaran ciki daya muke dashi mu hudu iyayenmu suka haifa ni ne babba sai Habibu sai shi Yahuza sannan kanwarmu Kattime To shi kadai ne ya tsalle a cikin mu ya tawo nan yake sana'oinsa har Allah yasa ya samu sana'a ya siyi gida kana yayi aure ya hayayyafa yanzu shekaranshi Takwas da rasuwa bayan karamar jinyar da yayi wanda muma sai labarin mutuwarsa mukaji......Dalili kenan da ya sanya nazo da kaina na dauke yaran har da ita mahaifiyar tasu na tafi dasu can garin namu ko sati daya ba suyi ba suka gudo........Tiryan tiryan Malam ya zayyane musu rayuwar dasu Wasila suka dinga yi tun farkon mutuwar mahaifinsu da irin rashin kunyar da mahaifiyarsu ke sawa suyi musu da yanda shi kuma yayi zuciya ya zare hannunsa daga kansu....Sai wannan karon da yaga abun yayi tsamari ya sanya yace bari ya dauki mataki na karshe kan abunda sukeyi. Ahamadu yace."Arrama yanzu idan ka tafi dasu can Garkon kana da wanda zaka bawa auransu ne."? Malam yace."Ba za'a rasa ba Alhaji kasan shi auran karkara ba'a tsawwala da yawa insha Allahu sati biyu ba zasuyi a gida ba zab daura musu aure." Yace."To idan babu damuwa ni ina son abani auran babbar kuma bana so a ja dogon lokaci idan da hali wannan juma'ar mai kamawa nake so a daure aure." Malam yace."Alhaji da dai 'karamar ka dauka dan sai naga kamar tafi babbar hankali hankalin ka zaifi kwanciya da ita karamar." Yace."Kar ka damu malam shi aure ni'ima gareshi watakila ta sanadiyar auran namu sai kaga tayi hankali fiye da tunani mai tunani idan da hali a amince mun in bada sadaki na yanzu." Malam yace."To to ai babu damuwa nima zanfi jin dadin hakan kaga sai in koma gida da karfin gwiwa ta kuma in sanar da 'yan uwa abunda ke faruwa." Ahamadu yace."Kwarai naji dadin yanda ka yarda dani ka amince min auran yarinyar da wuri ba tare da kaga waliyai na ba insha Allahu ranar juma'a zamu zo tare da kanin mahaifina Wanda shi kadai ne ya rage min a halin yanzu kasancewar nima tun ban kai matsayin wannan shekarun ba mahaifina ya rasu na rayu tare da yan uwansa wannan kuma da kake gani a zaune kusa dani abokina ne sha'kikina tare mukayi karatu kuma muke harkokinmu a tare insha Allahu tare zamu zo dashi ranar juma'a." Malam yace."To masha Allah Alhaji ai ni ganin farko da nayi maka naji hankalina ya kwanta da kai wallahi babu d'ar! zan baka auran Wasila koda banga Waliyinka ba nasan zaka rike mun ita da kyau da amana, babu abunda zance sai dai ince Allah ya saka da alkairi saboda ka gama min komai tunda har ka yarda zaka auri wannan yarinya." Ahamdu yace."Babu damuwa malam, ai an riga an zama daya kuma Allah dai ya kara girma." Mikew yayi ya nufi cikin gidan..........mintuna goma yayi a ciki ya fito hannunsa rike da wata doguwar takarda dake cike da kudi." Ya mikawa malam na fad'in"Wannan shine sadakin Wasila malam." Malam ya kalli uban kudin da ya mika masa sai ya girgiza kai a nutse yace."Ashe baka so auran yayi albarka ba Alhaji Annabi Muhammdu SAW yace."Mafi albarkar aure shine karamin sadaki wannan da yayi yawa duk da ban lissafa na gani ba amma idona ya gane min kudi ne masu yawa, saboda haka dubu biyar kacal zaka biya sadakin wannan yarinya." Ahamadu yace."Malam ka ka'rba don Allah ai ba wani kudi masu yawa ba dubu dari ne kacal kuma kasan dai yanda kudin mu suke basu sa wani daraja kar damu insha Allahu aure zaiyi albarka." Malam yace."Shi dai ba zai kar'bi wannan zunzurutun kudin ba a matsayin sadakin Wasila ya fiso idan yayi mata aure ta zauna mutuwa ce zata raba.....Ahamadu da Malam suka dinga ta'kardama da jayayya shi ya dage sai ya 'karba shi kuma yace ba zai kar'bi dubu dari ba dubu biyar zai 'karba....Khalifa ne ya raba gardama ya ciro kudi daga jikinsa dubu goma ne ya irga dubu biyar ya mikawa Malam yace."Ga sadakin Wasila daga Ahamadu." Malam ya sanya hannu biyu ya kar'ba yana fadin"Ubangiji Allah ya tabbatar da alkairi Allah ya basu zuria mai albarka." Khalifa ya amsa da "ameen rabbi malam muna godiya da karamci." Ahamdu yaji haushin abunda khalifa yayi masa amma bai nuna ba sai ya aje takardar kudin kan teble din gabansa dauki wayarshi ya kira Garba......Garba na zuwa yace maza ya fito da mota ta zuba kayan abinci komai da koma yazo ya dauki malam ya kaishi har Garko Garba ya wuce da sauri domin aiwatar da aikin da aka sa shi. Ahamadu yace."Malam yanzu Garba zai kai gida maganar su Wasila kuma da kaina zan sanya a kai maka su har inda kake daga gobe jibi insha Allahu." Yace."To Alhaji Allah ya saka da alkairi ya biya dukanin bukatu na alkairi." Bayan tafiyar Malam mai allo Khalifa ya kalli Ahmadu yace."Na lura wannan dattijon na arziki ne wallahi sai duk naji jikina yayi sanyi musamman yanda naga ya tsaya kai da fata akan ba zai kar'bi wannan kudin da ka bashi a matsayin kudin sadaki na fahimci yana so auranku da yarinyar yayi albarka wanda kai ba haka abun yake ba a zuciyarka, dan Allah ka kar ka watsa wa mutumin 'kasa a ido ka rike yarinyar nan amana ko dan saboda karamcinsa kamar yanda ka fad'a masa watakila ta sanadiyar auran sai kaga tayi hankali duk abubuwan da suka faru a baya su wuce kamar ba'ayi ba." Shiru yayi yana nazarin maganar khalifa din yace."Nima jikina yayi sanyi lokacin da naga mutumin sam! ban dauka zanga kamilin mutum daga bangaran yarinyar ba ashe ta fito daga tsatso mai kyau gaskiya wannan mutumin ba duniya ce a gabanshi ba ka duba ka gani kudi a wannan zamanin sam basu gabansa wasu iyayen da suke so in kaje neman auran 'yayansu ka sakar musu kudi a gurinsu hakan burgewa ce, shi kuma na lura albarka kawai yake nema." Khalifa yace."Shine ai shawarar da nake baka rike masa yarinyar shine zai sanya ya tabbatar da cewa kai d'in mutumin kirki ne."" Murmushi yayi yace.''Kai nifa ina nan kan bakana wallahi! sai naci uban yarinyar nan wallahi in keta ta kuma in saketa." Khalifa yace."Subahanallahi! wai me yasa kake hakane? ka sani kake takewa yanzu meye amfanin hakan da za kayi."? Sosa kanshi yayi yace."Ai kai dama ba za kaga amfani ba saboda ba kai akayi wa auran nan da zanyi zanyi shine da manufofi da dama kaga na farko zan tashi daga sunan Gwauro kamar yanda ta fad'a zata zame min garkuwata a siyance na biyu zan dawwamar da rayuwarta a cikin 'kunci da ba'kin ciki in takure ta guri guda in muzguna mata har sai ta durkusa gwiwa bibbiyu tana bani hakuri na uku kuma na taimake ta daga wannan yawace yawacen banzan da takeyi a gari tana zubda mutuncinta na killace ta a guri guda....Na hudu kuma auranta zai wanke ni daga zargin da tasa jama'ar gari suke min....Ita ta nufe ni da sharri ni na saka mata da alkairi kaga anan jama'ar suka ji labarin na aureta za tasha tofin ala tsine da zagi sannan ita da harkar Siyasa har abadah! na biyar bukatata ta biya na raba abokanan adawata da ita tunda yanxu kamar itace a matsayin yarinyar su wacce suke sanyawa nayi musu abu ba tare da shakkar kowa ba, nasan kafin su samu 'yar siyasa mai mutukar a'kida irinta za'a sha wuya, kasancewar siyasarmu ta yanzu ta zama sai a hankali duk inda mutum yasan zai samu nan zaije hakanan za kagansu yau su zagi wancan gobe su zagi wanannan sam basu da gwani mutum in dai zaka bashi na 'batarwa shikkenan magana ta kare, amma ita yarinyar ns fahimci ba wannan ke gabanta ta tsaya bangaransu su kadai shiyasa suka riketa hannu bibbiyu saboda sun lura abokiyar tafiya ce....Kuma kasan ba zasu ta'ba bari tayi aure ba zasuyi ta bata kudi tana shirme a gari rayuwarta ta lalace a banxa a wofi.''''' Khalifa yace."Kayi tunani me kyau gaskiya amma dai duk da haka don Allah ka sassauta mata idan ta shigo. Murmishi ya saki mai dauke da manufofi da dama ta'be bakinsa yayi yace."Kana 'bata bakin ka ne khalifa yanda yarinyar nan tasa ni 'bacin rai itama ranta sai ya 'baci." _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* [7/18, 10:18 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege16* Uwani ta fito daga kicin tana fad'in"Da alama dai mutumin nan ya gaji da tsayuwa ya tafi haba! jama'a wai babu dama aga Allah ya rufawa mutun asiri sai a dinga bakin ciki! kiga mutum da rigima haka kawai ka ni'ko gari gari ya gari kazo kace zaka dauke min 'yaya saboda munafurci nasan magulamata ne suka kai masa gulma shine shi kuma ya bazamo babbar riga yazo har gidana ya nuna min iko to ni babu wanda ya isa yace zaiyi min iko da 'yayana 'yan uwana ma ban d'agawa 'kafa ballanta wani saboda haka ke Rashida maza maza ki kira Wasila a waya kice tazo yau d'in nan ta dauke mu a mota mu bar nan tunda har wannan tsohon ya soma zuwa shikkenan kuma zai ta daga mana hankali gwara kawai a nemu mu a rasa a unguwar." Rashida tace"Ni wallahi tausayinsa nakeji gaskiya Uwani banji dadin abunda kikayi masa ba Kamar uba yake a gurinmu kin tozarta shi a unguwa." '' Ayyo kina so ki nuna min kinfi kaunarsa a kaina ni dana tsuguna na haifeki naci kashinki da fitsarin ki shine zaki butulce min shi me ya ta'ba tsinana miki a rayuwa." Rashida tace"Wallahi kafin babanmu ya mutu ya fada min lokacin da aka haifeni da ya rasa yanda zaiyi da hakika can kauye ya nufa gurin Malam mai allo din ya bashi katuwar tinkiya aka rada min suna da ita." Uwani tayi kasake tana kallon 'yar tata ashe kafin mijin nata ya mutu sai da ya fada musu abubuwan da suka faru a baya....."To ai hakika dama dole ce a wuyansu take idan basuyi ba ai sai a kira ki da shegiya gwara ma ki daina wannan magana dan bayan ya bada tinkiya anyi miki rad'in suna babu abunda ya kuma tsinana miki." Rashida tace."Gaskiya dai ki daina ci masa mutunci." Uwani ta fashe da kuka tana fadin"Sai ki zageni Rashida ki fito fili kawai ki zageni yau naga matsayina a gurin ki shiyasa ni Wasila tafi min ke sau dubu duk abunda tasan za tayi ta faranta min rai shi takeyi duk abunda nace tayi tana yi min babu musu ke kuwa fa sai dai ta nemo kudi kina daga kwance kice, to duk rashin mutuncin da kikeyi min sai na fada mata." Tana gama maganarta ta shige daki tana matse hawaye.....Wayarta ta dauka da Wasilan ta siya mata ta hau kiranta....Lokacin suna tare da mai girma governor suna meeting Wasila taga kiran amma bata dauka ba sai bayan sun fito daga dakin meeting din ta kira ta....Uwani na daga wayar ta fashe da kuka "Wasila maza ki zo gida Rashida na nan tana min rashin mutunci duka na ne kawai ba tayi saboda zuwan Malam mai allo." Rai a 'bace! ta kashe wayar ta nemi numbar Rashidar.....Rashida ta daga wayar tana zumbura baki "Wallahi Rashida ki shiga hankalin ki! dan Kutumar ubanki me malam mai allon ya tsinana miki da har kikewa mahaifiyarki rashin kunya har kin manta irin wahalar da tasha akanmu ashe dama kika bawa malam din yaci mata mutunci kamar yanda ya saba to wallahi sai ranki yayi mugun 'baci! kan hakan." ''Aunty Wasila ki saurara kiji abunda yake faruwa." Rashida ce ke ta magana amma taki sauraranta sai zaginta take cikin jin haushi ta kashe wayar....Wasila ta tsaya tana mamaki! lallai Rashida bata da mutunci ta gama wahala da ita amma ta kashe mata waya....Mahaifiyar tasu ta kira tace"Kinga Uwani na soma zargin yarinyar nan wallahi harda hadin bakinta gurin zuwan Mai allo gidanan dan haka hankalina ba zai kwanta ba komai dare zan shigo unguwar in daukeku ku zauna cikin shiri." Uwani tace"Nima dama shawarar dana yanke kenan dan tunda malam din yazo nasan sauran ma suna tafe haka kawai su rusa mana rayuwa waye zai koma kauye ya zauna? sai dai duk abunda zasuyi suyi." Duk dai magana ta kare ku zauna cikin shiri." Uwani tace "To shikkenan sai kinzo." kashe wayar tayi ta iske inda Camas take zaune tana kallonta. Har kusan karfe goma da rabi na dare Garba na layin su Wasila cikin matasa yayi basaja so yake yaga ta inda Wasila zata 'bullo, shiru asalima tunda ya zauna ko kare bai gani ba a bakin kofar gidan nasu.....Yananan zaune mutane suka fara raguwa saboda dare kowa na tafiya gida shima sai ya yanke shawarar tafiya dama a Mashin yazo roba roba ya sanya mukuli zai kunna kenan ya hango tawowarsu Wasila jikinta sai walwali ya keyi kasancewar material din dake jikinta mai kyalline wani bala'in kamshin turare ya bakunci hancinsa lokacin data giftashi ta suka shige ita da Camas! wace ta nufi gidansu ita kuma ta hau buga kofar gidan......Matasan dake kusa dashi ne suka fara magana kasa kasa..."Shegiya karuwa kawai ina su Mado nanan da sunci ubanta ta gama guje gujen ta dawo karuwar banza da wofi! ai sai munci ubanta wallahi." Zaginta sukeyi suna kwashe mata albarka garba na jinsu bai ce komai ba yana nan zaune yaga sun fito ita da sauran mutanan gidan.....Gidan suka kulle suka wuce simi simi kamar munafuka...nan yaji matasan dake kusa dashi na fad'in"Ai babu matsiyaciyar uwa sama sa wannan matar duk itace ta sanya ta take wannan rashin mutuncin dazu fa wan mahaifinsu ne yazo suka rufe masa kofa ai wallahi mun kusa tashin su daga unguwar nan." "Kai kasan me zamuyi ma yanzu."? girgiza kai yayi yace." Kone gidan zamuyi dan uwarsu in sun dawo su kwana a waje." Kai wannan shawara tayi kyau abokina." Tafawa sukayi suka mike tare.....Garba ganin sun bar gurin sai shima ya hau mashin dinsa yabi bayan su Wasila can ya hangosu tsallaken titi inda tayi parking din motarta suka shiga a take ya bi bayansu amma yanda yake binsu a hankali ba zasu dauka su yake bi ba. Dake unguwar masu hannu da shuni ce ko ina haske babu duhu da tarin kazanta daga can bakin titi Garba ya tsaya ya kafe mashin dinsa a hankali yabi bayan motar inda yaga ta nufi wani estete wanda manya manya mutane ke zaune a ciki Garba yayi mamaki sosai babu shakka yarinyar samu kudi ganin motar ta tsaya a bakin gate din wani tangamemen gida ginin zamani, yana kallo mai gadi ya bude gate din ta shigar da motar ciki, sai ya juya da sauri ganin sucurity na nufowa inda yake, da sauri ya tashi mashin dinsa ya bar gurin a guje......A daran ya shaidawa Ahamdu unguwar da Wasila take sam baiyi mamaki ba saboda yasan zasu iya yi mata abunda yafi haka, kudi ne gasu nan a banzace ayi abunda ya dace an'kiyi ana watsar dasu a banza a wofi jirgin sama ma zasu iya siya mata mutukar bukatarsu zata biya. Uwani da Rashida suka gigice ganin ubangidan da Allah ya mallakawa Wasila suka dinga shige da fice a gidan suna ta'be ta'ben abubuwa Uwani dai kusan zautuwa tayi saboda ta masifar rudewar da tayi taga uwar daula da duniyar da 'yarta ta cikinta ta samu.....Wasila tace "Ko wanne ya dauki daki daya ya ishe shi bukatar rayuwarsa Uwani kinga Abunda Allah yayi mana ko? da kina cewa muje muyi karuwanci shine zamuyi kudi da gaggawa to wannan sana'a da nakeyi mutukar ta karbe ka nan take zakayi arziki yanzu ina da kudi cikin account dina da ban san a dadin su ba kullum 'yan fadar mai girma governor tura min kudi suke bamu da matsalar komai a halin yanzu Allah ya yaye mana kuncin talauci ba tare da mun aikata sa'bo ba. Uwani tace" Sai yanzu kuma na gane abunda kike nufi Wasila wallahi ni a daukata yanzu babu abunda ke saurin kawo kudi da gaggawa kamar karuwanci ashe akwai sana'ar da tafi wannan to Allah nagode maka da bai sa kun dauki gurguwar shawarar da nake baku ba." To a ranar dai da kyar su Uwani sukayi bacci dan Wasila dakinta ta shige tayi wanka tayi kwanciyarta bacci mai dadi ya dauketa........A furgice! ta bude idonta tana salati! ta sanya hannu ta kunna fitilar gefan dago tana bin dakin da kallo kamar me neman wani abu....Kafafunta ta zuro kasa suka sauka kan kafet, ta jima a haka kafin ta mike ta nufi toilet fitsari kawai tayi ta dawo ta kwanta ta rufe jikinta da bargo amma banda fuskarta ta kasa kashe fitilar dakin tayi domin gani take kamar zai iya mamayarta kamar yanda ya mamaye ta cikin mafarkinta na yanzu, Tun da take a duniya ba ta'ba ta'ba mafarki wani d'a namiji ba sai yau! shin wai wannan mafarkin me yake nufi ne? meye ala'karta da wannan guy? ita dai tasan ba'kar gaba ce tsakaninsu to mai zai sanya yazo mata a mafarki yana mata murmushi saboda kuma tsabar wuce gona da iri har ya rungumeta yana tatta'ba mata sassan jikinta....Tayi sauri ta sanya hannunta a ramin cibiyarta sai taji tamkar hannunsa ne a gurin a lokacin da yake shafa mata cikin mafarkinta, jin tsigar jikinta ns tashi ya sanya tayi gaggawar cire hannunta daga gurin.....Rufin dakin ta tsurawa ido, itafa wannan mafarkin ya bata tsoro har yanzu tana hango fuskarsa da tattausan murmushi, shin wai abunda tayi masa bai dame shi bane da har zai zo yana mata murmushi, ita ta dauka zasu kulla gaba ne ita dashi wacce tafi ta da tsanani!!!!!!! Juyawa tayi ta rungume pillow tana lumshe ido....."Subahanallahi." Hannunsa taji a jikinsa ta mike a zabure! tana dube dube a dakin........Yau satin ta daya a gidanan amma bata ta'ba shiga tsoro da farga ba irin na yau! mikewa tayi ta zura hijab! ta bude dakin ta futa....Dakin da su Uwani suke nan ta nufa, gani take kamar in ta zauna a dakin ita kadai mafarkinta zai iya tabbata.....Duk suna tare dake bed din babbane su Rashida da Uwani anji Ac sai bacci akeyi, ta samu ta ra'be gefensu ta kwanta had'e da takure jikinta guri guda.......Ta jima a haka kafin bacci ya dauketa. *** Cikin Shiri ya fito daga bedroom dinshi, Garba da Hadi na zaune a katafaran palon nashi suna ganin fitowarshi suka mike a tare gaisuwa suka mika amsa yana mika musu hannu sukayi musabaha da juna Ahamadu bashi da girman kai da d'agawa........Yana mutumta dan adam!! Garba ya isa inda yake yana gyara masa babbar rigarshi da yake yau shigar manya kaya yayi dakarkiyar galila ce a jikinshi green color wuyan babbar rigar anyi masa aiki na manya mutune wanda mafi aka sari masu sarauta keyi, yana gyara links dinshi Garba ya miko mishi hula zanna bukar 'yar gasken ya d'ora saman kanshi a sai ya sake wankuwa da kyau gyaran fuskarshi yayi dai-dai da tsarin askin dake kanshi saisaye yake yi bai fiye tara suma ba amma baya kwal kwabo ana masa saidaye ne agyara masa fuskarsa dai-dai da zamani....Duk wanda ya kalleshi sai ya sake kallo babu wanda zaice ya kai matakin shekurun da yake kai a yanzu.....tare suka futa dasu Garba mutukar ba nisa zaiyi ba baya tafiya da securities su Garba kadai yake dauka su raka shi, Garba ya bude masa bayan mota ya shiga ya zauna Hadi ya zauna kusa dashi ya mayar da murfin motar ya rufe.....Da sauri Garba ya zauna maxaunin direba tun kafin su iso bakin gate din mai gadi ya bude gate din.....Securities din dake zaune a bakin gate suka dinga daga masa hannu da fadin "A sauka lafiya Allah ya tsare a dawo lafiya." Shima hannunsa ya daga musu yana amsawa da "ameen." Har suka futa daga gidan......Sai da suka hau kwalta tukkuna Garba ya tambayi inda suka nufa, ya shaida masa inda zai suje gidan Hajiya Babba dake Zooroad. Garba ya dauki hanya kamar yanda aka umarce shi. *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege17* Hajiya Babbah na xaune a palonta tare da wasu 'yan mata guda biyu Suhairat da Salimat 'Yayan mutun d'aya ne wato Hajiya Maryam wacce ta kasance 'kanwa ga Hajiya Babbah! kasancewar Allah bai bata haihuwa ba har mijinta ya rasu.mutane ke ta nani'ka mata 'yayansu mussaman 'yan uwanta waccan ta turo 'yarta gobe waccan ma ta turo 'yayanta jibi duk dan ganin daular dake tattare da gidan....Suhairat ce mai nacin zuwa gidan saboda kawai tayi katari da Ahamdu mutumin da ta kwallafa ranta a kanshi take masifar sonsa shi kuma bai san tana yi ba sai tayi zuwa goma gidan ba ganshi ba dan bai fiye zuwa da safe ko da yamma ba sai dare yake zuwa gaisheta, to yau dai sunji dadi jin Hajiya tace sunyiwa waya dashi yace zai shigo da wuri Suhairat ta sake gyara fuskarsa ta fesa turare ta 'kame! a kan mujera Salimat kuwa sai dariya takeyi mata tana fad'in"Allah yasa dai ya kyasa dan na lura kinyi masifar matowa a kan mutumin nan." Suhairat tace"Ke dai bari 'yar uwa ni wallahi da zai aureni da gudu zan yarda ina masifar sonsa komai nashi yana burgeni mutum kamili ga nutsuwa kamshin turaransa ma abin alfahari ne." Salimat ta dinga 'kyalkyala dariya tana tsokanar yar uwar tata......Cikin nutsuwa da kamala ya shigo palon bakinsa dauke da sallama. Dukaninsu suka mike tsaye suna masa barka da zuwa, kamshin turaransa ne ya cika musu hanci Suhairat sai murmushi takeyi tana gyara masa gurin zama....Ya zaune a nutse yana fadin" Suhairat kune yau gidan? ina Hajiyata." Wani fari tayi da ido tace"Wallahi kuwa Mune yau a gidan Hajiya na daki bari na kirata." Ta juya tana tafiya cikin wata iriyar siga.....Oho bai san tanayi ba dan idanunsa na kasan kafet, Tare suka fito da Hajiya babbah tana masa barka da zuwa ya amsa yana tambayar ta gida.....Suhairat ta dauko mishi lemo da ruwa ta tsiyaya masa ta mika mishi.....Ba tare da ya kar'ba yace."Bana jin zansha komai yanzu nagode Suhairat." Jiki a sanyaye ta ajiye cup din ta nemi guri ta zauna kusa da Hajiya......Yace."Ina ta son zuwa Allah bai nufa abubuwa sunyi yawa hajiya a gafarce ni." Tace."Ai babu komai Ahamdu dole ne ayi muku uziri saboda yanayin harkar taku ta jama'a bayan nan kuma nasan akwai hidimomi da yawa Allah dai ya taimaka." Ya amsa da "ameen." Palon yayi shiru Yana so yayi mata maganar dake tafe dashi amma zaman su Suhairat a gurin ya hanashi shi mutum ne mai sirri yafi son komai nashi a cikin tsari dan ya lura da yarinyar kanta rawa yake yasan dai zancen gizo baya wuce na koki ga yanayin yanda take masa kwarkwarsa za tace itama sonsa takeyi. Gyaran mirya yayi a nutse yace."Hajiya muhimiyar magana ce take tafe dani dan daga nan ma idan na tashi can gidan Kawu Almu zan nufa." Hajiya Babba tace "To babu laifi Ahamadu Allah dai yasa maganar dake tafe da kai irin wacce take bakina ce da nayi mutukar jin dadi." Murmushi ya saki wanda yasa Suhairat shagala gurin kallonsa Yace."Yana da kyau yaran nan su dan bamu guri." Hajiya ta kalli su Suhairat da suka kasa kunne suna so suji maganar ko kunya babu tace."Suhairat ku shiga ciki mana." Simi simi suka mike sam basu so hakan ba mussaman Suhairat tafi so ya fadin maganar a gabanta da jikinta na bata wani abu. "Hajiya na samu matar aure insha Allahu ranar juma'a ta jibi za'a daura aure." Maganar data fito daga bakinsa kenan.....Fuskarta da yalwataccan murmushi tace"Alhamdullihi Ahamdu baka ta'ba zuwa da labarin da yayi min dadi kamar wannan ba masha Allahu to amma kuma al'amarin baiyi sauri ba kuwa ko bazawara ce ne."? Ya girgiza kai "Budurwace Hajiya." Tace."To to masha Allah amma kuma abun yazo min bagatatan banyi shirin komai ba ko da yake dama haka aure yake dashi da mutuwa ba'a shirya musu in lokaci yayi sai anyi, shin yarinyar 'yar wace unguwa ce kuma." Yace." Yar wata karamar hukama ce a wannan jahar sunan garin nasu Garko amma anan tayi rayuwarta Unguwar dorayi daurin auran dai Can Garko zamuje ayi." Tace."To Ubangiji Allah yasa za'ayi damu ya tabbatar mana da alkairi." Ya amsa da "ameen Hajiyata, ni zan wuce can gidan Kawu Almu babu wani abu da kike bukata ko."? Tace." Alhamdullahi Ahamdu bana bukatar komai ka wadatani da duk abun bukata kafin wani ya kare kasa an kawo wani babu abunda zance sai da nace Allah ya saka maka da alkairi ya jikan iyayenka." Yace."ameen Hajiyata Ubangiji Allah ya barmin ke na dinga ganinki ina jin dadi." Tayi dariya da fadin"Wace ni Ahamdu ai mutuwa rigar kowa ce zan mutu kaima zaka mutu." Ya mike yana kallon a gogon dake daure a hannunsa yace."Duk da haka dai Hajjah ina fatan kiyi rayuwa mai tsayi a duniya tace."To Allah yasa Ahamdu Allah yayi maka albarka ya baka 'yaya masu albarka." ya amsa da ameen yana mata sallama har bakin kofa ta rakoshi tana sanya masa albarka Suhairat dake la'be bakin kofa ta silale 'kasan daki ta fashe da kuka "Shikkenan na mutu ni suhairat shikkenan karyata ta kare zaiyi aure ina zaune duk na kori masu sona saboda dashi bai san inayi ba na shiga uku na lalace." Kuka take sosai Salimat na bata hakuri Hajjah ta shigo dakin. Tace"Ke suhairat lafiya kike wannan kukan." Rungumeta tayi tana shashsheka take fada mata tsayin shekarun da tayi tana jiran Ahamdu amma yanzu yazo yace zai auri wata. Hajjah tace"Inda Ahamdu zai aureki da tuni ya aure ki Suhairat ni da kaina nace ki hakura dashi ki zabi miji cikin manema auranki ki aura kikaji ni ba zanyi masa tilas ba, saboda yaron ya daukeni a matsayin uwa yana min biyayya komai nake so yanayi min ban haihu ba amma an haifar min addua ce tsakanina dashi ni dai shawarar da zan baki shine ki hakura dashi ki fito da miji cikin ma nema auranki ki aura magana ta wuce." Suhairat ta mike daga jin hajjah tana kuka mayafinta ta figa ta dauki handbang dinta ta fice....Salimat ce kawai tayi wa Hajjah sallama tana bata hakuri kan abunda Suhairat din tayi mata.....Tana fitowa harabar gidan taga Suhairat ta figi mota a guje ta fice daga gidan....Girgiza kai kurrum tayi ta sanya direba ya dauketa domin kaita gida.....' Yan asalin unguwar galadanci ne. **** Wasila ta tashi da wata iriyar kasala da mutuwar jiki, dan ta jima ma a daki kafin ta fito cikin kayatacciyar kwalliya gold kamar yayi magana a jikinta har yatsun 'kafafunta gold ne tana sanye da legos less dan gasken tayi daurin ture kaga tsiya gashinta ta daure shi da katon ribbon ya kwanta a kafadarta idan ka kalleta sai ka dauka irin masu shegen karatun nan ce saboda yanda takeyin mu'amula cikin jan aji da isa......Uwani da Rashida sai girki suke su sauke su dora suci wannan su sha wannan duniya ta samu. Tunda ta kunna wayarta sa'konni ke shigo mafi yawanci daga abokanan harkarta ne maza sunfi yawa babu wanda ta duba a cikin messages din wayar dai kawai take latsawa tana ya mutse fuska, ita kadai tasan me takeji a jikinta har yanzu gabanta bai daina faduwa ba mutukar zata tuna da mafarkinta na jiya.....Kiran As ne ya shigo wayar ta sai da ta kusa katsewa sannan ta dauka suka gaisa yace anya zaki fito yau kuwa? Ya mutsa fuska tayi tace"Yau dai zan huta a gida Gaskiya sai dai gobe." Yace."To babu laifi ko nazo na taya ki hira ne."? a ya tsine tace"Ina da abokanan hira ka huta kawai." Mara zuciya sai ya sake cewa "Okey anjima zan shigo zamuje musha iska." Tace."Ba damuwa sai ka shigo amma dai ka bari sai bayan sallahar isha'i." Yace."Haka za'ayi gimbiya." Hira suka dan ta'ba tayi masa sallama da fad'in zata kwanta bacci ba dan yaso ba ya hakura. Kashe wayar tayi tana tsaki....Camas! tayi sallama ta shigo palon....Taci uwar kwalliya da material mai uban tsada wani shegen dinki akayi mata mai fitar da tsaraici gashi bata sa mayafin kirki ba Camas an samu duniya har mota ce da ita sannan itama Alhaji Ma'aruf yayi mata alkawarin mallaka mata gida cikin gidajensa da yake ginawa.....Tace."Kawata ya yau dai duk na ganki babu kuzari ne na jima da zuwa government house ina jiran zuwanki sai yanzu As yace yau ba zaki fito ba sai gobe." "Camas yau hutawa zanyi wallahi na gaji kullum kana cikin maza shegu suyi ta kare maka kallo wani ma yana sane zai zo ya gogi jikinka wai bai sani ba, na kusa daina wannan harkar tunda bukatata ta biya." Camas tace"Wallahi karki soma shin me na kasa yace ballanta ya bawa na sama me kika mallaka me kika ajiye a account dinki karfa ki manta yanzu lokacin da zaki sake zage damtse ki tatsi abunda kika tatsa wanda ko bayan mulki ya bar hannunsu kin samu kasonki me tsoka ai wallahi ni yanzu na fara har sai naga abunda ya turewa buzu nadi." Ajiyar zuciya ta saki a hankali tace" Duk da haka dai zan dinga daga kafa ba kullum zan dunga zuwa government house din ba, kina sane dai da kallon da jama'ar gari ke mana ko wasu fa karuwau suke daukarmu, na tsani ace min karuwa wallahi." Camas! tace" Sun dade basu kirani da karuwa ba abunda ya damesu ne idan kace zaka daka ta mutane sai su cuce ka.'' Shiru kawai tayi tana girgixa kai ta tsani a kirata da karuwa gwara Camas idan sun kirata da karuwa babu laifi tunda tana ta'bawa amma ita ba taji ba bata gani ba ana kiranta da kalmar da tafi tsana a rayuwarta. **** *RANAR JUMA'A* Su shida ne kacal a cikin motar Ahamdu Kawu Almu da abokinshi sai Khalifa da mahaifinshi Alhaji Iliyasu sai Garba dake gaban mota yana draving, kasancewar shine yasan gidan ya sanya zai jagoronce su.....Ahamdu da Khalifa suna sanye da kaya iri daya farar shadda ce kal dinki babbae riga da yar ciki hula iri daya agogo iri takalamsu iri daya hattata da links dinsu iri daya ne sosai idan ba fada akayi ba ba zaka bambance waye angon ba a cikinsu. Can bangaran su Malam mai allo kuwa sun shirya tsaf dan tuntuni malam ya shaidawa limamin dake sallahar juma'a a babban massalacin dake garin cewar bayan an idar da sallah akwai daurin auren da za'a gabatar.......To lokacin da suka sauka garin ana ta shirye shiryen tafiya massalaci dan haka a gurguje suka daura alwala suka bi ayarin mutane ya zuwa masjid d'in. Bayan liman ya gabatar da hud'uba kamar yanda addini ya tanada sai aka tayar da sallah........An idar da Allah anyi addua kana kuma aka shiga daurin aure.............Ana shafa fatiha Garba da Khalifa suka soma rabon alawa da goro gami da dabino cikin bakar leda za'a bawa mutum goro da alawa daurin aure yayi albarka jama'a sai addua suke gami da fatan xaman lafiya ga amarya da ango. _Muje Zuwa_ *BINTA UMAR ABBALE* *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege18* Su Kawu Almu suka rufawa Ahamdu baya zuwa gidan Malam mai allo dake cike taf da dangi, katuwar tabarmar dake shimfide a tsakar gidan suka zazzauna aka shiga gaishe gaishe 'yan uwa sai tambaya sukeyo waye angon ne tsakanin Ahamdu da Khalifa.....Ahmadu yayi kasa da kanshi a lokacin sai ya tsinci kanshi da jin kunya duk da a zuciyarsa auran yayi shine da wata siga ta daban amma sai yaji kunyar mutanan mussaman malam mai allo dake ta kai kawo yana hidima da mutane kana ganinshi kasan yana cike da farin ciki....Khalifa ne ya dinga nuna shi yana fad'in"Gashi nan wannan ne angon bani ba.'' Tsoffin ciki suka soma yi masa d'an biki suna tsokanarshi da fad'in ya tsinci dami akala tunda ya samu nasarar auran Wasila saboda haka ya riketa da kyau dan ba karamar mace bace." Shi dai jinsu kawai yake yi yanayin yanda suke mu'amular su ya bashi sha'awa mutuka kuma ya lura suna masifar son su Wasilar halinsu kawai suke gudu, magana cikin magana suke masa hannunka mai sanda kan yarinyar kan yayi hakuri da halinta da dai sauraransu, sai ya kara jin jikinsa yayi sanyi da al'amarin auran yanzu kuma ya soma da ya sani tunda shi har cikin zuciyarsa ba da manufa me kyau ya auri yarinyar ba amma kuma darajar iyayenta na nema ta sauya masa tunani. Lafiyayyan towon shika da miyar taushe aka kawo musu miyar taji manshanu gefe guda kuma ga soyayyan naman zabi nan fal katuwar silba......Babu wanda yayi wasa a cikinsu duka suka zage suka ci abincin dan tsabarta da kayatuwarsa tamkar a restaurant babu wata alama da zai nuna abincin karkara ne kwanika sabbi aka zubo musu dalili kenan da ya sanya suka saki jiki suka ci suka koshi suka kora ruwa mai sanyi irin na randa. Bayan sun kammala sai suka shirya tafiya gida,Malam mai allo ya ke'be da Ahamdu yana masa maganar kan ya za'ayi da tariyar Wasilar Yace." Ya bar komai a hannunshi.'' Malam mai allo yace."Nida nafi so yau yau yarinyar nan ta kasance a dakinta bana so mu shiga hurumin ubangiji ya kasance muna wasa da aure, tunda an daura auranan to ta tare a dakinta barin ta haka sasakai zai janyo matsala babba tunda dai ita bata san halin da ake ciki ba.'' Yace."Tabbas maganar haka take malam babu damuwa insha Allah yau zata tare a dakinta kamar yanda ka bukata din." Malam yace."To bari in baka sadakin a hannuka ka mika mata da kanka tunda dai mu ba ganinta Zamuyi ba." Yace."babu damuwa Malam." ya ciro dubu biyar din ya mika masa ya sanya hannu biyu ya kar'ba, kana ya shiga yi masa godiya sukayi sallama cikin mutunci da mutuntawa.....Har bakin mota suka rakosu sai da motarsu ta 'bacewa ganinsu sannan suka juya cike da farin ciki sun auran da Wasila saura Rashida zuciyarsu wasai mussaman malam mai allo yana fatan d'orewar zaman lafiya ga Ahamdu da Wasila. Cikin mota tunani kawai yake yi kan al'amarin duk ya rasa wane matsayi zai aje wannan auran nashi zuciyarsa na kawo masa shawarwari iri iri tabbas ko A lahira wani nacin albarkacin wani babu shakka yarinyar taci albakarcin dattijo malam mai allo a gurinsa, da ya dauki mummunar aniya a kanta albarkacin mutumin ya rage kashi tamanin daga cikin abunda ya tanadar mata amma dai duk da haka zai ba zai kyaleta ba sai ta gane bata da wayo......Haka suka isa gida tunani duk ya addabe shi yanzu ya za'ayi ma ya tunkari inda yarinyar nan take dame zai fara ne." ? Khalifa yace."Naga ka shiga tunani da yawa ka bari muje gida mu dan huta tunani ya dawo tukkuna nasan abunda ke damunka a yanzu amma aka bi komai a hankali mai sauki ne." Ajiyar zuciya ya sauke ya dan gyara zamanshi ya sake mai da idonsa ya rufe ba tare da yace komai ba. Cikin wata lafiyayyiyar lifaya ta fito Tana baza kamshi turarruka masu tsada da sanyin kamshi, Tayi ado da gold 'kirar dubai masu jajayen stones a jiki shi kanshi gyaran gashin da tayi wa kanta abun kallo ne tamkar wata balarabiya haka ta zama babu shakka kudi na iya canza mutum nan take Wasila ya zanzu dai da zata shiga cikin labarawan Itopia sai ta saje dasu saboda yanda fatarta ta goge ta 'kara fitar da kalarta chocolate color dama can haka kalar fatarta take Rashida ce fara itace ta d'ebo haske babansu Uwani kuwa ba za'a kirata fara ba kuma ba za'a kirata baka ba kusan kalar fatarsu daya da Wasilan amma dai yanzu ta Wasilar tafi kyau da gogewa, takalmi mai tsayi ta sanya kasancewar ba ta fiye tsayi sosai tana tsaka tsaki dai! Hannunta rike da pose da key na motar ta take takawa sannu a hankali.....Camas dake zaune na latsa waya ta kalleta "Wow! Kinga yanda kikayi kyau kawata, gaskiya lifayar nan ta miki kyau wallahi ke kin jima bakiyi kyau irin na yau ba tamkar wata amarya lalle ne kawai babu a hannunki da kafafunki.'' Murumsi tayi tace" Haka kawai yau nace bari nayi shigar bare bari ashe nayi kyau."? Camas! ta kwalawa Rashida kira ta fito daga kicin....Ganin Wasila ya sanya ta rude! "Aunty Wasila kece dan Allah nima ina son lifayar nan ki siyamin wallahi kinyi kyau! sai kallonta takeyi tana dariya Camas tace " Wai tambaya takeyi tayi kyau shine na kira ki ki fada mata." Rashida ta hau kod'ata "Wallahi aunty Wasila ko makaho ne yazo kusa dake ya tsaya sai ya kiyayi kansa babu wanda zaice kin hada jinsi da bahaushen mutum kamar wata balarabiya." Ganin yanda suke sambatu ya sanya ta dinga musu dariya...Uwani ma ta fito daga daki ta dinga nata shirma da zasu fita ta dinga yiwa 'yar tata kirari sai kace wata maro'kiya ita Wasila ma dariya suka bata tace"aikuwa dai tunda shigar lifaya nayi min kyau zan dawo yin irinta.... Suna shiga motar kiran As ya shigo wayarta ta dauki wayar tana dan ya mutsa fuskarta.....A nutse tayi sallama da sauri ya amsa yana fad'in "Gani a bakin gate din gidanki ki fito kawai muje mu dawo dan ma dai nayi alkawari ne da sai nace mu bari sai gobe ma futa yanzu aka kirani a waya karfe goma dai-dai muna da metting da shugaban 'kasa kin san tun safe ya shigo gari yanzu haka suna tare da mai girma governor." Tace."To mai zai hana mu bari sai gobe." Da sauri yace." Ai ni kuma ba zan fuskanci komai ba gurin metting din nan mutukar banyi tozali da kyakkyawar fuskar nan taki ba." Murmushi tayi ta kashe wayar ta kalli camas tace"Ga d'an anace nan ya iso kawai ina zama na wai na shirya muje shan iska komai abunsa dole ya hakura dani wallahi wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa Camas tace"Tunda dai yaki hakura ba sai kiyi kwance kwance ki kwashi rabonki ba." Ke dai kawai fito muje dare nayi kudi kam ai kamar mahaukaci haka yake samun a account. " Camas taji inama itace dan a zahiri As yafi Alhaji Ma'aruf sakin hannu shiyasa taso ace As din ne ke mu'amula da ita tasan da tuni ta wuce gurin........Kamshi turaranta shine ya buwaye shi, yana draving yana kallonta idanunsa sun kada sunyi jawur babu shakka yau Wasila ta kaishi makura ga bukatuwa da ita yana ganin koda bai shiga wannan ramin ba a'kalla dai ta bashi dama ya d'an rage zafi a jikinta....Da kyar suka isa 'katon gurin hutawar wanda sai wanda ya amsa sunansa ke zuwa gurin......gurin tamkar rana ko ina haske tar tar jama'a nata shigowa da motacinsu da yawa daga ciki tare suke da mata wasu karuwansu wasu matayen su kowa harkar gabanshi yake.........As yayi kwance a gabanta yana lumshe mata shegun idanunsa da suke cike taf da sha'awarta duk sun kankace saboda jaraba, ganin yana matsowa jikinta ne yasa tayi saurin matsawa tana 'bata fuska.....Yace."Yana da kyau yau daya ki bani dama ko yaya ne na ra'bi jikinki babu shakka zuciyata na azabtuwa da so da kaunarki ki bari na rungume ki ko zanji dadi a jikina" Ranta a bace ta kalleshi "Haba As wai yaushe ne zaka daina yi min irin wannan maganar? na sha fada maka ni ba 'yar iska bace amma ka kasa fahimta ko dan kana ganin Camas! kawata ce shine nima kake zargin halinmu daya da ita, Wallahi da zanyi karuwanci da tuni nayi amma ni ba layina bane kaje ka nemi karuwa ta debe maka kewa bani ba, idan kudin da kake turo min da wannan niyyar ne to dan Allah daga yau kar ka sake kuma tunda ka kasa daukata a matsayin abokiyarka to ka goge numbarta dake wayarka bana bukatar wata mu'amula ta sake shiga tsakanina da kai. Mikewa yayi zaune yana marairace fuska yana so ya kama hannayenta ta fuzge da karfi ta mike tsaye da sauri jikinta na rawa...Camas na can tare da wani alaji suna zance ta iskesu rai a 'bace tace" Ni zan wuce gida Kya biyo bayana." Mutumin yace."A bari nazo na kaiku mana." Ko sauraransa ba tayi ba tayi hanyar futa....Ita ko Camas! ganin alhajin nada kumbar susa a tare dashi sai tace"Rabu da ita Alhajina idan da wata bukata da kake nema a gurina yi min magana kawai kar kaji shakka." Ya shafa fuska yana lumshe mata ido yace."Muje mu kama daki zuwa gobe da safe sai na sallame ki." Ba tare da wata doguwar jayayya ba tabi bayanshi. As yabi bayan Wasila yana nema neman duniya bai ganta ba guri ne babba ga jama'a na shiga suna fita ya fita bakin titi ya jima a tsaye yana waige waige bai ganta ba, haka ya koma ciki domin daukar motarshi anan kira ya shigo wayarshi kan lokaci ya kusa da zasu zauna metting dole ya nufi government house din ba dan ransa yaso ba yaso ko yaya ne ya rage zafi da Wasila amma ya dauki alkawarin komai tsantsaninta sai ya rusa shirinta. Tana ganin futar motarsa ta fito daga inda ta 'buya babu shakka As so yake ya yaudareta ya rabata da budurcinta wanda da ta jima tana tattalinsa, tabbas zata janye jikinta dashi da lamuransa tunda ta lura shi baya abu dan Allah. Koda ta fito titin tsif! babu abun hawa na haya dama kuma ba kasafai a dai-dai ta sahu ke shigowa gurin ba saboda babban titi ne na masu hannu da shuni yawanci motocin gida sunfi karakaina a kan titin.....Tsoro yasa ta kasa tsaida motar kowa sai ta kama hanya ta dingi tafiya ga cokalelen takalmi a kafafunta. Tana daf da futa babban titi motar ta fito daga wani babban layi mai dauke da dogwayen gina gine, dole tasa ta ratse a gefe domin ta bawa mai motar hanya, haushi da takaici ya turnuke ta ganin yanda mai motar ke dallare mata fuska da hasken fitilar motar....Ta sanya hannunta ta kare fuskarta tana jan tsaki!!! Ahamdu dake gaban motar gabanshi ya fad'i Allah yasa dai idonshi ba gizo yake masa ba, sai da suka zo daf da ita ya tabbatar da zarginsa Itace! ma'kale a jikin bango tana jira su wuce! sai ya shiga tambayar kansa, Yarinyar nan daga ina take a cikin wannan daran? shin ita da waye? kuma meye ya fito da ita daga gida. Bashi da me bashi amsa dole sai ita, da sauri ya sanya Garba ya tsayar da motar ya bude motar da zama ya fito ya iske inda take ma'kure! *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *Free Pege19* Saboda yanayin hasken gurun ya sanya tun kafin ya karaso kusa da ita ta ganeshi gabanta ne yayi wata mummanar faduwa da azama! tayi kokarin barin gurin.....Taku biyu yayi ya cafki hannunta guda.....Cak! taja ta tsaya tana mai da nuffashi domin ganinsa ya sanya jikinta kyarma wanda shi kanshi sai da yaji a jikinsa sakamakon rike hannunta da yayi, Sai da ta dan samu nutsuwa sannan ta juyo fuska a had'e! Suka hada ido dashi yana tsaye shima tashi fuskar babu alamun wasa....Kafin tace"Komai ya mangantu.....'Karfe goma sha biyu na dare kina waje a matsayinki na 'ya mace mai daraja kin watsar da wannan 'kimar da Allah ya baki kin mai da kanki tamkar tunkiya kiyi nan kiyi can cikin dare saboda rashin sannin ciwon kai kin mai da kanki tamkar namiji namijin ma irin wanda bai san darajar kanshi ba." murmushi tayi mai ciwo tace." Idan hakane kai ma Ashe kana d'aya daga cikin jinsin irin mazan da ka fad'a yanzu, Kai ma me ya fito da kai da daddare idan ka yarda da kanka? kana kirana tinkiya kai kuma sai ka kira kanka da bunsur......! kamar ya sanan sunan da zata kirashi dashi yayi saurin kife ta da mari! jikinsa na kyarma! yace."Ahir!! d'inki ki kirani da wannan suna! na kira da tinkiya din domin sunan da ya dace a kira ki dashi kenan, dube ki don Allah wai ke kinyi kwalliya kina yawo sa'ko da loko kina rabawa jama'a jikinki a banza job wane wawa ya jaki ya jaki ki bishi saboda rashin martaba kai ya jama'a ba zasu kira ki da sunanan tinkinya ba."!? Wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubo mata a kumatu idan ta fahimci maganarsa anan shima yanayi mata kallon karuwa kenan? wai shin mai yasa mutane basa yi mata adalci ne a duniya ta tsani a kira ta da wannan suna, sunan tinkiya na nufin mace mara hankali mara ilimi mara nutsuwa da kamun kai....Tunda suke karawa da guy din bai ta'ba 'kona mata rai irin yau! ba su kansu hawayen dake zuba a fuskarta ta bata san sanda suka zuba ba, da budurcinta da komai yake kiranta da tunkiya.....Hannunta da cikin nasa ta fuxge! ta bar gurin a gaggauce!!! bayanta yabi ya sake ruke hannunta ta sanya karfi ta tureshi kuka take hai'kan! tsabar kalmar daya kira ta da ita tayi mata ciwo tana ji ma tamkar ta hadiyi zuciya ta mutu.......Yayi saurin tatar gabanta rai a bace yace."Idan baki tsaya ba wallahi yanzu a gurin nan zan tu'be ki na kwashi rabona duk da hakan ba halayyata bace zanyi miki hakane dan in nunawa duniya halinki....Gwara kawai ki tsaya ki daina sauri." Hawayen fuskarta ta goge tace"Kai baka isa ka tu'be ni ba wallahi sai dai na tu'beka! kuma sai nayi maka sintir! zaka san wanda ka mara." murmushi ya saki hakika dauriya da jarumatar yarinyar na burgeshi, yace."Idan kin isa ke mara kunya ce ki 'kara taku d'aya anan gurin wallahi sai na baki mamaki! sai na tu'beki! kuma na gudu da kayanki ki 'kara taku daya ki gani." Wasila ta kalli fuskarsa taga babu alamun wasa a ciki sai gabanta ya fadi tabbas zai aikata abunda ya fada bari kawai ta lallabashi su rabu lafiya amma sai ra rama abunda yayi mata. Tsayuwa ta gyara tace"Wai shin yanzu da ka tare min hanya me kake nufi dani.'" Yace."Abubuwan da nake nufi dake suna daya wa saboda haka shige muje ki shiga mota muje." Ta kalleshi she'keke! tana gyada kai! "Ko da kudi ba zan shiga motarka ba nasan idan na futa babban titi ba zan rasa abun hawa ba kawai ka fada mun dalilin da ya sanya ka tsare min hanya." "Kin san ke mai laifi ce a gurina ko? so bana son jayayya kiyi abunda nace dake idan ba hakaba zan kira Yarana a waya so zu su baki mamaki! duk yawansu sai sun kwanta dake sunyi miki fata fata!!!!!! Tsorata tayi dajin maganarsa mussaman da taga yayi kici kici da fuska yana kokarin dauko wayarsa,, sai ta sassauta murya a hankali tace" Dan Allah kar ka kira su muje motar nayi alkawarin kome kake so zanyi maka amma kar ka kira yaranka su wulakanta ni." Yace."Wuce muje." Gaba tayi da cokalalen takalminta har tana gord'ewa sai waiwaye take ko zata samu mafakar da zata arce babu gida gaba babu gida a baya.....Da kanshi ya bude mata mota ta shiga ya zauna kusa da ita fukarsa babu wasa, gabanta sai masifar faduwa yake shikkenan yau ta fada komar Ahamdu sai Allah kuma tsinewa babu irin wacce ba tayi wa As ba shine silar fitowarta da wannan daran da bai fito ba da tuni ta gida tare da mahaifiyarta da 'yar uwarta. 'Kasa tayi da kanta hawaye na d'iga ta dinga sanya gefan lifayar tana gogewa sam! ba taso ya ga gazawarta a kansa amma inaa ta kasa tsayar da hawayen dake zubar mata mutukar ta tuna kalmar da ya kira ta da ita sai taji zuciyarta ta karye *Tinkiya* wannan kalma tayi masifar ragargaxa mata jikinta da duk wani kuzarinta da kwanjinta a kanshi....... Gani tayi mai gadi na bude tangameman gate din gidanshi, tayi saurin dagowa tana kallonshi taga yayi masifar 'bata fuska, yana magana da securities din dake bakin gate din....Tsumu! tayi hankalinta a tashe kar dai guy nan ya kawo ta gidanshi ne domin ya keta mata haddi innalilihi wa ina ilahi raji'un! yanzu meye mafita.... Taga ya bude mota ya fita sai tayi yunkurin fitowa itama, da sauri ya mayar da murfin motar ya rufe da karfi dan har yana had'awa da hannunta, cije baki tayi tana duba ya tsanta, tunaninta kaf yanzu ya ta'alla'ka ne akan yanda za'ayi ta ku'butar da kanta daga hannunsa. Can ta hango sun nufi bakin gate tayi saurin mikewa kan site tana le'kansa taga yana magana da securities akwai ta zata sosai parking spece da kuma bakin gate din ba tajin abunda yake cewa amma yanda ta lura da fuskarsa babu wasa yana musu magana mai muhimanci.....Juyowa tayi ta fara kokarin bude motar gam! take da mukulli ko wane murfi a rufe.....Hawaye ya tsinke mata, Innalillhi wa'ina ilaihi raji'un! Sake mikewa tayi tana le'kensa, Can ta hangoshi ya durfafo inda take tayi saurin zaunawa! jikinta na kyarma, yana bud'e motar hankalinta a kai tayi wuf!! ta fito fit! har sai da ta tureshi yayi saurin tsayuwa cikin zafin nama ya cafki 'kugunta ya rike tam! ya had'e bayanta da 'kirjinsa! Jini hannunsa kan kirjinta ya sanya tayi masa wata wawar bangaza ta sanya tsinin takalminta ta daki gwiwarsa guda! yayi gaggawar juyo da ita mari ya kifa mata!!!!! ya rike fuskarta da hannuwansa suka tsirawa juna ido.....Numfashi take saukewa mai zafi !! tana hura hanci! ga idanunta yayi jawur! Tsananin tashin hankali da fargaba ya gani cikin 'kwayar idonta, Ya gyada kanshi cikin jajurcewa yace."Ki shiga taitayinki ki kuma nutsu wannan haukan da kikeyi babu inda zai kai ki a gurina muje ciki in fad'a miki wani abun al'ajabi."!! "Ba zan shiga gidanka saboda ni ba 'yar iska bace ka daukoni ne dan ka biya bukatarka ni nafi karfin ka idan kuma ka tsananta to za'ayi mutuwar kasko dani da kai a gidanan, dan nayi rantsuwa da Allah babu wani d'an iska da ya isa ya rabani da budurcina akan hakan zan iya aikata komai." Ya jima yana kallonta kafin yace."Ke! kina nufin kina sa budurci a yanzu, da har kike wani tada jijiyar wuya! okey to kar ki damu ba wannan bane manufata a kanki kawai dai yanzu na baki umarni kan ki nutsu kana kuma muje ciki na sanar miki da abun al'ajabin da ya faru dake." Taji wani irin shocking ya kama jikinta shin wai wannan wane irin abun al'ajabi yake so ya fad'a mata ne? Ji tayi wata jarumta tazo mata a take tace"Muje amma akwai sharad'i idan ka kusance ni sai nayi maka illah." Yace."Na yarda." Gaba tayi tana gurd'ewa ga lifayar tsabar wahala duk ta warware sai silmiyowa takeyi tana gyarawa gashin kanta duk ya baje a kafadarta ribbon din ya fad'i a bakin mota......Bayanta yake bi cikin nutsuwa yake 'kare mata kallo warwarewar lifayar ya sanya ya fahimci kayan dake jikinta t_shart ce mai karami hannu sai dogon wando na jins amma ya da'me ta d'am-d'am! ya fito mata da mazaunai tamkar suyi magana....Dauke kanshi kawai tayi yai saurin wuce ta yaje ya bud'e kofar palon....Yana tsaye ta 'karaso da hannu yayi mata alama ta shiga ta tsuguna tana kwance takalminta dake mai igiya ne... Nan ma kasa tsayuwa yayi saboda yanda ya hango brest dinta sun bullotso ta saman d'amammiyar rigar dake jikinta sai ya shige palon ya tsaya...Ta shiga ya mai da kofa ya rufe da key. Had'uwar palon da 'kayatuwarsa sam! bashi ne a gabanta ba burinta kawai ya fad'a mata abun al'ajabin ko ya nuna mata ta zuba masa furgitattun idanunta Cikin wani irin taku iske inda take tsaye ya zura hannunsa cikin aljihu dubu biyar d'in sadakinta ya zaro ya kama hannunta ya sanya mata kana ya kalleta ido da ido yace."Ri'ke sadakin auranki da kyau!! Yau! ni *Ahamdu Musa* na cika d'an halak na tashi daga sunan gwauro na 'yantu na cika cikakken namiji inda nayi tattaki 'kafa da 'kafa na iske har Garkin Gargo na d'aura aure da Wasilatu 'Yar gaske Kawunki Malam mai allo yace na baki sadakin ki a hannunki ki lissafa su dubu biyar ne."! Yana gama maganarshi ya sakar mata hannunta kud'in suka watse a kasan palon.....Bai damu ba ya nufi bedroom dinshi hankalinsa kwance.......Da wani irin mamaki take kallonsa har ya bude dakinsa ya shiga tana kallonsa tana jinn sautin miryarsa na amsa kuwwa a kunnanta *"Wannan shine sadakin auraki Ni Ahamdu Musa nayi tattaki kafa da kafa na iske garin Garko na daura aure da Wasilatu 'yar gaske na tashi daga sunan gwauro na 'yantu Kawun ki Malam mai allo yace na baki sadakin ki da hannuna."* Wannan maganganun kawai takeji a cikin kunnanta kamar yanzu yake fada mata idanunta tsaye a kofar dakinshi.......Kimanin minti goma tana tsaye a gurin tana jajanta maganar gani take ma kamar mafarki take sai da ta kai idanunta kan kudin da suke watse kasan kafet, sannan gabanta ta sake faduwa ta tsuguna kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta dinga daukar kudin tana hadawa guri guda tsaf! ta lissafa su dubu biyar....... *"Ni Wasilatu ni aka daurawa aure da sadaki dubu biyar sai kace bazawara!! Bazawarar ma mara gata da galihu tir'kashi!!!! A fusace! ta mike! ''Karye ne wallahi! Ni Wasilatu nafi karfin ayi min wannan wulakancin Ni za'a daurawa aure ban sani ba Wallahi wannan auran dashi da babu duk d'aya a gurina."!!! Sai ta nufi kofar dakin nasa gadan gadan!! hannunta rike da 'kudin sadakin auran na ta."* *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *NA SADAUKAR MUKU DA WANNAN PEGE 'DIN* Rahima Aliyu Hauwwa Saudia H.Rabi 'kofar bai Fatima Yakubu Nafisat Ahamad Zahra Kaduna Fatima Binta Jamila Abubukar Mum Basma Maimuna bichi Ummu Yusif Atou Tabalak Anty Zeey Kazaure Zainan Khabir Ishak Jamila Yusha'u JiddatulKhairi _*Kuna da yawa sosai masoya wanda baiji sunanshi ba afuwa zamu hadu a gaba ina mutukar alfahari daku masoya Ubangiji Allah ya 'kara 'kauna ta gaskiya*_ ~~~~~~~~~~~~~ *Free Pege20* Lest Free Pege A fusace! ta buga 'kofar d'akin ta shiga, yayi hanzarin juyowa jikinsa sanye da rigar wanka da alama yayi shiri tsaf wanka zai shiga dan yana daf da bakin toilet din....Idanunta a rufe ta durfafo inda yake tsaye yana kallonta ga mamakin sa sai yaga ta d'aga hannunta dake ri'ke da kud'in zata watsa masa yayi hanzarin ri'ke hannun! suka tsaya suna kallon junansu.....Sai yanzu ta lura da irin kayan dake jikinsa, rigar wanka ce mai bud'ad'addan gaba kuma bai daure ba ya sake ta faffad'an kirjinsa mai cike da yalwar gashi yana a bayyane kuma karamin wando ne a jikinsa wanda da ya d'ameshi. da sauri ta sunkuyar da kanta 'kas! gabanta na masifar fad'uwa Ganin yanda wandon jikinsa ya masifar matse shi ba ta ta'ba ganin zahirin namiji ba sai yau! Har yanzu hannunsa na rike da nata wanda kudin ke ciki yana watsa mata wani irin kallo yace."Kar ki kuskura kiyi min watsi da kudi a d'aki idan kikayi sai ranki ya 'baci! hakkin ki ne kije dasu duk wanda ki kaga damar bawa ki bashi wannan bai dami kowa ba." Hannunta ya saki ya kama hanya zai shiga toilet d'in! aikuwa ta watsar da kud'in kasan dakin tana fadin "Wallahi wannnan auran dashi da babu duk daya suke a gurina ka kwashi kudin sadakin ka bana sonka bana ra'ayin auran mutum irinka da har zakaje har mahaifata kasa a dauro maka aure dani to yanzu ba gobe ba sai ka sake ni dan wannan budurcin nawa na mai rabo ne." Da jarumta take maganarta kuma tsakaninta da Allah take....Ya juyo cikin wani irin yanayi yana bin kudin da ta watsar a 'kas! wato dai sai da ta watsar masa da kudi a d'aki saboda taurin kai!! Nufar ta yayi cikin tsanani na 'bacin rai!! Sosai ta tsorata! da ganin yanayinsa sai ta soma ja da baya yana sake tunkarar ta tana sake matsawa gabanta sai duka yake yana daka haka suka dinga yi har sai da suka dangane da jikin bango. (Garu) d'aga hannu yayi kamar zai mareta! sai tayi saurin kauda fuskarta ta sanya dukanin hannunwanta ta kare tana sakin 'karamin ihu!! Shiru taji ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi ta kafar hannunta yana tsaye daf da ita ya dafa hannunsa guda a jikin bango ya tokare ta sannan faffadan kirjinsa dake bud'e yana gogar hannayenta, 'Das!d'as gabanta yake fad'uwa lokaci guda ta rasa miyau! a bakinta ya bushe kamas!!! Sai zare ido takeyi wani irin tsoronsa ne ya shige ta mussaman yanda taga zahirin hallitarshi sai ta ganta wata 'yar ficika a tsakaninsa ya za tayi idan wannan 'katon mutumin ya hau ta duka. "Ashe rashin kunyarki ta banza ce! tunda har kika razana tin kafin nayi miki hukunci." Shiru ya dan yi yana kallonta yanda take kyarma! sai uban gumi take hadawa Murmushi ya saki mara sauti ya girgiza kansa kana yace." karki kuskura nayi sabo da dukan ki ko marin ki zaki sha wahala, aure ni nayi ra'ayin na aureki saboda na karya al'kadarinki kin shiga gidan redio kin zageni kin aibatani kinyi min kazafin na zina kawai saboda ki bata min suna a idon mutune to bukatarku bata biya har yanzu da mutuncina a idon mutane na aureki da mummunar niya ba zan munafurce ki ba amma kuma mutunci da 'kimar wannan dattijon ya sanya na janye kudirina a kanki! karyi tunanin ko zanyi wata mu'amular aure dake domin naji baki da wani zance da magana sai na budurci ki sani da budurcinki da babu duk daya suke a gurina domin bashi ne a gabana ba, zan killace a cikin gidana ne domin na taimake ki da wannan yawace yawacen da kikeyi kinga ke idan 'yar halak ce godiya ce zata biyo baya a tsakaninmu dalili kuwa na 'yan taki na aureki tare da killace ki guri guda, magana ta karshe da zanyi miki itace maza ki kwashe kudinki da kika watsar min 'kasan d'aki! ruwanki ne kiyi amfani dashi da kanki ruwanki ne ki bayar sadaka bai dami Ahamdu ba." Bakinta mutuwa yayi murus! sai dai Ubab hawayen dake ambaliya a fuskarta, tayi tayi ta d'ago fuskarta ta kasa saboda yanda taji duk wani alkadari nata ya karye amma Ahamdu yayi mata wulakancin da ba zata ta'ba mantawa dashi ba....Cikin tsawa yace."Kin kwashe kudin ko kuwa."! Hucin maganarshi ya daki fuskarta tunda har yanzu yana kusa da ita ta ina zata wuce ya babbake hanya.....Idonta ta zuba masa tana motsa baki! Ko kusa ko alama bata bashi tausayi ba sai ma wani irin tsanarta da yake ji, ya kauce daga jikinta yana nuna mata kudin da hannunsa.....Tsugunawa tayi ta dinga binsu daya bayan daya tana tsincewa tana sha'kar hanci ta gama ta mike tsaye ba tare da ta juyo ba......Tsaki yaja mai sauti ya wuce toilet abinsa. Yana shigewa toliet din ta fara dube dube a dakin kan mirror dinshi ta nufa ta hau duddubawa key take nema ba ta ganshi ba tayi d'age sosai tana lalube saman wardrobe dinshi, ganin tana wahala sai tayi nufin dauko drowar guda itama ta'ki daukuwa saboda yanayin katakon ba na wasa bane.....Da sauri ta bude wardrobe din tana dube dube can ta hango rigarshi da ya cire a rataye ta ciro tana zazzage ta babu komai a ciki sao gilashinsa da kuma carbinsa mai ma dannai.....Ta mayar da rigar a gaggauce! ta bude drowars ta fara dubawa nan taga tarin mukulai ba tare da 'bata lokaci ba ta d'aukesu ko rufe drowars din ba tayi ba ta fice daga dakin...Yaji lokacin da ta bude dakin ta futa sai jikinsa ya bashi a gaggauce ya cigaba da watsa ruwa a jikinsa ya dauro towel ya fito, nan yaga dakin a hargitse duk ta baza masa kaya....Ya fito palo da sauri, a take yaga kofar palo a bude bayan yasan ya rufe ta da key! Shaf ya manta towel ne a jikinsa da takalmin wanka ya fita a haka can ya hangota suna dambarwa da Masu gadi......Sosai ranshi yayi masifar 'baci! ganin yanda ta zakalkale tana musu masifa har da marin daya daga cikin yaranshi sai dungure masa kai take wai dole sai sun bude mata kofa ta fita!! Taku biyu yayi da niyar zuwa gurin towel dake kugunsa ya kwance nan ya tuna ashe daga wanka ya fito a gurguje ya koma ciki ya zura jallabiya ya fito, sai dai me!? 'Karamar 'kofa ya gani a bude Wasila ta shammace su ta fita.....Wasu daga cikinsu sun bi bayanta, Sauransu ya dinga zabgawa masifa kamar ya yari baki sai bashi hakuri sukeyi suna fadin"Wallahi shamtarsu tayi ta bude karamar kofa ta fita......Hadi ne ya paka mota a inda yake ya kar'bi key din motar rai a 'bace! ya shiga da gudu ya fice daga gidan.......Can ya hangota ta kusa fita daga Estate din tana wani irin gudu Su Garba na binta a baya....Yaji duk lamarin yarinyar ya fuce masa da kai wannnan zubda mutunci dame yayi kama, da ya sani ya shiga yi ace wannan ce matar auranka tana gudu maza na binta. Wani wawan burki! yaci a gabanta! Tsabar wuya da galabaita ya sanya ta zubewa a gurin tana mai da nuffashi!! Ya bude mota ya fito rai a 'bace! sai ta yunkura cikin zafin nama zata sake arcewa da azama! ya sanya mata kafarsa guda a tsakanin tata sai tayo kanshi zata fad'a! yayi saurin matsawa ta kirjinta ya daki jikin motar....Ta dago kafadunta tare da juyo da ita ba tare da 'bata lokaci ba ya kife ta da wani wawan mari! wanda sai da taga gilmawar taurari ta dinga jin dum!! dum!! a kunnenta....Luuuu!! tayi zata sake kifawa a jikinsa ya kauce! ta sake dukan motar a zabure!! ta bude idonta ta dinga ganin zatinsa dishi dishi a cikin idonta.....Kawai sai wasu lafiyayyun hawaye suka wanke mata fuska.....Motar ya bude ya tankad'ata ciki ya mayar da murfin ya rufe kana ya zagaya mazauninsa ya shiga yaja motar, Su Garba kuwa dama tuni sun juya..........Gate din a bude yake dan haka kawai sai ya shiga da motar duk suna tsaye ciro cirko ya tsai da motar ya tsaya yana musu fada da gargadi kan duk wanda yayi kuskuran sake barin ta ta futa daga gidan to a bakin aikinsa." Dukaninsu suka shiga bashi hakuri tsabar haushi bai ma tsaya ya sauraresu ba ya fuzgi motar a guje ya wuce. Yanayin parking ya fito hade da bude kofar da take tana kwance ruf da ciki kan site gashinta ya wargaje yayi buyaya lifayar ma ta cire dan saura kadan ta rabu da jikinta, Tsawa ya buga mata kan ta fito masa daga mota! shiru yayi ya sake kwatsa mata wata tsawar yaji shiru, sai da yayi magana sau biyar ba ta amsa ba, ya zura jikinsa cikin motar ya burkitota fuskarta ya tsirawa ido yana kallo....Idanunta a rufe ruf! dai-dai da gashin idon baya motsi! yaji faduwar gaba kadan ta kamashi Hannunsa ya dora a kirjinta minti biyu ya dauke! da sauri! ya kara hannunsa saitin hancinta nan ma yayi minti biyu babu alamun nuffashi a tare da ita....Babu shiri ya tattaro ta jikinsa ya taraiyaye ta daukar jarirai yayi mata ko motar bai rufe ba ya nufi cikin gidan da ita, hankalinsa a tashe. *_TO JAMA'A NAN NA KAWO 'KARSHEN FREE PEGE NA WANNAN LITTAFIN GA DUK MAI BUKATAR CIGABA DA KARANTAWA SAI YA DUBA BAYANAN DA NAYI A SAMA KAZO KA BIYA KUDINKA KA KARANTA DOMIN KAR AYI BABU KAI WANNAN LABARI DAI YANZU MA AKA FARA AKWAI TAFIYA A GABA WANNAN D'ANDANAN GISHIRI NE..........HAR KULLUM INA FAD'A CEWA KUD'IN KARATU KIKA BIYA BA NA MALLAKA BA IDAN KIN YARDA KIZO KI BIYA KI KARANTA IDAN BAKI YARDA DA WANNAN TSARIN BA TO DAN ALLAH KAR KIZO KI BIYA KI FUTAR MIN DA BOOK KI RUSA NI KIYI ZAMANKI NAGODE SANNAN DUK MAI BUKATAR KARANTA NOVLS DINA AKWAI COMPLETED KAN FARASHI MAI SAU'KI KAR KU MANTA DAI HAUSAWA NACEWA SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA_* 'WADANNAN SUNE LITTAFAN NAWA *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* *BABBAN YARO* *LADIDI KWADAGA* *MASHAHURI* *SADAUKI OMAR* *RUWAN DARE* *NI DA YAYA SADAM* *'YAR BANGAR SIYASA* Kar ku manta da cewar ni Binta Umar Abbale nice mamalakiyar wad'annan novels din.....Saboda haka ga duk wani mai bukatar ya karanta completed dinsu sai ya nemi numbar ta ya biya ya karanta hankali kwance, Ina kara tunasar daku cewar kada kuje ku biya wani ko wata kudin wannan novels din dana jera muku 'karya yake 'karya take zasu siyar muku da hakkin da bana su ba kumai ba zama lallai su baku complete ba shikkenan sunci kudinku a banza, hanya mafi sauki anan ita ce ku tuntu'be ta wannan numbars din nawa *08089965176* *07084653262* Masha Allah masoya sai naji ku🙋🏻‍♀️ *'YAR BANGAR SIYASA!!* 🌺 romantic love story🌺 *NA:* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *🌍Manazarta Writes asso* _'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~ *NA KUDI NE.......!* _Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_ *NA SADAUKAR MUKU DA WANNAN PEGE 'DIN* Rahima Aliyu Hauwwa Saudia H.Rabi 'kofar bai Fatima Yakubu Nafisat Ahamad Zahra Kaduna Fatima Binta Jamila Abubukar Mum Basma Maimuna bichi Ummu Yusif Atou Tabalak Anty Zeey Kazaure Zainan Khabir Ishak Jamila Yusha'u JiddatulKhairi _*Kuna da yawa sosai masoya wanda baiji sunanshi ba afuwa zamu hadu a gaba ina mutukar alfahari daku masoya Ubangiji Allah ya 'kara 'kauna ta gaskiya*_ ~~~~~~~~~~~~~ *Free Pege20* Lest Free Pege A fusace! ta buga 'kofar d'akin ta shiga, yayi hanzarin juyowa jikinsa sanye da rigar wanka da alama yayi shiri tsaf wanka zai shiga dan yana daf da bakin toilet din....Idanunta a rufe ta durfafo inda yake tsaye yana kallonta ga mamakin sa sai yaga ta d'aga hannunta dake ri'ke da kud'in zata watsa masa yayi hanzarin ri'ke hannun! suka tsaya suna kallon junansu.....Sai yanzu ta lura da irin kayan dake jikinsa, rigar wanka ce mai bud'ad'addan gaba kuma bai daure ba ya sake ta faffad'an kirjinsa mai cike da yalwar gashi yana a bayyane kuma karamin wando ne a jikinsa wanda da ya d'ameshi. da sauri ta sunkuyar da kanta 'kas! gabanta na masifar fad'uwa Ganin yanda wandon jikinsa ya masifar matse shi ba ta ta'ba ganin zahirin namiji ba sai yau! Har yanzu hannunsa na rike da nata wanda kudin ke ciki yana watsa mata wani irin kallo yace."Kar ki kuskura kiyi min watsi da kudi a d'aki idan kikayi sai ranki ya 'baci! hakkin ki ne kije dasu duk wanda ki kaga damar bawa ki bashi wannan bai dami kowa ba." Hannunta ya saki ya kama hanya zai shiga toilet d'in! aikuwa ta watsar da kud'in kasan dakin tana fadin "Wallahi wannnan auran dashi da babu duk daya suke a gurina ka kwashi kudin sadakin ka bana sonka bana ra'ayin auran mutum irinka da har zakaje har mahaifata kasa a dauro maka aure dani to yanzu ba gobe ba sai ka sake ni dan wannan budurcin nawa na mai rabo ne." Da jarumta take maganarta kuma tsakaninta da Allah take....Ya juyo cikin wani irin yanayi yana bin kudin da ta watsar a 'kas! wato dai sai da ta watsar masa da kudi a d'aki saboda taurin kai!! Nufar ta yayi cikin tsanani na 'bacin rai!! Sosai ta tsorata! da ganin yanayinsa sai ta soma ja da baya yana sake tunkarar ta tana sake matsawa gabanta sai duka yake yana daka haka suka dinga yi har sai da suka dangane da jikin bango. (Garu) d'aga hannu yayi kamar zai mareta! sai tayi saurin kauda fuskarta ta sanya dukanin hannunwanta ta kare tana sakin 'karamin ihu!! Shiru taji ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi ta kafar hannunta yana tsaye daf da ita ya dafa hannunsa guda a jikin bango ya tokare ta sannan faffadan kirjinsa dake bud'e yana gogar hannayenta, 'Das!d'as gabanta yake fad'uwa lokaci guda ta rasa miyau! a bakinta ya bushe kamas!!! Sai zare ido takeyi wani irin tsoronsa ne ya shige ta mussaman yanda taga zahirin hallitarshi sai ta ganta wata 'yar ficika a tsakaninsa ya za tayi idan wannan 'katon mutumin ya hau ta duka. "Ashe rashin kunyarki ta banza ce! tunda har kika razana tin kafin nayi miki hukunci." Shiru ya dan yi yana kallonta yanda take kyarma! sai uban gumi take hadawa Murmushi ya saki mara sauti ya girgiza kansa kana yace." karki kuskura nayi sabo da dukan ki ko marin ki zaki sha wahala, aure ni nayi ra'ayin na aureki saboda na karya al'kadarinki kin shiga gidan redio kin zageni kin aibatani kinyi min kazafin na zina kawai saboda ki bata min suna a idon mutune to bukatarku bata biya har yanzu da mutuncina a idon mutane na aureki da mummunar niya ba zan munafurce ki ba amma kuma mutunci da 'kimar wannan dattijon ya sanya na janye kudirina a kanki! karyi tunanin ko zanyi wata mu'amular aure dake domin naji baki da wani zance da magana sai na budurci ki sani da budurcinki da babu duk daya suke a gurina domin bashi ne a gabana ba, zan killace a cikin gidana ne domin na taimake ki da wannan yawace yawacen da kikeyi kinga ke idan 'yar halak ce godiya ce zata biyo baya a tsakaninmu dalili kuwa na 'yan taki na aureki tare da killace ki guri guda, magana ta karshe da zanyi miki itace maza ki kwashe kudinki da kika watsar min 'kasan d'aki! ruwanki ne kiyi amfani dashi da kanki ruwanki ne ki bayar sadaka bai dami Ahamdu ba." Bakinta mutuwa yayi murus! sai dai Ubab hawayen dake ambaliya a fuskarta, tayi tayi ta d'ago fuskarta ta kasa saboda yanda taji duk wani alkadari nata ya karye amma Ahamdu yayi mata wulakancin da ba zata ta'ba mantawa dashi ba....Cikin tsawa yace."Kin kwashe kudin ko kuwa."! Hucin maganarshi ya daki fuskarta tunda har yanzu yana kusa da ita ta ina zata wuce ya babbake hanya.....Idonta ta zuba masa tana motsa baki! Ko kusa ko alama bata bashi tausayi ba sai ma wani irin tsanarta da yake ji, ya kauce daga jikinta yana nuna mata kudin da hannunsa.....Tsugunawa tayi ta dinga binsu daya bayan daya tana tsincewa tana sha'kar hanci ta gama ta mike tsaye ba tare da ta juyo ba......Tsaki yaja mai sauti ya wuce toilet abinsa. Yana shigewa toliet din ta fara dube dube a dakin kan mirror dinshi ta nufa ta hau duddubawa key take nema ba ta ganshi ba tayi d'age sosai tana lalube saman wardrobe dinshi, ganin tana wahala sai tayi nufin dauko drowar guda itama ta'ki daukuwa saboda yanayin katakon ba na wasa bane.....Da sauri ta bude wardrobe din tana dube dube can ta hango rigarshi da ya cire a rataye ta ciro tana zazzage ta babu komai a ciki sao gilashinsa da kuma carbinsa mai ma dannai.....Ta mayar da rigar a gaggauce! ta bude drowars ta fara dubawa nan taga tarin mukulai ba tare da 'bata lokaci ba ta d'aukesu ko rufe drowars din ba tayi ba ta fice daga dakin...Yaji lokacin da ta bude dakin ta futa sai jikinsa ya bashi a gaggauce ya cigaba da watsa ruwa a jikinsa ya dauro towel ya fito, nan yaga dakin a hargitse duk ta baza masa kaya....Ya fito palo da sauri, a take yaga kofar palo a bude bayan yasan ya rufe ta da key! Shaf ya manta towel ne a jikinsa da takalmin wanka ya fita a haka can ya hangota suna dambarwa da Masu gadi......Sosai ranshi yayi masifar 'baci! ganin yanda ta zakalkale tana musu masifa har da marin daya daga cikin yaranshi sai dungure masa kai take wai dole sai sun bude mata kofa ta fita!! Taku biyu yayi da niyar zuwa gurin towel dake kugunsa ya kwance nan ya tuna ashe daga wanka ya fito a gurguje ya koma ciki ya zura jallabiya ya fito, sai dai me!? 'Karamar 'kofa ya gani a bude Wasila ta shammace su ta fita.....Wasu daga cikinsu sun bi bayanta, Sauransu ya dinga zabgawa masifa kamar ya yari baki sai bashi hakuri sukeyi suna fadin"Wallahi shamtarsu tayi ta bude karamar kofa ta fita......Hadi ne ya paka mota a inda yake ya kar'bi key din motar rai a 'bace! ya shiga da gudu ya fice daga gidan.......Can ya hangota ta kusa fita daga Estate din tana wani irin gudu Su Garba na binta a baya....Yaji duk lamarin yarinyar ya fuce masa da kai wannnan zubda mutunci dame yayi kama, da ya sani ya shiga yi ace wannan ce matar auranka tana gudu maza na binta. Wani wawan burki! yaci a gabanta! Tsabar wuya da galabaita ya sanya ta zubewa a gurin tana mai da nuffashi!! Ya bude mota ya fito rai a 'bace! sai ta yunkura cikin zafin nama zata sake arcewa da azama! ya sanya mata kafarsa guda a tsakanin tata sai tayo kanshi zata fad'a! yayi saurin matsawa ta kirjinta ya daki jikin motar....Ta dago kafadunta tare da juyo da ita ba tare da 'bata lokaci ba ya kife ta da wani wawan mari! wanda sai da taga gilmawar taurari ta dinga jin dum!! dum!! a kunnenta....Luuuu!! tayi zata sake kifawa a jikinsa ya kauce! ta sake dukan motar a zabure!! ta bude idonta ta dinga ganin zatinsa dishi dishi a cikin idonta.....Kawai sai wasu lafiyayyun hawaye suka wanke mata fuska.....Motar ya bude ya tankad'ata ciki ya mayar da murfin ya rufe kana ya zagaya mazauninsa ya shiga yaja motar, Su Garba kuwa dama tuni sun juya..........Gate din a bude yake dan haka kawai sai ya shiga da motar duk suna tsaye ciro cirko ya tsai da motar ya tsaya yana musu fada da gargadi kan duk wanda yayi kuskuran sake barin ta ta futa daga gidan to a bakin aikinsa." Dukaninsu suka shiga bashi hakuri tsabar haushi bai ma tsaya ya sauraresu ba ya fuzgi motar a guje ya wuce. Yanayin parking ya fito hade da bude kofar da take tana kwance ruf da ciki kan site gashinta ya wargaje yayi buyaya lifayar ma ta cire dan saura kadan ta rabu da jikinta, Tsawa ya buga mata kan ta fito masa daga mota! shiru yayi ya sake kwatsa mata wata tsawar yaji shiru, sai da yayi magana sau biyar ba ta amsa ba, ya zura jikinsa cikin motar ya burkitota fuskarta ya tsirawa ido yana kallo....Idanunta a rufe ruf! dai-dai da gashin idon baya motsi! yaji faduwar gaba kadan ta kamashi Hannunsa ya dora a kirjinta minti biyu ya dauke! da sauri! ya kara hannunsa saitin hancinta nan ma yayi minti biyu babu alamun nuffashi a tare da ita....Babu shiri ya tattaro ta jikinsa ya taraiyaye ta daukar jarirai yayi mata ko motar bai rufe ba ya nufi cikin gidan da ita, hankalinsa a tashe. *_TO JAMA'A NAN NA KAWO 'KARSHEN FREE PEGE NA WANNAN LITTAFIN GA DUK MAI BUKATAR CIGABA DA KARANTAWA SAI YA DUBA BAYANAN DA NAYI A SAMA KAZO KA BIYA KUDINKA KA KARANTA DOMIN KAR AYI BABU KAI WANNAN LABARI DAI YANZU MA AKA FARA AKWAI TAFIYA A GABA WANNAN D'ANDANAN GISHIRI NE..........HAR KULLUM INA FAD'A CEWA KUD'IN KARATU KIKA BIYA BA NA MALLAKA BA IDAN KIN YARDA KIZO KI BIYA KI KARANTA IDAN BAKI YARDA DA WANNAN TSARIN BA TO DAN ALLAH KAR KIZO KI BIYA KI FUTAR MIN DA BOOK KI RUSA NI KIYI ZAMANKI NAGODE SANNAN DUK MAI BUKATAR KARANTA NOVLS DINA AKWAI COMPLETED KAN FARASHI MAI SAU'KI KAR KU MANTA DAI HAUSAWA NACEWA SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA_* 'WADANNAN SUNE LITTAFAN NAWA *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* *BABBAN YARO* *LADIDI KWADAGA* *MASHAHURI* *SADAUKI OMAR* *RUWAN DARE* *NI DA YAYA SADAM* *'YAR BANGAR SIYASA* Kar ku manta da cewar ni Binta Umar Abbale nice mamalakiyar wad'annan novels din.....Saboda haka ga duk wani mai bukatar ya karanta completed dinsu sai ya nemi numbar ta ya biya ya karanta hankali kwance, Ina kara tunasar daku cewar kada kuje ku biya wani ko wata kudin wannan novels din dana jera muku 'karya yake 'karya take zasu siyar muku da hakkin da bana su ba kumai ba zama lallai su baku complete ba shikkenan sunci kudinku a banza, hanya mafi sauki anan ita ce ku tuntu'be ta wannan numbars din nawa *08089965176* *07084653262* Masha Allah masoya sai naji ku🙋🏻‍♀️ [07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr bngr Sys. *21* Kan makeken bed dinshi ya shimfidata a gaggauce ya bude ma dai-dai cin firjin dake gefan bed din ya dauko goran ruwa mai sanyi ya bude murfin ya tsiyaya a hannushi ya soma yarfa ma a fuska, sai da yayi haka sau uku tukkuna ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya numfashinta ya dawo amma kuma idanunta a rufe ruf sai dai gashin idanunta dake motsi.....Tsayuwa yayi a kanta yana me 'karewa fuskarta kallo, Tunda yake da yarinyar bai ta'ba tsayuwa ya kare mata kallo ba irin yau! tana da masifar kyau! wanda sai ka dade kana kallonta zaka fahimta babu abunda yafi tafiya da hankalinsa irin karamin bakinta mai dan tudun le'be dai-dai sumba, bai san sanda ya tsotsi leb'anshi ba ya dan lumshe idonsa tare da sake budesu a kanta, karaf! suka hada ido lokacin ta bude nata idon yayin saurin dauke kansa yana dan ja baya daga kusa da ita.....Cikinta ta rike da hannuwanta tana rintse ido hawaye ya soma shatata! "Wayyo cikina wayyo cikina! wayyo cikina."!!!! Abunda take ta fad'a kenan tana matagugu kan bed din......Sai ya tsinci kanshi da kid'imewa ya zauna kusa da ita yana kokarin rike hannunta ta fuzge! da 'karfi! tana cigaba da murkususu da kiran cikinta.....Hayewa yayi bed din ba tare da ya sani ba ya rirrike ta jikinsa sai kyarma! yake " Menene! ina ne yake miki ciwo sannu daina kuka ko kin bugu ne."? Duka ya jero mata wannan tambayar lokaci guda.....Shiru tayi masa ta sane ta dinga kwanciya a jikinsa tana mutsika masa jikinta anashi tana kuka da kiran cikinta......Bai san sanda ya zura hannunsa cikin rigarta ba yana shafa kasan mararta muryarshi sanyi kalau! yake magana "Sannu daina kuka bari na duba miki magani ina kin buga gurin da jikin mota dole yayi miki ciwo mybe ma yunwa kikeji ko."? Ba tace komai ba sai aukin tureshi da takeyi daga jikinta yana sake rirriketa shi duk a tunaninsa da gaske take cikinta ciwo yake.....Ya mike da sauri yans fad'in" Bari na duba miki magani dare yayi yanzu da na kaiki an duba ki.''' Yana fita taja tsaki ta mike da azama! taje ta rufe kofar dakin tabar key din a jiki.....Komawa tayi ta kwanta tana sa'ka wacce zata fisheta. Ya dawo dakin hannunsa rike da maganin ciwon ciki duk ya had'a uban gumi yana jan kofar yaji a kulle gam! gam!! Turus yayi da maganin a hannunsa yana tunani Babu shakka yarinyar nan yaudararsa tayi.....handle din ya sake murdawa yaji a rufe gam! gashi bedroom dinshi ne duk wasu abubuwan bukatunsa na ciki.....Wato tana so yayi mata magiya ta bude kofar shi kuma ya dauki alkawari kan sai dai ta gaji dan karan kanta ta bude tunda ya gane manufarta.....Wani bedroom din ya nufa ranshi a 'bace! amma yarinyar ta shammace shi gashi wayoyinsa na dakin hade da sauran makullan gidan.....Idanunsa suka sauka kan key din dake jikin kofar dakin da yake ciki....Da sauri ya mike ya isa gurin ya zare key din ya nufi dakin....Koda ya zura key din sai yaki shiga yayi yayi nan ya fahimci tabar key din a jiki. Ya juyo yana girgiza kai agogon bango ya kalla karfe daya na dare har da wani abu yarinyar nan ta hanashi bacci.....Idanunsa ne suka sauka kan pose dinta dake can bakin kofa yayi saurin isa inda take ya dauka tare da zama kan kujera yana budewa.....Wayarta babba da karama ce a ciki sai turaranta da wani zobe na gold a cikin gidanshi sai 'yan kudinta wanda basu wuce dubu takwas ba zuwa goma....Ya kunna wayar yana dube dube a ciki. Tana kwance ta 'kurawa cilling ido tana tunanin yanda za'ayi ta kubutar da kanta daga hannun Ahamdu, ta mike zaune da sauri tana dube dube! sai yanzu ta tuna da pose dinta....Tsaye ta mike lifayar jikinta na hard'e tayi gaggawar cireta ta jefar a gurin babu ruwanta da yanayin kayan dake jikinta ta durfafi kofar futa.....Har ta murda kofar zata futa sai kuma ta fasa tsoro takeji kar ya ritsata ta k sanya kunnanta jikin kofar wai ko za taji alamun motsi taji tsit! a hankali ta murza key din ta ja kofar ta bude.......Yana zaune kasan kafet tsakanin kujeru shine dalilin da ya sanya ba ta ganshi ba sai ta fara dube dube a palon....Ya zuba mata idanunsa yana kallonta tar cikin jan 'kwan dake palon mai hasken tsiya.....Can yaga ta nufi bakin kofar futa domin anan take tunanin ta yar da Pose din nata....Ya mike a hankali ya iske inda take hannunsa rike da pose din nata....Tana juyowa suka buga karo goshinta ne ya daki kirjinsa......Tayi masifar razana!!! da sauri tayi nufi guduwa ya tare ta tare da matseta a jikin labule......." 'Kas tayi da kanta kunya ta isheta sai yanzu ta fahimci a yanda ta fito tama manta shaf da kananun kayane a jikinta. "Kallonta kawai yake yi ya ma rasa abunda zai ce mata sai bin sasan jikinta yake da kallo yana ayyana abubuwa da dama a kanta. Pose din dake hannunshi ta zubawa ido....Ya dage mata gira tare da fad'in" Kin bude kofa ne sabida kizo ki dauki jakarki ko."? Tayi shiru yace."Kin yaudareni da ciwon ciki kin kulle min daki....Daga taimako sai sharri ya biyo baya kinga dake bani da alhaki a kanki da kanki kin bude kofar wai ke me wayo ko? Okey jakarki gata a hannunta zan baki abarka amma zan dauki abu biyu a ciki." Hannu ta kai da sauri zata fuzge! yayi sama da jakar yana kallonta sai d'age! takeyi Yace."Ki daina wani wahalar da kanki Ba komai zan dauka ba a ciki illah wayoyinki dukaninsu babu ke babu amfani da waya sai kinyi hankali." Ido ta zare! hannunta na kyarma sai rirrike hannunsa takeyi tana so ta fuzgo pose din....Dariya ta bashi ganin yand ta dage tana d'age! 'kafafu Ya d'an ture ta daga jikinsa yana matsawa, Biyo shi tayi muryarta na rawa "Allah sai ka bani waya ta." Abunda take fada kenan tana rirrike masa riga....Ya 'bata fuska da fad'in"Idan ba ki daina tatta'ba min jiki ba sai na 'bata miki " Wallahi kinji na rantse ke da wayar nan har abadah sai nayi niyya nan gaba na yarda da hankalin ki sannan zan yarda ki rike waya." Dajin wannan magana tashi sai ta fashe da kuka" Wallahi ban yarda ba haka kawai zaka takura min ka shiga rayuwa ta kace ba zan rike waya ba, Idan ka cuzguwa rayuwata nima sai na cuzguna maka kuma na fada maka wannan auran dashi da babu duk daya suke a gurina Gwara kawai ka sallame ni naje na cigaba da harkokina." Ko kallonta baiyi ba ya cire mata agogonta da turaranta ya ajiye mata kan kujera ya nufu bedroom dinshi yana fadin"Wahala ce bata isheki ba yarinya sai kiyi tayi ke kadai, Ahamdu bashi da lokacin ki." Yana shiga dakin ya murza key ta tsaya jikin kofar tana bugawa ya share ta kawai ya kwanta bed din shi tare da rufe ido bacci yake ji sosai bayan haka kuma ga gajiya ta dabaibaye shi......Tun yana jin bugun kofarta sama-sama har ya daina ji bacci yaci karfinsa.......Itama da ta gaji da dukan kofar sai ta silale kofar dakin tana kuka da kiran sunan Allah shiru palon tsoro da farga duk ya isheta haka dai tayi kwance bakin kofar dakin ga sanyi Ac yayi yawa a palon tsoro ya hanata taje ta rage, Yanda taga rana haka taga dare domin a kunnanta aka soma kiran assalatu. Kika futa da book din nan na barki da Allah kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr bngr Sys *22* Yana fitowa da shirin zuwa masalaci yaci tuntube da ita a bakin 'kofa yayi saurin matsawa yana dan haske ta da wayarshi, ta bude idanunta da suka ci kuka suka 'koshi ta zuba a kanshi....Wani irin mugun haushinsa da tsanarsa ne ya kamata haka kawai ya daukota ya rufe a gida yana azabtar da ita, Da sauri ta mike tsaye! yayi saurin kaucewa ya bata hanya ya dauka dakin zata shige sai yaga tayi kansa ta cikwokwiye shi tana kuka." Ka dauke ni ka mayar dani inda ka dauko ni ba zan iya wannan rayuwar ba bana sonka kan me yasa zakaje ka sanya a daura maka aure dani ai wannan zalinci ne, Wallahi gwara na kashe kaina kan in zauna da kai na tsaneka." kuka take hai'kan! tana sake rike masa riga sai shigewa jikinsa takeyi gashi ya dauro alwala. Yanda take gunjin kuka ya nuna masa da gaske takeyi abunda take fada har cikin ranta yake......Sai yaji rashin dadin hakan ranshi a bace ya ture ta daga jikinshi ya bar gurin da sauri! ta kuma mikewa a guje ta cimma sa ta baya ta rikeshi tam ta zagaye 'kugunsa da hannuwanta kirjinta na gogan bayanshi.....A zabure! ya juyo ya hankade ta hade da kifa mata mari! da hannu ya nuna ta "Kika sake kika 'kara ta'bani sai ranki ya 'baci! wallahi ba zan sake ki ba za kiyi ta zama a cikin kunci da bacin rai! ke da kin dauka nima sonki ne? Allah ya sawake na fada miki domin na karya alkadarinki yasa na aure ki shashasha kawai."! Juyawa yayi ya shige dakin....A gurguje ya sake sabuwar alwala yana jan tsaki ko yaya ta ra'bi jikinsa sai yaji sauyi a tare dashi abinda bai taba faruwa ba dashi.....Tana durkushe tsakiyar palon ya fito ko kallonta baiyi ba ya fice! yaji masifar haushin cewar da tayi bata sonsa yanzu ya soma zama da ita duk dan ya kuntatawa rayuwarta. Can gidan kuwa Uwani da Rashida na ganin sha biyu na dare ta wuce sai suka hakura da jiran ta suka kwanta ba tare da wata damuwa ba saboda sun san dama ta saba irin wannan tafiyar wani sa'in ta kwana wani sa'in kuma ta dawo.......Gashi Rashida ta kira wayarta tana shiga bata dauka ba sai tayi zargin ko tana tare da mutane ne dalili kenan da ya sanya suka kwanta ba tare da sunsa wata fargaba ba a cikin ransu. Bai jima da futa ba ta mike da azama! ta shiga dakin nasa nan idanunta suka sauka kan wayoyinta dake zube kan bed kusa da inda ya kwanta taga har da babbar wayarshi ma....Da sauri ta dauki babbar wayar ta tana duba contec numbar As take nema.....Sai taga ba kwata kwata babu sim card a wayar tayi saurin budewa wayar tana dubawa wai ko gocewa yayi taga duk babu, hannu na rawa ta dauki karamar ma taga itama ya cire sim card din gashi duka kan wayoyin babu numbar kowa ziro take........Hankali a tashe ta zube kan gadon tana rike kai! Wannan guy ya kassara ni! Innalilihi wa'ina ilahi raji'un! abunda take iya fada kenan jikinta na kyarma! babbar wayarshi ta kaiwa raruma hannu na rawa ta bud'e duka ta zare sim card din dake ciki ta zura cikin birziyarta rufe wayar tayi ta nemi guri ta zauna kan stoll tana jiran shigowarsa kwata kwata tunaninta ma baya kan ibadah burinta ta kubutar da kanta. Tananan zaune ya shigo dakin...Kallo guda yayi mata ya ga alamun ba tayi alwala ba ballanta tayi sallah! Ya sha kunu tare da fad'in"Tashi kije kiyi sallah."! Ba tayi masa musu ba ta mike yabi bayanta da kallo tana muskuta d'uwawu cikin damammen wandonta da sauri ya kauda kai yana fadin"Mara kunyar 'karya." Sarai taji shi girgiza kai tayi tace"Wallahi kome za'ayi ba zan bayar da sim card din nan ba nima sai an bani nawa. Sabon bursh ta bude ta matsa man goge baki a kai ta wanke bakinta tas ta dauro alwala ta fito.....Lifayar ta ta hango can karshen gadonshi ta haura kan bed din yana kwance yayi saurin gyarawa ganin kamar zata fado kansa, ba tare da ta damu ba ta dauko ta nad'a a jikinta ta nemi gefen kafet ta tada sallah! Yana kwance yana kallonta har ta tayar da sallahr. Hannu ya kai ya dauki wayarshi yana dan dubawa sai yaga babu sim card ya bude wayar yaga babu ajiye ta yayi ya dauki karamar ita ya bude yaga ta cire! Murmushi yayi......."Ke! waye ya baki izinin daukar min waya kiyi min bunkice."? Kai tsaye tace"Nima waye yace ka cire min sim card din waya ta ina ruwanka da kaya dukanin sirrina yana waya ta ka duba min ni banyi maka bunkice a waya ba kawai na cire sim card ne sai ka bani nawa sai na baka." Mikewa yayi zaune...sai ta zabura! ta matsa gefe da sauri! Hannu ya mika mata "bani Sim card dina tun muna shaida juna dake." "Allah sai ka bani nawa zan baka." Tafada cikin dakewa da jajurcewa."! "Nayi bunkice jiya a wayarki naga komai a ciki da irin mutanan da kike mu'amula dasu dalili kenan da ya sanya na cire sim card din, da da yanzu ba daya bane kina da aure yanzu ba kowa ya kamata kiyi mu'amula dasu ba sanna duk mutanan da naga numbarsu a wayarki basu da kirki babu wanda ban sani ba a cikinsu, ga yanayin yanda kika dauki wannan auran da rashin kima kina iya cigaba da mu'amula dasu dalili kenan da ya sanya na zare sim card din wayoyinki......Su kansu wayoyin anjima kadan zan bada kyautarsu ga mabu'kata." Ya kare maganarshi cike da rashin wasa. "Ni wayoyi basu ne damuwa ta ba kawai ka bani sim card dina sunfi muhimanci a gurina idan kuma kace ba zaka bayar ba to kai ma naka sun mula." Ya dan tsira mata idonshi yana kallo, kimanin minti biyu ya mike! Zabura tayi! Bai ko kalleta ba ya kwashi wayoyinta ya fita dasu a hannunsa.....Ajiyar zuciya ta sauke! ta rasa me yasa take jin tsoronsa duk lokacin da zai tunkareta....Tananan tsaye ya shigo dakin taga ya bude wardrobe din shi short nickar ya dauki da wata t_shart mai karamin hannu ya sanya a jikinsa ta matse shi sosai duk wasu hallitunsa suka bayyana....Ya zauna gefan bed yana kallonta, saurin sunkuyar da kanta tayi Yace."Mara kunya zo ki bani sim card dina zanyi kiran waya ko bakya ji." 'Ki tayi! Yace."Idan nazo nan fa ba zakiji dadi ba. "Nifa ba zan bayar ba sai ka bani nawa." Tafada muryarta na rawa ganinshi a haka ya sanya mata wani irin shau'ki wanda bata ta'ba shiga cikinsa ba sai taji tana sha'awar taji ta kwance cikin fafaffadan kirjinsa....Idonta lumshe! wanda shi kuma a lokacin ya mike ya iske inda take tsaye sai hucin numfashinsa taji! Tana bude ido ta ganshi daf da ita ya babbake gurin ko kyallinta baka gani ya rufe ta ruf a jikin bango (garu) Kauda fuskarta ta shiga yi ya sanya hannu yana juyo da fuskar tana sauke kauda fuskarta gabanta sai faduwa yake!!! Cikin hosky voice yace."Ina kika kai min sim card."!? Shiru tayi masa....Ya sanya hannunwansa ya kama hannunta yana dubawa. bude masa tafikan hannayen tayi ya laluba tsaf babu! Ha'bar ta ya d'ago ya tsurawa le'bunanta ido....Ta fuzge fuskarta daga hannunshi Yace."Ke! zafin kai! zaki nuna min ko."? Ta sanya hannu ta ture kirjinsa da fadin"Ka dauko min nawa sai na baka naka." Saukar hannunsa taji kan nonowanta! Ta 'kwallara 'kara! jikinta na makyarkyata! sam ba tayi tsammani ba!!! Ya d'an 'bata fuska kad'an "Meye haka."? Yafada yana kallon 'kwayar idonta. Shiru tayi tana so ta gudu ya sake matse ta da bango " Idan baki fito min da sim ba zanyi miki tsirara inyi miki sintir duk inda sim card dina yake sai na gani." ''Nima ka dauko min nawa." Tafada murya na rawa "Taurin kai ne dake Na fada miki dalilina amma tunda kin fiso nayi miki sintir irin naku na 'yan jagaliya to bari kiga." Da sauri ta buge hannunsa da ya dora kan blet din da ta matse 'kungunta dashi!! ya sake mai da hannunsa gurun fuzga daya yayi wa blet din sai gashi a hannunsa.....Ihun! hauka take masa tana tutture shi.....Ya 'bata fuska sosai da hannu daya ya hade dukanin hannuwanta ya rike ya daga sama ya kalleta ta kalleshi taga ya hade rai! sai hawaye ya wanke mata fuska da alama dai guy nan sintir din zai mata!!! "Ki daina 'bata hawayen ki a banza na fad'a miki ko a cikin wandonki kika 'boye min sim card sai na ciro kaya na." Yana gama maganarshi ya fara kokarin zare mata dogon wandon jins din dake jikinta.....Kafafunta ta sanya ta dinga harbinsa dasu tana bugunsa ko kallonta baiyi ba sai da ya zare mata wandon tayi saura daga ita sai pant! Kuka take tana masa Allah ya isa! Ya kalleta da jan ido "Kar ki 'kara yi min Allah ya isa."! babu wasa yayi maganar tace" To nima ka daina cire min wando wannan ai wulakanci ne." Yace."Ke! kika so a wulakanta ki." Hannu ya sa xai zare pant din! Sai ta kwala kara ta lauye ta lanjare! ta kanannad'e jikinta a jikinsa tana masa magiya! "Tsaya in dauko maka kar ka cire min wando! dan girman Allah ka tsaya kar ka tozartani!." Dariya yake so yayi amma ya dake! baiyi ba yace."Oya! maza dauko min." Yafada yana sakin ta. Gefe guda ta matsa tana nishi da aika masa da harara! yana kallonta bai ce komai ba sai da ta gama hararasa sannan ta zura hannu cikin rigar ta ta fara laluben sim card din......."Okey! nan kika boye ashe." Yafada yana bin nonowan nata da kallo. Banza tayi masa ta cigaba da lalube Yace."Bari kiga yanda za'ayi ki daina wani 'batawa kanki lokaci." Kafin tayi aune taji shi a jikinta ya sanya hannusa daya ra kasan rigar yana lalubawa! Tsabar yanda yake lalube mata nono sai da ya balle mari'kin bireziyar sai cud'a nonowan yake da hannunsa guda, kamar jaraba ita kuma ta kasa hanashi ji take tsigar jikinta na tashi nipples dinta na wani irin mikewa suna kaikayi sai taji kamar sosa mata yake Cikin wata kasalalliyar murya yace."Wai ina yake ne umhum? ko dai sai dai anyi sintir din! Bakinta ya mutu murus! sai dai ido da take kallonshi dasu, Ya riga ya d'imauce dan yanda yaji yana lugwigwita brest din a hannunsa so kawai yake yaga yayi tozali dasu a idonsa ya kama ta ya matse tsam! a jikinsa! ya dinga shafa bayanta da hannayensa dake cikin rigarta ya samu nasarar zare breziyar ya ciro ta ya yar ya gurun sai yaga nonowan sun sake masa girma a ido, tana kallonsa ya lumshe idonsa yana sakin zazzafar ajiyar zuciya bai ta'ba tsammanin shi cikakken mai lafiya ne sai yau!!!! Ganin yanda jikinsa ke kyarma! yasa ta dawo hayyancin ta tabi brexiyar ta dake kasa da kallo ta dawo da hankalinta kansa yana ta kallon kirjinta ture shi tayi dake jiki nasa ya shika sai ta samu nasar futa daga tsakaninsa ta dauki breziyar dake yashe a kasa ta zazzge sim card din suka fad'o kasa. Futa tayi daga d'akin hannunta rike da breziyar ta zauna daya daga cikin kujerun palon tana rintse idonta har yanzu bata dawo dai-dai ba tana tajin wani iri a jikinta ga nippls dinta ya dame ta da 'kyaikyayi tunani takeyi ya akayi har ta sake ya cire mata bireziya ya lugwigwita mata nono? Tsaki! taja "Amma mutumin nan ya shammace ni." Tana futa daga d'akin ya shafa kanshi har yanzu yana jin wani irin shauki a tattare dashi shauki da sha'awa irin wacce bai taba ji ba, Ya dauki sim card dinshi ya nemi gefan bed ya zauna ya sanyawa wayarshi......Khalifa ya kira suka gaisa Khalifa yace."Nayi ta kiran wayar ka bata shiga." Yace."Yanzu na kunna zaka shigo ko."? Yace."Kai da kake da amarya me zan zo nayi maka." Yace."Kai kyale amaryar nan dan Allah kawai ka shigo akwai shawawarin da zamuyi." Khalifa yace."Sai yamma zan shigo." Yace."Okey sai ka shigo." Numbar Garba ya kira.....Palo ya fito ya zauna kan kujera suna waya da Garba Yace."Duk ka had'o min kafatanin ma'aikatan gidanan." Garba Yace.",Angama Yallabai." Ya kashe Wayar yana kallonta idanunta sunyi Ja! Tsabar kuka da Halin sha'awar da take ciki a halin yanzu wanda ta kasa gane me yake damunta san samu ace har yanzu yana matsa mata nono da sai tafi so......Ya cuce ta gaskiya da ya ta'ba mata nono da tasan haka mutum yake ji da bata barshi ba.....Kallo guda yayi mata ya gane abinda ke damunta.....Yace."Yana da kyau kije ki suturta jikinki." A hasale tace"Kaine ka bani kayan da zan saka." Harara ya watsa mata" Kinga tashi ki bani waje zan gana da yara na bana son rashin kunya." Kin tashi tayi tana matse fuska! Cikin tsawa! Yace."Ko bakyaji ne."? Mikewa tayi a fusace! ta nufi bedroom dinshi! Ya bita da wani irin kallo mai cike da ma'anoni da dama yarinyar nan na nema ta sauya masa tunani. Kika futa da book din nan Ke da Allah!/Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *23* 'Daya bayan daya suka shigo sun kai su kusan bakwai ne Garba da Hadi sai securities su uku Abdulmumini mai wanki da goga da bawa shukoki ruwa sai kuma mai masa abinci (kuku) Duka suka mika gaisuwa zuwa gareshi.....Ya amsa musu a sake kana ya d'ora da fad'in"Dalilin da ya sanya na kira ku shine domin in shaida muku cewar Allah ya nufe ni da d'aura aure jiya kenan Garba da Hadi tare mukaje dasu har can garin da aka daura auran.....Ya kalli masu gadi yace."Jiya kun bata min rai sosai wanda har na yanke shawarar sallamarku ya za'ace yarinya karama kamar wannan ta iya futa daga gidan nan bayan kuna kallonta, abunda ya sanya na yanke shawarar rabuwa daku kan aikinku saboda nasan kuna da iyali dukaninku shine dalili amma gargadi na na karshe shine Kada ku kuskura ku bar yarinyar nan ta futa ba tare da sani ba,Idan haka ta faru to sai na daure mutum.....Ya kalli su Garba da fadin"Ku kara saka ido sosai a kanta. Garba yace insha Allah Ya kai idonsa kan Rabe (kuku) yace."Iyakacin ka kicin bana son wata alaka mai girma ta shiga tsakaninka da matata, kana gama abunda kake kayi tafiyarka." Rabe ya amsa da"Yes sir!." Yace.",AbdulMumini zaka cigaba da yin aikinka kaji ko duk sanda wanki da ya taru da kaina zan kira ka ka karba bance ka dunga shigowa ba kai tsaye dalili kaga yanzu bani kadai bane a gidan." AbdulMumini yace."Insha Allahu za'a kiyaye yallabai." "Masha Allah." Yafada yana dan gyara zaman sa a nutse yace."A wannan watan nake tunanin yi muku karin albashi, Insha Allahu." Sai duk suka saki fuska suna dariya godiya suka shiga yi yace."Kowa yaje ya rike aikinsa Allah ya taimaka." Suka amsa da "Ameen Allah ya kara maka suttura da tsawon kwana insha Allahu sai ka zama governor domin kaine muke saka ran za kayi adalci ga talakawa." Yace."Ku cigaba da addua dai Allah ya za'ba abunda yafi alkairi." 'Insha Allah kaine alkairi a jahar kano." Abinda suke ta fada kenan har suka bar palon. Rabe ne ya fito daga wata 'kofa dake cikin palon, da alama kicin ne domin naga anyiwa kofar ado da wani irin labule mai baza da kyalli hannunsa rike da wani faffadan tire na silba cike da kayan marmari irinsu inibi dabino kankana abarba lemo gwanda da sauraru an shiryasu tsaf gwanin ban sha'awa, wani dogon daining mai kujeru kusan takwas naga ya nufa ya aje tiren ya koma kicin nan ya soma fito da kayan kalaci ya jere tsaf! a danining din ya iso inda yake zaune yana duba jarida Leadership ta wannan satin...."Sir an shirya daining." ba tare da ya d'ago ba yace."Okey." Rabe yace."A tashi lafiya." Hankalinsa na kan jaridar har Rabe ya fita.....Ya kai minti talatin a haka kafin ya aje Jaridar ya mike ya nufi bedroom dinshi....Idanunsa ya sauka a kanta tana kwance a bed dinshi ta kifa cikinta ma'ana tayi irin kwanciyar da ba'a so. ya karasa inda take ya tsaya yana kallon bayanta mussaman bom!bom dinta yana mutukar daukar hankalinsa, zama yayi gefenta ya sanya a hannu a hankali ya burkitota kwanciya ya gyara mata ya kama gashinta daya wargaje ya had'e guri guda hannunsa yasa ya tufke mata ya zuba wa fuskarta ido gani yayi ta dan fad'a kwarmin idonta ya zurma ciki akwai alamun gajiya da yunwa a tattare da ita gashi bacci ya dauke ta ko da yake shima baccin rahama ne.....'Kirjinta ya zubawa ido yana kallo...Yaji tsigar jikinshi ta mike tsayin shekarun da yayi babu mace bai ta'ba shiga mawuyacin hali ba sai tsakanin jiya da yau da jikinsa ke gogayya da nata, Ya mika hannu a hankali ya dan shafi saman lebunanta! ajiyar zuciya ya sauke! runkufawa yayi dai-dai fuskarta ya dora bakinsa kan nata le'bunanta ya lasa da harshensa yaji wani irin santsi, da sil'bi! yanda take sauke nuffashi ya sake kid'ima shi bai san sanda ya sake lasar lebanunan ba...Motsi tayi yayi saurin mikewa a gaggauce ya fita daga dakin yana sauke zazzafar ajiyar zuciya. Baiyi wani cikakken karin kummalo ba ya bar daining din, Jikinsa duk ya mutu yana jin wata iriyar kasala ta dabaibaye shi, can palo ya koma ya kwanta kan doguwar kujera Fargabar komawa dakin yake saboda shi kansa bai yarda da kansa ba sam baya so zuciya ta jashi ya afka mata bayan bai shirya hakan ba....Rintse idonsa yayi yana hasaso yanayin tsarin hallitunta da manya manyan d'uwaiwakanta a duniya yana bala'in son mace mai wad'annan abubuwan nono da d'uwawuka!! mace ko mummana ce a fuska baya ganin muninta mutukar dai tana da wannan had'in!! Ya dora romat din dake a hannunsa saman kirjinsa yana lumshe ido....Oh! duniya kenan wai shine yau yake jin sha'awar 'ya mace ashe dai zai ga zuwan wannan rana.? **** Rashida da Uwani dai sun soma shan jinin jikinsu hankalinsu yayi masifar tashi sosai mussaman da suka kira Camas! a waya ta tabbatar musu da cewar tun a daran jiya suka rabu da Wasilar tace ta tawo gida, Ta shaida musu cewar itama tun jiya da daddaran take kiran wayarta bata dauka ba, dazu da safe ma ta kira akace wayar a kashe take. To jin wannan magana ta Camas! ta sanya hankalinsu ya tashi Uwani sai matsar kwalla take tana fadin"Allah yasa dai ba Magauta bane suka sace mata 'yarta, Rashida ma da taga abun dai ba na wasa bane sai ta hau kuka duk jikinsu yayi sanyi sun san Wasila nada makiya sosai suna zargin ko daga cikinsu ne suka sace ta Allah ma yasa kar su kasheta, adduar da sukeyi kenan kuma basu fasa neman wayarta ba. **** Wajejan karfe uku da rabi na rana ta farka daga baccin da ya dauketa, ta j idonta a bude kafin ta yunkura ta tashi zaune ji take jikinta tamkar anyi mata dan karan duka sai nu'kurkusa yake mata ga wata iriyar masifaffiyar gajiya data dabaibaye ta.....Salau! salau! ta mike ta nufi toilet...Ta hada ruwa mai dumi tayi wanka ta dauro alwala ta fito. jikinta daure da towel mai girma, kwata kwata bata sha'awar mayar da kayan jikinta ta zauna gefan bed din ranta a 'bace! kawai an kawo mutum an ajiye bashi da sutturar sawa Hatta da pant da breziya ka'idar ta ce bata maimaitasu kullum sai ta sanja haka ta cure kayan da ta cire da lifayar da jins din da shart din da undis din guru guda ta ajiye ta fita palon kirjinta d'amare! da towel! Nan ta ganshi yana bacci kan kujera ya mike sam'bal hannunsa guda a saman kirinsa sai daya hannun kuma ya dora saman kanshi. Cikin sigar 'kuntatawa ta tsaya kanshi......"Ka tashi ka bani suturar da zan saka." Wannan kalma ta dinga nanatawa gatsal! "Ka tashi ka bani sutturar da zan saka zanyi sallah lokaci na 'kurewa."! Ya dinga jin maganar a cikin bacci tamkar mai mafarki, sai kuma ya bude idonsa da sauri!! ita ya gani a kanshi....Yaji kansa yayi bala'in sarawa! ya tsani yana bacci a tashe shi!!! Ya mike cikin yanayi na 'bacin rai yake kallonta......" Wai ke me yasa kike abu irin na dabbobi ne? bacci fa nakeyi zaki tsaya min aka kamar doki."! Kwarai taji zafin maganarshi wato itace ma dabba......Itama cikin bacin rai tace"Akan na tashe ka ka bani sutturar da zan saka nayi ibadah kake kirana dabbah! meye laifina anan? ka dauko ni ka ajiye babu suttura babu ci babu sha dan nayi magana a zageni wallahi ka daina kirana da dabbah ki tinkiya domin ni ba ita bace."! Bai ce koma komai ba ya mik'e tsaye ta d'an ja gefe tana masa wani irin kallo.....'Ka'ida idan yana bacci aka tashe shi sai yayi ciwon kai da jiri dalili kenan da ya sanya yana mikewa ya tafi luuuuuuu! kamar zai fad'i! tayi saurin kaucewa! amma inaaa! sai da ya same ta ta fadi kan kujerar da ya tashi ya afko jikinta!!! Kanshi da fuskarsa tsakankanin 'kirjinta ya kwanta luf dashi sai kace yaro. Nauyi ne ya isheta ta ture fuskarsa tana turje jikinsa da kafafunta "Daga ni dan Allah.''! Tafada tana kumbura baki.....Can 'kasan ma'koshi taji yace." Sai jiri ya sakeni zan mike daga jikin ki ai kece sila waye yace ki tashe ni ina bacci sai kiyi hakuri har sai lokacin da na tashi." Tabd'ijam! kana nufin kaina zaka kwanta har sai sanda ka ga dama! Ni wallahi nauyin ka ya isheni ba zan iya daukar ka ba ka d'aga ni jikina ya soma tsami."!!!! Tafada tana ture shi da fuskarsa dake kwance kan kirjinta duk ya matse mata nono. 'Kara sakin jikinsa yayi sosai yana sake mikewa sosai a kanta, Wasila taga abun nasa kamar da zalinci sai ta soma kuka tana masa magiya ya daga ta da gaske nauyi ne dashi.....Yana jinta yayi mata shiru, tuntuni ya daina jin hajijiyar kawai tsabar taushin jikinta ne ya sanya ya manta da komai yayi kwanciyarsa kamar wanda yake kan katifa. "Dan girman Allah ka d'aga ni wallahi zaka kassarani bani da 'kwari! wayyo ruwan cikina da gwiwata duk sunyi laushi shikkenan jama'a zai 'karasa n.........Kafin ta 'karasa maganar ta ya mika hannunsa ya datse mata baki!! duk da haka ba ta daina magana ba....Mikewa yayi daga jikinta still hannunsa na damtse da bakinta, Ta mike zaune da sauri towel din tuni ya sunce daga jikinta yayi nasa guri cinyoyinta da lafiyayyun nonowanta suka wanke masa ido tar!!! yake kallonsu kamar wanda ta samu tv ana film din soyayya!! ta tattaro towel din da sauri ta kare kirjinta duk da haka cibiyarta da wasu gurare na jikinta a waje suke! Ta dinga janyo towel din dake 'kasan sa tana so ta rufe, ya janye hannunta idananunsa kan mararta da cibiyarta.....Tsorata tayi kwarai daga nin yanda yake wani wulkita idonsa, sai tayi gaggawar doke hannunsa dake damtse da bakinta ta ture shi da karfin gaske taja towel din ta daure jikinta,Tsaki! taja da fad'in" Allah ya isa."! Ya bita da kallo wanda ya rasa ko kallon menene Yayi masifar shiga rudani wai shin ina alwashin da yaci akan yarinyar nan ne? ina tanade tanaden da yayi mata suka tafi? karfa ace yarinyar nan ta rinjaye shi tun ba'aje ko ina ba, anya ba zaiyi wa kansa fada ba kuwa ya kama girmansa 'kankanuwar yarinya na ganin dama a kansa tana fada masa ko wace irin kalma Anya kuwa.'!!!!!!? Kika futar min da book Ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whadap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *24* Mikewa yayi cikin kasala da rashin kuzari ya nufi bedroom din, nan ya ganta tsaye gaban wardrobe dinsa tana masa bunkice, Tsawa ya buga mata "Me kika ajiye min a cikin kaya kike bunkita min."!? Yanayin yanda taga fuskarsa a murtuke yasa tasha jinin jikinta, Yayi mata wani irin karjini a ido, 'kas tayi da kanta tace" Kaya nake dubawa." Yana hararata yace."Ke kika ajiye a kayan a gurun da zaki hargitsa min."? Shiru tayi masa, ya nufi wardorbe din sai tayi saurin matsawa daga gurin, a duk sanda zai tunkari inda take wata iriyar shakka ce take kamata, yana dubewa ya ciro mata wata jallabiyar sa mai faffadan wuya da hannu zurmemiya yace."Karbi kisa wannan nayi wanka yanzu na fita domin sanin abinyi." Yanda yayi maganar ba alamun wasa a tare dashi yasa ta karbi rigar....Ya juya ya nufi toilet... Rigar take bi da kallo tana tunanin yanda za'ayi ta saka rigar nan katuwa tsayin ta yayi mata yawa fad'inta ma haka ga wuyan kurmame, haka dai ta hakura tasa rigar duk domin tayi sallolin dake kanta....Lifayar ta ta nada a jikinta ta hau kan dadduma ta tayar da sallah. Ya fito daure da towel iya kungunsa sai wani karami a hannunsa yana gogo kanshi...Kai tsaye mirror dinshi ya nufa ya fara shafa mai a jikinsa ya sanya turaran jiki kana ya gyara sajensa dama bai fiye barin suma ba a kanshi dai-dai misali ya taje ya gyara ta sannan ya shirya jikinsa cikin yadin kufta brawon d'inki hannu ne wanda aka bata lokaci gurin dinka shi yayi kyau mutuka mafi akasarin kayanshi ya dika ne masu kyau da tsada! Hula ya sanya ya daura agogo kana ya hau kan kafet din dake kusa da ita ya tayar da sallah. Ganin ta idar da tata sallar ne yasa ta mike daga gurin can bakin bed ta zauna tana saka wasikar jaki! Har ya idar da sallahr shi yayi adduao insa bata sani ba sai alamun bude kofarsa ne ya dawo da ita hayyacinsa, Ga yanayin alamun da taga ni a tattare dashi ta gane futa zaiyi sai ta mike da azama tabi bayansa. Yana tsaye tsakiyar palo suna magana da Garba, Ganin fitowarsa ya sanya ya sallami Garban ya kalleta babu cikakkiyar walwala a tare dashi......."Don Allah ka bani waya ta da sim card dina kaji."! Tafada tana marairaice fuska. Tsaki yaja ya kama hanyar fita, Tace"To dan girman Allah ka bani aron wayarka na kira kanwata nasan gidanmu hankalinsu na atashe mussaman mamanmu." Ya dan tsaya yana kallona na minti biyu karamar Wayar sa ya ciro daga aljihu Ta iske inda yake da sauri ta karba har tana hadawa da hannunsa, Numbar Camas! ta fara kira wayar nata ringing bata dauka ba Yace."Ke! bani wayata bana son 'bata lokaci." da sauri tace"Dan tsaya na kira daya layin na gani." Tsaki yaja ya fice daga palon....Ajiyar zuciya ta sauke da sauri ta zauna kan kujera ta sanya numbar Camas! test ta tura mata kamar haka. _Camas! Ina cikin masifa da tashin hankali da ukuba yanzu haka ina gidan Ahamadu Musa babu iya ka wai yaje can garin su mahaifina ya nemi aurena kawu malam mai allo ya bashi aurena da sadaki dubu biyar, Kiyi kokarin ki samo min mafita Camas! kaina ina cikin masifa_ Tana gama rubuta test din ta tura mata ta goge numbar da test din dan kar ya gani......Ta kira Rashida itama tana ringing bata dauka ba da sauri ta shiga kiran wayar Uwani is swich Up! Tsaki taja tayi shuru can ta yanke shawara Numbar As ta sanya a wayar ta soma kiran shi aikuwa kamar jira yake yi ya daga wayar, ta sauke ajiyar zuciya da sauri ta nufi dakin tana fad'in"As 'Yar gaske ce! Daga daya bangaran As yace."My love ina kika shiga munanan hankalinmu a tashe mahaifiyarki da kanwarki sun shiga damuwa yanzu haka ma duk muna tare dasu da Camas kawarki. Kuka ta fashe masa dashi tace"As Ina gidan Ahamdu Musa a halin yanzu.......Tiryan tiryan! ta shiga warware masa abunda ke da akwai! As ya shiga tsananin tashin hankali da bakin kishi Ahamdu Musa ne yayi masa wannan wulakancin? ya za'ayi ya jima yana rainon abu ace lokaci guda wani yazo ya lalata masa shiri!! Yace." Wallahi karya yake mu zaiyi wa wannan wulakancin wato ta in da ya bullo kenan to ki kwantar da hankali kuma ki tsaya kai da fata kan a'kidar ki duk rintsi kar ki sauka daga ra'ayin ki ni nasan saboda wata manufa tashi ya sanya ya aure ki ba wai dan sha'awa ko wani abu makamancin haka ba, domin tuntunin nasan wannan mutumin bashi da lafiya tamkar mata maza yake babu wani abu da zai iya a kanki, duk da haka dai ki kiyaye zamu dauki kwakkwaran mataki a kansa, sai ya sake ki komai abunsa wato ya gano kina da muhimanci a tafiyarmu shine zai dauke mana ke to daga nan government house zan nufa domin mu san abinyi." A hankali tace"Nima zargin da nake yi kenan ya aureni domin ya rusa tafiyarku ganin ina da muhimanci a tare daku shiyasa ya 'bullo ta wannan hanyar As kuyi da gaske na lura da gaske yake dan Duk ya tara ma'aikatan gidansa a aikana yace su sanya idonsu a kaina gidanshi tamkar kurkuku yake ko ina a rufe babu ta inda zan taimaki kaina." Jin wannan maganar tasa As ya sake zabura! Yace."Aikuwa duk yanda zamuyi ki fito daga cikin gidanan zamuyi kar ki damu." "Shikkenan As ina saurare dan Allah ku taim.......! maganar ta katse lokacin da ta ganshi a gabanta, bakinta ne ya soma kyarma!! " Ra....shi..d ki cewa...U....! Hannu ya mika mata alamun ta bashi wayar.....Dai-dai da lokacin da As yake cewa"My love kina ji na ko? ki kwantar da hankali ki saki jikinsa dashi ki nuna masa komai ba komai bane ta kanki zamu shirya plan dinmu a kansa ai ya janyowa kansa tabbas ajalinsa na kusa." Ahamadu najin muryar As din tar! dake saboda rashin dubara hands free ta bude ko kuma dai ta manta ne oho!!! Jajayen idonsa ya ware mata Hannu ya sake mika mata a karo na biyu!!! Ta mika masa wayar jikinta sanyi kalau....Wayar ya kara a kunnansa, Har yanzu As nata surutu da fad'in"My love kina jina kuwa kinyi shiru, karki wani damu da wannan abun zamu dauki 'kwakkwaran mataki a kansa." Kashe wayar yayi ya tsira mata rikirkitattun idanunsa....."Waye kika ce min zaki kira."!? Yafada yana kallonta cike da tuhuma....."Rashida c.....! Kafin ta karasa ya bata wani lafiyayyan mari! Ihu! ta kurma! ta haye kan bed ta tsaya hannunta dafe da kuncinta......A zabure! yace."Ni zaki rainawa hankali ko? Waye wannan da kika kira har yake kiran ki da masoyiyarsa."!.....Cike da rashin gaskiya tace"Kanwata ce Rash.....Bed din ya haye! ta manne jikinta jikin bango tana kare fuskarta,Wuyanta ya dam'ka! da karfi ya shake mata magogwaro yana mata kamshin mutuwa! Ta dinga 'kifta ido tana kakari idanunsa sun gwalalo sunyi jawur had'e da tara ruwa.....Lokacin duk wani tausayi da imani nasa babu so yake ya kashe ta, babu abunda idan ya tuna yake sake dugunzuma masa zuciya sai muryar gardin mutumin dake kiranta da Masoyiyarsa (My love) ba za'ayi haka dashi ba gwara kawai ya kasheta ya huta tun kafin ta tarwatsa masa zuciya.......Idanunta ne suka soma lumshewa jikinta ya soma shikawa luuuuuu! tayo jikinsa......Ya sake ta ta fadi kan bed din Ta suma! daukar ta yayi ya kai ta can bakin toilet ya ajiye ya bude firji ya dauko shegen ruwa mai sanyi kai tsaye ita ya nufa ya hau tuttula mata a fuska da jiki! Ta bude ido a zabure! tana a tishawa, cigaba yayi da zuba mata ruwan sanyin a jikinta, cikin rashin tausayi.......Saboda rashin kwarin jiki yasa ta koma ta kwanta jikinta yayi lakwas! sai makyarkyata takeyi tana jin saukar ruwan sanyin a jikinta amma ta kasa motsawa sai wasu irin hawaye ne masu zafi dake ziraro mata.....Sai da ya juye mata babban gora na ruwan swan kana ya jefe ta da goran ruwan ya sanya kai ya fice daga dakin ranshi ba'ki'kkirin. Littafin nan na kudi ne! Idan kika futa da book din nan Ke da Allah! Ki ka karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*[07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *25* Ransa a 'bace ya fita ya iske Garba da Hadi a bakin mota suna jiranshi tun kafin ya karaso Garba ya bude masa mota ya shiga kana kallon yanayin yanda ya fito kasan babu wasa, su kansu su Garban sun sha jinin jikinsu, sukan kwana biyu ba suga irin wannan fuskar shanun daga gurun ogan nasu ba, duk ranar da yayi irin wannan 'bata ran to babu shakka akwai abunda ya faru.....Da wuya kaga fushin Ahamdu dalili kenan da yasa idan anyi masa abu a take yake ramawa saboda shi bashi da ri'ko ko 'kan'kani ! ko wane irin laifi zakayi masa ba zai gaba da kai amma wannan karon yarinyar nan ta kaishi bango dole ne ya nuna mata fushinsa mugun kishi ne dashi mussaman kan abunshi, idan yana da abu yasan halalinsa ne baya so kowa ya ra'beshi, yayi masifar jin ciwon wannan kalma da As ke kiran yarinyar dashi (my love) idan ya tuna ji yake kamar ya zai shake dan bakin ciki!.........Maigadin gidan Khalifa ya bude gate din Hadi ya shiga da mota Khalifa na tsaye harabar gidan dama already Ya kirashi a waya ya sanar dashi gashinan kan hanya, da kanshi ya karasa inda motar take ya bude masa kofa ya fito yanayin yanda ya ganshi a hargitse ya sanya yasha jinin jikinsa babu shakka akwai abunda ke faruwa.....Tare suka jera suna tafiya har zuwa cikin gidan...Ya samu kujerar dake daura da kofar fita ya zaune hade da cire hularsa, Khalifa ya tsaya kanshi tare da fad'in'' Akwai damuwa a tare da kai dama tunda naji kace ga nan nasha jinin jikina Allah yasa dai lafiya." Kafin yace wani abu Hafsa ta fito daga daki taci kwalliya cikin boyal mai ruwan zuma tace"Lallai ango ne a gidan da muna cewa zamu zo gashi har na shirya sai kawai ka kira waya kace kaganan." Ya dan saki fuska kadan yace."Zuwana ba zai hanaki zuwa ba tunda kin san gidan sai kiyi tafiyarki." Tace"Ai amarya bata sanni ba mun bari dai sai ranar da kake gida sai muje Ga Zeey ma tazo yau kwananta biyu har ita muka shirya zamuje muga amarya sai kuma kayi mana bukulu." Cikin 'kosawa yace."Wai ke dole sao da mijinki zakije gidan ne? nifa bana son gulma irin taku idan yawo ne ya kama watarana ma bakya tambayarsa kike tafiya to tunda kin samu abokiyar tafiya ba sai kuje ba, muma mafi jin dadin sakewa a gidan dan idan kinanan kin dinga zurga zurga kenan kina hanashi fahimtar magana." Dariya tasa tace" A'a dai gwara muje tare da mijina in yaso sai ka gabatar damu tare a gurinta amma yanzu idan munje nida zeey bamu san abunda zamu ce mata ba tunda ba saninmu tayi ba." Khalifa yace."Ke da Zeey din ai gulma ce zata kaiku ba wani abu ba." Yar dariya tayi tace "Lallai Abban Afnan Wai gulma ni da nake so ma amaryar ta zama 'kawata sai kuma naje gulma." Yace."To meye na gayyato zeey dole sai anje da ita." Hafsa ta diririce! "Abban Afnan meye haka? Wallahi katari akayi Zeey tazo kai kanka ka san Zeey bata san Governor yayi aure ba, sai da tazo taji labari to meye a ciki dan taje gidan ai matar mutum kabarinsa wani baya auran matar wani hakanan wani baya auran mijin wani." Ahamdu Yace."Kinji mijinki naso ya tona miki asiri duk kin diririce to ai nagane komai." Rantsuwa ta soma yi tana so ta fahimtar dashi ba haka bane....Zeey ta fito daga dakinta, Siririyar mace ce fara mai fadin fuska da manya manyan ido da hanci mai fad'i sai bakinta mai dan tudu dai-dai misali bata da wata cikakkiyar 'kira ta matantaka! amma kuma kallo daya kayi mata zaka gane cewar wayayyar macece mai tarin ilimi da kagani kuma tana da shekaru ko kusa ko alama ba zaka hada shekarunta dana Wasila ba ta girme ta da kusan shekaru bakwai Wasila yanzu tana matakin shekaru 18 Yayin da Zeey ke da 26 Fuska a sake ta zauna kujerar dake fuskantarsa tana fadin"Ango ashe ana ganinku gaskiya Yallabai kayi wuyar gani ko a waya ba'a gaisawa. Akwai kyakkyawar fahimtar juna a tsakaninsa da Zeey dan haka sai ya saki fuska kadan yana fad'in"Kece mai laifi ai da baki kirana a waya kin san al'amura da yawa sun sha kaina sai hakuri." Murmushi tayi tana mamakin maganarshi wai fadi yake bata kiran wayarshi abunda a rana sai ta kira sau goma yaki dauka gajiya tayi da wulakanci ta kama kanta amma saboda ya kare kanshi yake kokarin dora mata laifi....Cikin bagarar da maganarsa tace"Kawai dai ka fad'i hakane domin kaji dadin bakin ka amma sau nawa zan kira wayarka kayi dauka gashi zahiri tana shiga babu amsa.. Kare kansa ya hauyi tace"Governor kenan ashe kayi aure babu labari."? Ya dan sosa kanshi still da murmushi kadan! wata iriyar kunyar ta ce ta kamashi amma dake namijin gaske ne sai ya basar yace."Wallahi kuwa lokaci yayi kisan kuma dama haka lamarin aure yake idan Allah ya kawo shi bagatatan sai ayi." Tace"Hakane to Ubangiji Allah ya sanya alkairi." Yace."Ameen nagode kwarai yanzu ki bani numbar ki sai nayi seving ko." Ta kalleshi da mamaki tace"Au! kace ma baka da no dina." A wayance yace."Kwanaki na bawa Garba Wayar ya rage min numbars na jama'a sunyi yawa ashe ya had'a da taki dalili kenan da ya sanya duk sanda kika kira bakya samun amsa akan lokaci." Yafadi hakane dan ya kare kansa amma tun ranar da sukayi musayar numbar ita dashi yana futa ya goge numbarta a ganinsa sam bai ga amfanin ajiye numbar mace a wayarsa ba. Zeey kuwa ta yarda da maganarsa dan haka da sauri ta soma fad'o masa numbar yana sanyawa a wayarsa yayi serving tare da fadin'" Kinga ma dunga gaisawa lokaci zuwa lokaci." Zeey tace"Aikuwa dai kam." Hafsa dake shirya abinci a dining tace"Governor yau fa mutuminka nayi ban sani ba ko zaka ci ko da yake amarya nasan kafin ka fito ta cika mata ciki da girkinta na amare. Hararata yayi yace."Wai kina nufin Towo ko me."? Tasa dariya da fadin "d'ayan ne." Yace."Alkubus."? Eh tafada tana murmushi....Yace."Ai ko d'awisu ta bani sai naci ko da cikina zai fashe." Duka suka kwashe masa da dariya Khalifa yace." Ai na sani ko ka koshi sai kaci wannan abu ni ban san me kake ji a cikinsa ba fulawa kayan basir." Mikewa yayi yana fad'in"Ballanta na ma ban koshi ba dan har yanzu 'bacin rai ya hanani cin wani abincin kirki." Sai da ya fadi maganar kuma ya dawo yana da ya sani ganin dukaninsu sun sha jinin jikinsu.....To dai babu wanda ya sake tado da maganar suka zauna a danning Hasfa ta zubawa kowa nashi....Ahamdu ya riga kowa cinyewa Ya sake zuba wani da kanshi Hasfa sai tsokanarsa take da fadin"Allah yasa santi yasa ya manta hularsa. Sai bayan sun kammala cin abincin ne ya kalli Hafsa a nutse yace."Wane guri ake miki d'inkunanki."? Ta kalli Khalifa dake goge bakinsa da tissue! Khalifa yace."Kana so ayi wa amarya kenan."? Ina so dai in siya mata d'inkakku a gurin nasan ba za'a rasa ba.' Khalifa yace." Bari nayi wanka nazo muje Yakasai Gidan Murtala." Yace."Kayi da sauri yamma tayi." Khalifa ya mike ya nufi daki Hafsa tabi bayansa domin hada masa ruwan wanka.....Ahamdu da Zeey suka shiga hira abunda ya shafi harkokin Siyasa da yanda talakawa me faman shan wuya a wannan gomnantin. Khalifa ne yake draving shi kuma yana zaune a gefansa suna hira Khalifa yace."Yanayin yanda ka shigo dazu ya sanya hankalina ya tashi to amma ganin ka sake kana hira dasu Hafsa yasa hankalina ya kwanta da har nayi tunanin ko kai da mutanan ne." Tsaki yaja Yace.'' Khalifa nayi abu yazo yana damuna kwata kwata yanzu na dawo ina dana sani da auran wannan yarinyar da nayi tsakanin jiya da yau ta zame min masifa da kyar nayi bacci n dare da sassafe muka tashi da masifa abincin kirki ta hanani naci.....Babban abunda ya 'bata min rai da ita shine na bata waya ta ta kira gidansu, ta kira min wani shege wai ni zata rainawa hankali naji muryar namiji take cewa dani kanwarta ce a take na sumar da ita kasan dai halina in raina ya 'baci."! Khalifa yace."Subahanallahi! gaskiya Wasila bata kyauta ba! Magana da wani namiji bayan tana da auren wani a kanta......"Za tayi abinda yafi haka ma tunda jahila ce shiyasa na tsaurara matakan tsaro a kanta." Khalifa yace."Kaima matakin da ka dauka yayi tsauri gaskiya ya kamata ka zaunar da ita ka fada mata yanda al'amura suka kasance a tsakaninku nasan halinka da isa da jin kai! Dole ta shiga rudani da tashin hankali tunda katsaham! taji labarin auran kome zata iya yi a wannan lokacin." "Khalifa yarinyar fa babu irin rarrashin da banyi mata ba ta'kiji saboda tsabar rashin mutunci dazu ni tayiwa Allah ya isa."! Khalifa yace."A kan me? Shiru yayi nauyin fada masa abunda yasa yake....Yace." Dole ne fa kayi hakuri da duk abunda za tayi maka gaskiyar magana kenan kuma kai kanka kasan duk yawancin abokananta maza ne abokan hurd'arta do ka fuskanci wannan matsalar." "Khalifa kasan Allah kasan Annabi Ba zan lamunci wannan iskanci ba, Zan iya raunatata nayi mata illah mai muni mutukar naga da aurena a kanta tana mu'amula da wani namijin a waje, shine dalilin da ya sanya ma duka na kwace wayoyinta na cire sim car din ciki na karairaya su....Domin nasan tilas mutsiyatan nan ba zasu rabu da ita ba tunda sun san tana musu amfani, Sam kar kayi tunanin ko sonta nakeyi kawai ina kishin aure na ne banda haka babu abunda ya shafeni da duk wata rayuwa da zata jefa kanta a ciki.'' Khalifa yace." Kai ma kuma kayi gaskiya nan, Amma dai duk da haka ina mai baka shawarar karka tsawwala mata da yawa ka tausaya mata." Yace."Idan ta tausayawa kanta shikkenan idan bata tausayawa kanta ba ita ta jiyo." Sosai ya sissiya mata kayan sawa masu tsada da dinki irin na 'yan burni shaddodi da lesuna sunfi yawa a cikin kayan kwata kwata atamfa hudu ce sai material uku sai dakakkun shaddodi da lesuna wanda aka zuba musu dinkuna masu kyau....Manya manyan ledoji hudu aka cika da kayan....Yaran dake aiki a shagon suka kai kayan mota Ahamdu ya fito da kudi ya biyasu suka fito daga gurin......Sai da ya koma gidan Khalifa ya dauki motarshi kana sukayi sallama da juna ya wuce gida. Su Uwani da Rashi Da Camas! har magariba suna bakin gate din gidan Ahamdu kamar wasu Mayu sai naci sukewa masu gadi su bude musu sun'ki Daga karshe ma da suka takura musu bulala suka fito da ita sukace idan basu bar gurun ba sai sun zanesu, babu shiri suka bar gurun ransu idan yayi dubu ya 'baci! Tun bayan futarsa a dakin take kwance a gurun tana tsiyayar da hawaye sai wata iriyar makyayata takeyi tana zabura sanyi sai ratsa jikinta ya keyi 'kashushuwan jikinta tana jinsu tamkar ana kwankwasa su da duste takure jikinta tayi guri guda jikinta sai d'ari yake yi yana mazari!!! Kafin kice kwabo ta soma ficewa daga hayyacinta. Littafin na kudi ne......! Kika futar min da book Ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema Ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *26* Yana tura kofar dakin ya ganta a kwance inda iya ajiyeta tun safe zuwa wannan lokacin ta riga ta gama fucewa daga hayyacinta domin idanunta sun juye sunyi fari tas ya tsun hannuwanta duk sun tankware sun tsaya cak! babu abinda yake aiki a jikinta a lokacin sai saman idonta dake dan harbawa kadan kadan Numfashi kuwa da kar take jawo shi yana kufcewa.....Da mugun sauri ya dire ledojin dake hannunsa ya nufi inda take, hannu yasa ya tattaro ta jikinsa yana tatta'ba ta, Yayi gaggawar cusa hannunsa cikin rigarta wani mugun zafi yaji a jikinta ya cire hannunsa sauri ya kinkimeta ta mike sambal tamkar Matacciya kan bed ya kwantar da ita, juyawa yayi da azama! sai kuma ya dawo kanta ya tsaya duk ya rude kansa ya juye ya rasa ma wane taimako zai mata....da alama daf take da shekawa barxahu ganin yanda take jin jiki da jawo nufashi da kyar! A gaggauce ya nufi toilet dinshi ya ciko karamar roba da ruwa ya dauki karamin towel ya tsoma a cikin ruwan......Yana zuwa ya cire rigarshi ya janyota jikinsa ya zare mata jallabiyar jikinta, tayi tik da ita tamkar yanda uwarta ta haife, yarda ya kalli sassan jikinta ba dalili baya so wani abu ya darsu a zuciyarsa taimako zaiyi ba wani abu....manne ta yayi a jikinsa suka sauko kasan kafet, ya ware kafafunsa ya sanyata a tsakiyar shi, Ruwan ya shiga tsanowa da towel din yana goga mata a jikinta sa'ko da loko ko ina yake shafa mata yanayi yana korar shaidan tare da kau da kansa daga barin kallon muradan zuciyarsa, Ya jima yana matsa mata ruwa a jikinta ko gezau ba tayi ba, a lokacin yaji wata iriyar nadama ta kamashi yana tsoron kar yarinyar mutane ta mutu a hannunsa, Kwantar da ita yayi ya mike da sauri yaje ya dauko wayarshi.....Kai tsaye numbar dector din sa ya kira yace maza yazo gidanshi akwai mara lafiya Emagency.....Ya dawo inda take yana kallon saman idonta dake motsawa, tsuganawa yayi ya sanya hannu ya dan ta'ba gurin! Yaji ta sauke wata iriyar ajiyar zuciya!! Da sauri ya cire hannunsa ya rike tafin hannunta sai yaji tana motsawa, ya damke hannun cikin nasa yana kiran sunanta a hankali........Hawaye sirara yaga suna zubowa daga idanunta gasu a rufe....Hamdala yayi ga Allah tabbas tunda yaga hawaye na fita daga idanunta ta dawo....Ya ciccibeta ya dora kan bed ya zauna kusa da ita hannunsa na rike da nata ya tsurawa fuskarta ido.......So yake kawai ta bude ido amma babu hali tsabar ciwon da kanta ke mata ya sanya idanunta sunyi nauyi sam ta kasa budewa jijiyon kanta sun tashi rad'a-rada hatta saman idanunta sai da jijiyo suka bayyana......Karaf! idanunsa suka sauke kan tsayayyun nonowanta da suke kallon rufin dakin....Yayi axamar dauke kansa yana sauke wata gawurtacciyar ajiyar zuciya, ji yayi gabanshi na wani irin zillo! yana so ya sake kallonsu yana jin tsoron abunda ka iya zuwa ya dawo, sai ya mike hannunsa ba tare da kalleta ba ya janyo bargo ya rufe mata jikinta still hannunsa na makale da nashi. Jin saukar bargo a jikinta ya sanya tayi wata iriyar zabura!! Idanunta ta bude suka sauka a kanshi! tayi saurin mayar da idanunta ta rufe tana jin wata iriyar tsanarsa cikin ranta da tana da yanda zatayi a kansa da sai tayi ta kassara shi bashi da imani bashi da tausayi nema yake yaga bayanta a duniya bata da babban makiyi da ya wuce shi.......Jin d'umin hannunaa cikin nata ya sanya ta tattaro ragowar karfin da take dashi ta fizge hannunta.....Ya dan kalleta, ta mayar da idanunta ta rufe hawaye na sake zuba....Mikewa yayi ya fita daga dakin ba....Yana fita dector Nasir ya shigo, suka gaisa kana yace dashi yana zuwa,Dakin ya koma tana kwance amma ta sake takure jikinta....."Tashi ki dan sa riga Dr zai shigo ya dubaki." Cikin taushin murya yayi maganar. Tana jinsa tayi masa shiru ya sake maimaita maganarsa nan ma kamar da dutse yake magana, bai sake cewa Uffan ba ya nufi inda ledojin kayanta suke ya dauko wata dakarkariyar shadda wacce akayi wa dingin doguwar riga ya nufe ta da rigar a hannunshi.....Jin tayi ya yaye bargon jikinta, tayi saurin bude idonta, Zabura tayi da mugun sauri! ta fuzge bargon hannunsa tana kare jikinta dashi wata lafiyayyar harara take! watsa masa, bai damu ba ya mika mata rigar a sar'ke yace."Karbi kisa a jikinki."! Kin 'karba tayi tana ji tamkar taje ta shakeshi tabbas ita dai tasan akwai kayan a jikinta jallabiyarsa da ya bata to ya akayi kuma ko dai shine ya cire mata to waye kuwa in bashi ba, sai ta shiga motsa kafafunta taji wai ko yayi mata wani abun, ba taji wani sauyi ba a jikinta ta sauke ajiyar zuciya ta koma ta kwanta tabarshi da tsaye da riga a hannu.....Hawa bed din yayi ya janye bargon tayi azamar mikewa zaune kallon juna sukayi ita dashi Yace."Bana son taurin kai kar'bi suttura kisa baki da lafiya likita zai shigo ya duba ki." Fuzgar rigar tayi daga hannunsa ba da son ranta sai dai kawai dan bata son katsalandan din da yake mata sai wani bude mata jiki yake....A gabanshi ta zura rigar tana gyarawa yana taimaka mata, mikewa yayi yaje ya dauki ledar pant cikin kayan da ya siyo mata ya farke ya ciri guda ya mika mata! Karba tayi tana kauda kai, Yace."Yi azama kisa Yana tsaye yana jiranki." Kin sawa tayi saboda nauyi yayi tsaye a kanta saboda rashin kwarin jiki sai ta koma ta kwanta tana takure jikinta. Yarinyar nan na so ta jaza masa matsala pant din dake hannunta ya karba ya runkufa kanta rigar jikinta ya soma tattarewa yana daga kafafunta da pant din a hannunsa yana kici kicin zura mata, Lokacin ta dinga jin wani irin hajijiya da rashin karfi a jikinta dalilin da ya sa ta kasa hanashi tana ji ya yaye rigar gabad'aya ya zura mata pant din sai gogar mata jiki yake mussaman duwawukanta ya matsa su da hannaye sa babu a dadi kafin ya sa mata pant din....Tabbas ba karya tayi ba Ahamdu sai da yayi ta maza ya iya sakin kafafunta dan a lokacin ji yake tamkar ya afka mata ji yake babu abinda yafi dadin ta'bawa a duniya kamar mazaunanta wani irin taushi da santsi ya dinga ji a fatar hannunsa yaji da hannuwansa zasu dawwama gurin mulmula gurun ba zai ta'ba gajiya ba, Ya jima zaune a gefanta yana saisaita kansa da tunaninsa gudun kar Dr ya ankara da wani abu, sannan ya mike ya fita. Tare suka shiga dakin da Dr Nasir dake rike da jakarshi irin tasu ta likitoci. Dr Ya tsaya a kanta da fad'in "Sannu Madam."! Daga masa kanta kurum tayi ba tare da ta bude idonta ba, Dr Yace."Madam ya kike jin yanayin jikin naki Yallabai yace zazzabi ne ke damunki."? Bude idonta tayi Kallon Farko da Dr din yayi mata ya gane cewar bata da ishashen ruwa a jiki kana kuma akwai alamun zazzabi mai zafi a tare dai ita. Ya kalli Ahamdu dake tsaye yana kallonta " Yallabai Madam na bukatar ruwa leda uku yanzu kuma alamu sun nuna tana jin jiki kwarai da yunwa da kuma gajiya, Yanzu dai ko yaya ne tasa wani abu a cikinta sai na daura mata ruwa insha Allah zata samu relief. " Ahamdu yace."Okey." Wayarshi ya kira Rabe (kuku) yace ya kawo abinci plate daya, Minti biyar Rabe Ya kwankwasa kofar dakin yayi azamar bude kofar ya karbi abincin....Dr Yace."Yallabai bari naje palo kafin ta gama cin abincin....."Okey." Abinda yace kenan Ya karasa bakin gadon hannunsa rike da plate din abincin. "Tashi kici." Yafad'a babu alamun wasa a tare dashi. Ta mike zaune hannunta na rawa ra karbi abincin ganinsa yasa jikinta har kyarma yake tsabar yunwa....Loma uku tayi amai ya dinga taso mata ta dai daure tana ci tana ya mutse fuska.....inaaa! da sauri ta jefar da plate din ta mike da sauri tana tangal tangal ta iske toilet ta dinga kakarin amai dan wanda taci sai da ta amayar dashi. Bakin toilet din ya tsaya yana kallonta tana rike ciki saman goshinta duk ya tara zufa sai hawayen wahala take, Tausayi ta bashi ya shiga toilet din ya debi ruwa yana wanke mata baki da hannuwanta da kafafunta, ya kamo hannunta suka fito sai lauyewa take tana lanjarewa jiri na dibarta, zubewa tayi tsakiyar dakin....Ya dauketa cak ya kaita bed din ya ajiye....Gumi kawai take shar'bawa tana dafe kirjinta, sosai ta bashi tausayi da gani tana jin jiki kamar yanda Dr din ya fad'a....Plate din abincin ya dauka ya de'bo cikin cokali ya kai bakinta. Kauda kanta tayi tana ya mutsa fuskarta kokari ma takeyi ta kwanta Yace."Yi kokari kici loma uku ko hud'u sai ki kwanta ko kin dai san yunwa ce ta janyo miki wannan aman." Shareshi tayi Ya sake magana tayi masa banxa, duk sai yaji rashin dadin hakan ya ajiye plate din ya fita.....Minti biyu suka shigo da Dr din yana fadin "Dama dole abinci ya'ki zama a cikinta saboda dad'ewar da tayi ba taci ba ta tara yunwa tayi mata yawa Yanzu bari nasa mata ruwa insha Allahu za taji kwarin jikinta idan tayi bacci ta tashi da kanta zata nemi abinci." Yace."Okey babu matsala." Dr Nasir ya soma hada ruwan shi kuma ya zauna kusa da ita yana me zura hannunsa cikin bargon yana kokarin fito da hannunta guda tana no'kewa had'e da fuzgewa ga idonta a rufe duk wasu maganganu da sukeyi tana jinsu......Rike hannun yayi da kyau duk kokarinta ta kasa kwacewa ya shiga matsa hannu yana nemo jijiya....Dr yayi saurin kama hannun inda ya gano jijiyar ya daura ruwan akai.....Ta danji zafi kadan ta dai daure har aka gama, ya mike hade da gyara mata bargon suka fita dashi da Dr din.....Lumshe idonta tayi bacci na fuzgarta tana tunanin Mahaifiyar ta da Kanwarta yanzu ko cikin wane hali suke tasan dai duk inda suke suna cikin damuwa da tashin hankali. _*Akwai Wani sirri da zan fad'a muku wanda ba kowa ne yasan wannan sirrin ba, Idan kinyi kin gwada to karki manta da Binta😀🤝🏻 Aha!! Kina fama da 'karanci ni'ima da bushewar gaba! Ko kuma idan mijin ki na saduwa dake kina jin zafi gurin na tsagewa yana miki zafi da rad'dadi a maimakon kiji dadi sai kuma a samu akasi shi oga na kwasar dadi ke kina cije baki na wahala, ni'ima itace tu'kahon duk wata 'ya mace komai kyanki da dirin ki idan baki da ni'ima kin zama hoto a gurin mai gida zakiyi ta fuskantar Matsaltsalo iri iri....Wannan dama ce ta samu a garemu a sau'ka'ke!!!!🙋🏻‍♀️*_ _*Matsala ta budewar Gaba na da ala'ko'ki dabab daban budewar gaba babban kalubale ne a gare ki 'yar uwa akwai matakan da zaki bi gurin ganin kin gyara matantakar ki duk domin kiyi martaba da mutunci a idon mijinki🙋🏻‍♀️*_ Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book ke da Allah kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *27* Uwani da Rashida ne zaune a palon gidan Wasila abin duniya ya taru yayi musu yawa, ga dai abubuwan more rayuwa da jin dadin amma kuma rashin Wasila a tare dasu ba karamin gi'bi yayiwa rayuwarsu ba, suna mutukar kaunarta mussaman mahaifiyarta Uwani, tabbas sai yanzu tayi tunanin irin had'arirrikan data jefa kanta duk dan suji dadi su samu walwala, Wannan al'amari da ya faru da Wasilar ba ko wane ya silar shi ba sai mai allo Saboda haka taci alwashin zuwa har can inda yake tayi masa wankin babban bargo, ta tabbatar da cewar Ahamdu kudi yaje yasa ya siyi Wasila a hannunsu su kuma sunga kudi suka yanke wannan hukuncin ba tare da saninta ba a matsayinta na mahaifiyar ta dan haka dole taje ta nemi hakkinta kuma ta ci musu mutunci iya son ranta. Rashida tace"Gaskiya Uwani da zaki bi shawara ta da sai nace kiyi hakuri ki bar wannan maganar, mutumin fa da aunty Wasila ta aura babban mutum ne mai kudi wanda duniya tasan shi, kema in baki manta ba nasan ba zaki mance alkairinsa ba shine fa mutumin nan da ya taimake mu ranar da mukaje siyayya da daddare 'barayi suka biyo mu, ni a ganina ma kamar gata Kawu Malam yayiwa aunty Wasila da daura mata aure da mutumin wallahi ba tsaran auranta bane." Uwani tace"Koma dai menene ni ba zan yarda ba sai naje naji ba'asin abinda ya faru, a kan me zasu daurawa 'Yata aure ba tare da sanina ba.'' Rashida tace"To sai dai ki tafi ke d'aya ni bazan biki ba dan gaskiya ina jin kunyar hada ido da Kawu Malam." Tace"To ai dama kin fi kaunarsa a kaina sam! bakya kishina Rashida to sai me! kije kiyi tayi shiyasa nake alfahari da Wasila saboda tana kishina da kaunar abinda nake so." Uwani ta dinga zazzagawa Rashida masifa kamar za tayi mata baki kan kawai tace ba zata raka ta Garko ba gurin malam mai allo. 'Bangaran Gidan Governor kuwa duk wanda ya san muhimancin Wasila a tafiyarsa ta siyasa sai da ya jajanta al'amarin mussaman governor da babu irin zagin da baiyiwa Ahamdu ba, shawarwari suke 'kullawa kan yaya za'ayi su fito da Wasila daga cikin gidan.....Camas! da yanzu ta zama a madadin Wasila tana zaune kusa da mutumin nata Alh Ma'aruf tace"Ga shawara nasan za tayi mutukar tasiri da amfani." Duk suka maida hankalinsu kanta....Tace." Mai zai hana kawai a dauki matakin she'kashi barzahu ta hanyar 'Yar gasken Tayi kwance kwance ta saki jiki dashi tanan ne zamu samu dama mai sauki a kanshi a take sai kaga anyi masa kwaf daya ba tare da mutane sun ankara ba, kaga mun ci riba biyu a kansa. Governor yayi murmushi yana fadin"Hakika wannan yarinya 'kwalkwarki naja sosai wannan shawara taki itace dai-dai a halin yanzu duk abunda mukayi jama'a zasu gane mu da sauri shi kansa ma zai gane mu abinda zamuyi shine mu dauke hankalinmu daga kanshi ta bangaran auranshi da Wasila, mu cigaba da harkokin siyasarmu kamar yanda mukeyi......As yace."To yanzu meye abinyi."? Camas! tace"Ku bar komai a hannuna da sannu zan aiwatar mana da 'Kudirinmu insha Allahu duk yanda zanyi zanyi in samu nasarar shiga gidan duk dai ya zuba matakan tsaro amma hakan bai zai hana na samu hanyar shiga ba, zan samu Wasila zamu tattauna kan maganar da muka yanke daku." As yace."Ban ta'ba ganin d'an akuya ba kamar *Ba Iya ka!* ashe kwance kwance yayi mana, yasan wannan yarinya nada amfani a tafiyarmu sai da ya san hanyar da yabi dare da rana ya rabamu da ita, Zai gane shayi ruwa ne."!!!! To kamar yanda Dr Nasir ya fada hakane ya kasance da Wasila misalin karfe goma shabiyu na dare ta farka lokacin ruwan da aka daura mata ya kare, Ta farka da wata matsananciyar yunwa cikinta sai 'kugi yake, hannunta ta dan daga kadan tana rintse ido sosai hannun yayi mata tsami! ta sanya daya hannun ta cire abin da akayi mata karin ruwan tana dan matsa gurin.....Tana zuro kafafunta da niyyar sauka daga bed din ya turo kofar dakin ya shigo.....Yana sanye da Pyjamas kirjinsa a bayyane kasancewar bai daure igiyoyin rigar ba....Da sassarfa ya karasa kusa da ita yana tambayar ta jikin nata....kasa kallonsa tayi ta rasa wane irin iskanci ne wannan haka kawai sai ya dinga zuwa inda take da kirji a bude shi gashi 'kato, duk sanda idanunta suka sauka a kan faffadan kirjinsa takan ji wani iri a tare da ita, shiyasa ko da wasa bata son kallonsa cikin irin wannan shigar....Yana tsaye yaga ta mike tsaye jikinta da kwari bata tangadi da layi irin na dazu nan ya fahimci ta dan samu rangwame ya bita da kallo har ta shiga toilet......Minti biyar tayi a ciki ta fito,Bakinta ta wanke ta dan dauraye fuskarta babu abinda take muradi sai abinci ko wane iri ne....Ta zaune gefan bed, shi kuma ya fita, Bai jima ba ya shigo dakin hannunsa rike da plate mai murfi ya ajiye mata kasan kafet...A nutse yace."Ga abinci nan dauki kici kafin kisha magani." Ya dauka za tayi masa musu sai yaga ta sauko kasan kafet din da sauri ta bude plate din abincin, tana juyawa.....Pride rice wacce tayi kayan lambu da hanta a take taji yawun bakinta ya tsinke ta ciko cokali da sauri ta tura a bakinta....Fita yayi da niyar dauko mata magungunanta, Yana dawowa ya iske ta cinye abincin nan tas! ko 'kwallon shinkafa ba ta bari ba, sosai ya shiga mamaki! ya dinga kallonta yana kallon plate din....Kunya ce ta kamata sai ta dinga dauke kanta tana zumbura baki.....Gyaran murya yayi yace."Kar'bi magani kisha idan kuma abincin bai isheki ba akwai a kicin Okey."! Kamar ta'ki karbar maganin sai dai ta karba sai taga kuma kanta zata cuta ta mika hannu ta karba....Ya kama hanya ya fice daga dakin abinsa......Ajiye maganin tayi tana tunani, Ita abincin nan bai isheta ba gashi tana jin kunyar zuwa ta 'karo....Mikewa tayi ta bude kofar dakin a hankali! Taga baya palon ta dauki plate din ta fita, da lalube ta iske kicin din, ta tsaya tana kare masa kallo, kicin sai kace d'aki anyi masa jere iri iri da na'urori har da Ac freezer irin na kwance guda uku shin kanshi Gas din dake kicin din bata ta'ba ganin irinshi ba, kicin din yayi masifar burgeta, ta dinga kalle kalle sai da ta gaji ta bude tukunyar dake kan gas din ta d'ebo abincin ta fito......Sun kusa buga karo dashi yayin da yake kokarin shigowa cikin palon ita kuma ta fito daga kicin din...Da sauri ta matsa gefe gabanta na faduwa! Ya kalli plate din hannunta yaga ta ciko da abinci , kamar yayi magana sai kuma yaja bakinsa ya kulle, ya nuna mata hanya da hannunsa, Simi-simi ta wuce kunyar duniya duk ta isheta karfa guy nan ya dauka ita mayunwaciya ce ko zulamammiya asali ma ita abinci bai dame ta ba takan iya yin ci biyu kacal a rana ko taci sau daya in dai za tayi ciye ciyen ta. Koda ta sanya abincin a gabanta kasa ci tayi tunda tayi loma uku sai ta ajiye cokali ta zabga uban tagumi tunanin rayuwa ta shiga yi, tun da suka taso ita da 'yar uwarta da mahaifiyarta suke shan wahala a duniya babu irin wuyar da mahaifinta bai sha kan asirinsa ya rufu har wanki da goga yayi kana kuma yayi faskaran ice ya sai da kayan miya duk wata sana'a da Yahuza mai rasuwa yasan zaiyi yanayi duk dan asirinsu ya lullu'bu! Sai dai kash! Allahn da ya hallici Uwani ya hallice ta ne mara godiyar Allah duk irin dauki ba dadin da Babansu yake yi a kansu bata gani, tun suna yara kananu take so ta koya musu bin maza tallah babu irin wanda bata dorawa Rashida, saboda itace mai dauka ita kuwa duk ranar data dora mata tallah to sai ta zubar da kayan a kwata tana sane dan haka sai ta daina dora mata, lokatan baya samari yan banabakwai har sun soma latse Rashida tun bata kai shekarun hakaba, wannan dalilin ne ya sanya bacin rai ya kwantar da Yahuza ashe kwanciya yayi wacce ba zai tashi ba yazo yayi mutuwa fuju'an!! Sai suka sake shiga tsananin takura da damuwa da rashi da kuma kangi na talauci! Uwani itama marainiya ce ita sam bata ma taso tare da iyayenta a hannun Kanin babanta ta rayu rayuwar da tayi a gidan Kawunta mara dadi ce tasha wuya sosai matansa suka mayar da ita yar aiki komai itake musu ga yayansu baza su sanya su aiki ba sai ita tanaji tana gani zasu tura yayansu makaranta amma ita tana zaune dan da Kawun nata yayi niyar sanya ta a makaranta sai su ka nuna rashin amincewarsu saboda suna ganin duk sanda ta fara zuwa makaranta to aikin gida zai dawo hannunsu, shi kuwa dama mutum ne da baya kaunar bacin ran matansa da yayansa, sai ya kyale Uwani ta dawwama cikin bauta babu a rabi babu boko... Gurin yawon cefane suka hadu da Yahuza a lokacin yana siyar da kayan gwari! Aikuwa tsabar kyawunsa ya sanya Uwani makancewa a kansa, duk da a lokacin manya mutane masu hannu da shuni sun fito suna sonta, ciki harda Ubangidan Kawun nata, tace Ita Yahuza take so, Kawu yayi yayi da ita ta amince da Ubangidansa ta'ki fafur! Gefe guda Matansa na kara ingita kar ta auri Alhaji Bala, domin suna ganin idan ta aureshi to ta wuce takaici sai suke bakin cikin hutun da zata samu suka dinga zugata da fadin"Idan ta aureshi matarsa sai ta kasheta dan Hajiya Larai bata zama da kishiya tasha haukawa kishiyoyinta, da jin wannan magana tasu sai Uwani ta sake rikicewa ta tsorata ta tuburwa kawu dole ta sanya yace da ita maza maza ta sanya Shi Yahuzan ya turo magabantanshi......Yahuza ya dauko Malam mai allo da Kawunsa suka zo har gurin Kawun Uwani aka tsaida maganar daurin aure........... Ranar da aka daura auran Kawun ya bata sadakinta a hannunta yace."Uwani tunda ke baki dauke ni a matsayin uba ba kina bujerewa umarnina to shikkenan kije na yafe ki daga zuria ta tunda Yahuza kika zaba kije babu ni babu ke kar in sake in sake ganin kafafunki a gidana duk sanda kika zo min gida to sai nayi miki korar kare kije yan uwan Yahuza su zama yan uwanki." Uwani ta dinga kuka tana bashi hakuri, fatafata! yayi mata ya kore ta....... Wannan shine dalilin da ya sanya Uwani take rayuwarta ita kadai daga ita sai 'Yayanta, kuma tun sanda Kawunta ya koreta bata sake taka kofar gidansa ba kana kuma bata barin su Wasila suje gidan. Abinda ya janyo musu rashin jituwa da Kawu mai allo lokacin da Yahuza ya mutu da yazo ya dauke mata 'yayanta tayi magana ya farfada mata magana mai zafi! ashe dama tun lokacin daurin auranta da Yahuza Kawunta ya dinga fadawa Malam din bata da hali bata jin magana gararrariya ce bata da biyayya dalili kenan da ya sanya yayi mata aure, to tun daga lokacin Kawu Malam yake mata kallon mara tarbiya gaba mai muni ta shiga tsakaninsu A cewarsa ai tunda ba tayi wa Kawunta biyayya ba to waye kuma za tayi wa....Da fadin wannan magana tasa ita kuma sai ta kudiri aniyar cewar in dai itace mahaifiyarsu Wasila to itama ta dauki alkwarin ba zasu ta'bayi masa biyayya ba zai ga rashin tarbiyarta a zahiri. Wasila kuka take sosai tana 'kara kulatar malam mai allo a ganinta duk shine silar fadawarta cikin wannan halin da take ciki, haka kawai zai kama ya daura mata aure da wanda bata so alhalin bashi ke ciyar da ita ba kuma bashi ke shayar da ita ba asali ma kullum cikin aibatasu yake ita da mahaifiyarta ta tabbata kudi Ahamdu ya sakar masa shiyasa ya rude ya yanke mata wannan hukuncin tayi al'kawarin insha Allahu daga shi har Ahamadun sai ta basu kunya auran da suka daura dashi da babu duk daya domin tananan a kan bakanta, sai ta kufce daga gidan. *_A jikin d'an yan zogale akwai Wani abu kamar fure zaku ganshi saman zogale to wannan abin ba karamin sirri bane a tattare da 'ya mace yana mutukar saukar da ni'ima nan take! duk bushewar ki da rashin ni'imar ki idan kina tauna wannan abun na jikin zogale kina matsi dashi sai kin zama 'korama! 'yar uwa ki gwada ki gani zaki bani labari! Ki cire ki sa a bakin ki ki tauna yayi laushi sai ki cusa a gabanki kina zaune a inda kike zakiji wandonki ya jik'e yini zakiyi kina tsarki, amma kuma 'yar uwa ki yawaita tsarki da ruwan d'umi domin in kina da ni'ima! kuma a bude kike kinga anyi biyu babu namiji naso yaji gam!gam! sannan yaji ruwa na gudana a jikinki inda yana sanya jijiyarsa a jikinki zai shi tamkar a cikin teku.....Wannan sirri na baku saboda kauna, ki gwada 'Yar Uwata🙋🏻‍♀️_* Kika futar min da book! Na barki da Allah! Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262*[07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *28* Da sassafe Uwani ta shirya tsaf lokacin ma Rashida bata tashi ba ta kama hanyar Garin garko....lokacin da ta isa garim Malam mai allo na tsangayarsa, ta iske matarsa bitan tana aikace aikace kamar yanda ta saba, Bitan ta shimfida mata tabarma tana mata barka da zuwa Uwani sai cika take tana batsewa tana fadin"Ni fa ba zama nazo ba nazo gurin mai gidanki." Bitan tace."Ayya aikuwa yana tsangaya tare da almajirai sai bayan sallahr azuhur zai shigo! Uwani tayi shiru tana dan tunani, Bitan ta kawo mata ruwa cikin kwanan silva ko kallon ruwan ba tayi ba ta mike tana fadin"Ni zanje tsangayar tashi domin inyi abinda zanyi in tafi." Bitan! tace"Haba Uwani idan hankali ya 'bata nutsuwa aka sawa ta dubu shi kiyi hakuri ki zauna mana har ya shigo gidan sai kuyi maganar ni nasan abinda yake tafe dake. Da fadin wannan magana ta Bitan Sai Uwani ta hau masifa dama 'kiris take jira tace"Ashe kin san abinda ke tafe dani amma kike cewa na zauna wato tare dake aka hada baki aka daurawa 'yata aure ba tare da na sani ba ko? kunga kudi kun rud'e daka ke har Mijin naki gashinan lokacin kankani har naman wuya kinyi to wallahi da sake kamar yanda malam ya tozartani ya wulakantani ya nunawa duniya ni ban isa ba to nima sai na kunyata shi gaban almajiransa. Bitan tace"Ki daina wannan maganar Uwani itafa rayuwa da kike ganinta 'yar sannu ce wannan balo'kokon da kikeyi duk a banza tunda dai aure an riga an daura ai magana ta kare kuma kina maganar munga kudi karya kikeyi mu ba makwadaita bane abin wani bai dame mu kije ki tambaya kiji yanda al'amari ya faru.'' "Babu wanda zan tambaya aini ba yarinya bace da zaki zaunar dani kina min wannan maganar na dauka wallahi idan nice na haifi Wasila sai nasa ta kunyata mijinki tunda bai san ya kamata ba." Bitan! tace"Ai sai kije kiyi tayi mai dora 'yayanta kan turba mara kyau kece zakiyi nadama mara amfani." Uwani ta zura takalmata tana fadin" Ke da mijinki ne zakuyi nadama amma bamu ba aure kun daura saboda kuna samu kwabo da dari to ba zaiyu ba sai na kwance wannan auran wallahi." Bitan! ta bita da kallo cikin tsananin mamaki! tabbas babu abinda yake damun Uwani sai jahilci a irin wannan zamani 'yarki ta auri mutum mai hankali kamar Ahamdu amma kice sai kin warware auran tabbas gaba tana tare da nadama. Uwani na fita kai tsaye tsangayar malam mai allo ta nufa, tun kafin ta 'karasa ya hangota domun uwani ba bakuwa bace a gurinsa, Sai ya gyara zaman sa kan kujerar karfen da yake zaune yana sauraran isowarta, Ganin ta iso inda yake tayi masa 'kerere a ka tare da fadin"Gurun ka nazo." sai ya fara kokarin mikewa daga kujerar ta daga hannunta "Dakata malam yi zamanka ba sai ka tashi ba." Ido ya zuba mata suma almajiran tun sanda ta fara magana suka dakata da karatun da takeyi suna kallonta. "To an yanka ta tashi! duk wani 'kumbiya 'kumbiya da munafurcin da kuka kulla ya fito sarari Allah ya toni asirinka ni Uwani na samu labarin abunda kukayi wa yarinyata Wasila, Na farko dukaninku da kai da 'yan uwanka baku san ci da shan Wasila da Rashida ba tsawon shekaru goma sha, kwabonku bai ta'ba shiga tsakaninmu daku ba, Kuna katsina muna daura muyi aikatau muyi sirfau muyi daukau da duk da sana'ar data kama domin mu ciyar da kanmu kuna a matsayin iyayen Wasila da Rashida baku sani ba, to tur! da wannan zumunci naku Allah ya wadaran irin wannan zumuncin......Sai da na gama shan wahala da 'yayana suka girma suka kawo munzali sannan ne zaka nuna min iko a kansu! bai zai yiwu ba! Shin malam wane irin zagi ne ba kayi min ba wace irin kalma ce bakayi jefe ni da ita ba ! amma kuma saboda tsabar son zuciya katsaham! sai na tsinci labari a gari cewa ka daurawa 'yata aure saboda kwadayin abin duniya! Yanzu bakaji kunyar wannan abun da ka aikata ba."!? Ta kare maganar tana tsare shi da manyan idanunta. Malam jikinsa yayi kwata'kes! tunda yake a duniya ba'a ta'ba tsinkashi cikin jama'a ba irin yau!!! amma babu shakka Uwani ta gawurta gurin rashin kunya da rashin arziki.....Ta sake tsareshi da ido tana fad'in"Kai nake jira ka bani amsa malam."? Gefan babbar rigarsa yasa ya goge gumin goshinsa, Yace."Idan kin koma gidana a nutse zanzo nayi miki bayanin yanda al'amura suka kasance." "Babu wani gidanka da zan koma in koma inyi me? hukunci na riga na gama yankewa shine idan kana takamar kaine waliyin Wasila to nice nan na tsuguna na haifeta saboda haka ka kwana da shirin wannan auran da ka daura shi da niyar biyan bukatar ranka sunanshi lalatacce don ko sati biyu baza'a cika ba sai Wasila ta fito, mu zuba ni da kai." Tana kare maganarta ta kade zaninta ta kara gaba, zuciyarta wasai! yau ta rama irin rashin arzkin da malam yake mata shekara da shekaru. Uwani na barin gurun malam ya sunkuyar da kanshi 'kasa masifar kunyar al'majiransa yake yi babu shakka dukanin maganganun da Uwani ta fada a kanshi gaskiya ne, tun bayan rasuwar dan uwansa Yahuza da ya dauko su Wasilan suka bujere masa tsayin shekaru goma sha biyu bai sai waiwayar inda suke ba daga shi har sauran 'Yan uwanshi, Uwani ita ya kasance take dauki ba dadi da 'yayanta har Allah yasa suka kai munxalin girma.....Hakikanin gaskiya yanzu shima ya gano laifinsa, zumunci ba abun wasa bane a lokacin da su Wasilar suka bujere masa a kwai kuruciya a tare dasu bai kamata yace zai wofintar dasu ba a matsayinsu na wad'anda basu da kowa a garin kano Uwani tayi namijin kokari a kansu da rayuwarsu.......Yanzu ya gano abunda suka aikatawa yaran sam bai cancanta ba kuma duk abinda Uwani tayi masa a halin yanzu bata dai laifi tabbas hakane kamata yayi kafin daurin auran a sanar mata kome zatayi dai na lokaci kankani ne magana ta wuce amma ga yanayin yanda yaga ta dauki lamarin da zafi dole yayi wa tufkar hanci idan ba haka babu shakka tana iya zuwa ta girgid'e wannan auran da ya daura wanda yake sanya ran mutuwa ce zata rabashi.....Ya sake sanya gefan rigarshi ya goge gumi kana ya dago yana kallon almajiransa sai hayaniya suke! bulala ya d'aga Yace."To a cigaba a cigaba.''!!! Su rud'e da karatu ko wannensu da allo a hannunsa. ***** Camas! na tsaye a bakin gate din gidan Ahamdu suna fafatawa da masu Gadi! Magiya take musu suna sake botsarewa "Kinga Hajiya Wanzu Mai gidan ya fita kuma bai sanar damu zuwanki ba, a 'ka'idar shiga wannan gida sai kana da shaida idan kina so mu barki ki shiga to ki nuna mana shaidarki." Daya daga cikin masu gadin ne yake wannan maganar. "Ni bani da wata shaida da zan nuna muku amma nace ku shiga ku shaidawa matar gidan cewar 'kawarta tazo Mai suna Hadiza 'Yar Camas! nasan kuka sanar mata da cewa nice zata baku Umarnin kan ku bude min kofa na shiga. Wanda yayi magana da farko shine ya sake magana da fadi'n " Kinga Hajiya ita kanta matar gidan da kike magana a kanta bata da wannan power din Itama cikin tsaro take babu wanda ya isa ya bamu umarni mu bi idan ba mai gidan ba." Camas! ta saki murmushi tana girgiza kanta, jakarta dake rataye a kafadarta ta fito da ita ta zuge zif din kudi ta dauko daure cikin kyaure ta lissafa dubu ashirin ta mikawa mai maganar....."Kar'ba na lura toshiyar hanci kake bukata babu damuwa idan kun kwantar da hankalinku ma yanzu zan fito." Shiru yayi yana kallon kudin hannunta, Sai ya juya yana kallon sauran 'Yan uwanshi, Sundu'ki! ne ya d'aga masa gira alamun ya 'karbi kudin....Sai ya sanya hannu ya karba da fad'in"To ki shiga amma minti ashirin kacal muka baki kiyi ki fito domin yallabai na iya dawowa da ko wane lokaci." Camas! tace"To babu damuwa yanzu zan fito." Suka bude mata 'karamar kofa ta shiga....Sundu'ki! ne ya tashi da kyar! dake irin mutanan ne masu masifar ki'bar tsiya shiyasa ma ake kiransa da suna Sundu'ki!!! Yace."Dan tsaya anan." Tsayawa tayi ya tafi tinkis tinkis yana duddubawa, Abdulmumini yake nema bai ganshi yaji dadin hakan yasan yaron munafiki ne zai iya fadawa Mai gidan abinda ke da akwai.....Ya dawo inda take tsaye yace muje na raka ki kofar da zata sadaki da cikin gidan....Tare suka jera ya nuna mata kofar daga can nesa godiya tayi ta 'kara gaba da sauri.......Wani abu ta dinga matsawa a jikin kofar......Wasila na takure kujerar palon ta mike zumbur!! bakin kofar ta nufa, "Waye."!? Tafada Camas! Tace" Yi sauri ki bude min Wasila." Jin muryar Camas! ya sanya da sauri ta bude mata kofar!! Tana shigowa suka rungume juna Wasila ta fashe da kuka ta jata suka nufi cikin palon Camas! sai bin ta take da kallo tana bin palon da kallo........A cikin wannan daular Wasila take ita nacan tana yawon bid'id'i! da maza! Tab!!! ai kam ba zatayi yawo ita kadai ba duk yanda za tayi sai tayi ta turgud'e mata wannan auran sun taru sun zama d'aya. Shawarwarin da take tayi kenan da zuciyarta A zahiri kuwa cewa tayi "Wasila ban ta'ba ganin yan iskan mutane ba kamar masu gadin gidanan shegu tsinannu zuwana uku sun hanani shigowa sai da na basu dubu ashirin tukkuna shima da sharadi kan minti ashirin kacal suka yarda nayi na fito......." Rabu da 'yan iska nima ranar sai na mari daya daga cikinsu ai ba laifinsu bane na ubangidansu ne babu babban mara mutunci irinsa." Camas! ta cire karamin gyalan dake jikinta tana kallon Wasilan tace"Wai dan Allah da gaske kike aure ne tsakanin ki da Ahamdu."? Wasila tace."Wannan wace irin magana ce Hadiza? ko zanyi miki karya ai ba zanyi miki irin wannan ba Yau tsayin kwanaki biyar kenan da daurin auren inda yaje jan garinmu aka dauro." Camas! tayi kwata'kes! itafa duk ta susuce! komai na gidan Ahamdu ya tafi da imaninta kai shi kanshi ma so take taji yanayin Jijiyarsa a jikinta sha'awarsa takeyi sosai da sosai. "Tabdijam! amma mutumin nan ya karya miki alkadari sai da aski yazo gaban goshi sannan zai miki haka wallahi ki san yanda zakiyi ki fece! daga hannun wannan mugun mugunta zai miki Jiya da muka zauna metteng Governor yake cewa mutukar ya sake samun hawa kujerar mulki ke zai baiwa mukamin mai bashi shawarwari! saboda ya yaba da kokarin ki a wannan tafiyar shine dalilin da yasa ma nayi duk yanda zanyi na shigo gidanan domin in shaida miki abinda ke faruwa Governor da sauran 'kososhin gomnati hankalinsu ya tashi da faruwan wannan al'mari sunce kuyi kokari ku kufce daga hannun Ahamdu ya aure ki ne ba kyakkyawar manufa ba, kuma kema ki zauna kiyi nazari da kyau ki gani sai da dadin yazo sannan zai miki wannan wulakancin ai wallahi ki nemi mafita tun kafin dare yayi miki. Wata zazzafar ajiyar zuciya ta sauke tace" Camas! na rasa yanda zanyi da mutumin nan Ahamdu! duk inda kike tubaninshi ya wuce nan wallahi! mugu ne! duk wata kafar mugunta da kika sani ya santa, tsakankanin kwanaki biyar din nan ni kadai nasan irin wuyar dana sha a hannunsa sau biyu yana sumar dani.......Har jinya na kwanta, yau ne kawai na dan samu sauki in kin lura zaki gani, babban tashin Hankalina Uwani da Rashida duk da nasan akwai kayan abinci a gidana babu wannan matsalar to amma nasan suna can hankalinsu a tashe saboda rashina." Camas! tace"Gaskiya kam hankalin Uwani ya tashi sau biyu muna zuwa gidanan dasu bamu samu damar shigowa ba to amma jiya naje can gidan naki na kwantar musu da hankali nace yau zanyi duk yanda zanyi na samu ganinki, A nan take shaida min cewar itama taje Can garinku Garko tayi wa mai allo wankin babban bargo sam! itama bata maraba da wannan auran naki." "Ai ki bari kawai Camas! babu babban wanda ya cuce ni irin mutumin nan ni nafi zargin kudi ya kuza masa shiyasa yayi min wannan wulakancin......Wai kamar ni budurwa a bani sadaki na dubu biyar wulakancin yayi tsanani." Camas! tasa dariya tana fadin"Ta'b! amma gaskiya tsohon nan bai da *M* Yo ko ni da nake a fanko ai ba zanyi arha irin taki ba, Wallahi naci alwashin sadakin aurena sisin gold ne da katuwar mota da katon gida......hahahaha kina nan kina 'boye budurci an bada shi kan mafi karancin kudin hahahaha."! Camas! ta dinga shaka mata dariya har da kwanciya. 'Bata rai tayi tace"Kin ga Hadiza bana son iskanci da rashin mutunci! Ki bar dariya Budurcina nan yanda yake dubu biyar din sadaki nan a ajiye ai na fada masa da auran da babu duk daya suke a gurina kar ma yayi tunanin zai samu budurcina shi kuma mai allo duk sanda na kufce daga wannan gidan to ya kwana da shirin garin Garko sai anjimu dashi." Camas! tace"Da kyau! kawata yanzu wane mataki kike dauka na kubutar da kanki daga hannun *Ahamadu Musa."?* _*Yawo babu takalmi a cikin ruwa yakan jawowa mace babbar illah! 'Yar uwa ki lura da kyau! Sanyi na saurin shiga ta kafafu ba zaki gane haka ba sai ranar da ya soma yi miki illah! ki tsare jikinki idan zakiyi aikin ruwa kina kokarin sanya silifas domin kare kanki da lafiyarki*_ Littafin na kud'i ne.....! Kika futar min da book ke da Allah kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *29* ''Kin san Allah Camas! na rasa wane mataki zan dauka na rasa wane tunani zanyi duk kaina ya kulle dana sa'ka wancan tunanin sai na warware yanzu ni ban san yanda zanyi na gudu daga gidanan ba, Ke da kanki kinga irin matakan tsaron daya zuba a gidanan da kyar suka barki kika shigo kuma ina jin sanda yake ce musu mutukar suka bari na fita daga gidan to a bakin aikinsu kuma sai ya dauresu.....Shiyasa jikina yayi sanyi na rasa wane mataki zan dauka a kanshi. Camas! tace"Kina da kudi a accont dinki ko."? "Sosai kuwa ni ban san ma a dadin su ba." Shikkenan ai magana ta kare kud'inki zasu share miki hawaye.....Kin san abinda zamuyi yanzu."? Girgiza kai tayi, Ki bani Atm d'nki a ciro kudi masu kauri muzo mu yaudari masu tsaron kofar gidan na lura suna da bala'in son kudin tsiya tunda dubu ashirin kacal na basu suka amince su cuci ubangidansu ina mai tabbatar miki da cewar kika basu dubu dari ko dari biyu zasu san yanda za'ayi bi futa daga cikin gidanan ba tare da kowa yaji ya gani ba sai yasu yasu." Wata ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi a take taji zuciyarta tayi wasai! da jin wannan magana ta Camas! tace"Haka za'ayi wallahi ni ko nawa suka ce zan basu amma kin san inda gixo ke sa'kar tun sanda nazo ya dauke mim pose da wayoyina Atm dina na ciki yanzu ya za'ayi."? Camas! tace."Kinji wata matsalar kuma ko da yake babu damuwa nasan idan na sanar da As abinda ke faruwa ko nawa ne zai bayar saboda shima ya damu da rashinki wallahi baki ga yanda duk ya susuce ba." Da sauri tace."Yawwa Dan Allah ki mai magana Camas! kuma ki shaida masa cewar wallahi ina fitowa to ya sanya ranshi cewa na zama tashi nayi masa wannan al'kawarin." Camas! tace"Kar ki samu damuwa kawata ni zan tafi, kinga har na wuce mintinan da suka bani." Mikewa tayi tana fadin"Don Allah ki gaishe min Da Uwani kice su kwantar da hankalinsu insha Allahu zan fito da wannan kurkun dana fada." Suna fitowa harabar gidan suka hada ido da Abdulmumini dake bawa shukoki ruwa yayi maza ya ajiye abinda ke hannunsa ya karaso inda take "Madam! akwai abinda kike bukata ne."? Harara ta watsa masa " Bakuwa nayi ko itama bani da damar yi mata rakiya."? Girgiza kansa yayi ya koma bakin aiki. Tsayawa tayi ta fasa raka Camas din bakin gate dan ta lura yaron kamar munafiki ne me yiwuwa idan mai gidan ya dawo ya fada masa ta fito yanxu har shakkarsa takeyi saboda tana jin tsoron kar ya kara yi mata sha'kar mutuwa shiyasa take kaf kaf dashi. Abdumumini yana bawa shukoki ruwa hankalinsa na kansu amma sam ba zaka fahimci hakan ba......''Camas! Ina ganin da kaina zan fara aiwatar da wannan aikin kafin ki sake dawowa ni zanyi kokari gurun ganin na kar'bi pose dina a gurinshi zan fara yi musu bayani duk sanda na samu sarari." Camas! tace"Yawwa kema kiyi kokarin yin haka nima mybe jibi ki ganni." Shikkenan ki gaida gida dan Allah kar ki manta da sa'kona gurin su Uwani." Camas! tayi gaba tana fadin"Insha Allahu daga nan can zan wuce domin na isar da sakonki." Abulmumini na ganin Wasila ta koma ciki sai yabi Camas! da kallo har ta isa bakin gate yana kallon sanda ta dan tsaya suna magana da Sundu'ki! na minti biyar kana taga ya bude mata karamar kofa ta fita....Al'amarin sai ya shiga bashi mamaki ya akayi suka bar wannan 'yar iskar matar ta shigo gidan da kagani ba mutuniyar arziki bace amma babu shakka zai sanya ido sosai a kan lamarin domin shi ba zai yarda a cuci mutumin da ya rufa masa asiri ba. **** Malam mao allo na komawa gida ya sanya babban danshi ya kira masa Kattime da Habibu domin ya shaida musu abinda ke faruwa.....Lokacin da ya gama zayyane musu irin tujarar da Uwani tazo tayi masa cikin almajiransa, dukaninsu sai suka hasala suka dinga zagin Uwani suna tsine mata, ganin yanda suka fusata yasa ya dakatar dasu da fadin"Ku saurara haka, sukayi shiru suna sauraransa sai mai da numfashi suke....Yace."Idan anbi ta 'barawo to abi ta mafi sahu! hakika muma muna da laifi babba kan wannan al'amarin da yake faruwa, Banga laifin Uwani ba akan abinda tazo tayi min na gane gaskiya kuma na amsa laifina da bamu wofintar da Yayan nan ba da babu abunda zai sanya ta samu damar zuwa cikin almajirai na ta fada mun magana, To d'an adam ajizi ne munyi kuskure sai dai mu kiyaye gaba kuma ni babban abinda ke daga mun hankali anan shine kada ta samu nasarar kashewa wannan yarinya auranta shine babbar damuwa ta." Kawu Habibu yace."Insha Allahu hakan ba zata faru ba ni da kaina zan kira Alhajin a waya na shaida masa abinda ke faruwa." Malam yace."To alhamdullahi ga hanya mai sauki dama ina ta tunanin ya za'ayi mu sadu dashi tinda da numbar wayarshi kirashi yanzu sai muyi magana dashi. Habibu ya fito da gudar dari biyu ya baiwa Musa babban yaron malam yace ya siyo masa kati can bakin kasuwa, Ba tare da bata lokaci ba Musa ya karbi kudin ya kama hanya ya tafi. Suna tsaye tare da Khalifa cikin babban boutique dinshi mai suma *A M B* ma'aikata sun kai talatin ko sama da haka suna ta sauke kaya da alama an shigo da sabbin kaya....Shiyasa gurun ya hargitse da yawa, Wayarshi dake hannun Garba ta soma ringing, Garba Yayi saurin mika masa wayar ba tare da ya kalli mai kiran ba ya daga da sallama a bakinsa. Jin muryar mai allo na amsa sallamar ya sanya ya dan risina kamar yana gabanshi ya gaishe shi kunya ce ta kamashi Tun ranar da aka daura aure bai sake waiwayar mutumin ba, Mai allo Yace."Ina magana da Alhaji Ahamdu ko."? Ahamd yace."Kwarai kuwa arrama ni ne ayi min afuwa arrama al'amura sun sha kaina wallahi ina ta so na kira waya nayi bangajiya Allah bai nufa ba." Malam mai allo yace."Ayya ai babu komai Ahamdu. ku da kuke da hurd'od'i da yawa ai dole sai na muku uziri, dama wata magana ce ta taso shine nace to tunda ka bamu numbar wayarka bari na sanar da kai." Ahamdu ya dan bar cikin mutane ya samu ke'bantaccan guri ya tsaya yace."Ina sauraranka malam."! Mai allo yace."Alhaji ba wai zan raba Wasila da mahaifiyar ta bane a'a ina so Yarinyar nan Wasila ta tsira da auranta, mahaifiyar yarinyar nan ta dauki alwashi kan duk rintsi sai ta lalata wannan auran domin ba ta da'de da barin garin garko ba, tazo har inda nake ta tabbatar min da wannan maganar shine na gaza samu nutsuwa nace bari na kira ka na shaida maka ka sanya ido sosai kana kuma ka tsaurara matakan tsaro kan shige da fice a cikin gidanka." Ji yayi jikinsa na tsatstsafo da gumi! Anya kuwa wannan Uwar arziki ce? Bashi da mai bashi wannan amsa, Dan haka sai yace."Gaskiya naji dadin wannan magana taka arrama zan kara kula sosai nima ba zan raba Uwa da 'Yarta ba amma mutukar naga tazo gidana da wata munufa to babu shakka zan sanya a hanata shigowa gidan." Malm mai allo yace."To masha Allahu Alhaji Allah yayiwa wannan auren albarka ka kula sosai insha Allahu zakayi alfahari da wannan auran." Ji yayi ya kara jin kaunar mutumin cikin ranshi bai san abinda yasa yake son auransa da yarinyar ba kullum adduarsa Allah yasa auran nan yayi albarka shi kuwa zai yi kokarin ganin ya rike yarinyar da kirki duk wani alwashin da ya dauka a kanta zai sauke su.....Sallama sukayi da juna cikin mutunci da mutuntawa.....Ya katse wayar sai yaji duk hankalinsa yayi gida ya iske Khalifa tare da Manager suna magana yace."Khalifa ka tsaya komai yayi Clearing ni zanje gida yanzu." Khalifa yace."Lafiya dai ko."!? Yace."Normal ba zan dade ba zan dawo insha Allahu." Yana gama maganar ya juya da niyar tafiya Garba da Hadi suka rufa masa baya. Ya dad'e tsaye a harabar gidan nashi a tsaye yana nazarin ko ina da ina na gidan.....Har masu tsaron kofar shiga gidan suka soma shan jinin jikinsu mussaman Sunduki da yayi 'kas! da kansa yana Allah Allah ya bar gurin babu shakka Alamun mara gaskiya ko a cikin ruwa gumi yake domin dai Sunduki wani irin gumi ne yake karyo masa yana jin tsoron kar yallabai ya fahimci abinda ke da akwai!!!! AbdulMumini ya karaso inda yake tsaye hannunsa rungume da tarin kayansa wanda ya wanke su tas ya gogesu ya shiryasu cikin wata leda mai sheki! gaisawa sukayi Ahamdu na tambayarshi aikinsa. Abdumumini yace."Aiki alhmdullihi Yallabai." Ahamdu yayi gaba da niyar shiga cikin gidan Abdulmumini ya rufa masa baya hannunsa rungume da kayan wanki........Dan juyowa yayi yace."Dakata nan tukkuna."! Abdulmumini yaja ya tsaya, A hankali ya sanya hannunsa jikin kofar yana latsawa......Tana can cikin daki a kwance abin duniya ya taru yayi mata yawa taji alamun ana so a shigo da sauri ta diro daga gadon ta nufi kofar fita, Allah yasa tayi wanka ta shirya cikin wani les mai ruwan goro (orange colour) yayi mata kyau sosai yayin da dinki ya zauna das a jikinta, sai kace an gwadata bata daura dankwalin ba sai ta lullube jikinta dashi, tun kafin ta karasa bakin kofar palon ta hangoshi tsaye dake kofar tana nuna mutum amma shi wanda yake waje bai ganin na ciki sai dai na ciki yaga mai shigowa, Ta bude a hankali taja gefe guda ta tsaya, juyawa yayi kawai ya kar'bi kayanshi dake hannun Abdulmumini ya sallameshi da fadin"Jeka kawai." Abdulmumini ya bar daga gurin da sauri....Shigeta yayi ba tare da ya tanka mata ba ya nufi bedroom dinshi.....Yana shiga ya tadda shimfidar bed din a hargite duk pillows din sunyi d'ai-d'ai kasan kafet din ragowar abincin da taci ga plate da goran ruwa da lemo duk a ajiye ko ina yayi kaca kaca babu kyan gani.....Wardrobe dinshi ya bude ya ajiya kayanshi yana dan jan tsaki ya fito ya sameta zaune kan kujera ta zuba tagumi. 'Bata rai yayi yace."Tashi kije ki gyara min daki." Ta kalleshi cikin wani irin yanayi Yace."Ban son kazanta bana shiri da kazamin mutum ina amfanin kin gyara jikinki baki gyara makwancin ki ba to daga yau kar ki sake kwanciyar min a daki ki dauki daya cikin dakunan dake palon nan bana son kazanta." Ranta ya 'baci dajin irin bakaken maganganun da yake ya'ba mata sai dai ta daure kawai saboda tana neman biyan bukatarta, ba tace masa komai ba ta mike a hankali ta nufi dakin....Bayanta yabi da kallo yana ayyana abubuwa da yawa a kanta kwana biyu yaga ta soma yin sanyi Allah yasa ta d'ore.....Yana kokarin shiga sukayi karo ta dauko plate din dazu zata fita dashi......Dauke kansa yayi ya wuce Lokacin kirjinsa ya gogi nata yaji wani irin yanayi a jikinsa sam! baya so yanayin da yake ji a jikinsa yayi tasiri kan yarinyar shiyasa yanzu ko kallonta bai fiye yayi dan yaji haushin Allah ya isan da tayi masa, Tana shiga dakin ta ganshi ya sunce kayan jikinsa yana kokarin daura towel tayi saurin dauke kanta ta nufi toilet da sauri gabanta na wani irin faduwa! Manta abinda ya shigo da ita toilet din tayi sai ta hau duru-duru!!! can taji alamun zai shigo tayi saurin Kwance pampo tana wanke fuskarta sai sannan ta tuna abinda ya shigo da ita, can wani guri ta nufa cikin toilet din dai ta dauki tsinsiyar laushi da makwashin shara, kanta a 'kasa zata fita suka buga karo yana daure da towel iyakacin sa ku'gunsa kirjinsa a waje! gigicewa tayi har sai da yaso ya fahimci hakan! tayi saurin ra'bewa tayi zata wuce ya matse hanyar yana yi mata wani malalacin kallo....Kas da tayi da kanta kamar munafuka duk ta muxanta mutukar za taganshi a haka! babu suttura wata irin shakkarsa takeji da tsoronsa, "Yau waye yazo gidanan."!? Ya fadi maganar yana tsareta da idananunsa dake mutukar saukar mata da kasala da mutuwar jiki. _*'Yar uwa ga shawara: Idan kina dauraye gabanki da ruwan sanyi bayan kun gama mu'amula ta aure da mijinki (sex) to ki daina domin yin hakan yakan iya janyo miki matsala babba, duk sanda kuka gama mu,amula ta auratayya da mijinki to ki samu ruwa mai dumi ki wanke gabanki tsaf! kana ki daura wankan janaba! kar ki saba kwanciya da janaba a jikinki komai rintsi idan kina da toilet a daki ki tanadi ruwanki idan baki da toilet a daki to kiyi addua dai-dai gwarwado Allah zai kare ki da kariyarsa ki fito ki tsarkake jikinki.....Ke kanki sai kinfi jin dadin hakan, Barin janaba a jiki na haifar da matsala babba na farko nan da nan idan an shiryo miki wani sharrin ya same ki a take saboda rashin tsarki, Na biyu shaidanu zasu dameki wannan najasar dake jikinki suma zasu zo su dora miki tasu ki tashi da ciwo ko dai wani abu makamancin haka......Allah yasa mu dace.*_ Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book ke da Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *30* Kasa hada ido tayi dashi ballanta ta bashi amsar tambayar da yake mata gabanta faduwa kawai yake yi tana adduar Allah yasa ba wani ne ya fada masa cewar Camas! tazo gidan ba, Hannunsa yasa ya dago fuskarta dake sunkuye ya kura mata idanunsa, duk sai yaga alamun rashin gaskiya a tare da ita,Yace."Dazu Kawunki wanda ya bani auranki ya kira ni a waya ya fada min wata magana, Idan kin san maganar gaskiya ce cewar mahaifiyarki tazo gidanan domin ta lalata miki aure to tun wuri ki hanata zuwa gidana, idan ba hakaba zan dauki mataki a kanta a da na aureki ne domin in wulakantaki kana kuma na karya alkadarinki na sake ki, to sai daga baya kuma na janye wannan 'kudirin nawa saboda darajar wannan dattijon mutumin wato Mai allo, yafi gaban na watsa masa 'kasa a ido ki godewa Allah Kawunki na sonki da alkairi duk wannan abun da yake nunawa a kanku kauna ce ba tsana ba, kinci albarkacin masu albarka zaki zauna tare da Ahamdu babu saki a tsakaninmu mahaifiyar ki karta 'kara zuwar min gida da manufa mara kyau! zan sanya su Garba su dauki mataki a kanta." Fuskarta ta fuxge dake tafin hannunsa tana watsa masa harara kwalla ta cika kwarmin idonta, bakinta na rawa tace"Mahaifiya ta kake kokarin ciwa mutunci a gabana."!? Yace."Meye abin cin mutunci anan gaskiya ce na fada." Girgixa kanta tayi tana kokarin had'iye wani 'kululun ba'kin ciki da yazo ya tokare mata a ma'kushi! Tace." To kaje ka fad'awa wanda ya fada maka cewar mahaifiyata tazo gidanka cewar Shi din azzalimi ne kuma ni banga gatan da yayi min ya zalince ni da ya had'ani aure da kai mugu mai ba'kar aniya.''! Cike da d'umbin mamaki yake kallonta, ashe rashin kunyar yarinyar har ta kai haka kamar wannan mutumin take kira da azzalimi me yayi mata na zalinci ta kira malam mai allo azalimi shi ta kirashi da mugu mai ba'kar aniya.....Al'amarin ma dariya ya bashi ya fahimci taji ciwon maganarshi kan mahaifiyarta, ya girgiza kai kurum yana kokarin shiga toilet din ba tare da ya tanka mata ba, taso yace wani abu daga nan ta zazzageshi in yaso ko mai zai yi mata sai da yayi mata, Duk lalacewar Uwa uwace tana masifar kishin iyayenta mussaman Uwani da duk wahalarta a kansu ta kare shiyasa suke fad'a da mai allo mutukar zai zagi Uwani a gabanta sai tayi masa rashin kunya sam basa shiri dashi ta gane kuma munafiki ne shine ya tunzura Ahamdu yazo yana kokarin zagar mata uwa." Hawayen da take ta kokarin dannewa sunki dannuwa dole suka fara zuba, Ta juya yayin da yake kokarin hada ruwa miyau! ta tofa masa a bayanshi, Yayi saurin juyowa yana kallonta, shi ya d'auka ma tuntuni ta fita ashe tana tsaye, hawaye ya gani na karakaina a fuskarta, shifa bai ga abin kuka da damuwa anan ba, ai bai fadi wata mummunar magana kan mahaifiyarta taba, Had'a ido sukayi tace"Allah ya isa na Allah ya bimin hakkina." Ya shiga mamakin Allah ya isan da take masa, Nufar ta yayi tayi kamar ta gudu sai kuma ta yanke shawarar tsayawa wallahi ya daketa sai ta murd'e masa mazakuta! ta kasheshi kowa ya huta shawarar data yanke kenan....Koda ya 'karaso inda take sai taga akasin haka, dankwalin kanta ya fuzge ya mika mata fuska a hade yace."Goge min kazamin Yawun ki da kika tofa min." A hargitse tace."Wallahi rantsuwar dan musulmi ba zan goge ba ko kasheni za kayi sai dai ka kashe."! Ya girgixa kai tare da fadin"Ni dai na fad'a miki dan na lura kin ji zafi kan maganata okey Yanzu dai bani da lokacin ki amma ki kiyaye shiga hannuna zaki gane baki da wayo." dankwalin yasa ya goge miyau din ya jefa mata a fuska, taja tsaki mai karfi ta futa daga toilet din, rashin a 'bace yayi wanka ya fito......Still kuka ya tada ta tanayi sosai idanunta sunyi jage jage da hawaye, sai ya dan ji tausayinta ya kamashi, babu shakka tana da kishi kuma duk rashin kunyarta tana martaba iyayenta, shi dai yasan bai fadi mummunar kalmar da zata tada mata da hankali ba amma ta zauna tana kuka, hakane shima nada kishin iyayensa yana gani aka taba martabarsu sai inda karfinsa ya kare, Kaya ya sauya ya fesa turare hade da daura agogo ya dora hula saman kanshi ya kama hanya ya fita daga dakin yana jin shashshekar kukanta har cikin dodon kunnansa. Ta jima xaune a dakin tana wannan kuka tana kuma tunanin yanayi na rayuwa, a duniya dai babu wanda yafi saurin 'kaskanta sai talaka idan baka da kudi sai a zage ka a tozarta ka a gabanka yaushe Uwani tazo gidansa da har zai tasa ta a gaba yana cin mutuncinta, Tunda suke 'yar tsama dashi bai ta'ba 'kuntata mata irin yau ba ta dinga jin wata iriyar tsanarsa na d'arsuwa a cikin zuciyarta shi kanshi malam mai allon mugun haushinsa takeji a ganinta duk shine yake 'kara rura wutar al'amarin........Da kyar ta tashi tayi sallah magariba ta zauna har aka tayar da isha'i ta gabatar da sallahr sai ta kwanta kan daddumar bakin ciki duniya ya taru yayi mata yawa. Sai wajejan goma da rabi na dare Al'amura sukayi sauki a babban boutique d'in...(Gurin sai da 'kananun kaya irin na yara da na manya maza da mata takalma irin su booth helf cover da na yara da manya duk zaka samu a gurun a goguna masu kyau deznar iri iri akwai a gurin kai mutukar kana so ka had'a dreesing na kece raini to idan ka shiga gurin ka gama saboda zaka samu duk wani abu da kake bukata )kayan dake cikin boutique din *A.M. B* Na mussaman ne dan sai ka gama xagaye kafatanin kasuwar kwari da sabon gari wambai da duk sauran kasuwanni baka samu irin oder shi ba Ahamdu na kawo kaya masu kyau da 'karko shiyasa kullum a gurin a ciki yake da Costoms duk wani ko wata mai ji da kansa burinshi ya shiga gurin yayi siyayya......Har wannan lokacin suna tare da Khalifa sai bayan sun tabbatar da komai yayi clear sannan suka wuce gida........ Khalifa na draving yace."Afnan fa ta damu kullum kuka takeyi wai sai ankaita gurin auntynta tun sanda taji muna maganar da momynta zamuje gurin amarya shikkenan take rigima wai a kaita gurin aunty amarya ita dai." Dariya yasa yace."Ai ni rigimar wannan yarinyar ita ke had'ani da ita haka kawai tazo ta hanani baccin dare tayi zamanta wallahi bana nemanta.' Khalifa yace." Kai dai kawai kace kar tazo ta hanaka amarci wa zaka mayar karamin yaro okey shikkenan tun da haka kace sai na kawo ta dan haka gobe ka shirya zamu zo tare da momynta kuma tare da kayanta zamu zo tunda anyi hutun skull sai ta zauna ta d'ebewa amarya kewa." Murmushi yayi ya dan tura hularshi 'keye yace."Kai a tunaninka amarci nake ci da wannan yarinyar? lallai Khalifa ka mance dalilin da ya sanya na aureta ko, shin mai zai sanya ni na 'bata lokacina a kanta da har zanci amarci da ita." Khalifa yace."Bafa zan dauki wannan maganar ba Alaji nasan dai idan bakayi me gabadaya ba to nasan kana tatta'ba ta dole ne nasan ba zaka sanya mata ido kawai kana kallonta ba." Murmushi yayi yace."Malam kai kake wannan tunanin ni sam! wannan yarinya bata bani sha'awa." Dariya kawai Khalifa yayi yace."Mubar maganar kawai ni dai ba karamin yaro bane na kuma san abinda za kayi da wanda ba zakayi ba Har cikin gidanshi Khalifa ya ajiye shi dake a motarshi suke ya bude motar ya fito suna sallama, Khalifa yace."Ka fadawa amarya idan Allah ya kaimu gobe tana da babbar bakuwa saboda haka sai ta shirya." Yace."Ni dai tunda ba bakuwa ta bace shikkenan." Ya juya yana kokarin shiga ciki Khalifa yace."Kayi mantuwa fa." Sai sannan ya tuna shi masa site din baya ya bude ya dauko wasu manya manyan ledoji guda biyu yana fadin"Na manta shaf wallahi." Garba ne ya karaso gurin yana musu barka da zuwa ya mika hannu ya karbi ledojin hannunsa, gaba yayi da ledojin a hannunsa shi kuma ya tsaya suna sallama da khalifa. Tsit! palon tamkar babu wani mai rai a ciki....Ya nufi bedroom dinshi nan ya tarar dashi kaca-kaca har yanzu shimfidar gadon a hargitse take kamar dai yanda ya fita ya bari sannan ga tsintsiya da makwashin shara nan a tsakiyar kafet gashi kuma bata dakin kamar yanda ya saba idan ya shigo ya ganta kwance tana bacci bata dakin yau! Ya ajiye ledojin hannunsa ya fita daga dakin.....Bedroom din dake kusa da nashi ya murda yaji a kulle gam ya wuce dayan shi yana murdawa ya bude babu kowa a ciki....Ya bude ba kusa dashi shima bata ciki zarginsa yafi tabbata akan ta kulle a cikin wanda ya murda yaji a rufe.....Ya dawo a gajiye shi mai zai iya asalima tsintsiya bai iya rikewa ballanta ya iya wata shara dama su Garba ne suke masa aikace aikacensa, dan haka ma yanzu Garban ya kira yace ya shiga ya gyara masa daki shi kuma ya zauna a palo yana duba wayoyinsa yini guda yau bai duba wayar ba test messages gasu nan rututu haka dai ya dudduba wad'anda zai iya ya bari......Mutum ne shi ma'abocin jin zafi dalili kenan da ya sanya ba ya zama da manyan kaya a gidanshi mutukar yana gida zaka same shi da gajeran wando iya gwiwa da shart ko kuma singilet ko cikin kayan bacci yafi tu'ammali da masu mad'aurai da botira idan ya ga dama ya daure ko yasa botiran idan bai ga dama ba ya bar kirjinsa a bude, yanzu ma wata irin zufa ce take keto masa ba abinda yake so sama da ya watsawa jikinsa ruwa, Garba na fitowa ya mike ya nufi dakin Garba ya d'ebi wayoyinsa ya bi bayansa dasu. _*Sanyi ko Basir na sanyawa gaban ki ya 'bude!!!! ki Haihu ki'ki kula da gabanki shima na sanya wa ki bud'e ba tare da kin fargaba, Namijin dare (ba'kin aljani) idan yana kusantar ki ya kan janyo miki masifar bud'ewar gaba, kuyi ta rigima da miji idan da tsautsayi da rashin hakuri sai kiga an rabu!!! wane mataki ya kamata mu dauka domin mu kare kanmu daga fad'awa cikin wannan tashin hankalin!?*_ Littafin na kudi ne........! Kika futar min da book! Ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *31* Koda ya shiga dakin kai tsaye toilet ya nufa yayi wanka ya fito sanye da rigar wanka, tsayuwa yayi gaban mirror ya goge jikinsa kana ya shafa vasilin a jikinsa gami da turaran jiki ya sanya Karamar t-shart mai yankakken hannu da boxer tamkar wani sauri dan 20 years haka ya dawo kuruciyarsa ta fito fili dama kuma in dai zai sanya 'kananun kaya haka yake zama dan saurayi sosai suke masa kyau sai da kuma bai da ra'ayin sanya su ya fita 'karkarin shi ya sanya a gida kawai....Parlor ya fito ya nufi daining komai tsaf tsaf Rabe ya jere masa kayan abinci babu alamun an ta'ba komai a gurin.....Cikin mamaki ya fara bude kulolin abin bai ga alamar wani ya d'iba, ya zuba iya dai-dai cikinsa yana ci a nutse yana had'awa da lemo, tunaninsa duk ya ta'allaka ne kan yarinyar babu shakka shima sai yanzu da ya zauna yayi nazarin abinda yayi mata yaga bai kyauta ba, bai kamata yayi nufin tozarta uwarta a gabanta ba duk lalacewar uwarka ba zaka so wani ya ci mata mutunci a gabanka ba, amma baya jin ko da wasa zai iya tunkarar ta da niyyar ya bata hakuri idan ta gaji da fushin za ta daina........Sai misalin sha biyu da rabi ya bar palon.....Yau kadai da zai kwanta shi kadai a dakin sai yaji wani iri tsayin kwanakin da tayi a gidan tana kwana a dakinsa har ya saba da hakan duk da kafin suyi bacci dukaninsu sai suyi fada sau nawa hakan nayi masa dadi in dai zai ga giftawarta a dakin, shi kanshi ya fahimci zuciyarsa ta damu da yarinyar kuma ya soma zargin wani abu ya soma ziyarta zuciyarsa dangane da yarinyar.....Da kyar! bacci ya dauke shi mai cike da tunani da mafarkin gashi yana saduwa da ita. To itama nata 'bangaran hakane ya kasance....Tun rana da suka rabu ta kudiri aniyar bar mishi dakinsa tunda ya kirata da kazama, har yana mata gorin daki kana kuma yana cin mutuncin mahaifiyarta a gabanta yasa taji sam ba zata iya had'a numfashi dashi ba domin wani irin tsanar sa takeji a cikin zuciyarta, haka ta kwana ba taci abinci ba tun bayan abincin da taci da rana har garin Allah ya waye babu komai a cikinta. Shida dai-dai na safe! Ya fito daga bedroom dinshi cikin shigar Kayan motsa jiki wani wando ne da rigarshi masu dan kauri wandon iyakacinsa gwiwa kuma ya matse masa jiki sai rigar mai yankakken hannu itama ta kamashi sosai power dinshi ya fito kafarshi na sanye da booth, ya nufi kofar fita ba tare da yayi tunanin buga kofar dakinta ba yasan 'batawa kansa lokaci zaiyi kawai idan ya gama abinda yake ya dubata.......Ke'batancen gurin da gym dinshi yake girki ya nufa, Ya hau kai ya soma yi babu ji babu gani Garba da Hani na tsaye a gefan hagunshi da damanshi, Ya jima kan Gym din kafin ya sauka ya kwanta kasan gurin yana hutawa, sararin samaniya ya zubawa ido yana kallo yana mai da numfashi Garba ya miko masa sassayan ruwan swn ya mike zaune ya karba ya fara tuttulawa cikinsa, a kuwa gumi ya yanke masa kamar wanda ya watsa ruwa, wata iriyar kwanciya yayi ya soma training a haka ya kai ya kawo haka ya dinga yi ko wace jijiya dake jikinsa ta mike gashin jikinsa ya mike tsabar yanda jikinsa ke budewa, sai da ya kai kimanin minti talatin yana mota jikinsa a kwance kana ya saurara, ya kar'ni karamin towel dake hannun Hadi, yana goge jikinsa Kira ne ya shigo wayarshi dake hannun Hadi yana daga kwance ya mika hannunsa ya 'karba, Hajiya babbah ce! mikewa yayi zauna ya kara wayar a kunnanshi ya risinar da murya yana gaisheta ta amsa da sakakkiyar murya tana tambayarsa iyali! sai yaji wani iri jin abinda tace wai ya iyali? ya waske da fad'in"Lafiyarsu lau hajiya ya gida kwana biyu uzirrika sun sha kaina ban samu na shigo mun gaisa ba." Tace."Aikam dai jama'a nata cigiyar ango ranar da nayi yini na da jama'ata kowa haka ya hakura, duk sunayi maka Allah ya sanya alkairi." Ya amsa da "Ameen Hajiyata mybe gobe ki ganni insha Allahu." Tace."To to ai sai mu d'aga tamu tafiyar tunda zaka zo da mun shirya zuwa gidan naka tare da matan Kawun ka Almu." Yace."To babu laifu Hajiya sai kunzo din zan tsaya jiranku duk da ina da babban uzirin da zai fitar dani goben amma babu matsala naji dadin zuwanku." Tace."Ai ba za'ayi haka ba kuma kada mu katse maka hanzari." Yace."Ko wane irin hanzari gareni idan ina neman albarka dole in tsaya in saurari zuwanku." Taji dadin maganarshi sosai tace"To Allah yayi maka albarka Ahamdu kaima Allah ya baka 'yaya masu yi maka biyayya." Ya amsa da "ameen ya rabbi nagode. Sallama sukayi ya mikawa Garba wayar kana ya mike da towel din a hannunshi yana karkade gwiwarshi da ta dan 'baci! Yace." Garba zan shiga in kwanta in huta yau babu in da zani Khalifa nan zuwa tare da iyalinshi idan ya kira waya kace na kwanta nasan sai bayan axuhur za su shigo lokacin na matse insha Allah." Garba yace."Okey sir zan fad'a mishi insha Allahu." Ya kama hanyar shiga cikin gidan.......Suka ce a tashi lafiya Yallabai." Ya amsa da "ameen." Yana daga musu hannu.....Dai-dai lokacin da ta fito daga dakin da take a dai-dai lokacin ya shigo palon......Sai da ta kusa faduwa saboda razana! masifaffiyar yunwa ce ta fito da ita wacce take baraxanar cinye mata 'yan hanji taji zata mutu ta futu afujajan domin samawa kanta abinci....Shi kuma wannan motsa jikin da yayi cikinsa kamar anyi masa yasa haka yake ji sai kokawa 'yayan hancinsa sukeyi...Kalon kallo aka shigayi tsakaninta dashi, fuskarsa akwai alamun sassauci ba kamar ko da yaushe ba, Juya tayi ta koma dakin fuskarta babu walwala har yanzu haushinsa takeji......Girgiza kai yayi ya nufi daining din, Rabe ya shirya break fast kamar yanda ya saba, a nutse ya had'a komai da kanshi ya zauna yana karyawa hankali a kwance. Gefan bed ta zauna ta zuba tagumi! abin duniya yayi mata yawai wai shin ya za tayi da wannan kad'dararran auran da aka la'ka ba mata, komai na rayuwarta ya tsaya! ta taso da kwajinta da bajinta an tsugunar da ita guri guda, wai me take jira ne? da ba zata nemawa kanta mafita ba, Wata zuciyar tace mata "Ta ina zaki nemawa kanki mafita cikin wannan gidan dake tsautsare da matakan tsaro? Shawarar Camas! itace abun dubawa dole duk haushinsa da takeji ta saki jiki dashi ta samu ya bata Pose dinta domin tsira da muhiman abubuwanta dake ciki, sashe na zuciyar ta yace mata " Kinga idan yaga kin saki jiki a gidan kin karbi auran hannu bibbiyu to zai dauka kin hakura xaki zauna zaman auran dashi kuma zai sassauta matakan tsaro a kanki daga nan sai ki samu damar guduwa abinki ki kai su 'kara kotu daga shi har malam mai allon.! Wannan shawara ta yanke a zuciyarta. Yana gama break fast dinshi ya nufi bedroom dinshi wanka yayi ya fito ya shiya still cikin 'kananun kayan dai, farare tas riga t_shart da wando 3Qutar mai aljuhunai gaba da baya, gaban rigar hoton zuciya ne an rubuta heart da bakin rubutu, sosai yayi kyau ya taje saisayayyiyar sumarshi mai tafe da sajensa cikin tsari! ya fesa turarenshi mai dadin kamshi, har yayi nufin kwanciya sai idanunsa suka sauka kan ledojin da ya shigo dasu jiya da daddare , 'Kananun kaya ne ya shigo mata dasu yasan za tayi amfani dasu tilas watarana, daukar ledojin yayi ya bude dakin......Idanunsa suka sauka a kanta zaune kan kujerar daining din da cup din tea a hannunta tana kurba tana hadawa da plantain, Ya karasa kusa da ita saitin kafafunta ya dure ledojin ''Gashinan nasan zasuyi miki amfani watarana." Kamar yanda bai kalleta ba sanda yake maganar haka itama ko inuwarsa bata kalla, Har yayi nufin barin gurin sai kuma ya tsaya ya d'an kalleta da gefan ido, Yarinyar nada wani irin madarar kyau! gani yake har yanzu bai gama saninta ba kullum sai ya sake ganin abinda ke burgeshi a jikinta....."amm!!! Magana yayi niyyar yi sai kuma ya dagata, Ta kalleshi sa kwala kwalan idanunta da suke furgita 'yan maza! ta wani risinar da kwayar idon cikin tashi tana masa wani malalacin duba, ta lura da akwai magana a bakinsa sai kawai ta dauke kanta tana cigaba da kurbar tea din a yangace sai kace wata d'iyar sarakai!! Hakan da tayi masa yasa yaji wata irin shakkar ta abinda bai ta'ba faruwa dashi ba kenan ace yana jin shakkun yiwa wata d'iya mace magana, Dauriya ya aro a take yace."Idan anjima muna da baki! nasan dai zaki shaida babban abokin nan nawa Khalifa, shine zai zo tare da Iyalinshi."! Ya kare maganar idanunsa tsaye a kanta. Ta'be bakinta tayi ba tare da tace masa komai ba.....Yasan taji abinda yace, sai bai tsaya sauraran iskancin da take masa ba ya kama hanya ya shige bedroom dinshi ya kule yayi kwanciyarsa. Tana kammala breakfast din ta dauki ledojin da ya ajiye mata ta shiga dasu dakinta. Zazzagesu tayi kan bed tana duddubawa, had'addun kananun kaya ne da wasu lafiyayyun kayan bacci amma kuma tsaraicinsu ya fito fili duk da ita kadai ke kwana ba tajin zata iya amfani dasu a jikinta saboda tsaro....Za dai tayi amfani da kananun kayan domin sun burgeta, dogwayen wanduna ne masu mannewa suma rigunan irin masu kama jikin nan ne da budaddan wuya, wasu ma babu hannu sai dai wasu 'yan igiyoyi sune ma dadin hannun rigar, duk wannan tana ganin zata iya saka su ai ba wani abu bane domin ita dai a rayuwarta tana masifar son kananun kaya tun ba da tasan suna mata kyau ba......Wanka ta shiga tayi ta fito daure da towel tsaye tayi gaban mirror tana gyara gashinta ta daureshi da katon ribbon ta tattaro gashin ta gaba ta tufke yayi jela ta sake shi yana reto a gadon bayanta, turaran jiki ta shafe a jikinta ta dan shafa mai sama-sama ba tare da tasa pant ko breziya ba ta dauko wasu shegun kaya cikin kayan dazu ta tusa a jikinta, Wow! Ita kanta sai da tayi mamakin yanda kayan suka kar'be ta sai wani juya takeyi sassan jikinta na motsawa ko yaya tayi motsi nonowanta sai sun motsa, ga d'uwawukanta sun wani fito radau sun kame guri guda rigar ta manne a jikinta harta da nipples dinta sai ta nuna, kayan sun kasance bakake ne masu taushin gaske, Duk da cewar Wasila ba fara'a bace kayan basu sanya ta muni ba sai ma wani bala'in kyau da sukayi mata,Sosai duk wanda ya ganta cikin wannan dressing din yayi sha'awar ta zama tamkar wata fure dan kyau, ta kama hanya a hakan ta fita palo tayi zamanta kan kujera tana kallo hankalinta kwance. _*Kamar yanda na fad'a a pege din da ya gabata cewar barin najasa ko wace iri ce itake kawo shafar jinnu Haka ne 'Yar uwa idan kina cikin al'ada ma'ana kina jinin haila duk rintsi kar ki kwanta sai kin daura alwala wannan alwalar da kikayi itace garkuwa a gareki.....Idan kun gama mu'amular aure da mijinki kiyi wankan tsarki idan akwai uziri ki daura alwala za ta zame miki garkuwa amma dai anfi so a wanke wannan janabar, Matsalar dake sanya kenan har Namij dare (bakin aljani!) ya aureki kenan kin bar janaba a jikinki yazo ya kwanta dake shima yana saduwa dake ba tare da kin sani ba, wannan ba'kin aljanin yana wa mata da yawa illah kuma da yawa mune muke jawo shi jikinmu saboda sakaci da rashin kula da tsare tsaraicinmu da kula da ibadah!!! Idan kina kaf kaf da jikinki kina kuma hirji da azkar to komai najin bakin aljani dole ya gusa daga inda kike....Allah ya kare mu da kariyarsa👏🏻*_ Littafin na kudi ne....! Kika futar min da book Ke da Allah kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *32* Mintuna talatin da zamanta a palon aka soma Knocking din 'kofar, ta d'an tsurawa kofar ido daga inda take zaune tana so ta fahimci wanene duk ba sosai take ganin shi ba, sake knocking din kofar akayi, tace"Waye ne."? Garba yace."Madam ni ne yallabai yayi 'baki Abokinsa ne tare da Iyalinshi, gashi duk wayoyinsa na hannuna." Shiru tayi tana nazari! tace."Okey yana bacci yanzu." Garba yayi shiru yana tunanin maganarta shi yasan muhimancin Khalifa a gurin abokinsa duk da yasan 'ka'idar abokinshi ce ba, a tashin sa daga bacci har sai ya tashi daga kansa, ai yana da kyau ta bude musu kofa su shiga, ya lura 'yar masifa ce yarinyar tun sanda ta mari daya daga cikin sucurites din gidan yake shakkarta haka kawai da mutuncinsa da komai ta tsinkashi a cikin mutane shiyasa baya shiga lamarinta tunda shi kanshi wanda suke zaune a gidan dominsa bata saurara masa ba, a babu wanda zata saurarawa duk zafi! irin Yallabai din, ya kasa kata'bus! a kanta sai rashin arziki take a gidan. Ganin har yanzu tana ganin inuwarsa a tsaye a bakin kofar yasa ta kira sunanshi "Garba."! ya amsa da sauri! tace" Bari na tashe shi shikkenan ko."? Yace."To madam."! Mikewa tayi ta nufi dakin, tasan baya so a tashe sa a bacci shiyasa ta 'kuduri aniyar ba'kanta masa rai! shima yaji in da d'ad'i! handile ta murda kofar ta bude, ta hangoshi kwance kan bed ya rungume fillo gam bacci yake sosai, ya dan rufe kafafunshi da bargo! A hankali ta isa inda yake ta tsaya tana kallon fuskarsa, kyakkyawa ne sosai sai dai babu kyan zuciya, kirjinsa ta kalla duk da ba'a bude yake ba sai da taji tsigar jikinta ta tashi, a take taji wani irin yanayi na ziyartar jikinta idonta ta lumshe ta sake bude su a kansa ajiyar zuciya ta sauke me zafi! kana ta bude mirya sosai tace"Ka tashi kayi ba'ki!!.'' ka tashi kayi ba'ki."! Wannan kalmar tayi ta nanatawa, ya soma jinta cikin baccin sa kamar mafarki yake yi sai kuma ya bud'e idonsa, da sauri!!! a take kanshi yayi wani irin sarawa, dishi dishi! yake ganinta kafin idanun su bude tar!! a kanta, Tana tsaye 'kerere a kanshi still tana maimaita maganar dake bakinta, "Ka tashi kayi 'baki."!!! Ya dafe kanshi dake masa wani irin ciwo! idanunsa suka burkice! har yaushe ya kwanta baccin da za a tashe shi? wane irin ba'ki ne wannan sam baiyi tsammanin Khalifa ba ne domin baiyi tunanin zasu zo da wuri!! Gabanta ne ya fad'i! ganin yanda duk ya wani jirkice idanunsa sun kad'a sosai! sai ta kama hanya zata futa....Hannunsa ya sanya ya fuzgota tayi zaman da'baro kan cinyarshi....Da sauri da sauri ta dinga jin saukar numfashinsa saitin wuyanta, kafin taji sha'kakkiyar muryarsa yana fad'in" Ban hanaki tashina daga bacci ba ko so kike ki kasheni."!? Jikinta ne yayi kwata'kes! tayi yunkurin mikewa ya matse ta sosai a jikinsa, Wuyansa ya d'ora kan kafadarta ya kwantar da kansa sosai, idanunsa ya rintse yana jin wani irin hajijiya a saman kanshi (jiri) Gabanta ya dinga faduwa tana ta so ta kwace jikinta ta kasa domin ya riketa tsam! duk ya kanainayeta a jikinsa........A hankaki a hankali jirin ya soma sakinsa, ya dan bude idonsa da sukayi masa nauyi yana kallon bayanta, idananunsa ta sauka kan kwantaccen gashin da yabi lafiyayyar fatar wuyanta yabi ya kwanta laya laya, ya dan janye jelar gashin ya dora fuskarsa a gurin yana sansanawa! Ji tayi tsigar jikinta ta mike, ta sake yunkurin kwace jikinta sai dai har yanzu ta kasa samun nasara dan gam take a hannunsa, ya jima da kanshi a tsakankanin 'keyarta da wuyanta yana goga fuskarsa a gurin kafin taji saukar hannunshi kan nonowanta, ya cika hannunsa dasu har da rara! bai wani ja lokaci ba ya soma yi musu murza ta Ala tsine uwar me 'karya!! Ihu! ta kurma! ta dinga zille-zille! a jikinsa tana fad'in''Meye haka!? wannan ai iskanci ne ni bana son iskanci ka bari wayyo nono na zafi ka daina."! Kamar 'kara ingizashi takeyi murza su yake yi sosai yana ta 'kokarin cusa hannunsa cikin rigar domin yaji su a zahiri cikin hannunsa, Allah ya bashi nasarar cusa hannunsa ta 'kasan rigarta aikuwa ya da duka hannunwansa ya kamo nipples dinta da suka wani mi'ke! suka sake tsayi sosai yaja da karfi! a take taji duk wani alkadari nata ya karye!! cije baki tayi! tana kiran sunan Allah....Jan nipples dinta da yayi sai taji tamkar yana mata susa! wani irin dad'i ne ya ratsa mata jiki, lokaci 'kankani nipples din suka rikice mata da 'kaikyayi! ajiyar zuciya ta dinga saukewa a jikinsa tana 'kara yin la'kwas a jikinsa, ta daina buge bugen da takeyi sosai take jin dadin yanda yake murzarta, Shima idanunsa a rufe a jirkitar da ita kasan bed din ta kwanta ya a za mata nauyinsa, nonon yake so yasha dan haka sai yayi nufin cire mata riga idanuna a lumshe sai wata lafiyayyar ajiyar zuciya take saukewa tana rirrike damtsensa, Gabakidaya ya sa'bule mata rigar nonowan sukayi tsalle suka fito nipples din su sukayi nufin tsone masa ido dan sunyi wani cirko cirko suna jiran a basu hakkinsu, aikuwa gigicewa yayi ya fara lasar su da harshensa yana dan ciza kadan kadan wani irin wawura ta kai masa masa tana shan yaji tare da sake ban'karo masa kirjinta fuskarsa ta kifa kan nonowan kawai sai ya zarce da tsotsarsu cikin wani irin salo me rikirkita tunani, da kanta ta dinga mi'ka masa tana kara danna kansa a gurin! sai shan yaji take tana jin yanda gabanta ke motsi yana zillo 'kyaikyayi kawai yake mata, Kansa dake tsakankanin kirjinta ta rungume kam! tana shafa saisayayyar sumar shi, kamar tayi kuka haka takeji sam bata ta'ba shiga cikin hali irin wannan ba, ji takayi tamkar su dawwama a haka duk jikinta ya saki tana cikin halin bukatuwa sosai! Ya zare bakinsa daka nonon ya dan kalli fuskarta gani yayi duk ta wani susuce ta koma wata kala, hannu ya dan sa ya shafa nonon guda daya, tayi saurin bude idonta, ido suka had'a dashi yana mata wani irin kallo! A furgice! ta ture fuskarsa ta mike da sauri! ta matsa gefe kirjinta ta kalla, a tsorace! ta jawo rigarta ta rufe nononta, Ya kai hannu zai cire rigar ta matsa da sauri! harara ta sakar masa ta dura daga bed din a haka zata futa, tana mamakin yaushe akayi ta bari hakan ta faru? Ya biyo bayanta da sauri ya hanata fita! kas tayi da kanta kunyarshi takeji tabbas da bata bashi hadin kai ba ba zai samu damar yi mata hakan ba bata da bakin magana! Rigar ya karba daga hannunta ya fara kokarin saka mata, dai-dai wuyanta ya ajiye rigar ya tsurawa nonowan ido yana kallo a duniya babu abinda ke burgeshi a jiki ya mace sama da wannan kallonsu kawai na sanyawa sha'awarshi ta motsa, Hannunsa ya kai yadan matsa guda. Ta sauke ajiyar zuciya tana buge hannunsa, rigarta taja kasa ta dan ture kirjinsa ta bud'e kofa ta fita daga d'akin! tsayuwa yayi a bakin 'Kofar yana sauke ajiyar zuciya, wani irin nishadi yake ji a tare dashi yana kara jin shauki da son kasantuwa da yarinyar ashe haka romancing yake da dad'i! ? To shi kuma Ubangayar ya yake? sai yaji a halin yanzu babu abinda yake so sai sex! yana so yaji dad'in da yafi wanda yaji a gurin romancing din da sukayi yanzu. Da kyar ya shiga, toilet yayi wankan tsarki dan sai da ya fitar da mazi sosai duk dai sharia ba tace dan ka fitar da mazi kayi wanka ba amma hankalinsa sai yafi kwanciya gurin yin wankan! Ya fito yana goge jikinsa wani irin nishadi yake ji a tattare dashi, yau yarinyar ta lasa masa zuma a baki yaji ashe shima cikkaken namiji ne? daga yau zai fara latsa ta domin ya kar'be wannan budurcin da ake tattalinsa. Wasila kam ta jima kwance a kan bed tana rungume da pilo tana ta mutsu mutsu! gabanta sai zubar da ruwa yake tana jin santsi da yau'ki da 'kaikayi duk ta rasa abinda ke mata dadi ga nippls dinta sun dameta da 'kaikyayi kuka tasa, ta kai hannu kan nipples din tana matsawa, sam! ba taji dadin komai ba tafi so shi dai ya sosa mata ko ya tsotsa! "Allah ya isa! ta fada a sha'ke! dana sani ban shiga dakin ba na jawowa kaina masifa."! Hawaye ta share ta mike zaune tana d'age rigar jikinta dake kamshin turarensa, Nan ta kali nonon nata taga kamar ma sun sake girma, ga nippls din ya wani tattare guri guda, yana kyaikayi! shashsheka tayi ta lumshe idonta ta saki rigar a hankali ta koma ta kwanta lakwas yau taga bala'in duniya, wai dama haka akeji shiyasa duk in da mata suka zauna zancen kenan da shaye shayen maganin ni'ima! to wai shin ita meke futowa daga jikinta!? Wasila haka ta lalace gurin burgima a bed tana matse pillow tana so ta samu sauki jarabar dake taso mata.....Cikin wannan hali ya shiga ya sameta ya shirya tsaf tsaf yana sanye da fari yadi anyi masa dinkin gida 'Yar shara (riga mai yankakken hannu) da manya manya aljuhunai a gabanta, hannunsa guda cikin aljuhu ya tsaya kanta, a hankali ta bude idonta tana kallonsa, ya dan tsira mata nasa idon da sukayi kar! dasu kamar ba dazu suka rikice da fitina ba, ita nata sun kankance duk girmansu sunyi wani ja! kamar me jin bacci haka take lumshe su tana cizan bakinta....Kallo guda yayi mata ya fahimci halin da take cik.... Basarwa yayi yace."Ki tashi kinyi bakuwa Hafsa ce matar Khalita ta kawo miki ziyara." Kamar za tayi magana sai kuma tayi shiru ta mike zaune tana daddauke kanta.....Idanunsa ne suka sauka kan nononta ya tsura shatin nipples dinta ido har yanzu suna tsaye duk gashinan yana gani...Tsigar jikinsa ta mike da sauri ya kauda kanshi, yace."Kiyi maza ki fito Okey." Hanya ya kama ya fita yana had'a hanya mutukar zai sake kallonta cikin wannan yanayi to babu shakka zai rasa nutsuwarsa ga baki a parlor za'ayi abin kunya shiyasa yayi gaggawar barin dakin....Yana fita taja tsaki! ta daddafa ta mike tsaye, toilet ta nufa, domin ta wanke jikinta da duk abinda ya 'bata mata jiki. _*Sanyi ko yawan yin sex da yawan haihuwa na janyo ki kasa ri'ke fitsari da kananun shekarunki sai ki dinga d'igar fitsari fitsari ya matso ki kafin kiyi wani yun'kuri ya soma zuba duk kibi ki bata jiki, wannan babbar illah ce, gareki idan kina fama da wannan matsalar 'yar uwa ko wani naki na fama da irinta to sai kubi matakin neman kare kanki domin tsira da lafiyar ki*_ Littafin na kudi ne.......! Kika futar min da book Ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr bngr Sys *33* Ya fito daga dakin ya tarar da Khalifa zaune kusa da matarshi suna hira ga 'yarsu a kusa dasu, sai abun ya bashi sha'awa sosai, bai sake jin sha'awar haihuwa ba sai yanzu ganin khalifa na kula da matarshi akwai kyakkyawar jituwa tsakanin khalifa Hafsa dan ko sa'bani suka samu, Hafsa ta kirashi yazo yayi musu sulhu baya shiga cewa yake fad'anku duk wanda ya shiga shine zai ji kunya, ido kawai yake sa musu suyi su gama, Afnan ta rugu da gudu ta rungumeshi, tana fadin "Dadyna ina aunty amarya momyna tace " Kayi min aunty na dawo gurinta ta dinga bani sweet. " Daukarta yayi ya jefa sama ya cafe suka kyalkyala dariya a tare! yace."Afnan iyayenki sun saba miki da shan za'ki ko!? ga yanan ha'koranki duk sun soma ru'bewa." Bata fuska tayi wai yace. hakoranta sun rube shine takejin haushi! Ya zauna kusa da khalifa yana fadin"Dan Allah ku daina bama yarinyar zaki kar yayi mata illah." Khalifa yace."Ga mai laifin nan a gabanka tana jinka, ita ke bata kayan zaki, kuma kaima kasan halin Afanan da rigimar tsiya kan alawa da buscit.'' Yace."Afnan ki daina shan kayan zaki idan kina so mu shirya kin jiko."? Tace."Dadyna ni ba zan daina ba sai dai in rage ina shan kad'an." Ta kyalkyale da dariya." girgiza kanshi yayi kawai yana lakuce mata hanci, ya mai da hankalinsa kan Khalifa dake masa magana......Khalifa ya kalleshi tare da fadin ''Ka shanya mu a parlo tun dazu shin ina amaryar take nema."? Ba tare da ya bawa maganar tashi mahimanci ba yace."Wanka take yanzu zata fito.'' Hafsa tace"Okey da har mun yanke shawarar tafiya kar muyi rashin hankali a gidan amare." Hararar ta yayi yana 'bata fuska, suka fashe da dariya, Yace."Hafsa kinci tuwo a kaina amma nasan abinda zanyi miki." Tace"Ai gaskiya na fada." Ya kalli Khalifa yana kanne masa ido yace."Wai ina wannan beb d'in nan dake sonka ya ma sunanta naga ranannan kunyi musayar numbar da ita." Khalifa yace."Nabila kake nufi tanan ko jiya ma munyi waya da ita." Aikuwa Hafsa taci kunu ta fara hura hanci! Ahamdu ya kwashe da dariya yana nunata da hannu ita kuma sai hararar Khalifa takeyi, shi kuma yasha kunu yana latsa wayarshi! wayar ta fuzge daga hannunsa ya kalleta cike da mamaki! Tace"Sai na duba numbar shegiya na goge dama ai ki baku fada nasan abunda kukeyi idan kun futa waje."! Yace."To ke da kina tunanin da ke kadai abokina zai zauna."? "Eh ko ba'a zauna dani kadai ba ai a barni nasha miya haka kawai sai ayi min kishiya." Bilhakki take maganarta sai faman hura hanci take....Ahamdu ya dinga yi mata dariya,, ita kuwa duk ta dauka gaske ne bata san kawai tsokana ce ba. Mikewa yayi ya barsu suna artabu ya shiga bedroom din Wasila dai-dai lokacin da ta fito daga toilet daure da towel iyakacinsa cinyarta, a hankali ya mayar da kofar ya rufe!! Tayi bala'in bata fuska, ta wuce da sauri gaban dreesing mirror ta tsaya, tana goge fuskanta....Ba san ya iso inda take ba sai hucin numfashinsa taji dai-dai wuyanta, gabanta ne yayi wata mummunar faduwa, tayi saurin matsawa har towel din na barazanar kwancewa daga kirjinta tayi saurin tare shi da hannunta guda. Mazewa yayi yace."Tun dazu kin shanya mutana a palor suna jiranki kar kiyi tunanin ko bakina nane naki ne domin ke suka zo saboda haka kiyi maza ki shirya ki fito ku gaisa." Kamar ta fada masa bakar magana sai ta share shi ta dauki mai ta wuce shi bed ta zauna ta fara shafa man gabanta sai faduwa yake, tsoro takeji kar ya sake ta'ba ta sake shiga irin wahalar data shiga dazu! Shikuwa ai ji yayi ba zai iya kyaleta ba dan ba karamin sha'awa ta bashi ba, sai ya bita bed din ya tsaya a kanta.....Ta dago kanta tana kallonsa taga ya kurawa kirjinta ido! hannu tasa ta kara tamke daurin da tayi da towel, ta fara kokarin mikewa, hannunta ya rike cikin nasa, Ta cire zata bar gurin sai ya dan tura ta da kirjinsa ta fadi kan bed din, ya runkufa kanta, dauke fuska tayi tace."Wai meye haka."? Murya na rawa ta fadi maganar, Ba tare da yace komai ba ya dan sa d'an yatsan sa a kirjinta yana yawo dashi, tayi saurin turewa tana ja da baya, ya sake matsarta yana yawo da hannunsa kirjinta har ya samu damar kwance daurin da tayiwa kirjin nata ta rike towel din da kyau! yana ja tana ja! Kuka tasa masa! "Wai me yasa kake so kaga tsaraicina ne? alhalin baka bani sadaki ba."? Da jin wannan magana da tayi sai yayi saurin kallonta, " Ina Sadakin da na baki ranar dana kawo ki gidanan.'' Harara ta watsa masa, "Wallahi Wasila tafi karfin wannan sadakin da kake magana akanshi idan kana so kasan wacece Wasila kaje ka sake sabon daurin aure kuma nice zan fad'i iya adadin kudin da zaka biyani na sadaki." Ya kalleta da mamaki a tare dashi!! "Ke kina da ilimin addini kuwa."? Dauke kanta tayi....Yace." A'ina kika ta'ba jin mace ta yanke sadakin auranta da kanta? Shiru tayi masa, yace."Na lura kina da masifar son kudi......Me zaki dasu? nan ma ba tace komai ba, yace."Kar ki sake min magana makamaciyar wannan ranki zai 'baci! Sadaki na auranki na baki tuntuni, ke kika san yaya kika da kayanki kuma kin jawo sai na amshi sadakina yau dan haka ma ki shirya." Yana gama maganarshi ya sauka daga bed din yana tattare fuska yace."Malama ki shirya ki fito suna jiranki." Ta mike tana sake damke kirjinta dake daure da towel taje tana nemo kaya.........Super Holland ta dauko cikin kayayyakin da ya siyo mata, yana kallo ta wuce shi ta nufi toilet da kayan a hannunta, wai ba zata shirya a gabanshi ba da sauri ya tare mata hanya yace."In dai ba zaki saka kayan a gabana ba to zanja ki a haka na kai musu ke ." Ranta a bace tace"To wai me yasa kake takura min ne? yanzu sa kayan ma sai nayi a gabanka."? Yace."Kin mata da d'azu na gama ganin abinda kike 'boyewa to meye na damuwa.''? Takaicinsa ne ya kamata! ta wuce ta barshi tsaye a gurin.....Babu yanda ta iya haka ta dinga kare karen jiki wai kada ya ganta tasa breziyya tana kokarin zura riga ya rike! taji tsoro sosai dan ba tayi tsammanin ya iso gurin ba, wuyan rigar ya shiga kana hannu guda ya shiga daya hannun ne bai shiga sanadiyar rike rigar da yayi!!!! Taga yana mata wani shu'umin kallon da ya kusa sanyawa ta zube a gurun! Ji tayi kafafunta na rawa, kafin ta ankara ya daga hannuwanta sama ya zare rigar! ya jefar manneta yayi a jikinsa ya zagaya hannunsa bayanta ya 'balle breziyyar ya jefar, ajiyar zuciya suka sauke a tare......Fatar bayanta ya shiga shafawa yana hadawa da kwantaccen gashin kanta, ta dinga jin tsigar jikinta na mikewa sanyi na ziyarta ta bata san sanda ta shige cikin jikinsa ba, ya sun jima a haka kafin ya d'ago fuskarta idanunta na rufe ya sumbaci le'bunanta ta bude ido a hankali ta sauke su a kanshi.....Murmushi ya sakar mata wanda ta kasa fahimtar ko na menene! Taji yace."Kiyi hakuri sai dare zanyi miki abin dazu yanzu kinga muna da ba'ki."! Kunya ce ta lullubeta sai tayi 'kas da kanta duk ta rasa ya za tayi, wai me yasa take saurin bada kanta ne gashi har ya gane ta daga ya ta'ba ta sai ta hau network! kamar mara lafiya haka ta zama sukuku! tana ji tana gani ya sanya mata breziyar da kanshi bayan ya gama lugwigwita nonowan sannan ya dauki rigar ya sa mata, mika mata zanin yayi yace."Wannan ne ban iya daurawa ba daura abinki." Ta karba da mataccen jiki ta daura, tana ji kamar ta fashe da kuka ji take ta tsani kanta da kanta yanzu yanzu tagama cin alwashi kan sadaki amma gari banza ta bari yaga abinda take boyewa, ta dauki dankwalin ta yafa ba ta daura ba, yace."Kisa kwalli a idonki kamar ba amarya ba." Kamar ta gaura masa mari haka taji, zuciyarta sai zafi take, ya dauko mata kwallin ya bata, jefar dashi tayi....Ya daga kafada alamun bai damu ba, "Wuce muje ko."! yafada yana tsareta da ido, Simi simi tayi gaba, ya bi bayanta yana murmushi shi wataran ma idan tayi abu dariya take bashi a kwai kuruciya a tare da ita...........Dan sai-saita fuskarta tayi yayin da ta fito, kafin ta ankara Afnan ta tawo a guje ta ru'kun'kume ta tana fad'in" Aunty amaryata aunty amaryata ce." *_'Yar Uwa yana da kyau a duk lokacin da ki kigama al'ada ma'ana jinin haila! Ki sanya miski ki goge gabanki kana ki dan goga zuma ki tsuguna a turaran suguno, sannan ki d'an sha kayan marmari, domin ni'imar ki ta dawo, duk lokacin da mace ta zubar da jini ko na haihuwa ko na al'ada ni'imarta na dan raguwa gurin na bushewa yana bukatar gyara sosai domin ki tar'bi mai gidanki da aka kwana biyu ba'a had'u ba🙋🏻‍♀️_* Littafin na kudi ne......! Kika futar min da book ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *34* Rike hannun yarinyar tayi tana dan murmushi tare da fad'in"Oyoyo baby ya sunanki."? Afnan tace."Halimatu amma ana kirana da Afnan." Tace."Ashe ma mamana ce daga yau sunanki momy." Afnan tasa dariya tana fadiin"Laaa! Dadyna wai na zama momyn aunty amarya." hannunsa ta rike tana kyalkyala dariya murna take yi wai Wasila tace ita momynta ce....Yace."Eh mana tunda kikaji ta fadi haka da gaske take." Yarinya ta ruga a guje inda iyayenta ke zaune tana fada musu. 'Karad'in yarinyar ya sanya Wasila dariya, ta 'karasa inda suke a nutse tace"Sannuku." Khalifa yace."Sannu da fitowa gimbiya amarya ." Murmushi tayi kawai ta zauna tana kallon Hafsa dake kallonta tana murmushi, tace."Ina kwananku." Hafsa ta amsa tana dariya tace."Ai kin cancanki a kira ki da wadannan suna, amarya ya gida ya bakunta." Tace."Alhamdullahi, cikin ranta tana jin yanda famliy din Khalifa suka burgeta ta lura matarshi na kirki shima kuma ta lura yana da mutumci ba kamar abokinsa ba......Khalifa yace.''Ga 'kawa nan na kawo miki ku gaisa ku san juna Matata ce ga yarinyata anan Afnan duk naji lokacin da take gabatar miki da kanta." Murmushi tayi tace"Afnan akwai karad'i Allah ya albarkaci zuria mungode da ziyara." Khalifa ya dinga mamakin hankali da nutsuwar yarinyar ashe duk kallon da suke mata na lalatacciya ba haka abin yake ba........Duk wannan gaise gaishen da sukeyi Ahamdu na can tsaye bakin window yana kallon harabar gidan nashi........Wasila ta kalli teble din gabansu ta taga ko ruwa babu, sai taji nauyi, ta mike a nutse tace"Bari na kawo muku ruwa ko."Hafsa tace "Mungode." kicin din ta nufa, Afnan tabi bayanta, tana fadin"Aunty amarya zan raka ki." Hannunta ts rike tace."To muje." Tana kokarin shiga kicin din ya juyo suka hada ido tayi saurin dauke nata ta shige kicin din da sauri shi kuma ya dawo inda su khalifa suke lokacin Hafsa na gulmar Wasila.....Khalifa yace."Gatanan tana gulma. Ya zauna kusa dashi Yana kallon Hafsan dake murmushi kunya ce ta kamata duk da ba wata mummunar magana ta fada kan wasilan ba. Khalifa yace."Wai cewa takeyi amaryar yarinya karama kuma akwai karancin ilimi a tare da ita amma kuma tana da hankali." Murmushi ya danyi ya ta'be baki yace."Khalifa bana jin wannan yarinyar ta cika 20yeares fa, duka bata fi 17 ba, karatu kuwa dama ai ba'a maganarshi a gurinta, bana tunanin tana da takardar scondry School." Hafsa ta bude baki! Yace."Yes hakane mana ai babu nutsuwar da zata sanya tayi karatun....Hafsa tace."Allah sarki amma dai yana da kyau ta koma makaranta gaskiya magana matar governor guda ace bata da takaradar kammala karamar makaranta gaskiya akwai babban kalubale. Yace."Hafsa ke kike tunanin wannan itafa wannan yarinyar a yanzu bata da wannan burin burinta shine ta samu hanyar da zata fita daga gidanan."? Tace"To a kan me."? Dake duk abinda ke faruwa ba tasa ni ba, khalifa na da amana sosai baya futar da sirrin abokinsa. Share maganar kawai yayi shima saboda ya lura da cewar batasan abinda ke faruwa ba kuma bata san yanda akayi auran nasu ba gaskiya yana mutukar alfahari da abokinsa yana da sirri sosai matarshi ma bai yarda taji labarin ba. Ta fito hannunta rike da wani madai-daicib tire da goran ruwa da lemo a kai sai kananun cups ta ajiye kan teble din tana fadin ga ruwa sannuku." Khalifa yace."Yawwa sannu amaryamu." Murmushi tayi kawai ta kama hannun Afnan suka nufi dakinta, ba tajin zata zauna in dai yana gurin a zaune..........Khalifa yace."A'a ya zaki gudu kuma." Karaf! yace."Kunya takeji wai ita amarya." Hafsa tasa dariya tace"Ai kunya halal ce! a gurin 'ya mace gaskiya mungode da tar'bar da akayi mana amarya." Ba tace komai ba ta bar suna ta surutu....Tana jin sanda yake fad'in"Ita wannan amarya bata da wata kunya dan ta ganku ne take sunkuyar da kai." Hafsa kuwa sai tare mata takeyi tana fadin "Sam! ba haka bane." Afnan ta hau kan bed dinta tana tayi mata surutu da labarin skull dinsu ita dai jinta kawai takeyi, ta rasa wane tunani zatayi da ta sa'ka wancan sai ta kwance sam! wannan gidan ba gidan zama ba hankalinta har yanzu na kan harkokin siyarsar ta, taga sai wani gayyato mata mutane yake sai kace wata wacce tazo zama." Sun jima suna hira dan sai da suka dauki kusan awa biyu tukkuna sannan suka niyar tafiya, har lokacin Afnan na tare da Wasila suna hira dan tun tana biye mata da surutun ta har tayi mata shiru itama ta gaji ta kwanta bacci ya dauketa....Ya shigo dakin ya same su kwance kan bed a tare ita Afnan din baccinta yayi nisa sosai itace dai take ta kokarin gayyato baccin yazo yaki zuwa. Mikewa tayi zaune tana daura dankwalinta, ya tsaya kusa da ita a nutse yace."Yarinyar nan fa tun bata sanki ba, take zumudin ganinki gashi ta makale miki ya za'ayi ne momynta tace zata kwana biyu a gurinki kina ganin babu matsala ko."? Yafad'i wannan maganar ne saboda kawai baya son shiga hakkinta idan taga zata iya daukar yarinyar shi bai da matsala, Jim! tayi itafa bata so ta sha'ku da kowa ballanta hakan yazo ya dameta wane irin zama za tayi a gidan! da har za'a na'nika mata yarinya, Domin kar ta watsa wa maman yarinyar kasa a ido yasa tace."Ni meye nawa a ciki gidanka ne fa, tayi zamanta." Yace."Eh ai nasan gidana ne ai kece matar gidan dole kina da hakki akai.' Shiru tayi masa, yace."alamu sun nuna kin amince kenan? Kallonsa tayi ya d'aga mata girarshi guda tayi saurin dauke kanta gabanta na faduwa, yace."Ki fito zasu tafi sai kuyi sallama ko." Mikewa tayi, ya juya baya yana tafiya kallonshi kawai takeyi sai wani magana yake mata yana dage mata gira kamar wani dan saurayi mutum da girmanshi da komai sai iyayin tsiya, Su Khalifa na tsaye suna jiran fitowarsu, dukaninsu basuyi tsammanin Afnan zata zauna ba sai suka gansu sun fito babu ita, cike da mamaki! Hafsa tace"Ina Afnan din."? Ahamdu yace."Ina ruwanki da ita kuma yanzu." Rike baki tayi tace"Nifa duk wannan abin da nakeyi wallahi cikin wasa nakeyi ko kayanta daka gani saboda kar tayi min kuka ne yasa na had'o mata muzo dasu, amma ni nasan rigimar Afnan ba zata barku kusha ruwa ba a gidanan." Khalifa yace."To nima dai haka nake gani amma dai shikkenan." Wasila tace"Kai don Allah ku kyaleta mana ai babu wata matsala bacci ma takeyi ai ni nasan ba zatayi kuka ba." Khalifa yace."Shikkenan ai dama bamu ce komai ba." Murmushi kawai tayi tace"To ku gaida gida mungode.' Hafsa tace"amarya yaushe zaki kawo min ziyara ne."? Dan murmushi tayi takasa magana sai shine yace."Idan ta kwana biyu zan kawo miki ita amma bana son gulma." Hafsa tace"Kasan kuwa idan mun hadu sai munyi gulmarku." Yace."To na fasa kawo ta tunda d'abia mara amfani zakuyi." Hafsa ta dinga dariya tana fadin"saboda rashin gaskiya ba, ai da kafarta nasan zata zo inda nake mu kashe mu binne." Murmushi kawai yayi bai sake cewa komai ba, suka nufi kofar fita a tare, Wasila tana tsaye daga inda take tana musu fatan alkairi da sauka lafiya. Sai da ya tabbatar motarsu ta fita daga gidan sannan ya koma cikin....Parlo yay zamansa yana kallo da tunanin yanda zai kai kansa gurin yarinar da daddare baya jin zai iya daga mata kafa a yau din nan. *** Camas! kuwa lokacin da ta bar gidan Wasila kai tsaye gidanta dake tishama ta nufa, lokacin su Uwani da rashida abin duniya ya damesu sun tasa lafiyayyan abinci a gaba sun kasa ci sai tunini suke, Da jin labarin da Camas tazo musu dashi sai hankalinsu ya kwanta, jin cewar Wasilan na cikin koshin lafiya gashi har ta bada sallahun a fada musu cewar tanan kalau kuma su kwantar da hankalinsu tanan fitowa ta cigaba da rayuwa a tare dasu, Uwani ce kawai taji dadin wannan magana amma ita Rashida sam bata sha'awar wasila ta fito daga gidan Ahamdu tana ganin Allah ya gama yi mata suttura tunda ya gamata da miji nagari kamar wannan bawan Allahn. *** Camas! bayan ta bar gidan su Uwani sai ta wuce can getshouse din As wato Alhaji Tasi'u lokacin yana tare da baki sai da tayi jira tukkuna ta shiga.....Yana ganinta yace."Tuntuni nake saka ran zuwanki shiru da yanzu nake tunanin kiranki a waya. Tace."Wallahi kuwa ai ina tafe na dan tsaya wani guri ne." As yace."Okey bani labarin yanda kukayi kin samu ganin Wasila.....Tace."Kwarai kuwa har mun shirya shawarar yanda za'ayi." Tiryan tiryan! ta fada masa yanda sukayi da Wasila da irin alkawarin da tayi kan in ta fito daga gidan Ahamdu to ya saka ransa cewar ta zama mallakinsa. As ya dinga washe baki yana shafa sumar kanshi tabbas idan hakane to ko nawa ne zai iya kashewa duk dan ta samu nasarar fitowa daga wannan gidan....Yace."Yanzu abinda za'ayi shine ki bani accont numbar naki zan miki sending din kudi masu dan kwari, wanda zasu isa kuyi abinda zakuyi dasu, gaskiya naji dadin wannan labari naki dole ne ma nayi miki alkairi." Camas! dadi ya isheta tasan As bashi da kwauro mutum ne shi mai sauki da dogon hannu har yaso yafi governor mi'kawa, itana wasilan duk da bazarsa take rawa, ta bashi account numbar dinta a take ya tura mata dubu dari hudu yace nata duba dari dubu dari uku kuma taje tabawa masu gadin gidan Ahamdu idan sunki amincewa ta dawo zai kara wasu. Godiya tayi sosai sukayi sallama da juna, tare da sharadin gobe zata fara aiwatar da aikinta... *** Tun yamma Hadari ke had'owa daf da magariba gari ya turnuke sosai da kura iska na tashi da ledoji.....Dai-dai wannan lokaci Afnan ta tashi daga baccin da ya dauketa tun bayan tafiyar iyayenta, Wasila da ta fito daga toilet ta ganta zaune a kan bed tana mutsika ido, tace."Afnan kin tashi." Yarinyar ta kalleta tana gyada kai...Tace."Kin sha bacci ko abinci baki ci ba tashi muje na rakaki kiyi brush baccin yamma bashi dadi ko kadan." Afnan ta sauko daga bed din suka nufi toilet Wasila ta matsa mata man goge baki a sabon brush, ta karba tana fadin"Aunty Amarya ina momyna da Abbahna."? Kai tsaye tace"Ai sun tafi tun dazu ke kina ta bacci." 'Dif! yarinyar tayi tana goge baki har ta gama wasila tace"To daura alwala muyi sallah sai kici abinci ko."? Daga mata kai tayi, Wasila ta kalli fuskarta taga babu walwala sam! bata kawo komai ba, ta mika mata, mayafin abaya ta yafa kana tasa hijab suka tada sallah.......Sanye da jallabiya ruwan toka ya shigo kanshi sanye da hular labarawa fara tas da ita ya saje sak da balaraban saudia....Ganinsu suna sallah sai ya zauna kan Sofa yana cigaba da jar carbin dake hannunsa.....Suna idarwa, Afnan tace"Dadyna! ina Abbahna." ? Ya kalleta da sauri yace."Ke! haka ake daga idar da sallahr babu addua sai magana." Rakykyakya'be fuska tayi sai hawaye shaaaa! ya bude baki cike da mamaki yana kallonta, hannu ya mika mata "Zo nan.! Taje ta tsaya tana goge fuska da bayan hannunta, Yace." Me akayi miki kike kuka."? Shiru tayi......"Ko auny Amarya ce ta dake ki."? Wasila tayi saurin kallonshi jin abinda yace....Afnan ta girgiza kanta..."Ni dai a kaini gidaaaaa."! Yarinyar tafada muryarta narawa still hawaye na zuba....Yace."Ai kinyi kad'an yarinya ba zaki bani wahala ba wallahi sai kinyi iya adadin kwanakin da kikace zakiyi sannan zai mai dake." Tsalle ta buga, ta hau kurma ihu! "Wayyo!! Abbana Momyna! ni gida zani ba zan zauna ba a kaini gidaa!!!! Hannunsa yasa ya toshe kunnansa, Afnan akwai lafiyar karadi sai kara take musu a kunne. Wasila tace" Kiyi shiru mana kin fasa zama dani kenan ashe bakya sona Momyna." ! "Umum! ni dai a kaini gida bazan zauna ba." Tafada tana tsalle tana tumami!! hanyar fita ta kama a guje!! Yayi saurin rike hannunta, yarinya ta dinga kokarin fuzgewa tana kuka.....Ya kalli Wasila dake tsaye tana mamakin yarinyar ko da yake dama iyayenta sun fadi rigamarta ."Zo ki rakani na kaita dama na sani ai ba zama za tayi ba wahala kawai zata bani." Tace"Afnan ba zaki zauna dani ba." Gyada kanta tayi tana kuka Yace."Kina batawa kanki lokaci ne kan yarinyar ba zama zatayi ba karshe ta hanamu bacci.'' Fita yayi da Afnan din tana ta kuka da kiran momynta, Wasila na bayansa da hijab dinta na sallah!....Ashe ruwa ake sosai kuma me karfi....Ya kalli Afnan din yace kinga ruwa ake ki bari ya tsagaita." Ihu! tasa! ni a'a ni momyna nake so." Ta dinga fada tana dukan fuskarta, Wasila tasa dariya da fadin"Lallai ma yarinyar kina kuka kina dukan kanki saboda tsabar masifa. Wayarshi ya ciro ya kira Garba yace ya kawo mishi mota dai-dai kofar palor zai fit...Minti biyar motar tayi parking daukar afnan din yayi ya sa'ba a kafada suka fita, cikin gaggawa Garba ya bude masa mota ya shiga, ta shiga ta zauna... Key din ya karba hannunsa, Garba yace."Allah ya tsare hanya." Hannu ya daga masa ya juya kan motar, suka nufi bakin gate.... Tun a mota ya kira Khalifa ya shaida masa abinda ke faruwa Khalifa ya dinga she'ka dariya takaici yasa ya kashe wayar yana rankwashin Afnan dake jikin Wasila sai faman ajiyar zuciya take. Lokacin da suka isa gidan ruwan ya dan tsagaita, khalifa ya kirashi a waya da fadin"Fito ka dauki masifaffiyar yarinyar nan ta kusa kashe min kunne da kuka." Khalfa yace."Ah haba dai ba zaku shigo ba." Yace."Ba zuwa nayi dan na zauna ba 'Yarku na kawo muku." Khalifa yace."Ai na bar maka ka juya da ita." tsaki yaja ya kashe wayar...Khalifa ya dinga dariya yana fadin"Dama afnan ce zata zauna a wani guri yasan dole hakan zata faru. Tare suka fito da hafsa, suna dariya da jajanta al'marin shi dai bai ce komai ba, afnan na ganin iyayenta ta sauka daga jikin Wasila taje ta rungume mamanta, Hafsa tace"Amarya afuwa afnan bata kyauta ba wallahi ta taso ku cikin ruwa. Dan mirmushi tayi tace."Ayya babu komai aikin yarinta ne ai.....Ahamdu kam juya motarshi yayi yana kallon afnan da fad'in"duk sanda nazo kika sake cewa sai kin bini sai na cire miki kunne! Makale kafada yarinyar tayi tana sauke ajiyar zuciya alamun taci kuka takoshi, Hafsa da khalifa dariya suke masa sun gane taji haushin abinda afnan din tayi musu, hannu suka daga musu har suka fita daga gate din gidan. Suna fita babban titi iska ta taso gari ya sake rikewa sabon ruwa ya kece kamar da bakin kwarya ake sheka shi har da kankara irin wannan ruwan ne, yasa dole ake tsaida ababan hawa saboda gudun afkuwar matsala, sai ya samu gefan titi yayi parking din motar, yana fadin"Yarinya ta taso mu haka kawai cikin ruwa." Shiru tayi masa, ita tsoron ma titin take shuru sai uban ruwan da ake shekawa wanda take gani kamar zai tafi da motar.......Kimanin mintina goma a tsakani babu wanda yayi magana a cikinsu sai dai saukar numfashinsu a cikin motar....A hankali taji hannunsa kan nata, tayi saurin kallon jikinta, ya akayi har ya zura hannu a cikin hijab dinta ba taji ba, tasan ta kudundune jikinta da hijab dinta sabida sanyi amma sam ba taji sanda ya zura mata hanninsa a ciki ba......Ji tayi yana shafa tafin hannunta a hankali a hankali yana murza tsakiyar hannu...Tayi nufin kwacewa ya rike da sauri ta kalleshi suka 'Kurawa juna ido....Wani irin shu'umin kallo taga yanayi mata yana lumshe mata tsumammun idanunsa dake mugun kassara mata ga'ban jikinta.... Littafin na kudi ne....! Kika futar min da littafi ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr bngr Sys *35* Bakinta ta motsa tana so tayi magana amma sai taji yayi mata bala'in nauyi, yanayin yanda yake shafa tafin hannunta yayi mutukar saukar mata da kasala inda har take jin sanyin da takeji na kara karuwa duk a sakamakon tashi da tsigar jikinka keyi......Jinta tayi ta kifa baya ta kwanta ashe shamtar ta yayi ya kwantar da kujerar domin ya samu sararin yin abinda zaiyi da ita, kafin tayi wani yunkuri ta ganshi ya rankwafo kanta, yana kokarin cire mata hijab din jikinta, rike hijab din tayi katamau! mirya ka...bari don...Allah."! Girgiza kansa yayi ya kwanta a jikinta yana sauke wata iriyar ajiyar zuciya....Sun jima a haka nauyinsa duk ya isheta sai motsi take yi gabanta na faduwa taga ya dago a gagauce ya tallafo fuskarta, bakinta ya wawura kamar mayunwacin zaki ya fara tsotsar le'bunanta yana tusa harshensa cikin bakinta, duk ya wani rikice abinka da wanda bai saba ba, Wani irin maganad'isu ne taji yana fuzgarta jin bakinsa cikin nata sai taji ta tamkar tana yawo kan gajimare wani irin gardin dadi bakinsa ke bayarwa, bata san sanda ta cafki sharshensa ta shiga tsotsa ba tana lumshe ido hade da shafa saisayayyar sumarshi......Ba kaji komai a cikin motar sai saukar numfashinsu da sautin motsin harshensu Yanda suke sucking din junansu tamkar zasu cinye kansu kansu Wasila sai kara sakin jikinta take tana manne masa a jiki, gabakidaya sha'awarta ta tashi, komai na jikinta ya amsa, zuwa wannan lokacin yayi nasarar rabata da hijab din jikinta ya zuge zif din rigar jikinta nonowanta ya fito dasu ya dinga wasa dasu da hannunshi, duk jikinta yayi lakas ta dinga jin danshi danshi a wandonta, Ido a lumshe take sakin nishi tana shafa kirjinshi da hannuwanta, wanda bata san ma tanayi ba, Jin saukar bakinsa kan nonowanta ya sanya ta dan saki 'kara tana sheshsheka ita dai tana bala'in son asha mata nono ji take kamar zata zautu aikuwa ta dinga tura masa tana sake rike wuyanshi, da sakin nishin da bata san tanayi ba......Jin yanda jijiyar sa ke harbinsa ya sanya ya zare jallabiyar jikinsa ya dawo daga shi sai gajeran wando ya dau hannunta ya cusa cikin wandon.....Cikin shauki da rashin sanin meye ta kama abar a hannunta ta dinga mulmulata a hannunta....Ahamdu yaji ba'kon abu a tare dashi a take jikinsa ya shiga rawa, zufa ta dinga keto masa tamkar babu Ac a motar, wani irin han'koro da haniniya gabanshi ya dingayi, wanda ya sanya yayi gaggawar cire bakinsa a kan nononta ya haye samanta, tsakanin nono yasa jijiyar ya hada hannunsa da ita a gurin ya matse sosai ya dinga jujjuyata a gurin joystick dinshi ta dinga zungurin ha'barta, dad'in abinda yake mata ya sanya, ta dinga lasar kan kamar me lasar alawa! ya dinga sakin wani irin nishi! yana kiran sunan Allah!!!! Gani yayi tana nema ta kashe shi da wannan salon da take masa, kawai sai ya gyara mata kwamciya a gigice yake kokarin zuge zif din siket dinta, dai-dai lokacin aka saki tsawa da walkiya har ta hasko cikin motar,.....Wasila ta dawo hayyancinta, hannunsa taji na yawo kan mararata tayi wani irin zabura tana tureshi! ya akayi har ya cire mata pant? Kuka tasa sanda ta ganshi kwance a jikinta, daga shi sai karamin wando, ta dinga kallon motar tana laluben kayanta ashe duk abinda sukeyi a cikin mota ne kuma kan hanya, innalilihi wa'ina ilaihi raji'un.!! "Ka d'agani don Allah baka ganin a mota muke kuma akan hanya ga ruwa anayi kaifa ba yaro bane kasan abinda ya dace amma kanayin abu irin na 'kananun yara." Abunda take fada kenan tana tuttureshi daga jikinta sai kuka takeyi, shi kuma sai sake mannewa yake a jikinta kamar mayan karfe yana cusa fuskarsa tsakanin cikinta da mararta. Tashin hankali ta shiga mara misaltulawa sai ta shiga dukan bayansa tana masa magiya, Ahamdu ya kasa kata'bus! ya manne a jikinta ya kasa motsi ko kadan ji yakeyi tamkar in ya sauka a jikinta zai mutu, wani irin hali ya shiga wanda bai taba jin irinshi ba, "Wayyo na shiga ukuna kafafuna dan darajar annabi ka taimaka ka sauka daga jikina ba zan iya ba, mu tafi gida a kan hanya muke kaga ana ruwan sama."! Sambatun maganganun da take kenan......Wanda ko kwara guda bai dauka ba, sai ma mikewa da yayi da kuzari ya sake gyara mata kwanciya, ya sake matseta a jikin kujera sosai ya gyara gwiwowinsa yanda zai ji dadi sosai ya fara kokarin wasa da jijiyarsa a virginal dinta, lumshe ido tayi tana sakin ajiyar zuciya ji tayi kamar ya sa mata zuma a gurin dan dad'i!!!! Santsi santsin gurin ya dinga d'ibar shi yana sashi jiri da maye shauki! " Ya Allah! Ya Allah."!!!! Abinda yake kira kenan yana sake damalmala jijiyarsa bakin ramin, kamar zai shiga sai ya fasa ya cigaba da wasa da ita a gurin.....Wasan yayi mata bala'in dadi dan duk surutun da takeyi dainawa tayi ta sa'kalo wuyansa da hannunta tana cije baki "Ahhh!! Ahhh! Ummm! abinda take iya fada kenan ta shashshafa jikinsa, wani irin ruwan ni'ima ne ke gudana a jikinta, wanda ya sanya shi gaggawar fara karanto adduar saduwa da iyali.....Kawai ya gyara gwiwarshi dake tsakankaninta kan kujerar mota da bata da wata jikakkiyar girma, ya matse ta sosai ya dafe hannausa daya kasan kujerar, dayan kuma kan joystick dinshi, Danna ta yayi da karfi! a take rabinta ya shige shi kanshi yaji lokacin da ya keta wani abu a cikin ramin kafin ya dan jujjuyata a ciki ya sake yunkurin danna ragowar da bata shige ba......." Wayyo zai kasheni ni Wasila na shiga uku! bana so kayi min haka ban shiry......! hannunsa yasa ya rufe bakinta ruf!!! shi kanshi a jigace yake wannan wahala haka!!! Murkususu takeyi har sai da suka fad'o kasan site still jikinsu na had'e dan har yanzu rabin jijiyarsa na cikin ramin, ta gagara shiga, a haka suka hau! dambe! da ita, shi kuma ya danneta sosai yana ta cuku cukun ya za'ayi sauran ya karasa shiga sai cizo take gallara masa tana motsi da kafafunta hakan ma ya taimaka masa sosai wanda yasa ya samu nasarar huda jikinta sosai ya dulmiya jijiyarsa cikin gurin da yake bukata, aikuwa yaji shi cikin wata iriyar ni'ima wacce tasan yashi sakin karamin ihu!!!! ahhh! sai sai kawai ya hau bugunta tun 'karfinsa yabi ya tattare mata kafafunta da nasa kafafun, yana hakarta kamar babu gobe, hannunsa guda daya damke da bakinta, ya hanata kuka, sai dai nishi da gwalalo ido kawai takeyi,, yana a hakan nonowanta na tsone masa ido rankwafo da kansa yayi ya cafki daya ya hau tsotsa yana cigaba da aikin suburbud'ar matuncinta. Tofa! Yau fa tuzuro ya samu sake Turuzo Sarkin ta'bargaza!😉 Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book ke da Allah kika karanta baki biya ba kema ke da Allah. Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*[07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *36* Sosai yake bugun ta yana wata iriyar sukuwa a kanta tamkar wanda yake kan doki, duk ya wani gigice zufa ce kawai take Zurarowa daga ko wace kusurwa ta jikinsa, Tsabar wahala tasa bakinta ya mutu sai da uban hawayen dake ta ambaliya a fuskarta, kafatanin karfin ta ya kare dan ba karamin galabaitar da ita yayi ba ta inda dan ya tsanta ma take jin wuyar motsa shi, tana dai jinsa yana sambatu da kiran sunan Allah, yana sake caccaka mata jijiyarsa cikin matuncinta, sai sanda yayi mata wani irin bugu be ta saki 'kara tana 'kamkame hannuwanta dake karkarwa a jikinsa, can taji ya sake yi mata wani irin bugu da karfi!!! gaske kafin taji ya saki 'karamin ihu!! yana fad'in"Subahanallah!!! ''Ya Allaaaaaa!! yaja sunan Allah da karfin gaske kafin ya rankwafo kanta, kirif! ya rufeta gabadaya da jikinsa yana sakin wani irin nishi! wanda kai kana jin yanda yake fita kasan na wahala ne! La'kwas tayi a kwance numfashinta na fita sama-sama wannan lokacin da mutuwa zata zo ta dauketa to da tayi murna da zuwan ta, ta rasa ma wane irin kuka za tayi me za tayi wa mutumin nan ta huce! duk tsayin shekarun da tayi tana tattalin budurcinta, sai da ya sami nasarar keta mata shi, karin abin takaici da ban haushi ma ya rasa a ina zai haike mata sai cikin mota a kan hanya, Ya ilahi! wannan wace iriyar masifa ce!? Wani siririn hawaye ne ya shiga kwaryowa daga idonta wanda ya shafi gefan fuskarsa dake manne da tata fuskar.....Cikin matsanan ciyar kasala da mutuwar jiki ya mike daga jikinta, tare da dan gyara mata kafafunta dake wargaje!!! Dafe kanshi yayi yana kiran sunan Allah! Wannan wane irin tsautsayi ne ya afka masa, cikin mota ya afka wa yarinyar nan shi kam wace irin zuciya gareshi mara hakuri! Kallonta ya dan yi yaga tana cije bakinta still hawaye sai zurara yake, tausayi ta bashi, ya dan kalli gabanta, yaga ta sake wargaje kafafun nata tamkar wacce ta bude domin gurin yasha iska...Tsirawa gurun ido yayi yana, kallo ganin jan jini yayi hade da sperm dinshi duk ya bata mata cinya da kan site din....Ya dauki gajeran wandonshi yana goge mata cinyoyinta, hannu yasa ya a vigirnal din tayi saurin motsawa, sai yayi saurin cire hannu yana dubawa, jini ya gani jawur! a jikin yatsansa, gabanshi ya fadi sosai, ya dan ja siket dinta wanda take kwance a kai.....''Yi h....'kuri ki d'an gyara jikin ki mutafi." Muryarshi na rawa ya fadi maganar......kasa motsawa tayi, ya dan gyara ya jayo jallabiyarshi ya zura, zuciyar sa duk babu dad'i ya gyagygyara kujerun motar kana, ya dawo inda take ya dago ta jikinsa, Rigarta yake kokarin sanya mata tana kokarin komawa ta kwanta, da kyar da ya zura mata rigar....Ya dauki katon hijab din ta ya zura mata, yana jin yanda jikinta ke wani irin kyarma, dalilin da ya sanya kenan bai sanya mata siket din ba dan ya lura, bata so a ta'ba gurin....Mikar mata da kafafunta yayi kan kujerar kana yayi mata ya zauna a mazauninshi ya tashi motar da sauri yaja suka bar gurin....Lokacin dama tuni ruwa ya dade da daukewa sai dan yayyafi da walkiya da ake. Lokacin da ya isa gidan nashi sai ya tarar da yaranshi sunyi cirko cirko a harabar gidan hankalinsu duk ya tashi da jimawar ogan nasu a waje, gashi sun kira wayarshi ba adadi ba'a dauka ba, duk sai hankalinsu ya tashi mussaman AbdulHadi da Garba da Abdumumini, suka kira Khalifa suna shaida masa abinda yake faruwa khalifa yace."Tun wajejen takwas sukayi sallama dashi, nan hankalinsu ya sake tashi ganin har karfe goma sha daya tayi bai shigo ba,shine suka tsaya yanke shawarar abinyi, to a dai-dai lokacin shigo gidan.......Gabadaya suka bishi can parking area din sun lullube motar suna jira ya fito.....A hankali ya dan sauke glass din motar Garba ya le'ko da kanshi, "Yallabai duk hankalinmu ya tashi jin shiru baka dawo ba mun dauka ko 'yan adawa ne suka tare ka." Yace."Garba na dan tsaya a wani guri ne, dama nasan dukanin ku hankalinku zai tashi okey lafiyata lau kuma nagode da kulawa, masha Allah kowanne ya koma bakin aikinsa." Godiya sukayi masa sannan suka koma bakin aikinsu......Ya jima zaune a motar yana tunanin abunda ya faru, shi kansa mamakin kansa da kansa yake! wai a cikin mota, yayi marking lov da mace! sosai yayi sex da yarinyar yasan kuma tunda wannan jinin ya fita ya fasa wannan tantanin na budurcin! tabbas ta tabbata shi din jarumin namiji ne ko a cikin maza sai tona samun irinshi.......Fitowa yayi yana kallon harbar gidan nashi, duk sun koma bakin aikinsu, sai ya bude motar yana le'kenta, shi nauyin ta ma yake ji sai yanzu yake tuno irin magiyar da take masa da yanda take hadashi da Allah da annabi kan ya rabu da ita......Yanda ya kwantar da ita haka take bata motsa ba sai dai idanunta dake rufe ruf tana saukar da numfashi sama-sama mai tafe da ajiyar zuciya.......Allah sarki Wasila baccin wahala ne ya dauketa, zura jikinsa yayi yana kokarin cicci'bota! ta farka a furgice! "Wayyo na shiga ukun! kar kayi min da zafi wayyo gind......!! jin tana so ta tona masa asiri ya sanya yayi wuf! ya rufe mata baki da tafin hannunsa, tayi saurin bude idonta tana kallonsa jikinta sai kyarma yake!!!! A hankali yace." Karki sake cewa uffan! Fito mu shiga ciki mun dawo gida! ." Hannunsa dake damke da bakinta ya cire ya dan riko hannunta, wai ta fito! Motsawar da za tayi taji kamar reza ta yanke ta! ''Wayy!!! kafin ta 'karasa ya damke mata bakin yana rarraba ido! marairaice fuska yayi yana girgiza mata kai! "Ki daure kin ji ko."! Cikin wata raunanniyar murya yayi maganar! Lokacin taji wani bala'in tausayin kanta ya kamata hawaye ya tsinke mata, Mikewa yayi tsaye ya dafa motar yana waige waige kamar wani mara gaskiya ya sake rankwafa cikin motar a hankali yace." Bari na dauke ki da kaina mu shiga ciki karkiyi kuka ki daina kiran wayyo kice."Kin godewa Allah."! Ta watsa masa matsiyaciyar harara tana cin laya a kanshi,,,, duk ya gani sharewa yayi ciccib'ota a hannunsa kafin ya sa'bata a kafadarsa ya dafe mazaunanta da hannu d'aya daya hannan kuma, ya rufe motar dashi....Da sauri ya nufi cikin gidan sam! baya so yaransa suka ga abunda ke faruwa. Ba zarce ko ina da ita ba sai toilet yayi kokarin tsayar da ita ta kasa tsayawa dan zamewa tayi ta zauna kasan toliet din tana wani irin kuka mara sauti! Duk ya susuce, ya rasa ma me zaiyi wane taimako zaiyi mata, can ya tuna ana shiga ruwan zafi, da sauri ya soma hada mata ruwan zafi cikin wani babban baho, ya dawo inda take, hannunta ya rike ya mikar da ita Ya ru'ko kungunta, wai lallai sai ta taka kafarta dan shi baya son yaga tana lanjare kafafu sai gabanshi ya fadi ya zaci ko ya ji mata ciwo, ganin ta kasa gaba ko baya ya sanya ya dauketa cak! ya saka ta cikin bahon, hijab din ya zare mata, ya zaunar da ita a hankali.....Cije bakinta takeyi tana sake daurewa, dan tasan wannan ruwan zafin shi e zai tamaiketa a duniya babu abinda take mutukar girmamawa da ganin darajar sa a jikinta sai matuncinta shiyasa kullum cikin tattalashi takeyi da gyarashi.....Tsayuwa yayi a kanta yana kallon yanda take rintse idonta tana sake wage cinyoyinta ruwan na ratsa jikinta tana sauke ajiyar zuciya....Yace."Kiyi wanka idan kin fito bari nazo." ko kallonsa ba tayi ba ballanta ta tanka masa ya kama hanya ya fice daga toilet din da sauri. Bedroom dinshi ya nufa kai tsaye ya wuce toilet dinshi a gurguje yayi wanka, ya sanya jallabiya, da gajeran wando duk abinda yake hankalinsa na gurinta, turare ya fesa ya kama hanya da sauri ya fita daga dakin. Lokacin itama har tayi wankan ta daddafo ta fito daga dakin tana zaune gefan gado daure da towel abin duniya ya isheta, lokacin da tana cikin ruwan zafin daina jin radadi tayi amma kuma yanzu, tana zama gefen bed dinta taji kamar an watsa mata barkona, hawaye ne suka zubo mata, ya shigo dakin yaga tana gogewa da bayan hannunta. A sanyaye ya tsaya a kanta ta sake yin 'kas da kanta ta tsani ta kalli fuskarshi a duniya bata da babban makiyi sama dashi......"Har yanzu zafi yake."!? Ya fad'i maganar cikin wani irin voice! kanta na kasa bata dago ba ballanta ta yi masa magana! Ya zauna kusa da ita yana laluben hannunta ta fuzge da sauri tana shashsheka......! Baiyi zuciya ba ya zura hannunsa kan waist d'inta ya rike cikin sigar rarrashi yana karyar da murya kamar bashi ba yace."Nima banyi miki hakan da wata manufa kin san dan adam! amma kiyi hakuri kinji ko, yanzu na gane ke din ta mussaman ce kamar yanda kika sha fad'a budurcin ki na mussaman ne, kuma ko nawa kin cancanci a biya ki, So ni ba wai sadaki zan 'kara miki ba, No! wannan maganar ta kau ni na riga na bada sadakina tuntuni, kawai ni zanyi miki alkairi saboda mutuntani da kikayi kika mallaka min abu mai tsada naki, ki fad'a min kome kike so a duniyar nan mutuk kudi ke siyan shi zan siya miki ki shi ke ko ni kaina kikace kina so xan baki ni har abadah.'' Ya 'kare maganar tashi cikin wata iriyar mayaudariyar murya......Wata irin harara take watsa masa, tamkar idanunta zasu fad'o sai zumbura bakinta takeyi.....Ya sanya hannu saman idonta, ta dauke kanta tana lumshs idonta, bakinsa ya kai saman fatar idanunta, ya sumbata....'Iluv u beby." Tayi saurin bude idonta jin abinda ya fada, girarshi guda ya daga mata (sigina) yana sakar mata kayataccen murmushi, ta'be bakinta tayi cikin zuciyarta tace''Wato saboda ka lashi zumata shine kake kirana da beb har da wani Iluv u sam! ba zata sa'bu'ba, ba zan sake yarda ka yaudare ni ba.........."A hankali yace."Akwai yunwa a tare dake na kawo miki abinci ko."? Dauke fuska tayi, yayi mirmushi kawai ya mike ya fita, minti biyar ya dawo dakin hannunsa rike da tire mai dan fadi kololin abinci ne a kai.....A ranar anci sa'a Rabe yayi farfesun kaji, abinci kuma yayi sakwara da miyar ganye sai hanta da yayi amfani da ita gurin hada miyar, Sakwara cimar Wasila ce dan haka ba tayi musu ba ta sauko a hankali kasan kafet, ta sa hannu tana ji.....Farfesun ya zuba mata cikin plate ya tura mata gabanta, ya jingina jikinsa jikin gado kawai ya sa mata ido yana kallonta, Ashe yarinya ce mai wata iriyar baiwa bai sani ba, Allah ya rufa masa asiri bai saketa ba kamar yanda da ya dauki alkawarin sati daya kacal za tayi a gidansa ya saketa, Addua ya shiga yi wa malam mai allo domin shine silar da ya sanya ya janye kudirinsa a kanta yasan da ba don shi ba to da tuni ya dade da sakin yarinyar.......... Littafin na kudi ne....! Kika fitar min da book ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *37* Ganin kallon da yake mata yayi yawa ne ya sanya ta ajiye cokalin hannunta tana ya mutsa fuska, yace."Ya kika daina cin abincin ki cifa ki koshi sai ki dan sha paracetamol zakiji kwarin jikin ki." dan turo baki gaba tayi tace"To ka daina kallona." Ya dan saki murmushi mai sauti yace."Baki san na kalle ki."? Daga kai tayi, saisayayyar suman kanshi ya shafa yana kashe mata ido daya yace."Kece din ai kikayi abin kallo shiyasa na kasa daina mamaki a kanki , amma dai tunda baki son na kalleki na daina." Sai ya mike a hankali ya zauna gefan bed din yana kokarin cire jallabiyarsa yace."Kici kizo ki kwanta a nan." Saurin dauke kanta tayi ganin yana nuna mata kirjinsa, ji tayi tsigar jikinta ta tashi, ashe dai shima ba kanwar lasa bane, ya iya soyayya gaskiya, ammafa ita gani takeyi duk wannan abin da yake mata ba don Allah yake mata ba kawai saboda ya lashi zumarta yaji irinta ne shiyasa yake so ya yaudareta ya dinga morarta.......Har ta kammala cin abincin tana sa'ke sa'ke a kanshi, madarar holandia ta bude tana sha tana lumshe ido gardi da sanyin madarar yayi mata dadi, sai da ta shanye roba guda sannan ta mike, a hankali ta nufi bed din tana dan cije bakinta har yanzu gurin radadi da zafi yake mata ji take tamkar an zuba barkona a gurin.....Kokarin kwanciya takeyi, ya janyo hannunta ta fada saman kirjinsa, blanket ya jawo ya rufesu kana ya warware towel din dake daure a jikinta, fatar jikinsu ta hade guri guda, a tare suka sauke ajiyar zuciya ita dashi, gashin dake kwance a kirjinsa ya dinga sosa mata kirji yayin da shi kuma nonowanta suka dinga sukan kirjinsa suna sake sanyashi cikin halin bukatuwa, daurewa kawai yake yana shafa dogon gashin kanta da bayanta a hankali a hankali yake marmatsa mata mazaunanta yana lumshe ido hakan yayi mata dadi sosai dan sai taji kamar tausa yake mata ta dinda lumshe idonta tana sake makalewa a jikinsa, d'umin jikinsa yayi mata yanda take so, bacci mai dadi ne ya soma fizgarta taji muryarsa cikin kunnanta......"Baki fad'a min me kike so na baki gift ba." shiru tai masa, ya dan karkaro da fuskarsa ya mannawa lips dinta sumba yace."Nasan kina jina kikayi shiru nace ki fada mun dukanin bukatunki zan miki mutukar zaki zauna dani mu raya sinnar ma'aiki." Da jin wannan magana tashi, sai tayi zumbur ta mike daga jikinsa, ya shiga mamaki, da sauri ya rike hannunta shi ya dauka wani abin ne yace."Lafiya dai." "Ka daina tunanin zan cigaba da zaman aure da kai na gane kawai saboda ka dandani zumata kaji yanda take shiyasa kake so nayi ta zama kana mora ta to ni ba'a abinda nake bukata a gurinka ဝ,a yanzu nafi bukatar rabuwa da kai sama da komai, tunda bukatar ka ta biya a kaina to sai ka sak.....! Kafin ta karasa ya rufe mata baki! ya janyota ya kamkame! kam! jikinsa har rawa yakeyi...Shi yanzu ko bakin bindiga a dora masa a ma'kogwaro aka ya saketa ba zai saketa ba sai dai akashe shi....Wannan masifaffan dad'in da ya samu a jikinta a wannin da suka wuce su kawai yake tonowa....." Kada ki sake fad'in Wannnan maganar Wasila."! Tunda suke dashi bai ta'ba kiran sunanta ba kamar yau! Ya cigaba da cewa''Bana jin tunanin zan iya rabuwa dake koda kuwa za'a kashe ni sai dai akashe ni! Na tabbata ke alheri ce a tare dani kuma kece kike zame min matar sunna matar da ta dauke min wani nauyi da yayi shekara da shekaru a jikina yana damuna, ina rokon Allah ya bani zuria mai albarka a tare dake, ki kauda dik wani abu da ya faru a baya, yanzu zamuyi zama sosai ni dake irin wanda ma'auta sukeyi nayi miki alkawarin rike ki da amana Insha Allah. Kalamansa sun so suyi tasiri a tare da ita, wata zuciyar tace"Kada ki yarda ki zauna da wannan tsohon haka kawai da kuruciyar ki bayan haka kuma baki cimma burinki ba idan kin zauna aure da Ahmadu shine yaci riba dake ba ke ba, ki nuna masa bakya neman komai a hannunsa kin fiso ki futa ki nema da kanki. Kalamai ya dinga yi mata masu sanyi da kassara jiki! yana dan shasshafa jikinta, Jinsa kawai takeyi amma ba tajin zata iya zaman aure dashi gaskiyar magana kenan, ya gama zamanshi tsofai tsofai dashi yazo yace sai ta zauna aure dashi saboda yaga da akwai mamora a jikinta to bazai yiwuba. Baccinta tayi ta barshi yana magana shi kadai, jin saukar numfashinta k'asa-kasa yasa ya fahimci cewar tayi bacci sai ya sake ringumeta tsam! a jikinsa, yana kokawa da zuciyarsa kar ta rinjaye shi a kanta. Bacci sukayi mai dadi ita dashi baccin da suka dade basuyi irin shi ba mussaman ita uwar gayyar da asuba da 'kyar ya cireta daga jikinsa duk ta nannade shi fuskata dai-dai tashi numfashinsu na bugun juna....Rufe mata jiki yayi ya sauke daga bed din ya nufi toilet, wanda ya soma yi kana ya daura alwala ya fito....Dai-dai lokacin ta bude idonta ta ganshi yana goge jikinsa da karamin towel, a gurguje taga yana shiryawa har ya kammala ya juyo idonta tayi saurin rufewa, har sai da ta ya fita daga dakin, kana ta daddafa ta mike zaune, blanket din ta dan janye daga jikinta taganta sintir girgiza kanta kawai tayi, ta fara kokarin sauka hannunta ta dora kan wayarshi, tayi saurin dauka tana dubawa, ajiyar zuciya ta sauke a hankali ga dama ta samu, sai da kuma bata san meye security na wayar ba, Sunanshi ta rubuta da babban baki, ta'ki budewa, sai ta gwada rubuta sunan nashi da karamin ba'ki sai kuwa ta bud'e! Murmushi ta saki tana fadin"Alhmadullhi." Numbar camas tasa da sauri ta fara kiranta....Camas nacan duniyar bacci taji shigowar kira cikin baccinta dake dama bata kashe wayarta sabida yanayin sana'arta wani dan iskan ma da asubah zai kiranta kuma taje.....Muryar Wasila ta daki dodon kunanta ta mike da sauri tana fadin"Wasila lafiya da asubah haka."? "Camas! ya fita sallah ne na samu na dauki wayarshi , wai shin ya akw cikine? guy nan fa naga da gaske yake wallahi, jiya sai da ya rabani da mutuncinta sannan sai wani karyar da wuya yake wai dole na zauna dashi yana so na da sauransu.....Kai tsaye Camas! tace" Wallahi kada ki yarda dashi yaudarace kawai yana so ki zauna ki cigaba da bashi dadi ne ya samu kankanuwar yarinya ai kawai kiyi takanki yana gama morarki zai sake ki. "Ke har sai kin bani shawara ma! a she kin manta ra'ayina, ko nasha fada cewa ni ba zan auri mai shekaru ba yaro karami zan aura domin mu mori kuruciyarmu tare namijin da ya kwana biyu sai a hankali a lokacin da kake da kuruciya shi kuma a lokacin zai tsufa ya kasa biya maka bukatarka, wannan dalilin ne ya sanya naji sam bana sha'awar auranshi.....Camas! tace" Ato gwara dai kiyi da gaske dama yau nake cewa zanzo gidan naki jiya As ya bada kudi zan shigo muyi yanda zamuyi." Tace"Shikkenan misalin karfe nawa zaki shigo." ? Gaskiya da wuri zan shigo dan yau ma zamu zauna da governor wajejen goma da rabi ki saurari zuwa." Wasila taji kamar tabi Camas! gidan gomnati, tace"Shikkenn sai kinzo din." numbar Rashida ta kira a kashe ta Uwani ma a kashe, har tayi niyyar kiran As sai kuma ta fasa tana jin tsoron kar tana tsaka da kiranshi ya shigo ko kuma ya gane alama....Duk sai da ta goge numbobin mutanan da ta kira ta ajiye masa wayarsa. Kafin tayi wanka sai da ta dade cikin ruwan zafi, kana tayi wanka da alwala ta fito daure da guntin towel.....Gashin kanta take kokarin busarwa ya shigo dakin.....Kai tsaye bed ya nufa ya kwanta rigingine yana kallonta har ta gama busar da gashin ta gyarashi tas ta daure shi cikin katon ribbon......Riga da wando ta dauko masu dan kauri tasa a jikinta ta daura dankwalin abaya kana ta hau kan dadduma ta tada sallah. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya dauke idonshi da kanta, yaji dadi sosai da ya dawo ya tadda ta tashi cikin kuzari da lafiya kuma ya lura jikin nata ya dan sake tinda ta daina cije bakinta da tafiya da kyar. Tese message ne ya shigo wayarshi, ya mika hannu ya dauka yana dubawa, sabuwar numbar ce, ya bude yana dubawa _Kai Wawa! kayi gaggawar sakin wannan yarinyar da ka aura domin ba tsaranka bace idan ka'ki kuma wallahi rayuwarka na cikin had'ari_ Daya message din ya bude yana karantawa cikin mamaki......... _Za kayi tunanin ko daga abokanan hamayyar ka ne to ko daya kar kayi tunanin haka, mu daban muke kuma muna bibiyar lamarin wannan yarinyar dake tare da kai! saboda haka kwanciyar hankalin ka shine ka saketa idan ba haka ba to sai mun kashe kaaaa!_ Zufa ce ta shiga ketowa daga ko wace kusurwa dake jikinsa test messages din yake maimaitawa yana mamaki har ta karaso inda yake bai sani ba, sai maganarta da yaji a tsakiyar kanshi....."Ya muke ciki da kai? Ya dago kansa yana kallonta cikin tsananin mamaki! ta tsaya kanshi tana masa magana ga tsal ga tsal!! D'an bata fuska yayi yace."Wannan wane irin abu ne? ba tarbiya ce bace wannan babu gaisuwa kin tsaya min aka kina min magana babu d'a'a." 'Kasa tayi da kanta ganin kamar ranshi ya 'baci! Wayar hannunsa ya mika mata yace."Ko ina da masaniya kan wannan test din." Ta kar'bi wayar tana dubawa.....D'an ta'be bakinta tayi ta mika masa wayar ba tare da tace komai ba.....Yace."Kinyi shuru ko kin san masu numbar ne? ki fada min nayi wa tufkar hanci al'amarin ba ni kadai zai shafa har dake." Tura baki tayi tace"Ni ban san komai ba." Ya mai da kanshi fuskar wayar yana sake duba test din....Kimanin minti biyar ya dago kansa yana kallonta, tana nan tsaye inda take, yace."Koma dai su waye to kice musu basu isa su sanya ni na rabu dake ba komai sharrin su, zasuyi su bari, Ahamdu yanzu ya soma auran Wasila babu gudu babu ja da baya idan kuma mutum ya cika shi d'an iska ne to ya bayyana kanshi." Yana gama maganarshi ya mike ya fita.....Zama tayi gefan bed tana nazari, ko dai Camas ce ta soma aikinta? babu shakka itace to ko dai As ne yasa sabuwar numbar don ya tsorata Ahamdu din to ko ma dai waye hakan yayi mata dadi gwara a tsoratar dashi, yaji baya bukatar zama da ita. Yana fita ya nufi bakin gate, duk suna xazzaune suna ganinshi suka mike da sauri gaishe shi suke yana amsawa kafin ya mai da hankalinsa kansu, dik sun nutsu suna sauraransa, Yace."Ina so ku sake sanya ido sosai a cikin gidan nan nasan dani daku amana ce ta hadamu to ku rike min amanata ku kula da akinku, zan sanya Cctv cemara a gidan nan saboda wani dalili ba wai dan kun gaza ba ko wani abu daban! No! ina da dalilina nayin hakan, walau mace ko namiji ban yarda ya shigo gidan nan ba sai kun shaida min a waya na tabbatar muku da ku barshi ya shiga, ina fatan kun fahinta." Suka amsa da insha Allah zamu kula sosai Yallabai." Sallama yayi musu ya koma cikin gidan. Yana shiga parlor Rabe ba shirya daining kai tsaye daning din ya nufa, Rabe ya mika gaisuwar sa ya amsa a sake kana yace."Ya hada mishi tea, da sauri Rabe ya sha masa tea mai kauri amma bai sanya masa sugar sosai ba kwara biyu kacal yasa saboda yasan ogan nashi baya son zaki da yawa, soyayyar doya da kwai ya zuba mishi a plete zai shafe biredi da buttur ya hanashi alamun baya son buttar din ya dauki cup din tea din yana kurba kadan kadan........break fast dinshi yayi hankalinsa kwance sam! bai wani daga hankalinsa kan mutanan da sukayi mishi test messages ba yasan duk karya ne wai shi zasuyi wa barazana wannan messages din nada nasaba da government house zasu ninke shi baibai ne kuma ya tabbatar da cewar ita wasilan tasan duk abinda yake faruwa yana ganin ma kamar da hadin bakinta......yanzu ne ma yake jin wani karfin gwiwar xama da yarinyar tunda ya lura tana da rana a gurinsu. Ta dauka zata ganshi a zaune ya zabga tagumi ko taga damuwa a tare dashi, sai taga cup din tea a hannunsa yana kur'ba da latsa wayarshi ga fuskarsa a sake kamar ma murmushi yake yi aikuwa dai murmushin yake yi, dan message Khalifa ya turo masa yana masa bangajiyar dukan ruwa, sannan wai Afnan tana gaishe su, kana kuma tace abawa amarya hakuri! Shine fa abin ya bashi dariya yake murmusawa, Jin motsin fitowarta yasa ya dago kanshi...Tayi saurin kauda nata kan kamar munafuka tayi nufin koma wa dakin...."Ki zo ga sa'ko Afnan tace a baki." Yafada still da mirmushi a fuskarsa, ta dan juyo tana kallonshi, girarsa guda ya daga mata (sigina) yana sakar mata mirmushi...Ta tsani wannan halin da yake mata shi ba yaro ba ya dinga abun yara....da kamar kar ta je sai kuma ta nufe shi, tana tsayuwa kanshi ya jawo ta ya zaunar kan ciyarshi, wayar ya mika mata yace."Khalifa ne ke baki hakuri tare da Afnan."! Ta dan ya mutsa fuska tana duba message din.... ya mayar da hankalinshi wuyanta yana bala'in son gashi a rayuwarsa, zame dankwalin kanta yayi ya tusa hannunsa cikin gashin ribbon din ya cire gashin ya zubo a fuskarshi, sansanawa yake yi yana sauke ajiyar zuciya, da sauri! ya cire hannuwansa daga 'Kungunta ya d'ara kan brest din ta yana.......... _*Barkamu da sallah Jama'ar musulmi fatan munyi sallah lafiya Ubangiji Allah ya maimaita mana yasa muga ta shekaru masu yawa Binta tace ayi bukin sallah lafiya, sai dai kar a manta da ita gurin rabon nam................😉😅!*_ Littafin na kudi ne...! Kika futar min da book keda Allah kika karanta kema baki biya ba keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *38* Jin saukar hannunsa kan brest dinta ya sanya ta dan zabura da sauri xata sauka daga jikinshi, ya sake matseta tsam! tsam! yana sake murza breast din da hannuwanshi, ji tayi jikinta yayi bala'in saki, ta lumshe idonta tana sauke ajiyar zuciya, hucin numfashinsa ne ya dinga dukan wuyanta hakan ya dinga saukar mata da matsananciyar kasala, motsi tayi still dai tana so ta rabu da jikinsa dan bata son a sake samun nasara a kanta, sai kawai taji ya dauketa daukar jirarai ya nufi bedroom dinshi da ita, kasa kata'bus tayi, tana ji ya kwantar da ita a hankali, ya kwanta gefanta, sai tayi axamar tashi zaune, yayi gaggauwar jawota tafad'a jikinshi, tsirawa fuskarta ido yayi yana yi mata wani malalacin kallo, baice komai ba ya tallafo fuskarta yana so ya hada bakinsa da nata, sai ta rufe taki bashi damar hakan...Kawai sai ya soma tsotsar kumatunta yana hadawa da kunnunta, ajiyar zuciya ta dinga saukewa a hankali a hankali take shigewa jikinsa tana lumshe idonta, shi kuwa da ya lura da abinda yake mata tana jin dadi sai ya bada himma sosai, da kanta ta sakalo wuyansa da hannunta tana sake tura jikinta jikinsa, wani irin dadi takeji yana ratsa ta....A hankali ya kwanta da ita, idanunta a rufe, ruf ya zare jallaiyar jikinsa, ya bar gajeran wando, Ya dan daga kafafunta a hankali, ya dauka za tayi motsi sai yaga tayi shiru sai sauke numfashi takeyi, dogon wadon ya fara kokarin zarewa, ta dora hannunta kan nashi, ba tare da ta bude idonta kallon fuskarta yayi yaga idanunta a rufe, ya cire hannunta a hankali ya karasa cire wandon ya kai hannu kan pant dinta ajiyar zuciya ta sauke tana lasar lips dinta, ba tare da ya cire pant din ba ya kai kanshi gurun ya sumbuta, kafin ya dage rigar ta ya lashi ramin cibiyarta, hannunta ta dora saisayayyar sumarshi tana wata iriyar shashsha'ka, Shima ya riga duk ya wani susuce, jikinsa ya soma kyarma, ya dagota 'kam yayi mata ya zare rigar jikinta, manya manya nonowanta suka wanke masa ido, yaga yana nipples din suka sake girma da kauri sun tsuke guri guda, hannu yasa ya dan ja guda daya, ta zabura! tana sakin nishi, bakinsa ya dora a kai ya fara sha, yana lumshe idonsa! Ajiyar zuciya ta shiga sauke wa tana sake sakin jikinta tare da bud'a masa kafafunta sosai ya shige cikin jikinsa ya manneta ta a jikinsa bakinsa 'kam! kam! kan brest dinsa sai sha yake yi tamkar yaron da ya shekara bai sha nonon uwarshi, hannunsa ya kai kan daya brest din da ya isheta da kaikyayi, ya kama nipple din yana mirzawa, ji tayi tamkar zata shid'e saboda dadi, a take ta dinga jin ruwan ni'ima na gudana daga jikinta bata bukatar komai sai sex sai wani irin abu gabanta ke mata......Sun jima manne da juna kafin ya mikar da ita ya zauna da ita a jikinsa, bakin gado ya zura kafafunsa suka sauka kasa still tana manne a jikinsa bakin sa kan nononta yaki ya cire, ita kuma ta sarkafo wuyansa da hannuwanta sai shafa bayanshi take da suman kanshi, hannunta ya kamo ya dora kan jijiyarsa dake cikin wando ta mike sosai! ta dan rike a hankali tana matsawa, kallonta yayi da burkitattun idanunsa ya d'aga mata gira, wai ta cigaba da ta'ba masa, Ita abin ma tsoro ya bata ganin abar tayi wani irin tsayi da kauri!! ya zura hannunta cikin wandon yana lumshe ido!! saman ta dan murza kadan da hannunta, Ya sauke ajiyar zuciya yana sake kamkameta tare da tsotsar nonon dake bakinsa. Lumshe idonta tayi sai taji tana jin dadin ta'ba jijiyar a hannunta, kawai sai ta shiga shafa ta a hankali tana lailaya saman ta, "Ahhh! Subahanallah!!!!! Abinda yake ta fada kenan yana sake cizon nononta kamar zai cinye shi ya huta, a take ta dinga jin santsi santsi a hannunta hakan ma ya taimaka mata sosai gurin lailaya wa a hannunta, a gigice! ya dan gyara da ita a jikinsa ya zare wandon ya sauka sai gwiwarshi abar tayu tsalle ta fito ta tsaya 'kam! tana harbi! shagid'addun idanunta ta zuba su a kan joystick din, kafin ta sauke a jiyar zuciya mai zafin gaske, mazaunanta ya d'aga da hannunsa ta sake rike wuyanshi sosai shi kuma ya kamo jijiyar da hannunshi, ya saita dai-dai ramin ya fara kokarin sanyata, to da yake akwai ruwan ni'ima sosai! bai wani sha wahala ba ta shige amma dai ta dan ji zafi amma ba irin na jiya ba, ware kafafunsa yayi sosai ya xaunar da ita, suka tsirawa junansu ido, ya kai harshensa ya lashi lebunanta ido ta rufe, tana dan motsa jikinta jijiyarsa dake cikin raminta ita ke mata motsi so take taji ya fara sosa mata inda ke mata 'kaikayi, yasa hannunsa ya juyo da fuskarta ta kalleshi da mici micin idanunta da sukayi jawur........Girar shi ya daga mata guda, kafin ya tallafo mazaunanta a hankali ya soma yin sama da 'kasa da ita...."Ahhh!!! Ta fad'a tana shan yaji! ai bata san sanda ta cigaba da yanda yake ba, sai ya kyaleta kawai ya mai da hankalinsa kan nononta yana shansu da tand'esu.....Ihu!! ta soma saki tana 'kara bugunsa da karfin gaske kamar dai wacce ta saba da harkar har bata so ta su'bce daga ramin a gigice! take mai da ita, tana sake bada himma yayin da take jin ta tamkar tana yawo a gajimare saboda tsananin dad'in dake ratsa ta, ji takeyi da zata dawwama a haka ba zata damu ba, jijiyar sa sai ta'bo mata gurin dad'inta take....."Wayyo... Allah dad'i nake ji kamar zan mutuuuu...." Tafada muryarta na sar'kewa, bakinsa ya cire daga brest dinta ya Juyo da fuskarta tana fuskantarshi har yanzu bakinta ya'ki mutuwa sai sambatu takeyi tana sake bugunsa (Ta tabbata dai 'Yar Gaske jaruma za kuwa ta siye zuciyar Ahamdu da wuri) A gaggauce ya hade bakinta da nasa, suka fara tsotsar junansu, hakan yayi mata dadi sosai, da sosai ta cigaba da bugunsa fat! fat! fat! tana sake ruko wuyansa shi kuma yana sake bude mata kafafunshi domin jin dadinsu.. *_Duk namiji baya son mace tayi masa gim! a kwance lokacin da suke sex suna so idan sunyi miki abu kema kiyi musu idan da hali ma, ki hau kansa ki buge shi sosai da sosai, zaki ji dadi kema ki jiyar dashi dadi, kuma zaki kara martaba a idonshi 'Yar uwa harkar auratayya ba'a jin kunya idan kikace haka kuwa to wallahi xaki zama koma baya a gurin miji dan tsanar ki zaiyi yayi ta hango wata, ki dage ki zama karuwa a gurinsa duk salon da yayi miki kema kiyi kokarin yi masa, sai kiga kun zauna lafiya, mafi akasarin abinda ke faruwa kenan,a zamantakewar aure, kiga anata samun sa'bani to daga kinyi bunkice sai ki gano ga in da matsalar take, saboda haka mata mu dage kwarai gurin ganin mun mallaki mazajanmu ba tare da munbi boka ko dan tsubbu ba_* Lokacin da suka zo yin relizing, 'kam! 'kam! jununsu sukayi, suna wani irin abu da sambatu, shi dai Ahamdu yafi kiran sunan Allah ita kuwa Uwar kwadayi da zulama ai ba abinda take sai ihu! da tand'ar bakinta, tabi ta makale shi tana ihu!! har sai da ya rufe mata baki da nashi kana aka samu lafiya.....Plate yayi kan bed din tana samansa, kimanin mintina goma hankalinsu ya dawo jikinsu, ta bude idonta ta ganta kwance a samanshi, gashi har yanzu jijiyar bata fuce daga jikinta, ba da azama ta mike tana kakkare jikinta, hawaye ne ya wanke mata fuska sosai...."Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un."! Abinda ta fada kenan tana shashsheka! Ya janyo hannunta ta fuzge! tana nuna shi da ya tsa, mikewa yayi zaune ya janyo gajeran wandonshi dake kusan kafafunsa ya rufe jikinsa, kana ya kalleta ta kalleshi, ganin hawaye sha'be sha'be a fuskarta sai ya bashi mamaki...Magana zaiyi sai ta daga masa hannu kawai, kamar ta hadiyi zuciya ta mutu, taja bed shirt ta kudindine jikinta dashi ta mike tana tangadi ta nufi toleit, Ya jima yana mamakinta kafin ya mike ya bita toilet din, sai kawai ya tadda ta ta hada kai da gwiwa tana ta razgar kuka....."Wai kukan me kikeyi ne kamar wacce ta aikata haram."! "Haram na aikata tunda ba'a son raina ba yaudarata kake."! Tafadi maganar tana shashsheka....Yace." Kada ki sake fadar wannan maganar! Kina wasa da aure ko? kinyi aurtayya dani bisa 'ka'idar musulunci kuma kice haram kika aikata baki da hankali ashe." "Eh din bani dashi! tafada tana mikewa tsaye ya kalleta cike da mamaki! Ta cigaba da cewa " Me yasa tunda kasan halina kake ta'bani bana so bana son zama da kai dole ne, ni a sake ni naje na cigaba da harkokina bana son auran." Ranshi ya baci sosai ya fitar da hannu a fusace! ya bata lafiyayyar mari! "Ashe baki da kunya Ni zaki tsaya kina fadawa wannan maganar? zagina zaki ko me? Kukanta ya sake yin 'karfi tace" Ni ba zan zage ka ba amma nace bana sonka kawai ka sakeni dole ne."!? Yaji wani bala'in takaici ya rufe shi, bai sake ce mata komai ba, ya fara hada ruwan wanka rashi idan yayi dubu ya baci tunda yake babu wanda ke iya kallon kwayar idonshi ya fada masa maganar da ya gadama kamar yarinyar, 'Yar karama da ita ta iya yi mishi rashin kunya ya kuma ya kasa daukar mataki, Yana jin yanda take kuka da 'kunkuni ya dinga ya'ki da zuciyarsa a kanta, ko kusa ko alama baya so yake dukanta, tausayi take bashi sosai yasan kuma 'kuruciya ce ke damunta da tana da hankali da duk ba zatayi mishi wannan rashin kunyar ba....Ya gama wankan shi ya fice ya barta a toliet din....... Littafin na kudi ne....! Kika futar min da book ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 11:50 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys *39* Da kyar ta samu tayi wanka ta fito daga toilet din idanunta jawur zuciyarta ba'kikirin wani irin haushin kanta da kanta takeji tana ganin da ta jajurce da dik haka bata faru ba, amma daga yau ta dauki alkawari ba zata sake bari ya kusance ba dole ne tayi taka tsantsan dashi......Har ya kwanta sai ya mike da hanzari ya fita, Garba na can zaune cikin wata rumfa dake harabar gidan ya hangi fitowarsa, da sauri ya mike ya iske inda yake, yana isa yace."Garba ka dauki waccan motar da na fita da ita jiya ka kaita car wash yanzu." Garba yace."Okey sir." Key din motar ya mika mishi ya koma ciki Garba ya nufi parking area din domin daukar motar.....Yana shiga dakin tana fitowa daga toilet din ko kallonta baiyi ba ya nemi guri ya kwanta dan bacci yake jo sosai, Ta zumbura baki tana watsa masa harara ta wuce....Wardorbe ta bude ta dauko riga da siket na kanti dake kusan kullum sai ya shigo mata da sabbin kaya shiyasa kullum cikin 'bata su take yi, ba tare da tasa breziyya ba ta sanya rigar kana tasa pant ta zura siket din ta gyara gashinta ko mai bata shafa ba ta fice daga dakin tana me buga kofar da karfi! Bude idanunsa yayi yabi kofar da kallo, Ya maida idon ya rufe yana girgiza kanshi. Dainig ta zauna ta hada break fast tanayi tana nazari itafa ta dauka fita zaiyi kuma ya nemi guri ya kwanta ga Camas! tace za tazo.....Bayan ta gama break fast din sai ta koma dakin. nan ta tarar baccinsa yayi nisa sosai ta lallaba a hankali ta dauki wayarshi kan stool ta zauna da sauri ta turawa Camas test! _Camas! Ya za'ayi ne guy nan fa bai fita ba gashi a kwance yana bacci_ Camas na driving tana duba test din sai ta bata amsa kamar haka. _Aikuwa ganinan ma akan hanya dan na kusa zuwa_ Amsa ta bata kamar haka. _Okey shikkenan bari nasan yanda za'ayi yanzu zan fita gurin masu gadin tunda bacci yake_ Tana tura mata ta goge numbar ta ajiye masa wayarsa hijab din da take sallah ta zura ta kama hanya ta fita..... Suna hango zuwanta duk sai suka sha jinin jikinsu, mussaman Wanda ta ta'ba mari kwanaki kas yayi da kanshi....Ita kuwa tayi bala'in shan kunnu ta karasa inda suke....Rige rigen gaisheta sukeyi ta amsa a ya tsine kana tace"Ina da bakuwa yanzu zata zo saboda haka tana zuwa ku bude mata kofa ta shigo. Duk sukayi kas da kansu sanin da sukayi cewar abunda ta fad'a ba mai yiwuwa bane dalili yallabai din nan bai fita ba kuma bai jima da sake yanka musu winning ba, Ganin duk sun sunkuyar da kansu kasa ne yasa ta buga musu tsawa tana kallon Sunduki tace"Yana ga duk kunyi shiru ne, nace muku bakuwa ta zata zo ko baza ku bude mata bane."? Garba yace."Madam! bamu ji daga bakin Mai gidan ba." Hannu ta daga masa,"Kai Garba ka fita daga idona na rufe na lura duk kafi kowa za'kewa a gidan....Shi mai gidan ne ni kuma matar gidan ce ni wakiliyarsa ce saboda haka ba dole bane sai kaji daga bakinsa." Yace."Madam! kiyi hakuri bari mu fara kiranshi a waya tukkuna." Ranta yayi masifar baci! a hasale tace."kar ka ma wahalar da kanka bacci yake yi." Yace."Okey to idan ya tashi sai muyi maganar." Ji tayi kamar ta gaura masa mari....Camas ! tayi parking din motar ta ta firo tana dan kwankwansa gate din, Garba ya bude karamar kofa, Yana lekenta ya ganeta sarai babbar kawarta ce, Camas ta tawo gadan gadan zata shiga, Garba ya mai da kofa ya rufe, sai ta tsaya turus! Wayar ta ta fito da ita tana kiran numbar da Wasilan ta kirata da ita domin ta shai mata......Wanda yayi dai-dai da shiga Wasila dakin a fusace! zata tashe shi daga baccin sai kiran wayar ya shigo ta dauka, da sauri ta fita palor....."Camas! 'Wannan dan iskan Garban ya kafe kai da fata sai da izinin mai gidan zaki shigo karki damu yanzu kome za'ayi za'ayi zan tashe sa a bacci ki dan jira minti biyu." Camas! tace."Okey to shikkenan." Kashe wayar tayi ta koma dakin....Bacci yake sosai da alama kuma yana jin dadin baccin ta tsaya kanshi as'useul "Ka tashi ina da magana da kai."! ka tashi ina da magana da kai! kalmar da take ta faman nanatawa kenan.....Ya bude idanunsa da sukeyi masa mugun nauyi, ya ganta tsaye 'kerere a kanshi, ranshi idan yayi dubu ya 'baci! har yaushe yarinyar nan zata daina yi masa kutse ne!? ya sha fad'a mata yana da matsala idan yana bacci ba'a tashin sa amma ta'ki ji! Hannu bibbiyu ya dora saman kanshi yana jin wani irin jiri da hajijiya, bakinsa ya shiga motsawa da alama salati yake yi da kiran sunan Allah, Sai taji ya dan bata tausayi, kadan, ta dan tsira masa ido tana kallon yanda bakinsa ke motsi yana sake rintse idonsa, kafin ya bude idon akanta Saurin sunkuyar da kanta tayi saboda ganin yanda kwayar idonsa ta wani burkice kamar ma ba ita yake kallo ba, mikewa yayi tsaye! tace" Ina so in magana da kai 'kawata ta kawo min ziyara sun hanata shigowa wai sai ka basu umarni." Ba tare da yace mata komai ba ya kama hanya domin barin dakin, so yake ya bar mata dakin tun kafin ta kashe hi. Da sauri ta tari gabanshi........Aikuwa ya wanke fuskarta da mari mai shiga jiki, tayi saurin dafe kumatunta ba tare da tsammani ba! Tureta yayi ya bude kofa ya fita, Hawaye ya wanke mata fuska a fusace! tabi bayanshi, " Sai dai kuma me? Bakin kofar daya bedroom din taga ya yanke jiki ya fad'i!! A gigice ta nufi inda yake tana tatta'ba jikinsa, Ya rike hannunta guda yana kokarin aro jarumta ya mike, tsaye, sabida yanayin karfin nasu ba daya bane yasa ta afka kansa, sai ya koma ya kwanta kasan ties tayi kwance a jikinsa, tana jin yanda numfashinsa ke fita da sauri da sauri.... Kimanin minti goma suna a haka, kafin taji ya dauketa cak! daga jikinsa ya ajiye 'kasan gurin ya mike kallo ta bishi dashi har ya bude bedroom din ya shige tare da mai da kofar ya rufe.....Ta jima zaune a gurin kafin ta yanke shawarar binsa....Yana kwance rigingine ta same shi yana lumshe ido so yake ya koma baccin amma yaki zuwa, Simi-simi taje ta tsaya kanshi....Ya bude idonsa yana watsa mata harara, Da sauri tace"Don Allah ka taimaka kace su barta ta shigo kaji."! idanunsa ya mayar ya rufe, yana jinta sai magiya take masa harda kuka, idanunsa a rufe yace "Je ki dauki min wayata." Da sauri ta tafi....Ta shigo hannunta rike da wayar....Yana dubawa yaga miss call har guda uku kuma bai san numbar ba bai damu ba, ya nemi numbar Garba ya bashi umarnin budewa Camas! kofa....Yana gama wayar ko godiya ba tayi ba ta buge sikit dinta ta fuce daga dakin......Ko kalli bai bita dashi ba saboda tsabar yanda yake jin haushinta. Tana tsaye tsakiyar parlor Camas! ta shigo, tana fad'in"Kai gidanan akwai matsala wallahi ace kullum kafin a bar mutun ya shigo sai an gasa shi a rana tukkuna." Da sauri Wasila ta rufe mata baki ta kama hannunta suka shige bedroom dinta, Camas! ta dinga kallon bedroom din tana sha'awar ina itace ke dashi, komai na dakin na waje ne ya tsaru sosai dakin sai kamshin turaran Ahamdu yake ta zauna kan sofa tana bin Wasilan da kallo gani tayi mata tati fresh har 'kiba ta kara sai kyashi da bakin ciki ya sake nunkuwa a cikin zuciyarta amma ko da wasa bata nuna a fili ba....Tace"Kikace Ahamdu na gidan bai fita ba.''? Wasila tace"Eh mana ke da baya gidan ai sai dai ki juya dan wallahi komai nacin mu wancan matsiyacin garban ba zai bari ki shigo ba, ranar nan ma da kika shigo dan baya nan ne amma yanzu ya kafa ya tsare a bakin gate sai kace na ubanshi wataran sai na masa rashin mutunci wallahi." Camas! tace"Ai fa naga alama dan dana shigo wani irin bahagon kallo naga yanayi min na watsa masa harara na wuce." Wasila taja tsaki da fad'in"Rabu da dan iska kawai meye labari? ina fatan kina zuwa kina duba su Uwani ko."? Tace"A haba kullum kafin na fita sai naje mun gaisa na kwantar musu da hankali kuma babu abunda suka nema suka rasa dan As na tsaye a kansu." Ajiyar zuciya ta sauke tace"To nagode kawata yanzu wane shawara muke ciki." Camas! tace"Duk yanda za'ayi yau ba zan bar gidanan ba sai na kar'bi numbar wayar saya daga cikin su amma kuma numnar wannan katon zan karba naga kamar shine babban su." "Eh hakane ki kar'bi tashi sai ku kashe magana." Camas! tace"Bani labari hajiyata jiya kina min bayani kice har an buge harka sadakin 5k dai ya tabbata hahahaha." Camas! ta kare maganar tana kyalkyala dariya. Takaicin duniya ya kashe wasila tace"Ke banza daina dariya Guy nan fa a hannuna yake wallahi dan tunda ya lashi zumata yaji ya susuce ke bakiga rawar jiki so yake ma na fadi me nake so ya bani nice na'ki fad'i saboda ba wannan ne a gabana ba burina ya sakeni shi kuma a yanda na lura burinshi bai wuce na kwantar da hankalina na zauna dashi ba." Camas! taji duk ta sare da jin maganar da Wasila keyi tasani ai! dama babu namijin da zai kusanci wasila yaso rabuwa da ita, dama ai tunda taga yanda maza ke rubibinta tasan sun gano tana da muhimanci ne kana kuma tana dauke da wani sirri a jikinta, shiyasa take mata hassada ta ko wane fanni. Ya'ke tayi tace"Ai shine nake fada miki dama ba don Allah yake zaune dake ba, ni na tabbata da cewa irin su ne daga zarar sun gama morar kuruciya mace suke sakinta me ya hanashi aure tuntuni ni nasan yana neman mata tinda ya nemi kawaye na sosai sun tabbatar min dalili kenan ma da yasa yaki aure yake zamanshi a haka Wasila kiyi gaggawar nemawa kanki mafita ni tsoro nakeji ma kar yayi miki ciki nasan shikkenan kuma alkadarin ki ya karye." Da jin zancan Camas! sai gabanta ya fad'i! Ciki! Ciki! Allah ya kiyaye!!! Aikuwa camas! ta farkar da ita yanzu guy nan ya dubga mata ciki ai ta shiga uku! Tace."Camas! wallahi duk abinda ya faru tsakanina dashi tsautsayi ne amma na dauki alkawarin ba zan kara bari ya kusance ni ba har na bar gidan.....! "To kinga kuwa da kin samawa kanki mafita." Camas! ta fadi maganar tana duba wayarta tace"Kinga test din As har guda hudu sai tambaya yake ya ake ciki yanzu yace na baki wayar yana so ku gaisa." Ba tare da shakkar komai ba ta karbi wayar ta kara a kunne. Ahamdu kuwa hankalinsa ne ya kasa kwanciya da bakuwar Wasilar sai ya mike a hankali ya bude kofar dakin ya fita, Kai tsaye kofar dakin ya tura ya shiga......Dai-dai da lokacin da Wasila ke waya da As tana fad'in"Nifa ka fahimce ni As ba cewa nayi zan zauna dashi ba nima hanyar da zan ku'buta nake nema kawai ka kwantar da hankalinka kuma idan mun nemi gudumawa a gurinka to kayi mana, insha Allah zan fito mu cigaba da gudanar da harkokin m...........Idanunsu ne ya game da juna lokacin da ya shigo dakin kuma duk yaji komai a kunnenshi, sai kawai bakinta ya soma rawa tana so ta tona kanta da 'kyar dai! ta aro jarumta tace"To shikkenan Duk sanda zaku zo Camas tasan gidan sai ta rako ku.......Ya 'karaso inda suke hannuwansa goye a bayanshi..... [12/08, 7:55 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *41* Tuttureshi takeyi daga jikinta tana wani irin kuka da rokanshi da Allah ya kyaleta, shi kuma yana sake jin wani irin kuzari da karfi! A jikinsa inda yake ta sukuwa a kanta yana ha'karta sai kace wanda yake cikin gona yana aikin noma! Wani irin gumi jikinsa yake tsiyayyarwa sai ya hadu da gumin jikinta fatar jikinsu ta dinga motsi tana mannewa da juna.....Tun tana ihu da gunjin kukan har ta daina tayi la'kas! tanaji yana ta jujjuyata yana sarrafata yanda yake so yana hakarta da bugunta da wani irin karfin gaske! hawaye ne kawai ke karai kaina a fuskarta, lokaci kankani zazzafan zazzabi ya rufe, jikinta ya dinga kyarma!!!! Ahamdu kam bai san tanayi ba yana can duniyar dadi mai cike da nishadi tabbas yarinyar ta cika mace takai inda ake so akai tana da masifar dadin da yake sawa kansa ya kwance wanda har yake kasa sarrafa kansa ya shiga sambatu, bai san yanayi ba, wannan karon ma sambatu ya dingayi yana kiranta sunanta, har ya samu satysifeind....Kamar yanda ya saba sai yayi kwance a kanta, ya sakar mata dukanin nauyinshi a kanta, sai bayan mintina goma ne nutsuwarsa ta dawo jikinsa, nan yaji yanda jikinta ya dauki zafi! kuma sai wata iriyar makyarkyata takeyi hakoranta na haduwa, Da sauri ta mike zaune yana me dora hannunsa tsakanin wuyanta da akwai alamun zazzabi a tare da ita, gajeran wandon shi ya zura kana ya dan yane mata jikinta da blanket ya mike ya nufi toilet, wanka tayi ya fito a gurguje ya shirya kana yazo kanta ya tsaya, Ayya! ita a lokacin ma ta dad'e dayin bacci! Hannunsa ya dora saman kanta wanda yaga jijiyoyin gurin sun tashi nan ma yaji zafi rau!!! ya aiyana aranshi cewar kukan da taci ne ya janyo mata zazzabi da ciwon kai sam bai ji tausayinta ba, saboda tayi masifar bata mishi rai amma kuma yanzu ta dan wanke masa zuciyarsa tunda ya samu gamsuwa da jin dadi a tare da ita....Parlo ya fito da wayarsa a hannunsa yana neman numbar Dr Nasiri wato dactor din da yake duba lafiyarshi. Camas! sai da ta shafe rabin awa a cikin mota tana kuka kafin ta daddafa da kyar ta kunna mota ta bar gurin........Kai tsaye gest house din As ta nufa saboda tun tana bakin gate din gidan Ahamdu yake ta kiran wayarta ta kasa dauka tasan dai yana can hankalinsa a tashe, tabbas bata ta'ba tsammanin cewar Ahamdu mugun azzalimi bane sai yau. Tana shiga ta tarar da As tsakiyar daki yana kai komo. Tun kafin ta zauna ya tare ta da fad'in" Wai shin meke faruwa ne? tun dazu nake ta faman kiran wayarki babu amsa, na kira 'Yar gaske tanayi mun maganar banza shin haka mukayi daku dama." Camas! ta kalleshi da jan ido tace"As kalleni da kyau ka gani."! As ya dan 'kura mata ido yana kallonta, sai yaga shatin hannu a kwance a kumatunta ga gefan idonta ya dan kumbura bushashshen jini a hancinta na dama." "Subahanallahi! Camas! accident kika samu ne a kan hanya."? Yafada yana binta da kallo shifa sam bai lura da yanayin data shigo ba sai da tayi masa magana tukkuna.......Girgiza kanta tayi tana goge hawaye tace." Ahamdu ne yayi min jini da majina."!!! As yace."Subahannalahi! Wai meke faruwa ne? kada kice min yana gidan a sanda kikaje." Murmushi me ciwo tayi kafin ta girgiza kai tace"In kaga yanda nasha wahala kafin na samu shiga gidanan sai kayi mamaki! Ahamdu yana gidan kuma shine ya bada umarin yaranshi su barni na shiga bayan mun zauna da Wasila ne muna magana a lokacin ne ka kira waya to tundaga sannan labari yasha bam!bam! domin dik irin zantukan da kukayi da Wasila a waya a kunnanshi, idan nace maka yanzu wasila na raye to nayi maka karya dan sha'ke! mata wuya yayi, ni kuma yasa yaronshi ya zaneni da wata murtukekiyar bulala duba kafafuna fatar duk ta kwailaye."! Ta kare maganar tana nuna masa kafafunta. As ya dinga shawagi a dakin, Yana fad'in",Ahamdu Ahamdu!! Wannan mutumin shu'umi ne! Ni dama nasan wannan plan din naku ba zai yuwu ba saboda nasan mutumin nan da bin diddigin tsiya, ya iya cin mutunci, kuma jikina na bani ba zai saki Wasila ba dan amsar da yasa ta bani a dazu ta dameni, Hakan ya hawo kawai na yanke shawarar wani abu guda a kanshi, ke kanki kin san irin yanda nake sha'awa da kulafucin kawarki ko? nayi mata hidima da kudina da jikina duk dan ta mallaka min kanta, sai da aski yazo gaban goshi sannan lokaci guda zai ce zai yanke min jin dadi, ba zan yarda ba mutukar a kan 'Yar gaske ne, zamu zuba ni dashi, mulki kuwa sai dai yaga anayi komai nacin sa. Camas! tace"Yanzu As wane mataki kake ganin zamu dauka kan guy nan nifa ba zan yarda wannan tozarcin da yayi min ya tashi a banza ba, sai na rama amma kuma hanyar da zan bi na rama ce din ban sani ba, kana gani duk hikima da dubara irin na wasila ta kasa kubta daga tarkonsa." Yace."Idan Yar gaske zata yarda da shawarar dana yanke to duk abun zai zoma na da sauki sosai zamu ci riba biyu a kanshi, yanzu abinda zamuyi shine! mu bari a kwana biyu sai mu sake tun'tubar ita 'Yar gasken a waya amma maganar zuwa gidanshi ta 'kare zamu bullo masa ta bayan gida. Camas! tace"Shikkeen to Yanzu dai ka kaini asibiti tukkuna dan wallahi duk jikina yayi tsami! yau naga tujara da wulakancin da tunda uwata ta haifeni ban gani ba. As yayi murmushin takaici yace."Idan wannan mutumin ne to baki gama ganin komai ba a kan halayyarsa.....Key dinshi na mota ya dauka yace."Tashi muje ki kyale matsiyaci 'karyarsa ta kusa 'karewa." Camas! ta mike tana ya mutse fuska, tabi bayansa suka fita daga dakin. ****** Sosai Wasila ta kwanta jinya, dan har sai da wannan karon tasha ruwa leda uku, kwana biyu a tsakani duk ta fyad'e! tayi wata rama sai haske da ta'kara sam! bata cin abinci sai yayi da gaske sannan take ci tanayi tana kuka, yanzu kwata kwata ya daina sakar mata fuska, kullum fuskarshi a daure tam! shiyasa daga yace tayi abu ko bata so takeyi sai bayan ya fita sannan ne take cin kukanta ta 'koshi. Tana zaune gefan bed dinta sanye da wata riga mai karamin hannu ta dan kamata kadai sai dogon wando na jins a jikinta, daurin da tayiwa gashinta duk ya tuje, dan bata dade da tashi daga bacci ba, saboda yanayin magungunan da take sha ya sanya cikin nata budewa bini bini cin abinci yanzu ma robar yohgt ce a hannunta tana sha tana goge hawaye, wannan masifa ta isheta kullum kana gida a kulle an kulleka, saboda tsabar mutun yana ta'kama da kudi da iko, wannan lamari na mugun bata mata rai, duk tunani da basirar ta ya toshe kan lamarin kawai ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido....... yana Sanye da wani farin yadi irin kashimir d'in nan wanda akayi masa dinkin zaman gida ('Yar shara) idanunsa sakaye da farin glass ya tura kofar dakin ya shiga da sallama a ciki ciki a bakinsa. Ba tare data d'ago kanta ba itama ta amsa a ciki! Ya karaso gabanta ya tsaya, kamshin turaran sa ya isheta, amma dai bata dago kanta ba sam yanzu bata so ta hada ido dashi tunda dai shi ya kasance azzalimin mutum ne! '"Ya jikin naki."? Yafada yana bin jikinta da kallo mussaman kirjinta, da yaga ya sake wani kumbari dake sam breziyya bata dameta ba sautari haka take saka riga ko vest babu shiyasa in tasaka karama irin me mannewa a jiki sai su sake wani tudu shatin nipples din su fito radau! cikin rigar yanzu ma hakane ya kasance! Yayi saurin kauda kansa, yana dan sauke numfashi, kwana biyu kacal da yayi ba tare da ya ra'bi jikinta yana jin wata irin kasala da damuwa, daurewa kawai yakeyi a kanta, ace lafiyarta lau, babu abinda zai hanashi biyan bukatarshi kawai dai ya bari ne taji kwarin jikinta. Sai da ya sake wata maganar sannan tace."Naji sau'ki."! Ya dan tsirawa karamin bakinta ido yana kallo, kafin yadan shafa sajenshi yace."Alhmdullahi haka ake so dama Sai ki tashi kije parlor kina da ba'ki." Tayi gaggawar dago kanta aikuwa idanunsu ya sar'ke guri guda, tayi saurin sunkuyar da kanga kasa gabanta na faduwa......Yace."Hajja babbah ce da kanwarta suka zo dubaki dama kuma suna ta sa rana zasu su ganki basu samu dama ba sai yau ." Tayi shiru tana sauraransa, tasan Hajjah babbah a baki amma bata ta'ba ganinta ido da ido ba, sautari wani lokacin gabanta yake kiran ta a waya su gaisa kuma ta lura yana masifar ganin girmanta tunda dai ita tasan ba itace ta haifeshi ba a tarihin rayuwarsa amma ta gane tana da mahimanci a rayuwarsa.......A hankali ta mike tsaye, jikinta sam! babu kwari ta nufi wardrobe domin dauki hijab!! Yabi bayanta da kallo yana lumshe idonsa, yana masifar kaunar hips din ta, kamar itace ta dasa abinta ya zauna ram! kuma ta iya sarrafashi gurin tafiya. Tana jiyowa yayi gaggawar dauke kanshi, wata irin sha'awa na yunkuro masa anya kuwa yau! ba zai rage wa kansa wahala ba, shifa idan masifar sa ta ciwo shi kawai yayi shine samun kwanciyar hankalinsa. Gaba yayi tabi shi a baya salau-salau! Hajjah babba tare da Aunty Kubura da Salimat Suhairat suna zaune a parlo suna hira katon teble din dake gabansu cike da kayan marmari da lemuka masu sanyin gaske! Salimat kaf hankalinta na kan 'kofar dakin tun bayan shigar Ahamdu dakin takasa nutsuwa wani irin masifaffan kishi ne ke cin zuciyarta, idanunta sunyi wani irin ja! so takeyi kawai taga macan da tasha gaban mata tayiwa mata zarra! da har ta samu nasarar auran Ahamdu cikin sauki........ suna fitowa dik suka bisu da kallo Hajjan babba sai washe baki takeyi ita kuwa aunty Kubura kadaran kadahan! take, Suhairat sai l'eka bayan Ahamdu take tana so ta hango Wasila, ya dan kauce kadan yana fad'in"Kuyi hakuri fa Hajjah tana toilet ne shiyasa ba mu fito da wuri ba." Kafin hajja tace wani abu Suhairat ta mike tsaye da sauri! tana nuna Wasila tace"Ke! 'Yar Gaske! dama kece matar Yayanmu."! Wasila ta d'ago kanta da sauri tana kallon Suhairat! sai taga tamkar ta san fuskarta a wani guri.....Kallon junansu suka shiga yi kafin 'kankanin lokaci naga Wasila tayi wani bala'in shan kunu! tana watsawa Suhairat din kallon banza.............! Littafin nan na kudi ne! Kika futar min da book keda Allah kika karanta kema baki biyani hakkina ba keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [12/08, 7:55 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *42* Salimat ma dake zaune tayi masifar mamakin al'amarin, Wasila yarinyar da tayi 'kaurin suna a jahar kano yarinyar dake harkar bangar Siyasa da maza! marasa d'abi'a da kamun kai! Yarinyar da duniya da mutanan cikin ta keyi mata kallon banza, Yarinyar da idan taje makaranta bata aikin komai sai shashanci da guje guje da kula kulan maza, Suhairat da Salimat sunyiwa Wasila farin sani a lokacin suna karamar makaranta pramary skull, ta *'Dandago* Lokacin babu wanda bai san Wasila ba a cikin makarantar saboda rashin mutuncin ta da kuma yanda ta raina malamai, sam ba karatu ke kaita ba kayan tallah take tafiya kamarsu alawar madara da gullisuwa kantin gana aya ji'kakkiya da sauransu, haka zata ciko jakarta dasu, daga an futa break ta fito ta baza kayan sana'arta tayi ta cini ki......Ita da Camas! halinsi yazo daya sosai shiyasa suke kawance ita Camas! d'an malale take dafowa ta zubo a karamar kulla itama idan an fita break tayi ta siyarwa, sam! basa gane komai na karatu, ta wani bangaran gwara Wasila kan Camas, Wasila tana iya rubutawa ta karanta, Camas! kuwa ko sunanta bata iya rubutawa, Malamai sun sha korar su daga aji saboda surutu sai su fita suna dariya da murna da fadin dama haka suke so, sai su sami gindin bishiya suyi zamansu suna cin gyada da shewa babu abinda ya damesu su dama suna zuwa makarantar ne domin su kasa su siyar su samu kwabo da dari......Lokacin da headmaster ya gaji da abunda sukeyi a makaranta, dan har sun soma lalatawa wasu dali'ban da d'abi'un su, sai kawai ya koresu daga makarantar yace ko wacce tazo da iyayenta, Rashida ta dinga kuka ganin an kori yayyanta, su kuwa bakin ciki duk ya ishesu suka dinga d'urawa Headmaster din ashar! suna ganin kamar yana musu bakin ciki ne da kudin da suke samu su sam! ba karatu sukaje ba, Uwani tace"Ai kuwa wallahi gobe da kaina zan yafa mayafi naje na samu shugaban makarantaer ai wannan wulakanci ne kawai muna samun abin bukata zai cuce mu, zan fada masa ke marainiya ce ubanki ya mutu. Kashe gari da safe suka nufi makarantar Lokacin Mahaifin Camas har ya mai da ita suka ganshi yana kokarin fitowa, sama sama sika gaisa kana suka wuce ofis din headmaster, Uwani na shiga ta fashe da kuka, duk malaman dake zazzaune suka zuba mata ido, sai ta kama hannun Wasila tace"Malam wannan yarinyar marainiya ce ubanta ya mutu jiya tazo tana kuka tare da shaida min cewar wai ance ta daina zuwa sai Ubanta yazo tukkuna, Wasila bata da Uba ya mutu nice gatansu ita da kanwarta." Headmaster yace."Baiwar Allah daina kuka zauna kiji dalilin da ya sanya na koresu daga makaranta ita da kawarta. Uwani ta zauna tana share hawaye Headmaster ya fara yiwa Uwani bayani kan shirme da shiriritar da sukeyi a makarantar sam! basa gane karatu sai auki tallah da kula kulan maza." Uwani tace"Insha Allah xasu gyara ai nayi mata fada sosai a gida nace ta tsaya tayi karatu shine gatanta." headmaster yace."Ashe kin gane, yanzu shikkenan tunda kin kawo mana uzurinki, yarinyar zata cigaba da zuwa makaranta amma na soke zuwa da kayan tallah! duk sanda ta sake zuwa da kayan tallah to sai na koreta." Uwani tace."Insha Allahu zamu kiyaye." Headmaster ya kalli Wasila da tayi fi'ki-fi'ki da ido tab! bata jin zata daina tallah a makarantar wallahi jinsu kawai takeyi. Yace." Wuce maxa ki shiga aji saura in kuma ganin ki a zaune a filin makaranta kina siye da siyarwa, Simi simi ta wuce ciki Uwani tayi musu sallama ta tafi. To tana komawa gida Uwani tace"Kinga Wasila dokar da headmaster dinku ya kafa ba mai yiwuba bace, zaki sanja tsari ne idan kinje da kayan sana'ar ki to ki dinga zama a aji kina siyarwa kar ki fito harabar makarantar nasan yau da gobe mutane suka gane zasu shigo su siya." Wasila tace"Wannan shawara tayi, To haka dai ta cigaba da zuwa da kayan sana'ar ta, 'yan matan ajinsu na siya na wasu ajin ma na shigowa su siya, tsayin shekara biyu headmaster bai san abinda ke faruwa ba.. Salimat itace suke ajiya daya da Wasila, Suhairat tana aji shida, su kuma suna aji biyar, ranar Suhairat ta shigo ajinsu bayan an fito break tana neman Salimat! kawai sai taga an kewaye Wasila ana ta siyan alawar madara da kantu!!! Suhairat dake tana da mukami a makarantar, sai ta nufi gurin, tana wani cin kunu ita gata mai yalon dankwali tace"Ke Wasila ashe bakiji gargadin da headmaster yayi wa masu kawo tallah ba a gurin Assamble ba shine dake ke mai taurin kai ce kike sauya salo kike tara mutane a aji suna siya to yau asirin ki ya tono." ! Sai kawai ta hau watsi da botikayen kayan siyarwa duk suka watse a ajin.....Wasila ta kurma wani uban ihu!!! ta cakumi Wuyan Suhairat ta hau jibgarta cizo da yakushi Camas! na taya ta Suhairat ta dinga kuka tana neman dauki, Wasila ta haye ruwan cikinta sai da ta sumar da ita sannan taji dad'i......Aikuwa yan aji suka dinga ihu! da gudu Rashida ta nufi ofis din malamai ta sanar musu....A take suka shigo, aka yayyafawa Suhairat ruwa ta farfado tana kuka fuskarta duk tabon cizo da yakushi.... Headmaster ya tarkatasu gabadaya suka nufi ofis........Suhairat na kuka take bayanin abinda ya faru Wasila da Camas! suna 'karyatawa da fadin sharri tayi musu.....Headmaster ya kalli Wasila bayan ya gama jin bayanin Suhairat yace."Kin nuna min ke d'in 'yar halak ce kuma ke *'Yar gaske!* (Wannan sunan na 'Yar gaske daga bakin headmaster ya fito shine asalin fara kiranta da sunan) to tunda sannan ta ara ta yafa takewa kanta kirari da cewar ita d'in *'Yar gaske* ce har jama'ar gari suka dauka. Headmaster ya cigaba da cewa" Baki da wani amfani a cikin makarantar nan tunda dai ba karatu kika zo kasuwanci kika shigo gashi har kin sumar da yarinyar mutane kina nema kiyi kisan akai a makaranta ki jaza mana masifa to daga yau na sallame ki daga wannan makarantar har abadah."!!! Wasila ta dinga kuka tana bashi hakuri! amma yaki sauraranta, yasa aka daukowa Suhairat! paracetomal tasha da ruwa kana yace ta tafi gida ta huta, dama kuma tsakanin makarantar da gidansu babu nisa tsallaka titi za'ayi kawai su Wasila ne suke hawa mota. Wasila da Camas! suka fita ransu idan yayi dubu ya 'baci! Camas! tace"Wallahi nima nabar makarantar har abada shege dan iska kawai dama ya tsanemu." Wasila tace"Camas! zuciyata kamar ta fashe haka nakeji tsinanniyar nan tayi min asara ta kusan dari hudu gashi tasa an koreni.'' Hawaye ta share tana jin wata irin tsanar Suhairat cikin ranta.....Uwani najin labarin abinda ya faru tayi ta kutuntumawa! Suhairat ashar! tana tsine mata har da cewa sai taje gidansu ta ci mata mutunci." Wasila ce ta tausheta tace kawai ta bari ai taci ubanta tunda har sumar da ita tayi, to jin haka yasa zuciyar Uwani tayi sanyi.......To ashe tsugune bata 'kare ba, suna zaune da daddare sunyi tagumi babu abinci yunwa duk ta ishesu, sai ga sallamar dan sanda a bakin kofa......Itace ta le'ka sai kawai taga Suhairat a tsaye ita da wani saurayi da alama Yayan tane. Suhairat tayi saurin nuna ta tana fad'in "Itace yallabai." Kafin tayi aune! ya fito da ankwa ya kama hannunta ya daure! kallonsu tayi bakinta na motsi ta rasa me za tace! Yayan Suhairat yace."Sir me ake jira da itane." Dan sandan yace."Maza muje division sai kiyi bayani." Uwani da rashida suka fito suna ihu! da tambayar abinda ya faru, cikin rashin kunya Suhairat tace"Ki tambayi 'yarki." Wasila ta kalli Uwani tace"Ku daina kuka! Babu matsala kuzo muje." Uwani da rashida suka bi bayansu sai share hawaye sukeyi jama'ar unguwa na binsu da kallo. Lokacin da suka shiga stion din D.P.O nan yana dube dube! ganin kyakyawan mata Uwani da yaranta sai ya dauki hankalinsa, yace."Maza kwanci mata wannan abun me yake faruwa ne." ? Dan sandan ya kwancewa Wasila Hannunta, sai kawai ta fashe da kuka tana fadin"Shikkenan D.P.0 daga anga mutum bai da gata a duniya sai ay ta tozartashi, Wallahi duk wanda ya cutar damu Allah zai saka mana." D.P.0 yace."Daina kuka kiyi min bayani." Zama tayi kan banci tace"Ai bani ce zanyi bayani ba gatanan a tsaye ita da yayanta." D.P 0 ya kalli suhairat da ita da yayanta yace."Kuyi min bayanin abinda ke faruwa, Suharait ta soma inda inda! D.P.0 yace."Daka gani kece baki da gaskiya ina ruwanki dan tana zuwa da kayan tallah ko kuma kece shugabar makarantar."? Suhairat tayi fiki fiki da ido! yace."Idan da hali ma sai nace ki bata tara tunda kin tozarta kin zubar mata da kayan sana'arta kuma kin sa an koreta daga makaranta, to amma a bayanin da kikayi min kince ta sumar dake to ai kece kikaja haka ina ruwanki da ita? Kije babu wani hukunci da za'ayi mata ke ya kamata ayiwa hukunci." Suhairat da yayanta jikinsu yayi sanyi simi-simi suka fita daga gurin....D.P.O ya kalli Wasila yana murmushi yace."Yan mata meye sunanki ne? saboda mutuncin da yayi musu yasa tace sunana Wasila nan ta bashi takaitaccen tarihinsu, ya tausaya musu sosai yace."Kada ki damu kinji ko, ni da kaina zan mayar daku makarantar ku zana jarrabawa tunda lokaci ya kusa, komai zai wuce." Ya dauki dari biyar ya basu suyi kudin mota.....Sai murmushi yake mata nan Uwani da ita kanta Wasilan su gane akwai alamun tambaya gurin D.P.O Yace."Gobe da wuruwri ku shiryo keda kawar taku kuzo nan ku sameni zan mai daku makarantar." Tace"To yallabai mungode." Sallama sukayi masa kana suka fito daga gurin hankalinsu ya kwanta su zuwa division din ma yayi musu dadi tunda sun samu kudin da zasu siyi garin kwaki suci dama yunwa suke ji. A daran Wasila taje gidansu Camas! ta fada mata abinda ke faruwa, Camas ta dinga she'kawa Suhairat da wanta dariya tana fad'in"Wallahi Wasila ni na dade da sanin cewar kina tattare sa sirrika a tare dake ke d'in 'yar baiwa ce shiyasa nake so ki zage ki mori 'kuruciyarki kinga wallahi sana'ar karuwanci zata kar'beki tunda kina da duk wani abu da d'a namiji yake bukata a jikin 'ya mace, namiji mutukar lafiyayye ne shi ya kalleki sai yaji sha'awarki." Da jin irin maganganun da Camas! take masa ya sanya ta had'e rai! sosai tace"Kada ki sake min irin wannan maganar banzar idan ba haka ba kuwa wallahi zamuyi fada dake fadan da bamu ta'bayin irinshi ba , a duniya akwai abunda na tsana sama da karuwanci da har zaki dangatani dashi bana so kada ki sake, wannan budurcin nawa insha Allahu sai na kaishi dakin mijina." To ganin yanda ranta ya'baci ne yasa ta dinga bata hakuri Wasila tayi tafiyarta ranta idan yayi dubu ya baci hakika taji bala'in haushin camas da irin maganar da take mata, Tundaga ranar Camas bata sake yi mata maganar ba amma dai ita in ta samu wanda zasu sha minti ya latseta ya bata kudi tana yarda tun Wasila bata gane har dai tazo ta gane, ta dinga hanata amma taki dainawa kawai sai ta zuba mata ido. Tun bayan komawarsu makarantar al'amura sukayi sauki dalili sun hakura da siye da siyarwa da sukeyi a makarantar sai suka dukufa gurin wanki da guga na mutanan dake unguwar tasu, idan kuma ta samu aikin wanke wanke gidajan amare taje tayi su biyata........Gaba mai tsanani ta shiga tsakanin Wasila da Suhairat tsakaninsu kallon banza ne da tsartar da yawu, amma basu ta'ba caccaar baki ba a tsakaninsu, har lokacin da Suhairat suka fita daga makarantar ta shiga scondry lokacin ita kuma Wasila da Camas Da salimat suka shiga aji shida, tsakanin Salimat da Wasila gaisuwa ce dan ita Salimat halin ta ba irin na 'yar uwarta bane Suhairat ita bata shiga abinda bai shafeta ba shiyasa ma dik gabar dake tsakanin wasila da Suhairat din bata shiga ba duk inda taga Wasila tana mata magana......Shigar su Wasila aji shida sai idanunsu ya sake budewa, sosai sunanta ya 'bace! daga Wasila mutane suka koma kiranta da 'Yar gaske.......Saboda yanayin da'kikancin su yasa suka fad'i a jarrabawa, su biyu ne kawai basu ci ba, Wasila ta nufi ofis tana kuka wai wallahi tayi kokari amma za'ace ba zataje scondry ba, Malam Isa shine suke dan shiri da ita, shine ya shiga ya fita ya sama musu makaranta 'yan mata ta *Sani mainage* Wasila da Camas! aka shiga socondry sai rawar kai ya 'karu, da 'yan matanci, lokacin kuma dama ana tashan balaga suka dinga tsula tsiya da rashin mutunci a makarantar, Lokacin jarrabawa nayi suka fad'i ! sunaji sunaji suna gani 'Yan ajinsu suka shiga Ss1 su suna js3 haka aka kawo 'yan 'kananun yara aka gwamutsasu! ba'kin cikin wannan yasa suka sallama makarantar suka hakura akan su tsaya wata shekarar ta zagayo, su ka daina zuwa makarantar gabadaya, Rashida na ganin sun daina zuwa itama sai ta nemi guri ta zauna alhalin ita tayi gaba sune a baya taga gwara ta hakura da karatun tunda babu su a makarantar...... *Wannan shine abinda ya faru a tarihin Wasila da ya shud'e!* *Mun dawo labari* Hajjah Babba tace"Da alama kun shaida junanku akwai alamun sannaya a tare daku." Salimat tace"Sosai kuwa Hajjah Tare mukayi pramiry da ita Sunanta Wasila Yahuza." Suhairat kusa wani irin mamaki takeyi da al'amarin ya akayi wannan 'kazamar yarinyar jahila 'yar tallah kuma 'yar bangar siyasa ra jagaliya ta samu nasarar auran Masoyinta??? Bata da me bata amsa dole sai ita wasilar sai kawai ta shiga watsa mata mugun kallo tana ji kamar taje ta sha'ke mata wuya dan takaici. A nutse ta gaisa Hajja ta amsa tana tambayar ta jiki tace"Naji sauki tana wasa da hannunta, Ta gaishe da Aunty Kubra itama ta amsa babu yabo babu fallasa, itama ta shaida fuskar yarinyar, a cikin 'yan watannin da suka gabata ta ta'ba ganinta a tv tare da governor da mukarrabansa a lokacin da sukeje duba aikin titin Wuju wuju! shine tashar stv suka nuna su, tayi ta mamakin yanda akayi wannan al'amari ya faru to amma dai zata bugi cikin 'yar uwarta Hajjah taji ko tana da masaniyar akan yarinyar dan gaskiya duniya da mutanan dake cikinta basuyi mata shaidar arziki ba mybe ma domin su cimma wata manufa tasu a siyasance ya sanya suka shiryo wannan auran kuma suka yadauri Ahamdu din ya aureta dan su kasheshi ko su shirya masa wata ma'karkashiyar........... hira sukeyi wanda ita jinsu kawai takeyi so take ma taje ta kwanta dan har yanzu jikinta bai gama kwari ba, sai kawai taji muryar Suhairat na fad'in"Yaya Ahamduo ya akayi ka auri abokiyar adawarka ina ce itace Yarinyar data shiga gidan redio taci maka mutunci ta ta'ba martabar iyayenka kana kuma tayi maka 'kazafi na zinaaaa."! Dukaninsu suka mai da hankali kanta a lokacin da take wannan maganar.......... Littafin nan na kudi ne...! Kika futar min da book keda Allah! kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [12/08, 7:55 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *43* Hajjah tace"Wace irin magana ce wannan kikeyi Suhairat? maganar ko dad'in ji babu a bakin ki." Da sauri ta bude baki za tayi magana ya d'aga mata hannunsa, fuskarsa da akwai alamun 'bacin rai! yace."Hajjah kar kiyi mamaki! da jin maganar Suhairat gaskiya ne Wasila tayi harkar siyasa a cikin harkar ma na ganta na aureta dan karan kaina ba wai da wata manufa ba." Ya mai da hankalinsa kan Suhairat da jikinta yayi sanyi sam bata zaci wannan amsa daga bakinsa ba ita ta dauka zaiyi mamaki! idan yaji maganar, Yace."Ke kuma suhairat daga yau kada na sake jin magana makamanciyar wannan ta fito daga bakin ki, nasan komai dangane da Wasila so bana bukatar bayani, ni da kaina naji na gani naje har can mahaifarta kawunta ya bani auranta kuma ya bani cikakken tarihinta naga asalinta da duk danginta, daga yau kada ki kara kiranta da 'yar jagaliya." Aunty Kubra tayi saurin fad'in"Ahamdo kayi hakuri dan Allah wallahi na rasa meke damun Suhairat wautarta tayi yawa bayan haka kuma ai kowa da kuruciyarsa mu kam mun yaba da yarinya sosai tana da hankali Ubangiji Allah ya sanya alkairi ya kawo 'kazantar daki." murmushi yayi ya amsa da "Ameen Aunty Kubra nagode." Suhairat kam tunda ta sunkuyar da kanta kasa ta kasa dagowa kunya duk ta isheta sosai taji haushin yanda ya gwaleta a gaban Wasilan ba, tayi da ta sanin fadar maganar inda tasan hakane zai faru, Ya'ke kawai ta cigaba dayi tana dan saka bakinta cikin hiraransu, dan dai ma macace mai wayewar kai da saurin sabo amma babu shakka taji haushin maganar Suhairat sai da kuma gogan nata ya wanke mata rai taji dadin yanda ya gwasale Suhairat din ya nuna musu ita din ba daga sama ta fad'o ba tana da daraja da martaba kuma ya nuna musu cewar yana kishinta tunda dai bai bada goyon baya kan su ci mutuncin taba......A hankali ta mike tace"Hajja ni zan shiga na kwanta jikina babu kwari sosai, ku gaida gida mun gode sosai." Hajja tace"To babu laifi Allah ya sawake yasa kaffarane gida kuma zaiji insha Allahu." Kama hanya tayi ta wuce daki ba tare da tacewa Aunty kubra komai ba dan ta lura da satar kallonta da takeyi a kai a kai sosai ta shiga mamakin kan abinda yasa matar take kallonta, gaskiya ta dora zarginta kan matar sam sai taji bata kwanta mata a rai ba. Da shigar ta bedroom din da kwanciyarta bai fi Mintina goma ba ya shigo.....Saurin rufe ido tayi ta soma saukar da numfashin karya alamun bacci takeyi, Ya jima tsaye a kanta kafin ya zaune gefan gadon ya sanya hannunsa yana janye bargon dake lullu'be a jikinta.....Ta sanya hannunta ta ri'ke bargon tana motsa gashin idonta......Sai da ya janye bargon sannan hankalinshi ya kwanta, hannu ya kai ya riko nata hannun, sai tayi saurin bude idonta tana kallonshi, as'usel Ya dan daga mata girarshi guda yana lasar lips dinshi, da sauri ta dauke kanta daga kanshi gabanta na faduwa, Allah yasa dai kar yace zai hauta dan ta lura idan fitina da jarabar sa ta motsa ya dinga d'age mata gira kenan........Bai ce komai ba ya haye bed din sosai....Sai ta soma kuka tana jan jikinta, Ya saki baki yana kallonta da mamaki a tare dashi yace."Me nai miki kuma? Ta'be baki tayi cikin shagwa'ba tace"Kai ne ai naga kana d'age min gira ni bana so."!!!! Sai yasa dariya yana sosa saisayayyar sumar kanshi yace."Ni ban san ma inayi ba, okey to dan na d'aga gira shine me."!? "Kai ma ai ka sani ni dai don Allah ka kyaleni wallahi bazan iya da wannan wahalar ba." Yace."Sai magana kikeyi a rufe ki fito fili kiyi min bayanin abinda yake da akwai ni ban fahimta me zanyi miki to." !? Ta sanya hannu ta goge hawayen fuskarta Tace"Dan Allah kar kayi min komai."! Yace."Ni babu abinda zan miki nima zan kwanta ne na huta Okey." Shiru tayi masa tana binshi da kallo har ya shiga cikin bargon ya kwanta rigingine tana kallon rufin dakin, Ganin kamar hankalinsa baya kanta yasa ta dan kwanta amma duk da haka a tsorace take dashi.........Sai da ya bari ta saki jikinta tukkuna ya juyo sosai tare da zura hannunsa, tsakanin waist dinta yana kokarin kwance belt din dake daure a kugunta, Kuka ta soma tana cire hannunsa da fadin"Ni dai kada kayi min komai kaga fa bani da lafiya kai da kanka kace jikina baiyi kwari ba wallahi bazan iya daukar ka ba.""Fuskarsa na tsakanin wuyanta yana shanshanata yace."Babu abinda zanyi kawai zanyi ya babyna yake kwance a mararki jikina na baki nayi kyaykyawar ajiya a cikin ki." Gabanta ne ya fad'i! da jin maganar da yake fad'a! *Ciki!* Allah ya tsareta, abinda ta fada kenan a zuciyarta, tana jinshi ya samu nasarar kwance blet din ya dan zame wandon kafin ya samu damar cusa hannunsa kan mararta ya shiga shafawa a hankali a hankali yana sauke mata numfashi a tsakanin wuyanta, tsigar jikinta ce ta soma tashi, a hankali a hankali ta shiga sauke ajiyar zuciya sai motsi takeyi tana d'an ture hannunsa, dake ta 'kokarin ya cusa cikin pant dinta, Inaa! ai sai da ya zura hannunsa cikin pant din ya sauke wata gawurtacciyar ajiyar zuciya jin hannunsa ya sauka a fatar gabanta dake da wani irin santsi da taushi! sumul babu d'ogon gashi a gurin, dake Wasila bata wasa da gyara gabanta kusan duk sati take aski shiyasa kullum gabanta yake tas babu kazanta, hannunsa ya d'ora dai-dai ramin yana dan shafa fatar gurin a hankali a hankali, a take ya soma jin ajiyar zuciyarta tana sake narkewa ta daina motsin da takeyi, ya cigaba da shafa fatan gurin yana d'an zura yatsansa a cikin a ramin yatsansa ya dangwalo ruwa mai ya'uki da santsi murmushi yayi kad'an! Tabbas yarinyar nada lafiya sosai kuma sha'awarta a kusa take *babu shakka maza na mutukar bukatar macan dake da saurin kamuwa wasan yafi tafiya dai-dai da kuma muhimanci, sa'banin wasu matan da za'a jima ana musu wasa kamar ba'ayi, duk macan dake janyo sha'awarta ta karfi da yaji to gaskiya ta bunciki kanta bata da lafiya kuma ba komai ke damunta ba sanyi ne....Masana kan mata sunce sha'awar 'ya mace tana farawa ne daga farcenta tafin hannunta kunnanta nononta kafin ta zo gabanta, wata macen ana kama hannunta sha'awarta zata tashi, lafiyayyar mace kenan! Amma dai sau tari mata sha'awar su tafi tashi a lokacin da ake ta'ba nonansu da murza nipples din a take duk wata sha'awar mace ke tashi* Jin yanda ruwan jikinta ke fita yana bin hannunsa ya sanya ya gane tana jin dad'i wasan da yake mata, sai kawai yayi dubarar zare dogon wandon jins din jikinta kana ya sa'bule pant din, kafafunta ya gyara mata sosai a nutse ya dukufar da kansa 'kasanta ya shiga yi mata abinda bai ta'ba yi mata irin shi ba. Nishi ta soma sa'ki tana rintse idonta da tand'e bakinta, jin yanda yake lasar gabanta ya sanya cinyoyinta suka soma rawa kar!! kar! kar!! Ta dora hannunsa kan saisayayyar sumar kanshi tana shafawa hade da sake tura masa jikinta sosai sai nishi takeyi tana rintse ido.....Cinyoyinta da suke rawa ya sanya hannunsa ya dan sake ware su, suka bude sosai ya dafe su da kowane hannunsa kana ya kafa kanshi a gurin ya cigaba da tsotsa yana lashe ruwan dake fita a gurin.........Kuka ta dingayi tana shashsheka da fad'in"Wayyo zan mutu zan mutu!! dad'i! wannan abin kamar kar ka bari!! Nagode makaaaaaaa!! maganar ta sha'ke a makogwaronta lokacin da taji wani bala'in da'di na ziyartar ta, a take ta ru'kun'kume! kanshi ta sake bangere masa jiki tana tura masa da saki wani marayan ihu!!! ashe relizing zatayi shine take wannan iface! ifacen!!!! Yana jin d'umin sparm dinta a bakinsa hakan bai sa a ya cire ba har sai da ta gama jikinta yayi lakwas sannan ya cire bakinsa daga gurin....... Dagota yayi ya hau cire mata riga, a d'okance yake shifa idan ba nononta ya sha ba baya jin dai-dai tun dazu suke tsone masa ido, suna bayyana ya sauke wata lafiyayyar ajiyar zuciya! cikin kuzari ya dam'ki daya ya hau murzawa kana ya kifa kanshi kan dayan ya soma sha yana zu'ku nipples din da bakinsa........Sabuwar sha'awa ce ta sake taso mata, sai ta sake sakin jikinta sosai ta rungume kanshi dake tsakanin kirjinta, tana sake tura masa nonon tana lumshe idonta, saisayyar sumarshi ta shiga shafawa tana sauke ajiyar zuciya, gabanta ne ya soma yi mata 'kyakyayi so take kawai taji jijiyarshi na sosa mata, shi kam gurun breast dinta ya lalace! sai sanda yaji saukar hannunta kan jijiyarsa sannan yayi wata iriyar zabura! da sauri ya zare bakinsa daga nonon nata, ya cire rigar jikinsa kana ya kwance tazugen shi wandon ya sabule da gaggawar gaske, sai kallonsa takeyi tana kallon yanda gaban nashi yayi fam! a cikin gajeran wandon shi taji gabanta ya sake wani motsi, bata san sanda ta kai hannunta kai ba, yayi saurin rike hannunta dake kan joystick din, kallonta yayi cikin wani irin rauni da tsananin bukatuwa, Tayi kas da kanta, tana jin yanda joystick din ke motsi a hannunta, hannun ya cusa cikin wandon yana d'age mata gira.....Ta gane abinda yake nufi, a hankali a hankali ta shiga shafa joystick din tana dan murza masa,!! Tana kallonshi ya gagara zama kan bed din sai motsi yake yana cije bakinsa, da sauri taga ya cire hannunta ya zare wandon jikin nashi, tayi saurin dauke kanta ganin joystick din tayi tsalle ta fito kamar zata tsone mata ido.....Kwantar da ita yayi a hankali ya hau kanta ya raba 'kafafunsa, kan cikinta amma bai sakar mata nauyinsa, ya saita joystick din saitin bakinta......Kauda kanta ta dingayi ya dinga juyo da fiskarta yana marairaicewa as'usel yana d'age mata gira kama yanda ya saba yi mata, ta gane abinda yake so, dole tasa ta kama da hannunta tana dan murzawa kadan kadan kafin ta sanya harshe ta soma lasa sama-sama! Ajiyar zuciya ya shiga saukewa yana shafa nipples dinta ........"Waiiiiii! Wani irin dad'i ne ke ratsashi! jin yanda take tsotsar masa ya gigije sosai ya dinga tura mata bakinta yana zurkud'a mata bakinta ya cika yayi fam! kuka tasa tana tuttureshi! kamar shima zaiyi kukan ya dinga girgiza mata kansa kafin ya janyo maganar dake bakinsa da kyar! yace."Ci......Gaba dayiiii! Ahhhaii Ya Allah! Allah yayi miki albarka!!!!! Subahanallah! Kinfi min komai a rayuwata bani da abinda zan biyaki! Komai nacin mai naci sai dai ya hakura a kanki zan iya rasa rainaaaaa."!!! Kalmomin da yake firtawa kenan yana sake tura mata a baki, duk kamaninsa sun sauya abun tausayi!!!! Ita kuwa kallonsa takeyi cike da mamaki! Zai iya rasa ransa a kanta, lallai yana jin dadin abinda take masa. Da sauri ya zare joystick dinshi daga bakinta, ya ware cinyoyinta jikinsa sai karkarwa yake yi ya soma kokarin shigar ta, sakin jikinta tayi sosai tana dan ware masa kafafunta tana taimaka masa har ya samu ya shiga, dukaninsu suka sauke gawurtacciyar ajiyar zuciya kafin ya soma yi a hankali a hankali tana sake tura masa, hade shafa kirjinsa, da kanshi, Runkufawa yayi ya dora fuskarshi kan nononta guda ya soma tsotsar nipple din ta sake jin wani irin dadi na ratsata, gaskiya guy ya iya soyayya yanayi mata yanda take so! Jin yana bugunta a hankali yasa ta sa'kalo wuyansa da hannunta ta soma tura masa tana dan bugunsa a hankali a hankali, Hakan sai ya sake bashi karfin sosai ya soma hakarta da kyau! waw!! hakan yayi mata sosai! dama haka take so taji jijiyarshi na ta'bo inda take so! sai kawai ta shiga taimaka masa ya zamana ita dashi ne suke aikin tanayi yanayi suna sake mannewa da junansu, bakinsu sarkafe da juna suna tsotsar harshen junansu, wani salo tayi masa wanda yasa shi fitar da karamin hawaye......Cinyoyinta ta ware sosai kana ta dage su sama ta had'e su guri guda, shi kuma ya shige jikinta sosai ya manne joystick dinshi ta 'kure jikinta yanaji yana ta'bo wani abu mai mugun dad'i!! bai san sanda 'yan 'kananun hawaye suka soma fita daga idonshi ba, nishi kawai yake saki yana gurnani, ya sanya hannuwansa duka biyun ya tallado d'uwawunta ya dinga matsawa yana makyarkyatar jiki, yarinyar nan naso ta kashe shi kwata-kwata ma ya kasa bugunta ita ke bugunshi, yaji motsa jikinsa ma ya kasa ba wai saboda rashin karfi ba, a'a kawai baya so yayi motsi ne gudun kar dad'in da yake kwasa ya su'bce!!!! Kusan tare suka samu gamsuwa ita dashi suka ru'kum'kume junansu, da kyau, Ita tana ihu!! da kiran wayyo dad'i! shi kuma yana kiran sunan Allah! da shi mata albarka😊 _*Ba wai ina koya iskanci bane A'a ina koya miki yanda zakiyi mu'amular aure da mijinki ne.......Ba nufina na 'bata tarbiya ba nufina na gyara tarbiya na kuma gyara zamantakewar aure, mafi akasarin abinda ke kashe aure kenan rashin iya mu'amula mussaman gurin sex (jima'i) maza da yawa na bukatar jarumar mace mai juriya sannan suna son mace mai salo salo gurin wannan harkar, Wallahi idan kika iya to kin huta da takaicin namiji zai dinga shakkar yi miki wani abun saboda yasan kina bashi dadi yana gamsuwa!! Yawwa kada ki karanta ki nishadantu ki baki aikata ba😊 mutukar kina da aure to ki daure ki dauki darrusan dake book din nan zaki amfanu sosai.........budurwa ko bazawarar dake karanta book din nan pls duk sanda kika karanta wani pegen da yasa hankalin ki ya tashi kikaji sha'awa ta kamaki na roke ki ki yafe min😁 kada ki bi wata hanyar ki biyawa kanki bukata, idan kin ri'ke darrusa na to nasan gaba idan kinyi aure zasuyi miki amafani......Ku d'auki abunda ke da amfani cikin book din nan ku watsar da mara amfani🙋🏻‍♀️*_ Littafinan na kudi ne.....! Kika futar min da book na barki da Allah! Kika karanta book din nan baki biyani hakkina ba kema na barki da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *44* Ajiyar zuciya ta shiga saukewa tana d'an ture kirjinsa da hannuwanta hawayen da take ta kokarin hanasu su zuba suka fara gangarowa kumatunta, shashshekar kukanta ne ya sanya ya dan motsa jikinsa wanda yayi masa bala'in nauyi kasala duk ta dabaibaye shi, bacci ne kawai a idonshi, mikewa yayi zaune yana kallonta, ta rufe idanunta da sauri yayin da hawayen ke sake wanke mata fuskarta, wandonshi ya laluba ya suturta jikinsa, kafin ya mika hannuwansa duka biyun ya tarairayota jikinsa lauyewa takeyi tana komawa kan bed! sai kuka takeyi, sosai ya shiga mamakin kukan da takeyi ya rasa me yasa duk sanda suka gama auratayya sai tayi kuka alhalin duk sanda zasuyi ba yayi mata tilas! bata ta'ba bijire masa ba, daga zarar ya ta'ba ta shikkenan zata bashi hadin kai amma kuma sai daga baya tazo tana kuka......Rashin abinda zaice mata ne yasa kawai ya mike ya nufi toilet domin tsarkake jikinsa, Yasan kukan da takeyi baya rasa nasaba da zamanta a tare dashi babban burinta shine ya saketa taje ta cigaba da harkarta wanda shi ana sa ganin ba dai-dai bane, yarinya karama irin ta tana cakuduwa da maza wasu daga ciki ma sun haifeta sunyi jika da ita....Talauci mugun abu ne, yasan rashi ne ya sanya ta shiga harkar jagaliya domin samun kudi, dan bukatar rayuwa to amma kuma yaji dadi sosai da bata watsar da martabarta ta 'ya mace ba, hakan ya burgeshi sosai shiyasa ma yake 'kara jin kaunarta da tausayinta cikin ransa, baya tunanin zai iya rabuwa da ita har abada. **** Kwana biyu da faruwar al'amarin ta warware sosai, sai dai kuma ta daina sakin jikinta dashi kullum tana takure a daki sai ya fita tukkuna take dan sakewa, To shima dai tunda yaga tana jan jikinta dashi yasa ya d'aga mata 'kafa bai cika shiga huruminta ba sai da wani dalili zai nuna mata ba wai dan yayi aurattaya yake zaune da ita kawai Allah ya sanya masa kaunarta ne cikin ranshi kuma duk wani take taken ta a kanshi ya sani! har yanzu ya lura ba tayi na'am da zama a gidan ba dan dai ta rasa yanda za tayi ne.....Wannan dalilin ya sanya shi had'a CCTV Camera a gidan, idan yana dakinshi yana kallon duk wani motsinta, kana kuma ko bai yini a gida ba yana dawowa gida, ya huta zai duba abunda ya wakana a lokacin da baya nan.....Wani sa'in idan yana kallonta ta cctv din har tausayi take bashi, dan kusan yini takeyi kuka da damuwa, tayi ta zurga zurga tsakanin bedroom dinta da parlo sai ta gaji sannan ne zata zauna a parlor tayi kallo garin kallon bacci ya dauketa, sai taga magariba ta kusa sai ta shige daki ta kulle, hakan sam bai dame shi ba tunda dai yana da spire na key din dakinta idan ya dawo ya gama komai yakan bude ne ya shiga ya dubata koda tayi bacci. Yau ta kama Sunday ne yana gida bai fita, yana tsaye a filin motsa jiki jikinsa sanye da Js ya gama motsa jikinshi Garba na zuba mishi ruwa saman kanshi da yana wanke fuska, kira ya shigo wayarshi dake hannun AbdulHadi, Ya girgixa kanshi da fuskarshi kana ya tsane da karamin towel ya mika hannunsa ya 'kar'bi wayar yana dubawa.....Khalifa ne ya kira, bayan sun gaisa Khalifa yace."Hafsa zata zo dubiya wai tace ace amarya kar tayi fushi." Yace."Sai bayan da taji sauki sannan zata zo kace tasha zamanta kawai." Khalifa yace."Kasan lokacin itama anyi mata rasuwa tana zurga zurga zuwan gidan gaisuwa ne sai jiya akayi sadakar bakwai shine fa tace lallai yau sai tazo ta dubata, dan har tana tsokanarka wai ko an samu 'karuwa ne."!?Khalifa ya 'karashe maganarshi cikin barkwanci......Dan ya mutsa fuska yayi yace."To wa ya sani ni dama karuwar aka samu dana fi kowa jin dad'i wallahi." Khalifa yace.",Himma kawai zaka bayar kullum kayi sau ashirin sai magana ta kare." Dariya ya soma yana girgiza kai yace."Kai bar wannan maganar kawai! Yanzu Kuna kan hanya kenan."? "No! muna gida bamu fito ba tukkuna ammafa Afnan tace za ta zauna tare da amarya dan har mun hada mata kayanta." Da sauri yace."Ka sake kazo min gida da wannan yarinyar sai na cire mata kunne! ai ni mun'bata! kawai kunbi kun shagwaba yarinya da kuka da rigimar tsiya." Khalifa yasa dariya yana fad'in"Halinta ne rigima da shagwaba kasan kuma ko wane yaro da yanayin kuruciyarsa." Tsaki yaja kawai yace."Ni dai na fad'a maka kar kazo min da ita." Khalifa yace."Kai da momynta ni ba ruwana." murmushi yayi yace."Ai zata zo ta same ni." Khalifa yace."Zamu shigo misalin sha biyu zuwa d'aya na rana." Yace."Okey to bari nasan da masu gidan." Sallama sukayi, da juna, Kana ya wuce cikin gidan, Garba yabi bayanshi. Tayi wanka tsaf! ta shirya jikinta cikin dakakkiyar shaddar galila irin ta mata, kalar shaddar ta kasance C green ce anyi mata wani irin stone work rigar duguwa ce ta zauna sosai a jikinta ta fitar mata da tsarin hallitarta, yau ta danyi make up ba kamar da ba ta shafa hoda kana ta zirara kwalli ta goga jan janbaki a le'benta, tayi amfani da wasu had'addun pashion yari da abun wuya da hannu sai walwali takeyi, kasancewar ba ta iya daurin dankwali ba, kawai sai ta nannad'ashi ta daura kanta daurin da tayi ya fito mata da tarin suman kanta ba'kakirin sai she'ki takeyi abin sha'awa, Gefen bed ta nema fuskar nan kamar an aiko mata da mala'ikan daukar rai! kuka ma take so tayi abin duniya ya isheta.. Bai tunkari inda take ba sai da yayi wanka tukkuna ya Shirya jikinsa tsaf! kana ya fara duba Cctv domin ganin a wane irin hali take, Kawai sai ya ganta a kame a bed taci uwar kwalliya kamar ka dauketa ka gudu, sai dai kuma ya hango damuwa a tattare da ita, koda yake dai dama kullum cikin damuwar takeyi, maimakon ya fita kawai sai ya nemi guri ya zaune jikinsa dik yayi sanyi ya zubawa cctv din ido yana kallon duk wani motsinta. Gani yayi ta mi'ke a hankali ta nufi bakin window ta d'age labule tana le'kawa.....Ya zubawa bayanta ido yana kallonta, Ta kai minti goma a tsaye a gurin kafin yaga ta juyo a gaggauce ta fad'a kan bed ruf da ciki ta cire dankwalin kanta tana ya mutsa gashin kanta, tana kuka da dukan katifar dake shimfide a bed din......Ya mike da sauri ya nufi dakin nata, Tanan nan yanda take tana wani irin kuka da dukan bed din sam! bata san ya shigo dakin ba.....Sunkuyawa yayi ya tattarota ta jikinsa, ta kalleshi fuskarta jage jage da hawaye! sai ta fuzge ta koma ta kwanta tana kuka da fad'in "Na shiga uku Allah ka kawo min a gaji."!!! Sai yaji duk wani karsashi nashi ya sare ya zaune kusa da ita jikinsa yayi sanyi, shin wai yarinyar nan wace irin 'kiyayya take masa da take wannan kukan da kiran ta shiga Uku! Hannuwansa yasa ya rike hannunwata dake dukan bed ya burkitota sosai ya jayota jikinsa, matseta yayi ya rufe mata baki da hannunshi guda, kawai ya zuba mata ido yana kallonta, hawaye sai kace ruwa ake akwara mata shatata kawai sukeyi." Kimanin minti goma suna haka kafin yaji tayi sanyi a jikinsa kuma ta rage zubar da hawayen ya tallafo fuskarta tana kallon tashi fuskar, idanunta ta lumshe sam bata so ta kalleshi shi din ya kasance azzalimi ne a gurinta......"Me kike bukata nayi miki wanda zai sanya ki ki daina shiga cikin wannan yanayin na damuwa da tashin hankali? shin me kika nema kika rasa a gidan Ahamdu! menene nake miki wanda kike kiran kin shiga uku, Ki fad'a min dukanin bukatunki amma banda guda daya, ni kuma nayi miki al'kawarin insha Allahu zan yi kokari gurin ganin kin samu abinda kike muradi." Shiru tayi masa tana sauke ajiyar zuciya, ya dan dora hannunsa saman le'bunata jan! janbakin da tasa yayi mata kyau sosai burinshi ya tsotsi lebunan domin sun masifar bashi sha'awa, Gyaran mirya yayi yace."Ke! nake sauraro!? Dan motsa jikinta tayi sai ya saketa ya cigaba da binta da kallo, ta gyara zamanta tana daura dankwalinta kafin tace"Nifa bana bukatar kudi ko wata kadara a gurin ka ni kawai ka rabani da wannan 'kadarran auran ka takure min rayuwa ina rayuwa cikin kunci da damuwa, ka hanani hulda da kowa uwa uba mahaifiyata da 'yar uwata na can guri daya ban san a wane hali suke ciki ba, ka kar'be min wayoyina ballanta na kirasu naji dadi, kullum ina cikin wannan uban gidan a kulle sai kace mayya! ni nagaji!! nagaji!! nagaji! kawai ka sakeni! na huta."!!!! Ta'karashe maganar cikin wani irin kuka mai shashshe'ka. Ya jima kanshi a 'kas! yana jin wani irin d'aci! a ma'kogwaronsa, Yaji bala'in shaushin yanda take kiran auransu da kaddara! illah 'kuruciya kenan! Sai ya dinta tuno had'addun 'yan matan dake rubibinsa a da da yanzu yana watsar dasu, kusan kullum sai ya goge messages sama da ashirin da wani abu duka na matane wasu ya sansu wasu bai sansu ba basu ne a gabanshi ba shiyasa ma sam! baya tsayawa ya duba, ballanta ya basu amsa, haka al'amarin ubangiji yake da ya tashi jarrabarsa sai ya jarrabeshi da auran 'karamar yarinyar da bata wuce ya haifeta ba gashi tana bashi wahala da fad'a masa dukanin maganganun da suka zo bankinta!!! Kokari yayi ya danne abinda ke damunsa ya dago kanshi yana kallonta tana kuka idanunta sunyi fululu! Ya zaro karamin hankici a a cikin aljihunsa, hawayen fuskarta ya shiga goge mata, tana kauda kanta hade da zumbura baki, sai da ya goge mata tas kana yace."Zanyi miki abu biyu da kika bukata amma banda na farkon....Kwanaki idan baki manta ba ni Ahamdu na tabbatar miki da cewar Ni ba zan rabu dake ba kome za'ayi kuwa, maganar na baki takardar saki ki ajeta gefe guda, Maganar mahaifiyarki da 'yar uwarki ni ban rabaki dasu ba, amma yanzu ki kwantar da hankalinki idan Allah ya kaimu gobe Ko Jibi ki shirya zan kaiki ki wuni tare dasu, maganar wayoyinki kuma, tuntuni na bayar dasu amma babu matsala idan mun fita zan siya miki wasu, maganar 'karshe da zan fada miki itace Kada na sake jin kin kira auranan namu da sunan 'kaddara idan ina kusa dake sai na fasa bakin ki! Ni wannan auran alkari nake so zama da samu kyakkyawar zuria da makoma, Saboda haka ki kiyaye kuma ki shiwa kawunki albarka a yanzu kuruciya ke damunki shiyasa kika kasa gane abinda ake so ki fahimta okey! nan gaba kadan nasan idan kinyi hankali zaki gane gaskiya." Ita dai jinsa kawai takeyi tuntuni ta shiga tunanin yanda za'ayi ta tsira a ranar da suka fita dama babban burinta ta futa daga gidan to duk hanyar da zatayi ta kubuta ta sani.....Yace."Yanzu kije ki wanke fuskarki ki sanya kwalli zakiyi bakuwa Hafsa ta kira waya tace xata zo dubaki." Simi simi ta sauka daga bed din ta nufi toilet zuciyarta wasai! Allah Allah take gari ya waye ta samu ta ku'butar da kanta... Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 10:55 pm] +227 98 36 59 34: 'Yr Bngr Sys *45* *'Dan sulaika communication center* Nan yayi parking din motar kafin su fito sai da ya lalabi glass dinshi ya sakaye idanunshi saboda baya son sanya ido na jama'ar gari, fuskarshi dai ba 'boyayya bace tunda gashinan pastes dinshi na yawo sa'ko da luko na cikin gari da kewaye, yasan tilas ya shiga gurin nan jama'a zasu shaida shi, Handbag dinta ta gyara kafin ta sanya hannu ta bude kofar motar tana kokarin fitowa taji saukar hannunshi a bayanta, mayafinta da ya fad'i kan kafad'arta ya gyara mata ma'ana ya d'ora mata saman kanta, Ta dan juyo tana masa murmushi, Dan 'bata fuska yayi yace."Wannan gyalan naki na tuna asirin tufafin dake sanye a jikinki bashi da sirri gare ki kuma kin san da haka kika dauki riga mai faffad'an wuya kikasa bayanki duk a waje." Da sauri ta hau gyagygyarawa tana fad'in"Ai haka akayi yin d'in ki ba laifina bane." Yace."Wannan d'inki na banza ne, kyawun shi ki sanya a gidanki ba ki fita dashi ba kwata kwata ban lura ba sai yanzu dan haka ki zauna cikin mota in shiga in siyo miki wayar." Marairaice fuska tayi"Dan Allah ka bari mu shiga tare na gyara wuyan rigar ai." Tafada tana sake gyarawa.....Girgixa kanshi yayi ya dan zura jikinsa kan jikinta ya kulle motar kana ya bude bangaran da yake zaune ya fita daga motar ba tare da yace mata komai ba.....Kamar ta fashe da kuka, ta bishi da kallo tana jan tsaki! idanunta ya sauka kan wayayonshi dake aje, da sauri ta dauki daya hannu na rawa ta saka numbar As ta soma kira, As ya gane numbar dan haka da sauri ya dauka! Tace"As gamu cikin gate din *'Dan sulaika* ya shiga ciki zai siya min waya da badan ya kulleni cikin motar da tuni na fice sai dai ya dawo ya tarar bana nan." As yace."Kar ki damu Sweetie yanzu *Mada!* yayi min waya cewar kan idanunshi kuka shiga gurin, yanzu abinda za'ayi shine! Mada da Kwage Lauje da sauran 'yan uwansu, zasu tare hanyar da kuka bi idan kin samu kin fito daga motar ki tsallaka titi ki bi hanyar ki ta dama zakiga motana a pake kawai sai na daukeki mu wuce." Murmushi tayi tace"Hakan yayi kyau Ogana naji dad'in hakan insha Allahu muke da nasara a kanshi." murmushi ya saki cike da samun nasara yace."Kada ki damu Swetie komai nayi miki banfadi ba." Tace"Allah ya bar kau.....Jin ana ta'ba motar ya sanya ta zabura! da sauri ta kashe wayar! Ya bude motar ya shigo yana dan kallonta tana rike da wayarshi tayi fi'ki fi'ki! alamun rashin gaskiya, Yace."Kirana akayi ne."? Girgiza kanta tayi tana kokarin goge numbar As d'in.....Tace"Ina duba pictures dinmu ne." Murmushi yayi ya mika mata wata leda mai she'ki da tambarin Dan sulaika jiki yace." kar'ba." Da sauri ta sanya hannu ta karba tana duba tamfatsa tamfatsan wayoyi ne guda biyu masu tsadar gaske ko wacce na cikin kwallinta, kwalayen wayar ta shiga budewa, tana murmushi a hankali tace"Nagode." Baice komai ba ya mi'ka mata wata 'yar 'karamar cover layin mtn ne da glo yace."Gashinan ko wanne nada rigstar akai sai ki sanya ko Allah ya sanya alkairi amma ki sani mutukar naga abinda ba shikkenan ba zan kwace wayoyina kamar yanda na kwace na baya." Shiru tayi mishi kokarinta ta bude wayar tasa layinkan ya karba ya sa mata, kana ya jona mata guda a charge Tace"Idan tayi ka tura min pictures din.".....Dan kallonta yayi yace."Sai mun koma gida Okey." 'Kasa tayi da kanta bata so hakaba amma dole ta hakura, motar ya kunna ya tuka suka fita daga gurin. Can gidanta na Tishama suka nufa, sosai yayi mamakin lamarin, Governor Lawan Rabo mugu ne azzalimi yana kwashe kudin talakawa yana kyauta da bajinta dasu, Yarinya 'kankanuwa ya dauki Uban gida irin wannan ya mallaka mata Tishima Unguwace ta masu kudi kuma ginaginan dake GRA din manya ne da wuya kaga karamin gida a guraran, Ya silala motar tashi cikin gate din gidan ya samu guri yayi parking kana ya juyo yana kallonta ita kuma sai kokarin bude mota take.....Yace."Ki daina wahalar da kanki shin kin manta na kulle kofar."? Shaf ta manta ya kulle zumudi take kawai taga fita. Yace."Juyo ki kalleni." Kallonsa tayi tana dan gyara fuskarta. Babu wasa a fuskarshi da maganarshi Yace."Shin wannan gidan da kike ciki waye ya mallaka miki shi kuma kina da takardar shaidar mallaka."? Shiru ta danyi tana kallonshi, itafa bata son neman fitina ina ruwansa da gidanta tunda ba kwabonshi ne ya siya mata ba." Zai sake magana tayi saurin cewa"Gomnati ce ta mallaka min kuma takardun gidan banki." Hararata yayi yace." Ba cewa nayi ki fada min gomnati ce ta mallaka miki gida ba cewa nayi cikin manyan 'yan siyasan da kike mu'amula dasu waye cikinsu ya siya miki gidan."? Kai tsaye tace"Mai girma governor ne." Ya sake watsa mata harara! yana naxarin maganarta dama dai sai shi d'in gaskiya magana gidan zaifi miliyan hamsin, wannan ai haukane da jahilci yanzu zarginsa ya soma tabbata kan governor lawan rabo kwakwalarshi ta lalace shiyasa yake hauka a siyasan ce ya rasa akin yi da dukiyoyin jama'a yazo yana siyan manya manyan gidaje yana ajiye wai shi me wayo idan ya sauka a mulki su zame masa kadara, aikuwa ya dauki alwashin mutukar Allah ya bashi mulki a hannunsa sai ya had'ashi da hukumar Efcc sun binkiceshi duk wasu kud'ad'e da ya sata sai ya fito dasu, idan bai fito dasu ba sai yasha d'auri! Ya kalleta sai wani 'kif!kif take da ido irin na marasa Yace."Wane banki kike amfani dashi."!? Da sauri ta kalleshi shin wai me yasa yake cin dunduniyar ta ne? me yasa dole sai ya san sirrinta."? Ganin ya zuba mata ido babu walwala a tare dashi yasa tace."Union bank ne." Gyada kanshi yayi yace."Zamuje tare dake domin kar'bar takardar gidanan sannan ina so nayi bunkice cikin asusunki."! bata san sanda tace"Kai!!!!!!!! da mamaki tafad'i maganar. Girarshi guda ya d'aga mata yana sakar mata wani killer smile kafin yace."Ina so in kubtar dakene! dan bana so kisha wuya a gaba, ina me tabbatar miki da cewar ni *Ahmadu* mutukar Allah ya bani wannan jagorancin to duk wani 'barawo! mugu! mazanbaci! macuci! dake fad'in jahar nan sai nasa an kamo min shi na tuhume shi, kan zalincin da yayiwa jama'a cikin wadanda zan d'aure har dake mutukar kikayi min gardama kan abinda na umarce ki, zanyi mulki ne tsakanina da Allah babu sani babu saboda zaki futo da dukanin kud'ad'an da kika 'barnatar ba tare da bin 'kaida ba."! Gabanta ya dinga faduwa tana ta kallonsa lebenta na rawa, wai shin shi wann guy ba zai kyaleta ta sarara bane? ashe tsugune bata kare mata ba koda sun rabu ita dashi zai cigaba da bibiyarta da dukanin abinda takeyi.....Tsoro ne ya kamata lokacin data tuno da cewar har yanzu fa Pose dinta na hannunsa kuma muhiman abubuwanta na ciki ciki kuwa har Atm dinta, amma kuma dole tayi gaggawar zuwa banki domin ta rufe dik wata kafa da zata tona mata asirinta gurin shi......Ganin duk alamun rashin gaskiya ya bayyana a tattare da ita ne yasa yace."Kije ku gaisa ina nan ki fito mu koma gida." Sai abun yazo mata biyu! lallaima wato shi da yana nufin ta shiga su gaisa yanzu ta fito su koma gida, Wallahi ba zai yuwuba! Kuka tasa kariris! 'bakin ciki biyu ya had'e mata, Tace"Ni wallahi bazan koma ba sai dare! kwana nawa rabona da mahaifiyata da 'yar uwata sannan kuma kace na fito yanzu." Ta dinga kuka tana shashsheka! Zuba mata idonsa yayi yana kallo, to meye abin kuka anan kuma? Kawai tace yay hakuri sai dare yazo ya dauketa sai ta hau kuka mtsss! sangarta da shagwaba na damunta......."Ya isa." Yafada cikin sanyin murya....Shiru tayi tana kallonshi, Ya ciro hankicinshi mai kamshi ya shiga goge mata fuska, yace."Shikkenan na bari sai dare okey karfe! bakwai ko shirya ana idar da sallahr isha'i zan shigo mu tafi." Daga kai tayi! Yace."Ki gaishe min da momyn tamu." Kallonsa tayi Wai Uwani yake kira da momynsa, ai ita gani take ma ya girmeta ko kunya wai momyn tamu! Tace"To." Za taji." Bude mata motar yayi yace."Shikkenan."? Daga kai tayi tayi gaggawar ficewa." Kawai sai taga Uwani da Rashida a tsaitsaye idanunsu kan motar ashe tun bayan shigowar motar tasu cikin gidan sukayo waje suka tsaitsaya suna jiran ta fito.....Shima da ya juya motar ya gansu sai dai su ba zasu ganshi ba kasancewar motar mai duhun gilashi ce (tintac) baiyi tsammanin da Uwani a cikinsu ba dan ya dauka ko 'kawayenta ko dai wasu daban! Saboda idan ka kalli Uwani a yanzu ko kusa ko alama ba zakace itace ta haifi su Wasila ba, saboda Allah yayi mata kyawun jiki sosai dan kusan ita Wasilan ta gado, zaka fi tunanin ko yayarsu ce ita..... da gudu taje suka rungume juna suna murna kana suka wuce cikin gidan cike da farin ciki haduwa da junansu. Uwani sai kallon 'yar tata takeyi bayan shigarsu palon suka zazzauna kan kujera Wasila ta gaisheta tana tambayarsu bayan rabuwa, Rashida kuwa kallonta takeyi sosai tana mamakin yanda ta kara cika da kwarjini ta kara haske fatarta tayi luwai, abin sha'awa, ashe ba ita kadai ba har ita Uwanin mamakin sauyawar yar tata take cikin sati biyu kacal wasila ta zama wata hamsha'kiya komai na jikinta abin kallone hutu da jin dadi ya bayyana a tare da ita..........Uwani tace"Bayan rabuwa sai alkairi Wasila munanan kewa da damuwa sun dame mu amma ke kina can hankalinki a kwance kin hada 'kiba abinki ijin dai ba ciki kika bari kika dauka ba dan ni na soma zargin wannan sauyawar da kikayi. Wasila tace"Haba Uwani wannan wace magana kike ? wane irin ciki kuma ai tunda naje gidanan d'an yatsana ban bari ya rike ba. Uwani ta sauke ajiyar zuciya tana fad'in"Alhamdullhi to yanzu me muke ciki." Wasila tace "Mun riga mun gama magana da As insha Allah komai yazo karshe zan cigaba da rayuwa tare daku aurena da wannan mutumin ya kare daga yau." Uwani tace"Naji dadin hakan! Dan na lura bashi da mutunci bai daukeni a matsayin mahaifiya yana kallona a tsaye ya tuka motarshi ya tafi, ko ya tsaya ya gaisheni to idan nice nasha wahalar haihuwarki da rainon ki sai kin rabu dashi har abada mu zuba mu gani." Rashida tace"Wallahi anti Wasila ki kiyaye kiyiwa kanki fad......"Zanci Uwarki! kika sake min wata magana anan gurin!!!! Rashida tayi shiru tana kallonta ta cigaba da surfa mata ashar tana fad'in"Banza mara zuciya da kishin kai! a gabanki fa ya kad'a kansa ya tafi ba tare da ya gaishe da uwarki ba, kudi hauka ne! ni wallahi duk wanda zai ta'ba min martabar Uwata sai inda karfina ya kare, na lura ke din 'Yar jam'iyyarsa ce shi da wancan tsohon me allo to wallahi zaki fice min daga gida dik sanda kika sake min maganar banza." Rashida ta ta'be bakinta ta mike ta shige daki tana 'kunkuni." Tsaki taja ta maida hankalinta kan Uwani Tace"Wannan yarinyar bata da hankali wallahi." Uwani tace"Haka nake fama da ita kullum zagina ne kawai ba tayi." Wasila ta dinga zaginta tana fadin"Aikuwa mutukar tace zata goyi da bayan Ahmdu da mai allo to zata bar mata gidanta in yaso sai ta koma can garkon da zama.......Uwani tace"Wannan hukuncin da kika yanke shine dai-dai. Nan Wasila ta shiga warware mata abubuwan da suka faru da ita gidan Ahamdu da yanda ya dinga sumar da ita yana mata kamshin mutuwa amma kuma bata fada mata cewar mu'amular aure ta shiga tsakaninta dashi, ta fada mata irin bindiddigin da yake mata da furucin sa kan gidan da suke ciki cewar idan ya kar'bi mulki sai ya tuhumeta idan ya kama ma ya daureta sai ya daureta kan kud'adan mutane." Uwani tace"To ai kema baki sukayi ba sata Kikayi ba saboda haka kada ki wani damu duk barazana ce babu abinda zai iya yi miki, Amma kuma nafi so, gobe mu kama hanya mu wuce potsikum sai 'kura ta lafa sai mu dawo mu san abinyi, sai dai kawai yaji kira daga kotu." Tace."To shikkenan yanzu dai dole zanje banki in samu na ciro kudi masu dan kwari a hannuna kafin zuwa goben." Da misalin karfe biyar da rabi na Yamma Wasila da Camas! suka fito daga bakin union duk wasu kud'addanta ta sanya ankwashe mata su daga asusunta an maida accont din Camas kudin sun tasamma miliyan hud'u da d'aruruwa, Cikin rashin dubara da wayo ta barwa Camas! Atm din a hannunta suka wuce gida, Sai gab da magariba suka isa, Uwani tayi musu girki mai dad'i da nama sukayi sallah tukkuna kafin su zauna zaman cin abincin, kira ya shigo Wayarta....Sabida tsabar yanda ta haddace numbarshi yasa ta gane, gabanta ya dan fadi sai dai ta dake! tayi masa sallama Ya amsa yana tambayar ta mutan gida tace"Sunanan kalau." Yace."Ina fatan kin shirya ko dan ganinan kan hanya." A kumbure tace"Abinci zanci." Murmushi ya saki wanda har sai da taji sautinsa a kunnanta, taji tsigar jikinta ta mike, yayi amfani da wata iriyar murya "Ki aje min nawa."! Ta sakejin wani bakon yanayi a jikinta jin muryar da yayi amfani da ita, Sai tayi saurin fad'in" To! ta kashe wayar dan bata so ya samu nasarar kashe mata jikinta....Uwani tace"Shine ko."? daga kai tayi kawai tana jujjuya abincin, Jin muryarshi kawai ya sanya mata kasala da mutuwar jiki!Uwani tace"Kiyi da azama yana zuwa ku tafi ni wallahi so nake inga komai ya faru na gaji da wannan abu." Wasila ta sakejin wani karfi da kuzari gami da dakiyar zuciya yazo mata, ta dan caccakali abincin ta ajiye cokalin kana ta 'kame kan kujera tana jiran zuwanshi. Littafin na kud'i ne....! Kika fitar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [07/08, 10:55 pm] +227 98 36 59 34: *_Afuwa jiya nayi mistake gurin sa numbar a mai makon 46 sai na sake sanya 45 nasan dai babu matsala tinda book din na tafiya kan tsari.......VIP 'Yar Banga! sannu ku da 'kokari! ina 'kaunarku kuna fitar da book ina 'kara samun costomars😅🤝🏻 masu karantawa baku biya ba kuma sannuku da kokari 😎yawwa! guys mu cigaba da gashi!! ku d'auki abu mai amfani na cikin book d'in nan ku watsar da mara amfani......Muje zuwa_* 'Yr Bngr Sys *47* Kimamin mintuna goma sha biyar da kiran wayarshi, ya sake wani kiran yana sanar mata da cewar gashinan a bakin gate dan bai shigo ciki ba ma saboda yanayin akwai hadari sosai dan har an soma iska da walkiya yace maza maza ta fito su tafi. Ta mike da sauri tana gyara jakarta, Uwani tace"Kada fa kiyi da wasa kina samun kufcewa ki nemi mafaka ki 'buya idan ya bar gurin sai ki fito, Tace"Ai As ma yana gurin dan yayi min bayanin yanda zanyi." Camas dake danna wayarta tace"Ni kam inanan sai gobe ma had'u a gest house din As nasan dai can zaki kwana ko." ? Tace"E mana amma da wuri zan fito xamu wuce fataskum sai komai yayi normal kana mu dawo." Tace."To shikkenan." Rashida dai na zaune bata sanya musu baki ba cikin maganarsu duk haushi suke bata har Uwanin sam basu san inda yake musu ciwo ba, shiyasa tayi al'kawarin daina sanya musu baki a maganarsu idan ta kwa'be musu ita 'yar kalloce tinda ta fad'a musu gaskiya sun'ki ji. Har bakin gate Camas da Uwani suka rakota, sai da ta fita tukkuna suka koma ciki.....Tana fita aka soma yayyafi da sauri ya bude mata motar ta shiga tana gyara mayafinta, ya kunna motar suka bar gurin, Sai da suka hau titi sosai ya d'anyi gyaran murya yana kallonta yace." Ya mutanan gidan ina fatan kin mi'kamin gaisuwa gurin momy kafin naje da kaina." babu yabo babu fallasa tace"Eh tace tana amsawa." Motar tayi shiru bayan maganarta ruwa ya soma yin 'karfi gabanta na cigaba da fad'uwa! Saboda yanayin goslow din dake tsakanin tal'udu da goran dutse ya sanya yayi yanke hanya ya shiga ta wajan ma'kabarta zai bi ta 'yan rake yana ganin hakan zaifi masa saukin shiga unguwarsu tasu ta tudun yola, duk wannan yanke yanken da Ahamdu yake yi da mota, Motar su *Mada!* na biye dashi amma saboda tsananin taku mutum ba zai gane hakan ba, Sosai yake gudu sam baya son ruwa yayi karfi wanda zai tilas tashi yatsawa a kan hanya shiyasa ya kara karfin motar, Wanda ita kuma sai zazzare ido takeyi kamar kace kyat! ta ruga a guje tunani takeyi ko tana ina su *Mada!* zasu fito........Kasancewar ruwan ya soma 'karfi ya sanya masu siye da siyarwar dake kan titin kansakali mahad'ar 'yan rake ya sanya suka fara kwashe kayaiyakinsu kowa na neman tsira titin tayi shiru hanya tayi tsit! sai saukar ruwa sai kuma ababen hawan dake ta sharara gudu kan kwalta kowa na so ya isa gida. Yana fitowa daga tsukin titin kansakali ya hau titi sosai, yana kara karfin motar! Kawai motar su *Mada!* ta daki tashi motar wanda ya sanya hannunsa ya goce daga kan sitiyarin motar ta gangara wani layi! Dake titin dama motoci basu fiye binshi ba ya sanya jama'a basu ankara ba, bayan haka kuma ga ruwan da akeyi babu kowa a gurin masu wuce wa a baben hawansu basu fahimci komai ba dan dik wanda yaga motar Ahamdu cikin layin zai dauka a fake take dan bata nuna komai ba da zai dauki hankalin jama'a. Ya jima yana kiran sunan Allah kafin yayi gaggawar bud'e motar ya fito ruwa na dukanshi, Can ya hango motar su *Mada!* ta silalo gurin.......Ya tsaya yana kallon motar har tayi parking kafin ya ankara yaga sun fito su uku ko wanne fuskarshi rufe da ba'kin abu, dake namijin duniya ne bai wani razana ba sosai! suka durfafo inda yake! Mada ya fito da wata bindiga yana saita shi da fad'in"Kud'i ko kuma mu dauki ranka."! Yace."Ai babu mai daukar ran mutum sai wanda ya halliceshi! *Lauje* ya kai wa bakinshi duka da sauri ya rike hannunsa yana girgiza masa kai! Yace."Kuce kawai na baku kudi sune bukatar ku amma kada ka kuskura ka ta'ba min lafiyata." Zuruf! ta bud'e motar ta fito, sai ta fashe da kuka tana wata makyarkyata sosai tsoro takeji gani takeyi anya su *Mada!* ne kuwa, ganin sun saita shi da bindiga yasa gabanta faduwa ta shiga kuka tana basu hakuri." Da sauri *Lauje* yaje ya bud'e motar ya hau dube dube a ciki a take ya bude wani gurin cikin motar ya fito da daurarrun kudi a hannushi, ya dinga jefewa ! 'Kwage! yana cafewa! Wasila ta isa inda yake a hankali tace"Lauje." Yace.'Yar gaske maxa ki fece daga nan.'' Data tabbatar da sune sai kawai ta silala ta bayan motar zata gudu, tana waigowa ta hangi Ahamdu da Mada suna kokawa! saboda tsabar tsaurin ido irin na *Mada* so yake ya lalube jikin Ahmadu, ya dauke masa wayoyinsa shi kuma ya hanashi, Sai kawai taga *Mada!* ya daddage! ya sakar mishi duka a 'kirji! Ihu! tayi da 'karfin gaske! wanda ya sanya shi saurin juyowa, yana goge ruwan fuskarshi, dan har lokacin ruwa ake me 'karfi! Can ya hangota tana 'kwarma! ihu zata tsallaka titi! Yayi nufin binta, *Mada!* ya tad'e kafafunsa, santsin gurin ya sanya ya zube 'Kas! cikin zafin nama ya rike kafafun shi shima ya makar dashi a gurin! a gaggauce! ya mike! da azama! ya murd'e? hannunsa ya 'kwace! bindigar dake hannunsa! ya saita wuyanshi...... *Mada!* ya hau 'kif'kifta ido! Yana kare fuskarsa da hannunsa!....A kausashe yace."Waye! ya aiko ku."? *Mada!* yayi shiru yana yi wa *'Kwage!* Inkiya da idanunshi, *Kwage!* ya lalla'bo ta bayan Ahamdu ya kir'ba mata wani irin duka! Ahamdu yayi taga taga zai fad'i! da sauri *Mada* ya tureshi ya mike a guje! sukayi inda motar su take suka shiga, Ahamdu ya saita bindigar hannunsa zai harbesu wayam! babu bullet sai da ya duba ta sosai sannan ya gane ashe ta gaibu ce! Can ya d'ago kanshi ya hangi motarsu ta fice daga layin...... Wata irin walkiya akayi mai hasken gaske! Walkiyar da ta zame masa madubi gurun hango Wasila tana kurd'awa wata hanya tanayi tana waiwayen bayanta, Da sauri ya nufi motarshi ya shige ya kunna da gudu yabi hanyar da bi, Ganin hasken mota yasa ta juya da saurin tana waigen bayanta, bata tantance cewar shine ko bashi bane, ta juyo da sauri tana cigaba da sauri aikuwa facal? ta fad'a cikin wata kwatuwar kwata mai zurfi! Kuka tasa tana kiran sunan Allah! ganin ruwa ya shanyeta har yuwanta shikkenan mutuwa tazo, sai kawai ta dinga kwarma ihu! tana fad'in"Azo acece ni! Azo! aceceni!" Jin wannan sautin ya sanya As dake cikin motarshi a can gaba ya fito a gaggauce! ya durfafi inda yake jiyo sautin muryartata, To shima Ahmadu hankalinshi ne yayi masifar tashi, dan gani yayi ma kamar motar bata guda ya bude ya fito ya soma gudu yana so ya cimma inda yake jin ihunta! Had'uwa sukayi da As! d'in, sai suka shiga kallon kallon, Ga Wasila tsakiyar kwalbati ruwa na neman tafiya da ita dan ma ta rike wani karfe ne da tuni ruwan yayi gaba da ita! Ahmadu na gane Waye baiyi wata-wata ba ya kir'ba! masa wani irin naushi a 'kirji! As ya ri'ke kirjinsa yana tari! Ahamdu ya sake kir'ba mishi wani naushin da yafi na farko! As ya zube a gurin yana jawo numfashi da 'kya!!! Facal! facal! d'in da yaji a cikin ruwan ne ya sanya ya dawo da hankanlinsa nan ya hangota tana d'ad'dago kanta sama! da hannunta guda! Da sauri ya afka cikin ruwan, dan har sai da yayi motsi saboda yawan ruwan da ya taru ! Daukota yayi a kafad'a ya daddafo ya fito yana kwantar da ita, ta sume a gurin...... A hankali a tashe ya ciro wayarshi da ruwa ya jika jagab! baiyi tunanin idan yay kira da wayar zatayi ba saboda yanda take digar ruwa, amma abin mamaki yana fara kiran yaga tana shiga ajiyar zuciya ya sauke, Stion ya kira yay musu bayanin komai da kuma kwatancan garun! Ya mai da wayar jikinshi bayan ya gama, inda take yazo ya tsuguna ya fara danna 'kirjinta a hankali a hankali ruwa ya dinfa fita ta bakinta da hancinta kafin wani ruwa yayi fit ya fito ta hancinta ta bude idonta a razane! ta mike tana zazzare! idonta! Ganinshi tsugune gabanta ya sanya ta fashe da kuka jikinta ya soma karkarwa shikkenan kashinta ya bushe! Bai ce mata komai ba, Ya mike tsaye tare da goya hannuwansa a bayansa ya nufi inda As ke sheme!!! Yana tsaye a kanshi yana nazarin shi motar Police ta shigo gurin.....suka fito su kusan biyar suna haske gurin da torchlight din hannuwansu, Ganin Sananniyar fuskar Ahamdu ya sanya su mamaki! sosai gaisawa sukayi yace."Yanzu babu lokacin bayani ku daukeshi kawai ku wuce dashi stion da safe zan shigo." Suna haska fuskar As suka razana! Ganin sanannaniyar fuskarsa Ahamdu yace."Kuyi abinda nace kawai."Sanin halin Ahamdun da rashin wasa ya sanya suka bi umarinsa, bayan haka kuma dama sun gaji da mulkin *Lawan Rabo* baya basu albashi kan kari babu promotion da sauransu wasu daga cikin ma'aikatansu ma duk ya koresu daga aiki acewarsa wai basa aiki shiyasa ya sallamesu, dama suna ciki dashi da masu bashi shawara, irin su As din dan haka suka ga su baza su 'ki bin Umarnin Ahmadun ba, suka fito da wani gadon karfe cikin motarsu suka dora As a kai suka haura dashi motar, kana sukayi wa Ahamdun sallama suka bar gurin. Ya juyo inda take takure kanta tsakanin kafafunta tsananin razana da fargaba ya sanya jikinta maxari sai kace wacce aka kad'awa gangi tsoro nadama gami da dana sani duk sun baibayeta yanzu da badan Ahmadu ba da tuni ruwa ya cinyeta! hakika fadawarta cikin ramin kwatar yasa ta sare ta sadakar da cewa mutuwa zatayi sai gashi wanda take 'kokarin gujewa shine ya ceceta, wata irin nadama takeyi sai kuka takeyi ma'kogwaronta ya bushe 'kamas!!! Taga inuwarshi a kanta, Idanunta jage jage da hawaye ta d'ago tana kallonsa, ganin fuskarsa a daure ya sake fad'ar mata da gaba, kawai sai taji wani masifaffan fitsari ya matsota! Cikin ba'kin ciki da takaici ya buga mata tsawa "Tashi mu tafi."!!! Gurin sai da ya amsa da sautin muryarahi, Ta mike jikinta sai kyarma! yake tana d'igar da ruwa duk tabi ta 'kankame! hannuwanta a jikinta, ya nuna mata hanya da hannunsa, Tana cire 'kafa da niyar tafiya fitsarin dake cinta ya kufce! sakin sa tayi kawai ta cigaba da tafiya tana kyarma! Bayanta yabi hannuwansa goye a bayansa yana jajanta al'amarin. Gaban mota ta bude za ta shiga yace." Rufe min mota." Da sauri ta rufe! ta bude murfin baya ta shiga ta zauna tana kuka da nadamar rayuwarta.... ya shiga a gaggauce ya Kunna motar suka bar gurin. Gwajab! gwajab! din da motar takeyi ne yasa As dawowa hayyacinsa ya mike zaune a zabure! yana fad'in' Karya kakeyi Ahmadu! Ba zan jima ina shuka ba ranar girbi tazo kace ban isa inyi ba, Wallahi sai ka saki yarinyar nan ko ni ko kai, a fad'in garin nan.""!! Daya daga cikin police din yace."Yallabai yi a hankali shin wai meke faruwa ne tsakaninka da Ahmadu Musa." As yayi saurin dawowa hayyacinsa yana bin motar da kallo sai ya ganshi tare da 'yan sanda, gabanshi ya fad'i! Yace."Kai ina zaku kaini."!? "Yallabai Ahmadu ne ya kiramu a waya ya shaida mana muzo gurin nan domin mu dauke ka mu kai ka stion mu rufe." Ya buga musu tsawa da fad'in"Ina ce dai bai fad'a muku abunda ke tsakaninmu ba."? Dan sandan yace."bai fada mana komai ba, amma kuma ga yanayin maganganun da kakeyi munso mu fahimci wani abun." As yaji gabanshi ya yanke ya fad'i! A duniya ya tsani mutuncinsa ya zube gurin mutanan gari da kuma iyalinshi, yanzu idan Ahamdu ya sanar da Media cewar yayi nufin daukar matarshi me duniya da mutanan cikinta zasu daukeshi, sai kawai gumi ya soma yanko masa daga ko wace kusurwa ta jikinshi, Yace."Maza ku saukeni a gida Ahmadu bai da hurumin daureni domin bai da wani mu'kami a siyance idan dauri ne ma nine zanyi masa." Babban cikinsu yace."Sam! ba haka dokar aiki take ba ku da kanku kuke fad'in cewar ba mayin aiki tsakani da Allah bama bin doka dan haka babu wani karin albashi da za'ayi mana, saboda haka daga yau zamu fara aiki tsakani da Allah a kanka." As ya shiga rarraba ido yana kallonsu ma'kogwaronshi ya bushe kamas! yace."Kunfi kowa sanin mukami na a siyasa me zai sanya kuyi min haka ku fad'i ko nawa kuke so zan baku ku kaini gidana kuma bana so kowa yaji wannan maganar." Mai maganar cikinsu yace."Yallabai alamu sun nuna mana kaine mara gaskiya tsakanin ka da Ahmadu, saboda haka dole ne muje stion dake domin yin aikinmu kamar dai yanda na fad'a maka da farko cewar kuna fad'in bama aiki kan 'ka'ida shine zamu fara ta kanka." As yayi kwata'kes! yana zazzare ido cikin motar............. *_Tofaaa! Karshen tika tiki tik! 'Karya fure take bata 'yaya! Tsalle d'aya za kayi ka fad'a rijiya sai kayi dubu baka fito ba._* Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book! keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Littafin na kudi ne.......! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah! WhatsApp numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *48* Shashshekar kukunta ne ya dameshi yana draving yana jan tsaki ya rasa ma wane irin mataki zai dauka kanta, domin tayi mutukar bashi mamaki! sam! bai ta'ba tsammanin za'a iya had'a baki da ita a cutar dashi ba, ashe dama ita da akwai abinda take shiryawa shiyasa tun jiya yaga ta saki jikinta tana ta zumud'i, to wai idan ta bi As din ina zai kaita? shi da kansa yake tambayar kanshi da kanshi, tabbas yarinyar ba 'karamar mara hankali bace wato ita tafi so tayi ta yawo a gari tana shiga cikin maza tana cakuduwa dasu! da auransa a kanta zata bi As suje inaaaa? Sitiyarin motar ya daka da karfi har sai da ya kufce daga hannunshi motar tayi wani irin abu!! Jikinta na bala'in rawa tace"Kay....hakuri dan Allah."! Ko kallonta bai ba ya kunna motar a guje yake janta yanayi kamar ma yace ta fice masa daga mota saboda tsabar haushi da takaici.......Lokacin da suka isa gida ruwa ya dauke ma'aikatan sa na katuwar rumfar da suka saba zama suna jiran dawowarshi. kafin ma yay parking din motar sun isa inda yake suna masa barka da zuwa, ba tare da ya bude motar ba ya amsa musu, kana kowa ya koma inda yake. Ya bude motar tashi ya fito itama ta bude ta fito jikinta na wani irin d'ari da karkarwa....Bin bayansa take simi simi har yanzu bata daina zubda hawaye ba. Bai wani saurareta ba ya shige bedroom dinshi domin yay wanka ya sauya kayan jikinshi zazzabi zazzabi ma yake ji a jikinsa kasancewar dama shi tunfil-azal ba mutum ne me son ruwan sama ya dake shi ba......Ta jima tsaye a parlon tana kuka kafin ta lalla'ba ta shige nata bedroom ta hau cire kayan jikinta ta daura towel ta nufi bandakin, to kafin tayi wankan ma sai da taci kuka ta koshi kana ta fito kanta nayi mata wani irin bala'in ciwo mara misali, tana kuka taje ta kudundune jikinta da bargo, tana rufe idonta......Shigowarsa dakin ya sanya ta mike zaune da sauri tana matsawa lokon gado dan tana ganin kamar zai daketa ne ko yayi mata wata illar mugun tsoronsa takeji tunda ta lura idan ranshi ya 'baci bai iya hukunci ba. Kayan sanyi ya sanya a jikinsa masu kauri kanshi sanye da hular sanyi ya rufe har kunnanshi mugun sanyi yake ji mai shiga jiki ga zazza'bi na damunshi haka kawai ta janyo masa lalura. Kafin yace komai ta soma kuka tana d'ad'daga hannuwanta sama da fad'in"Don Allah kayi hakuri wallahi ni babu ruwana, dama shin......Kasa karasa maganar tayi ta hau inda inda tana rawar baki." Ya zuba mata idanunsa yana kallonta fuskarshi babu walwala ko ta kwabo, yace."Ki nitsu ki daina wannam firgice firgicen da kikeyi." Hannunta tasa ta rufe bakinta hawaye na ambaliya a fuskarta, ya zauna gefan gadon yana kallonta har sanda ta dan samu nutsuwa, Kawai taji sautin muryarshi yana fad'in"Me kuka shirya akaina ke da mutanan naki? Kuna so ku kasheni ko.'!? Tayi saurin kallonshi tana girgixa kanta......Yace."Hakane mana." " Wallahi ba haka bane." Yace."To naji, Ina zaki bi As kike gudu."? Sai hawaye ya soma shatata! yace."Ba kuka nace kiyi min ba." Tayi shiru tana kallonshi, yace."Kiyi min bayani dallah dallah kan a'lamarin.'' Tayi shiru tana me sunkuyar da kanta kasa! Tsawa ya buga mata yace."Zazzabi nakeji a jikina yi min bayani abinda nace ba kuka nace ki min ba." bakinta na rawa ta shiga wassafa masa yanda suka tsara ita da As da yanda in ta kufce daga hannunsa zasu gudu fataskum sannan kuma ta kaishi kotu shi da mai allo kana idan al'kali ya raba auransu ta dawo ta cigaba da harkokinta, Ya dinga kallonta yana girgiza kanshi, Mahaifiyarta bata da hankali ko d'an! abinda yake ayyanawa kenan cikin ranshi, to idan ba rashin hankali ba me zai sanya ki zauna kina tsarawa 'yarki shirme da abinda zai cuceta har ta dinga kokarin kashe mata aure, amma babu komai shi ya san abinda zaiyi musu. "Na yarda babu abinda ke damunki sai jahilci da da'kikanci! Allah yayi miki suttura kina nema ki butulce masa, me nayi miki? me kuma me allo yayi miki da har kike nufin tozarta mu ki kaimu gaban al'kali! kan anyi miki alkairi ke zaki mayar da sharri! ko da yake tarbiyace baki samu ba tun farko ku kusa ko alama ni bana ganin laifin Kawunki saboda yayi iya bakin kokarinshi a kanku, k eda 'yar uwarki da ita kanta 'Yar uwar taki! amma dake keda da maman taki duk taron mahaukatane kuna adawa dashi Okey ni Ahamdu mutukar na cika d'an halak! sai nayi muku abinda kuke bukata, kafin ki tozartani ni zan tozartaki! Ni Ahamdu ba'ayi min na bari! idan kinga na bar abu nine nayi niyyar bari, Yau zaki gane asalin waye ni."!!!! Kuka take sosai tana fad'in"Don Allah dan annabi kayi hakuri wallahi kuskure nayi kuma bazan 'kara ba nayi nadama ni na hakura ma da komai zan zauna da kai nasan kai mai kaunata ne tunda har ka ceto ni lokacin dana fad'a ruwa nagane rayuwa ba'a bakin komai take ba." Yace."Tubanki na banxa ne Siyasar banga da Jagaliya kike so kiyi to zan baki lasisi a hannunki." Yana gama maganarshi yasa kai ya fice daga dakin." Ta kwanta tare da takure jikinta tana ta kuka da makyayatar jiki. A daran ya kira dr Nasir yazo ya danyi mishi treatment ya bashi maganguna dan zazzabi da mura mai karfi ce ta kamashi, abinci yaci yasha magani kana ya shige bedroom dinshi ya rufe yayi kwanciyarshi akwai bacci me nauyi ya daukeshi. Yanda taga dare haka taga rana, lokaci zuwa lokaci gabanta na wata irin faduwa, idanununta sun kada sunyi jawur tsabar kuka da damuwa da kuma tsananin zazzabi da ciwon kan dake damunta...........Asubah nayi taje tayo alwala ta fito ta duba doguwar riga mai hula mai dan nauyi tasa a jikinta kana ta tayar da sallah......Kwanciya tayi kan dadduma tana lumshe ido bacci mai dad'i yana fuzgarta, ya turo kofar dakin ya shigo, a zabure! ta mi'ke zaune tana gyara zaman hijab dinta da ya karkace.......Yana sanye da jallabiya fara tas da ita har yanzu kanshi na sunkufe da hular sanyi har kunnanshi kafafunshi ma safuna ne farare ya iske inda take zaune kanta a kasa tana watsa da 'yan yatsunta! Hannunsa guda dake cikin aljuhunsa ya zaro ya fito da wata takarda fara a nannad'e ya mi'ka mata......Dake kanta a 'kas! yake bata ankara ba sai da yace."'Kar'ba." tayi saurin d'agowa tana kallon hannunshi, gabanta yayi wani irin bugu! Innallihi wa'ina ilahi raji'un! Sai le'bubanta suka soma rawa suna had'uwa!!! "M....me zan kar'ba." Tafada tana kallonsa da gwala gwala idanunta da suka gaji da kuka." Kai tsaye yace."Abinda kike bukata ne nayi miki."! Sai hawaye ya wanke mata fuska! ta sa hannunta dake karkarwa ta kar'bi takardar! Shi kuma ya kama hanya ya fice daga d'akin......Kasa bude takadar tayi ta ajiyeta a gabanta ta 'kura mata ido le'banta sai rawa yake had'e da jikinta cikin ranta take fad'in "Ubangiji Allah yasa mutumin nan ba sakina yayi ba a lokacin da nayi nadama nake sha'awar zama dashi." Ihu! ta kurma bayan ta warware takardar ta karanta abinda ke ciki. _Ni Ahmadu Musa Na saki matata Wasila saki d'aya idan ta samu miji tayi aure_ A sukwane ta bud'e 'kofar dakin ta fice palor hannunta rike da takardar tana gurshen kuka ta nufi dakin shi, lokacin yana 'balle magani zai sha kawai ta afko dakin......Kafafunshi taje ta rirrike tana kuka da shashsheka! "Dan girman Allah kada kayi mun haka! Wallahi nayi nadama bazan sake ba, zan zauna da kai bisa amana, ka mai dani dakina kar muyi haka da kai."!!! Baice mata uffan ba ya afa maganin abakinshi ya kora da ruwa ya aje goran ruwan kan bedside kana ya kalleta duk tayi wujiga wujiga! har wata 'yar rama tayi tsakanin jiya da yau d'in ga kuma alamun tashin hankali da fargaba da nadama nan a tare da ita, Yace." Lokaci ya 'kure miki ai bakiji abinda nace bane ? Idan kin samu miji kiyi aure Ahmadu ya barki har abadah."! Sai ta sake shi tana masa wani irin kallo! kamar zauntacciya tace"Wallahi babu inda zanje ina cikin gidana ni bana son saki ai kaine ka kar'be min budurcina kuma sannan zaka mayar dani 'karamar bazawara da 'kananun shekaruna, ni babu inda xanje dan ni ba bazawara bace kuma ni bani da wani miji idan ba kai ba.........Yayi bala'in shan kunu yana sake tamke fuska yace."Tun wuri ki kwashe duk wani abu da kika san naki ne a gidanan ki fice min a gida minti talatin na baki wallahi idan ba haka zan sanya su Garba suyi miki rashin mutunci sai kin fita da kwayayyar fata kamar yanda 'kawarki ta fita dashi." Bubbuga 'kafafunta ta shiga a 'kasan dakin ta na yayyaga takardar sakin tana kuka wiwi da majina da hawaye sun had'e a fuskarta tana fad'in"Ni ban saku ba, babu inda zanje wallahi ba zaka mayar dani bazawara ba." Sosai ya shiga mamakinta da maganar ta wai ba zai mayar da ita bazawara ba ashe tana kishin kanta haka? amma kuma take neman saki da kanta har da ikirarin shiga kuto gashi kuma an saketa anyi mata yanda take so tana nadama! Tabbas bakin al'kalami ya riga ya bushe yanda yayi rantsuwa a kan ya gama zama da ita har abada ya gama taje ta 'karata da ba'kin halinta. Da ta dameshi da kuka ya mike a zafafe! yana zare mata ido! bata tsorata ba sai ma sake gyara zamanta da tayi a dakin tana takurewa, yaje ya hau janta domin ta fice masa daga dakin kukanta na damun 'kwalkwarshi! Nan fa d'aya! labule ta kama ta rik'e tsam! tana turjewa wai ba zata fita ba......Ya kwad'a mata lafiyayyan marin da yasa taga gilmawar taurari a idanunta! Shouting dinsa taji a kunnenta yana fad'in" Kin fi son muyi irin wannan rabuwar ko okey......Janta ya so mayi ta rike 'kafar gado tana kuka da fad'in "Nayi nadama ba zan sake ba ni babu inda zani nan ne gidan mijina."! Sosai ta rike kafar gadon ta'ki saki! Kawai ya tattaro ta gabadaya ya dauketa bai dire ta ko ina ba sai palo, yana kokarin juyawa ta rike masa kafafu! Yau yaga jaraba da naci da 'kulafuci!! Fuzge kafarshi yayi yana jan tsaki! ya koma dakinshi, Ranshi idan yayi dubu ya 'baci.....Ita kuwa bayan shigewar sa dakin kwanciya tayi kasan carpet tana wani irin kuka da kiran mutuwa tazo ta dauketa ta huta da wannan kad'arar data afka mata. Littafin na kudi ne....! Kika fitar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* alliya: 'Yr Bngr Sys *49* Kofar dakin nashi ta tsirawa ido tana daga inda take kwance hawaye sai zurara yake daga idanunta, shikkenan ta cuci kanta! shikkenan ta tashi daga budurwa ta koma bazawara! abinda ke tayi mata yawo kenan a kwakwalwarta! Wani sashe na zuciyarta yake kara tunasar da ita abinda ta manta, itace fa take so a saketa kuma yanzu murna ya kamata tayi ba kuka ba, da ba tayi wannan tunanin ba sai yanzu? Hawaye ya sake kece mata, sam ba tayi wannan tunanin ba sai yanzu da Allah ya jarrabeta da son auran take tunanin zawarci! mikewa tayi xaune tana goge hawayen fuskarta palon take bi da kallo tana 'kissima abubuwa da yawa, Dole ne ta nemawa kanta mafita, dan daga yanzu ta daina daukar hud'ubar mahaifiyarta a ganinta duk itace ta ingizata fadawa wannan halin, zawarci da kuruciyarta, yanzu ta daina ganin laifin Rashida gashinan Allah ya nuna mata gaskiya tun kafin ayi nisa, Hotonshi dake manne a wata kusurwa ta dakin ta zubawa ido! hawaye masu zafi suka sake yanke mata, wani irin bala'in sonsa taji sabo na ratsa zuciyarta, ta mike ta isa inda hoton yake tana kallonsa, yana zaune kan wata had'addiyar kujera sanye da farar shadda! sai murmushi yake yi! tsayin ta ba zai kai inda hoton yake ba tana so ta dauko ta kasa, sai ta kura mishi ido tana fad'in "Tunda ka sakeni dole na tafi na bar maka gidanka! nayi nadamar abinda nayi maka! ba'a hada baki dani ba akan a cutar da kai kamar yanda kake zargina! kawai nima shaidan ne ya zugani amma yanzu nagane abunda kake so ka gane! zan tafi in bar maka gidan ka tunda ka saken.......! sai ta kasa karasawa ta zube a gurin tana dukan kujera hade da wani irin kuka mai cin rai!!! kimanin minti goma tana cikin wannan halin kafin ta mike zumbur! ta nufi dakinta, Wani tunani tayi a yanzu dai babu mai sasanta al'amarin nan sai mai allo shine zai shiga cikin maganar yasa Ahamadu ya mai da ita. Ta dauki karamar jaka ta zuba kayanta, wayoyin da ya siya mata tun jiya ta mantasu a motarshi, hakan bai dame ta ba a yanzu, hijab din da take sallah ta zura ta fito tana goge hawaye, kofar dakin shi ta kalla har yanzu tananan a kulle, taji zuciyarta ta sake karyawa, tabbas ya nuna mata shi din dan halak ne! sam bata ta'ba tsammanin zai saketa kaitsaye ba sai gashi tun bata dangana shi da al'kali ba ya yanka mata ticket, ta bude kofar palon ta fita zuciyarta na tsananin harbawa, shikkenan duk wannan daula da jin dad'in sun zama labari Shikkenan duk uwar soyayyar da yake mata lokacin da suke marking love ta yanke, ta sanya hannu ta share hawaye tana tuno irin rayuwar jin dadin da suka dingayi yanda suke soyayya suna jiyar da kansu dadi! kuka tasa tana girgiza kanta haka nufi bakin gate ta kasa tsaida hawayen fuskarta yanzu idan Ahmdu bai mai da ita ba wace irin rayuwa za tayi........Dukaninsu sunyi mamakin ganinta da jakar kaya tana kuka, Garba ya hana abude mata kofa ta fita yace dole sai ya sanar da mai gida....Ta tsaya gefe tana goge fuska tana addua Allah yasa idan yazo ya tausaya mata yace ta koma gidan......Ya kirahi a waya lokacin baccinsa baiyi nisa ba sosai ya daga wayar Garba yay masa bayanin abinda ke faruwa. Kai tsaye yace."Ku bude mata kofa kuma kabi bayanta kaga ina ta nufa." Garba yace."Shikkenan yallabai." Kashe wayar yay yace su bude mata kofar, Jikinta a sanyaye taja jakarta ta fita daga gidan......Garba sai da ya dai-daici ta fita babban titi kana yabi bayanta, aikuwa yaga tana tare abin hawa! shima ya tare ya shiga yace da direban ya bi bayan babur din dake gabanshi duk inda yayi, haka kuwa akaiyi, Wasila ta sauka a bakin titi ta biya me babur kudinshi ta ganganra domun shiga Estete din da gidanta ke ciki, Garba na biye da bayanta bata sani ba. Sai bayan yaga shigarta gidan ne ya kira wayar Ahamdu ya sanar mishi da cewar ga inda taje Yace."shikkenan kyaleta kawai ka dawo gida." Garba ya mai da wayarshi aljihu ya bar bakin gate din. [8/8, 12:03 PM] .: Uwani Camas! Rashida na zaune suna karyawa Wasila ta tura kofa ta shiga, dukaninsu suka maida hankalinsu kofar shigowa, kawai suka ga Wasila ta shigo fuskarta a jeme idanunta yayi wani irin ja! sun kara girma ga fuskarta ta nuna al amun tashin hankali da nadama gami da dana sani! Da sauri Uwani ta mike tsaye tana fad'in" Yaya na ganki haka? Cikin damuwa yanzu dama muke maganarki ina cewa kiyi maza maza kizo mu taf.......Kafin ta 'karasa maganar dake bakinta taga Wasilan ta zube tsakiyar dakin tana kuka hade da dafe kanta tare da fad'in"Na shiga uku na lalace."!!! Uwani gabanta ya yanke ya fad'i sai ta dur'kushe gaban 'yar tata tana karkarwar jiki ta rirri'kota jikinta tana tambayar ta abinda ya faru!!! Wasila ta shiga tutture ta tana shashshekar kuka da fad'in "Kece kika jawo min wannan masifar duk wani wahala da zan shiga a rayuwa ta kece!!!!! Uwani taji wani gumi ya tsinke mata! Wai shine meke faruwa ne? Rashida da Camas! suka iso inda take durkushe tana kuka! Kawai sai ta kama Rashida ta rungume 'kam!'kam! tana wani irin kuka.! Rashida taji zuciyarta ta karye itama sai ta soma kuka tana tambayar ta abinda ya faru!! Cikin hard'addiyar magana tace"Rashida ya sakeni! Ahmadu ya sakeni!! ya sakeni Rashida na gane abinda kike ta so nagane yanzu Uwani ta cuceni na cuci kaina innalilihi wa'ina ilaihi raji'un"! Da jin wannan maganar dake fitowa daga bakin Wasila sai kawai Uwani taja tsaki tana fad'in" To sai me? dan ya sakeki? dama ai haka muke bukata bai wahalar da kanshi ba bai wahalar damu da sharia ba, dan haka sai muji dadin yin harkokinmu cikin kwanciyar hankali, ni wallahi na dauka ma ko wani abun yayi miki ko kuma zakice kina da ciki shiyasa ma hankalina ya tashi." Wasila ta d'ago kanta tana kallon Uwani sai ta hau girgiza kanta takaici da bakin ciki fal ranta, Wai Mahaifiyarta ce ke murna da mutuwar auranta dan dai bata san yanda takejin bakin ciki bane cikin zuciyarta......Bakinta na kyarma! tace"Uwani murna kikeyi da mutuwar aurana."? Uwani ta kalleta cike da mamaki tace"To ai abun murna ne abinda muke nema ne fa ya samu to meye zaki damu kanki. Ta hadiye wani kutun bakin ciki da ya tokare mata a makoshi, tace"Nayi nadama nayi dana sani Yanzu nagane abinda 'Yar uwata keso na gane, dakin mijina shine suttura a gareni daku baki daya! Na gane duniya ba matabbata bace, a jiya dani daku da As mun nufi Ahmadu sharri sai Allah ya mayar dashi kanmu, idan da da 'karar kwana da sai da a tsinci gawata a wani gari ruwa ya tafi dani, nan ta shiga warware musu abinda ya faru da ita jiya da irin taimakon da Ahamdun yayi mata, Uwani taja tsaki da fadin"To sai me dan ya fito dake daga ruwa aiko bai fito dake ba, idan Allah yasa zaki rayu zaki rayu....Wasila nifa bana sonki da wannn mutumin tunda bai san mutuncina ba bai ganina da daraja da mutunci, Yafi daukar wancan munafikin mutumin da daraja, sabida haka na tsani tarayyarku ke dashi wannan sakin da yayi miki shine dai-dai ni a gurina Nasan ke ba karamar mace bace zaki samu wanda ya fishi ki aura." Hawayen dake fuskarta tagoge tace"Uwani wai me yasa kike da ri'ko ne!? ki rabamu da dangin mahaifinmu saboda tsananin rikonki sannan kin sanyamu muyi musu rashin kunya kawai saboda ra'ayinki kin hanamu muje inda suke komai mai allo yayi mana mun yafe mishi kuma ni yanzu na daina ganin laifinsa a kanmu tunda muma ai bamu ganin kimarshi muna mishi fitsara da rashin kunya shiyasa ya kyalemu kuma sau nawa yana daukarmu kina zugamu mu gudo gida.....Ni yanzu shi kadai ne gatana shi zan nema domin ya sasanta ni da mijina domin hauwasa nacewa ta inda aka hau tanan ake sauka." Uwani ta mike tsaye! ranta idan yayi dubu ya 'baci tace"Wasila idan kika saka kafa kikeje gurin wannan mutumin to wallahi ban yafe miki ba! mutukar nice na haifeki naci wahalarki kikaje gurin makiyina ban yafe ba, Saboda baki da hankali har zaki kirani mai riko meye banyi muku ba keda "yar uwarki shine har kike kokarin fifita Kawunki a kaina to na fada miki kikaje Garko gurin mai allo sai na tsine miki kin bi duniya." Wasila da Rashida suka fashe da kuka jin abinda Uwani ke fada, zagi ta uwa ta uba takeyi wa mai allo daga karshe ma fashewa tayi da kuka ta shige daki........Camas! dake tsaye ta kalli Wasila tace"Nifa wallahi banga abinda damuwa ba dan ya sake ki Haba kawata kamar ba kece wacce na sani ba shin wai me ma Ahmadu nan yake dashi ne ? Kawai ki watsar dashi ki cigaba da harkokin ai kamar yanda Uwani tafada wallahi sai kin samu wanda ya fishi kudi kyau mukami da sauran jin dadin duniya kefa matar manya ce." Wasila ta shiga girguza kanta bakin cikin duniya ya taru yayi mata yawa! Wai jama'a me uwani take so da itane shikkenan tunda tace bata yafe ba idan taje gurin mai allo ta amince da hakan zata zauna a gida amma kuma sai ta nemi mai ciyar da ita, Bayan haka kuma tayi al'kawarin har abada ta bar harkar jagaliya zata zauna ta killace kanta a gida.....Tace"Camas! dole fa naji ciwo mutuwar aure babu dadi wallahi ban san ina son mutumin ba sai da haka ta kasance dani, kina maganar zan sake samun wanda ya fishi ni bana fata nafi so kawai na koma dakina." Camas! tace."Yanzu dai kina nufin kin bar Siyasa kenan."? Tace"Kwarai kuwa na bar wannan harkar abadah." Uwani tace"Baki isa ba wallahi! Waye zai dinga daukar dawainiyarmu." Wasila ta kalleta sosai tana nazarin maganarta, tace"Uwani kinga ni bana son ki d'aga min hankali tunda kin hanani zuwa gurin kawuna shikkenan maganar dawainiya kuwa kowa yayi dawainiya da kanshi, wannan gidan ma da muke ciki kada ki sanya ranki zaki dawwama a cikinsa, domin har yanzu governor bai bani takardar shi ba, da ko wane lokaci yana iya tashinmu mussaman idan yaji hukuncin dana yanke, saboda haka dake da Rashidan kowa ya nemi mafita, kada kuma kiyi la'akari da cewar ina da kudi a banki, kudina basu da wani yawa nima zan nemi wata sana ar ne." Uwani tace"Ai ba lallai sai siyasa zakiyi ba akwai sana'oi da zaki ki samu kudin da zaki cigaba da daukar nauyinmu saboda haka kije kiyi shawara ni dai na fada miki ban amince ki koma gidan wannan mutumi ba kuma ban amince kije gurin wannan dattijon banzan ba." Tsabar bakin ciki da takaici bai bar Wasila tace komai ba idan ta fahimci maganar Uwani tana so ne ta turata d'aya sana'ar da tuntuni take so tayi ita kuma ta ta'kiyi (karuwanci) Mikewa kawai tayi ta shige daki ta barsu suna surutu Har dai Fada ya hard'e tsakanin Rashida da Camas! domin dai Camas! ita ke kara inginza Uwani tana sake baud'ewa! Yayin da Rashida ta fahimci haka sai ta hau cuccusawa Camas! ashar tana fad'in ta fice ta bar musu gida su dai Allah yasa sun gane gaskiya kuma karuwanci insha Allahu ba zasuyi ba, ita dai tunda ta dauki karuwanci sana'a to taje tayi! Camas! ta rataya jakarta ta fice daga gidan bayan sun gama zage zage da Rashida. Littafin na kudi ne......! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *50* As ne zaune a tsakanin 'yan sanda sai zare ido yakeyi rigar jikinsa duk tayi jirwaye fuskarsa duk tayi burd'in burd'in da cizon saura idanunsa sunyi jawur! fuskarsa ta kara baki sai maikon yake yi tamkar wanda rana ta daka!......."Yanzu Yallabai tinda kace baka son kowa yaji maganar nan daga mu sai kai sai kuma Ahmadu to mun amince zamu rufa maka asiri amma tare da alkawarin muma zaka yi mana ihisani baka so sunanka ya 'baci a gari mutane suyi maka kallon kwarto manemin matan mutane to zamu lullube sirrinka baza mu watsa a media ba muna so muji nawa zaka biyamu." As yace."Ku fadi ko nawa ne wallahi zan baku bana so Ahamadu yazo gurin nan ya sameni saboda nasan karon mu dashi ba zaiyi kyau ba, kuma ni ku daina zargin na nemi matarshi harkar siyasarmu ce ta hadamu da ita ba wani abun ba." dan sandan yace."Ka daina maganar Ahmadu domin tuntuni mun kirashi a waya ya tabbatar mana da cewar mu sake ka saboda bashi da lokacin ka, yanzu tsakaninmu da kai ne." As ya sauke ajiyar zuciya yana jin sanyi cikin ranshi yaji dadi sosai da Ahmadu bai tona asirin abinda ke faruwa ba.....As yace."Nace ku fadi ko nawa kuke bukata zan baku." Babban cikinsu yace "Za bamu miliyan hamsin." As ya zare ido yana kallonshi. Ba zaku samu miliyan hamsin ba yanzu." Dan sandan yace."Ashe kuwa kana so muyi maka tonan silili." As yace."Bana so kuyi min tonan silili wallahi zan duba nagani amma dai yanzu zan fara sa muku miliyan talatin daga baya sai na cika muku sauran." Sukace Su basu yarda ba As ya shiga tunanin ina zai samu kudi cash a hannunshi duk kudinshi yana siyan filaye ne da gidaje da gonaki! yanzu duka kudin accont dinshi basu fi miliyan saba'in ba dama yana sanya rai kan governor zai bashi wata kwangila to anan yake so yayi cuwa-cuwar shi, wata shawara ce ta fad'o masa yace."kuyi hakuri ku kar'bi! Miliyan talatin nayi muku al'kawari nan da sati biyu zan baku ashirin din." Sukayi a rubuce ta da sharadin idan bai cika musu ba sun shirya tsaf zasu tozarta shi. Ya mike yana karkade rigarshi ya dauki hularsa yasa kana daya daga cikin 'yan sandan ya daukeshi a mota ya kaishi gidanshi, dake Tarauni. Bacci yayi mara dad'i mai cike da mafarkai marasa dadi, sai wajejen azuhur ya tashi yay wanka ya fito damuwa fal cikin ranshi, bayan yay sallah ya dauki waya ya kira Khalifa tare da shaida masa cewar yazo gidanshi yana son zasuyi magana! Hausawa sukace abokin kuka shi ake fadawa mutuwa.....Baici wani abincin kirki ba, ya kwanta a kan kujera yana duba wayarshi, nan yay ta ganin numbers din mutane da rocuding din Wasila da As duk wani magana da Wasila keyi da As da Camas sai da ya gani dake wayarshi tana adana mishi abubuwa koda kuwa ya goge su, Al'amarin yayi ta bashi mamaki! ashe haka yarinyar nan tayi nisa, dama duk sanda ta dauki wayarshi abinda takeyi kenan! sosai ya dinga mamakin hatsabibancin ta, yana ganin rabuwa da ita shine yafi al'kairi a rayuwarshi.....Amma kuma har yanzu yana jin wani irin tsunkuli da zuciyarsa takeyi masa mussaman idan ya tuna da abubuwan da suka faru a tsakaninsa da ita a cikin zamantakewar da sukayi sai yaji gabanshi ya fadi sai ya kira sunan Allah yake samu sassauci! Hannunshi ne ya subce ya danno ma'adanar hotunanshi kawai hotunan da sukayi ita dashi ranar da al'amarin zai faru, suka wanke masa fuska, ya dinga duban hotunan yana mamakinta, sam! babu wata alama data nuna masa a ranar da zai gane ta shirya plan! Aje wayar yay dan baya son ya cigaba da kallonta sakamakon wani irin abu da yaji yana taso masa a cikin zuciyarsa, girgiza kanshi kawai yake yi babu shakka yarinyar nan tayi mishi ba zata! **** Bayan shigarta daki kuka taci ta 'koshi kana taje tayi alwala tai sallah ta fito palo nan ta tarar dasu Uwani zaune suna mai da magana ita da rashida zama tayi kan kujera kafin tace"Rashida bani abinci naci rabona da abinci tun jiya dana bar nan." Rashida ta mike da sauri ta nufu kicin....Ta kalli Uwani dake shan kunu! tace"Uwani ina Camas."? Tace"Tuntuni tayi tafiyarta bayan rashida ta gama zaginta." Tace"Wane irin zagi kuma? Ke rashida me Camas! tayi miki kike zaginta." Tafada tana kallon Rashidan dake kokarin ajiye mata abinci a gabanta." Tace."anti Wasila bayan shigarki daki Camas! ta dinga zuga Uwani wai sai munyi karuwanci kamar yanda takeyi shine nace ta tashi ta fita amma ban zageta ba." Uwani tace"Ma'karyaciyar banza da wofi kika zageni ma ballanta Camas." Wasila ba tace komai ba dan ba taji haushin zagin da rashida tayi wa Camas din ba saboda itama ta tsani tayi mata maganar karuwanci wato saboda taga bata gurin shine take zuga Uwani tana kara hawa! aikuwa da yardar Allah ba za suyi karuwanci ba........Abincin take cuccusuwa tana ya mutsa fuska duk da abincin me kyau ne amma sam bata jin testing dinshi a bakinta abubuwan da suka dame suna da yawa....Rashida ta mika mata ruwa tasha kana tace"Ki bani wayarki in kira Camas muje atm zan ciro kudi kudin dana cire jiya na bar jakar cikin motarshi bani da ko kwabo yanzu sai dari takwas da sukayi min shaura." Rashida tace "Aikuwa babu kudi a wayar." Tace dauko min jakata dana zo da ita a daki." Rashida taje ta dauko mata jakar ta bata dari biyu tace taje ta siyo kati." bakin titi. **** "Wai shin kiran me kake min ne? da alama dai an samu harka dan idan naga irin wannan kiran naka har dadi nakeji wallahi." Khalifa ne ke wannan maganar lokacin da yake kokarin zama kusa dashi Ya dan gyara zamanshi yana fad'in"Ba alkairi ne yasa na kira ka ba." Khalifa yayi saurin kallonshi fuskarsa ta rage walwalar da ya shigo da ita yace."Allah yasa dai lafiya." ? Ya mike tsaye ya nufi bakin window hannuwansa duka a bayanshi, Khalifa ya bishi da kallo yana nazarin palon baiji motsin mutum ba, jikinsa yayi sanyi a hankali ya mike ya iske inda yake tsaye ya dafa kafadarsa a hankali yace."Meke faruwa ne? ina matar gidan take."? Ya juyo da wata iriyar fuska mara dad'in kallo yace."Na saketa."!!! Kalmar ta dinga yiwa Khalifa amsa kuwwa! a kunnansa, ya bude bakinsa na sar'kewa yace."Ka saketa."!? Girgiza kanshi yay yana so ya tabbatar masa! Khalifa ya dinga binshi da kallon mamaki kafin yace"Me ya faru! me yasa ka saketa!? me yasa ka yanke irin wannan hukuncin mara dad'i! duk da Allah ne ya hallatashi amma ba abune mai dad'in ji da fad'e a baki ba wallahi bakaji yanda naji a jikina ba fad'ar wannan kalma da kayi." Ba tare da ya cewa khalifa uffan ba ya wuce shi yaje ya nemi guri ya zauna! hade da rufe fuskarshi da tafukan hannayeshi! Khalifa ya zauna kusa dashi yana me dafa kafadarshi da fadin"Ka fad'a min abinda ke faruwa ni ka barni cikin duhu."! Ya jima hannunsa rufe a fuskarsa kafin ya cire ya tsirawa khalifa ido tiryan tiryan ya shiga fad'a mishi abubuwan da suka faru ya kunna mishi rocouding muryar Wasila da As da irin tsare tsaren da sukeyi a kanshi, ya kuma tabbatar mishi da cewar ajiya Allah ne ya tsareshi dan a yanda 'yan daban gidan gomnati suka zo mishi to babu shakka zasu iya kasheshi ko suyi masa rauni.' Khalifa ya jima yana mamaki gami da jajanta al'amarin! hakika abinda wasila ta aikata babban abune wanda ya cancanta da ayi mata ko wane irin hukunci, to amma kuma baiji dadin hukuncin da ya yanke a kanta, da tayi shawara dashi da farko ba zai yarda ya saketa ba, zai fahintar dashi cewar sakin bashi ne sulotion, ya zauna da ita tinda yayi wa kawunta alkawari kuma yayi mata uziri! duba da cewar akwai kuruciya a tattare da ita in yaso yayi mata horon da za tagane abinda ta aikata babban abu ne, shawara ta karshe da zai bashi shine yayi aure yayi rayuwa da matarshi a cikin gidan tana kallo yasan dole za tayi hankali ta shiga taitayinta amma yaji zafin sakin da yay wa yarinyar mutune ya mai da ta karamar bazawara. Ajiyar zuciya ya sauke yace."A gaskiya banji dadin wannan abu ni da kayi shawara dani ba zan bari ka saketa ba, amma yanzu tinda har haka ta kasance please ka dauki niyya ka kuma 'kudirta a ranka kan cewar ka mayar da ita ni da kaina zanje na dawo maka da ita, sai shawara ta biyu shine kayi gaggawar yin aure domun ta gane kuranta. Ya kalleshi yana ya mutse fuskarsa yace."Kafi kowa sanin idan na bar abu na barshi har abadah! a yanzu idan da wacce na tsana a duniya to wannan yarinyar ce na natseta wallahi, bani kaunar ganinta, saboda haka maganar ma in da wo da ita bata taso ba, aure kuma sai na huta zanyi." Khalifa yace."Kar kayiwa mai allo haka Ahamdu! ka duba daraja da furfurar dattijon! ka duba amanar da ya baka! aure baifi sati hudu ba har anyi an gama! wannan wace irin rayuwa ce."! Kai ya shiga girgizawa yana wani irin mirmishi na takaici yace."Komai abinka ba zan dawo da yarinyar nan ba taje kawai! shi kuma mai allo da kaina zanje nai mishi bayanin komai." Khalifa ya dinga kallonshi yana girgiza kanshi tabbas yasan halin abokin nashi! da zuciya da kuma ramuwar gayya ba tun yau ba! Yasan bai da hakuri ko kad'an! mutukar kayi mishi abu bai rama ba to shine yaga dama. *** Ta kira wayar Camas! ta kai sau ashirin bata dauka ba, sai abu ya shiga bata mamaki! taje wayar tayi tana fadin"Ko bata kusa da wayar ne bari anjima na sake kiranta......Ita kuwa Camas! a lokacin suna tare da As yana shaida mata abinda ya faru dashi itama tana shaida masa irin hukucin da Wasila ta yanke kan cewa ta bar harkar Siyasa kuma ta tabbatar masa da cewar Ahamdu ya saketa yanzu haka tana gidanta. As yaji dad'in labarin Camas! sai dai kuma baiji dadin furucin da tayi ba na cewa ta bar harkar siyasa hakika ta zama wani jigo a tafiyar tasu, dole ya shirya yaje gidan domin ya rarrasheta ta dawo kawai su cigaba da fafatawa, Camas! na fita daga gest house din As kira ya sake shigowa wayarta koda ta duba taga Numbar Rashida ce sai ta kashe tana jan tsaki tasan dai zancen gizo baya wuce na 'koki! Tana kokarin shiga motarta text ya shigo ta bude tana dubawa. _Camas! kina ina ne? inata kiran wayarki baki dauka ba dan Allah kizo gidana yanzu zamuje banki zan cire kudi yanzu ina jiranki_ Tsaki taja mai tsayi lokacin da tagama karanta text din ta bude mota ta shiga tana fad'in"Shashasha kawai ai kud'in nan sun shiga accont dina kenan! ke kin tsira da gida ni na tsira da kudi a tafiyar nan! babu abinda baki mallaka ba dan'kareran gida iyayen kudi gwala gwalai, ni kuwa fa in banda wannnan fankon motar babu abinda na tsira dashi, saboda haka na cinye kudi wallahi komai za'ayi sai dai ayi." Tuka motarta tayi ta bar gurin hankalinta a kwance. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *51* Wasila tayi ta tsammanin amsar Camas! taji shiru har wajejen karfe goma na dare bata daina kiran Camas! a waya ba, gashi dai tana shiga amma kuma taki dauka......Uwani tace"Wai kiran me kike mata ne? ni nasan da wuya Camas! ta dawo gidanan dan baki ga irin zagin da rashida tayi mata ba." Tace."Uwani ba wannan matsalar bace, kin san na fad'a miki jiya Ahmdu yace zai min bincike cikin accont dina sai na yanke shawarar kwashe kudina dake ciki na mayar accont din camas! kudin suna da yawa fa kusan miliyan biyar ne zuwa shida, a jiya na ciro dubu hamsin to jakar tawa na motarshi, ban dauko ba, wannan dubu dayan ma da nayi kudin mota gurin zuwa nan na siyi kati Allah ne ya taimakeni na tsinta cikin jakar dana zo da ita, kinga yanzu duka sau dari biyar a hannuna gashi ina ta kiran Camas a waya taki dauka." Uwani ta soma tunani cikin fargaba da faduwar gaba tace"Anya Camas! ba amanarki zata ci ba kuwa irin wannan kira da ake mata ai yaci ace ta dauki wayar idan ba da abinda ta shirya ba. Rashida tace"Aikuwa wallahi ko tana yawo da ubanta sai ta fito da kudin nan tabd'ijam! miliyan shida za ta cinye lallai bata da hankali. Wasila tace"Allah nima jikina ya soma sanyi da al'amarin anya kuwa! amma dai bari na sake kiranta mu gani." Nan ta shiga kiran wayar Camas! gashi dai tana shiga amma babu amsa! dukaninsu hankalinsu yay masifar tashi mussaman Wasila da tasan wannan kudin su kadai ne suka rage mata kuma sune zasu taimaka mata ta 'bangarori da dama tunda dai ta 'kudiri aniyar barin harkar jagaliya......Sai kusan karfe daya na dare sannan sukaje suka kwanta dukaninsu babu wanda yay baccin arziki sai juyi sukeyi mussaman wasila da abubuwa suka taru sukai mata yawa, kuka take sosai shashshekar kunanta yasa Uwani mikewa zaune tana kallonta, Tsakanin d'a da mahaifi sai Allah sai taji tausayin 'yar tata itama ta hau share hawaye tace"Wannan kukan bashi ne mafita ba a gurinki, wai shin meye abun damuwa da tashin hankali dan wannan mutumin ya sakeki ke ba abin alfahari bane a gurinki za kici karanki babu babbaka yanzu fa wata dama kika samu da zaki cigaba da neman kudinki gashi Allah ya sanya miki nasibi a cikin harkar kina nema ki 'barar da damarki, ni dai idan zakiji maganata shine gobe idan Allah ya kaimu ki shirya ki tafi gidan gomnati domin cigaba da gudanar da harkokin siyasarki." Wasila taja majina tana goge fuska tace"Nifa Uwani na fada miki bazan sake yin wannan harkar ba na fada miki ni yanzu babban damuwa ta shine idan Camas! ta salwantar min da kudina ya zanyi da rayuwata da wane kudi zan kama sana'a me zan juya ni ba zanyi karuwanci ba kuma ba zan koma wannan harkar ba." Uwani tace"Idan ya kasance Camas! ta salwantar miki da kudi ba sai ki maka ta kotu ba, sannan kina maganar sana'a to tunda kince ba zaki koma harkar siyasa ba kuma kince ba zakiyi karuwanci ba to me zai hana ki shiga wasan hausa (film) nasan mutukar kin shiga wannan harkar zakiyi arziki na ban mamaki." Wasila ta dinga kallon mahaifiyar tata cike da tsananin mamaki! wai me yasa uwani take hakane? kullum bata da buri illa taga ta dorasu turba mara kyau! idan akwai abinda ta tsana a duniya bai wuce wannan harkar ba film! duk lalacewa ta tattare a gurin koda kai mutumin kirki ne kana wannan harkar jama'a ba zasu kalleka da kima ba. Ba ta sake cewa da ita koma ba ta koma ta kwanta tare da juya mata baya tana addua cikin ranta tana jinta tana sake kwarzanta mata nasarorin harkar film din da yanda 'yan mata ke samun mahaukatan kudi mutukar sun shiga harkar....Uffan bata sake ce mata har dai taji shiru hakan ya tabbatar mata da cewar bacci ya dauke ta, sai ta mike a hankali taje ta dauro alwala ta fito a nutse ta tada sallah nafila tayi raka'a biyu ta dade sujjada karshe tana kuka da addua da fadin"Allah ya kawo mata agaji ya yafe mata kusa kuranta na baya.....Addua ta shafa ta kwanta kan daddumar bacci me nauyi ya dauketa. Asubah suka tashi sukayi sallah Uwani ta koma tayi kwanciyarta, Wasila da Rashida suka zauna suna shawarwarin ya za suyi, Tunda yanzu ma sun sake kiran Camas! din bata dauka ba, Rashida tace",Anti Wasila bari gari yay haske sai muje gidansu shegiya macuciya dama ni tuntuni bana kaunar abotarku da ita na tsaneta wallahi." Hannunta rike da wayar tana ta trying tace"Rashida bamu da tabbacin samun Camas! a gidansu shin ko kin manta ne? ko lokacin da muke unguwar sai tafi sati biyu bata kwana a gidansu ba tana can yawon bin maza watarana ma gidanmu take zuwa ta kwanta." Rashida tace"Na tuna yanzu to ya za'ayi a same ta."? Shiru tayi tana nazari itafa ba tasan ya za'ayi a sami Camas! ba dan bata tantance in da take ba......Rashida tace",Anti Wasila ki shirya sai na raka ki government house din nasan za'a iya samunta a can." Girgixa kanta tay tace"Har abada na bar wannan gidan tunda banda ala'ka dashi a halin yanzu, kuma bai zama lallai a samu Camas! a can ba, ban'ki ma idan anje gest house din Alhaji Ma'aruf mybe a iya samunta a can."! Rashida tace"To ki shirya muje can d'in." Shiru tayi tana naxari kafin tace"Rashida ba zanje ba kawai kyaleta don Allah ni na hakura taje kanta tayi wa in ta min maganar kudin shikkenan idan batai min ba na barta da Allah." Rashida tace"Ni dai da zaki min kwatacen gest house din da naje naci ubanta wallahi sai ta baki kudinki." Girgiza kanta tayi tace"Rashida ba zakije wannan gurin ba kawai dai tinda nace na kyaleta da Allah shikkenan." Rashida tace"shikkenan bari na hada mana abin kari." Wasila ta mike suka shiga kicin din tare, sto ta bude tana duba abinda yay musu saura na kayan abinci shinkafa ce gatanan duka bata kai rabin buhu ba sai kwalin indomee biyu da taliya da macaroni mansu ma ya kare da kayan maggi babu siga saura kwali daya gwangwanin madara da milo biyu ya rage, hankalinta yay masifar tashi tace"Rashida abinda yay saura kenan?" Rashida tace"Eh mana kinga ni dai.'' Frige ta bude wayam! babu komai a ciki sai robobin lemo da ruwa wanda suka sha suka mayar ciki......Tace"Innalili wa'ina ilaihi raj'iun." Fita tayi daga kicin din ta koma palo ta zauna, tana kuka yanzu idan kayan abincin nan ya kare ya za tayi.......Shikkenan zasu komai rayuwar kuncin da sukayi a baya, Sai hawaye ya shiga zubowa daga idanunta tana tausayawa rayuwar da zasuyi nan gaba. Tananan zaune Rashida ta fito da fulas din shayi da wata karamar kula data zubo musu indomee a ciki ta aje taje ta dauko sauran kayan da zasuyi amfani dashi gurin cin abincin, ta hada musu suka fara karyawa Wasila dai cin indomee kawai take hankalinta duk baya jikinta tunaninta ya ta'allaka gurin yanda za tayi asirinsu ya rufu....Rashida tace"Anti wasila ina gold din da kika siya kwanaki ba sai ki siyar dashi ba nasan kudin zasu isa ki fara sana'a dasu." girgiza kanta tayi cikin tsananin damuwa da neman mafita tace"Rashida kin mata ranar da Ahamdu ya dauke ni da sunan matarshi, ranar nayi ado da da gold din har nasa lifaya keda Camas! kuka dinga kwarzanta kyawun da nayi gabakid'aya gold dina na gidan Ahmadu in banda wannan zoben dake hannuna." Rashida jikinta yayi sanyi sosai babu shakka suna cikin tsaka mai wuya dama abinda takeji kenan gashi kuma ya faru, tace"Shiyasa tuntuni nake hanaki wani abun saboda dama ni tuntuni na dawo daga rakiyar Uwani wallahi duk wata masifa da muke ciki itace ta jefamu kullum burinta muje mu samu kudi ita tana zaune a gida, Allah ya baki miji nagari me kudi babba mai hankali wanda zai rike ki da kyau ta zugaki kin kashe auranki, gashinan komai ya jagu'be! dama abinda nake ta tunani kenan." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Rashida mu bar wannan maganar don Allah hausawa nacewa tun ranar gini tun ranar zane duk abinda kikaga ya samu bawa to da sanin Allah, ammafa wani abun mutum shike janyowa kanshi Ni da uwani mun so zuciyarmu kuma gashinan ta kaimu ta baro amma babu komai Allah yasa ya zama izina a garemu ni da ita, yanzu mu gama karyawa sai muje can d'orayin gidansu Camas ko Allah zai sa mu same ta." Uwani nacan na bacci suka shaida mata inda suka nufa cikin bacci tace dasu Allah ya kiyaye suka kadai kansu suka fita daga gidan. Asabe mahaifiyar Camas! na zaune a kujera 'yar tsuguno tana tsince shinkifa taji sallamarsu, ta amsa tana musu sannu da zuwa tabarma ta shimfida musu tana fad'in "Wasila yau kece a gidan namu, Ina tace Hadiza zata rakani inga inda kuka koma Allah bai nufa ba sannunku da zuwa." Suka shiga gaisawa, Asabe na tambayarsu Uwani sukace tananan lafiya lou. Wasila tace"Camas! kuwa tanan."? Asabe tayi kasa da kanta ran nan a 'bace tace"Yaushe rabon hadiza da kwana a gida ai tafi wata uku sai dai takanzo duk bayan sati biyu to wannan karon ma kinga satin ta uku bata zo ba." Wasila tace"Ayya! mybe tananan tafe." Asabe tace"To Allah yasa." Shiru sukayi kafin su ta mike Asabe tace"Har zaku tafi bazaku tsaya kuci abinci ba." Wasila tace"A'a Asabe mungode." Har soro ta rakosu tana fadin su gaishe da Uwani da kyau kafin tazo. Suna fitowa Wasila tace na fad'a miki dama kinga munyi asarar kudin motarmu ko? gashi bamu dana komawa gida tsakanin dorayi da tishima akwai nisa sosai dan da kyar ma aka kawo su a dari biyar kona pure watar basu dashi.....Rashida tace"Mu shiga gidanmu wanda muka bawa malam 'Dayyabu nasan idan yananan zai bamu kudin mota da zamu koma gida." Wasila taji dadin maganar Rashida sai suka nufi layinsu na da, suna shiga layin suka hango, gidansu ya koma katin sai da kayan provision! tsayawa sukayi suna mamaki! wani yaro da yazo wucewa ya shiga kallonsu yaso ya ganesu Wasila tace"Kai waye cikin provision din can." Yaron yace."Jazuli ne na gidanmu malam d'ayyabu ne ya siyar masa da gidan shi kuma ya ruge yayi kanti." Wasila da rashida suka shiga mamaki! ashe malam dayyabu haka yake sun bashi gida domun ya zauna ya siyar ya kar'be kudin ya gwammace yayi ta yawon haya da yara da mata, cikin unguwar dama su Wasila da gidan malam dayyabu sune talakawa, gwara su wasila ma gidan kansu ne shi kuwa malam dayyabu gidan haya ne duk lokacin karbar kudi sai anyi rigima dashi masu unguwa sun taru a kanshi sannan zai bada kudin, shinda wasila ta tausaya masa suka bar mishi suna ganin tunda sun samu wani me zasuyi dashi ashe bayan tashin su da sati biyu malam dayyabu ya siyar da gidan ya kama haya ragowar kudin yasa a aljihu yana cin karansa babu babbaka dasu.......Ajiyar zuciya suka sauke a tare suka kama hanya suka bar gurin zuciyarsu cike da wasi wasin yanda zasuyi. Sosai suka dingi tafiya kan titi wanda tun suna magana suka daina tafiya kawai sukeyi suna yanke yanken hanya har Allah yasa suka fito titin gadon 'kaya! Rashida ta sharce gumin dake goshinta tana haki! tace"anti wasila zama zanyi na huta na gaji wallahi." Wasila tace"Mu samu guri mu zauna nima nagaji." Suka sami guri dai-dai Gate din shiga Management suka zauna suna hutawa, sunanan zaune daliban dake makaranta suka soma fitowa 'yan mata maza zawara da matan aure wasu na fitowa da motocin su wasu wasu kuma na tare abin hawa! Wasila ta dinga kallonsu suna bata sha'awa suna da gata suna da galihu sunyi dacen iyaye sun tsaya musu kan ilimi su kuwa fa! sune nan sune can! Sai taji zuciyarta ta karye hawaye ya tsinke mata! tayi gaggawar sunkuyar da kanta kasa tana sharewa bata so Rashida ta gani sannan kuma jama'ar dake gurun suma bata so su gani, tana dago kanta suka had'a ido da Suhairat ita da kawayenta bakin wata mota! Zasu shiga macace take driving din, da sauri ta kauda kanta gabanta na faduwa tace"Rashida tashi mu tafi." Rashida tace"Anti wasila dan bari mu sake hutawa wallahi gurin akwai iska." Tace."Rashida hutun jaki da kaya kikeyi kawai ki tashi mu tafi mu samu mu fita babban titi na sabon titi." Rashida ta mike tana yafa mayafinta sukayi gaba.......Motarsu Suhairat ce taci burki a gabansu, da sauri suka matsa baya Suhairat ce ta bude motar ta fito sauran suna ciki suna hangensu Gabansu ta tsaya tana watsawa Wasila kallon banza tace"Ke matar babban mutum ina zuwa haka? ya naga kina yawo a kasa ko satar hanya kikayi kika fito yawon tazubar d'in da kika saba."!? Wasila tayi shiru tana kallonta Rashida tace"Haba Suhairat wace irin magana ce wannan? kin manta anyi muku tsakani da anti wasila meye ruwanki da ita yanzu." ? Suhairat tayi dariya tana gyara zaman glass din dake idanunta tace"Rashida daga tambaya sai cibi ya zama 'kari! ai gani nayi bai dace ace kamar wasila matar *Ahamadu Musa* na yawo 'kasa ba, ai kamata yay mu ganta cikin katuwar mota wacce ta amsa sunanta, ko da yake dai ina jin satar hanya tayi ta fito, Okey karfa ku damu da maganata, ba wani abun nake nufi ba, saboda haka na barku lafiya." Wasila da Rashida suka bita da kallo har ta shige motar tasu suna kallonta tana she'ka dariya tare da tafawa da 'kawayenta tana nuna wasila da hannunta su kuma sai dariya sukeyi, kafin wacce take driving din ta figi motar a guje suka bar gurin. Wasila ji tayi gwiwowinta sunyi bala'in sanyi ta inda har ta kasa motsa kafafunta da niyar tafiya sai kawai ta nemi gefan titi ta zauna rana na kwallare mata fuska zufa! ta shiga ketowa daga jikinta Rashida itama ta zauna kusa da ita tana fad'in"Amma wallahi suhairat din nan bata da mutunci shegiya guzumar banza wacce ta rasa mashinshine anti wasila ki kyaleta don Allah mybe suna da labarin Ahamdu ya sake ki shiyasa suke murna da dariya amma babu komai ai duk abinda mutum yayi kanshi. Ba tace komai ba tana dai sauraran Rashidan da duk rarrashin da take mata ita kuma sai nanata kalmar innalilihi wa'inna ilaihi raji'un takeyi a zuciyarta, ji tayi komai na rayuwa yayi mata zafi ta dinga nadamar kuskuran da tayi a baya, kanta ne ma ya soma yi mata ciwo, rana ce ko damuwa ce ko kuma rashin bacci ne? babu wanda ya sani sai Allah. Kusan mintina ashirin suka dauka a zaune a gurin masu babur din a dai-dai ta sahu sai tayi suke musu wai ko zasu shiga kowa na ganin lamun ba shiga zasuyi ba sai ya buga babur dinshi yayi gaba!.................. Cikin 'kwalleliyar ranar dake kan ganiyar ta, suka fita, titin sabon titin gidan 'kankanra lokacin sunyi masifar galabaita mutuka gashi ko na pure watar babu Wasila taja hannun Rashida suka fake wata inuwa still dai a bakin titin suke zaune suna mai da numfashi suna kallon ababen hawan dake shige da fice a gurun......."Wasila anti Wasila yunwa nakeji da shiru kinji ma'kogwarona kuwa kai anya ba zamu nemi taimako ba kuwa."? Wasila tace"Nima nagaji Rashida taimako a ina zamu nema."? Anti wasila mu nemi left gurin masu motar gida sai sunfi sauki akan masu a dai-dai ta sahu tunda su kinga sana'a suka fito." Wasila tace"anya kuwa Rashida." "Allah anti wasila ba zamu iya kai kanmu gida ba akwai fa nisa gashi ko rabi ba muyi ba." Wasila tace"Akan muyi left din nan ai gwara mu tambayi wannan me shagon na tsalleke watakila ya taimaka mana." Rashida tace"Bari naje ki zauna dan na lura kamar jiri ke d'ibanki." Tace"Wallahi jiri nake rashida yi sauri kije Allah yasa ko dari biyu ya bamu." Rashida ta tsallaka titi domin zuwa gurin me shago........Mai shago najin bukatar Rashida yace "Duba daya ma zan baki amma shigo ciki na aunaki." Rashida ta gane abinda yake nufi duba da irin yanayi kallon da yake mata na iskanci! sai kawai taja tsaki! ta fita daga shagon......Ba tayi shawara da Wasila ba kawai ta soma d'aga hannu tana tsaida motacin mutane........ Khalifa dake driving yay saurin kallonshi hankalinsa na kan jaridar dake hannunshi yana dubawa yace."Duba wacan yarinyar kamar Wasilan ka." Yay gaggawar hanya nan ya hango rashida na d'agawa motarsu hannu, ya mai da kanshi kasa ya cigaba da abinda yake! Sai da suka kusa isa gurun rashida khalifa ya gane ba ita bace amma kuma gaskiya suna kama sai dai ita wannan tafi wasila haske! A hankali ya tsaida motar dai-dai inda Rashida take tayi gaggawar zuwa gurin........."Khalifa ya sauke gilashin motar a hankali yana kallonta, rashida ta marairace fuska muryarta na rawa tace"Dan Allah Yayana ka taimaka mana ka rage mana hanya nida 'yar uwata wallahi tun daga d'orayi muka zo nan a 'kafa kudin motarmu ya 'kare." Tunda rashida ta soma magana yake jin wani iri, maganarta sak! data Wasila, ta gefan ido ya dan kalleta, sai gabanshi ya fad'i! wannan fuskar ai kamar ya santa yarinyar nan ce kanwar Wasila, shiru yay bai ce komai ba, shi kuwa khalifa da bai san abinda ke faruwa ba yaji tausayin rashida yace."Ina 'yar uwar taki." Rashida tayi saurin fad'in gata can tsallaken titi." Yace."Yi maza ki kirata." Cikin farin ciki rashida ta tafi, dake hankalinta na kan khalifa sam! ba tayiwa Ahamdu cikkaken kallo ba ballanta ta gane shi. "Anti Wasila taso ga mota can zat a daukemu Allah sarki wallahi me motar nada kirki." Wasila na daga inda take zaune ta dinga kallon had'addiyar motar tana mamaki! anya kuwa, wata zuciyar tace wasila idan baku shiga motar nan fa babu wanda zai taimakeku gwara ku shiga ko bakin asibiti ne sai ya saukeku in yaso sai ki siyar da zoben hannunki." Sai ta yarda da shawarar da zuciyarta ta bata, ta mike tana karkad'e jikinta suka nufi motar. Khalifa tun kafin su karaso yake mamaki! Fuskar wasila ba bakuwa bace a gurinshi itace wallahi." Ya furta ba tare da ya sani ba, kalmar ta sanya shi dago kanshi yana kallon inda yake kallo, kawai sukayi ido hudu da ita, sai dai ita bata ganinshi shike ganinta kasancewar gilashin motar me duhu ne. Yace."Mutukar zaka dauki yaran nan cikin motar ka ka saukeni dan Na rantse ba zan had'a nuffashina dana wannan yarinyar ba." Khalifa ya dinga kallonshi cikin tsananin mamaki! yace."Haba! taimako ne fa shin bakaji abinda 'yar uwarta ta fad'a ba, tun daga dorayi zuwa nan a 'kafa akwai wahala, kayi hakuri kawai a daukesu ai ba wani abun bane." Sai kawai ya hau kokarin bude mota zai fita.....Khalifa yace." A'a me yayi zafi! bari kawai na basu kudin abun hawa ba sai ka fita ba." Yace."Hakan shi yafi maka alkairi." Khalifa ya bude ma'adanar kudinshi dake cikin motar dubu ashirin ya 'kirga ya zuge gilashin motar, suka had'a ido da Wasila sai tay saurin matsawa baya gabanta na faduwa, dan ta hango gefan fuskar mutumin nata kanshi a kasa yana kallon jarida......Khalifa shima bai nuna ya ganeta ba, sai ya mikawa Rashida kudin yace."Kanwata 'karbi kudin nan ku hau abun hawa, kinji ko abokina nada uziri shiyasa amma da da kaina zan dauke ku na kaiku har gida." Hannu na rawa Rashida tasa ta kar'bi kudin tana godiya ta kalli Ahamdu tana fadin"Mungode sosai Allah ya saka da alkairi." A nutse ya dago kanshi yana kallonta, itama ta shiga shock ganin fuskarshi, Yace."Ki godewa Allah." Sai ya mai da kanshi 'kasa, Khalifa ya kunna motar yana fadin"A gai da gida ko." cikin nauyin baki tace"Mungode." ta bar jikin motar, sai da motar ta bar gurin sannan ta wuce cikin sanyin jiki ta nufi inda Wasila ke tsugune kusa da wata bishiyar darbejiya kanta na kasa gabanta sai faman faduwa yake tana fadin"Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un a zuciyarta. *_Ba cinye wa bace ba kuma burgewa bace ki dinga cushe cushen maganin matsi a matantakarki, ruwan d'umi kawai ya isa ya sanya gabanki ya matse ko da kuwa kinyi haihuwa goma ne, yana da kyau idan kin haihu a gida kije asibiti domin a duba matantakar ki ko kin samu matsala a gyara miki in kika zauna a gida bakije asibiti ba, akwai matsala idan kin 'karu guri ya had'e a haka mijinki ya shiga yaji kwararo! shikkenan kuma matsala ta afku a tsakaninku🙋🏻‍♀️_* Littafin na kudi ne......![13/08, 6:37 pm] +234 906 803 2427: 'Yr Bngr Sys *53* Malam mai allo na shirye shiryen tafiya tsangayarshi, su Ahamdu suka sauka a garin......Tanimu d'anshi na biyu shine ya shaida masa zuwan ba'kin, Ya fito cikin babbar riga da koren rawani a nannade a kanshi, ganin su Ahamdu tsaye jikin motarsu ya sanya ya washe bakinsa, ya shiga yi musu barka da zuwa yana fad'in"Gwara da Allah bai sa na fita ba, dama yanzu nake shirin fita gurin karatu da sai da muyi sa'bani sannuku da zuwa sannuku." Cikin gidan suka nufa akwai wani babban zaure a soro wanda yake saukar baki a ciki dama kullum sai Bitan ta shiga ta gyara ta kunna turaran wuta dan haka ma yanzu dakin sai kamshi yake yi, Ahmadu da khalifa suka zauna......Malam mai allo ya zauna kan buzunsa yana fad'in"Wallahi ko jiya sai da nayi zancen ku nake cewa Hajara da Bittan su shirya suje suga dakin yarinyar nan akwai kuma 'kwan zabi dana aje mata sunanan da yawa nace su tafi mata dashi ta soya tunda nasan in tazo nan garin tana yawon soyawa taci." mirmushi kawai Ahamdu yay yana tausayawa mutumin bai ce komai ba ya shiga gaisheshi ya amsa cikin walwala da farin ciki kai kana ganinshi kasan yana cikin farin ciki....suka gaisa da khalifa cikin farin ciki da barkwanci kafin ya tashi da sauri yana fad'in"Bari nasa bitan ta kawo muku abinci da ruwa." Yana fita dakin yay shiru Khalifa yayi gyaran murya yana kallonshi yace."Yanzu baka tausayawa wannan mutumin ba! ya kake tsammanin zaiji idan ka sanar dashi abinda ka aikata dan Allah ka janye kudirinka ka kudurta a ranka ka mayar da ita, kar ma ka fada masa komai kawai kace kazo gaisheshi ne." Shiru kawai yay baice komai ba, a zahirin gaskiya mutumin ya bashi tausayi sosai yasan zai shiga tashin hankali mutukar yaji da abinda yake tafe dashi, ammafa duk da hakan baya tunanin yanje kudirinshi shi kanshi a yanzu ya rasa wace irin 'kiyayya yake wa yarinyar sam yanzu baya ma so a dangantashi da ita, dan haka gwara kawai ya sanar mishi da abinda ke faruwa hausawa nacewa ta inda aka hau tanan ake sauka. Malam mai allo ya shiga dakin yana gyara babbar rigarshi, sai fara'a yake yace." Kamar na sani yau na tashi Tanimu da sassafe ya tatso nono ashe ina da baki kai masha Allah naji dadin zuwanku Ahamdu." Yafada yana gyara zamanshi kan buzunsa.....Bitan ce ta shigo hannunta rike da wata kwarya me zane zane da fefe a samanta da ludai guda biyu tana fadin"Sannunku da zuwa."Khalifa yay saurin kar'bar kwaryar furar yana amsawa, ta dan tsuguna gefe tana gyara lullu'binta suka fara gaisawa, Ahamdu duk nauyi da kunya ya isheshi ganin yanda mutanan ke rawar jiki a kansu, Bitan na kokarin fita Kawu Habibu da Haraja suka shigo suma suna cike da murna da farin ciki, Mai allo ne ta tura danshi, Tanimu yaje ya sanar musu da zuwan su.....Suka gaggaisa cikin mutunci da mutuntawa Ahamdu duk jikinsa yayi sanyi da karamancin mutanan, Mutanan nada kirki da mutunci da kara babu shakka da karamcinsu Wasila ta dauko to da taji dadi, wannan mugun halin mybe daga can dangin uwarta ta daukoshi, abinda yake ta fada kenan a zuciyarsa......Khalifa ne ya iya shan furar shi kam ko ludai daya bai sha ba, tun daga sannan mai allo yasha jinin jikinshi dan bai san Ahamdu da irin wannan fuskarba babu walwala babu sakewa tun dazu suke hira da khalifa yayi shiru abinshi sam ba'ayin doguwar magana dashi zaiyi shiru mai allo jikinsa yay sanyi sosai, Gyaran murya yay ya mai da hankalinsa kan Ahamadu yace."Jikina na bani akwai babban al'amarin dake tafe daku dan hauwasa sukance labarin zuciya a tambayi fuska hakikanin gaskiya alhaji Ahamdu ba haka nasan fuskarka ba, a sanin da nayi maka kai mutum ne mai walwala da sakakkiyar fuska ina fatan ba wani laifin wannan yarinya tayi maka ba, dan dama kullum cikin addua nake ubangiji Allah ya zaunar da ita dakinta ya kareta daga rudin duniya dana mahaifiyarta." Khalifa dai 'kas yay da kanshi kunyar had'a ido yake da mai allo din da kaninshi Habibu, dan yanzu da ya sani ma yake da bai rako ahamdun ba sam baya son abinda zai daga hankalin mutane......'Dan numfashi ya sauke a hankali kafin yay gyaran murya yace."To Alhamudullihi arrama! naji dadi da ka dan fuskanci wani abu daga kallon yanayi na, Da farko dai kaine ka bani auran wannan yarinyar ni kuma biya sadaki na kar'ba bisa amana, to wani babban dalili ya sanya na yanke hukunci a kanta wanda nasan ba zai maka dadi ba, kayi hakuri haka Allah ya kadarta bazan boye maka ba Allah ya gafarta malam naso na rike amanar da ka bani amma zuciyata ta'ki aminta, da hakan.......Wannan yarinya tayi min abun da ya sanya naji na tsaneta gabakidaya bani son ganinta cikin gidana, ba kuma na son cigaba da zama da ita a matsayin matata, dalili kenan da ya sanya ni na saketa saki day........Kafin ya 'karasa mai allo yayi saurin fadin kalmar "Innalilhi wa'ina ilaihi raji'un!!!! Ahamdu yayi kasa da kanshi, mai allo ya shiga goge zufa da babbar rigarshi gumi ne kawai yake karyo masa, Kawu Habibu kuwa fad'i yake " Garin yaya haka ta faru!? me yarinyar nan tayi maka me zafi da har zaka saketa Alhaji Ahamdu kada kayi mana haka." Shi dai shiru yayi kawai kanshi a kas......Mai allo yace."Alhaji Ahamdu ka sanar min abinda ke faruwa me wasila ta aikata maka ka saketa nasan dai tabbas ba zaka aikata wannan abu ba sai da kwakkwaran dalili ina so kar ka rufe min komai ka shaida min abinda ke faruwa. Cikin nutsuwa ya shiga warware musu irin badakalar dake faruwa ya kuma kunna musu muryar Wasila da As din a lokacin da suke kulle kullensu, ya kuma tabbatar musu da cewar dalilin kenan da ya sanya yaji zama da ita ya fice masa daga rai! bayan haka kuma koda ya zauna da ita to zuciyarsa za tayi tai masa wasiwasi a kanta ba zai iya yarda da ita ba........Mai allo yace."Banga laifinka ba Ahamdu banga laifinka. Hakika yarinyar nan ta cuci kanta ta cuci rayuwarta, tunda irin rayuwar data za'bawar kanta kenan to babu mu babu ita, duk wani hakki nasu munyi kokari mun saukeshi amma kullum cikin bin zugar shaidan takeyi da bib zugar mahaifiyarta, Wasila ta cuci kanta ta samu dama ta watsar babu komai Ahamdu mungode sosai da jajurcewa kuma naji dadi matuka da kazo kasanar dani abinda ke faruwa dan da baka sanar dani ba ba zan sani ba, kullum zan ta tunanin yarinyar na dakinta tunda dai ni nasan ba zasu zo inda muke ba, amma babu komai, zamu kyalesu mu zuba musu ido dan ba zamu inda suke ba, duk sanda duniya ta koya mata hankali na tabbata zasu zo su nemi inda muke." Muryarshi na rawa ya 'karashe maganar wanda har Ya dan bashi tausayi sai dai baice komai ba kuma ya gagara hada ido dashi ballanta khalifa da tunda aka fara maganar kanshi a kasa baice komai ba........A hankali ya dan gyara kadan ya zura hannu cikin aljihu kudi masu yawa ya ciro ya aje gaban mai allo din yace."Allah shi gafarta malam mu zamu wuce saduwar alkairi insha Allah zumuncinmu ba zai yanke ba ka kwantar da hankalin ka banyi haka da nufin in 'bata maka rai ba, nayi hakan ne dan ganin kamar shine maslaha." Mai allo ya mike yana gyara babbar rigarshi yace."Haba Alhaji ai wannan yarinya ba zata rabamu ba kuma ni ban 'kullace ka ba kasan shi aure da mutuwa rai garesu dik sanda kwanasu ya kare shikkenan Ubangiji Allah yasa haka shine alkairi amma ba zan gaji da fad'in cewar yarinyar ta cuci kanta ba." Har bakin mota suka rako su, Kawu Habibu kuwa ai tsabar bacin rai ya hanashi magana sosai yake ganin hauka da wautar yarinyar ta auri babban mutum attajiri irin wannan ta cutar da kanta, shi kam ai da yana da 'ya mace da yay masa huce haushi da ita.......Suna tsaye a gurin har sai da motar ta 'bacewa ganinsu. Suka juya suka koma cikin gidan jikinsu duk a sanyaye...........Khalifa na drving yana girgiza kanshi gaskiya da ya sani kawai yake gurin rako Ahamdu mutane masu mutunci da karamci kawai ya watsa musu ' kasa a ido! meye rayuwa! yarinyar nan tayi laifi ta gane kuranta tayi nadama ta bada hakuri me ya kamata ayi sai a yafe mata Allah ma hakuri yake da bayinshi, kwata kwata baya son wannan d'abi'a ta abokinshi, ri'ko da ramuwa ba d'abi'a ce me kyau ba, ko babu komai yarinyar nan taci darajar masu daraja irinsu mai allo amma ya watsa wa idonshi kasa ya kalli tsabar idonshi yake shaida masa ya sakeki 'Yarshi. "Kasan Allah wannan abu da ka aikata ina me tabbatar maka da cewar sai kazo kayi nadama a gaba! Allah da kanshi shine ya halatta saki ya kuma umarce mu muyi amma ka sani duk ranar da akayi shi sai al'arshi ya girgixa! Ubangiji baya son kalmar gashi dai shi ya hallice ta, kuma kasan dole akwai jarabta wanda ubangiji keyi wa ma'aurata da irin haka ta ritsa dasu, ita yarinyar tata me kyauce tunda dai ta baka hakuri, ta kuma nemi yafiyarka, ka daina ganin kamar kasha wallahi Allah sai ya jarrabeka da masifar kaunar yarinyar a kuma lokacin da tayi maka nisa."! Khalifa ya karashe maganarshi cikin bakin ciki da damuwar abinda abokin nasa yake yi.......Yace." Sai dai kai Allah ya jarrabeka amma bani ba ni babu wani nadama da zanyi dan na rabu da wannan yarinyar Allah da zuciya yake aiki ba da wani abu so ka daina wannan maganar kawai." Khalifa bai sake cewa dashi komai ba kan maganar suka shiga wata hirar khalifa ya kudiri aniyar daga yau ya daina sanya bakinsa kan maganar tunda dai haka yake ganin shine dai-dai da rayuwarshi shikkenan ********** Kwanaki hud'u da faruwar al'marin, Wasila nata ciwo a tsaitsaye amma bata bari Uwani ta fahimci komai saboda duk sanda amai zai taso mata a sace take zuwa toliet ta kalato shi wani ya fito wani yaki fitowa ita da kanta ta zargi ciki a tare da ita sai dai tana so ta saci jiki Rashida ta rakata suke asibiti domin a tabbatar mata......Watarana haka takw wuni ba taci abinci ba saboda yanxu ba komai ke mata dadi a baki ba, wani sa'in ma abu in ta kalla bai mata za tai ta kalato amai tana ya mutsa fuska, duk daran duniya kuwa da zazzabi take kwana, Rashida taso ta fuskanci wani abu to amma ganin kamar wasilan na nuna mata lafiyarta lau yasa ta yi shiru da bakinta. **** Camas duniya sabuwa, ganin Wasila ta daina kiran wayarta ya sanya ta saki jikinta ta soma fito da kudi suka hada kai da wani babban dillali dake harkar filaye da gidaje cikin unguwani masu kyau da tsada, ya kaita wasu manya manyan filaye a unguwar rijiyar Zaki cikin masu kudi, ya nuna mata su, yace."Kinga idan kika siyi wannan filayen to ina me tabbatar miki da cewar shekara me zuwa kudinsu ya ninku kin mayar da kudinki kinci riba, mai kauri, yanzu idan kina bukatar siyan filayen zaki biya miliyan hudu duk biyun kowane guda daya miliyan biyu ne, kafin shekara guda nasan zaki siyar dasu gabadaya miliyan takwas kinga kin zama hajiya babbah." yana dariya yake maganar yana kuma kara tabbatar mata da maganarshi, jin uban kudin da zata ci riba akai yasa ko neman ragi bai ta ta amince tace"Suje ya dauko mata takardun filayen sai su wuce banki ta bashi kudin.....Jiki na rawa Usaini dillali yay gaba tabi bayansa **** As dai sarkin kulafuci da binbini bai hakura ba kusan kullum sai yazo gidan Wasila yayi ta magiya ta fito idan ta ga dama ta fita watarana kuwa haka zai karaci zamansa a mota ya tafi.......Yanzu ya daina so yayi lalata da ita so kawai yake ta amince masa ya aureta sabida jahlici kuma yake neman aure ba tare da ya bari tayi iddah ba, As din da ita Wasilan dik basu san abunda suke ba gwarama Wasilan zamu iya cewa bata sani ba tunda ba ilimin addini tayi cikakke ba shi kuwa As ya sani yake takewa yake zuwa zance...........Da dai yaga ta'ki bashi had'in kai sai kawai yace."Ya basu notice na wata biyu duk wani abu da suka san nasu ne to su kwashe su bar gidan idan ba haka ba to zaiyi musu tozarci da wulakanci tunda dai basu gaji mutunci ba, Uwani ta dinga bashi hakuri tana kwantar da kai, shi kuma ya dinga fad'a mata ba'kaken maganganu a fakaice! takaici ya sanya Wasila barin gurin, ta rasa yaushe Uwani za tayi hankali ta daina zubda mutuncinta saboda taulaci, sai wani rarrashin As din take kamar za tayi masa sujjada. **** Yau satin ta biyar da fitowa daga gidan Ahamdu rayuwa tayi musu tsanani sosai dan tuntuni kayan abincinsu sun kare sai dai kullum rashida ta fita bakin titi tayi musu cefane, watarana ma basa karyawa da safe da rana suke cin abinci suci da dare........Wasila ta rame tayi uban haske sosai dan duk wanda ya kalleta yaga mace mai yaron ciki nonowanta sunyi girma ainun! hannayenta da kafafunta sun dashe goshinta kullum cikin zuba kyalli yake yi........Uwani tayi masifar tashin hankalinta ta dinga zazzaginta tana fad'in "Wato ni zaki munafurta ko? to tun kafin na haifeki na san meye duniya ni zakiyi wa duniyanci ko!? to wallahi ko 'kinki ko kinso sai an zubar da wannan cikin dan ba zaki haifeshi ba." "Uwani nifa ba zan aikata sa'bo ba wannan cikin fa da ubanshi ba shege bane kawai ki kyaleni ki tayani addua Allah ya rabumu lafiya." Uwani tayi kwafa tace"Ashe dama kina sane kikayi cikin har zakice min babu abinda ya shiga tsakaninki da me cikin tom shikkenan gobe da wurwuri mu shirya dani daku muje can gidan wanda yayi miki cikin mu shaida masa abinda ke faruwa domin ba zamu bar garinan ba sai ya sani tunda kince baza a zubar ba to sai a sanar da me shi." Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon Uwanin tana nazarin maganarta, tana ganin kamar shawarar Uwani abar dubawa ce, hakan nada kyau, gwara kafin su bar garin yasan da zaman cikinsa a jikinta... Littafin na kudine.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [13/08, 6:37 pm] +234 906 803 2427: 'Yr Bngr Sys *54* Da tunanin maganar Uwani bacci ya d'auketa, aikuwa gari na waye wa Uwani ta azalzalesu kan suyi shirya da wuri suje gidan dan kar ya suje basu sameshi ba, jikinta a sanyaye tayi wanka ta shirya cikin daya daga cikin shaddodin da ya kawo mata lokacin tana gidanshi, vasilin akwai ta shafa a jikinta ta daura dankwalinta kana ta zura hijab ta fito palo, nan ta tarar dasu suna cin dumamen towon masara da rashida tayi musu jiya shine suka aje d'umame domin su karya dashi da safe Rashida tace "Anti Wasila gashi can na aje miki naki nasan ki da son dumame." Girgiza kanta tayi tace"Bana jin zan iya cin wani abu yanzu sai dai idan mun dawo." Uwani na sud'e yatsun hannunta tace"Wai meye tun jiya da nayi maganar zuwa gidanan mutumin nan kike wani salo salo ne? ko kina zargin xaice cikin ba nashi bane."? Girgixa kanta tayi tace"Nifa Uwani gani nakeyi da mun hakura da zuwa wallahi bana son wulakanci gidan akwai tsaro sosai bai zama lallai ma mu samu ganinshi ba, maganar ciki kuma ni bana jin wani tsoro ko shakka ciki nashi ne tunda yafi kowa sanin yanda ya sameni." Uwani tace"Ai yau komai tsaronsu sai sun bari mun shiga gidan ai dalili me 'karfi ne yake tafe damu." Rashida tace"Ai shine dan Allah anti Wasila ki kwantar da hankalinki." Sai da suka fito Babban titi a kasa kana suka suka samu a dai-dai ta sahu ta daukesu har zuwan Unguwar tudun yola. Tunda suka doshi bakin gate din gabanta ke gaduwa! tafiya suke fakam fakam! dama tun a bakin babban titin mai babur din ya sauke su, ya juya , sai suka shiga layin gidan da kafafunsu.......Suna shiga Estete din Su hango Garba a bakin gate din gidan, Gabanta ne ya fad'i sosai sai ta soma kiran innalilihi wa'ina ilaihi rajiun....To shima Garba shigowarsu estete din ya dauki hankalinsa dan da yana niyyar komawa cikin gidan sai yaja ya tsaya yana jiran isowarsu.......Ganin Wasila ya sanya ya shiga mamaki sosai suka gaisa Uwani tace"Munzo gurin mai gidane muna tafe da muhimiyyar magana dan haka ayi mana iso zuwa gurinshi." Garba yace."To babu laifi bai jima da shiga ciki ba ya dawo sallahar asubah bai kuma sanar damu zuwanku ba amma babu matsala bari na farar sanar dashi a waya tukkuna." Garba ya matsa gefe guda yana laluben numbar Ubangidan nashi.......Cikin sanyin jiki ta jingina jikinta jikin gate din gidan tana dan sauke numfashi gami da adduar Allah yasa idan ya fito ya gansu ya mutuntasu, a rayuwarta ta tsani wulakanci da tozarci! Garba yay ta traying din numbar Ahamdun ana ce masa wayar a kashe take, sai ya karaso inda suke da wayar a hannunsa yace."Kunga wayar tashi a kashe take wallahi mybe bayan shigarshi ya kasheta dan wani sa'in idan zai kwanta baya barinta a kunne saboda baya son damu idan yana bacci idan ba sauri kuke ba zaki iya jira nan da awa biyu ko uku ya tashi, ko kuma kuje ku dawo." Uwani tace"A'a bari dai mu jira d'in." Yace."Shikkenan." Har ya shiga gidan sai kuma suka bashi tausayi yace."Ku shigo ciki ku xauna cikin wancan rumafar." Wasila tace"Babu damuwa kawai zamu tafi ba sai mun shigo ba." Uwani ta harareta tana fad'in "Kina da tabbacin dawowa gidan ki sameshi domin ki shida masa abinda kike dauke dashi da har zakice ga zance ga magana tunda dai muna da tabbacin yana gidan bacci yake ai sai mu jirashi ya tashi." Ranta ne ya d'an baci! shin wai dole ne sai ya san tana da ciki ne, idan ta haihu ta kawo masa d'anshi ko 'yarshi kada ya kar'ba! Ina dalili kawai zasu zauna cikin maza sai kace wasu al'majirai! Tace"Tunda dai ku zaku zauna to ni zanyi gaba sai kun taho." Uwani tace"Ai sai kije me kunnan 'kashi wacce ba'a fada mata magana guda taji." Ba tace komai ba ta kad'a kanta ta wuce wani irin ba'kin ciki na sasakar zuciyarta, Allah yasa duk wannan abin da suke Garba baya gurin ya koma ciki amma ya bar musu karamar kofar a bude, sai suka shiga, can cikin rumfar suka nufa suka samu guri suka zauna zaman jiran fitowarshi........Wasila kam bakin titi ta nufa ta samu babur ya dauketa ya mai da ita gida, sam ba zataje ta zauna masa a gida ba ciki dai nashi ne komai za'ayi in ta haifu dole ya dauki abinshi. Bacci yake yi mara d'ad! sai mutsu mustu yake yana rungume pillow ya juya can ya juya nan! ya takure jikinsa guri guda yana sake matse pillow da cije bakinshi, da alama mafarki yake yi mafarkin kuma mara dad'i ga yanayin yanda yake ta juye juye yana ya mutse shimfidar gadon...........Ya jima cikin wannan yanayin kafin naga ya bude idanunsa da sauri bakinshi na motsi da alama salati yake......Idanunshi na kalla nagansu tamkar garwashin wuta saboda ja! kuma sun dan risina........Ya mike a hankali tare da zuro kafafunshi kasan gadon yana me dafe kanshi da hannunsa guda, kimanin minti goma ya dauka kafin naga ya mike tsaye! yana layi da tangad'i! idanunsa ya sauka gaban rigarshi, wani abu ne a mi'ke tsaye carr! yana nema ya huda rigar ya fito! Toilet naga ya nufa cikin wata iriyar tafiya kamar wani sabon d'an kaciya.............Wani mugun mafarki yay wanda yayi mugun daga mishi hankali da ya sanya duk wata sha'awarshi ta tashi cikin mafarkin burinshi kawai ya samu biyan bukata gami da abinda yake muradi, Tun bayan rabuwarshi da yarinyar tsayin sati biyar bai ta'ba mafarkinta ba sai yau da ya kwanta baccinsa na bayan sallahr asubah! Tazo mishi cikin 'kananun kaya masu fitar da tsairaci! wanda yay bala'in tashin hankalinsa ya kamato ya fara romancing dinta, salon da takeyi masa ne yayi masifar gigitashi, jikinsa na kyarma ya cire mata kayan jikinta shima ya cire nashi ya manneta sosai a jikinsa yana watsa da dukanin sassan jikinta tana taimaka masa sosai, yana jin dad'i.....Dai-dai lokacin data hau saman shi tana kokarin sanya jijiyarsa cikin ramin da yake kulafucin jinsa a ciki dai-dai lokacin da yake cikin shauki da zumud'in jinsa yana sukuwa da nin'kaya cikin 'koramar dake masifar d'imautar dashi! a dai dai lokacin mafarkin da yake ya sake shi, ya bude idanunsa a razane! yana jin wani irin motsi da jijiyarsa ke masa mararshi na bala'in kartawa tana murdawa!! tsabar sha'awa da bukatuwa. Da kyar jiki na kyarma yay wanka ya fito yana goge jikinsa har yanzu gabanshi na mike carr! duk yanda yaso ya kwanta yaki kwanciya, ya zauna gefan gadovda towel a hannunsa yana ya mutsa fuskarsa jaraba ce take cinshi ya rasa yanda zai yi da rayuwarshi wanda yay amma zufa yake yi......Da can bai saba da wannan fitinar ba sai da ya fara takalar yarinyar sannan yasan dad'in abin, abin mamaki! duk tsayin lokacin da bari a gidanshi, bai shiga cikin wannan mugun halin ba sai yau, to ko dan yana cikin bacin rai ne oho, yau dai tsananin sha'awa da bukatuwa ke damunsa kuma babu wacce yake so yaji yana ci irin yarinyar.....Gard'inta da dad'inta ya soma yi mishi ya yawo a 'kwalkwarshi nan ya shiga tunano suffofin jikinta mussaman manya manyan nonowanta da shaffan cikinta, ya dinga tuno ruwa da ni'imarta da taushin fatarta da gardin bakinta......Rigingine yayi yana kallon rufin dakin le'banshi na rawa yana kiran sunan Allah. Can bakin gate kuwa, Uwani da Rashida sun gaji da jira Garba nacan cikin 'Yan uwanshi Rashida taje tace masa dan Allah ya sake gwada kiran wayar tashi ko ya tashi daga baccin....Garba ya fito da wayarshi yana sake traying din numbar tashi......Wayar nata ringing bai d'auka ba dan bayan fitowarsa daga toilet duk ya kunna wayoyin ya ajesu kusa dashi, ya dinga kokarin daukar wayar ya kasa kawai sai ya share wayar yanaji tana ta ringing 'kararta har tsakar kanshi Garba Ya kalli Rashida data zuba mishi ido tana kallonsa yace."Kinga wayar na shiga amma bai dauka ba mybe yana wani uzirin ne bari zuwa anjima sai a sake kira." Rashida ta koma ta zauna kusa da Uwani jikinsu duk yay sanyi sun gaji da zaman jiran tsammani. Kimanin rabin awa da kiran wayar tashi Garba ya sake kira......Wannan karon ya d'aga wayar amma sam! garban baya jin abinda yake fad'a! Da kyar dai Garban yaji yana fad'in."Ko ma su waye ka shaida musu cewar bana jin dad'i gobe su dawo in, Allah y kaimu." Garba ya kashe wayar yana kallon rashida da jikinta yay bala'in sanyi.....Yace."Kuyi hakuri bai da lafiya amma yace ku dawo gobe.''Uwani taji kamar ta zundumawa Garba zagi! sai dai ta daure tana jan tsaki 'kasa-'kasa tace"Rashida muje." Gaba sukayi Garba ya bisu da kallo yana tunanin abinda ke faruwa har yanzu su basu san abinda ya faru tsakanin ogan nasu da matar tashi ba. Sai da suka fita babban titi kana suka tuna da cewar fa basu da ko kwabo dan Wasila tayi tafiyarta da jakarta 'bacin rai ya sanya dukaninsu basu tunanin hakan ba.....Babur din a dai-dai tasu su tsayar suka nemi alfarmar ya kaisu har kofar gida sai su bashi kudinshi....Mai babur ganin sun matsu yasa ya zuga musu kudi wai dubu daya da dari biyar zasu bayar....Uwani tace"Muje indai zaka kaimu gida zamu baka." Suka shiga suka zauna shi kuma yaja babur din yayi gaba. Ya jima yana mur'kukusu da kiran sunan Allah kafin ya samu sassauci a tare dashi ya dan mi'ka hannunshi a hankali ya dauki babbar wayarshi ya kunna! Ma'adanar hotunanshi ya bud'e hannunsa na kyarma ya lalube folder dake dauke da pictures dinsu da sukayi tare......Ya tsirawa fuskarta ido yana wata irin makyarkyata, wayar ya kai kan fuskarshi ya sumbaci dai-dai bakinta tana dariya lokacin da yake musu selpie ranar da zasu rabu!! Hakoranta reras! farare tas dasu, tsantsar kyawunta ya bayyana kanshi......Ya tsirawa kirjinta ido dake mayafin da tasa mai shara shara ne a ranar kuma d'inki mai saukakkiyar kafad'a ne ya dinga kallon brest dinta yana sauke ajiyar xuciya! Ji yake tamkar ya fasa wayar ya fito da ita ta biya mishi bukatarshi yarinya fitinanniya ta mai dashi fitinannan karfi da yaji, mugun da ya sani yake da shigarta rayuwarsa da yana zaune lafiyar Allah tazo ta mai dasho jarababbe mai kulafucun tsiya.......Wayar ya dora a kan kirjinsa ya rintse idanunnusa yana kiran sunan Allah. A hankali a hankali ya soma jin jijiyar tashi na kwanciya tana risina ya dinga murna sosai yana ajiyar zuciya.....mi'kewar da zaiyi yaji danshi a jikinshi matse matsin cinyarshi to mazi ne ko kuma me gabad'aya, shi dai ya sani! babu cikkaken kuzari a jikinsa yaje ya sake wanka ya fito yana dan jin sassauci a tare dashi. *** Wasila na kwance 'kasan ties taji shigowarsu, sai ta mike zaune tana dan ya mutse fuskarta....Uwani tace"Bani duba daya da dari biyar in sallami mai babur din can! kina sane kika tawo kika barmu ba kudin mota." Tace"Uwani duka fa kudin nan saura dubu goma sha biyar ciki zamuyi kudin mota kana abinda yay saura a kudin mu siya musu tsaraba kin san dai ba zamu kwashi jiki muje musu gari hannu rabbana ba." Uwani tace"Ni dai bani kudi bana son wata magana." Mikewa tayi taje ta dauko mata ta bata Uwani ta mikawa rashida da fad'in"Kai masa kudinshi ai yayi mana mutuncin ma." Rashida ta kar'bi kudin da sauri ta fita. Uwani ta zauna tana zauna kan kujera tana jan tsaki tare da cire mayafinta tace"Banta'ba ganin mara kirki da mutunci irin wannan mutumin nan ba wallahi, Duk wannan xaman da mukayi muna jiranshi 'karshe cewa yay ba zai fito ba sai dai mu dawo gobe saboda tsabar shi bashi da mutunci." Wasila ta dan bude idonta tana kallon mahaifiyarta ta ta mayar da idonta ta rufe tace"Sai fa dana fad'a miki kingani dai ai da idonki munyi asarar kudin mota a banxa." Uwani tace"Aikam gobe sai mun sake komawa dan baza fa mu tafi ba bai san da cewar kina tare da cikinsa ba. Cikin jin haushi tace"Wai dan Allah Uwani dole sai ya sani ? dik ranar da ya kamata ya sani zai sani ni bana son haka wallahi na fad'a miki wahala kawai zaki sha da asarar kudin mota ba samun ganinshi zakiyi ba dan mugun dan wulakanci ne in bai sa kansa yin abuba babu me sa shi yayi dan haka kawai ki hakura idan kuma kince dole sai kin sake zuwa to ni bani da kudin motar da zan baki." Uwani jikinta yay sanyi tace"Ai shikkenan tunda kin'ki cikin a jikinki yake kuma kece kike wahala dashi yau da lafiya gobe babu lafiya, saboda kulafuci kin'ki bari a zubar dashi! kuma kin'ki bari a sanar da meshi ni ina ganin idan an fad'a masa kina da ciki zaiyi wani abu akai dole ne ya bayar da kudin rainon ciki in da zaki masa kinga ai zasu taimaka mana ko." ''Uwani kyaleshi kawai dan Allah insha Allahu Allah bazai hana ni abinda zanci ba duk ranar dana haihu da kaina zan kai mishi d'anshi amma ba zamu dinga zuwa gidanshi muna zama cikin rana ba sai kace masu neman gafara." Uwani tace"Ai shikkenan tunda haka kika ce." Rashida ta shigo tana fad'in"Wallahi wata masifaffiyar yunwa nakeji sosai bari na dora mana taliya tafi sauri." Da sauri ta shiga kicin din....Uwani kuma ta mike ta nufi daki tana surutai....Yayin da Wasila ta rufe idanunta tana jin dama Allah bai hallice ba ta *Astagafirullah! sautari bawa yakan fad'i wannan kalmar a yayin da ya shiga cikin wani yanayi mara dad'i sai ya dinga ji dama ya mutu ko kuma dama Allah bai halliceshi ba, Wa'iyazubillahi! Ai cikakken mumini baya zama haka kawai ba tare da Allah ya jarrabeshi ba, mutukar kaga a'lamuran ka na tayi dai-dai a duniya to ka binciki kanka, Ubangiji naso ya jarrabi bawanshi shi kuma bawan ya kar'bi jarrabawar hannu biyu tare da ya'ki da tawakkali kan cewar Allah ne yayi masa ba wani ba, Cikar mutum shine yarda da kaddara mai kyau ko mara kyau! babu kyau dan Allah ya jarrabeka ka dinga jin kamar ko baya sonka ne A'a sone ya jawo haka dan ba kowa yakewa abinda yayi maka ba, idan ka kar'bi kaddara da jarrabawar da yayi maka shi kuma sai yayi maka tagomashi me kyau! Allah kasa mu dace* ******* Bayan sati uku al'amura da dama sun faru ta 'bangaran Ahamdu da Wasila ko wane bangare babu dad'i bangaran Ahamdu na cikin tsananin takura da masifaffiyar sha'awa dan har jiyya ya kwanta sai da Dr Nasir ya dorashi kan magani tukkuna ya dan samu sa'ida amma dai duk da haka duk daran duniya sai yayi hauka a dakinshi lokaci 'kankani ya zabge! kullum cikin 'bacin rai yake har khalifa yaso ya fahimci damuwa a tare dashi amma bai tambayeshi saboda ya soma zargin ko Allah ya soma ta'ba shi shima ai dama ba zai sha ba sai ya fuskanci kalubale tukkuna. 'Bangaran Wasila kuma Al'amura sun tsanantaa domin wani irin ciwon ciki takeyi sosai da sosai wanda ya sanya ta yanke shawarar zuwa babban asibitin murtala dake cikin gari a duba......Ana ya gobe zasu tafi Pataskum suka shirya ita da Rashida suka nufi asibitin murtala Muhammad da tsakiyar birin kano. Saboda yanayin yanda takejin rashin 'karfi a jikinta ya sanya ta nemi guri ta tsuguna Rashida tabi layin kar'bar kati ta kar'bo mata kana ta mike suka kama layin ganin likita.............Dr nayi mata kallon farko ya gane tana jin jiki saboda ya hango rashin wadataccen jini a tare da ita da damuwa da kuma rashin bacci! Ya tambayeta abinda ke damunta, nan ta shaida masa cikinta ne ke mata ciwo sosai sai kuma zazzabi da jiri! Dr yace."Kina da ciki ko."? Daga kanta tayi hawaye na kokarin zubo mata.....Rubuce rubuce yay jikin wata farar takardar yace."Maza kije kiyi scanning yanzu ki kawo min." Ta kar'ba ta mike a hankali ta fita.....Rashida na tsaye jikin wata bishiya ta hango fitowarta ta karasa tana tambayar ta tace"Rashida muje lamco de yace sai nayi scanning! Rashida taji kwallah na kokarin zubo mata a idonta tace"Anti Wasila Allah ya rabaki da wannan cikin lafiya yana baki wuya Wallahi." Girgiza kanta tayi ta sanya hannu ta d'auke hawayen da ya sauka kan kuncinta cikin zuciyarta tace"Ameen." suka kama hanya suka fita wajen asibitin inda gurin Scanning din yake.......Allah yaso ta sako dubu biyu da dari biyar cikin jakarta shiyasa komai yazo da sauki.....Suka shiga gurin suka kama layi....Mai siyar da pure water ya kawo mata keda hufu ta siya a take ta shanye uku ta bawa rashida daya tasha....Kamar jira ake tasha ruwan mararta ta shiga wani irin juyi tana murd'a mata sosai takeji zafi zufa! sai yanko mata takeyi, cije bakinta take tana kiran sunan Allah har layi yazo kanta ta mike da kyar ta shiga dakin scanning din da kyar ta hau gadon......tana cijewa da daurewa gami da kiran sunan Allah aka ga mai mata ta sauko, a hankali ta gyara zaninta ta karbi sakamakon ta fita tana cire 'kafafu da kyar......Rashida ta rike hannunta suka fita, a hankali a hankali suke tafiya har suka isa gate din shiga cikin asibitin.....dai-dai lokacin kafafunta suka ri'ke gabakid'aya ta kasa d'agasu! Salati ta soma sai ta tsugune! a gurin tana kiran sunan Allah, Rashida ta tsuguna kusa da ita tana kuka hannunta gam! gam! da nata fad'i take "Anti Wasila sannu tashi mu shiga ciki dan Allah kiyi hakuri kinga mutane na wucewa." Jirkitattun idanunta ta d'ago tana kallonta dasu gumi duk saman goshinta hannunta na rawa tace"Rashida mutuwa zanyiiiii ni ka d'ai nasan irin ciwon da nake ji a marata." Rashida ta goge hawayen fuskarta hankali a tashe ta soma waige waige a gurin tana neman wanda zai taimaka musu. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasp numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE*🎉🎉🎉 [14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *55* Wata matace ke 'kokarin shigowa asibitin hannunta rike da kati ta kusa yin tuntu'be da Wasila dake durkushe tana rike cikinta......Da sauri tace"A'a ya kuke zaune anan ko ba haihuwa za tayi ba."? Rashida ta goge hawaye tace"Ba haihuwa zatayi ba Daga scanning muke shine ta kasa tafiya cikinta ne ke ciwo." matar tace"To maza kamata muje wancan rumfar ai nan kan hanya ce."Rashida ta kama hannunta ta dora kafadarta matar ta riko kugunta suka mikar da ita tsaye.......Horn din da ake zabgawa ne ya sanya matar juyawa a fusace tace"Mutane babu uziri shikkenan dan kana cikin abin hawa na 'kasa bai da 'yanci sai ai ta zabga masa horn mtsss! ta karashe maganar tana tsaki hade da dan matsawa motar ta kunno kai cikin asibitin.........Hafsa dake draving ta dan juyo tana kallonsu, sai kawai idanunta suka saukan Wasila tana sunkuyar da kai hade da rintse idonta.....Da sauri ta samu guri tayi parking ta fito.....Zeey dake kusa da tace"Ki shiga ki fito ni inanan." Tace"Zeey fito dan Allah Wasila ce matar governor ina tsammanin bata da lafiya fito da sauri." Zeey tai saurin bude motar ta fito......Suna karasa inda suke Hafsa tace"Sannu Wasila baki da lafiya ne."? Jin muryar Hafsa yasa tayi gaggawar dago kanta tana kallonta, a hankali ta lumshe ido bakinta ya bushe 'kamas! ta d'aga mata kai.....Hankali a tashe Hafsa ta kalli Rashida dake share kwalla tace"Kunga likita? kuma meke damunta dan da kagani tana cikin matsala sosai." Rashida tace"Munga likita har yace taje tai scanning to daga dawowarmu ne sai kuma jikin ya rikice." Hafsa tace"Muga scanning din." Ta mika mata da sauri ta bude tana dubawa....Da sauri ta dago tana kallon wasilan Ciki! mamaki takeyi sosai lallai babu yanda Allah baya tsara lamarinshi......Tace"Zeey dan Allah ku kamo ta keda Kanwarta ta muje." Wayarta tayi gaggawar fito dashi ta soma kiran 'kawarta dake asibin mai suna Aliya likita ce ta mata, tace"Aliya ganin nan na shigo asibitin ku amma ina tare da mara lafiya." Aliya tace"Okey ku shigo ofis dinmu ina shirye shiryn tashi ma dan dai kawai kince zaki shigo ne." Tace''Gamunan." Har da ita gurin rirrike Wasilan suka mikar da ita tsaye.......Sai me suna fara tafiya jini ya soma zirarowa daga kafafunta.....Salati suka sa Rashida ta dinga kuka tana rirrike wasilan da fadin"Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un." A gaggauce Aliya ta karaso gurin, a take sukayi gaggawar dora wasila kan wani keke kai tsaye dakin 'yan 'bari Aliya tace a nufa da ita.....Hafsa Rashida hankalinsu yayi masifar tashi.....Hannu na kyarma ta kira wayar Khalifa ta shiga shaida masa halin da ake ciki....Lokacin ma yana hanyar zuwa gidan abokin nashi dan haka kawai sai ya juya akalar motarsho zuwa asibitin Kasancewar sun tari al'amarin da gaggawa ya sanya suka samu nasarar tsayar da zubar jinin dake barazana ga d'an tayin dake kwance a mahaifarta.....Sistar Aliya ta fito daga room din tana cire safar hannunta, ofis dinta ta nufa nan ta tarar dasu sunyi jugum! ta zauna tare da zare glass din idonta, Hafsa tace"Allah yasa dai cikin nan bai zube ba dan wallahi zubar jinin nan ya tsoratani." Sistar Aliya tace"Ciki nan daram! ammafa Allah ne kawai ya kare wallahi dan saura kadan ya zube dan dai munyi gaggawar tarar abun ne da tuni sai da labari." Hafsa da Rashida suka sauke ajiyar zuciya suna hamdala....Sistar Aliya tace" Ammafa samun kwanciyar hankali shine dole sai anyi mata daurin mahaifa domin mahaifarta na saurin budewa, ko tana aiki karfi ne."? Da sauri Rashida ta girgiza kanta, Sistar Aliya tace"Tun bayan sati uku da suka gabata mahaifarta ta bude sakamakon aiki ko duguwar tafiya mai tsayi Allah ne kawai ya tsare wannan cikin ni nayi mamaki wallahi." Hafsa tace"Naji dadi sosai kawata babu damuwa za'ayi komai indai cikin zai zauna ka kira Abban Afnan yanzu zan shigo. Aliya tace"Wai ya kuke da itane naga duk kin tashi hankalinki.'' Tace"Matar Abokin Abban Afnan ce muna shiri da ita sosai." Aliya tace"Okey naji kince Khalifa zai zo ina mijinta." Tayi saurin fad'in "Yayi tafiya ai kuma amanarta na hannun khalifa kinga dole ya kula da ita." Aliya tace"Dole kuwa tunda shi aka bawa amanarta....Scanning din take dubawa tana girgiza kanta tace" Gashi cikin yayi kwari wata uku da sati biyu." Hafsa ta shiga tunani, Eh tabbas hakan zata iya faruwa tunda satittikan cikin yayi dai-dai da lokacin auransu. Khalifa ne ya shigo cikin asibitin, ya kira wayar matarshi, ta fito daga ofis din Aliya ta masa jagora har dakin da Wasila ke kwance ita kadai ce ba a dakin babu kowa tayi zuru zuru da ita sai nadamar rayuwa takeyi lallai 'yaya mata na cikin hadarin rayuwa idan suna da ciki, wahalar da ta shiga dazu ta bata tsoro tayi tunanin ma mutuwa zatayi dan lokacin da taga jini ya soma zuba daga jikinta hankalinta yayi masifar tashi......Shigowar khalifa dakin ya sanya ta sunkuyar da kanta kwalla na taruwa a idonta....Khalifa ya karasa bakin gadon zuciyarsa duk ta karye tausayi kawai yaran suke bashi, A nutse sistar Aliya tayi mishi bayani tace" Tana jiran Dr Alfindiki ya fito zasu shiga da ita teatar room domin ayi mata aiki, bai wani tsaya dogon tunani ba ya sanya hannunshi ya kuma bada umarin a daure mata mahaifar duk domin samun zaman lafiyar cikin dake kokarin zubewa. Rashida ta tinga share hawaye Hafsa na rarrashinta, Ita kuwa Wasila idanunta bushewa sukayi 'kamas! hausawa sukace da wata wuyar ai gwara wata ita yanzu wace irin wahalace bata sha ba shiyasa sam bata damu ba tana ganin Allah ne mai rayawa da kashewa. Cikin nasara akayi mata aiki aka fitowa da ita dakin da suke sistar Aliya tace ta zauna ta huta tukkuna sai sai su tafi gida amma kuma ta kafa mata sharad'ai sosai kan dole ta kula da kanta babu aikace akaice da zurga zurga sannan kuma ta daina zama da yunwa ta kuma nemi magunguna na karin jini." Bayan fitar Aliya daga dakin, Khalifa ya dinga tausarta yana bata hakuri kana yace tunda haka ta kasance cewar tana da cikin Ahamdu to lallai zaiyi mishi bayani domin ya sani....Tace"Ni dai bana so ka fada mishi don Allah ka bari duk ranar da Allah ya saukeni lafiya sai ya sani amma bana so yanzu ya san inda ciki a tare dani.....Khalifa yace."Hujjarki zaki fada min da kike cewa bakya so ya sani? mutum da abinshi, ai ya zama dole ma ya sani idan sanadiyar cikin yasa ya mayar dake dakinki dama haka muke so." Tace"Bana son haka nafi so kowa Allah ya hadashi da dai-dai dashi dama kaddarar wannan cikin ne Allah ya hadani dashi duk sanda na haife shi kuma zai bashi abinshi." Khalifa ya girgiza kanshi yana kallon tsananin wauta da rashin wayo a tare da ita. Hafsa da kanta ta fita bakin asibiti ta shiga wani kanti da suke siyar da dogwayen riguna da hijab ta siyo mata riga kala biyu da hijab biyu sai pants da audiga.......Zeey sai jin haushi takeyi tana ganin duk 'yar uwar tata ta 'bata musu lokaci gurin wata shashashar da basu da hadi da ita taji zafi sosai dan ganin yanda Hafsan ke ta rawar jiki kan Wasilan.......Jikinta babu kwari suka fito daga dakin....Khalifa ya bude musu motarshi suka shiga, duk gabad'ayansu....Yaja motar suka fita daga asibitin Har cikin gidan ya shiga da motar, Uwani ta fito ta tsaya dama yini tayi cikin fargaba da tashin hankali ganin 'yayan nata sun fita tun safe amma yanzu gashi har karfe shida na yamma basu dawo ba dalili kenan da ya sanya hankalinta tashi.......Fitowar Wasila daga motar yasa ta fuskanci da akwai matsala, sai dai tayi kokarin kar'bar su khalifa hannu biyu suka shiga cikin gidan Khalifa ya shaida mata shi din abokin Ahamdu ne ya kuma shaida mata abinda ya faru da Wasilar shine dalilin da ya sanya ma suka dade basu dawo ba, Sai kawai ta tsinci kanta da yi masa godiya har muryarta na rawa, wato ita tanan sake da baki 'yarta zata mutu akan titi lallai akwai mutanan arziki a duniya.......Khalifa ya shaida mata abinda Dr Aliya tace dangane da ita Wasilan dole sai an kiyaye an kuma sa ido, har sai sanda cikin yayi kwari tukkuna....Uwani tace"Insha Allahu za'a kiyaye....Yace."Insha Allahu zan sanar da Abokina abinda ke faruwa mybe ma gobe mu shigo dashi ko da daddare nasan yaji labarin cikin nan zai bukaci sanin abinda ke faruwa....Uwani tace E hakan nada kyau sosai dan muma munyi wannan maganar kuma munje can gidan nashi domin mu shaida masa sai da bamu sami ganinsa haka muka dawo gida." Khalifa yace."In sha Allah zai zo da kafafunshi kar ku damu...Kudi ya basu kimanin dubu ashirin yace su rike a hannunsu tukkuna, kana ya mike Hafsa dw zeey ma suka mike suna musu sallama, Wasila da kyar ta mike tsaye domin rakasu, godiya kawai takeyi dan ta rasa ma da wace kalma za tayi amfani lallai yau taga ranar d'an adam Khalifa da matarshi nada hali irin na mutanan arziki. Tun a cikin mota Khalifa da Hafsa suke mamaki ikon Allah kenan! Hafsa tace"Shiyasa ba ba'a saurin yin saki komai 'bacin ran da mutum yake ciki kafin ya yanke hukunci ya samu nutsuwa, ko ni anan gurin naga wautar governor wallahi duk dai komai kaga ya faru da mutum kaddara ce amma dai rashin hakuri shike jawo wani abun, yarinya karama da ko 2years bata cika ba take fuskantar kalubale irin wannan Allah Abban Afnan da ba dan zuwana asibitin nan da sai da cikin nan ya zube in ba wani tsananin rabon ba." Khalifa yace."Tun yaushe nake nuna masa gaskiya ya'ki fahinta kin sanshi fa taurin kai gareshi sai abu ya kwabe yazo yana nadama ni wallahi na yarda da tuban yarinyar nan bana haufi a kanta kuma ina masa sha'awar ya mai da dakinta tunda dai har rabo ya shiga tsakaninsu.........Tace"Aikuwa dai amma ina jin idan yaji labarin tana da dauke da cikinsa zai sauko zai kuma so ya dawo da ita duk domin cikin jikinta." Khalifa da Hafsa har suka isa gida suna zancan Cikin wasila da yanda ta basu tausayi Zeey kam dama tun a hanya ta sauka tace zataje gidansu friend dinta sai suka sauketa ta samu abun hawa ranta a 'bace! sosai take kishin Wasila da ita da abinda ke cikinta. Duk rashin imani irin na Uwani sai da ta tausayawa 'yar tata ta dinga rarrashinta taci abinci tasha magani sai ta kwanta, Wasila ta dinga mamaki ashe Uwani dama nayi mata irin wannan son, taji kwalla ta taru a idonta, tana so ta faranta ran uwarta da 'yar uwarta amma babu hali Kudi suna suke magana, gashi kuma ita tayi al'kawarin barin harkar dake kawo mata kudin da suke jin dad'i. Bayan sallah isha'i Khalifa na shirin zuwa gidan Abokin nashi motar shi ta shigo gidan......bayan motar ta tsaya Garba yay gaggawar bude masa motar ya fito....Khalifa ya karasa gurinshi tare da mika masa hannu yana fad'in "Fitowar nan da nayi, nayi ta ne da niyar zuwa gidanka sai gaka kazo.'' Yace." Okey Allah yasa alkairi ne zai kawo ka." Khalifa yace."Idan kaji ana alkairi d'aya kenan muje ciki." Suka jera a tare suna tafiya domin shiga cikin gidan kai kana kallon yanda suke mu'amula kasan abokai ne masu tsananin zumunci da kaunar junansu. Littafin na kudi ne......! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *56* Hafsa ta gansu sun shigo tare sai ta saki fuskarta sosai tana dariya tace"Sannu da zuwa gwara da Allah bai sa ka bawa mijina wahala ba kazo dama bana so ya fita ya barni ni kaina a gida naji dadin zuwanka." Ya danji wani iri da jin maganar Hafsa!wato shine mara galihu kenan wanda bai da mata mai tattalin sa yana yawo da daddare babu me cewa dan me.''? Kan kujera ya zauna yana jan kafafun Afnan dake kwance kan kujerar tana kokarin yin barci, jin muryarshi yasa ta bude idonta a hankali ta shige jikinshi tana fadin "Dadyna yaushe kazo ina Aunty Amaryata."? Rungume ta yay yana shafa kanta yace." Baby Afnan iya rigima baki bacci ba."? Kai ta daga mishi tana lumshe idonta....Hafsa tace"Yanzu nan ta gama rigima ai ta gaji ta kwanta tana son yin bacci 'kiriniya da fitina a gurin Afnan sai a hankali." Dan hararata yay yace."Ke waye yasan abinda kikayi kina yarinya gwara nata me sauki ne." Hafsa tasa dariya tare da wucewa daining tana fad'in "Governor da Afnan kenan ai fada a shirya." Shima dariyar yake yana shafa kan Afanan din yana lallabata tayi bacci. Khalifa ya zauna kusa dashi yana me cire halar kanshi da fad'in"Yau na sha zurga zurga Wallahi da tun safe ban zauna ba." Yace."Shiyasa nayi ta tsammanin shigowarka naji shiru kasan dai maganar nan ba zata yiwu ta waya dole sai mun tattuna akai , Alhaji Danliti ya matsa min da kiran waya kan dole sai mun bashi rancen kudi har miliyan saba'in wai zai shigo da kaya, kudinshi sun yanke kasan sam bana son mu'amula dashi saboda bai da dad'in sha'ani." Khalifa yace."Mu aje maganar Alhji 'Danliti a gefe guda ni muhimiyyar magana ce nake tafe da ita." Ahamdu ya kalleshi a nutse yace."To ina sauraranka." Khalifa ya dan gyara zamanshi sosai ya mai da hankalin sa kan abokin nashi ya bude bakinsa a nutse yace."Shin kasan matarka da ka saki tana dauka da cikin ka har na tsayin watanni uku da sati biyu." Yaji wani irin shocking a jikinshi ya zubawa khalifa yana kallonshi yana so yayi mishi 'karin bayani. Khalifa ya gyara fuskarsa sosai alamun maganar da zaiyi mai muhimanci ce Yace."Wasila na da ciki kamar yanda kaji na fada maka da farko, Dazu ina kan hanya ta ta zuwa gidanka Hafsa ta kira ni a waya kan cewa inyi gaggawar zuwa babban asibitin murtala dake cikin gari ga abinda ke faruwa, dalili kenan da ya sanya kaji ni shiru banzo ba............Khalifa ya shiga warware masa abunda ya faru da Wasilan da irin sirad'in da ta tsallake dashi kanshi cikin jikinta da yake cikin wasiwasi da 'kila wa 'kala ya kuma tabbatar masa da cewar mutukar ana so cikin ya inganta a kuma haifeshi cikin salama da nutsuwa da kwanciyar hankali tilas yarinyar ta samu kulawa mai kyau sannan ne za'a samu dukanin abinda ake so." Tunda Khalifa yake maganar yake jin wani iri a jikinshi, ya shiga lissafin watannin cikin dai dai lokacin auransu ne dan a hasashen sa ma yana zargin haduwarsu da yarinyar ta farko ta same shi...........Jikinsa ne yayi sanyi sosai kafatanin hankalinsa ya karkata kan ingantuwar d'anshi da samun xaman lafiyarsa a cikin uwarshi, gabanshi ya dinga faduwa yana addua da godewa Allah da bai sa cikin ya zube a kan hanya ba! Ji yay wani irin gumi na keto masa, Khalifa ya lura abokin nashi ya shiga rud'u da tashin hankali sai ya dafa kafad'arshi a nutse yace."Yanzu wace shawara ka yanke dangane da yarinyar dashi babyn dake cikin cikinta." ? Ya dan kalli Khalifa cikin yanayi na damuwa yace."Nama rasa me zanyi wallahi Khalifa nagode kwarai da gaske Allah ya bar abota da zumunci mai amfani yanzu idan da babu kai mybe da tuni na rasa gudan jinina, bana haufi kan cikin yarinyar nan nawa ne Khalifa nasan lokacin da nayi abina." Khalifa yace."Haba babu komai wallahi ni da kai yanzu 'yan uwane mun wuce a kira mu abokai duk abinda nayi maka kaina nayi wa, ina tambayar ka matakin da zaka dauka dangane da yarinyar da abinda ke cikinta babu shakka dukaninsu suna bukatar kulawa mai kyau.......Yace."Khalifa kasan dai halina idan nayi magana kan abu ko kuma na yanke hukunci kan abu bana ta'ba barin abu daga baya in waiwayeshi, amma tunda haka ta kasance Zan sakata gida in killace ta sannan in hada mata komai na jin dadin rayuwa ta zauna ta cigaba da kula min da yaro na har sanda Allah zai sa ta haife mun abuna.....Idan ta haihu in taga zata shayar dashi ok idan taga bata da ra'ayin hakan zan nemi mai raino insha Allah amma bana ji sanadiyar wannan yaro ko yarinya na cigaba da zaman aure da ita. Khalifa bai so jin haka da gareshi ba amma bashi da magana dama kuma yayi al'kawari kancwa ya bar cewa dashi ya mai da yarinyar, yasan duk sanda ya gane mahimancin ta a gurinsa zai dawo yana neman shawararshi, Sai kawai yace."Shikkenan hakan yayi dan gaskiya na fahimci akwai matsatsi da rashin sukuni da rashin abinci mai kyau a tare da ita da Mahaifiyarta da yar uwarta ina ganin idan anyi hakan zasu samu sakewa sosai kai kuma zaka samu lada kuma dan Allah ko bayan ta haihu ka kar'bi d'anka ko 'yarka to ka bar musu gidan da komai na ciki su zauna sada'katuljariya zaka samu lada." Yace."Khalifa a yanzu yarinyar nan zan iya yi mata komai albarkacin gudan jinana da take dauke dashi kasan ni idan nayi kyauta bana waiwaye saboda haka bayan gida ma ni mai iya mallaka musu wani abun ne kar ka damu da wannan." Khalifa ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Hafsa dake karasowa inda suke......Ta zauna kusa da mijinta a hankali kai da ka gani kasan itama tana cikin damuwa, Wai shin Shi governor wane irin mutum ne? ace ayi ta abu d'aya haba ai yaci ace ya hakura ya dawo da yarinyar nan, ta lura kamar ma ya fiso yayi ta zama a haka babu aure da shekarunsa da komai shiyasa mutane ke masa kallon mara lafiya da sauransu. Irin abinda take ta fad'a kenan cikin ranta........Ya d'an kalli agogon hannunshi shifa da ba dan dare yaja ba da ya dauki khalifa sunje ya gano yarinyar nan ba wai dan ita zaije ba a'a dan abinda ke cikinta cikin fargaba yake sosai yana ganin kafin gari ya wace cikin zai iya zubewa...... Babu zato khalifa yaji yace."Tashi muje nagano yarinyar nan." Khalifa ya kalleshi cikin mamaki yace."Yanzu da daran nan dubi time fa sha d'aya shaura." Ya d'anja tsaki yana mutsika goshinsa yace."Gabad'aya hankalina ya kasa kwanciya Khalifa ina jin a jikina kafin safiya cikin nan na iya zubewa ko wani abu ya faru, nasan mutukar banje na ganota ba ba zan iya rintsawa ba." Khalifa ya dinga kallonshi yana jijjiga kai yace."Shin wai ita kake son gani ko kuma abinda take dauke dashi."? Da sauri yace."No ni abinda ke cikin cikinta nake son gani ba wai ita ba meye gamina da ita." Khalifa yayi wani murmushin takaici yace."To ina me tabbatar maka da cewar ko kaje yanzu wahalar banza xakayi dan nasan tayi bacci kuma ka'idar masu lalurar ciki ba'a tashinsu daga bacci, kuma kana maganar ba dan ita zakaje ba to shi cikin naka in kaje ganinsa zakayi ido da ido ko kuwa zaka ce ta d'aga maka riga ne ka gani."? Ya shiga kallon Khalifa yana me nazarin maganarshi, Ya akayi kwakwalwarshi ta toshe ne? shifa a tunaninsa idan yaje yace ta bud'e masa riga yaga d'anshi! sai kuma yanzu maganar Khalifa ta sanya ya hango kuskuransa, yanzu dai babu aure a tsakaninsa da yarinyar nan yasan ko yaje bashi da hurumin rike mata koda d'an tsaya ballanta yace ta bud'e masa riga yaga d'ansa Gumi ya shiga karyo masa ya ciro hankici yana gogewa ranshi sai 'kuna yake yi yarinyar nan tayi bala'in cutarsa yasan kuma yanzu shi da kwanciyar hankali har sai yaga d'anshi a hannunshi tukkuna Khalifa yace."Hakuri za kayi gobe idan Allah ya kaimu sai mu je da wuri ku gaisa kasan kuma ko kaje babu ruwanka da ita tunda ba muharramarka bace." Sai yaji kamar ya kwad'awa Khalifa mari da jin maganar da ya fad'a Yaja karamin tsaki yana me mikewa tsaye da fad'in "Allah ya kaimu goben zan shigo da wuri muje, kuma a goben nake son sauya musu gurin zama duk domin samun nutsuwa da kwanciyar hankalina inaji a jikina mahaifiyar yarinyar nan zata iya zubar min da ciki koda kuwa ita yarinyar bata so." Khalifa yace."Kai kake wannan hasashen amma a dazu munyi magana da mahaifitar yarinyar ta tabbatar min da cewar kwanaki sunzo har gida domin su shaida maka abinda ke faruwa basu sami ganinka ba kaga kuwa idan hakane to bata da hannu gurin zubewar cikin ka." Yayi shiru yana nazarin khalifan kafin ya kad'a kanshi yana fad'in"Koma dai menene ni bazan ta'ba aminta dasu ba tunda sun shani na warke Allah ya kaimu goben kawai." yana gama maganarshi ya nufi hanyar fita, Khalifan ya mike yabi bayanshi.....Hafsa kam dama tuntuni tayi shigewarta d'akin Governor bai ta'ba 'bata mata rai irin yau ba mutum sai kace fir'auna zuciya kullum babu kyau ace kayi ta ri'kon mutum a ranka. Yanda yaga dare haka yaga rana ya kwana yana juye juye da zumud'in son gari ya waye duk domin zuwa ganin gudan jininshi dake kwance cikin mahaifar Wasila......Asubar fari ya mike ya shiga toilet wanka ya soma yi kana ya dauro alwala ya fito ya shirya tsaf ya nufi masjid, ya kasance mutum na farko bayan liman da ya fara isa masalacin, sai ya zauna cikin nutsuwa ya fara jan carbi kafin liman ya tada sallah. Misalin 'karfe takwas sun shirya tsaf! sun fito da jakkunansu, da duk abinda suka san nasu ne a cikin gidan, suka fito tare Uwani da Rashida suke jan akwatinan kayansu yayin da Wasila ke bin bayansu cikin sanyin jikinta, wani irin yanayi mara dad'i takeji a cikin zuciyarta.....Bakin gate suka nufa, Wasila ta fito da keys din gidan ta mi'kawa d'aya daga cikin masu gadi tace"Idan As yazo su bashi. masu gadin gidan kamar zasuyi magana sai kuma sukaja bakinsu sukayi shiru suna kallonsu suka fice daga gidan da akwatinan kayansu.......A jigaje ta 'karisa bakin babban titi dan wannan tafiyar da sukayi ya sanya ta haki! dan har sai da suka samu guri suka zauna ta huta tukkuna kafin su cigaba da tafiya.......Babur din a dai-dai sahu suka samu ya daukeshi zuwa tashar kabuga. "Wai wannan wane irin wulakanci ne ? na shigo gidanka tun safe ka shanya ni a palo sai kace yaronka ina ta fama zaman jiranka kai kana can kanayin abinda ya dameka, idan ba zaka fito ba zanyi tafiyata ba wai ban san gidan bane."!!! Ahamdu yake waya da khalifa lokacin da yake kai komo a tsakiyar palon nashi......Khalifa ya fito daga bedroom d'insu kunnanshi ma'kale da waya yayin da Hafsa ke biye da bayansa hannunta rike da turare da kuma hularshi tana gyarawa. Ahamadu ya dinga watsa musu harara kamar idonsa zai fad'o 'kas! Yace." Ga d'an iska kun bari yana muku jiran gida kun shigo ciki wai me yasa bakwa gajiya da abu guda ne."!! A zafafe yake maganar......Hafaa ta gumtse dariya kanta a 'kas tana sanyawa mijin nata links din hannunshi tace"Allah ya huce zuciyar governor ba wai abinda kake tunani muke ba, lokacin da kazo gidan bamu dad'e da tashi ba shiyasa." Ya maka mata harara yace."Ke kika san wannan ni a gurina karfe shida na safe ba safiya bace lokacin duk wani me himma yake tashi domin gudanar da harkokinsa na yau da gobe ke kuma a lokacin kike sake ma'kalewa wai ke gaki wacce ta iya soyayya." Khalifa yace."Wai meye laifina nan ne? tayi fa 'kokari sosai kawai kazo mata gida da asuba kuma kace sai kaga yanda kake so ba zai yuwu ba lokacin da kazo ma ni ko tashi banyi ba wayarka ce ta tasheni." Yace." Dan Allah ni muje dubi time kun 'batawa mutane lokaci mtsss!. Duk suka bishi da kallo cikin mamaki masifa yake musu sai kace sune suka sashi ya aikata abinda ya aikata shine kuma zai zo ya d'aga musu hankali basuji ba basu gani ba... A mota ma sai mita yakewa Khalifa, wanda tun baya ramawa har ya shiga ramawa ya dinga yi masa shagu'be duk domin ya fahimci cewar shifa d'an taimako dan haka ba zai zo ya dinga d'aga mishi hankali ba idan yana so ya cigaba da samun nutsuwa da kwanciyar hankali to yayi gaggawar dawo da iyalinshi gabansa, To wannan magana da khalifa yayi itace ta kashe masa baki yayi shiru sai dai jefe jefi yakan ja tsaki ya duba agogon dake daure a hannunsa. Dai-dai gate din gidan khalifa yay parking ya shiga horn da sauri daya da sauri mai gadi ya bude gate din dan duk sun dauka As ne sai bayan motar ta shiga cikin gidan ne suka gane cewar bashi bane..........Shine ya fara fitowa kafin Khalifan ya fito.......Dake masu gadin biyu ne daya sai ya tsaya bakin gate din daya kuma ya nufi in da suke....Gaishesu ya shiga yi yana so yayi magana amma be san me zaice ba yaso dai ya shaida fuskokinsu mussaman Khalifa da shine yayi zuwan karshe cikin gidan.......Shine ya fara yin gaba da nufin shiga cikin gidan sosai Kafin Khalifa yace."Ka d'an dakata na kira wayarsu naji ko." Dan tsayawa yayi yana ya mutsa fuska, Khalifa ya kira numbar wayar Rashida dan itace me waya kuma numbar ta ya kar'ba, Wayar na hannunta tayi saurin d'agawa tana kara wayar a kunnanta lokacin suna tsakiyar tasha suna ciku cikun hawa mota........Tayi ta fadin "hello " hello "hello network da hayaniya sun hanata jin muryar Khalifa inda shi kuma nashi 'bangaran yana jin muryar ta rad'au! sai dai dik inda take tana cikin hayaniyar jama'a da ababen hawa! Fad'i yake " Rashida kina jina? kina jina." Da karshe ma sai wayar ta tsinke yay gaggwar cirota daga kunnanshi yana dubawa.....Mai gadin dake tsaye yace."Yallabai mutanan gidan fa basa nan dan tun sassafe suka fita da akwatinan kayansu da alama sunyi balaguro ne."! Ya wani juyo a sukwane! yana kallon gate man d'in bakinsa na motsi......Mai gadin yace."Amma dai ina kyautata zaton yanzu basu isa tasha ba ko sun isa baici ace sun tashi ba tunda kasan dole kafin mota ta tashi sai tayi lodi sai dai kuma muma bamu san inda suka nufa ba." Jikinsa ya soma wani irin rawa! yana kyarma! kafafunsa suka shiga kyarma Cikin tsawa da d'aga mirya Yace ."Wane irin wawanta ne wannan!? Wane irin sakarci da hauka ne yasa zaku barsu su fita! meye amfaninku a gidan!? waye ya basu izinin fita da jakkunan kayansu!? ina kuma suka tafi? Ina zasuje! min da gudan jinana? sai muryarshi ta shiga rawa yana wa tsawa masu gadin mugun kallo babu marasa tunani da kwakwalwa kamarsu da har suka barsu suka fita daga gidan sun riga sun cutar dashi mutukar sukayi sanadiyar zubewar cikinsa dama tun jiya yake ji ajikinsa akwai abinda zai faru, Ya kalli khalifa yana tsuma!!! Yace." Ko ina suka nufa sai na lalubosu! dan basu isa su yanke min wannan hukuncin ba, kawai ka shiga mota muje." Yana maganar ne a sanda yake nufar motar tasu cikin gaggawa da kuma saurin gaske ya bude motar ya shiga khalifan dake tsaye cikin mamaki! ya rasa ma tunanin da zaiyi ashe wasila bata da hankali dama? tanajin abinda likita tace dangane da lafiyarta da babynta amma zata dauki jiki suyi tafiya mai nisa cikin mota mai kwajab kwagab! babu sakarkaru sai masu gadin gidan da suka barsu suka fita daga gidan........Da saurin gaske yabi bayan abokin nashi ya shiga motar da gaggawa ya mayar da murfin ya rufe Ahamdun yaja motar da karfin gaske, ya nufi kofar fita daga gidan cikin sauri wanda yake bakin gate din ya matsa gefe guda yana zazzare idonsa. Littafin na kudi ne......! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap Numbar *07084653262*[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *57* Zaman motar ne ya isheta ta dinga ya mutse fuskarta tana dan tsartar da yawu ta tagar motar kanta ne ke sarawa tana jin wani irin amai na taso mata, hayaniya ta mutane duk ta cika mata kunne ga warin fetur da tsamin hammatar wata mata dake kusa da ita d'aga rigarta ta fito da nono ko kunya ba taji tana shayar da yaronta alhalin motar da akwai maza a cikinta, haushin matar ya sanya ta dinga dauke kanta tana jan tsaki wasu matan sam babu kintsi da kamun kai cikin motar haya mai dauke da mazan da ba muharraman ta ta fito da nono kowa nagani gashi da ta motsa warin hammatar ta zai buga......Mutum biyu kacal ake jira motar ta tashi Wasila duk ta kosa su tafi ko ta sha'ki iska mai dad'i bayan warin hammatar matar ma mazan dake ciki wasun sy wari sukeyi abinka da wanda rana ta daka....Uwani da rashida kam hira sukeyi suna cin awara da suka siya kafin su shiga motar...Kira ya shigo wayar rashida dake kan cinyarta. Da sauri ta kalli Wasila dake zura kanta tagar motar tana shakar iska tace"Anti Wasila kinga Khalifanan ya sake kira." Tace"Ki daga mana to." Rashida ta d'aga wayar tare da fad'in "Hello." Khalifa dake driving yay sauri mika mishi wayar ya kar'ba da sauri yana kokarin kara wayar a kunnensa ta fad'i 'kasan site sakamakon rawar da hannunsa yake yi....Kasancewar wayar ta bugu da karfi yasa ta mutu ya dauko da sauri ya kunna ta bude, ya lalubi numbar yana sake kira, A dai-dai lokacin ne kuma wasu matasa suka shigo motar direban motar ya Umarci rashida ta gyara sosai domin su samu gurin zama garin gyarawa wayar dake cinyarta ta fad'i kasan motar ba tare da ta sani ba....Aikuwa shi wanda zai zauna kusa da ita ya sanya hannunsa ya dafe ta, a take yay dubarar cire sim din lokacin da Rashidan ta juya suna magana da Wasila ya jefa wayar karkashin kayanshi, Rashida matsatsi da xafin mota ya sanya ta manta da wayarta burinta kawai su tashi saboda zafin ya isa.....Aikuwa sai da direba ya cika motarsa tsaf sannan ya shiga ya zauna maxauninsa ya tashi motar suka fita daga cikin tashar suka dauki hanya Abin kamar al'mara kiran wayar yake ana ce masa a kashe take, ya kira ya kai sau ashirin maganar dai daya ce wayar a kashe take! Ya d'ago kanshi yana wata irin zufa bakinsa na rawa yace."Khalifa wai meke faruwa ne? Wayar nan fa ta'ki shiga kana ji da kunnanka a kashe take Why! Wad'annan yaran naso su sanya zuciyata ta buga!!!!!!! Khalifa tsorona Allah tsorona Annabi kar cikin nan ya zube, ko a samu wata matsalar nasa raina akanshi."Ya 'kareshe maganar cikin rauni da sarewa da al'amarin. Sosai ya bawa Khalifa tausayi yace."Ni ina tunanin network ne matsalar Amma kar ka damu abokina insha Allah cikin nan ba zai samu matsala ba muje tashar kabuga insha Allah xamu samesu idan ma motarsu ta tashi ai mun san inda suka nufa kai tsaye sai mu wuce can garkon ni da kaina zanyi wa mai allo bayanin komai." Hularshi ya cire ya ciro hankici ya goge fuskarshi da saman kanshi, Yana jin wata irin fargaba na kamashi yanzu da wane ido zai kalli mai allo to me ma zaice masa idan sunje? Yace"Khalifa bani da wani bayani da zan iya yiwa mutumin nan saboda ina jin kunya wallahi in ce masa saboda d'ana ko 'yata dake cin Wasilan zan dauketa kasan da akwai nauyi." Khalifa yace."Kar ka damu zanyi mishi bayani." Ya shiga girgiza kanshi yana fad'in "Kamar nasan abinda zai faru shiyasa jiya nace maka muje inda suke da yanzu duk hakan bata faru." Khalifa yace."Ni nayi mamaki wallahi saboda jiya lafiyar Allah muka rabu dasu ko da wasa basu shaida min cewar zasu tafi wani gurin ba amma basu kyauta ba wallahi kuma Wasila tayi wautar gaske." Girgixa kanshi kawai yake yana adduar Allah yasa su samesu a tasha don shi kam yana bala'in jin kunyar had'a ido da mai allo. Khalifa ne kawai ya iya fitowa daga motar bayan shigarsu tashar ya kutsa cikin mutane direbobin motoci yana dube duben motocin mutane, ko kusa ko alama bai hango koda kyallin mayafin wata daga cikinsu ba, haka ya gaji ya nufi inda motar su ke fake.....Shi kuwa uban gayyar tamkar wani zautacce ko kuma mara kunne yana ri'ke da waya a hannunshi sai kiran numbar Rashida yake tamkar mai kunnan 'kashi ko kuma kurma yana jin abinda matar nan ke fad'a masa cewar wayar a kashe take amma ya kasa daina kiran wayar.......Ganin Khalifa ya doso motar tasu cikin sanyi jiki ya sanya shi rarraba ido yana jiran karasowarsa... Khalifa yace."Babu fa alamun yaran nan cikin tashar nan kawai shiga mota muje." Jiki a mace ya bud'e mota ya shiga duk yayi wani laushi kamar mara lafiya....Khalifa yaja motar suka fita daga tashar duk rayukansu babu dad'i.......Sai da suka hau kwalta sosai kana ya sauke numfashi yana huci! yace."Khalifa Allah banta'ba ganin sukuwar uwa irin uwar wad'annan yaran ba, ni yanzu ma ita nake jin haushi wallahi." Khalifa yace."Gaskiya tayi wauta itama data d'auki yarinyar nan da wannan lalurar suka dauki hanya bayan sai da na fad'a mata dokar da likita ta kafa kan 'yar tata shiyasa wallahi mace komai shekarunta watarana ta tafka maka wani abun haushin sai kaji kamar ka d'ora hannunka akanka. Yace."Nifa babu ruwana Allah cikina ya samu wata matsala sai na dauki mataki kanta da ita da uwar tata." Khalifa yace."Ai kaji irinta wai kai me yasa kake hakane? Matar nan fa ta tabbatar min da cewar sunzo har gidanka da maganar cikin basu samu damar ganinka ba suka hakura suka koma kan me yasa za kaga laifinta anan bayan tayi kokarin ganin an fita hakkina." Tsaki! yay yaja bakinsa yayi shiru yana muzurai! da ya tuno wani abu sai gabanshi ya fad'i! gaskiya yana bala'in son cikin nan nashi a yanzu ji yake zai iya hakura da komai na rayuwa mutukar cikinsa zai tsira. Tafiya suke mota na gwajab gwajab yayinda ciwon ciki da mara ya tsananta a gareta ta! ta dinga sunkuyar da kanta tana zufa da kiran sunan Allah gumi ko ta ina d'iga yake a jikinta, tsabar yanda take jin jiki sunan Allah kawai take kira tana jin wani irin imani na ziryartar ta anya kuwa wannan cikin bashi ne ajalinta ba? abinda take fad'a kenan cikin zuciyarta. Sun isa garin Garko Lafiya sai da kuma lokacin mai allo ya jima da fita tsangaya, Tanimu ne yay musu jagora har makarantar tashi.....Mai allo na tsakiyar al'majiransa ya hango zuwansu sai ya mike a nutse yana fara'a yana musu barka da zuwa......Cikin wata rumfar kwano da babu kowa a jiki suka nufa. Ma allo da kanshi ya karkade musu tabarma suka zauna sai aka shiga gaishe gaishe, Ahamdu sai sunkuyar da kanshi yake duk kunya ta dabaibayeshi sai yanzu yake jin kunyar dattajon yaga shi kuwa sai fara'a yake yana tambayarsa gida da harkokin yau da kullum. Khalifa yace."Alhamudllhi malam komai na tafiya yanda akeso sai da aita tayamu da addua." Mai allo yace."Addua munanan munayi har sai da numfashin mu ya dauke." Khalifa ya ja gwaron numfashi kafin ya gyara zamanshi a nutse yace."Allah shi gafarta malam dama mun biyo sahun yaran nan ne wato ina nufin Wasila da 'kanwarta da kuma mahaifiyarsu, domin muji shin sun iso lafiya! sannan kuma muna da tabbacin cewa nan suka nufo dalili basu da wani gurin in ba nan d'in ba, Allah shi gafarta malam babu maganar rufe rufe cikin maganar nan Yarinyar nan Wasila na dauke da ciki har na tsayin watanni uku da satika kuma akwai matsala mai girma tattare da ita da d'an dake jikinta wannan shine babban dalilin ma da ya sanya shi Abokin nawa yace."Lallai ilallah sai munzo domin mu tabbar da zuwan nasu cikin 'koshin lafiya." Mai allo ya dinga kallon Khalifa cikin mamaki da kad'uwa ya d'an gyara zamanshi kafin yace."To Idan na fahimci inda maganarka ta dosa anan shine kana so ka sanar dani cewar kun biyo sahun su Wasila domin kuna tunani ko nan suka zo kamar yanda ka fad'a hakane ko? Khalifa yace."Hake Malam." Mai allo yace."To a gaskiya ni dai har na fito daga gida banga zuwansu amma ban sani ba ko bayan na fito suka iso bari nasa yaro yaje ya duba a gida." Ya mike ya fita daga inda suke. Ahamdu ya kalli Khalifa cikin sarewa da tsananin damuwa yace."Anya Khalifa anya yaran nan suna nan kuwa? jikina na bani ba nan suka zo ba." Khalifa yace."Ka dai bari tukkuna mybe bayan ya fito daga gidan suka sauka garin kamar yanda ya fad'a d'in in banda abinka idan ba nan suka zo ina zasuje da yafi nan d'in." Yay shiru yana jin wata irin zufa na karyo masa, mikewa yay ya fito daga rumfar kwanon ya kama kallon hanya sai kace wani zautacce ga rana sai kwalle masa ido take. **** Misalin 'Karfe biyu da rabi na rana suka sauka garin Fataskum, bayan sun sauka daga mota Uwani ta dinga rarraba ido tana dube dube hanya dan garin gabad'aya ya sauya mata yau kusan shekaru goma sha biyu da rabonta da garin, tin tana goyon Rashida lokacin Yahuza na dan da mutuwa tunda tayi wannan zuwan bata sake waiwayar garin ba, dama mutum hud'u ne suka rage musu a dangi Babban yayansu mahaifiyarta da suke kira da Kawu Madu sai Mai binshi Kawu Isa sai kuma Iya mai waina da Tabawa dama su biyar iyayensu suka haifa mahaifiyarta itace ta uku ita ke bin Kawu Isa sai Iya mai waina sai kuma Tabawa! Mahaifiyarta itace kawai tayi aure a wani gari, amma dukaninsu cikin garin Fatskum suke tare da iyalinsu mutukar sun fita daka garin to sunje wani garin ziyara.....Tun bayan rasuwar mahaifiyar Uwani Kawu yaso daukarta domin su dinga kallonta a matsayin 'yar uwarsu, mahaifinta ya'ki lamince masa haka suka hakura suka bar mishi 'yarshi, gashi bashi da cikakkiyar lafiya shima a lokacin ya hana a tafi da itane domin ya dinga kallonta tana d'ebe masa kewar mahaifiyarta.......Sai da cutar ajali ta kamashi ne 'kaninshi ya daukeshi ya kaishi gidanshi dake akwai shago a wajen gidan nan ya ajeshi yake kula dashi, to shine fa tun daga lokacin Uwani ta soma shan wahalar rayuwa gidan Kawun nata har mahaifinta ya kwanta dama, a lokacin ta 'kara shiga tsaka mai wuya ga wuya ga maraici ga tsananin azabah! Saboda zalinci irin na Kawun ya siyar mata da gidan da ya zama gadonta ya sanya kudin a aljihunsa ya cinye matansa na zugashi da fad'in Ai idan yaci Allah ba zai tuhume shi ba tunda dai shima yana ciyar da ita...........Sai da sukayi aure da Ayuba ya jagorance da kanshi sukaje can Fatsukum din dangin mahaifiyarta da kwatance, to tun daga sannan ta gane hanya........Saboda matsatsi da talauci da kuma rashin kudin mota ya sanya bata zuwa garin a kai a kai, sai ta dauki shekaru masu yawa kafin taje to wannan karon dai shekarun data dauka ba taje ba sun fi na baya.......Da tambaya suka iske gidan Kawu Madu dake shi d'in ba 'boyayyen mutum bane a garin yasa basu sha wahala ba, Suna zaune kan katuwar tabarma shida abokanansa gabansu katon farantin silba ne jere da kwanuka, da jug jug na ruwa da alama abinci suke shirin ci ya hangosu, Sai ya shiga wasiwasi da tunani to sai da suka iso inda suke ya tabbatar da cewa su d'in ne Yace."Uwani ko ba ita bace."? Tace."Nice Kawu."! Sai ya washe bakinsa yana fad'in "Kece kike tafe da ranar nan babu shakka yau an tuna damu kenan gaki ga zuriarki lallai yau patskum nada manya 'baki sannuku da zuwa." Mi'kewa yay yana 'kwalawa yaran dake wasan langa langa a 'kofar gidanshi kira.....Suka rugu a guje yace."Maza ku kwashi kayan nan ku shida dasu gida.....Yaran suka dinga ihu! suna fad'in "Yeeee! munyi 'baki daga birni da gudu suka runtuma cikin gidan suna jan akwatinan kayan nasu **** Can ya hango yaron da aka tura gidan ya fito daga wata hanya yaji tamkar yaje ya tareshi ya tambayeshi, sai dai kawai ya daure ya bi yaron da kallo har ya isa inda mai allo yake ya tsuguna yana masa magana." mai allo ya Umarceshi da ya koma gurin zamanshi kana ya mike daga kan kujerarshi Ya nufo inda yake tsaye babu yabo babu fallasa a tare dashi, tun kafin ya karasa inda Ahamdun yake ya hango damuwa da tashin hankali a tare dashi, sosai ya shiga mamaki yana tunanin to bayan rabuwarsu ya mayar da ita ne har ta samu cikin ko kuma bayan ta fito daga gidan cikin ya bayyana ? babu me bashi amsa sai su ya sauke ajiyar zuciya lokacin da ya karasa inda yake a nutse yace."Alhaji mu shiga ciki sai muyi maganar." Ga yanayin yanda mai allo ke masa magana yasa ya fahimci akwai damuwa, jikinsa babu kuzari ya juya yana tafiya me allo ya bi bayanshi. Mai allo ya zauna kan tabarma yana kallon Ahamdu A nutse ya soma magana kamar haka "Yau shekaru takwas kenan rabon da Wasila da 'yar uwarta Rashida su tako 'kafarsu garinan! shiyasa nayi mamaki mutuka! a lokacin da kuka zo min da wannan maganar, amma kuma banyi muku musu ba saboda nasan hakan zata iya kasancewa tunda muma kullum cikin tunanin zuwansu muke nasan duk tsiya yarinyar bata da wasu iyaye sai mu, kuma nasan dole watarana zata kawo kanta inda muke duk kuwa da tsananin 'kiyayyar da suke mana ita da 'yar uwarta......Ni da 'Yan uwana da sauran dangi kullum cikin saurare muke da kallon hanya muna jiran tsammanin zuwansu garinan, tun bayan rabuwar auranka da ita muka yanke shawara kancewa mun dauke hannunmu da kansu gabakid'aya wanda har 'Dan uwana Habibu da ya fusata yace. Duk ranar da suka shigo garinan to sai ya koresu ni ne na hanashi nace mutukar sunzo inda muke to zamu kar'be su hannu biyu amma idan basu nemi in da muke ba to zamu kyalesu da halinsu da kuma mahaifiyarsu, to a gaskiya ni nafi gazgata zaton cewar Yaran nan sun bi bayan mahaifiyarsu can garinsu." Mai allo ya 'karashe maganarshi yana so ya tabbatar musu da gaskiyar lamari......Khalifa ne kawai ya iya magana Yace. "Allah shi gafarta malam ko zamu iya sanin garin su mahaifiyar tasu."? Mai allo yayi shiru yana d'an tunani kafin yace." Wallahi sunan garin ya kwanta min a raina, tun da kasan can d'in ba nan ne inda cibiyar mahaifinta yake ba, shi kanshi 'kanina Yahuza a hannun Kawunta ya aureta amma dai na ta'ba ji sau d'aya 'kanin nawa ya ambaci sunan garin har yace watarana zai daukeni ya kaini mu gaisa da danginta to kuma sai Allah ya dauki abinshi. Khalifa da gogan naku bakinsu ya mutu murus! Saboda dukaninsu sun rasa tudun dafawa sun ma rasa wane tunani zasuyi shin yanzu ina zasu samu yaran nan? Su dun tunaninsu babu inda suka dashi sai nan dan suna tunanin itama Uwanin a nan take ashe ba haka bane! Gashi gurin wanda suke tunanin samun cikkaken bayani shima yace bai ma sannan sunan garin da suka nufa ba........Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys *58* Cike da farin ciki da walwala ya shiga gidan nashi yana kwalawa matarshi kira..........Kuluwa ta fito daga wani guri wanda alamu suka nuna cewar madafi ne (khicin) hannunta da wata katuwar mara da alama kwasar towo take, tace"Malam ganin nan Allah yasa lafiya irin wannan kira hak.....Kafin ta rufe bakinta sai idanunta ya sauka kansu Uwani da 'yayanta, lokacin 'kan'kani ta kirne fuska tana fad'in "A'a yau kuma Uwani ce a garin."? Uwani dasu Wasila duk sunga sauyin fuska a tare da ita, lokacin da take maganar da alama dai batayi maraba da zuwan su garin ba.......Kawu Madu yana washe hakoransa yace." Wallahi kau nima nayi mamaki sosai dan baki ji dadin da nakeji ba, abinci zamuci dasu malam tsalha na taso domun in shigo dasu gidan." Kuluwa tace"To sannunku da zuwa ku shigo ciki." Kawu Madu yace."Uwani ku shiga ciki a baku abinci ku huta ai da alama ma kun kwaso rana." Uwani tace"Aikuwa wallahi munsha zaman mota da gajiya." Kawu Madu ya juya ya fita yana fad'in "Bari nasa Ayuba yaje can cikin kasuwa ya siyo muku ruwan sanyi." Uwani da Rashida suka shiga daukan jakkunansu dake yashe a tsakar gidan suka nufi dakin Kuluwa, suna shiga katuwar rumfa ce sai dai babu shinfida a cikinta sai guntattakin tabarmi da ledoji ko ina kaca kaci da kwari ka 'kananin kyankyasai ga wani uban 'kuda da yake tashi a rumfar da wani kafirin zarnin fitsarin yara......Tun lokacin da suka shiga rumfar Wasila ke yatsine ya tsinen fuska zuciya sai masifar tashi takeyi aikuwa kafin tayi wani yun'kuri amai ya kece mata! a guje! tayi waje ta nemi bakin rariya ta tsuguna ta dinga kelayashi tana kwallah......Rashida ce tsaye a kanta tana mata sannu duk ta shiga damuwa. Bayan ta gama aman ta bata ruwa ta wanke bakinta da fuskarta kana ta mike jiri na d'ibarta......Rashida ta rike hannunta wai su koma cikin d'akin girgiza kanta tayi da kyar tace"Rashida rabu dani don Allah zuciya tashi takeyi idan na koma gurin nan zan iya yin wani aman." Aikuwa karaf a kunnan Kuluwa ta rike baki tana fad'in "Ke ja'ira yarinyar me kike nufi? daga zuwa zaki fara yiwa mutane sanabe da iyayi kina nufin kazama ce ni kome." Rashida tayi saurin girgiza kanta tana fad'in "Ba haka take nufi ba baba." Kuluwa tace"To me take nufi da har zata shiga dakina ta rugu waje da gudu tana kwara amai." Rashida tace "bata da lafiya ne dama tun a mota cikin ta ke ciwo." Kuluwa ta girgiza kanta tana fad'in "Maji ma gani dai idan tusa zata hura wuta, kome kuke tafe dashi dai-dai nake daku to kaji."! Tana gama maganar ta ta shige madafi domin cigaba da aikinta. Uwani na cikin dakin abin duniya yayi mata yawa, tunani takeyi yanzu wace irin rayuwa zasuyi cikin gidanan! tun da can baya tasan Kuluwa macace mara mutunci da muguwar kaxanta sam bata so kowa yazo inda take tabi ta asirce Kawu Madu sai abinda tace yayi yake ji shima wani lokacin tsoranta yake yi, Ta dinga tunanin irin wuyar da zasu sha ita da 'yayanta a gidan dan ga dukanin alamu Kuluwa ba tayi maraba da zuwansu ba, tunani take ko su tafi gidan Kawu Isa ne? sai ta tuno shi kuma ai bai da gidan kanshi haya yake kuma daki guda ne suke gamutsuwa dashi da matarshi da 'yayanshi.....Iya mai waina kuma ba ita kadai bace a gidanta tana da kishiyoyi kuma babu wadataccen gurin zama, dole dai gidan Kawu Madu din shine gurin zamansu, Kwallace ta taru a kwarmin idanunta tayi saurin gogewa, lokaci guda duniya ta juya musu baya, sun fara d'and'anar jin dadin rayuwa kuma sun koma gidan jiya............Sai a lokacin nadama mara amfani ta kamata ta dinga tunanin abubuwan da suka dinga faruwa a baya da irin kud'ad'en da 'yarta ta rike da samun nasarar auran Ahamdu tayi, Yanzu ne ta gane auran Ahamdu da 'yarta shine rufin asirinsu tasan da Wasilan na gidanshi har yanzu da tuni basu shiga wannan gararanbar ba. Kuluwa ta shigo dakin hannunta rike da wata katuwar langa tana kallon Uwani tace"Naga kamar kema kina cikin alhini da damuwa to Allah yasa dai ba abin kunya kukayi a can ba kuka gudo nan dan naga alamun ciki a tattare da waccan 'yar taki." Uwani ta kalleta ranta ya 'baci da maganarta amma saboda sanin halinta yasa tace"Eh kuluwa ki daina shakka ko kokwanto Wasila na da ciki amma kuma da Ubanshi." Kuluwa ta ta'be bakinta tana fad'in "To yanzu naji zance Allah ya rabasu lafiya sai ki kira su kuci abinci gashinan babu yawa dai aci da hakuri tunda ban san da zuwanku ba." Uwani tace"To mungode." Kuluwa ta fita daga dakin, tana gyara daurin zaninta wanda yayi da'kal! da'kal da daud'a! Uwani ta le'ko tana kiransu Wasila dake zaune jikin bishiyar darbejiya dake gidan.........Rashida da kyar ta lalla'bata suka koma dakin....suna shiga ta fito da sauri tana fad'in "Rashida ba zan iya ba wallahi mutuwa zanyi zuciyata tashi takeyi." Karaf a kunnan Kuluwa cikin fusata tace"Ke! buhun ubanki nace! Buhun ubanki kaji min shegiyar yarinya ciki haukane da zaki zo min gida kina min iskanci! har ki dinga cewa zuciyarki tashi takeyi to bari malam ya shigo wallahi kinji na rantse ba zaki zauna min a gida ni ba'a kawo min iskanci ehe! dama ai baku bane tilashin mu ita Uwanin itace tilas dinmu dan haka sai ku koma inda kuka fito abin arziki baya zama na tsiya." Takarashe maganar tana kumfar baki kai daka ganinta a fusace take! Uwani ta fito daga daki tana bata hakuri saboda tasan halin ta zata iya cewa su Wasilan baza su zauna a gidan ba kamar yanda ta fad'a, Hakuri take bata tana karyar dai muryarta sai rawa take! Kuluwa ta cigaba da aikinta tana sababi! da zagin Wasila Uwani ta dauko langar abinci ta dire a gabansu tana fad'in " Ku kiyaye da wannan matar idan kuna son zaman lafiya bana son abinda kikeyi Wasila kinga bamu da gatan da yafi nan, Kuluwa macace mara hakuri zata iya sa Kawu yace ku bar mishi gida kamar yanda ta fad'a saboda haka duk abinda zakiji na tashin zuciya ki dinga daurewa kina hakuri haka take muguwar kazama ce tun tana da kuruciyarta gashi har girmanta......Wasila bata iya magana ba rashida ce mai magana tace"Gaskiya Uwani gidan nan baiyi wallahi duba fa ki gani ko ina kazanta da kashin dabbobi dubi bandaki babu kofa sai buhu kiji warin masai dake tasowa har nan kawai mu zamu tafi Garko ke kiyi zamanki nan tunda kece tasu." Uwani ta marairaice fuskarta muryarta na rawa tace"Rashida kin san yanda nake son ku kuwa ? bana so kuyi nesa dani shiyasa na'ki aure na 'kare rayuwata tare daku, ina 'kaunarku saboda nasan bani da kowa sama daku, Uwata ta mutu Ubana ya mutu mijina ya mutu sai ku kawai nake kallo naji dadi idan kuka tafi Garko kuka barni wace irin rayuwa kuke tunanin zanyi a cikin garin nan."!? Tausayin mahaifiyar tasu ne ya kama su, sai suka hau goge hawaye, suna adduar Allah ya kawo musu dauki da gaggawa amma hak'ikanin gaskiya mahaifiyar tasu tasha wuyar rayuwa ta kuma yi wahala dasu bai kamata su guje mata ba, Zama tayi kusa dasu tana bud'e langar abincin aikuwa sai wani irin towon dawa ba'ki'kikirin yayi musu sallama! towon sai shaining yake ga wata uwar miya kamar fitsarin jaka, sai wake guda guda a cikin miyar tana ta warin daddawa......A guje Wasila ta mike ta nufi bakin rariya ta dinga kakarin amai tana zubar da kwalla! Kuluwa tayi azamar fitowa daga kicin da ludayi a hannunta....Wannan karon Uwani da kanta taje ta rirrik'e 'yar tata tana mata sannu ita kuwa sai rike ciki take tana mur'kususu da kiran sunan Allah! Kuluwa ta dinga kallonsu bakin cikin duniya kamar ya kasheta 'Kwafa tayi ta koma kicin din! Yau ba gobe ba zasu bar mata gidanta dan bata ciki da iskanci da wulakanci......Kawu Madu ya shigo gidan yana sa'be babbar riga sai kawai ya gansu cirko cirko Uwani da Rashida kan Wasila dake durkushe tana kakari......Yace."A'a Uwani meke faruwa ne Me yasa me ta take amai haka."? Kafin Uwani tace wani abu Kuluwa tayi zuruf ta fito daga kicin fuskarta a murtuke tace" 'Kyankyamina takeyi shine take amai tunda suka shigo gidanan basu shiga dakina ba can bakin bishiya suka zauna saboda suna kyankyamina saboda haka yau ba gobe ba zasu bar min gidana dan wallahi ba zan dauki wannan iskancin ba." A take Kawu Madu ya sha kunnu yana kallonsu rai a bace yace."Ashe baku da tarbiya dama? matar tawa kuke 'kyankyami!? to shikkenan dama ai baku ne tilas dina ba Mahaifitarku ce saboda haka zaku bar min gidana tunda baku da mutunci." Uwani ta shiga share hawaye tana fad'in "Kawu ba haka bane wallahi yarinyar nan nada ciki mai laulayi yana bata wuya dama tun a mota take amai har yanzu ba wai suna 'kyankyamin Kuluwa bane." Yace."Uwani."! ta amsa yace."Shin yaushe kikayi wa yarinyar ki aure babu labari gashi nace tana da ciki."! Kuluwa tace"Nifa malam ban yarda ba wallahi wannan yarinya cikin shege tayi shine suka kwaso jiki suka gudo nan sabida gudun abin kunya dan haka wallahi ba'a gidan nan ba idan kuma kace tilas sai sun zauna to ni zan fice na baku guri." Hankalin Kawu Madu ya tashi, Yace."A'a ba za'ayi hakaba Kuluwa ai duk wannan magana ma bata taso ba, ke Uwani zo ki zauna kiyi min bayanin abinda ke faruwa." Uwani ta bishi kan tabarma suka zauna tare Kuluwa ta 'karaso gurin hannunta rike da ludayi ta zauna kujera 'yar tsugo tana fad'in "Eh ai gwara muji bayanin komai domin mu samu kwanciyar hankali." Uwani ta share hawaye a hankali ta soma warwarewa masa abubuwan da suka faru da rayuwarta ita da 'yayanta komai bata rage masa ba sai da ta fad'a mishi......Kuluwa tace"Duniya kenan yanzu ke Uwani bakiji kunya ba, wato lokacin da kuka samu kudi kuka samu dad'in duniya baki tuna damu ba sai da wahala ta taso ki sannan zaki tuna damu ki kwaso jiki ra'be ra'be da 'yaya kizo ki d'ora mana nauyi to ba zata ta sa'bu ba! Mu ba zamu dauki nauyin ki kuma mu d'auki nauyin 'yayanko ba, Dan haka gobe gobe yaran nan zasu bar gidanan suje can dangin mahaifinsu tunda suna raye, kema abinda yasa ba zamu kore ki ba saboda mun san ko kinje can gidan Kawunki ba zai kar'be ki ba saboda haka ke kad'ai zamu ri'ke saboda kece tamu." Kawu Madu yace."Kwarai kuwa Kuluwa wannan magana taki gaskiya ce, Yaran nan baxa su zauna mana a gida ba sabida bamu da hakki a kansu dan haka kamar yanda kika fada hakane kwana guda zasuyi su bar mana gida suje can cibiyarsu.........Uwani ta dinga kuka tana fad'in "Haba Kawu ku duba al'amarin fa kada kuyi min haka bani da kowa sai 'yayana bani da uwa da uba bani da miji sai 'yayana su nake gani naji sanyi a raina." Kuluwa tace"To ai tunda hukuncin da muka yanke bai miki ba to sai ki bi 'yayan naki haba! wannan 'kulafucin son 'yaya dame yayi kama.'' Ta mike tana jan tsaki ta shiga dakinta.....Kawu Madu ma ya mike yana fad'in "Na fad'a miki Uwani na yanke hukunci Kuluwa ta yanke hukunci saboda haka shawara ta rage gareki." Ya buge babbar rigarsa ya 'kara gaba. Wasila da Rashida kam! basu ciwo ba dalili dama sunfi son su tafi can garkon shiyasa sukaji dadin hukuncin da Kawu madu ya yanke a kansu amma basu nunawa mahaifiyar tasu ba, sai suka shiga kwantar mata da hankali da fad'in ko sun tafi insha Allahu zasu dinga zuwa a kai akai suna dubata.....Uwani dai jinsu kawai takeyi abin duniya ya taru yayi mata yawa bata ta'ba nadamar rayuwa ba irin yau. Kuluwa ta dinga shige da fice a tsakar gidan tana sakin 'ba'kaken maganganu wanda ya sanya jikin Uwani yi sanyi taji a zuciyarta gwara kawai su Wasila su bar gidan dan ba zata iya jurar rashin mutuncin kulawa tana aibata mata yara da kiransu karuwai watarana tana ganin zata iya mayar mata da martani kan maganar da takeyi, ta dinga jin wani irin d'aci! da bakin ciki a raina ashe haka abun yake da ciwo a duk sanda aka danganta d'anka da wannan suna (karuwai) gaskiya ta gode Allah da ya bata 'yaya masu hankali da hange nesa tasan da bada hakan ba da tuni sunanan da kuluwa ke kiransu dashi ya tabbata tunda ita da kanta ta dinga turasu karuwancin, tagode Allah da yasa wannan cikin dake jikin Wasila ta sameshi ta hanyar halak ba haram ba. Kuluwa na ganin irin tsarabar da suka kawo sai ta hau washe bakinta ta dauki turmin atamfofi irin na leda guda biyu tace wannan ni zan d'inka in sa a jikina wannan yadin kuma na malam ne, sauran kuma Iya mai waina da Tabawa su kasafta a tsakaninsu." Su dai kallonta kawai sukeyi duk tabi ta kwashe kayan ta shige dakinta dasu sai murna takeyi ko Kawun ma bata nunawa ba. Sai dare suka samu suka sanya abinci a cikinsu shima abincin Inna Tabawa ce ta kawo musu cikin katuwar Samira shinkfa da wake ne da manya da wani uban yaji da yaji gishiri da citta! haka suka cuccusa dan gwarashi kan narkeken towon dawan da Kuluwa ta kawo musu, Wasila dai kad'an taci tasha maganinta ta nemi gefenan tabarma ta kwanta tana mai da nuffashin wahala.............Duhu sosai gidan babu wadatacciyar fitala sauro da kwari ka sukayi sallama! Wasila ta gigice ta dinga soshe soshe kukan sauro duk ya cika mata kunne! Uwani tace "Ku tashi mu koma daki mu kwanta kunga mutanan gidan sun shige sai mu kadai a tsakar gida ga sauro." Rashida tace "Yanzu cikin wannan kazantar zamu mu kwanta ga yara nasan suna fitsarin kwance." Uwani tace"To ya zakuyi ai da zama cikin sauron nan gwara cikin rumfar." Wasila tace"Uwani ku shiga ku ku barni anan Rashida ki dauko min zanin atamfa cikin kayanmu in rufe jikina." Uwani tace"Akwai fa damuwa kwanciyar ki anan." Tagoge kwallah tace"Uwani nan yafi min kan in shiga dakin nan inzo ina kakarin amai da daddare d'an abincin da naci ya dawo, kuma wannan matar tazo tana miki masifa." A sanyaye Uwani tace"Shikkenan ai." Ta mike a hankali ta shiga dakin rashida tabi bayanta......Nan su kaga yara birjik a rumfar ko wanne ya wargaje kafafunshi wasu sun soma sakin fitsari abinsu sai barci suke.....Uwani ta ra'ba can wata kusurwa ta karkad'e wani buhu ta shimfida ita kuma rashida ta nufi dakin Kuluwa dan jakkunan kayan nasu na cikin dakin........Nan ta tarar da Kuluwa ta bude musu kaya sai bunkice takeyi musu, tana ganin rashida sai ta diriri ce ta hau ya'ke...."Am...dama ai nace bari na gyara muku kayan naku in adana muku su guru guda." abinda tace kenan tana sosa kanta....Rashida bata ce komai ta dauki zannuwa uku na atamfa ta fito daga dakin....Ita kuluwa tana ganin rashida ta fita daga dakin sai ta cigaba da bincika kayan ta dauko manya manyan shaddodin Wasila masu uban stone work ta d'aga 'kasan katifarta ta sanya ta mai da katifar......Da sauri ta gyara jakkunan kayan ta fito daga dakin tana zare ido. Wasila kudindine jikinta tayi. ita kadai kwal a katon tsakar gidan ko tsoro bataji gari yayi shiru sai kukan tsintsaye kawai ke tashi.......... Cikin ikon Allah bacci mai nauyi ya dauketa ta dalilin magungunan da takesha Fitowar Kawu Madu daga dakinsa ne ya tayar da ita Sai taji ana kiran sallah da alama asuba tayi, Kawu Madu ya kalleta yana mamaki yace." Ke anan kika kwanta." Sunkuyar da kanta tayi kawai sai ya girgiza kanshi ya nufi bandaki da buta a hannunsa........Yana fitowa ya daura alwala ya nufi masalaci, Kasa shiga bandakin tayi sai kawai tayi gaggwar tsugunawa a bakin rariyar tayi fitsarinta ta kwara ruwa, kana ta matsa gefe guda ta daura alwala ta bar gurin. Shimfidar data kwanta ta dauke ta cire dankwalin kanta ta gyara hijab dinta ta tada sallah......Uwani da rashida suka fito a tare suma alwalar suka daura nan tsakar gidan sukayi sallah domin dai cikin rumfar babu guri bayan haka kuma ko ina kasa 'kafarka fitsari ne. Suna zaune a tsakar gidan gari yayi haske Kuluwa ta fito tayi alwala ta goge bakinta da gawayi kana ta shiga kichin ta kunna wuta ta dora ruwan kunu sannan ta nufi daki domin yin sallah. ၥYaran dake dakin suka soma fitowa su kusan bakwai wasu jikinsu da fitsari wasu babu ba tare da sunyi alwala ba suka soma wasa a tsakar gidan wasu kuma tuni sun fice waje da abubuwan wasan su......Su Wasila suka dinga mamakin wannan rayuwa....Nan rashida take shaida musu abinda taga kuluwa nayi musu da kayansu....Fitowarta yasa tayi saurin yin shiru to itama Kuluwar a kunyance take dan haka sai tayi saurin fadawa kichin tana sosa kai! Wasila abin dariya ya bata sai ta shiga girgiza kai tana fad'in ''Ni dariya ma take bani wallahi." Rashida tayi dariya kasa kasa tana kallon kicin din. Wani tsalan kunu ta kawo musu cikin kwanon sha da kufuna guda uku sai 'kullin sikari akai....Uwani ta gaisheta tanayi mata sannu suma suka gaisheta Ita kuwa ta kasa tsayawa a gurin kunyar hada ido da rashida take......Tana shiga kicin Wasila ta saka fuskarta cikin hijab taci dariyarta ta koshi, kai mara gaskiya dai ko a ruwa gumi yake. Fitowa tayi daga kicin din da katon farantin silba da narkeken d'umamen towo an yanyanka shi sai miya tsululu towon sai iyo yake cikin miyar....Ta kalli rashida tana fad'in 'kawata ga d'umame nan idan kunsha kunun sai kuci kwaji dad'in tafiya da karfinku." Rashida tace"Mungode Kuluwa." Da sauri ta bar gurin tana kwalawa yaranta kira wai suzo su dauki kununsu da duk ta zuba musu a kufuna 'kudaje sai bin bakin kufunan sukeyi.....aikuwa da d'ai- da d'ai yaran suka dinga shigowa suna daukar kufonan kunun suna sha ba tare da sun wanke bakinsu ba. Kawu Madu ne ya shigo da sauri yana fad'in "Ina Wasila da Rashida." Sukace gamu Kawu Yace." To maza ku fito ga motar abokina ya kawo ice yanzu zai fita cikin gari sai yaje ku a tasha ku shiga mota." Suka mike da sauri Rashida ta shiga dakin domin dauko musu jakar kayansu, dama tasu daya ce ta uwani daya. Uwani ta mike tana yakar zuciyarta hawaye ne yake so ya 'balle mata tana mayar dashi, suka je bakin kichin din da Kuluwa ke ciki tana zaune dirshan gabanta da karon bokintin da ta dama kunu tana katsewa gefanta kuma tukunyar miya ca bude ga ludayi a kasa....Uwani tace"Zasu tafi." Sai ta hau washe baki tana fadin"Bari na taso inyi rakiya ni kuwa me zan baku. 'Yayan nan."? Fitowa tay ta shiga dakinta da sauri ta dauko wata yar takarda fara ta mikawa rashida tana fad'in 'Kawata ga yariruka kwa sanya ku gaishe da kawunan naku." Rashida ta karba tana godiya tabi bayan Wasila da Uwani da suka riga sukayi gaba. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *59* Tun a mota yake jin alamun zazzabi zazzabi a jikinsa yasan kuma ba komai ne ya jawo mishi faruwar hakan ba sai alhini da damuwar da yake ciki idanunsa sun kad'a sunyi jawur! jijiyar kanshi ma ta tashi, yanda le'bunanshi suke a bushe haka ma'kogwaron shi yake dan rabonshi da ruwa ko abinci tun jiya da daddare da yasha coffee kafin ya kwanta, sam ya ma manta da wani abinci saboda tsananin damuwar da yake ciki....Yana kallon khalifa na tu'ki yana kur'bar lemo amma shi sha'awa ma baya bashi bakinsa duk ya bushe yana jin wani irin abu ya tokare masa a ma'kogwaronsa. Ganin tashin hankali murarar a tartare da abokin nasa yasa ya d'an kalleshi bayan yayi parking din motar cikin gidanshi, Yace."Kayi hakuri abinda zan iya cewa da kai kenan! ka cigaba da addua kawai kan Allah ya tsare maka cikinka da ita kanta yarinyar wannan damuwar duk ba ita mafita ba, tunda dai Allah ya raba ganawa sai ka bar mishi ikonshi, ni munyi magana da ita a jiya ta kuma shaida min cewar mutukar ta haihu to zata kawo ma'ka d'anka har inda kake." Saurin kallonsa yayi yace."Okey ashe da sa hannunka ta gudu kenan." ? Khalifa yay saurin girgiza kanshi yana fad'in" No ka fahimce ni mana! Jiya nake fad'a mata cewa dole sai na sanar maka da maganar cikin ta nuna bata so nace mata ai tilas ka sai ka sani shine tace ko anfad'a maka ko ba a fad'a maka ba in ta haihu zata kawo maka d'anka kaji dalilin da ya sanya nayi maka wannan maganar amma wai maganar da sanya hannuna a cikin guduwarsu bata taso ba." Girgixa kanshi ya shiga yi yace."Ban san a ina zanga 'kawarta ba mybe a samu wani labari a gurinta." Khalifa yace."Eh to ai kuma inda za'a sameta ne aiki." Yace."Zan duba wayarta baza'a rasa numbar ta ba." Khalifa yace."Yawwa hakan yayi kyau Allah yasa a dace yanzu dai ka kwantar da hankalinka mu shiga ciki kaci abinci ka huta tukkuna insha Allahu komai zaizo da sauki." Girgiza kai kawai yay yace."Khalifa hankalina ba zai ta'ba kwanciya ba sai naga yarinyar nan, na 'kwallafa raina kan cikin jikinta burina kawai in ganta kuma in tabbatar lafiyar abinda ke cikinta." Khalifa yace." Shine ai nace damuwa da tashin hankali bashi ne mafita ba addua itace mafita kawai ka kwntar da hankalinka ka cigaba da addua.'' Murmushi mai ciwo yay khalifa bai san yanda yake ji a zuciyarsa ba shiyasa yake cewa ya kwantar da hankalinsa a maganar kwanciyar hankali ta 'kare a gurinsa yanzu mutukar ba ganin yarinyar nan yayi ba. A Tare suka fito daga motar tamkar wanda 'kwai ya fashe musu a ciki suka nufi cikin gidan. ga gajiya ga rashin samun nasara. **** Dake akwai tafiyar 'kafa tsakanin bakin titi da cikin 'kauye yasa suka samu babur irin na (kafu-kafu) ya shiga dasu ciki har 'kofar gidan Mai allo aka ajesu, kana suka biyasu hakkinsu.....Suna kokarin shiga gidan ya fito da cazbaha a hannunshi, kawai sai yay tozali dasu. Ya bude baki yana kallonsu cike da mamaki. Idanun Wasila ya kawo ruwa rau-rau! ranar naka sai naka! Wai itace tazo garin Garko da 'kafafunta! Hawaye suka zubo mata a kumatu, kai a 'kasa suka isa inda yake suka zube gwiwa bibbiyu suna kuka! Tausayinsu ya kamashi da sauri yace."Ku tashi mu shiga ciki.'' Jikinsu a sanyaye suka mi'ke rashida taja akwatin kayan nasu suka bi bayansa. Kamar dai koda yaushe Bitan na zaune a tsakar gida tsaf da ita jikinta sai kyallin mai yake da alama bata jima da yin wanka ba tana sanye da wani leshi ruwan ganye(kore) irin nada ta d'aure kanta tamau! da dankwalin leshin, cinyar ta farantin shinkafa ne tana tsincewa sai kawai ta tsinkayi muryar mijin nata yayi sallama, Da sauri ta d'ago kanta tana kallon bakin 'kofa, Yanzu yanzu ya fita ko mantuwa yay abinda take ayyana cikin ranta, sai kuma taga su Wasila a bayanshi. Tace"A'a malam su wa nake gani a bayanka yau.''? Yace."Gasunan nima fita ta na hango zuwan su Wasila ce da Rashida." Bitan! ta ri'ke ha'ba babu yabo babu fallasa a fuskarta tace"To masha Allah sannunku kuzo ku zauna ga gurin zama." Mai allo yace."Kuje ku zauna." Sukaje suka zauna kusa da ita sai sunkuyar da kai suke mussaman Wasila dama itace akuyarta tayi kuka a garin.....Mirya na rawa tace"Kawu ina wu ni mun sameku lafiya." ? Yana daga tsaye yake amsawa yana nazarinsu....Rashida ma ta gaishi ya amsa, kana suka shiga gaishe da bitan itama ta amsa cikin kulawa kafin ta mike a nutse ta nufi kicin....Mai allo ya dinga kallonsu zuciyarsa na karyewa 'yayan Yahuxa tamkar 'yayan cikinsa suke, duk yanayin da ya gansu na dad'i ko na rashin d'ad'i dole ya shiga damuwa, kallon farko da yay musu ya fahimci akwai damuwa da firgici a tartare dasu mussaman Wasilan da tayi firgai firgai da ita kamar ma mara 'koshin lafiya. Bitan ta fito daga kicin hannunta rike da samira mai hannun roba, ta aje a gabansu ta koma kicin din da sauri ta fito hannunta rike da wani farin jug ta bude randa ta debo musu ruwa ta aje a gabansu ta zauna tana fad'in" Kuci abinci kunji ko ku daina kuka da damuwa rayuwar nan kowa hakuri yake da ita." Malam yay gyara murya yana kallon matar tashi yace."Zan fita kamar yanda na niyyata idan Allah yasa na dawo sai na zauna dasu, Insha Allah." Bitan tace"To malam ubangiji Allah ya tsare a dawo lafiya." ya amsa yana kokarin fita, Wasila da Rashida har rige rige suke gurin yi masa adduar dawowa lafiya ya amsa musu a lokacin da yake kokarin fita daga gidan. Bitan taga sun kasa cin abincin tace"Ku saki jikinku fa kuci abinci insha Allahu ba zaku samu wata matsala dani ba, ni dama tuntuni ina tausayawa rayuwarku mutukar kun gane gaskiya kuma kun gana mahimacin Kawunan ku a gurin ku , ai magana ta wuce suma kansu Kawunan naku hankalinsu a tashe yake, amma nasan yanzu hankalinsu zai kwanta tunda kun dawo garesu." Sai suka sake jin kwarin gwiwa a tare dasu, Rashida ta bude samirar abincin dake gabansu, burabusko ne (biski) yayi shar shar dashi sai kamshin man'kuli zuryan yake, ga maggi star guda biyu a gefe da yaji....Wasila taji yawunta ya tsinke sosai taji sha'awar cin burabuskon ta mike a nutse ta wanko hannunta, ta dawo ta zauna Rashida ma mikewa tayi taje ta wanke hannunta sukayi bisimillah tare da fara cin abincin. Bitan ta mike a nutse ta shiga kicin ta kunna wuta, Girgi zata dora musu na mussaman, sabida yaran sun bata tausayi sosai da sosai sam basuyi sa'ar uwa ba duk wata wahala da suka shiga mahaifiyarsu itace sila shiyasa kwata kwata basa shiri da ita sabida munanan haleyenta gashi tayi ta zagin mijinta a gabanta, duk abinda za tayi wa yaran za tayi musu ne saboda Allah da kuma maraicinsu, ba dan halin Uwarsu ba.. Tas suka cinye burabuskon basu rage komai ba, Wasila tafi rashida ci dan daga karshe ma rashidan cire hannunta tayi ta bar mata ta 'karasa cinye tayi gatsa tana hamdala hankalinta ya kwanta sosai da tsabtar Bitan shiyasa kome ta girka ta bata zata iya ci......Bitan ta fito daga kicin hannunta rike da wani ma dai-dai cin kwando dafaffan 'kwai ne a ciki da yawa ta aje a gabansu tace ku 'kara da wannan yanzu zansa yara sunyi min cefene na sake dafa muku abinci. "Wasila tayi murmushi tana fad'in " Bitan mungode Allah ya saka miki da alkairi." Murmushi kawai tayi ta koma kicin tana cigaba da aike aikenta. Hajara ce tayi sallama ta shigo gidan tare da d'an autanta Lamir yana biye a bayanta.......Tsayawa tayi bakin kofa tana kallonsu, Sunkuyar da kai sukayi kamar munafukai. Bitan ta fito daga kicin taganta tsaye a bakin kofa tace"Ki shigo mana ai ba abin mamaki bane addua bata fad'uwa 'kasa banza." Hajara tace"Ai dole nayi mamaki Bitan! Yaushe suka zo kuma."? Bitan tace"Ke dai shigo ki zauna." Hajara ta karasa kan tabarmar ta samu guri ta zauna idanunta a kansu Wasila ta dinga tunano rigimarsu da Hajaran tana shan duka a gurinta a duk lokacin da sukazo garin, dan kwata kwata basa shiri sunfi shiri da Rashida......Cikin jin nauyi suka gaisheta ta amsa tana fad'in "Kunga uwar bari kenan."!? Sukayi 'kus! kansu a 'kasa, Hajara zata fara sababi! Bitan ta dakatar da ita da fad'in " Haba Hajara wannan ba kana bane! Kullum fa addua kuke kan Allah ya karkato da hankalin yaran nan gareku Allah kuma ya amsa adduarku sannan kice wani abu, don Allah kar ki fad'i wata mummunar magana kan yaran nan ki kyalesu ma suji da abinda ya damesu. Hajara ta fashe da kuka tana fad'in "Haba Bitan! al'amarin nan fa akwai dam uwa da ba'cin rai wallahi yaran nan sun sanya mu a fargaba da tashin hankali mussaman waccan mai 'katon kan tana sunkuyar da kai munafuka kawai Ai dama nace duk sanda kika kwaso kafafunki kika zo sai na ci miki mutunc.......Bitan tace" Ashe bakiji maganata ba kenan haba hajara."? Hajara ta kwance bakin zaninta ta goge hawayen fuskarta tana fad'in "Allah ya ji'kan ka Yahuza." Ai sai Wasila da Rashida suka sa kuka! Suna bata hakuri! Takaicin duniya ya ishi bitan Hajara tazo ta dagula al'amari ta tayarwa da yara hankali sai koke koke sukeyi......To itama hajaran da taga sun ki su daina kukan sai ta shiga rarrashinmu itama ba yin kanta bane tunawa tayi da d'an uwanta....Rashida da Wasila suka dinga bata hakuri da fad'in "Insha Allahu baxa su sake guje musu ba tunda sun gane basu da kowa a duniya da wuce su......Hajara taji dad'in wannan magana tasu sai tace " Komai ya wuce insha Allahu. Hajara bata koma gidanta ba har sai da malam mai allo ya dawo suka gana da juna sannan tayi musu sallama ta tafi gidanta da al'kwarin dawowa gobe idan Allah ya kaimu. Bayan sallahr isha'i mai allo ya samu nutsuwa duk suna zaune a tsakar gida bayan sun gama cin abinci, mai allo ya gyara zamanshi kan buzunsa yana kallonsu a nutse yace."Naji da dadi kuma nayi farin ciki da har kuka gane mahimancinmu a gurinku, yanzu kun gane cewar baku da wani gata a duniya da wuce Allah da ma'aiki da kuma ni da 'yan uwana, Mahaifiyarku ta dauke ku ta kai ku can cikin danginta, sun nuna muku cewar su basu da ala'ka daku , kamar yanda kuka fad'a min cewar da kyar ma suka bari kukayi kwana a guda a gurinsu, ni a ganina ba suyi lefi ba kamar yanda kuke tunani sun nuna muku mahimcin danginku ne, me yasa basu kori ita mahaifiyar taku ba? saboda sun san tasu ce kuma bata da wani guri da za taje idan ba gurinsu ba, naji dadi da faruwar hakan, na kuma tabbatar da cewar hakan zai sake sanyawa ku shiga cikin hankalinku ku gane meye rayuwa, alhamdullhi, Allah ne abin godiya a garun mu baki d'aya." Shuru yayi yana sauke numfashi kafin ya cigaba da magana yana me kallon inda Wasila take zaune, Yace."Jiya mijinki yazo garinan cikin tsananin rud'ani da tashin hankali yana shaida min cewar wai kina dauke da cikinsa a jikinki shin hakane ko ba haka bane? tunda dai ni kafin wannan zuwan nashi wattani uku da suka wuce yazo har nan ya shaida min cewar ya sake ki saki d'aya wanda a lokacin mukayi ta tsammanin zuwanki baki zo ba sai yanzu. Tun lokacin da mai allo ya firta maganar mijinta yazo taji duk wani kuzari nata ya dauke yawun bakinta ya tsinke gabanta ya shiga fad'uwa da 'karfi da 'karfi sai kawai ta soma fad'in kalmar innalilihi cikin zuciyarta, muryar mai allo ce ta dawo da ita hayyacinta yace."Ke nake sauraro Wasila." Ta d'ago kanta idanunta cike da 'kwalla tace"Eh Kawu in da ciki." Yayi jim! kafin yace."To masha Allahu, yanzu akwai aure a tsakaninku kenan? ko ku kuma bayan rabuwarku dashi cikin ya bayyana kanshi."? Ta goge hawayen dake kuncinta tace"Bayan mun rabu cikin ya fito.'' Shiru yayi yana girgiza kanshi kafin yace."Gaskiya mana, yazo nan hankali a tashe a jiyan ni har na soma tunanin ko da akwai aure a tsakaninku ashe shi saboda cikinsa ya biyo bayanki, to babu lefi ai idan Allah yasa Habibu ya dawo daga tafiya, tunda shine yake da numbar wayarshi sai ya kirashi ya shaida masa abinda ke da akwai, amma maganar zai daukeki ya killace ki kiyi mishi rainon ciki duk bata taso ba, anan ma zaki raini ciki ki kuma haife lafiya ba tare da wata matsala ba insha Allahu, wannan dai hakkinsa ne dole a fad'a mishi halin da kike ciki duk saboda jininsa da kike dauke dashi a jikinki." Kuka tasa tana fad'in "Dan Allah Kawu kar a fad'a masa bana so kawai a bari idan na haihu sai a bashi d'anshi Ni bana so yazo inda nake." malam ya shiga kallonta yana mamakin gursheken kukan da take. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *60* Mai allo ya dan gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Kiyi shiru ki kwantar da hankalinki ki daina kuma kuka, sanar dashi ba yana nufin cewa zaki koma gidanshi bane, A'a za sanar mishi ne domin fita hakkinshi, ba wai dan muna neman wani abu a gurinshi ba, yana da kyau ya san cewar har yanzu kina nan dauke da cikin nashi, kuma ya samu nutsuwar zuciyarshi, ni ba zanyi miki dole ba kamar yanda nayi a farko, ba zance tilas ki koma domin ki cigaba da zama dashi ba, zaki zauna ki samu nutsuwar zuciyarki ki haihu lafiya kana ki za'bi namijin da yayi dai-dai da rayuwarki ki aura." Bitan tace"Wannan magana da kayi itace mai kyau, saboda haka ki daina kuka kuma ki samu nutsuwa da kwanciyar hankali ko dan saboda cikin jikinki insha Allah babu wanda zai miki tilas kan ki koma zama gidan shi tunda bakyaso to Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi." Wasila ta shiga goge hawayenta tana sauke ajiyar zuciya, Bitan ta mike ta nufi wani daki minti biyu ta fito daga dakin hannunta rike da fitilar kwai ta gyara a nutse ta gyara fitilar ta kunna ta koma dakin.....Kimanin minti goma tayi a ciki ta fito tana fad'in "Na gyara muku shimfida sai ku kwanta ku huta mussaman ke Wasila naga alamun gajiya a tare dake kiyi bacci sosai sai ki samu sassauci da nutsuwar zuciya." Suka mike a nutse suka shiga dakin..........Bitan ta zauna kusa da mijinta suka cigaba da tattaunawa dangane da al'amarinsu Wasilan. Dakin na shimfide da lede sabuwa da lalubewa masu dan kauri sai katifa ma dai-dai ciya mai cin mutum biyu jakar kayanu ajiye a gefe, dakin dai ya ishesu su biyu ba tare da wani ya takurawa wani ba.....Wasila ta cire hijab din jikinta, ta janyo akwatin kayansu tana dubawa kaya mara sa nauyi zafi takeji idan da son samu ne ma ta watsa ruwa, saboda zafin da takeji, Da kyar ta samu wasu riga da wando irin marasa nauyi sosai ta saka a jikinta, ta nemi ta gyara tufkar gashinta, Rashida dake kokarin kwanciya kan katifar tace"Anti Wasila ni kuwa zan baki shawara.'' Ta kalleta tana fad'in "Wace irin shawara."? Rashida ta mi'ke zauna a hankali tace" Dan Allah ki koma gidan Ahamdu wallahi shine marufar asirinki yanzu idan kince wani auran zaki sakeyi to ai baki san wanda zaki aura ba, kin san yanzu auranan zamani nan sai a hankali, amma ni ba tun yau ba nake sha'awar auranki dashi wallahi, kuma idan kin duba kinyi tunani fa za kiga bashi da laifi dangane da abinda ya faru a tsakaninku, ke koma yana da laifi to naki laifin yafi nashi, saboda haka nake baki shawara kan dan Allah idan yazo da niyar mai dake gidanshi ki amince kawai ki koma zakiji dadi muma muji dadi." Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon 'yar uwar tata tace"Wato Rashida har yanzu kwadayi da hange ne cikin ranki ko? Rashida ta girgixa kanta alamun a'a.......Ta cigaba da cewa''Idan ba kwadayi ba me zai sanya kice min in koma gidanshi? Kince nafi shi laifi Eh na yarda na fishi laifi kuma na amsa laifina amma me yasa lokacin da nayi nadama na nemi afuwarshi bai yafe min ba? lokacin da nake kuka nake neman gafarar shi a lokacin ji nakeyi zan iya zama dashi cikin ko wane hali saboda yayi min hallaci ya kuma yi min abinda ba kowa ne zai iya ba, ni ba nufina a kasheshi ba ko a cutar dashi, amma na lura shi abinda yake zargi kenan......Kinga duk mutumin da yake zarginka hankalinsa ba zai ta'ba kwanciya dani ba, Ni nasan koda na koma gidanshi to koma mu 'kan'kare za'ayi sabida yana zargina, sannan kuma ni bana jurar wulakancin da raini sam mutumin nan baya ganin mahaifiyarmu da daraja da mutunci ban san dalili ba ko dan yana da kudi ne oho! , naji ciwo sosai ranar da kuka zauna a gidanshi keda Uwani ya wulakanta ku, yana da kudi yana ganin babu wanda ya isa! sannan kice na koma gidanshi, ai ko zan koma auranshi sai ya mutunta mahaifiyata, ballanta ma bana sanyawa zuciyata cewar watarana zan koma gidanshi in cigaba da zama a matsayin matarshi, kawai Allah ya hada kowa da dai dai shi." Rashida tace"Wallahi ba Kwadayi bane ni kawai mutumin yake burgeni yana da kirki da tausayin talakawa kinsan dama ance dan adam tara yake bai cika goma ba, kuma ni a ganina ba wai baya ganin girman u wani bane kawai dai kinsan wasu masu kudin kuma ranar da mukaje ai bai san cewar mune ba shiyasa, ni daina zan cigaba da tayaki addua kan Allah ya karkato da hankalinsa kanki gaki dauke da cikinsa ai dole ma nayi sha'awar ki koma hannunshi kuji dadin rainon danku." Tsaki taja tana fad'in "Ranki zai 'baci mutukar kika sake yi min wannan banzar maganar."! Rashida tayi shiru tana kallonta.....Mikewa tayi taje ta kwanta tare da rufe kafafunta, maganar rashida tasa duk wani bakin cikin dake damunta ya dawo sabo, dal! ta dinga jan tsaki tana juye juye, hawaye ta share tana sake tuno lokacin da take birgima da ihu a gidanshi tana rirrikeshi ya taimaketa ya hakura ya mai da ita yanayi mata wulakanci, ai wallahi ta bar auranshi mutukar ta cika ita d'in 'yar halak ce........Da kyar bacci ya dauketa mai cike da mafarkai marasa dad'i. Washe gari da safe da rubutu ta fara karyawa malam mai allo ya fara rubuta mata a'lkur'ani ya Umarceta tayi bisimillah tasha kana ta shafe cikinta dashi, sai da ya tabbatar tayi yanda yace din sannan hankalinshi ya kwanta...........Bayan sun karya ne, sai sukayi wanka, rashida ta taya Bitan gyaran gidan ita kuwa Wasila dama tana yin wanka ta kwanta bacci mai nauyi ya dauketa. **** Ya tashi cike da rashin walwala da rashin kuzari gabakid'aya duniya tayi mishi zafi ya rasa abinda zaiyi ya samu sassauci, da kyar ya samu ya kur'bi tea kofi daya, yayi kwance kan kuje daga shi sai singlet da wando iya gwiwa, wayarshi yake dubawa, ya bude ma'adanar hotonanshi, ya lalube pictures dinsu yana kallo, ji yayi hankalinsa ya tashi ya mike zaune yana rawar jiki, dan wayar har sai da ta kusa faduwa ya riketa da kyau, ya kurawa fuskar wayar......Da sauri ya mike ya nufi dakinshi, drowars ya shiga budewa nan naga ya fito da Pose dinta da sababbin wayoyin da ya siya mata, zama yayi gefan bed ya kunna wayar yana dubawa, numbobin mutum uku ya gani tashi data As sai kuma wacce yaga ansa Hdz Camas! da sauri ya dauki numbar awayarshi dan yana zargin itace numbar yarinyar da yake nema tayi mishi karin bayani......sai da ya kira sau uku kafin A daga wayar, Camas na kokarin shiga sabuwar motarta kira ya shigo wayarta koda ta duba taga sabuwar numbar bata damu ba saboda tasan tana hurd'a da mutane sosai Ta daga wayar da sallama a bakinta. Ya amsa a nutse yana fad'in "Ina magana da Hadiza ko."? Tace " Eh ko kace Camas! dan haka jamaa ke kirana." Ajiyar zuciya ya sauke, wanda har sai da taji a kunnanta, ya mike ya kunnanshi makale da wayar ya fito palo ya zauna kan kujera a Yace " Nasan Zakiyi mamakin me magana dake, Ni ne Ahamdu Mijin kawarki Wasila." Camas taji gabanta ya yanke ya fadi har sai da wayar ta kusa faduwa, baki na rawa tace"Yallabai ina wuni." ya amsa a nutse yace."Tambayarki zanyi.' Tace."Allah yasa na sani." jikinta duk yayi sanyi dan tayi tunanin ko zai tambayeta kan kud'adan wasila ne wanda ta riga tayi fata fata dasu mussaman da taji labarin sun bar gari gabad'aya sai ta sake sakin jikinta tana facakarta da kudi. Yace."Ko kin san ina 'kawarki suka koma da zama."? Shiru tayi tana tunani, Yace."Ke nake sauraro." Tace"Yallabai ban sani ba wallahi dan nima sai labari naji a gari wai sunyi tafiya amma dai nafi tunanin ko can kyauyensu suka nufa Garko." Yace."Basu nufi can ba domun kawun su ya tabbatar min da cewar basu je mishi ba ya dai ce yana tunanin sunbi mahaifiyarsu, shin ko kin san inane garin su mahaifiyar tasu." Tayi shiru tana tunani kafin tace"Wallahi na san sunan garin amma ya kwanta min bari yanzu in kira mahaifiyata a waya nasan ita bazata rasa sani ba, insha Allah zan kira ka sai na fada maka." Yace."Okey to ina sauraranki."! Camas! ta kashe waya tana tunani cikin mota, shin me yasa guy nan yake son sanin inda Wasila take, ko dai zai mayar da ita ne a matsayin matarshi, tabdijam idan hakane kuwa wallahi ba zata fad'a mishi ba, key tasa zata tashi mota, kiranshi ya shigo tayi banza da wayar har ta katse....Ta tashi motar ta tanaji wayarta nata famar ringnig amma taki dauka, har sai da ya gaji ya hakura. Yana zauna rike da waya ya rasa ya zaiyi amma yarinyar nan ta shammace shi gabakidaya ya d'o ra buri da tunani a kanta yana tunanin koda sunanan garin da suke ya ji ya san mutukar sun shiga garin tunda ba'ki ne nemansu ba zaiyi wuya ba, bai hakura ba ya cigaba da kiran wayar yana ta adduar Allah yasa ta dauka kawai sai yaji ta kashe wayar ma gabad'aya, ya dinga bin wayar tashi da kallo tamkar wani zautacce. **** Yau kwanansu hud'u a Garko hankalinsu ya kwanta sosai Wasila ta mirmure ta samu lafiya sai abun da ba'a rasa ba, kuma laulayin ya danyi sauki sai dai jefi jefi take amai shima da safe takeyi kafin ta karya......Bata aikin komai Bitan da Rashida suke aikin gidan kullum malam mai allo cikin siyo mata kayan gon yake irinsu d'ata da goba mangwaro da sauransu, sannan kullum sai tasha rubutu da tofi safe da dare, ita kanta yanzu ta soma samun kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya mussaman in ta juya gabas yamma kudu da arewa tana ganin 'yan uwanta da danginta na shige da fice a gidan.....Ita kanta Hajara kullum a tafe take idan bata zo yau ba to gobe zaka ganta tazo kuma bata zuwa gidan hannunta haka kawai sai ta tazo musu da tsarabar kayan kwadayi................. Malam mai allo da kanshi ya shiga kasuwar garin ya siyo musu abubuwan bukata dai-dai karfinshi yanzu babu wani abun da zasu nema su rasa a gidan dai-dai silafas na yawo a tsakar gida mai allo ya siyo musu ko wanne da nashi. ****** 'Bangaran Ahamdu kuwa jinya ya kwanta ta tsayin sati uku har sai da Hajjah tazo gidan tayi jinyarshi wanda sai a lokacin ma ita ta san abinda ke faruwa, aikuwa ta shiga yi mishi fada tamkar ta ari baki, taji ciwon abinda ya aikata shi ba yaro karami ba, an samu yayi auran kuma baije ko ina ba ya fara saki, ai mutane ma sai su daukeshi karamin mutum......Ahamdu baya so ya fada mata dalilin da ya sanya hakan ta faru kawai dai yace mata tsautsayi ne da kaddara, ita kuma tace lallai sai ya kaita gidansu yarinyar tayi bikonta, nan yake shaida mata shima yanzu halin da ake ciki bai san inda yarinyar take ba, Hajjah ta dinga mamaki Yace."Naje can garin nasu gurun waliyyinta shine ya tabbatar min da cewar bata gurinshi amma yafi tunanin tabi mahaifiyarta garinsu, to inda aka samu matsala shine shima bai san wane gari ne ba."Hajja dai ta dauki laifin kacokan ta dora a kanshi ta kuma ce idan haka zai dinga auran yaran mutane yana saki to babu ubanda zai bashi auran 'yarshi mutukar ba kwad'ayayyan abin duniya bane......Tace kuma lallai idan ya samu sauki ya dauketa ya kaita can gurin mai allon a bashi hakuri a bisa abinda akayi mishi, bai musa mata ya amince da maganarta saboda dama can baya tsallake umarinta **** Bayan Sati biyar.......Cikin Wasila ya fito sosai dan har ya hud'a zani yayi kurcici dashi kamar an kifa 'kwarya yanzu yana matakin wata biyar da kwanaki, tayi kyau sosai ta murje ta daina laulayi yanzu komai tana ci ta zauna lafiya ta daina amai da sauransu, sai dai kuma yanda cikin ke mata motsi a cikinta ne yake damunta, ga wani uban cin abinci da takeyi mutakar tana jin yunwa idan bataci abinci ba sai jikinta yay ta kyarma shiyasa kullum bitan cikin d'orawa da saukewa takeyi bata bari abinci ya yanke mata, sabida Wasila ta zama rumbu. ***** Sun shirya tsaf tsaf! shida Hajja suka fito harbar gidan nashi, ya fito da wayarshi yana neman numbar Khalifa sai kiranshi ya shigo da sauri ya kara a kunnanshi Khalifa yace "Anya kuwa tafiyar nan dani za'ayi kuwa! Wallahi Hafsa ce ta tashi da zazzabi me zafi yanzu yanzu zan kaita a dubata muna zargin dai ko an samu 'karuwa ne." Yace."Ayya! Allah ya sawa'ke! babu matsala bari mu tafi kawai insha Allahu zamu shigo nida Hajjah sai mu dubata." Khalifa yace."Okey babu damuwa A mika min gaisuwa gurin aramma." Yace."Zaiji insha Allahu." Yana kokarin kashe wayar ne Khalifa yace."Allah yasa idan kaje kawai ga mutuniyar taka tana cire kafa da kyar! dan cikin nan yanzu nasan yayi kwari." Ya d'anyi ya'ke wanda hausawa suke fad'in yafi kuka ciwo "Khalifa bana tunanin akwai cikin nan fa." Khalifa yace."Kar ka cire tsammani abokina." Yace."To Allah ya amshi adduarka." Khalifa yace."ameen ya rabbi sai kun dawo kenan."? Yace."Insha Allah." Kashe wayar yayi ya mayar aljihu kana ya nufi parking spece lokacin Garba nata 'kokarin karkad'e mota Hajjah na gidan baya a zaune, kawai shima sai ya bude ya shiga ya zauna kusa da ita, Garba ya shiga ya zauna maxauninshi ya kunna motor a nutse suka fita daga gidan, Yayin da ma'aikatan shi ke faman yi mishi fatan alkairi da dawowa gida lafiya. Littafin na kudine......! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biyaba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *61* 'Katuwar tabarma ce shimfid'e a tsakar gidan, Wasila na kwance hannunta rike da mafici tana fifita zafi ake sosai a garin ga dukanin alamu ruwan sama na dab da sauka mai allo yana gefe kan buzunsa da wani ma dai-dai cin allo a hannunshi yana rubutu, Bitan da Rashida suna daga can gefe suna aikin gyara zabbi wanda malam ya sanya d'anshi Tanimu ya yanka su saboda Wasila wai ta dinga samun kuzari da karin jini da lafiya shiyasa ba'a daukar lokaci ake soya mata kaji da dafaffan kwai duk sanda ya fita kasuwar cikin gari kuwa sai ya siyo mata manya manya kifi masu kyau da kara lafiya.........Ya d'an kalleta tana kwance tana aikin fifita sai gumi take Yace."Da alama dai yau garin ruwa ne zai sauka shiyasa zafin ya tsananta da yawa." mikewa tayi zaune tana gyara daurin dankwalinta tace" Kawu malam Allah zafin nan duk ya gigitani na rasa yanda zanyi." Murmushi yay yace."Bake kad'ai ba wasila nima Allah Allah nake in gama miki rubutunan in fita insha iska a waje duba dai dik girman gidanan babu iska ga rana ta game ko'ina." Bitan dake sauraron hirar tasu tace"Ai idan kaga irin wannan ranar to tabbata ta ruwa ce dan haskenta yayi yawa, dubi gabas ka gani hadari ne sosai shiyasa nake sauri in gama ayyukana kafin ruwa ya sauka." Wasila tace"Allah gwara ayi ruwan ko a samu sassauci ni akwana ma anayi.'' Mai allo yasa dariya yana fad'in "Wato ke kanki kika sani ko? idan anyi an kwana ana ruwa 'yan kasuwa suce me? wani fa sai ya fita zai samo abinda zai kaiwa iyali." Tace"Allah Kawu malam zafin ne ya isa Allah na tuba." Bitan tace"Aike Wasila dole ne kiji zafi saboda lalurar dake jikinki dama haka masu ciki suke da jin zafi." Tace"Aikam dubi wuyana kuraje duk sun fito, ni ruwan sanyi ma nake so." Mai allo yace."Wannan ne kuma baki isa ba! za'ayi miki komai wanda kike so amma banda shan 'kankanra." Marairaicewa tayi tace"Kawu malam ba 'kankanra zansha ba ruwan sanyi fa nace don Allah a taimaka asiyo min." Shiru yay yana cigaba da rubutunsa, ta dinga magiya tana karyar da kai! Yace."Bari Tanimu ya shigo." Da sauri tace''Kawu ka bawa rashida kud'in ai tasan gurin." Yace."Bana son aiken rashida gurin nan akwai maza." Shiru tayi tana had'iyar miyau da kyar ma'kogwaronta duk ya bushe! Kallonta yay ta bashi tausayi kwata kwata yanzu baya so yaga abinda zai 'bata mata rai ko ya sata a damuwa, ya kalli Rashida dake wanke hannunta bayan sun gama aikin, yace."Zo kar'bi maza jeki bakin gada gurin masu siyar da ruwan sanyi ki siyo mata kar a bada mai 'kankara." Rashida tace "To ta karaso da sauri ta 'karbi kudin, hijab tasa ta kama hanya ta fita bayan ta dauki wani jug mai dan girma. Tana fita dalleliyar motarshi ta karyo kwana zata shigo cikin layin......Yara yaran dake wasa a bakin hanya suka watse suna ihu da bin motar da kallo, Rashida na tsaye a bakin kofar gidan motar tayi parking a wani fili dake gefen gidan.....Wucewa take kokarin yi yay gaggawar bud'e motar ya fito gabanshi na wani irin fad'uwa, babu abinda yake fad'i cikin zuciyarshi sai alhamdullihi."!!! Rashida tayi saurin dafe kirjinta tana kallonshi Sai kuma ta washe baki wanda kana ganinta kasan tana cikin farin ciki.......Garba ne ya bud'ewa Hajja mota ta fito tana mita da fad'in " Zaman mota ai sai ya saka ciwo tafiya ba tafiya ba 'kafafuna duk sunyi tsami.'' Hannunta ya d'an ri'ke kana ta gyara sa takalminta da lullubin mayafin ta da ya sauka kafadarta........Rashida ta karaso gurin cike da nauyi da jin kunya take musu barka da zuwa! Ya dinga amsawa da sakakkiyar fuska kamar bashi ba sai wani dariya yake yana godewa Allah lallai Khalifa Waliyi ne ashe dai da gaske a maganarshi , ya tabbata tunda yaga 'yar uwarta itama tana ciki........Ya kalleta a nutse yace."Ina fata mai allo na nan." Tace."Eh yana nan yau bai fita da wuri ba ya tsaya yiwa anti Wasila rubuta." Da jin maganarta sai yaji tamkar an tsiyaya mishi ruwan sanyi mai madara a ranshi yaji duk wani kunci da tashin hankalinsa ya kau! sai ya dinga zumud'in shiga gidan, yana fad'in "To kije ki shaida mishi cewar mune muke tafe." Da sauri Rashida ta nufi cikin gidan cikin murna da farin ciki sai kace wacce akace ga mahaifinta ya dawo duniya......... Lokacin da shiga gidan Wasila ta tashi hakanan Bitan ma tana kicin tana gyara tukunya, ta zube a gabanshi da walwala a fuskarta tace"Kawu ga Alhaji Ahamdu mijin anti Wasila nan shida mahaifiyarshi yace a sanar maka da zuwansu." Mai allo ya jinge allon dake hannunshi yana kallonta Yace."To Masha Allah sune suke tafe cikin wannan ranar? maza karkade tabarmar nan ki gyara musu guri bari na shigo dasu Allah yasa ma ban fita ba da munyi sa'bani." Rashida ta shiga karkad"e tabarma tana sake share gurin da marmatsar da abubuwan dake kan hanya.....Mai allo ya sanya takalmansa a nutse ya fita daga gidan.........Tana 'kokarin fitowa daga band'akin ne hancinta ya sha'ko mata masifaffen 'kamshin turaransa da ba zata ta'ba mancewa dashi ba......Gabanta ya yanke ya fad'i lokacin da ta tsinkayi muryarshi yana sallama a gidan ta kuma tsinkayi muryar mai allo yana fad'in "Sannunku da zuwa Alhaji sannu kun d'auko rana Hajiya sannu da hanya, ku shigo ciki......'Kyauran band'akin ta ri'ke gam! jikinta na kyarma! ta dinga fad'in innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! me ya kawo shi? me yazo yayi mana? me yake nema kuma? babu wanda zai bata amsa, ta cigaba da rike kyaure tana rawar jiki tana kuma juyo muryoyinsu a lokacin da suke gaisawa da juna. Jikinta ta duba daga ita sai zanin atamfa dan da zafi ya isheta bayan fitar rashida ruwa ta cika a bokiti taje ta kwara a jikinta wai ko ta samu sassauci babu abinda ke jikinta sai zanin atamfar da dankwalinshi, kamar za tayi kuka yanzu ni ya zanyi na fito ga mutane gashi ba suttura a jikina? tunanin da take kenan ta juyo muryar Mai allo na fad'in " Rashida shiga ki kira 'yar uwarki mana ni kaina a 'kasa ina rubutu ban san sanda ta tashi daga gurin nan da tana kwance a gurin nan da kake zaune." Yafad'a yana nuna masa inda yake zaune, sai ya shiga bin gurin da kallo kamar zai ganta a gurin......Rashida ta duba dakin bata ciki, Bitan dake kokarin fitowa daga d'aki tace"Ai inajin tana band'aki wanka take kasan dama yini take watsa ruwa bata son zafi ai." Mai allo yace."To to koda naji." Ahmadu kuwa jin abinda Bitan tace sai kawai ya shiga rarraba idanunsa a cikin gidan yana laluben ta ina zata fito......Aikuwa sai yaji motsin 'kyaure a wani 'bangare da sauri ya mai da idanunshi gurin......Ta fito a hankali kamar wacce 'kwai ya fashewa a ciki take tafiya, zanin jikinta ya d'angale saboda daurin kirji da tayi sai tayi amfani da dankwalin gurin kare kirjinta da fuskarta.......Gogon ya wani susuce a gurin ya dinga kallonta tin daga kafafunta har zuwa kanta, jikinsa yay wani bala'in sanyi lokacin da ya hango tudun cikinsa dake jikinta, rintse idonsa yayi yana tasbihi ga Allah ya sauke wata gawurtacciyar ajiyar zuciya, Ya bud'e idanunsa da sauri a dai-dai lokacin da take 'kokarin shiga d'akinsu santsin takalmin dake kafarta ya kusa kayar da ita, tayi axamar rike kyauran d'akin tana salati zubewa tayi bakin kofar lokaci guda zanin jikinta ya kusa sa'bulewa dankwalin da ta rufe kanta da kirjinta tuni yayi nashi guri, wani irin 'kullewa marar tayi tana murd'a mata.........kawai ganinsa tayi tsaye a kanta ya wani gigice yana sa'be babbar riga dama manyan kaya ya saka tunda duk sanda zaije gurin mai allo baya zuwa da tazarce na shadda ko yadi riga da wando da malin malin yake sanya........Shine yay bake bake a gurin yana fad'in "Subahanallahi! Kafin ta juyo miryar Bitan na fad'in " Haba Wasila sai da fa na hanaki saka takalmin nan saboda santsin sa sau nawa yana kokarin kayar dake dan dai kawai Allah na kiyayewa ne, kinga ni dai yau ga abinda ya ja miki." Bitan ta 'karashe maganar tana kokarin mikar da ita! Rintse idonta tayi tana fad'in "Wayyo cikina mara ta ciwo Bitan Ya Allah."!!!! Da sauri yay nufi shiga dakin zufa na karyo mishi Hajjah ta dakatar dashi tana hararshi, ita ta shiga dakin suka kama Wasilan suka janye ta daga bakin kofa! Shi kuma ya cire hularshi yana fifita da ita! Wannan wane irin tsautsayi ne? daga zuwanshi yana murna Allah dai ka taimake ni."! Abinda yake fad'a kenan ya koma ya zauna yana cigaba da fifita da hularshi fargaba duk ta cika masa zuciya......Mai allo ya kalleshi cikin naxari sai kawai ya girgiza kanshi yana murmushi a cikin zuciyarshi ya cigaba da d'auraye rubutun dake jikin allon hannunshi, Yace." Tuntuni naji Bitan nayi mata magana kan ta daina saka takalmin nan saboda rashin ji ta'ki dainawa, gashi yana so ya cutar da ita, tunda abin ya kasance da haka da kaina zan dauke takalman na fita dashi.'' Ya aje hular dake hannunshi a gefe yana fuskantar mai allon sosai, Yace."Shine babban damuwar dama, akwai kuruciya da rashin sanin ciwon kai a tare da ita shiyasa take aikata komai yanzu daba dan Allah ya takaita ba da mummunar faduwa za tayi." Mai allo yace."Allah dai ya kikeye." Mikewa yay hannunshi rike da rubutun ya nufi dakin......Binsa yay da kallo yana ji kamar yabi bayanshi sai dai kallon da Hajjah tayi mishi a d'azu yake tunawa. Mai allo ya tsaya bakin 'kofar dakin yana mikawa Bitan rubutun hannunshi da fad'in "Bata tasha kana kuma ki shafe mata jikinta dashi, za taji sassauci rashin jin magana ne irin na mutan yau, takalma zan daukesu yanzu in fita dasu idan ya kasance ta shiga bandakin babu takalmi sai ta shiga haka ai lalurace tunda shi takalmin na baraxana da lafiyarta" Hajjah babah tace"Kwarai kuwa malam ka kwashe takalman a fita dasu tunda suna neman cutar da ita kuma mutukar tana ganinsu to ba zata daina sakawa ba." Mai allo ya sunkuya bakin kofar ya kwashe sabbin takalman 'yan madina ya samu leda ya zuba a ciki ya daure ya rataye jikin wata kusa dake bangon gidan yana fad'in "Anjima idan zan fita zan fita dasu in bawa yara sayi amfani dashi." Yana zaune yana kallon mai allon duk ya rasa abinda ke damunshi hankalinshi na cikin dakin burinshi ya sake tozali da ita da cikin jikinta, jikinsa ne yay sanyi ganin babu wata sakewa irin tada a tare da mai allon yasan dai sun gaisa cikin girma da mutunci amma duk wannan rawar jikin da mai allon keyi masa ya daina magana ma ba sosai sukeyi ba......Hajjah babbah da Bitan suka fito daga dakin, Hajja na fad'in "Ciki fari dama ai kyaga wauta iri iri Allah dai ya rabasu lafiya.'' Duk suka amsa da " ameen." Har dashi gogan da yabi ya zubawa hajja ido yana so yayi magana sai dai yayi shiru ya sunkuyar da kanshi 'kasa, tunda khalifa baya gurin to yanzu hajja itace garkuwa a gurinshi amma shi kanshi yanzu ya gane ya tafka babban kuskure sosai mugun kunyar mai allon ne ma ya rufeshi yanzu da wane ido xai kalleshi yayi mishi bayani dangane da abinda yake tafe dashi. Hajjah ta gyara zamanta a nutse tace"Malam gurinka nazo domin magana mai muhimanci nake tafe da ita.'' mai allo ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Hajiya ina sauraranki." Hajja tace"Malam da farko dai ina me baka hakuri a bisa abinda ya faru, nasan dole rayukan ku su 'baci saboda duk mutumin da akece an saki d'anshi dole ne ranshi ya 'baci mussaman idan anyi bunkice an duba anga babu 'kwakkwaran dalilin da ya sanya aka aikata sakin kamar dai yanda al'amarin nan faru, yarinyar nan wasila an saketa ba tare da wani dalili me karfi ba, tabbas an shiga hakkinta mutuka!! kuma irin wannan sakin shine ubangji baya so.....To amma nasan dai kai mai ilimi ne kuma kasan kaddara dai- dai gwargwado kasan cewar duk abinda Allah ya kaddara sai ya faru a kan bawanshi to sai ya faru, saboda haka ina so dukaninmu mu dauki wannan abun a matsayin kaddara wacce ta riga fata......Kuma hakika naji dad'i sosai da ya kasance cewa sakin an aikata irin wanda musulunci yake so, akwai sauran dama a halin yanzu, dan haka muke ro'ko ayi hakuri yarinyar nan ta koma d'akinta." Mai allo ya sauke ajiyar zuciya mai 'karfi! yana kallon matar.....Hakika matar nada mutunci da kima da kuma sanin ya kamata ko ga yanayin kalamanta, baya jin zai iya wani ja'inja kan maganarta mutukar shi Ahmadu da yarjewarsa take masa bikon matarshi, zai amince da maganarta, sam baya so a zo ayi abu irin na baya ma'ana a koma gidan jiya, Ahamdu ne me aure ba Hajjah ba kuma shi ake so ya furta da bakinshi kan cewar ni wane na janye sakin da nayi wa mata wance na mayar da ita dakinta yanzu tana matsayin matata kamar yanda addinin musulunci ya tanada, to mutukar yaji wad'annan kalmomi daga bakinshi, bashi da tace addini ya riga ya halasta masa matarshi tunda dama ba tayi iddah ba." Yace."To masha Allah Hajiya, ai dukanin abinda kikaga ya faru dama da sanin Allah duniya babu wanda ya isa ya tsarawa kanshi rayuwa face wacce Allah ya tsara masa, auran Ahamdu da Wasila ya 'kare a lokacin da Allah yake so, kuma a sanda yake so zai iya sanyawa su koma su cigaba da zama mutukar rabo bai 'kare a tsakaninsu ba, Ni bani da tacewa anan gurin hakanan itama yarinya bata da magana, tunda a yanzu addinin musulunci ya bashi dama a hannunshi, zai iya yankewa kanshi hukunci, ina nufin ya d'auki aniya a zuciyarshi kancewa ya mayar da matarshi ko kuma akasin hakan duk wannan damar yanzu a hannunsa take, Yanzu ni shi nake jira ya furta min da bakinshi cewar ya amince yarinyar nan ta cigaba da zama matarshi ko A'a."? Mai allo ya 'kare maganarshi hankalinshi a kwance. Hajjah babba tace"Eh gaskiya ne malam maganar ka na kan hanya a yanxu magana na bakinsa dani da kai duka 'yan fatan alkairi ne domin dukaninmu ba zamu haramanta abinda ya halasta ba saboda haka magana yanzu tana gurunka kai muke sauraro." Hajja ta'kare maganarta tana me zuba masa idanunta.........A nutse ya d'ago kanshi zaiyi magana kenan, Ta fito daga dakinsu, sai duk suka zuba mata ido har ta tattako a hankali ta 'karaso inda suke zaune! gaban mai allo ta dur'kusa tana hawaye da rike masa hannuwa tace"Kawu kaine fa kace ba zaka sake takurani ba! Kawu ashe ka manta al'kawarin da kayi min ranar da muka zo garinan kace ba zaka sake yi min tilas ba, zaka barni da kaina na za'bi miji wanda yayi dai-dai da rayuwata na aura." Da sauri! ya d'ago kanshi yana kallonta jin abinda take fad'a! da cikinsa za take tunanin yin aure? Kafin ya gama tunani ya juyo muryarta na shashshe'ka tana fad'in "Kawu ni daina bana son na koma gidanshi, sabida ba zan iya rayuwar da nayi dashi a baya ba, Zargina yakeyi Kawu nasan kasan aure da zargi a musulunci ya haramta ni kawai a kyaleni na haifu lafiya sai a bashi d'anshi." Cikin kuka da yanayi na damuwa take maganar gashi ta ruk'e hannun Kawunta katamau! Dukaninsu suka bita da kallo mussaman gogon da duk jikinsa yayi sanyi ya dinga kallonta yana hango tsabagen 'kiyaysrshi a cikin kwayar idanunta......Sai yaji wani irin ba'kin ciki da takaici ya turnu'keshi! wato har wani kuka take tana nadama da fad'in ba zata koma gidanshi ba, to me yake mata da za tace ba zata koma gidanshi ta cigaba da yin rayuwar da tayi a baya ba? shin tun da suke yaushe yayi zarginta? shine zai fad'awa kowa cewa ita d'in kamila ce kuma nitsatstsiya tunda ta kawo mishi burducinta! bai ta'ba zarginta ba sai sanda wannan al'amarin ya faru!!!! 'Kwafa yay cikin ranshi, ai magana a hannunshi take ba'a hannun wani ba, malam mai allo na shirin yayi magana, Ya rigashi da gyaran murya kafin yace."Ai maganar saki tuntuni na janyeta malam yarinyar yanzu haka a matsayin matata take, wannan dalilin ne ma ya sanya ni dauko Hajja domin tazo ta baka hakuri a bisa abinda ya faru tsautsayi ne da kaddara amma insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba." Mai allo ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace."To madallah Alhaji naji dad'in wannan kalmar taka kuma Wasila zata koma gidanka insha Allahu amma ina so in baka shawara ko kuma in tunasar dakai duk da cewar ka sani, Allah da kanshi ya hallata saki amma kuma baya so a akaita shi, kayi kuskure a lokacin daka yanke hukunci, bance yarinyar ba tayi maka laifi ba tabbas tayi laifi wanda ya dace ka dauki ko wane irin mataki a kanta, amma banda saki, ni a ganina ba tayi abinda za'a saketa ba, saboda ita mace komai girmanta da shekarunta abar tausayi ce ballanta yarinya 'karama irin wannan!? Ka saketa tana da ciki, abinda ba'aso sannan ta amshi laifinta ta nemi afuwarka ka koreta daga gidanka, bazan 'boye maka Alhaji yarinyar nan ta wuya da wannan cikin na jiki kafin su zo nan kenan, sai bayan zuwansu, dana tsananta gurin yi mata tofi da rubutu sannan ta samu lafiya har kazo ka ganta haka, ina fad'a maka da can kwanakin baya kazo da sai ka tausaya mata mutuka dan abincin kirki bata iyaci sai yame yame irin nasu, to Alhamdullhi yanzu lafiya ta samu tana iya cin komai ta zauna lafiya, saboda haka nake baka shawara da kuma tunasarwa kan cewar duk wani abu da matarka za tayi maka na kuskure to ka dinga sanya hankali da nutsuwa kafin ka yanke hukunci akai dan saurin saki bashi ne hukunci ba, wallahi Alhaji da kazo bayan yarinyar nan ta haihu to banga dalilin da zai sanya in tilas ta mata cewar sai ta cigaba da zama da kai ba, zan dai baka dama ka shiga cikin zawarawanta idan har kana da muradin hakan." Ya dinga kallon mai allo cike da d'umbin mamaki! wato shine ma zaibi layin zawarawa sai kace wani shashasha! tsaki yaja cikin ranshi mai allo bai ta'ba 'bata masa rai ba irin yau! amma sai ya shanye ya dake! ya hakura tunda dai magana ta'kare ai shikkenan........A nutse yace."Arrama insha Allahu hakan ba zata sake faruwa dukanin abinda ka fad'a gaskiya ne tsautsayi da 'kaddara basa wuce kan kowa, saboda haka insha Allahu magana ta wuce a gurina zan rike yarinyar nan tsakani da Allah da manzonsa, Saboda haka yanzu sai su shirya kayansu ita da 'yar uwar tata mu tafi in yaso sai ta dinga d'an d'ebe mata kewa har Allah ya sauketa lafiya"...............Da jin maganar dake fitowa daga bakinshi yasa ta mike da sauri ta shige d'akinsu tana wani irin kuka mai cin rai!!? Ta sanya hannuwanta duka ta dunga dukan katifar dake shimfid'e a tsakar d'akin. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whsap numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *62* Rashida ce ta shiga dakin ta tsaya kanta tana kiran sunanta, "Anti Wasila dan Allah ki daina kuka ni wallahi banga abin kuka da damuwa anan ba,Allah na yarda da nadamar mutumin nan yanzu kuma yana sonki dan da baya sonki ba zai tayar da hankalinshi a kanki ba, kawai ki hakura ki koma dakin ki shine mutuncinki damu gabakid'aya." Idanunta jaga-jaga da hawaye ta dago tana kallon 'yar uwar tata dake durkushe kusa da ita, "Rashida nifa bazan koma yanzu ba sai na haihu haka kurrum kai tsaye zaizi yace ya mai dani sai kuma na kwashi jiki na bishi babu wani shiri da da yanxu ba d'aya bane yanzu nasan ciwon kaina." Rashida tace"Eh gaskiya kuma hakane to da zai bari ki haihu shikkenan yafi sauki hakan amma yanzu ku kin koma nasan hankalinsu mai allo ba zai kwanta ba. To a can tsakar gida kuma sai fafatawa ake tsakanin mai allo da Ahamdu da kuma Hajjah inda mai allo ya kafe kai da fata yace Wasila ba zata koma ba sai ta haihu sannan Ahamdu da Hajjah sai rarrashinsa suke da kawo masa misalai wanda suke nuni da cewar in ta koma d'in ai babu matsala insha Allah zasu kula da ita da kyau dan har hajja tayi al'kawarin zama tare da ita har sai ta haihu tayi ar'bain tukkuna sannan ta tafi gidanta, Malam mai allo yayi shiru yana nazarin maganarsu, shi dai hankalinsa yafi kwanciya da zaman yarinyar a gabanshi to amma bashi da yanda zaiyi dole ya hakura ya basu tinda yanzu suke iko da ita, Yana mutukar ganin girman hajja sabida matar tasan abinda takeyi sosai.....Yace."To shikkenan ai tunda kun rinjayeni na bar muku amma kuyi hakuri ku barmin rashida dan naji kana cewa tare zaku tafi da ita." Ahmadu ya marairaice sosai yana rarrashin mai allo kan yay hakuri ya basu har rashidan zamanta tare da 'yar uwarta zai d'ebe mata kewa sosai mai allo dai sun gama kashe mata jiki sai kawai ya amince musu amma kam zai sha kewa dan d'an zaman da sukayi dasu na watanni uku sun saba da juna sun sha'ku sosai. Bitan na kicin ta kwalawa rashida kira ta fito da sauri ta nufi kicin......Bitan ta kammala abinci tsat tsaf ta jera kwanukan silba kan wani katon faranti shima na silba sai she'ki yake kwanuka uku ne akai d'aya lafiyayyan towon farar shinkafa ne tas dashi a nad'e cikin leda d'aya miyar taushe ce da taji gyada da alayyahu da yakuwa, d'aya kwanon kuma farfesun naman zabbi ne sai kamshi yake yayi shar shar dashi, tace"Dauki ki kai musu sai kizo ki dauki wancan jug din ki kai musu ruwa." Rashida ta dauki abincin ta fita. Mai allo ya mi'ke ya bar gurin domin su samu sakewa suci abincin a nutse Ahamdu ya saki jikinshi yaci abincin sosai irin wanda ya Jima baici irinshi ba, hakika ya yarda da kula da tsabtar matar shiyasa ya zage sosai ya cika cikinshi Rashida kam na daki na rarrashin Wasila suci abinci ta'ki hawaye kawai take! tarasa abinda yake damunta, mai allo ya d'aga labulen dakin yana fad'in "Ina Wasila."? Da sauri ta goge hawayen ta tace" Gani Kawu, Yace."Kiyi hakuri kinji ko kiyi hakuri ki kyautata hakuri a karo na biyu na umarce ki da kiyi biyayya kibi abinda nace miki insha Allah zaki samu alkairi a gaba, bani na fad'a ba Allah ne ya hukunta hakan! duk macen da mijinta ya saketa saki d'aya kafin ta 'kare iddah mijinta ya dawo yace ya janye sakin ma'ana ya mayar da ita ko bata so dole ta koma ta cigaba da zama dashi a matsayin mijinta, dan haka nake sake baki hakuri nake kuma ro'konki da kibi mijinki ki koma d'akin ki insha Allahu za kiji dad'i kuma kiyi alfahari anan gaba." Mai allo ya gama kashe mata jikinta da maganganunsa shiru tayi tana tsiyayar da hawaye mai allo ya saki labulen dakin zai tafi tace"Kawu ina da magana." Ya dawo da baya yana kallonta......Tace"Kafin na koma to ina so muje can pataskum gurin Uwani kaga tunda muka zo ba muje saboda yanayin rashin lafiyana ba kuma musan halin da take ciki ba." Mai allo yayi shiru yana nazarin maganarta ta Yace.''To babu laifi sai kuje domun ki shaida mata abinda yake faruwa, yana da kyau a fita hakkinta a matsayinta na mahaifiyarki tasan halin da ake ciki, bari na sanar da Alhajin abinda ke faruwa." Labulen dakin ya saki ya nufi inda suke zaune Sun gama cin abinc i suna hira mutumin ya saki jikinsa sosai dan har ya kira Khalifa a waya ya shaida masa abinda ke faruwa.....Mai allo ya dan jingina jikin bango a nutse yace."Anya Alhaji tafiyar nan zata yiwu yau kuwa."? Yayi saurin kallonshi yana so yaji dalilin da zai hana yiwuwar tafiyar......Mai allo yace."Yarinyar nan na bukatar ganawa da mahaifiyarta hakan nada kyau sosai mahaifiyarta tasan halin da ake ciki ta kuma sanya mata albarka, a zamantakewar auranta, dan haka nace ko zamu bari rana ita yau! insha Allah sai kadawo ka d'aukesu kafin sannan sunje sun dawo ta sake nutsuwa tukkuna. 'Dan 'bata fuska yayi yace."A'a malam ina ganin rana d'aya ma zamu iya zuwa mu dawo Ba tare da anja dogon lokaci ba, ni da kaina zan kai su su dubata insha Allah gobe zamu dawo tare da khalifa sai su shirya muje daga can sai mu wuce kawai.'' Mai allo yace."Babu laifi hakan Allah ya kaimu lafiya." Hajjah tace "Amin amin ya rabbi mungode malam Ubangiji Allah ya kara girma da dattako." Mai allo yace."Babu komai hajiya mudai fatan anan shine Allah yasa anyi kenan Allah ya d'orar da zaman lafiya." Ya d'an gyara zamanshi as'usel kamar ko da yaushe dai ya ciro kudi masu yawa a jikinshi ya dora saman buzun mai allo yace."Malam zamu koma Allah ya saka da alkairi." mai allo yace."Alhaji Ahmadu baka gajiya kullum cikin hidima kudin nan sunyi yawa." Yace."Babu komai malam Allah ya bamu mu bayar meye amfaninsu in ba'a badasu ba." Mai allo yace." To maddalah mungode kwarai Allah ya kara arziki da wadata." Ya amsa da "ameen." yana gyara babbar rigarshi. Hajja ta le'ka d'akin su Wasila tana gyara lullu'binta tace"To Ina kuke zamu tafi Wasila kina ina.''? Wasila dake kwance kan kafita ta fara kokarin mikewa zaune Hajja ta shiga dakin tana fad'in "A'a yi kwanciyarki kinji ko sannu! Dan Allah kiyi hakuri karki sa damuwa cikin ranki insha Allahu abinda ya faru a baya bazai faru ba yanzu ki kwantar da hankalinki ki daina damuwa kuma ki daina kuka." Kanta a kasa tace"Insha Allah Hajja nagode ki gaida gida." Tace"Gida zaiji insha Allahu gobe inanan ina jiran zuwanku." Shiru tayi tana mayar da 'kwallar dake kokarin zubo mata......Hajja ta fito daga d'akin kawai sai ta ganshi ya 'kurawa kofar dakin ido kamar zai shiga, kai kana kallonsa kasan a dame yake daurewa kawai yake yana kokarin dauke abin daga ranshi duk dan kar girmanshi ya zube a idon yarinyar da mutanan gida.....Hajja tace"To ko zakuyi sallama ne naga kanata kallon dakin....Girgiza kanshi yace "Tunda kunyi sallama babu damuwa ai gobe zamu had'u insha Allah." Tace"To babu lefi." Bitan ce ta fito daga daki hannunta rike da wata roba mai murfi mai kamar kwanon sha robar da fulani ke zuba nono a ciki, daya hannun nata kuma ledar fura ce a cure tace"Hajjah ga wannan babu yawa, tun zuwanku naso in dama muku ayyuka sunyi yawa." Hajja ta kar'ba da walwala a tare da ita tace"To godiya muke Bitan Ubangiji Allah ya saka da alkairi kwarai naji dadin yanda kika kar'bemu hannun biyu mungode sosai." Bitan tayi murmushi kawai tana fad'in "Babu komai hajiya mune da godiya ai ku gaishe da gida Allah sauke ku lafiya." Hajja ta amsa da ameen kana tabi bayan Ahmadu da ya riga yayi gaba." Suna tsaye da mai allo suna sallama, Garba dake zaune cikin mota ya fito suka gaisa da mai allon kana ya koma ya jingina jikin motar yana ganin tawowarshi ya hude mishi mota ya shiga Hajja ma shiga ta zauna da sauri ya zauna a maxauninshi , Ahmadu ya shiga dagawa mai allo shima yana daga mishi hannu gami da yi musu fatan sauka lafiya. Bitan ta le'ka dakin nasu sai ta tarda rashida ita kadai a zaune Wasila tayi bacci Tace"Au bacci tayi kenan."? Rashida tace"Eh tun dazu nayi nayi taci abinci ta'ki ci." Bitan tace"Kyaleta na fad'a miki tana tashi daga wannan bacci xata nemi abinci da kanta." Rashida tayi dariya tana fad'in "Aikuwa yanzu ma kawai dan tana cikin 'bacin rai ne amma anti Wasila da abinci ba dama." Bitan tasa dariya tare da fitowa daga dakin. Aikuwa hakane ya kasance da wata masifaffiyar yunwa ta tashi da kyar taje ta wanke bakinta ta nufi kicin Bitan tace"A'a kar ki fara da abinci d'azu malam yace." Kafin kici komai kisha wann an rubutun." Dakin bitan din ta nufa ta kar'bi rubutun ta tsuguna da bisimillah a bakinta tasha ragowar ta shafe cikinta dashi kamar yanda ta saba.....Bitan ta mike da kanta taje ta dauko mata abincin ta gyara zama sosai zauna kana tayi bisimillah ta fara cin abincin........ Sai bayan da ta kammala cin abincin ne tace "Bitan ina Rashida."? Tace" Bata jima da tafiya gidan Innar ku ba, malam yace taje ta fad'a mata abinda ke faruwa. Ta sunkuyar da kanta kasa a hankali tace"Yanzu Bitan sai na koma gidan mutumin nan."? Bitan tace"To ya zakiyi Wasila shine alkairi don Allah kiyi hakuri ki daina wasiwasi insha Allahu babu wani abunda zai sake biyowa baya kuma insha Allahu zaki haihu lafiya." Shiru tayi tana tunanin shin idan ta koma gidan ko wane irin zama zasuyi dashi, ita yanzu ta daina jin sonsa a ranta, kawai zata koma ne ta zauna tare dashi saboda an rinjayeta. Bayan magariba da mai allo ya shigo ya sake tabbatar mata da maganar ya kuma umarcesu da su had'a kayansu su kuma shirya da wuri don kar yazo yana jiransu.........mai allo kwana yayi yana karatun al'kurani mai girma sai da ya had'a izifi sittin kana ya tofa cikin tsabtattaccen ruwan sama, ya samu jarka mai kyau ya zuba ya rufe da murfinta ya aje a guri guda, kana ya mike a nutse ya fito ya d'aura alwala ya wuce massalaci. Karfe tara shaura na safe sun shirya duk suna zaune a tsakar gidan har da Inna Hajara data dako sammako tazo gidan, ita da mai allo sun tasa Wasila a gaba sai fada suke mata mai tafe da nasiha irin fadan da iyaye kan yiwa 'yayansu a lokacin da za'a kaisu dakin mazajensu, Gatan da bata samu ba a farko, sosai take share hawaye tana jin wani iri a jikinta tabbas duk wanda yayi rashi iyaye nagari yayi babbar asara, Ada babu mai nuna mata ga yanda za tayi itace ke zartar da hukunci kan mahaifiyarta da 'yar uwarta dan sai abinda tace sannan Uwani da Rashida keyi, shiyasa takejin wani irin a jikinta, gaskiya babu abinda za tacewa mai allo da Hajara da ita kanta Bitan din dan sun nuna mata kauna da so da kulawa, duk mutumin zai fad'a gaskiya yayi maka fad'a kan wani kuskure naka to babu shakka masoyinka, dan haka sai ta dauki aniyar zama lafiya gidan Ahamdu kamar yanda suke bukata ta kuma yi musu alkawari kan insha Allah za tayi mishi biyayya iya iyawarta."albarka suka shiga sanya mata suna cike da farin ciki mara misaltuwa Wannan karon cikin babbar mota (Sieana) sukaje garin wacce ke dauke da kayan abinci dana masarufi, Ahmadu yayi niyar farantawa mai allo kamar yanda shima ya faranta mishi saboda ya fahimci tsayuwar shi kan Wasilan da abinda ke cikinta yasan bashi da abinda zai biyashi a bisa abinda yayi mishi, sai dai hausawa nacewa yaba kyauta tukwici.....Almajirin malam ne ya hangi zuwansu lokacin da yake kokarin shiga gidan malam din, dan haka koda ya shiga gidan sai yake shaidawa malam din zuwansu, Wasila taji gabanta ya fadi har sai da ta rasa miyau a bakinta, tayi shiru tana kokarin maida kwalla ita har ta gaji da zubda hawaye..........Mai allo ya shigo dasu, cikin gidan yana musu barka da zuwa, Garba da Hadi sune suka shiga shigo da kayan abincin cikin gidan malam ya cika da mamaki yana so yayi magana Khalifa yayi saurin tareshi da fadin malam kada kace komai don Allah ba wai munyi hakan bane domin mu biyaka mun san bamu da abinda zamu biya dashi wannan ihisani ne kawai mukayi maka saboda karamcinka." Mai allo ya girgixa kanshi yana fadin anya abun baiyi yawa ba kuwa? Khalifa yace."Beyi yawa ba malam ka sanya albarka kawai." Yace."To nagode kwarai Allah ya sanya alkairi ya kara arziki da wadata." Khalifa ya amsa da ameen ya rabbi." Inna Hajara kuwa mamaki take sosai ita bata ta'ba 'karewa mijin Wasilan kallo ba sai yau! sai take ganin kamar ma yafi karfin wasilan dama haka Allah ke tsara lamarinshi Addua ta shigayi kan Allah ya xaunar da ita lafiya a dakinta. Malam ya sanya Tanimu ya dauki jakar kayansu ya kai motar, kana dukaninsu suka fito daga cikin gidan......Ita dashi aka bari a baya, sai ta dinga ra'bewa tana so yayi gaba shi kuma ya'ki tafiya da sauri yana tafiya sannu sannu yana kallonta ta gefan ido sai 'boye fuskarta take ci kin mayafi, tana kauda kanta, tuntu'be tayi da bakin 'kofa yayi gaggawar rike mata hannunta yana d'an janyota jikinsa, da sauri ta bude fuskarta tana zumbura bakinta, jikinta ta janye daga nashi, ya danyi gyaran murya a hankali yace."Meye amfanin rufe fuskar da ki keyi ke ba amarya ba."? Shiru tayi mishi ta dan 'kara sauri gabanta na fad'uwa bata so wani ya juyo ya gansu suna jerawa, ganin yanda take tafiya da sauri da sauri yasa shima ya 'kara sauri har suka iske inda motar take......Khalifa da kanshi ya bude mata bayan mota ta shiga, Rashida na kokarin ta shiga ta zauna kusa da ita yace."kanwata zo ki zauna nan." Sai ta zauna inda ya nuna mata,Inna Hajara kuwa hawaye ta fara sharewa ta kasa daurewa, ganin hakan ya sanya su Wasila suka fara kuka mai allo yace."Wannan shirme ne hajara Alhaji ku tafi kawai idan ba haka yanzu xata sanya yaran nan koke koke."! aikuwa yana ganin Wasilan na kuka yayi saurin shiga motar ya zauna kusa da ita, yana d'aga musu hannu mai allo ya mi'ka mishi ma dai-dai ciyar jarkar rubutun dake hannunsa yace."Kullum ta dinga tsiyaya tana sha safe da dare tana kuma shafe cikinta dashi." Ahmadu ya kar'bi rubutun yana godiya da fad'in "Insha Allah malam Allah ya biya bukata." Mai allo ya d'aga masa hannu yana fad'in "Ku sauka lafiya Allah ya tsare Alhaji Allah ya saka da alkairi." Shi da khalifa suka amsa da "Ameen malam Allah ya saka da alkairi." sai da motar ta 'bace daga gurin sannan suka koma gida duk jikinsu a sanyaye mussaman Bitan da Inna Hajara, to shima dai mai allon daurewa kawai yake yi saboda yayi mutukar sha'kuwa da yaran kuma yana jinsu cikin ranshi. Hawaye take sharewa tana d'an kauda kanta tare da kare fuskarta da mayafinta, 'kamshin turaranshi da hucin numfashinsa duk ya isheta ta rasa ya za tayi gabanta sai fad'uwa yake, sai kawai taji hannunshi a jikinta ya kamo hannunta dake cikin mayafinta ya ri'ke cikin nashi a hankali ya soma murxawa yana kallonta ta gefan idonshi.......Kokarin cire hannun nata ta shigayi ya rike tam! ya had'e 'yan yatsunsa da nata guri guda ya rintse gam gam! kamar wanda yake bata amana ko kuma yake d'aukar mata al'kawari!!! Ajiyar zuciya ta shiga saukewa ta kauda kanta tana kallon hanya, a hankali taji hucin numfashinsa dai dai fuskarta, a razane ta juyo sai kawai fuskarsu ta had'u guri guda! bakinshi ya sauka kan nata bai jira komai ba, ya sanya harshensa ya lashi le'bunanta yana sakin ajiyar zuciya! ya d'auke fuskarshi ya gyara zamanshi kamar bashi ba, Ta dinga jin wata irin fargaba da fad'uwar gaba sai kawai ta shiga rarraba idanunta cikin motar tana kici kicin kwace hannunta dake rintse da nasa......... Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *63* Jin yanda yake sake rintse hannunta dake cikin nashi ne ya sanya tayi saurin kallonshi, suka had'a ido tayi saurin saukar da nata 'kasa tana motsi da bakinta, so take tayi magana amma saboda tsabar kwarjinsa ya sanya takasa, sai kawai ta cigaba da kallon gefe guda tana jin yanda yake shafa tafin hannunta a hankali a hankali, lokaci 'kankani taji duk jikinta yayi sanyi idanunta suka soma lumshewa da alamun bacci a tare da ita, kanta ta dora jikin murfin motar tana takure jikinta hade da runtse idonta gam! wannan abin da yake mata sam bata so wani ya gani a cikinsu khalifa dake gabansu, Allah ma yasa hirar da sukeyi ta dauke musu hankali da yake rashida akwai saurin sabo duk garin da suka wuce sai ta tambayi khalifa sunan garin shi kuma ya fada mata tare da cikakken bayani.......Yana kallonta ta takure jikinta a jikin murfin mota idanunta a rufe, sai ya sake matsawa jikinta sosai ta bude lumsassun idanunta da suka soma sauyawa bacci ne ko meye oho! a hankali ya kamo ha'barta ya d'ora kanta kan kafad'arshi kana ya zura hannunsa 'kar'kashinta ya ri'ke 'kugunta sosai ya matso da ita jikinsa ya ri'ke da kyau!! Rintse idonta ta sakeyi tana sauke ajiyar zuciya gabanta na d'an fad'uwa kad'an-kad'an! Kamshin turaran jikinsa ne yayi masifar tafiya da imaninta abinda ya sanya ma kenan ta sakeyin luf a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, jikinta ya soma shikawa bacci na fizgarta mai dad'i......Jin shirun tayi yawa ne ya sanya Khalifa d'an juyowa yanayi masa magana, sai kawai idanunsa ya gane masa abinda ke faruwa, Abokin nashi ya gani ya wani yi la'kas! dashi hankalinsa kacokan na kan Wasilan da bacci me nauyi ya dauketa a jikinsa, shi kuma ya kurawa fuskarta ido fuskarshi dauke da wani munafikin murmushi.....Khalifa ya danyi gyaran murya yana fad'in "Kaga yanzu mun wuce gaidan! garinsu Alhaji Yunusa mutumin nan dake kawo mana shanun sallah." Ya dago kanshi yana kallon khalifan yana ya mutsa fuska yace."Nagane shi koba wannan madamfarin mutumin ba? kasan akwai sallahr da ta gabata nasa shi ya kawo min shanu irin wanda nake sadaka dasu, ya kawo marasa lafiya cikin guda goma uku ne suka rayu naji ciwon abinda yayi min shiyasa na daina siyan shanu a gurinshi." Khalifa yace." Nima tuntuni munyi hannun riga dashi dama ai nine na had'aku dashi ko?" Gyad'a kanshi kawai yayi ya sake gyara zamanshi wanda hakan ya sanya kanta ya sauka a kirjinsa a maimakon kafadarshi, gyara ta yay sosai ya tallafeta da hannunshi guda.....Khalifa ya kalleshi shima ya kalleshi sai yayi mishi nuni da Rashida da bakinshi, basarwa yayi ya nunawa Khalifa shi ina ruwanshi da wata rashida! Abinda basu sani ba kuwa shine ba rashida ba har su Garba sun d'an hango abinda ke faruwa basarwa kawai sukayi......Murmushi kawai Khalifa yayi ya juya yana mamakin abokin nashi, idan ance masa yana son yarinyar sai yace ba hakaba gashi lokaci 'kan'kani duk ya wani susuce a cikin mota. Kuluwa ta fito daga cikin d'akinta hannunta rike da wani 'kullin kaya, wanda zanin da aka d'aure kayan yayi da'kal-da'kal da daud'a, ta nufi inda Uwani ke sunkuye da wata 'katon baho a gabanta, wacce ta cika ta da kayan wanki ta zuba klin da sabulu a hannunta tana cud'awa! Kuluwa ta dire 'kullin kayan dake hannunta tace"Uwani idan kin gama wankin dan Allah ki d'an sa'be wa 'kananan yaran nan kayansu tuntuni nake so nayi wanki bani da sabulu kina dai kallo kwana biyu gidan sai a hankali yanzu Kawunki baya fita komai ya rinca'be mana." Uwani ta d'ago kanta cikin tsananin wahala da gajiya tace"Kuluwa kinga dai sabulun nan banawa bane na mutane ne dan Allah ki bari a wankewa mutane kayansu ya fita wai me yasa duk sanda zanyi wanki sai ki kwaso min kayan yara kice na wanke alhalin kin san sabulu da omo ba nawa bane nima aikatau nakeyi a biyani." Da jin abinda Uwani ke fada sai Kuluwa ta fusata ta soma sirfa mata masifa da fad'in wallahi duk sanda ta sake yi mata musu kan abinda ta umarce ta dashi to sai ta bar mata gidanta." Uwani dai ta cigaba da gurxar wankinta bakin ciki duniya kamar ya kasheta, tun safe take wankin jama'a har yanzu bata karya kummalo ba, ko da yake sai ta g ama wankin ta kai sannan zata samu kudin da zata siyi abin karin dashi dan tuntuni Kuluwa ta daina bata abin kari a gidan, da daddare kawai take bata abinci shima d'an mitsitsi idan towo ne kuwa sai ta lakata mata 'karshen kwasa cikin kwano wanda yaro 'karami ma yaci ba zai isheshi ba. Tana gurxar wanki hawaye na 'kokarin su'bce mata, wannan wace iriyar masifa ce take cikinta? tayi dana sani tayi nadama tayi da ace abinda ya wuce zai dawo baya data yi gaggawar gyara kuskuranta, wannan wuya da take sha tasan duk itace ta jawowa kanta, Allah ya kawo musu dauki ita da 'yarta ya had'ata aure da mai kudi mai mu'kami amma sabida hange da mummunar kaddara ta dinga zugar 'yar tata ta kashe auranta, yanzu wa gari ya waya? wahalar da take ciki a yanzu ta wuce wacce taci a baya, a gidan Kawunta ana bata abinci taci ta koshi anan kuwa sai dai ta nema ta ciyar da kanta, Kawu Madu sallamamman namiji ne mijin tace sai abinda kuluwa tace ayi a gidan yake yi shiyasa duk abinda yake faruwa da rayuwarta baya tofawa, tun bayan tafiyarsu Wasila da kwana uku Kuluwa ta soma gallaza mata kyara! da hantara! da masifa! da kuma horan yunwa! ganin hakane ya sanya Ta nemi Inna Tabawa tana kuka take shaida mata halin da take ciki, itama Tabawar ta tausaya mata sosai sai da bata da yanda za tayi tunda itama talakace, sai kawai ta bata shawarar kan cewar ta kama sana'a sai ta rike kanta, saboda ba komai ne yake sanya Kuluwa nayi mata rashin mutunci ba saboda tana bata abinci ne." Uwani tace"Dama can baya nayi sana'ar wanki indai zan samu anan to wallahi zanyi na rufawa kaina asiri." Tabawa tace"Kada ki damu idan Allah ya kaimu gobe kizo gidana mu tafi cikin gari Unguwar amare zamu mubi gidajen mutane idan suna da wankau su bamu." Uwani tace"To shikkenan." Aikuwa gari na waye wa Ta shirya ta tafi gidan tabawa, suka dauki hanyar cikin gari.......gida biyar suka samu wanki aikuwa Uwani ta zage ta wanke musu kayansu ta shanya musu tsaf suka biyata kudinta, ranar sai yamma suka dawo gida, Uwani ta bawa Tabawa kudi cikin kudin da samo ta 'boye sauran a jikinta......Tun daga sannan Uwani ke zuwa unguwar amare tana musu wanki watarana kuma ta d'oro kayan saman kanta ta tawo dashi gida sai ta wanke su bushe tsaf sai ta kai musu su bata kudinta. Da 'kyar Rashida ta iya gane hanyar gidan ta dinga nunawa Garba hanya yana bu ta cikin kunyar gonakin mutane gwajab gwajab din da motar take ya sanya ta bud'e idanunta tana d'an motsawa, sai kawai taga duk rabin jikinta a jikinshi, yayin da shi kuma yayi wani irin zama a cikin motar kamar wanda zai kwanta yayi hakan ne domun taji dadin yin baccin a jikinsa........Da sauri ta mike zaune tana gyara xamanta had'e da gyara mayafinta ta d'ora saman kanta.......Ya mi'ke zaune sosai yana ya mutsa fuskarsa, hakuri kawai yake yi amma wannan kwanciyar da tayi a jikinsa ta ya mutsa shi, sosai ya d'an saci kallonta sai yaga tana hamma! da alamun baccin bai isheta ba, sai kuma ya mutsa fuska takeyi cikinta ne ya soma 'kullewa yunwa na sasakarta dama 'ka'ida ne idan tayi bacci ko yayane ta farka sai taci abinci.......Jikinta ne ya soma rawa, ta dinga zare ido tana mutsu mutsu ta rasa ya za tayi a yaron dake cikinta yana mata wani irin motsi da zillo tare danno mararta kamar me shirin fitowa waje, cikin rawar murya tace"Rashida ina kayanmu suke."? Rashida tayi saurin juyawa tana kallonta ganin yanda idanunta suka kad'a ne ya sanya ta gane yunwa takeji da sauri tace" Suna bayan mota." Still murya na rawa tace"To sai kizo ki dauko min kin san dai cewa nayi ki rike min a hannunki saboda zan iya bukatarshi cikin ko wane irin yanayi me zai sanya kisa a cikin akwati.'' Rashida tace."Yi hakuri anti Wasila ai mun kusa sauka." Tsaki taja tana motsa bakinta.....Ya kalli Rashida cike da kulawa yace."Menene."? Tace." 'kwai dafaffe ne Bitan ta bata shine tace na ri'ke mata a hannu na ni kuma wallahi na manta nasa a cikin jakar kayanmu gatacan a bayan motar." Shiru yayi kawai ya juya bayanshi da kanshi ya kinkimo jakar kayan nasu ya d'ora saman cinyarshi ya zuge zif din jakar ya soma dubawa.....Nan ya d'auko daurin leda yaluwa da dafa ffan 'kwai a ciki kusan guda ashirin, a jikinta ya d'ora ledar ya mai da zif din jakar ya zuge kana ya maida ita inda take ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Gashinan karkiyi kuka gama naga shi kike shirin yi." Shiru tayi masa ta cigaba da kokarin kwance ledar.......Kar'ba yay ya kwance mata ya d'auko d'aya ya soma 'bare mata , ya mi'ka mata ta kar'ba da sauri gutsira biyu tayi masa ta cinye.....Tana kallon hannunshi dake kokarin 'bare mata wani, Haka dai yayi ta aikin 'bare mata kwai tana taunewa sai da taci guda tara sannan ta hakura ya mi'ka mata ragowar ruwan swan din da yasha d'azu ta 'karba tana sha tana lumshe idonta sai yanzu taji dama dama a jikinta. Uwani na tsaka da shanya kan katanga taji tsayuwar mota, dake katangar bata da tsayi sosai ana hange na waje kafin ta ankara taga Rashida ta fito daga cikin motar Wasila ma ta fito da sauri ta ajiye rigar dake hannunta ta nufi cikin dakin da take kwana mayafi ta dauko tayi hanyar fita tana kokarin yafawa a jikinta, a soro sukayi kicibus da Rashida sai ta rungumeta tana fad'in "Rashida sai yau kuka tunani dani ko? ke da waye a cikin mota ina Wasila ya jikin nata."? Rashida ta dinga kallon mahaifiyarta ta ganinta gaje gaje yayi masifar daga mata hankali, Wasila ta shigo ta gansu sai itama ta shiga bin Uwanin da kallo jikinta sharkaf da ruwa......Gashi duk tayi wani wujuga wujuga da ita. Uwani ta rumgume Wasila tana hawaye tace" Yarinyar nan kullum dake nake kwana nake tashi a raina Alhamudullihi jiki yayi kyau masha Allahu ga cikin ki ya girma dama ai nasan mutukar kun koma gaban mai allo zai kula daku mutum ne shi mai tausayi kuma yana kaunarku." Wasila da Rashida suka shiga binta da kallo jin abinda take fad'a kan mai allo wai yau Uwani ce ke yabon mai allo lallai duniya. Gidan suka shiga gabad'ayansu, Wasila ta dinga bin gidan da kallo ko ina kaca kaca da kazanta iri iri ga wani wari na tashi da alama shaddar gidan ta cika tana bukatar agaji warin yayi yawa.....Ta dinga bin mahaifiyarta da wani irin kallo na tsantsar tausayi da jin kai. a hankali tace"Uwani wannan wane irin 'kuraje ne a jikinki? dubi yanda fatar jikinki ta kod'e kinyi wani iri duk kin rame."! 'Kwallah ta cika kwarmin idon Uwani tace"Ku mu shiga ciki babu komai." Bin bayanta sukayi suna mamaki tabbal akwai abunda ke faruwa da mahaifiyar tasu.........Kuluwa ta fito daga dakinta kirjinta daure da dadd'aud'an zani!!! kanta babu d'ankwali tamkar hammatar d'an iska yayi wani cibiri cibiri dashi dan saboda tsabar dauda gashin kan nata har ya soma d'aukewa da kanshi wani guri da a kwai wani gurin babu.....Ganinsu Wasila yasa tasha kunnu tana fad'in "Ku kuma yaushe kuka zo."? Wasila tayi saurin kauda kanta daga kallonta dan ji tayi tsigar jikinta na tashi kallon gashin kanta ya sanya mata tashin hankali amai na taso mata....Rashida tace" Yanzu muka zo Baba mun same ku lafiya."? Kuluwa tace "Lafiya lau ina fata dai yau zaku juya domin dai muma bamu da abinda zamu baku koda yake dai ga uwarku nan na neman kudi zata iya daukar dawainiyarku." Babu wanda yace mata ta tafasa ballanta ta sauke suka shige dakin ina Uwani ke zaune tana jiran shigowarsu......Nan suka tarar da ita a zaune a gefen wata guntuwar tabarma ta zabfa tagumi! Wasila ta dinga bin dakin da kallo daki sai kace zai rufta ya durkushe gashi babu labule babu ledar kasa sai wata guntuwar tabarma wacce take nuni da cewar nan ne makwancin mahaifitar tasu.....Kwallah ta zubo mata murya na rawa tace"Uwani wannan wace irin rayuwa kike ma'kaskanciya, wannan d'akin da kike ciki ya ru'be wallahi saura kad'an ya rufta bakya tsoro watarana ya rufta dake." Uwani na hawaye tace"Ya zanyi Wasila! Ya zanyi? nice na cuci kaina na kuma cutar daku na tabbata da kina gidan Alhaji Ahmadu da duk wannan wahalar bamu shigeta ba, nasan da tuni munfi karfin gurin zama da ci da sha da suttura, na cuci kaina na cutar daku Ubangiji Allah ya yaye mana wannan masifa."!!! Ganin tana kuka sai suma suka fara kuka ta goge hawayenta tana fad'in "Idan dan kunga ina kuka kuma kukeyi to na daina yi sai kuyi shuru." Wasila ta goge fuskarta tana kallonta.....Uwani a nutse ta soma basu labarin wahalar da takesha a gidan da yanda kullum take cin ruwa sai kace agwagwa. Wasila tace"Ai dole sanyi ya kamaki Uwani wannan wace irin masifa ce ace kullum mutum na cikin ruwa dubi fatar jikinki ta kod'e ta bushe ga wasu kuraje marasa kyawun gani sun feso miki a jiki. Uwani tace"Wai sunanan ina sha musu magani da ai sunfi haka yawa a jikina." Wasila ta shiga girgixa kanta tana tunanin yanda za tayi ta kubutar da mahaifiyarta daga wannan ukuba. Uwani ta kalli Rashida tace"Wai waye ya kawo ku a mota ne."? Rashida tace"Alhaji Ahamadu ne mijin aunti Wasila." Da sauri ta kalli Wasilan tana neman karin bayani......Rashida itace ta shiga fada mata yanda al'amura suka faru.....Uwani ta dinga washe bakinta tana fad'in "Alhamdullhi Allah nagode maka daka amsa adduata kullum.burina mutumin nan ya dawo garemu naji dadin wannan zuwan naku kuma yau zanyi bacci harda munshari." Wasila tace"To sai ki sauya kaya kije soro ku gaisa dan da kunya a shigo dasu wannan 'kazamin gidan." Uwani ta mike da sauri ta bude jakar kayanta ta dauko atamfar data rage mata dan duk kayan da tazo dasu Kuluwa ta sace taje ta siyar, sai dai kawai in ta fita taga kayanta a jikin mutane idan ta tambayesu sai suce kuluwa ce ta siyar musu shaddar wasila ma data sace gidan ma gari ta kai suka siya.........Suna kokarin fita daga cikin gidan Kawu Madu ya shigo gidan yana washe bakinsa hannunsa rike da kud'i sabbin 'yan dubu dubu kar kar dasu......Kuluwa yake kwad'awa kira ta fito daga d'aki da saurin gaske dan har zaninta na 'kokarin fad'uwa ta rike da kyau! tana fad'in "Malam ya akayi ne." Yace."Ki fito kizo ki dangwali arziki ki barshi ashe yarinyar nan Wasila matar babban mutum ce, ikon Allah yafi gaban wasa! Kuluwa kinga uban kudin da mijinta ya bani yana waje shi da abokinsa sunzo cikin wata 'karuwar mota kamar jirgin sama."! A d'amauce! Kuluwa tayi hanyar waje tana tafiya kamar zata kifa 'kasa saboda sauri! Kwata kwata ta manta a halin da take ciki babu dankwali da riga daga ita sai daurin kirji..... Littafin na kudi ne....! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah What'spp numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *64* Da sauri Uwani ta tare bakin 'kofar fita tana kallon Kuluwan cikin mamaki tace"Haba Kuluwa dubi yanayin da kike ciki babu suttura a jikinki kanki babu dankwali sannan kuma kike 'kokarin fita haka gaban siriki karfa ki manta mutumin nan babban mutum ne kamar yanda Kawu ya fada miki idan kin fita haka ai kin zubar mana da kima da mutunci ." Kuluwa ta hau ya'ke tana washe baki tace"Wallahi duk na manta babu riga a jikina Uban kudin dana gani hannun Malam su suka gigitani amma bari inje in sanyo riga ku jirani dan Allah." Da sauri ta koma cikin gidan jikinta sai rawa yake.....Wasila da Rashida suka bita da kallon mamaki matar mayyar kudi ce duk ta fita daga hayyacinta.....Kawu Madu kuwa na tsaye sai dariya yake yana ta dangwalar miyau a hannunshi yana lissafa kudin hannunshi, kamar zautacce ya kalli Uwani yace."Uwani kudin nan dubu hamsin ne wallahi! kai masha Allahu gaskiya naji dad'in zuwan mutumin nan Uwani ashe haka Allah yayi wa 'yar arziki amma saboda baki da hankali kika kashe mata aure, saboda kina mata bakin ciki, waye ya fada miki yanxu ana wasa da auran irin wad'annan mutanan? ai duk abinda ya faru ya fad'a min yanzu kafin na shigo sai ku godewa Allah da Allah yasa ya mai da auran dan da bai mayar da auran ba to da kun cutar damu wallahi dan wannan arzikin sai da mugani a nesa amma yanzu ko banza nasan zamu dinga samun zakka a kai a kai! idan Allah ya nufa ma wataran sai da kawai naji ance na fito an biya min kujerar makkah." Kawu Ya 'kare maganar tashi yana dariya had'e da gyara babbar rigarshi yana sake gyara xaman kudinshi a aljihu........Kuluwa ta karaso cikin wata kod'ad'diyar atamfa da wani ya mushashshen mayafi da duk ya tattare saboda tsabar yaga jiya da yau wai nan sune karshen adakarta, sai wani washe baki take ta kalli Uwani tace"Ai haka yayi ko."? Uwani dai shiru tayi dan bata da abince wa sam ma bata so Kuluwa ta bisu gani take zata iya yin wani abun na rashin hankali ita kuma bata so yanzu mutuncinsu a zube a gurin Ahmadu......Kawu ne yay gaba suka biyo bayanshi A babban soron gidan suka tsaya Kuluwa sai l'eken kofar gidan take dan Kawu cewa yayi su tsaya anan zai shigo dashi Kuluwa duk ta 'kago sai d'aga kai takeyi tana lekawa.....Wasila taji tamkar ta gaura mata mari shin wai ita wannan matar wace irin mata ce mara kintsi da kamun kai.? 'Kamshin turaranshi ne ya bakuncin hancinsu gabad'aya, Uwani ta gyarq lullubinta hade da sunkuyar da kanta 'kasa kunyar hada ido take dashi sosai, Ita kam kuluwa fad'i take "Sannunku da zuwa Alhaji sannuku." Ahmadu da Khalifa suka samu gefe suka tsuguna a nutse aka fara gaishe gaishe, Ahmadu ya kasa tantance mahaifiyar matar tashi duk da ya ta'ba ganinta sau d'aya amma dai baya tunanin Kuluwa itace saboda yanda ta za'ke da yawa sai banbad'anci takeyi tana musu hirarraki Mikewa sukayi a tare Khalifa ne ya fara yin gaba shi kuma ya tsaya yana gyara rigarshi, kuluwa ta tsura mishi ido Kudi ya fito dasu daure a kyaure ya mi'kawa Wasila dake gefanshi a hankali yace."Ki bawa Momy ko." 'Kin 'karba tayi Kuluwa tayi wuf ta kar'be kudin tana washe baki da fad'in "Ai kunya ba zata bari ta kar'ba Alhaji Mungode kwarai Allah ya tabbatar da alkairi ya baku xaman lafiya." Uwani da Wasila ba suji dadin Abinda Kuluwa take ba, sai basu da yanda za suyi da ita......... Kuluwa da Kawu har bakin mota suka rakosu suna musu godiya da fatan alkairi, jama'ar garin sun taru suna mamakin irin bakin da Kawu Madu yayi, sai bayan motarsu ta 'bace daga gurin ne Kawu ya shiga yi musu bayani cewar Ai sirikin sa ne mutumin dake auran 'yar gidan Uwani 'yar 'kanwarshi..... Uwani cikin gidan ta koma ta shiga daki ta had'a tagumi hawaye takeyi sosai takejin kewayar 'yayan nata amma ko babu komai zamansu a gidan Ahmadun sai yafi mata kwanciyar hankali fiye da su zauna a wani guri itama ta yarda mutumin nason 'yarta dan da baya sonta da bazai mayar da ita ba duk da tarin laifin da tayi masa. Bayan azuhur suka sauka gajiya gami da jiri da zaman mota suka taru sukayi mata yawa, dan da kyar ma ta iya fitowa daga motar kafafunta duk sun sage sunyi tsami! Tana dan ya mutse fuska t a rike hannun Rashida tana kokarin zama gefan shuke shuke! Ya fito daga cikin motar hannunshi rike da babbar rigarshi, Garba ya kar'bi rigar da wayoyinshi, hankalinshi na kansu yaga tana matse fuska cike da kulawa yace."Lafiya menene."? Shiru tayi mishi." Ya kalli Rashida yace."Ku shiga ciki mana karki bari ta zauna anan." Rashida ta kama hannunta suka soma tafiya, 'kafarta ta dama ce ta ri'ke ta kasa takuwa, ta rintse idanunta tana salati, dama tun a cikin mota takejin yanda cikin ke tattare mata yana dunkule mata guri guda, kwallah ta cika mata ido bakinta na rawa tace"Rashida 'kafana d'aya ta ri'ke gefan marata ya daure." Rashida tace"Ki daure anti wasila zaman mota ne yaja mu shiga ciki ka zauna sai in matsa miki kafafun naki." Yana tsaye suna magana da Garba yaga sun tsaya sai ya sallami Garba ya nufi inda suke.......Rashida na ganinshi tace"Wai kafarta ciwo take." Yace"Subahanallahi! to me ya jawo hakan."? Rashida tace "Nima ban sani ba watakila kuma zaman mota ne." Ya kalli Wasilan yaga tana kuka tana kokarin zama kasan gurin......Yace."Kada ki zauna anan mana tashi mu shiga ciki ki samu kiyi wanka sai ki kwanta ki huta." Shiru tayi ta'ki tanka masa bala'in haushinsa takeji a ganinta ba kowa ne ya jawo mata wannan masifar ciwo ciwon ba sai shi.....Ganin tana had'a zufa a gurin rana na dukanta yasa ya sunkuya ba tare da yayi shawara da ita ba ya dauketa cak daukar jira jirai yayi mata ya nufi cikin gidan da ita......Duk da halin da take ciki sai da taji wani iri kunyar ma'aikatan gidan duk ta rufe ta tasan dai dole idan wasu ba sugani ba wasu zasu gani Uwa uba ga 'Kanwarta Rashida, rufe idanunta kawai tayi ta 'boye fuskarta cikin 'kirjinshi.....Rashida tabi bayansu tana sinne kai fuskarta dauke da murmushi sosai mutumin yake burgeta saboda irin kulawar da yake bawa 'yar uwarta. Hajja tace"Subahanallahi! me ya faru haka."? Yace"Zaman mota ya sanya kafafunta tsami ta kasa tafiya dasu." Hajja tace"Aifa dama zaman mota ma ga mai lafiya babu dadi ballanta ga mai ciki sannu Wasila ka shiga da ita ciki tayi wanka sai suci abinci su huta.'' Baice komai ba ya shige da ita bedroom dinshi, kai tsaye bad ya kwantar da ita ya nufi toliet. Mikewa zaune tayi a hankali tana d'an mikar da kafafunta wacce tafi takura mata da ciwo ta dan tasa kad'an! ta rintse idonta tana kiran sunan Allah can taji zillo a cikinta ta bude idanunta da sauri tana sauke ajiyar zuciya, yanzu zai isheta da kusurkusur a ciki idan ba abinci taci ba babu zaman lafiya.....Fitowa yay daga toilet din yana tattare hannun rigar dake cikin shi tayi saurin dauke kanta ya 'karaso inda take ba tayi aune ba taji ya dauketa, da sauri ta kalleshi ya d'aga mata girarshi guda, dauke kanta tayi tana zumbura baki kamar zatayi kuka itafa wannan za'kewar da yake a kanta sam baya burgeta taga sai wani rawar jiki yake mata tasan dai ba komai ya sanya shi yake mata hakan ba sai dan tana dauke da cikinshi.....A hankali ya dure ta tsakiyar bandakin yana mata wani munafikin kallo ya dora hannunshi a wuyanta, tureshi tayi ta jingina da bango (garu) gabanta ne ya soma faduwa, Ya sake matsowa kusa da ita, sai kawai ta saka kuka tana ture kirjinshi, cikin taushin murya yace"Wanka zanyi miki ba wani abu ba, ke kuka baya miki wuya ko."? Cikin nauyin baki da yanayi na gajiya tace"To ka barni mana nayi da kaina da can kaine kake min?" Ya shiga kallonta yana girgiza kanshi, yace." Daga yau nake so duk wata d'awainiya taki ta dawo hannuna ni mutum ne mai tausayin masu lalura irin taki, insha Allah mutukar ina gida zan dinga dauke miki dukanin laluranki har Allah ya saukeki lafiya." Shiru tayi tana kallonshi anya kuwa zata amince da wannan dad'in bakin nashi? itafa tafi tunanin saboda cikin sa da take dauke dashi ne yasa yake rawar jiki a kanta.......Saukar hannunsa taji a bayanta yana kokarin zuge zuf din rigarta, ta dinga tureshi tana hawaye hakan be dameshi ba sai da ya cire mata kayan jikinta tas, ya kurawa cikinta ido da yayi kurcici a mararta, wata kwallah ce ta ciko a idanunsa, ya tsuguna gwiwa bibbiyu 'kasan toilet din ya dinga sumbatar cikin yana shafashi da hannunshi, Wann an k'wallar dai da yake ta 'boyewa sai da ta sauka, yay gaggawar gogewa, tana kallonshi taji ya dan bata tausayi, dan janye jikinta tayi ta matsa gefe tana zum'bura baki.....Ya sake binta yana rike hannunta duk jikinsa yayi sanyi wani irin masifaffan son yarinyar yaji yana bin dukanin ilahirin jikinsa......A hankali yaja hannunta suka isa inda kwamin wanka yake ya dauketa ya shiga da ita cikin ruwan da ya had'a, ido jawur yake kallonta yana jin wani masifaffan fleening na taso mishi, soso da sabulu ya dauka ya shiga cud'a mata jikinta yana sakin ajiyar zuciya, kamar kwai yake ta'bawa haka yake cud'ata sai da ya tabbatar ya wanke ta tas kana ya dauki towel mai kauri ya nad'eta a ciki......Daukar ta yayi ya fito da ita ya zaunar gefan gado.....Vasilin ya dauko ya nufi inda take zaune, warware towel din ya shiga yi ta rike towel din mirya na rawa tace"Ni ka bari shafa mai ai bai da wuya zan shafa da kaina." Girgiza kansa yay saboda idan yace zaiyi magana cikin halin da yake ciki zai iya tona asirin kanshi, ya kar'be towel din daga hannunta ya aje gefe guda, a hankali ya haye bed din ya raba 'kafafunshi ya sanyata a tsakiya ya shiga shafe mata jikinta da vasilin din, girman nonowanta da yanda suka sake kumburi da bun'kasa shine yake gigitashi yake d'imauta shi ya dinga kokarin daurewa duk dan kar ya nuna zulamarsa a fili al'amarin ya gagara bai san sanda ya jefar da vasilin din ba ya sanya hannuwanshi duka biyun kan nonowan ya shiga lailayasu yana jan nipples din tare da sauke masifaffiyar ajiyar zuciya...... Da sauri ta mi'ke zaune tana kuka tana kare jikinta da blanket ta dinga watsa masa harara tana share hawaye......Hannu ya d'aga mata yana so yayi magana sai kuma ya fasa, jiki a sanyaye ya sauka daga bed din ya bude wardorve ya dauko mata riga da zani na atamfa (vilsco) ya mika mata muryarshi a 'kasa yace."Kar'bi ki sanya." Hannunta na rawa ta kar'ba saboda bata so tayi musu yace zai 'kara kusantarta, yana mi'ka mata kayan ya kama hanya ya fice daga d'akin hankalinshi a masifar tashe. Da 'kyar tasa kayan tayi kwance a bed tana siyayyar da hawaye sam bata jin zata iya sakewa dashi kamar da a yanzu babban burinta bai wuce ta rabu da cikin dake jikinta lafiya ba............Bacci ne ya fara fizgarta sam yanzu bacci bayayi mata wahala, mussaman yanzu da ta samu daki mai cike da 'kamshi da sanyin na'urar sanyaya guri, bacci mai nauyi ya dauketa. Jin shuru bata fito ba ya sanya Hajja tace Rashida ta shiga dakin ta gani ko lafiya? Rashida na shiga ta tadda ta kwance a bed tana bacci, murmushi kawai tayi ta fito tace "Hajja bacci takeyi." Hajja tace tace"Koda naji ai shuru din tayi yawa, to ga abinci can ke sai ki zuba wanda zai miki kici idan ta tashi sai taci nata." Rashida tace"Nagode hajja." Daining din ta nufa domin cin abincin. Ahmadu kuwa kai tsaye ke'bantaccan gurin hutawarshi ya nufa dake bayan gidanshi, yayi kwance kan wani irin gado mai kamar lilo yana lilashi idanunshi a rufe abin duniya yayi mishi yawa, ada da bata kusa dashi yana daurewa amma kuma yau din nan da ya kusance ta yaji hankalinshi ya tashi sosai wanda har baya so ya sake shiga gidan ya ganta gudun aikata abinda baiyi niyya ba, ya kuma lura da yarinyar kamar tana tsoranshi yanda take zabura idan ya kusanci jikinta tilas dama hakan ta faru a tsakaninsu tunda rabuwa ce sukayi ita dashi mara dad'i! amma dai shi yanzu babu sauran wani 'kulli a cikin ranshi ya amince da tubanta kuma yana so suyi zama na kwarai zaman da kowane ma'aurata keyi, ammafa ya zauna yayi tunani da nazari hakan ba zata kasance ba har sai yayi kokarin dauke idonshi daga kanta, ba zai yuwu ba ace daga dawowarta ya fito da zulamarshi a fili dole ya dinga dauke kansa yana kuma nuna mata ba wannan ne ma'kusudin abinda ya sanya ya dawo da ita gidanshi ba, da wannan shawarar ya mike ya nufi cikin gidan dai-dai lokacin da ake kiran sallah la'asar.....Hajja da Rashida ne zaune a palon suna kallo suna hira ya shigo sannu yay musu ya nufi bedroom dinshi hajja tace"Yana da kyau idan ka shiga ka tasheta tayi sallah barcin yamma bashi da dadi ko kad'an Mafi akasarin masu ciki kuma sunfi s on irinshi." Yace."Kwarai kuwa Hajja annabi ma ya hanemu da yin bacci tsakanin azuhur da la'asar bari na tasheta yanzu." Yana shiga dakin ya tarar da ita ta tashi idanunta na kallon rufin dakin....Ya karaso kusa da ita cike da kulawa yace."Ki tashi kiyi sallah ina fatan 'kafar naki ya daina ciwo."? Daga masa kanta tayi yace."To alhmdullhi." Toilet ya nufa ta bishi da kallo tana ayyana abubuwa da yawa a kanshi ya fito daure da alwala ya fice daga dakin, a hankali ta sauko daga bed din ta nufi toliet din bakinta ta wanke sannan ta d'aura alwala ta fito, sallahr ma da kyar tayi saboda yana take jin wata shegiyar yunwa idanunta har rufewa sukeyi saboda rawar jiki wuyanta da hijab din da tayi sallah ta fito tana rarraba ido a palon......Hajja da Rashida na daki suna sallah sai shi kad'ai ne kan kujerar daining yana had'a abinci ya hangi fitowarta, had'a ido sukayi ta dauke kanta jikinta babu kwari ta nemi kujera ta zauna, ya gama had'a abincin cikin plate ya dauko a nutse ya kawo mata inda take, ba tayi musu ba ta 'karba ta dora saman cinyarta ta fara ci da bisimillah a bakinta ya kawo mata ruwa da lemo ya aje gabanta ya juya domin komawa daining din ta bishi da kallo tana mamakin yanda ya zama wani silent babban mutum mai kudi da shekaru gami da tarin ilimi na boka dana isilma shine ya mayar da kanshi bawa a gurinta, mamaki take sosai sai kuma wani sashen zuciyarta ke fad'a mata cewar "Duk wani abu da zai miki shi a yanzu yanayi miki shine saboda d'anshi ko 'yarshi da kike dauke dashi amma da babu cikinsa a tare dake kallo baki isheshi ba sai dai idan jarabarshi ce ta kawo shi. Girgixa kanta tayi kawai tana adduar Allah yasa ta sauka lafiya tagani zai cigaba da hidima da ita ko kuwa. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book na barki da Allah! Kema kika karanta baki biya ba na barki da Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *65* Koda ya kammala cin abincinshi sai ya mike a nutse ya nufi bedroom dinshi yana tafiya tamkar wanda 'kwai ya fashewa a ciki, shi kad'ai yasan abinda ke damunshi, hakika dawowarta gidan nashi na barazana da lafiyarshi dan tun suna cikin mota yake ta fama da joystick dinshi yana hanata aikata abinda takeso dan duk abinda yake daurewa yake yi a yanzu dai idan ba samu yayi ya rage damuwa ba to tabbas dai ya san yau da 'kyar idan zai iya rintsawa........Wanka yayi ya shirya cikin yadin kashmir d'an gasken milk colour mafi akasari kayanshi farare ne bai fiye sanya abu mai duhu ba duk da ya kasance farin mutum, ya tsaya gaban mudubi yana gyara wuyan rigarshi kana kuma ya dan gyara saisayayyar sumarshi ya daura agogo a hannunshi, turaranshi mai dadin kamshi ya fesa ya fito palo hannunshi rike da hularshi yana gyarawa, Tunda ta daga kanta sau daya suka hada ido dashi ta mai da kanta 'kasa gabanta na fad'uwa, ganinshi tayi tamkar sabuwar hallita kamar wanda aka 'bareshi a akwali (sabo) yayi wani fresh dashi fatarshi tayi luwai luwai annuri sai sauka yake kan kyakykyawar fuskarshi.....Hajjah tace"Au na d'auka yau d'aya zaka zauna a gida tunda matar gidan ta dawo sai ku tattauna a tsakaninku amma naga ka shirya zaka fita." Ya danyi gyaran murya yana d'ora hular a kanshi yace."Ba zan jima ba zan dawo insha Allah akwai ba'kin da zanyi zamu had'u dasu can gest house d'ina dan already ma yanzu suna can suna zaman jirana." Hajja tace"To Allah ya kiyaye a dawo lafiya." Rashida tace"Yayana Allah ya tsare." Ya amsa cike da kulawa. Ya d'an saci kallonta dai-dai lokacin data d'ago kanta suka had'a ido dashi, murmushin sa mai tsada ya sakar mata yana d'an d'aga mata girarashi guda kamar dai yanda ya saba, tayi gaggawar mayar da kanta 'kasa kamar bata so tace"Adawo lafiya." Bai tsammanin hakan ba sai yaji dad'i sosai yace."Amin amin." Ya nufi kofar fita, tsintar kanta tayi da binshi da kallo har sai da ya fita sannan ta mai dauke kanta tafiyarshi ma abar kallo ce komai nashi a nutse yake ya cika namijin da ko wace mace zatayi sha'awar aure amma ita har yanzu tana shakku a kansa dan tana jin tsoron ta sake sakin jikinta dashi wani abun ya had'asu na kuskure yazo ya saketa ko yaci mata mutunci amma itama tana hango tsantsar son da yake mata a 'kwayar idonsa. A can gest house din nashi Khalifa ne tare da Alhaji Muktari daura dan takarar governor jahar katsina ya kawo masa ziyara tare da dashi da mu'karrabansa, dake jam'iyarsu daya shiyasa suke zumunci kuma kusan halinsu yazo d'aya da juna, Alhaji Muktari ya ta'ba zama governor a jahar katsina yanzu yana so ya maimaitane yana kuma so ya karya al'kadarin governor dake ci a jahar tasu mai suna Engineer Haruna Haruni mutum ne mugu wanda yake mulki bisa zalinci halinsu d'aya da mai girma governor Lawan Rabo governor dake ci a jahar kano, duk wani 'kulla 'kulla gami da cuta da zalinci tare sukeyi dan duk abinda Lawan Rabo yayi a jahar sa to lashakka Haruna haruni shima sai yayi a tashi jahar, Wannan dalilin ne ya sanya Alhaji Muktari zuwa gurin abokin nashi domin su shawarta abubuwan da zai amfane su ya kuma amfanin al'ummar jahohinsu...............Tunda Governor Lawan Rabo ya samu labarin zuwan Alhaji Muktari garin sai ya dami kanshi, sosai ya kira Abokin nashi ya shaida mishi abinda ke faruwa, Haruna Haruni yace." Nasan ba zai bar garin ba tilas sai shigo ku gaisa kada ka nuna masa komai kamar yanda suke abunsu a lullube muma zamu bisu a haka, ai yanzu ya'ki d'an zamba ne muke kan kujearar mulki sai munso wani zai hau ka daina tayar da hankalinka kan komai kuma Amadu ya daina firgitaka, komai fa na hannuka a yanzu koda Amadu ne ya cika za'be sai munyi juyin mulki ballantana kuma muna da mai matacciya wannan maimai d'in ko sun so ko sun'ki sai munyi idan zaka shigo katsina ka shigo a shirye domin tilas ma a wannan karon mu kauce hanya mubi matasan yaran nan a sannu su samo mana 'kananun yaran da zamu bawa mai matacciya yayi mana aiki a kansu, tabbas dai nasan baka mance abinda ya faru ba a shekaru uku da suka gabata." Lawan Rabo ya sauke ajiyar zuciya yace."Tilas shawararka ita ce abun dauka a gaskiya yanda naji dad'in wannan kujerar zai yi wuya na barta kai tsaye kai ni ko da d'an da na haifa za'a bu'kata zan iya badashi tunda dai nasan ai ba gama haihuwar nayi ba.'' Haruna haruni yace."Haka ake son cikkaken namiji jarumi me a'kida, kada ka damu idan Muktari ya shigo fadar gomnati ka kar'beshi hannu biyu zamu 'bullo musu ta bayan fage, mulki dai sai dai suga anayi insha Allah duk jama'ar da suke dashi sai ta dusheshe ranar za'be mune zamu lashe." To Wannan maganganun da sukayi ne ya sanya Governor Lawan Rabo kwantar da hankalinshi kamar tsumma a randa, ya tabbatar suna da ya'kinin akan cewar mutukar bokan da yayi musu aiki da 'kuk'onan kawunan yara yana nan a raye cikin duniyar to sun tabbata sai sun watsa shirin su Amadu da Muktari Amadu na isa gest house din nashi Alhaji Muktari ya soma tsokanarshi da fad'in "Da har ina cewa bari mu tafi tunda dai mu gaisa da Khalifa ya isa kai sai ayi maka uziri tunda kana tare da Uwargida." Amadu ya zaune kan kujera yana murmshi hularshi ya cire yana kallon Khalifa yace."Nasan wanda ya fad'a maka cewar ina tare da Uwargida" Khalifa yace."Nine na fad'a mishi da kayi zamanka ma yayi maka uziri ko bakaji abinda yace bane." Murmushi yayi yana girgiza kanshi yace."Uwargida bata da 'koshin lafiya me kuke tunanin za'ayi."? Alhaji Muktari ya bashi hannu suka tafa suna dariya a tare Yace."Yana da kyau dai muje na dubata kafin na wuce, dan Khalifa yanzu yake shaida min an samu 'karuwa to Ubangiji Allah ya raba lafiya." Amadu yace."Ameeen ya rabbi, yace." Khalifa ya fad'a maka na samu 'karuwa shi bai fad'a maka tashi 'karuwar ba.''? Alhaji muktari ya kalli khalifa da son jin 'karin bayani." Khalifa yasa dariya yana kallonshi shima Amadu yace."Shima iyalinshi juna biyu gareta." Alhaji Muktari ya shiga girgiza kanshi yana kallonsu da fad'in "Gaskiya mutanan nan bakwa wasa." Khalifa na dariya yace."Bama wasa ko dai baka wasa Alaji matanka biyu 'yayanka shida ai kaine shugaba gwara mu da mace daya muke zaune." Alhaji muktari ya dan tura hularshi 'keya yana gyara zamanshi yace." Ai mata biyu shine jin dad'i Alaji sai ranar da kukayi zaku gane haka.'' Amadu dai murmushi yake yace."Duk mutumin dake da mace biyu bashi da kwanciyar hankali Alaji bana jin zan iya had'a mace biyu a gidana in dai ba Allah ne ya 'kaddara ba." Khalifa na d'auke da murmushi a fuskarshi yace."Ni kam ina tsammanin had'a mata biyu anan gaba dan gaskiya ina da ra'ayin yin hakan." Alhaji Muktari ya bashi hannu suka tafa.....Amadu kuwa kallonshi yay da mamaki a fuskarshi yace."To tunda ka tona asirin ranka sai na fad'a mata kasan ni da Hafsa akwai amana ba zan yarda kaci amanarta ba." Khalifa yasa dariya yana fad'in "Kafi tsuntsu gudu dan Allah! haka kawai Allah da annabi sun halasta min ace kada nayi, Kasan Allah idan lokacin aurena yazo dole ne Hafsa tayi hakuri dan ina da wannan niyyar." Amadu ya dinga girgiza kai yana kallonshi, shi kam a nashi ra'ayin bai son had'a mata biyu ko sama da hakan a ganinshi duk damuwa ce mutukar matarshi zata dinga dauke mishi dukanin laluranshi bai damu da lallai sai yayi wani auran ba koda kuwa ya samu mulki a nan gaba. Tattaunawa suka shigayi da sabbin tsare tsaren da zasuyi mutukar Allah ya cika musu burinsu akan abinda suke nema mutukar sun samu nasarar d'arewa kujerar mulki to babu shakka Al'ummar jahar kano da katsina zasuyi farin ciki zasu ga sauyi ta ko wanne 'bangare Misalin 'karfe tara da rabi na dare suka fito daga gest house d'in Alhaji Muktar yace yana so ya duba Wasila kafin ya koma dan gobe da asubah yake so su wuce, To dan kar ya watsa masa 'kasa a ido ne ya sanya ya amince da bukatarsa, saboda baya son abinda zai sanya girma da mutuncinsa ya zube a idonshi, baya so suje gidan Yarinyar tayi wani abun wanda zai nuna babu jituwa a tsakaninsu domin har yanzu ya lura da ita bata wani saki jikinta ba sosai. Goma shaura motarsu ta shiga cikin gidan garba nayi parking ya fito cikin sauri ya bude musu kofa suka fito, tare suka nufi cikin gidan dukaninsu harda khalifa. Rashida ce ita kad'ai a palon tana kallo Hajjah tuni ta shige daki ta kwanta dan tanayin sallah isha'i take kwanciya, Wasila kam bata jima da barin palon ba itama wanka ta shiga tayi ta kwanta dan har yanzu jikinta bai dawo dai-dai ba akwai sauran gajiyar hanya Rashida ta mi'ke tsaye tana musu barka da zuwa, ta gaishe su a nutse tana kokarin shigewa Har zai yi mata magana sai kuma yaja bakinshi yayi shuru ya kalli Abokan nashi a nutse yace."Bari na fito da ita." Khalifa yace"Kada kayi wannan dad'ewar da ka saba." 'Karamin tsaki yaja ya yana girgiza kanshi ya tura kofar dakin ya shiga wanda yayi dai-dai da lokacin da ta fito daga toilet jikinta daure da towel iya cinyarta.....Sallamar dake dauke a bakinsa ce ta gagara fitowa, da kyar ya janyo dauriyarshi da jarumtarshi ya shiga dakin, 'Dan tsayawa tayi tana kallonshi tana turo bakinta gaba, shiyasa ta'ki shiga dakinsa ta gudo nata ashe bata tsira ba yazo zai takura mata, 'Bata fuskarta tayi ta wuce a hankali taje ta zauna gaban mirror tana bud'e man shafawa Bayanta ya tsaya yana kallonta ta cikin mudubin tana shafa mai a hankali tana shafawa a hannunta, ba tare da yace komai ba ya sanya hannunshi cikin vasilin din ya soma shafa mata sassan jikinta, jin saukar hannunsa a jikinta ya sanya ta sauke ajiyar zuciya me tafe da tashin tsigar jiki, hannunsa ta cire wanda yake kokarin cusawa cikin towel din ta sake daure kirjinta dashi, bai ce mata komai ba, ya dan rankwafa a hankali ya d'an ja 'kafafunta ya soma shafa mata vasilin din a cinyoyinta da kafafunta.......Ido ta tsira mishi yayin da kanshi ke 'kasa, taji wata 'kwallah na kokarin zubo mata daurewa tayi ta dauke kanta da sauri lokacin da ya dago ganshi, bayan ya gama shafa mata vasilin din, Ta mike tana sake rike daurin towel din a kirjinta wardrobe ta nufa ya bi bayanta, kayan bacci masu taushi ya dauko ya rike hannunta a hankali yake kokarin kwance towel din, tasa kuka tana tureshi, ya mi'ka mata kayan da fad'in "Kiyi gaggawar sanyawa tunda baki so nasa miki akwai 'baki na jiranki a palo abokina ne yazo duba jikinki.'' Cikin rawar murya tace" Ni ka fita to nasa kayan zan fito yanzu." Harararta yayi yace."Meye abinda zaki 'boye min a jikinki ? wai ke dan Allah yaushe zaki daina wannan 'kauyancin ne? Shiru tayi mishi ta nufi bed da kayan a hannunta, zama tayi gefan gado ta soma zura dogon wandon tana kare cinyoyinta da towel, shi dariya ma take bashi wallahi, yay tsaye a kanta har ta gama sanya kayan ya mi'ka mata 'katon hijab d'inta na sallah tasa kana ya nuna mata hanya da hannunsa......Gaba tayi yabi bayanta haka suka fita palon. Alhaji Muktari ya kalleshi a lokacin da suke karasowa inda suke yace."Ashe dai da gaskiyar khalifa shiyasa kafin ka shiga ya tuna maka.'' Amadu yayi sauri bagarar da zancen dan baya so ta fahimci inda zancen nasu ya dosa, shi baiga wani dad'ewar sa a ciki ba sa'ido ne kawai irin na khalifa. Ta gane khalifa, d'ayan ne bata gane ko waye ba, a nutse ta zauna kusa da mijin nata ta shiga gaishesu, Alhaji Muktari ya shiga mamakin 'kan'kanuwar yarinyar wai itace matar abokinshi Yo ai wannan za tayi sa'ar babbar 'yarshi Sa'adatu, babi shakka dole abokin nashi yace bashi da sha'awar 'kara wani auran saboda yasan yana da wacce zai mori 'kuruciyarshi da tsufanshi. Cikin kulawa yake amsawa ya dan tsokanta ita kuma sai sunkuyar da kanta take kunyar mutumin takeji sosai ganin kamar ma ya girmi mijin nata, Wanda sam ba haka bane Alhaji Muktari sa'an Amadu ne dan shima baifi shekaru arba'in da biyar ba , kawai dai dan yayi aure da wuri ne kuma yana da jikin girma ba kamar Amadu da bai da 'kiba ba, Tana zaune tana sauraransu suna hira duk ta 'kosa ta bar gurin ta d'an muskuta a hankali zata tashi, Ya ri'ke mata hannunta ba tare da ya kalleta ba ya juya suka cigaba da magana da Khalifa, tamkar zata fashe da kuka haka ta kalleshi to meye amfanin zamanta a gurin bayan sun gaisa ba sai ya kyaleta taje ta kwanta ba......Kirane ya shigo wayar Khalifa sai lokacin suka san dare yayi sosai sha d'aya da rabi Hafsa taji shuru bai dawo ba ta kira wayarshi, Ya mike da sauri yana kallon agogonshi, yace"Ashe dare yayi sosai sha d'aya da rabi yanzu." Duk sai suka mi'ke tare Alhaj i Muktari yace."To Uwargida kuma amarya xamu tafi Allah ya 'kara sauki ya kuma saukeki lafiya insha Allahu muna nan zuwa ni da iyalina duk ranar da kika haihu." Tace"To Allah ya kawo ku lafiya mungode." Ta kalli khalida da yayi gaba hankalinshi duk yayi gida tace"A gaishe min da Afnan da momynta." Yace."Zasuji insha Allahu.......Ta dauka zai musu rakiya sai taga ya tsaya bakin kofa yana fad'in To Alh sai munyi kenan a sauka gida lafiya nagode da ziyara insha Allah nima ina nan tafe." Khalifa yace."Wai kana nufin daga nan zaka tsaya."? Yace."Meye a ciki to akwai gajiya a tare dani ina so huta ne." Khalifa yasha jinin jikinsa, ya kalli Wasila dake tsaye a kusa dashi yabi ya rike mata hannu gam kamar wacce zata gudu.....Yace." 'Kanwata ina fata baki mance abinda Dr Aliya ta fad'a miki ba ko." Wasila tayi jim!! Tana nazari sai kuma ta kalli Khalifan jikinta a sanyaye ta daga kanta.' alamun bata mance ba........A ranar da akayi mata d'aurin mahaifa Dr Aliya ke shaida mata cewar dole ne ta nemi wata hanyar domin biyawa mijinta bukata mutukar ana so cikin jikinta ya zauna lafiya to banda yawan sex da ayyuka masu tsauri, a lokacin da Aliya ke yi mata wannan jawabin sam bata d'aukeshi da mahimanci ba saboda tasan bata da aure lokacin, To da yake duk a gaban khalifa tayi jawabin yasa yanzu ya sake tuna mata kuma ta gane inda ya dosa, tabbas kuwa dole ne tayi taka tsantsar dan tayi bala'in sanin waye Amadu idan ya hauta ya dunga suburbud'arta mancewa yake da kowa da komai a lokacin shi dai burinshi kawai bukatarsa ta biya........Hannunta ya rike zugwi zugwi! ya nufi bedroom dinshi da ita, ya mai da 'kofar d'akin ya rufe da key, sai sannan ya sakar mata hannu, jikinta babu kwari ta nemi gefan gado ta zauna, shi kuma ya nufi toilet domin watsa ruwa. Ya fito daure da towel ya ganta zaune tana gyangyad'i Gyaran murya yay ta zabura da sauri ta bud'e idonta tana kallonsa, gabanta ya fad'i ras! ganinsa daure da guntun towel! da sauri ta haye bed din ta ja blanket ta rufe jikinta har fuskarta, ita kam ko me zaiyi ba zata bari ya hau kanta ba gani take idan ya sa mata wannan 'katuwar abar tashi zata iya haihuwar dole....Ganin razanar da tayi ya bashi mamaki sai kawai ya girgiza kanshi ya bude sif ya dauko jallabiya da gajeran wando yasa a jikinshi, kana ya nufi ke'bantaccen gurin da yake ibadarshi, kafin ya isa kira ya shigo wayarshi ya dauka yana dubawa Khalifa ne, Yace."Dama dazu ina so nayi maka bayani to babu dama gaban Mutane.....Khalifa ya fad'a mishi sharud'an da Likita ta fad'a kan Wasilan ya cigaba da cewa ko za kayi kar ya wuce sau d'aya dan kar ka wahalar da yarinyar mutane kuma ka wahalar da d'an dake cikinta......Yace."Okey shine naji kuna magana da ita d'azu kuna wani 'boyewa."? Khalifa yace."Meye abin 'boyewa nifa zumud'in da naga kana yi ne yasa na tuna da maganar kai ma kanka ko ba'a fad'a ba ai ka d'aga 'kafa! A hasale yace."Kai kaga ki likita tace ko bata ce dama ni banyi niyyar yin komai ba dan haka sai da safe." Kashe wayarsa yay ya ajeta yana jan tsaki ya nufi kan dadduma......Khalifa kam nashi 'bangaran dariya yasa dan ganin yanda lokaci 'kankani zuciyar abokin nashi ta hasala....Wasila kam tun tana rawar jikin ta daina dan bacci me dad'i ne ya dauketa cikin bargonshi mai cike da kamshin turarirrkanshi masu dad'in 'kamshi da kashe jiki. Littafin na kudi ne! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *66* Nafila yayi raka biyu bayan ya idar da sallahr sai ya bude al'kur'ani mai girma ya karanta iya yanda ya sawwa'ka ya jima hannunsa a sama yana addua sannan ya rufe da fatihatulkitabi ya shafa a fuskarshi, a nutse ya mike ya nufi bed din ya xauna yana kallonta bacci take sosai kuma daga ni tana jin dadin baccin a hankali yaja bargon ya shiga ya kwanta kusa da ita tare da d'an jawota jikinshi ya d'ora hannunshi 'kasan mararta yana shafawa a hankali a hankali bakinshi na motsawa da alama addua yake yi a nutse ya tofe musu jikinsu bakid'aya kana ya ja bargon sosai jikinsu ya rufe idanunsa yana adduar Allah ya taimakeshi bacci mai nauyi ya daukeshi, cikin ikon Allah kuwa baccin ya daukeshi, kuma baccin da ya jima baiyi Irinshi ba. Wajejen karfe hud'u shaura na asubah ta farka da wata matsananciyar yunwa, jiki na kyarma tayi yunkurin mi'kewa, yay gaggawar rike ta idanunsa ya bude ke kyace dama ba bacci yake yi ba, Amadu bashi da nauyin bacci ko kad'an, a hankali yace."Menene."? Shiru tayi tana mutsika idanunta, sai ya mi'ke zaune yana me cire bargon dake jikinsu ya sanya hannunsa guda a jikinta ya shafa wuyanta, babu alamun zazzabi a jikinta, Yace."Menene? ko zakiyi wani uzirin ne? muryarta na rawa tace"Yunwa nakeji." Yace."Yunwa."? Daga kanta taji hawaye na kokarin zubo mata, Yace."Dama baki ci abinci ba kika kwanta."? "Naci dama duk dare ina tashi naci abinci." Ya shiga girgiza kanshi a hankali ya mike ya sauka daga bed din ya fita daga dakin Kicin ya nufa yayi dube duben shi babu abinci sai kawai ya jona kettle ya dora ruwan tea yana tsaye yayi ya juye mata a cup ya nufi dakin dashi, lokacin ta fito daga toilet daure da alwala dan an soma kiran sallah." Ya aje tae din kam bedside yana fad'in "Ga tea nan babu abinci a kicin din wallahi." Zumbura bakinta tayi ita me zatayi da wani tea banda ya sata jin wata yunwar, Fita tayi daga dakin Yabi bayanta kicin ta nufa, ya tsaya bakin kofar kicin yana fad'in "Ki koma ki kwanta bari na tashi hajja sai ta sarrafa miki wani abun." Girgiza kanta tayi tace"Kawai tana baccinta sai a tasheta tayi girki nima zan iya." Shiru yay yana kallonta tana kunna gass cocar, Shi da kansa yayi alkawarin daukar dukanin laluranta baiyi tsammanin harda shiga kicin ba, a lokacin da suke tare a can baya bai santa da wannan cin abincin ba yanzu dai yafi tunanin cikin da take dauke dashi ne ya sanya ta, kicin din ya shiga ya kar'be tukunyar hannunta wai zai d'ora mata abincin......Tausayi ya bata ta kar'bi tukunyar taje ta zuba ruwa ta tazo ta dora tukunyar gefanta ta bude taga lafiyayyar miya wacce taji nama zu'ku zu'ku.....Sai kawai ta bud'e sto ta dauko supargetti guda d'aya, yay daurin kar'bar taliyar a hannunta, ta rike tana girgiza mishi kai tace"Ka barshi zan dafa babu wuya fa." Ya d'an tsira mata idanunsa itama shi take kallo tana sake jin wani irin yanayi a jikinta gaskiya ta lura ya mato akan sonta, da girmanshi da komai ya dinga biye mata da dukanin abinda take so.....Yace."Kin tabbata zaki iya." Daga kanta tayi yace."Okey bari nayi wanka da alwala na wuce masjid.'" ya wuce ta bishi da kallo tausayi tausayinsa take ji a cikin ranta. Tana tsaye taliyar tayi ta tsaneta kana ta juye cikin fulas ta dauka ta nufi daki dashi, lokacin har yayi wanka ya sanja jallabiya hannunsa rike da cazbaha, sai kamshi yake ta matsa mishi hanya shi kuma ya fita ba tare da wani yace da dan uwanshi komai ba. Kicin din ta koma ta dauko plate sannan ta samu wani abu ta zuba miyar a ciki ta dawo dakin ta zauna kasan kafet a nutse ta zuba abincin ta soma ci sai da taci ta koshi sannan tayi sallah ta koma ta kwanta, bacci na fizgarta taji shigowarshi.......Ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi lokacin da yake kokarin karasowa kusa da ita......Zama yayi gefanta a nutse yace."Tashi zamuyi magana." Ganin babu wasa a tare dashi yasa ta mike xaune tana wasa da hannunta.....Cikin kulawa ya kalleta yace"babu gaisuwa ko."? Ta dan kalleshi da gefan ido sai taga ya tsirawa jikinta ido, kanta ta sunkuyar a hankali tace "Ina kwana." Ya amsa da sakakkiyar fuska kana yace."Ya kwanan boy." Shiru tayi yace."Kamata yayi ma kafin mu fara magana na fara gaisawa dashi." ba tace masa komai ba, dan janyota jikinsa yana laluben jikinta, hannunsa ya d'ora saman mararta yana shafawa, ta dinga jin hucin numfashinsa a fuskarta, rintse ido tayi gabanta na faduwa tsigar jikinta na tashi, ya d'ora bakinshi saman goshinta tare da fad'in "Allah yayi miki albarka." Ta bude idanunta dake rufe tana kallonshi, mikar da ita yayi zaune yace"Yanzu hankalina ya kwanta na duba yarona yana da kyau ma muje kuga Dr insha Allah." Ba tace komai ba tana dai kokarin gyara rigarta, sai da ya tabbatar ta samu nutsuwa kana ya kalleta a nitse yace."Wane guri kika tsaya a karatun ki na al'kur'ani da hadisai nasan dai kinje isilamiyya ko.'? Taji gabanta ya fad'i! ta kalleshi idanunta na kokarin kawo ruwa, ina suka ga gatan da zasuyi karatu....Shiru tayi masa tana wasa da yatsun hannunta, Yace."Koda yake dai yanzu ku kin fad'a min ga inda kika tsaya bai da amfani tunda dai ba tilawa kikeyi ba, yanzu ki shirya ko ince ku shirya keda kanwarki insha Allahu kullum da asubah zamu dinga zaman karatu dani daku zamu fara tun daga fatiha da izinin Allah zamu sauke al'kur'ani mai girma mutukar kun bani had'in kai! Idan kin san ba'ki kin iya karatun al'kurani da sauran litattafan addini insha Allahu karatun nasara (boko) ba zai miki wuya ba zan d'anko muku mai muku lesson kafin ki haihu sai ku koma makaranta ko bakya so."? Yafada yana kallonta cike da kulawa......Hawaye ta share murya na rawa tace"Ina so mungode." Yace." Kin kammala secondary skul ko." ? Shiru tayi kunya duk ta isheta, ya sake maimaita tambayarshi, da kyar tace "Tunda muka fad'i jarrabawa muka daina zuwa." Yace."Okey duk ba wani abun bane insha Allah zakiyi karatu mutukar kin mai da hankalin ki ni kuma zan tsaya miki da yardar Allah." Hawaye taji sun zubo mata a fuskarta, tace"Mungode Allah ya saka da alkairi." Sai ta fashe da kuka harda shashsheka, rungumeta yayi sosai yana rarrashinta tare da shafa kanta, tayi luf a jikinshi tana sauke ajiyar zuciya.....Ya dago ta daga jikinshi yana goge hawayen fuskarata yace."Ki rabu da wannan 'kawar taki wacece sunana? bata da kirki duk wani lalacewa da rayuwarku tayi da ita da kuma rashin gata wanda baku dashi amma insha Allahu nine zan zama gatan ku in dai zaki zauna dani da tsarkakkiyar zuciya abinda ya faru a baya ya wuce a gurina na yafe miki insha Allah Allah ya yafe mana gabad'aya." Hannunsa cikin nata tace"Dama tuntuni mun rabu da Camas! nagane ita ke zugani ina yin wasu abubuwan marasa kyau tunda abun nan ya sameni ta gujeni ta gudu da kudina kusan miliyan biyar har yanzu ban san ina take ba." Yace."Duk abinda kikace ta aikata miki zata iya domin nima na nemi taimako a gurinta lokacin da muke neman ku kafin kuje gurin mai allo, yarinyar ta'ki ta bani cikakken bayani 'karshe ma sai ta daina d'aga waya ta idan na kira." Girgiza kanta ta shigayi tana mamakin halin dan adam ko a mafarki idan ance mata Camas za tayi mata haka ba zata yarda ba sai gashi babu shakka mutum abin tsoro ne. Yace."Je ki kira Rashidan mu fara zaman karatun yanzu." A hankali ta sauka daga bed din ta fita daga dakin, Ya dauke idonsa bayan fitar ta yana girgiza kanshi, yana jin zai iya sadaukar da farin cikinsa da duk wani jin dadinsa mutukar yarinyar zata samu walwala da farin ciki. Lokacin da ta shiga dakin, Hajja na zaune kan dadduma da carbi a hannunta ita kuma rashida ta idar da sallah tana kwance kan daddumar bacci na kokarin dauketa.......Ta samu guri ta zauna a nutse suka gaisa da Hajja tana tambayarta jikinta, Tace jiki da sauki alhamdullihi." Rashida ta mike tana mutsika idanunta suka gaisa tace"Kizo zamuyi karatu." rashida ta mike tare da zura hijab dinta suka fita daga dakin, hajja kuwa ido tabisu dashi haka kawai take tausayawa yaran. Palo suka taddashi zaune kan katuwar dadduma gabanshi da al'kur'anai da kuma sauran litattafan addini........Ya bawa ko wacce al'kur'ani guda d'aya ya umarce su bude 'kasa, zasu fara daga fatiha ne. Ko wacce ta bude nata a nutse yayi bisimillah ya soma karatu cikin nutsuwa da 'kira'arshi mai kyau da dad'in saurare, nutsuwa sukayi sosai suna saurarashi, sai da ya maimaita musu fatiha da fala'ki da nasi sau uku sannan yace su karanta masa yaji." A tare sukayi bisimillah suka soma karatun cikin nutsuwa, ya dinga sauraransu har suka kammala, yaji dadi sosai yanda ya biya musu haka sukayi, yace su rufe alkur'ani suka, Ya dauki littafin ahlari yana dubawa, a nutse ya soma karanto musu yana musu bayani dalla dalla bayanin jinin haila da hukunce hukuncensa bayanin janaba itama da hukuncinta shuru sukayi suna sauraranshi, dan wani gurin idan ya fada kunya ce take rufesu sai suka lura shi bai damu ba karatunsa yake yana so su fahimci abunda yake so su fahinta, bayan sun kammala karatun sai ya sallami Rashida ya mai da hankalinshi kan Wasila tana zaune jikinta duk yayi sanyi bata ta'ba tsammanin yana da ilimi irin hakaba sai taji ya sake yi mata wani kwarjini a idonta, A nutse yace" Wasila meye banbanci a cikin wankan haila da janaba niyya iri d'aya ake ko kuma ta bambamta."? Ta dan kalleshi a nutse tace"Akwai bambamci mana." Yace."Kiyi min bayani sosai." Tace"Niyyar wankan haila daban niyyar wankan janaba daban amma duk wankan iri d'aya ne." Yace."Meye janabar meye kuma haila."? d'an tura baki tayi tana mi'ke kafafunta ita tagaji da wannan tambayoyin yace."Idan baki min bayani ba zan dauka baki da ganewa da saurin fahimta." Tace"Janaba itace "Kamar mutum yayi rayuwar aure da mijinshi to janaba ta hau kanshi sai yayi wanka wanda ya zama farillah kamar yanda annabi ya koya mana." Yace."Na gamsu da wasu bayanan naki sai dai kuma har yanzu baki fayyace min meye janaba ba da yanda zan fahimta kince rayuwar aure ni dake yanzu haka rayuwar aure mukeyi ina so ki fahintar dani shin rayuwar aure wace iri? Kamar zata fashe da kuka tace"Kamar yaya."? Yayi murmushi yana kallonta a nutse yace."Kamar yanda nayi miki bayani." shuru tayi mishi yace."Nasan rashida ta fiki gane karatu bari na kirata tayi miki bayani kuma mutukar tayi miki bayani abinda nake so ku fahimta sai nayi miki bulala! ita kuma nayi mata kyauta.'' mi'kewa yake kokarin yi ta rikeshi tana kuka "Ni wane bayani zanyi to bayan nayi maka bayanin abinda na fahinta! Ni kar ka kira rashida me ta sani a cikin abinda kake fad'a ai har gwara ni nafi ta fahinta." Ya koma ya zauna yana dariya, yace."Ai saboda nasan kin fita fahintar ne yasa na sallameta ke nace ki zauna kiyi min bayani, to gashi kin kasa min bayani gamshashshe wanda zai sa na gamsu." Hawaye ta share tana zumbura baki, gashi ta rirrike masa riga kusan ma rabin jikinta duk yana jikinsa, Cikin kasalalliyar murya yace."Tashi muje ciki ni nayi miki bayanin yanda abin yake, in yaso bayan na gama sai ki fahimci yanda janaba take a kan mutum." Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya, ya dan janyeta daga jikinsa yana kokarin mikewa ta rikeshi! ita bata so ya kira Rashida ai abin kunya ne ma ya tambayi rashida yanda janaba take! Shima dama wasa yake yi......Yace." bakya jin kunyar wani ya fito ya ganki haka kina kuka kamar kankanuwar yarinya."? Tace"Dan Allah kada ka kira Rashida wallahi na fahimta." Yace."Nima da wasa nakeyi ai, ai nace muje d'aki na nuna miki ko." Sauka tayi daga jikinsa ta koma gefe guda tana ya mutsa fuska......Girgiza kanshi yay ya mi'ke a nutse yana fad'in "Kinbi kin nukurkusa min jikina yana tsami! kizo kiyi min tausa." Kallonshi tayi kawai ya wuce bedroom dinshi Yana shiga ya cire jallabiyar jikinshi ya kwanta bed yana rintse idanunshi, da so samu ne ya samu ko dan romantic ne ya samu yayi to amma sam baya son takurawa yarinyar zai dai cigaba da daurewa Allah yasa zai iya............Bacci me nauyi ya daukeshi ita kuma ta zauna a palon saboda tana jin tsoro ta shiga dakin yayi mata wani abun, Hajja da rashida suka fito daga dakin.........Dai-dai da lokacin da Rabe ke shirya musu daninng, Wasila na kallonsu suka nufi daninng din tayi zamanta a inda take har suka kammala suka isketa Hajja tace"Lafiya baki karya ba ko bakijin dadi ne."? Tace"Hajja kafin asubah naci abinci bana jin yunwa yanzu sai zuwa anjima nasan zan nemi abinci." Hajja tace" To shikkenan ki dai dunga ci kina koshi domin ki samu kuzari da kwarin jiki duk da nagani baki wasa da cin abinci." Rashida tace"Ai hajja wannan baby nasan kato ne anti wasila fa kullum cikin cin abinci take babu dare babu rana." Hajja tasa dariya tana fad'in "Ai lafiyace ta jawo haka ana so mai ciki ta dinga cin abinci sai kiga ta haifi yaro lafiyayye mai ban sha'awa." Wasila dai murmushi tayi kunyar hajja take, sai ma ta mike ta nufi daki tana murmushi ita kanta tasan dolene ta haifi katon d'a dan ganin irin abincin da take narka sai kace jaka.......Kusa dashi taje ta kwanta a hankali ta d'ora kanta kan kirjinsa tana lumshe idanunta, sai taji saukar hannunsa a bayanta, tayi yunkurin mikewa ya riketa sosai! idanunsa a rufe! sai tayi luf a jikinsa tana sauke numfashi, jin baiyi mata komai ba yasa ta saki jikinta sosai bacci ya dauketa a jikinshi. Littafin na kudi ne! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *67* To haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya cikin kwanciyar hankali gami da samun nutsuwa, sosai Amadu ke kula da Wasila ita da abinda ke cikinta, sunje asibiti likita ya tabbatar mishi da lafiyarta data yaronshi, yanzu itama ta saki jikinta sosai dashi tana zama suyi hira sosai in yana gida kuwa ta dinga kwanciya kenan a jikinshi daga tace wannan sai tace wancan Hajja da Rashida suyi ta kallon drama dan wataran ma idan sukayi wani abun hajja barin gurin takeyi, Rashida ma tayi ta jin kunyarshi tana mamakin yanda yayarta ta samu sake a gurinshi take zuba sangarta gami da shagwaba iya yanda take so shi kuma yana biye mata.......Idan suka zo zaman karatu da asuba ma sai sun gama rungume rungumensu kafin Rashida ta fito, dan wani sa'in idan wasilan ta rikitashi baya iya yi musu karatu me tsayi zaije ya kwanta yace sa had'u da daddare, to ka yaje ya kwanta haka zata bishi ta nan'ika da jikinshi, dole sai ya marmatsata sannan hankalinsu ke kwanciya ita dashi, akwai ranar da yaso ya sadu da ita ta hanashi, gashi ya kai 'kolulowa gurin bukata idonsa jawur ya fita daga d'akin, tayi kwance a bed tana hawaye, ita tsoronta Allah tsoranta annabi kar garin jin dad'insu yaronsu ya samu matsala, shiyasa bata so yace dole sai yayi sex kawai dai su tsaya iya romantic din har Allah yasa ta haihu........Ranar fushi yayi da ita ya shirya yayi ficewarsa harkokinshi, sai bayan tara da rabi na dare ya shigo gidan lokacin ita da Rashida ne a palon zaune suna kallon wani india film Rashida tayi mishi barka da zuwa ya amsa cike da kulawa yana tambayarta hajja tace"Taje ta kwanta.....bedroom dinshi ya nufa, yana jiyo muryarta nayi mishi sannu da zuwa, ya'ki amsawa, ta mike a hankali dan cikin nata ya fito sosai yanzu zama take da 'kyar ta mike da kyar tunda yanzu cikin ya kai watanni bakwai, bayanshi tabi wanda tana murd'a kofar dakin taji a rufe, ta tabbata key ya sanya, jikinta a sanyaye ta dawo ta zauna kusa da 'yar uwarta idanunta na kawo ruwa, wannan alamun da ya nuna ya nuna mata fushi yake da ita.....Rashida tace"Anti Wasila akwai abinda ke faruwa tsakaninki da Mijinki dan naga alamu tun a gurin karatu." Tace"Wane alamu kika gani.'? Tace"Yanzu fa ya shigo Kinyi mishi sannu be amsa ba, anti Wasila Allah kina 'kure hakurin mutumin nan sai bashi wuya kike nasan laifin naki ne wallahi." Cike da mamaki take kallonta tace"Har kike rantsewa laifina ne."? Rashida tace"Eh mana ni dai tsayin wata biyu da nayi a gidan nan banga abinda mutumin nan yayi miki na 'bacin rai ba kullum.cikin kyautata miki yake yi yana rarrashinki da kula dake, kinga kuwa dole nace laifinki ne." Shiru tayi tana nazarin maganar 'yar uwartata, babu shakka tsayin wata biyu da sukayi a gidan idan tace ga laifinsa tayi masa sharri kullum cikin tattashinta yake watarana ma abinci shike bata a baki, ta haye jikinsa tayi ta nu'kur'kusa bai ta'ba gajiyawa ba, tabbas laifi daga gurinta yake, Ta kalli rashida a nutse tace"Nasan dai ke me hankali ce rashida idan na fad'a miki dalilin da ya saka yake fushi dani zaki daina ganin laifina, a gabanki komai ya faru kuma a gabanki likita ta gindaya min sharad'ai, kinfi kowa sanin irin 'bakar wuyar da nasha kafin wannan cikin na jikina ya zauna, duk wani 'kokari inayi masa domin na biya mishi bukatarshi duk hakan bai isheshi ba dole sai ya kwanta dani ni kuma ina tsoron wani abun ya faru dani da yaron dana ke dauke dashi a mahaifata." Rashida tace"Lallai anti Wasila dama saboda wannan matsalar ne yasa kike ta bashi wahala, gaskiya kin zalince shi wallahi ai itama likitan ba tace kar ayi ba cewa tayi a dinga d'aga 'kafa, tun a lokacin da cikin yake 'karami take wannan maganar to yanzu kuma ya girma ni ina ganin babu abinda zai same ki da yaron dake cikin ki kawai dai dan kin kasa kwantar da hankalinki ne yasa kike ganin kamar wani abu zai faru dake." "Gaskiya Rashida bana jin zan iya amincewa da bukatarshi dan ni 'kadai nasan irin 'bakar wuyar da nake ci babu ciki ma ballanta yanzu da wannan cikin ai nasan mutuwa zanyi kawai yayi hakuri Har Allah yasa na haihu.'' Rashida tace" Ni wallahi bana so naga kina 'bata masa rai duk sai naji babu dadi dan Allah ki bashi hakuri anti." "Ki kyaleshi zai huce da kanshi, ni ba zan iya wannan bita zaizai d'in ba, sai ma ya d'auka na damu dashi ne." Rashida ta 'bata rai! ta tsani halin taurin kai irin na 'yar uwarta wallahi, kawai dan taga yana sonta ne shiyasa take masa wulakanci ita sam ba taga aibu ba dan ta bashi hakkinsa rana daya yayi ai ba laifi bane. Wanka tayi ta shirya cikin kayan bacci ta nemi gado ta kwanta tana jiran shigowarsa kamar yanda ya saba, ko mai dare idan ya dawo koda tayi bacci sai ya tashe ta akwai wani Ice cream da yake siyo mata mai dad'i sai tasha shi take samun nutsuwa, yau tana tunani ko ya siyo ko bai siyo mata ba, tana dai jiran shigowarshi d'akin.......daga zaman jira bacci ne ya d'auketa, ba ta tashi farkawa sai kusan d'aya da rabi! ta kwanta da tunanin Ice cream dan har mafarki tayi ta mi'ke zaune tana dube dube a d'akin wai ko ya shigo ya tarar tana bacci ya aje mata duk ta gama dube dubenta bata ga komai ba, ranta ya 'baci sosai ta riga ta kwallafa ranta dashi dan tayi masifar sabo da shan Ice cream din, bude kofa tayi ta nufi d'akin nashi, har yanzu kofar a rufe take......Yana 'kokarin mikewa daga kan dadduma yaji alamun ana ta'ba 'kofar dakin, a nutse ya karasa bakin kofar ya murza key din dake jiki kofar ta bud'e ita ya gani tsaye tana cikin rigar bacci iya gwiwa mai hannun shimi cikinta ya fito sosai dake rigar irin me kwanciya a jiki ce, kanta babu hula sai dai gashin kanta daure yake cikin katon ribbon, Ya d'an bita da kallo babu yabo babu fallasa yace."Menene."? Kamar zata fashe masa da kuka tace"Ina Ice cream din."? Yace."Ajiya kika bani da zaki tambaye ni Ice Cream yau ban shigo dashi ba." Tayi narai narai da ido tana shirin yin kuka, kofar dakin yake kokarin rufewa, tayi saurin shiga dakin tana kalle kalle......Ya nufi bed ba tare da yace mata komai ba ya zare jallabiyar jikinsa daga shi sai boxer ya haye bed dinshi yaja bargo ya rufe jikinsa.......Ta jima tsaye a dakin tana sha'kar bakin ciki kafin tace"Kaine fa kayi al'kawari kace kullum zaka dinga kawo min tunda babynka yana so da kasan ba zaka cika al'kawari ba da baka d'auka ba." Yanda ta fad'i maganar zaka gane a kufule take dama ance zuciyar me ciki a kusa take.....Yana jinta yayi mata shuru, yana lumshe idonsa, Girgiza kanta tayi da tayi niyar fita sai kuma ta fasa tinkis tinkis ta karasa bakin bed din ta tsaya babu zato yaji gunjin kuka a tsakiyar kanshi, kuka take sosai hawaye na zuba a fuskarta, ya mike zaune da sauri yana kallonta, hannunta ya rike ta fuzge tana cigaba da kukanta, ya 'mike da sauri ya lalubi jallabiyarshi da ya cire ya zura da sauri ya kama hanyar fita daga dakin, idan akwai abinda ya tsana a duniya to bai wuce kukanta ba, ya kan rasa tunaninshi gabadaya idan yaga tana kuka da damuwa, Ice cream dinta na mota, 'bacin ran da yake dauke dashi ne ya sanya bai shigo mata dashi ba, bayanshi tabi dai-dai lokacin da taga ya bude kofar palon ya fita, sai tayi tsaye a tsakiyar palon tana jiran dawowarshi Ya shigo hannunsa rike da ledar Ice cream din ya ganta tsaye a tsakiyar palon, kai tsaye inda take ya nufa ya mi'ka mata ledar Ice craem din babu kunya ta sanya hannu ta 'karba tana tura baki ta juya zata barshi a gurin, ya rike hannunta na dama, ta juyo tana kallonshi, Hausawa suka ce me nema baya fushi, dik yanda yaso daurewa kasawa yayi kawai sai ya tsinci kansa da rungumeta a jikinshi yana shafa gashin kanta, a hankali ya talfo fuskarta yana so ya hada bakinshi da nata, ta dan kautar da fuskarta, harshensa ya sauka kan ha'barta sai kawai ya shiga tsotsa ha'barta da kumatunta da le'bunanta, tsigar jikinta ta shiga mi'kewa, kafafunta ne suka shiga kyarma ta dan ture fuskarshi tana so ta bar gurin ya matseta sosai dan har sai da tayi 'yar 'kara, shaf ya manta da cikin jikinta saboda hankalinshi baya tare dashi, harshensa ya zura bakinta ya shiga tsotsa yana lumshe idanunsa, itama rintse idanunta tayi ledar hannunta na 'kokarin fad'uwa 'kasa! daurewa takeyi amma ta kasa kawai sai ta yar da ledar hannunta ta sarkafo wuyansa da hannuwanta tana wani irin rawar jiki ta shiga shan baki nshi, tana lumshe idonta, tayi bala'in missing din bakinshi da yawunsa mai za'ki da gamsawara, sosai suke sucking din junansu, har dai suka gagara tsayuwa ya zauna kan kujera ya dorata a cinyarshi, suka cigaba da sucking din bakin junansu duk sun wani gigice sun ma'kal'kale junansu. Littafin na kudi ne...! Kika futa da book din nan keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *70* 'Dumin jikinta da kuma yanayin yanda take shafa jikinsa ya sanya jikinsa ya mutu bacci me dad'i ya daukeshi, a hankali ta d'ora hannunta kan nasa dake 'kasan mararata sai taji ya sake janyota jikinshi ya rike kugunta cikin jikinta yayi wani irin zillo lokaci guda mararta tayi mata wata irin dam'ka! rintse idonta tayi tana cize bakinta ta kasa motsawa kawai saboda bata so ya tashi a baccin da ya daukeshi......Ta jima tana jin ciwon mara kafin a hankali a hankali yayi sauki! sai da baccinsa yayi nisa sannan tayi dubara ta zare jikinta anashi ta gyara mishi bargon jikinsa kana ta fita daga d'akin Palo ta tarar dasu Rashida suna hira ta dan zaune a hankali tace"Rashida had'o min tea ba zan iya zaman dainnig din nan ba." Rashida ta mike da sauri tana fad'in "To anti Wasila.'" Hajja ta kalleta cike da kulawa tace"Sannu kinji ko ai yanzu tilas kiyi ta jin sauyi iri iri a jikinki tunda ciki ya tsufa sai dai fatan rabuwa dashi lafiya." Tace"Wallahi kam hajja ni kadai na san abinda ke damuna duk dare da kyar nake bacci ga ciwon kwankwaso." Hajja tace"Dama ai me ciki komai na jikinta ciwo yake ciwon kwankwaso kuma dole ne gabobinki ne suke budewa insha Allahu idan kika zo haihuwa ba zaki sha wuya ba." Tace"Allah yasa Hajja." Rashida ta 'karaso hannunta rike da madaidaicin cup da tea a ciki sai plate wanda ta hado mata da soyayyan dankali da kwai. 'kasa ta sauka ta dan mike kafafunta ta soma kur'bar tea din tana had'awa da dankalin. **** *Camas! tare da Usaini dillali* Malam Usaini dillali yayi nasarar damfarar Camas kudin manya manyan filaye guda uku kud'in sun kai kimanin miliyan shida da rabi dan bayan kudin Wasila har da nata tasa a ciki kusam miliyan biyu usaini yayi mata roman baka inda yake cewa kafin shekara kudin filayen zasu kai miliyan goma ko fiye da haka, duk ya bata dakardun gaibu ya gudu ya bar gari dama ba'asan daga inda yazo ba..........Camas ta zama tamkar mahaukaciya lokacin da taje taga filayenta wani attajiri yana aikin gina gidan gona dashi, ihu! ta dinga kurmawa tana zagin masu aikin gurun wai filayenta ne waye ya basu damar ta'ba mata.....Tana wani irin huci! ta d'auko musu takardun filayen tana nuna musu, duk suka kar'ba suna dubawa, sai suka kwashe da dariya sunayi mata kallon mahaukaciya, babban cikinsu yace."Amma ke jahila ce wallahi wane shegen ne ya fada miki wannan takardar fili ce? hahaha! takardun wuta da ruwa ne saboda dakikiya ce ke baki fahimci abinda aka rubuta a jiki ba." suka dinga dariya suna kallonta........Wayarta ta dauko a fusace! take neman numbar husaini sai dai kiran duniya sai ace mata layin ma baya aiki kwata kwata, ta sharce gumin dake goshinta ta kallesu daya bayan daya tace''Idan kun san wata baku san wata ba, 'yan sanda zan kira muku sune zasu rabani daku shegu tsinannu barayi." Daya daga cikinsu yace."Zaki ci ubanki yanzu." Waya ya ciro ya kira mutumin da ya sanyasu aikin......Minti goma sai gashi cikin wata arniyar mota, ya karaso gurin yana me neman karin bayani, kawai tsaurin ido na Camas! sai ta hau kund'uma masa ashar har tana 'kiransa 'barawo mutumin ranshi ya baci da sauri ya kira *Anti daba* yace suje da ita su tuhumeta a inda yay sata idan ta'ki fada musu su ragargajeta! Tun a gurin suka dinga kwada mata mari suna haurinta da kafafunsu, sosai ta tsorata ta dinga kuka tana bawa mutumin hakuri yace."Ai sai kin fada musu inda naje nayi sata." Camas hankalinta yay masifar tashi ta dinga kuka tana data sani, haka dai *Anti Daba* suka tasa kyeyarta har ofis dinsu. **** Cikin kaya marasa nauyi ya fito palo yay bacci har ya gaji, baccin da ya jima bai yi irinshi ba.......Kai tsaye daining ya nufa dan da wata irin yunwa ya tashi daurewa yayi yayi wanka gami da sallah sannan ya fito palon , hankalinta a kanshi lokacin da ya fito palon sai ta fara yunkurin mikewa Rashida tace"Anti Wasila ki koma ki zauna ki fada min abinda kike so sai nayi miki." Girgiza kanta tayi tace"Aikin lada zanyi Rashida." Hajja da rashidan suka bita da kallo lokacin da ta nufi inda yake wanda su sai lokacin ma suka san ya fito palon Har ta'karaso inda yake idanunsa na ka nta, ya dan sassauta fuskarsa yana yi mata wani irin kallo wanda kana ganinsa kasan na tausayi ne. A hankali tace"Ya jikin."? Sai ya tafi tunani shaf ya manta plan dinshi, da sauri ya dan ya mutsa fuska yace."Yanzu kam alhmadullhi." tace"Ka jima kana bacci dan har nayi tunanin tashinka kaci abinci kasha magani gashi lokacin shan maganin ya 'kure biyar ta kusa." Ya aje cokalin hannunshi yana kallonta a nutse yace."Gwara ma da baki tasheni ba dan da kin tasheni mybe ki 'kara min wani ciwon ne tunda kin san bana so a tasheni ina bacci.' Tace."Eh nima tunanin da nayi kenan." Ya cigaba da kokarin zuba abincin, cikin nutsuwa ta kar'bi plate din tana kokarin zuba mishi ta hada masa komai ta tura gabanshi. Yace."Allah yay miki albarka." Cikin zucci ta amsa, tana goge hannunta da tissue yace."Sai ki 'karasa ladanki ko." Ta kalleshi tana son karin bayani. Girarsa ya daga mata fuskarsa da murmushi me kayatarwa, tayi kasa da kanta tana dan murmushi ta gane abinda yake nufi sai kawai tayi niyyar barin gurin, yace."Idan baki bani da hannuki ba to ba zanci ba." Ta juyo tana kallonshi cikin shagwaba tace"Bafa mu kadai bane a palon." Yace."Eh nasani tunda kina jin kunya dauko abincin muje daki.'" Makale kafada tayi tace"ka bari idan anjima sai na baka yanzu dai kaci wannnan da kanka." Ya wani lumshe idonsa yana mata shu'umin kallo yace."Idan anjima ba abinci nake so ki bani a baki ba, wani abu nakeso ki bani." Tace"Koma meye nayi alkawari kai dai kaci kasa magani." Yace."Kince Kinyi alkawari ko."? Daga kanta tayi alamun E yace."To zo ki zauna gabana naci abincin ina kallon fuskarki.'' Dariya tasa tana kallonshi, tace"Idan na zauna kusa da kai ba zakaci abinci sosai ba idan ka gama ci na dawo.'' Da murmushi a fuskarsa yace."A ganinki idan kina kusa dani zan kasa cin abinci ko? baki sani ba xaman ki a kusa dani shine zai sanya na cinye abincin ba tare da nasani ba." Kujerar daning din ta gyara ta zauna tayi tagumi tare da tsira masa ido tace"Shikkenan gani na zauna amma minti biyar na baka ka cinye abincin gabanka." Yanda ta fad'i maganar ya bashi dariya yace."ki dai 'kara minti biyar su zama goma abincin fa nada yawa." Murmushi tayi tace"Tom na kara minti uku." Yace." Okey." Agogon hannunshi ya d'an duba biyar da minti da minti biyu......Sai yay bisimillah ya fara cin abincin da sauri da sauri yana had'awa da lemo Dariya take kunshewa ganin yanda yake cin abincin hannu baka hannu kwarya wai baya so lokacin ya cika bai cinye abincin ba...........Ya d'ago kanshi suka had'a ido lokacin ya cika bakinshi da abinci me cike da ganyayyaki ga nama dariya take tana nuna bakinsa da hannunta 'kasan ha'barshi kan gemunsa duk miya! ta dinga kyalkyala dariya tana kallonshi......'Bata fuska yay da sauri ya kalli agogon hannunsa yaga biyar da kwata....Kallonta yay da sauri! itama tayi saurin kallon agogon hannunta, biyar da minti goma sha shida, Still dai da mirmushi a fuskarta ta d'aga masa hannunta mai daure da agogo tana nuna masa lokaci, 'Bata rai yay yace."Agogonki na latti." tace."Agogona dai-dai yake tafiya kai ka 'kara minti hud'u kan mintinan dana baka dan haka al'kawarinmu ya rushe. Murmushi yay wanda ya tsaya iya la'bbanshi ya mika hannunsa yana kokarin daukar tissue tayi saurin cirowa tana goge mishi bakinshi dai-dai inda ya 'bata a gurin cin abincin.....Kunyace ta rufe ta ganin yana mata wani irin kallo ta juya zata bar gurin......Hannunta ya rike yana me narkar da kwayoyin idanunsa cikin nata. Taji wani irin yanayi a jikinta, a duk sanda zai mata irin wannan kallon nashi takan ji tamkar wani mayen son shi a cikin zuciyarta. Mairairaice fuska yay ya mai da kanshi karamin yaro ya wani kankance murya yace." Ina so ki zama mutum mai cika alkawari kan abinda kika al'kawaranta, kada kice min komai kece kikayi min al'kawarin zaki bani du abinda na nema idan naci abinci yanzu kuma kice min alkawari ya rushe." Yanayin yanda yake kallonta da kuma yanda yake magana kasa-kasa yasa ta fahimci inda ya dosa, sam dazu bata gane abinda yake nufi ba sai yanzu da ya nuna mata zahiri......Jikinta a sanyaye tace"To ai baka da lafiya. " Ya dan kalleta cike da bege gami da tsantsar sha'awa yace."Duk cutar dake damuna dana kusance ki za tayi nata guri ke dai kawai ki bada kai bori ya hau." Gabanta na fad'uwa tana d'an kallon gefansu Hajja tace"Tom na amince amma dan Allah kada kayi min da karfi kuma sau daya za kayi." Da sauri yace."Haba!! ai nasan duk abinda ke faruwa ba zan mayi da kaina ba kece zakiyi abinki yanda kike so." Cike da rashin wayo tace"Yawwa dama ni bana so ka dunga buguna da karfi bana so wani abu ya same ni da abinda ke cikina." cikin rauni gami da tsoro take maganar Yaji wani irin tausayinsa na ratsashi, hannunta ya rintse a cikin nashi yace."Ki kwantar da hankalinki bbu abinda zai sameki keda yarona lafiya zaki haihu, kuma nace miki yanda kike so zakiyi sai dai idan kingaji na taimaka miki." Ajiyar zuciya ta sauke tana kallonshi. Da kyar ta iya cin abincin dare saboda tsabar fargaba motsi kadan gabanta sai ya fad'i! bayan sun gama cin abincin suna kallo a palo shi lokacin ma baya gidan ya dan fita, Ta mike a hankali tana kallonsu Hajja da rashida tace"Hajja zan shiga na kwanta yau bacci nakeji." Hajja tace.''Nima yanzu zan tashi dan har na fara gyangyad'i. Allah y bamu alkairi." Rashida tace"Lallai wallahi ku tsaya ku 'karasa kallon film din nan yayi kyau sosai." Hajja da Wasila babu wanda ya kulata kowanne da abinda ya dameshi. Ta jima zaune a gefan gado tana tunani ko kawai ta rufe kofarta ko ta gudu dakinsu Hajja tunda ta lura yana jin kunyar biyota dakin....Wani bangare na zuciyarta yace."Ki daure kiyiwa mijinki biyyaya ki samu aljanna kika sani ma ko zaki haihu ko bazaki haihu ba ko ki mutu da cikin a jikinki." Xuciyarta ta karye hawaye ya shiga zubo mata Jikinta a sanyaye taje tayi wanka ta kimtsa jikinta tsaf sai kamshi turarrika take ta kwanta tana jiran shigowarshi.... Cikin baccin da ya soma daukarta taji alamun shigowarsa dakin....Idanunta ta bude tana kallonshi ya nufi toilet tasan wanka zaiyi. Ya fito daure da babban towel ya tsaya gaban mudubi yana goge jikinshi......faffad'an bayanshi ta tsurawa ido tana kallo ta lumshe idanunta tana sauke zazzafar ajiyar zuciya.........Motsin zamansa taji a kusa da ita ta bude idanunta, cike da kulawa yace "Baki bacci ba." ? Dan d'aga masa kanta tayi tana kokarin mikewa zaune Yace."Ki koma ki kwanta mana." ta koma ta kwanta gabanta na dan faduwa tace"Kasha maganinka ko." Kallonta yay sai kuma yayi saurin cewa"Zan dai sha yanzu kafin na kwanta." Ya manta da wani magani dan bashi ne a gabansa ba, ashe ita hankalinta na kansa. Ya mike ya fita daga dakin, mintina goma ya dawo...... Paracetamol kawai ya 'balla ya watsa a bakinsa ya kora da ruwa, ya aje gorar ruwan saman fridge ya nufi bed din......Tana kallon zuwanshi sai ta rintse idanunta tana takure jikinta. Bargon ya dan ja a hankali ya shiga ciki idanunta ta rufe dai-dai lokacin da taji hucin numfashinsa a kusa da ita.........Hannunshi ya sanya ya d'an juyo da ita suna fuskantar juna........Ya sanya dan yatsansa kan le'banta na 'kasa yana shafawa a hankali. Shuru tayi duk kuzarinta yakare, cikin kunnanta ya kira sunanta, taji wani irin yarrrr a jikinta. A hankali ya cire mata rigar jikinta ya kai kanshi kan cikinta ya sumbata tare da fad'in Allah yay maka albarka yarona." Wasila na jinsa nata magana da dan cikinsa kamar me magana da mutum, mamaki gami da tausayinsa ne ya kamata ta lura yana masifar son abinda ke cikinta tun bai iso duniya ba. shafa sassan jikinta ya shigayi yana sa harshensa yana lasar sa'ko da luko na jikinta yana aika mata da wasu zafafan kesses masu hargitsa lissafi! wani irin rawa jikinta ya shigayi tsigar jikinta ta soma mikewa kamar dai koda yaushe jikinta ya mutu sosai ta saki jikinta ya dinga jagwalgwala iya son ranshi dan babu inda bai tsotsa ya lashe ba a jikintajagwalgwalata romantinc sukeyi irin wanda basu ta'bayin irinsa ba, cikin jikinta bai hanasu aikata komai ba, Amadu ya aikata komai cikin nutsuwa dan ita ya barwa fagen tayi iya yinta mai gudun kada ciki ya samu matsala sai gashi ta manta dashi, tana biyan bukatar ranta, sai da tayi iya yinta sannan ya shi ya soma nashi cikin nit suwa tana taimaka masa tare da shashshafa sassan jikinsa, duk sun rikice sun had'a zufa fatar jikinsu sai mannewa takeyi guri guda, kusan tare suka samu gamsuwa suka rungume junansu suna sauke numfashi. Littafin na kudi ne! Kika futar min da book keda Allah! kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *71* Can 'bangaran su Uwani kuwa, tun bayan tafiyarsu Wasila sai ta dan samu sassaucin cuzgunawa daga gurin Kuluwa, ta daina kyararta tunda ta gane tana da amfani, shi kansa Kawu Madu din lallabata yake yi wai su shirye suje ga gidan Wasilan tunda basu ta'ba zuwa ba, Uwani ta shiga tunani kan maganarshi tana jin tsoron daukarsu suje garin ganin gida suje su jawo mata abin kunya tasan ba komai ne yake d'awainiya dasu ba sai kwadayin abin duniya, kawu madu kullum cikin naci yake da dai ta gaji sai tace "Shikkenan zasuje amma sai karshen wata, kuluwa tamkar ta zuba ruwa a kasa tasha saboda murna da farin ciki. *** Sosai *Anti Daba* suka sa'bawa Camas kammani saboda ta kasa kawo musu shaida gamshashshiya wacce zata nuna musu da cewar ita d'in me gaskiya ce, kwanta biyu a hannunsu suka saketa bayan sun mata kashedi mai tsauri kan kada ta kuskura ta kara zuwa filayen nan tace nata ne duk ranar data sake zuwa to sai sun mata dukan mutuwa......A jigace ta fito bakin titi inda tayi parking din motarta ta nufa, wayam! babu ita a gurin, ashe ranar saboda tsabar rud'ewa a jikin motar ta bar key din, kuma akan idanun wasu matasa, aikuwa tana bada baya suka dauke motar, sai yanzu ta tuna abinda ya faru tsugunawa tayi bakin titi rana na dukanta ta dinga kukan bakin ciki, sai da tayi ta gaji ta samu babur ta hau government house ta nufa. ****** Yau dai basu samu damar zaman karatu ba dan basu tashi da wuri ba, Rashida ma gajiya tayi da zaman jiransu ta bar gurin, basu fito palo ba sai takwas saura, lokacin Hajja da Rashida har sun karya suna zaune suna hira...... Kai tsaye inda Hajja ke zaune suka nufa a nutse suka gaisa Wasila sai sinne kai takeyi kunyar hajja takeji sosai, barin gurin tayi ta nufi daning shi kuma ya zauna suna magana da Hajjan.........Suna break fast ta d'an kalleshi sai akaci sa'a shima ita yake kallo, kasa tayi da kanta, ya gane duk sanda take son yi masa magana kunya na hanata, yace."Akwai abinda kike bukata ne."? Ta dago kanta a hankali tace"Ina so ka dan bani waya ta ina so mu gaisa da Kawu duk da dai bani da numbar wayar Kawu Habibu wacce zata sadani dashi nasan baza'a rasa a gurinka ba.' Murmushi yayi yana goge bakinsa yace."da akwai numbar Kawu Habibu a wayata sai da kwanaki nayi ta kiran wayar baya dagawa nasan fushi yake dani kan abinda ya faru.'' A hankali tace"Kawu Habibu fushi ne dashi nima bama shiri sosai munfi yi da mai allo." Wayarsa ya mika mata yace."Ki duba sunanshi nayi serving da Habibu garko." Wayar ta amsa tana budawa taga hotonsu ita dashi a fuskar wayar hoton da hafsa ta daukesu lokacin da suka zo hoton yay masifar kyau......... 'Dan kallonshi tayi hankalinsa na kan karamar wayarsa yana dubawa, ta dauke kanta tana sauke ajiyar zuciya bata ta'ba tsammanin haka yake da saukin 'kai ya mai da kansa karamin yaro duk dan saboda farin cikinta. Tayi ta kiran layin Kawu Habibu gashi dai tana shiga amma bai dauka ba, Ta dan kalleshi sai taga yayi murmushi, a nutse yace."Mutukar fa zai ga numbarta ce ba zai dauka ba har yanzu nima kunyar hada ido nake dashi nasan abinda nayi ban kyauta ba amma ai na bada hakuri kuma ya cancanta a yafe miki ko." Cikin wani irin yanayi yake maganar.......Sai taji tana jin zafin Kawu Habibun meye abin ri'ko da daukar gaba, ai itace mai laifi tunda duk abinda ya faru itace ta jawowa kanta itama yanzu ta daina ganin laifinsa bisa ga sakin da yay mata ta wani gefan ma farin ciki take da hakan ta faru tunda gashi tayi hankali tasan inda yake mata ciwo. Rau-rau tayi kamar zatayi kuka tace"Kawu Habibu haka halinshi yake kayi hakuri." Yace."Nine zan bashi hakuri ai kada ki damu duk sanda Allah ya saukeki lafiya zan daukeki muje har gidanshi na bashi hakuri ai tunda ina sonki babu abinda ba zanyi ba." Hawaye suka zubo mata ta tsira masa ido tana kallonshi ta rasa wane irin so yake mata! Yace"Ke kam bakya gajiya da koke koke goge hawayenki." Ya mika mata tissue kin kar'ba tayi tana shashsheka, hannunta ya rike ya mikar da ita suka nufi dakinshi. Rungumeta yay ya rarrasheta tayi shuru kana ya bud'e wata drowar dake gefan gadonshi ya dauko mata wayoyinta da jakarta, cinyarta ya aje mata yace."Ki duba kiga abinda baki gani ba sai ki fada min." A hankali ta bude jakar tana dubawa komai nata data sani na ciki ga sabbin kudinta nan na sadakin auranta da sauran tarkacenta a ciki ta aje jakar tana kokarin kunna wayar, ya kar'ba ya kunna mata. Numbar Kawu Habibu ta dauka a wayar tata ta soma kiranshi, aikuwa ya dauka duk suka cika da mamaki. Muryarta na rawa tace"Kawu Ina kwana" Ya amsa yana tambayar wacece.''? Tace."Kawu nice Wasila." Tana ji ya sauke ajiyar zuciya yace."Wasila ya kuke ina fatan kunanan lafiya ko? ina mijin naki."? Ta dan kalleshi yana zaune yana jinsu, tace"Kawu gashinan kusa dani yana jinka." yace."Masha Allah." Tace"Kawu dan Allah kayi hakuri ka daina fushi nice fa mai laifi dan Allah ka yafe masa kamar yanda mai allo ya yafe masa." Kawu Habibu yace."Wasila ni tuntuni na yafe masa abinda ya faru kawai duk sanda na tuna sanda yazo gabanmu yace ya sakeki raina yake 'baci sosai, amma ni bana rikon mijinki." Tace"To Kawu me yasa idan ya kira wayarka baka dauka." Shuru yayi tace"Kawu kayi hakuri magana ta wuce nima nayi alkawari insha Allahu bazan sake baku kunya ba." Yace."Masha Allahu dama haka nake so naji." Amadu ya kar'bi wayar daga hannunta, a nutse yay sallama Kawu Habibu ya amsa cikin mutumci suka gaisa da juna, Kawu Habibu kunyar abinda yayi masa taso ta hanashi magana, inda shi kuma Amadu ya nuna masa komai ba komai bane ya kuma tabbatar masa da cewar abinda ya faru a baya insha Allahu ba zai sake faruwa ba a gaba..........Kawu Habibu yaji dadin maganarshi sosai da sosai dan yanzu babban burunsu shi da dan uwansa shine yarinyar ta zauna a dakin mijinta. Mika mata wayar yay bayan sun gama ta karba tana fad'in "Kawu dan Allah idan ka koma gida ka bawa mai allo wayar ina so mu gaisa dashi." Kawu Habibu yace."Insha Allahu idan na koma gida zan bashi yanzu haka nayi tafiya wani gari zan kuma kwana biyu acan sai dai na koma din." Tace."To Kawu Allah ya dawo da kai lafiya." Ya amsa da "ameeen." Sukayi sallama cike da kaunar junansu..........Ajiyar zuciya ta dan sauke kanta a kasa, yanzu tana masifar kaunar kawunanta saboda ta gane yanxu sune gatanka........Hannunsa taji cikin nata yana saka mata wani abu, ta dago kanta tana kallonshi, tana kuma kallon hannunta, wasu takardune guda biyu ya saka mata cikin hannunta........Kallonshi tayi tana neman karin bayani. Yace." Kada kice komai ni nayi niyya kuma idan nayi kyauta ba'a cewa dani dan me? na jima da mallaka miki wasu kadarori nawa tun ranar da na amshi budurcinki na mallaka miki rumfunana biyu dake cikin kasuwar sabon gari, naki ne a halin yanzu halak malak, tun daga ranar dana mallaka miki kawowa yau din nan duk wani abun da aka samu na cinikayya suna cikin asusuna, insha Allah zamuje a bude miki account zan sa miki kudinki a ciki, bayan wannan kuma akwai sabuwar motar dana siya miki tana can gareji a ajiye, yanzu ki rike key d'in a hannuki." Ya mi'ka mata key din motar yana murmushi. Hannunta ne ya shiga rawa, ta rasa ma abinda zatace masa sai kawai hawaye ya 'balle mata, rungumeta yay tsam a jikinsa yana shafa bayanta, cikin shashshekar kuka tace"Nagode mijina Ubangiji Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana Allah ya rabaka da sharrin masu sharri Allah ya bamu zaman lafiya da zuria masu albarka." Ya dinga amsawa yana dan bubbuga bayanta a hankali. **** Cikin ikon Allah da hukuncinsa komai na tafiya dai-dai a zamantakewar auransu, ta samu nutsuwa dashi ya samu nutsuwa da ita, yayin da karatunsu na al'kur'ani yayi nisa sosai yanzu sun wuce izifi ashirin tunda kullum sau biyu yake musu kari, bangaran littafan addini kuwa sun wuce matakin su ahlari da fikhu yanzu manyan littafai yake musu irin su Minhajil musulum zaduzjaujen Ismawi balaga......bangaran ilimin addini Wasila da Rashida ba'a cewa komai sai godiyar Allah. Cikinta ya shiga wata na tara, lokacin kuma ciwuka suka tsananta yau ciwo gobe ciwo haka dai take daurewa duk sanda bala'in ya isheta sai ta shiga daki taci kukana ta koshi.............Gashi baya xama a gida sosai kusan kullum sai sun fita da jama'arshi yawon campain, wani sa'in ma kwana sukeyi ko kuma su dawo cikin dare lokacin ta dade da yin bacci, ga Rashida ta soma zuwa makaranta abun dai duk babu sauki ta kowanne bangare wani lokacin hajja itake zama tana debe mata kewa idan kafafunta sunyi tsami ta matsa mata a gaskiya babu abinda zata ce da matar sai dai addua. Akwai ranar da Anti Kubura ita da yaranta suka zo gidan suka tarar da Hajja na matsawa Wasila kafafunta duk sai suka shiga mamaki mai tsanani yanzu kamar hajja ke aikin matsar kafa.....Anti Kubura ta kufula ranta yayi masifar 'baci ta kalli Wasilan shekeke tace"Wato asiri da surkullen naku na fulani ya dawo kan baiwar Allah wacce bataji ba bata gani ba, kawai saboda tsabar rashin arziki ki mike kafafu ki sanyata matsar kafafu shin itace tayi miki cikin da zaki dinga sata aikin wahala? ke ko kunya bakiji ba." ! Hajja tace"A'a kubura nice nasa kaina ba itace ta sani ba, to idan ma itace ta sani laifine dan na matsa mata kafafunta ai lalura ce! bana son irin abinda kikeyi kubura." Hajja ta karashe maganarta cikin jin rashin dadin abinda tayi.....Suhairat da takeji kamar taje ta turmushe Wasilan ita da cikin jikinta tace"A'a Hajja wallahi da sake! baxai yiwu ba idan suna cin 'kasa to su kiyayi ta shuri! asirinsu da surkullansu ba zaiyi tasiri a kanki ba, shi da Yaya Amadu da yaga zai iya sai yaje yayi, amma kamar wannan mara gata da galihu ta saki a gaba kina mata matsar kafa! ai bata isa ba idan ita bata san darajarki ba to mu mun sani." Wasila ta soma kokarin mi'kewa ta bar musu gurin......Hajja ta dan rike hannunta tana mata sannu, hawayen dake kokarin zubo mata ta mayar ba tace komai ba tabar gurin, tana jin Suhairat na zaginta da kiranta 'Yar iska jahila mai bin maza." Wannan kalmomi sunyi mata ciwo sosai, kawai ta kwanta kan gado ta shiga kukan bakin ciki da takaici! Illar ka aikata mummunan abu kenan bata ta'ba zina ba amma gashi anzo har cikin gidanta ana kiranta da karuwa me bin maza... Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *72* Bayan shigar Wasila d'aki Hajja ta shiga yiwa anti kubura da Suhairat fad'a kan abinda sukayi bai dace ba suzo har gida s suna zagin matar gida......... aikin matsar kafafu itace tasa kanta ba wai Wasilan ce ta sanyata ba, tace mutukar idan kun san tashin hankaline zai kawo ku to ku daina zuwa dan kun san idan Amadu yaji ba zaiji dadi ba bana kaunar abinda zai 'bata masa rai kamar yanda baya kaunar abinda zai 'bata min rai! Ke suhairat ki iya bakinki wallahi naji kina kiranta karuwa a gidan ubanki tayi karuwancin? to wallahi kika sake Amadu yaji wannan maganar zai iya daureki kuma wallahi ba zance masa dan me ba tunda bakinki ne ya jawo miki." Da jin abinda Hajja take fada sai kawai anti kubura ta fashe da kuka tana fyace majina tace"Haba Hajja ashe kudi yafi zumunci kada fa ki manta ni dake uwarmu daya ubanmu daya, Amadu kuwa bake ce kika haifeshi ba dan mijinki ne amma kike kokarin za'barsa akaina shikkenan nagode."Anti kubura ta karasa maganar tana mikewa, tsaye suma Suka mike ransu a 'bace! Hajja tace"Yanda kika dauki al'amarin ni ba haka na daukeshi ba Kubura nagode kwarai yau ni kikewa gurin haihuwa ko babu komai." Anti kubura ta kad'a kan 'yayanta suka fita daga gidan ransu a tsananin 'bace! Hajja kuwa sai da ta matse hawaye kafin ta mike ta shiga cikin daki. Rashida da ta dawo gidan duk sai ta gansu wani iri babu cikakkiyar walwala alhalin ba haka ta tafi ta barsu ba, sai da suka ke'be da 'yar uwarta take tambayarta abinda yake faruwa, Wasila na hawaye take fada mata irin zagi da cin mutuncin dasu Suhairat da mahaifiyarta suka zo sukayi mata. Rashida ta fusata sosai tace"Wallahi anti Wasila da ina gidan sai na rama mi ki wannan ai rashin mutuncine da iskanci su shigo har cikin gidanki suna zaginki na rantse da girman Allah duk ranar da Suhairat ta sake zuwa gidanan ta zage ki sai na nuna mata wacece ni sai ta futa da fashashshan baki." Wasila tace"Ki kyaleta rashida tayi na farko tayi na karshe nima na dauki al'kawarin kan duk ranar da ta sake zuwa taci min fuska cikin gidana sai ta gane bata da wayo........... To Yau ma bai shigo gidan da wuri ba sai kusan sha biyu da rabi na dare lokacin tayi bacci har ta gaji dan wajejan takwas ta kwanta yanzu kwanciyar ma wuya take mata sai tayi ta juye juye da zarar bacci ya dauketa bata minti talatin sai ta farka, jin shigowarsa dakin ya sanya ta mike zaune......Yace."Baki bacci ko jikin ne.'? Girgiza masa kai tayi, yace."Okey bari nayi wanka ko." ba tace masa komai ba ya nufi toilet, tana zaune ya fito ya kimtsa jikinsa ya fita daga dakin Minti biyar ya dawo hannunsa rike da ledoji guda biyu ya aje kasan kafet ya bude fridge ya dauki lemo da ruwa........Lokacin da yake kokarin zama kasan kafet ne ya fahimci damuwa a fuskarta, ya kalleta cike da kulawa yace." Menene? Hawayen da take 'boyewa suka su'bce ta soma kuka da shashsheka Yaji duk wani annushuwa da farin cikin da ya shigo dashi ya dauke, jikinsa na kyarma ya zauna kusa da ita yana me rungume kafadunta da hannunsa....."Kiyi shuru ki fada min abinda ke damunki bana son wannan kukan naki." Abinda yake fada kenan yana goge mata fuska da hannunshi. Kwanciya tayi a jikinsa tana cigaba da kukanta. Hankalinsa yay masifar tashi ya dinga rarrashinta da kalamai masu sanyi,da kyar tayi shuru yace."Kukan da kikeyi bai da amfani saboda yana sa hankalina tashi ki fada min abinda ke damunki." A hankali tace"Meye tsakaninku da Suhairat."? Sai ya shiga tunanin wacece ma Suhairat? can ya tuna yarinyar anti kubura ce kanwar Hajja. Yace."Kanwata ce me ya faru.''? Ajiyar zuciya ta sauke tace"Ai kai baka da wa ko 'kanwa." Yace."Eh hakane ita suhairat din yarinyar kanwar Hajja ce anti kubura." Tace."Kace mata kada ta sake zuwar min gida tunda ba alkairi ne yake kawota ba." Ya danyi shuru yana mamakin maganarta, cikin nutsuwa yace "Kince ba alkairi ke kawota ba sai ki fada min abinda ya faru dan na fahimci dama keda ita tuntuni kunsan juna." Tace."Idan na fada maka abinda ya faru ranka zai 'baci watakila ma ka dauki tsatstsauran mataki akansu har ita anti kuburan, fad'ar maganar bata da amfani tunda ba alkairi ba ne, dalili kenan da ya sanya nace ka hanasu shigowa inda nake dan mutukar suka sake zuwa suka zagi iyayena sai na rama.".....Ranshi yaji ya 'baci jin abinda tace Yace."A gaban hajja kukayi wannan shashancin."? Mikewa tayi daga jikinsa tace"Nifa kar kaga laifina nasu ne dan bar musu gurin ma nayi saboda abinda ya dameni shi ya dameni." Yace."Shikkenan tunda bakya so su shigo miki gida zasu daina shikkenan ko?" Babu kunya tace"Eh." Yace."Sauko kici abinci." Tabi ledojin dake gabansa da kallo, a hankali ta sauka ta dan mike kafafunta shi kuma ya shiga bude ledojin manya manyan kaji ne gassasu wanda sukaji hadi sosai sai kamshi sukeyi. A nutse suke ci suna dan hira yana bata labarin irin nasarorin da yake samu ta 'bangaran siyasar shi, yanzu babu local goment din da basu kai ziyara ba kuma ko ina sukaje cike da nasara suke dawowa, al'amarin siyasar dai ya dauki zafi sosai da sosai ta inda ko ina ka zaga a fad'in jahar kano zance Amadu Musa ake da fatan Allah ya bashi mulkin jahar kano a hannunsa, pastes dinshi sai yawo suke a titi kasuwanni gami da jikin gidajen mutane, gabakidaya al'ummar jahar kano sun gaji da mulki Lawal rabo sauyi kawai suke bukata a jahar tasu. Sosai taji dad'in irin nasarorin da yake samun ta 'bangaran siyasarsa dan har sai da fuskarta ta nuna alamun jin dadi ta dinga yi masa addua gami da fatan nasara akan dukanin abinda ya sanya a gaba.........Da kyar ta yunkura ta mike tsaye ya dan bita da kallo lokacin da ta nufi toilet sai ya mai da hankalinshi kan abincin dake gabanshi......brush tayi ta tsuguna tana fitsari dan yanzu haka takeyi bini bini fitsari kuma idan ta tsuguna ba wani na kirki takeyi ba.? tana tsarki taji wani abu me yauki na biyo hannunta bata damu ba dan tun da cikinta ya tsufa take ganin abubuwa iri iri, da kyar ta mike tsaye tana cije baki ji Tayii kasan mararta yayi mata wata irin dam'ka! salati tayi ta dan rike kofar toilet din tana mai da numfashi. A hankali ta lalla'bo ta fito lokacin baya dakin sai ta kwanta kan bed tana lumshe idonta......Bacci ya soma fizgarta taji motsin shigowarsa ya shiga toilet yay brush ya fito ya kashe fitila yaje ya kwanta kusa da ita......Kamar dai zai daure sai ya kasa hannunsa yasa ya dan janyota jikinsa yana shafa bayanta da gashinta Gabanta ya shiga faduwa tana addua Allah yasa kada yace wani abu dan yanda take jin ciwo bata jin zata iya wani abun.....Aikuwa dai abinda yake nufi kenan dan sai kesses yake mata tare da kokarin sabule mata rigar jikinta. Cikin sanyin murya tace"Dan Allah kayi hakuri yau cikina ciwo yake." A marairaice yace."Nayi kokarin yin hakan nakasa ki daure nayi koda sau daya ne hankalina zai kwanta." Shuru tayi masa, ya cigaba da wassaninsa da sassan jikinta yayin da take sake jin ciwo na tsantsanta a gareta ta dinga cije bakinta tana kokarin daurewa, lokacin da ya shigeta wani irin murd'a da dam'ka mararta tayi ta rirrike damtsansa tana salati! shi kuwa ai baya ma cikin nutsuwarsa dan duk sanda zai jishi cikin wannan gurin yakan manta da hankalinsa.....Jin kamar an 'kara mata ni'ima ya sanya ya kwarkwance ya dinga buga sambatu yana bugunta sam ya mance lalurar da take tare da ita. Kuka ta dinga yi tana masa magiya ya rabu da ita, lokacin yake kara kuzari da karfi kukanta na kara ingixashi kan abinda yake yi............nishi ta dinga fitarwa sama-sama yaron dake cikinta yana dunkulewa guri guda yayinda mararta take mata wata irin dam'ka tana murd'a mata!! "Wayyo Allahna ka kawo min agaji kada na mutu na shiga uku abinda nake gudu sai ya faru."! sambatun surutun da take kenan! ya rufe mata bakinta yana sake bugunta da karfi shima yana daf da kawowa ne shiyasa ya rasa nutsuwarsa...........Jikinta ne yayi lakwas duk wani kuxari nata ya kare sai idanunta suka hau lumshewa tana shiga ganin bibbiyu cikin idanunta. Sai da ya tabbatar da duk ya fitar da abinda ke mararashi sannan ya hakura, aikuwa yana zare jijiyarshi wani irin jini ya ambulo daga jikinta.......Yaji saukarshi kan cinyarshi, cikin gaggawa ya kunna fitila dakin yay haske kawai sai yaga idanunta suna kafewa tana jawo nunfashi da kyar ga jini sai ambulowa yake daga gabanta. Salati ya sanya a d'imauce ya sauka daga bed din, yay dira dira sai ya dawo bed din a gigice ya dauki jallabiyarsa yasa da gajeran wando.....Hannunsa na kyarma ya dauki wayarsa ya kira Dr Nasir yace gashinan zuwa hospital dinshi emagency........Garba ya kira a waya yace maza ya fito da mota.......Yay gaggwar maida wayar aljihunsa ya tarairayota jikinsa sai rawa yake yaga tayi lakaf komai nata ya daina aiki! Kawai sai yaji ya tsinke da al'amarin cikin gaggawa ya fita daga dakin ya kira Hajja a gigice ta fito ita da rashida suka shiga dakin. Rashida na ganin halin da yar uwarta take sai ta fashe da wani irin kuka tana fad'in "Anti Wasila kada ki mutu ki barni wayyo na shiga ukuna." Rirrike hannunta tayi tana kuka, ita kuwa hajja ba yarinya bace ganin babu kaya a jikin Wasila ya sanya ta fahimci abinda ke faruwa, wato rashin hakurinsu yasa sun jawowa kansu matsala, na'kuda mai tafe da jini ai hadari ce sosai. Da sauri ta umarceshi wanda yake tsaye ya rasa yanda zaiyi da ya sani yake yafi dubu....Tace"Ka dauko mata kayanta ka sa mata muje asibiti." Sai sannan ya dawo hayyacinsa ya nufi wardrobe cikin saurin gaske. Rashida ce ta sa mata kayan shi kuma ya dauketa a hannunshi suka fita daga dakin........Garba ne ya tukasu zuwa asibitin dr nasir yayin da jikin wasila ya sake rikicewa sai salati takeyi tana yin wani irin nishi wanda kana jinsa kasan tana cikin halin ciwo........Amadu addua kawai yake mata hankalinsa duk ya tashi lokacin ita kuma ta dinga rirrike masa hannunsa tana wani irin murkususu a jikinsa. Littafin na kudi ne.... Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *73* A mutukar galabaice aka shiga dakin haihuwa da Wasila, Dr Nasir da wasu narses biyu suka rufu a kanta har sai da suka samu nasarar tsayar da jinin dake zuba daga jikinta, lokacin kuma ta daina duk wani yunkuri da takeyi duk karfinta ya kare bata gane wanda yake kanta, Dr Nasir ganin halin da take ciki na baraxana da rayuwarta ya sanya ya fita daga dakin da sauri, nan ya iskesu a tsaitsaye Amadu sai zurga zurga yake a gurin hankalinsa a tashe. Dr yace."Yallabai muje ofis zamuyi magana." Amadu ya juyo yana kallonshi, ganin yanayin fuskar dr din ya sanya jikinsa yin sanyi sai kawai yabi bayanshi yana mi'kawa Allah a'lamarin. Dr Nasir yace"Yallabai yarinyar nan ta galabaita sosai dan duk wani karfinta ya kare, ba zata iya haihuwa da kanta ba kayi hakuri ka sanya hannu yanzu mu shiga idata tiyata." Wani irin gumi ne ya shiga yanko masa, idanunsa sunyi jawur ya karbi takardar dake hannun Dr din jiki a sanyaye ya sanya hannu ya aje takadar yana me dafe kansa Dr ya mike a hankali yace"Yallabai ka kwantar da hankalinka insha Allah za'ayi nasara." Kanshi na 'kasa har dr din ya fita daga ofis din bai dago ba dik ya rasa yanda zaiyi yana ganin kamar rashin hakurinsa ne ya janyowa yarinyar shiga wannan matsala........Hannu yasa ya goge gumin fuskarshi ya mike ya fita daga ofis din da sa'bulallan jiki.....Hajja da rashida na ganin yanayin sa ai duk hankalinsu ya tashi,Rashida kam kuka tasa tana adduar Allah ya raba 'yar uwarta da wannan wahala da take ciki. Dr Nasir na komawa dakin sai yaga nurses din sun rufu a kanta, tun kafin ma ya fadi abinda ke bakinsa daya daga cikinsu tace"Dr insha Allah zata iya haihuwa da kanta dan gashinan yaron ya soma fitowa sai da babu karfi a jikinta wanda zata taimaki kanta." Dr nasir yace."Alhamdullhi kuyi mata duk wani kokari da kukeyi mu gani idan bata haihu ba nan da minti goma za'ayi mata Cs domin ceto rayuwarta. yana gama maganar sai ya fita daga dakin yaje yana shaidawa Amadu halin da ake ciki hannunsa ya daga sama yana rokon Allah ya sauketa lafiya. To cikin ikon Allah Wasila ta dan samu karfi da kuzari a jikinta ta dan dunga taimakawa kanta gurin yin nishi yayin da su kuma narses din suke mata dabaru irin nasu, har Allah yasa kan babyn ya soma fitowa sai kawai suka yanke shawarar yankata domin rage mata wahala guri daya suka yanka, aikuwa tana yin wani yunkuri babyn ya fito tare da mahaifarshi.....Lokacin taji wani irin sanyi duk wani ciwo da takeji ya dauke da kyar ta kalato miyau ta hadiya ma'kogwaronta ya bushe kamas. Cike da farin ciki narses din suka shiga gyara babyn suna kwarzanta kyawun yarinyar gata katuwar gaske tamkar ba haihuwar fari ba.........Wasila na jinsu sama sama tsabar wuya da galabaita ta hanata motsa koda d'an ya tsanta ballanata ta bude ido taga abinda ta haifa. Da saurin nurse ta fita cike da walwala da farin ciki ta samesu sunyi jugum jugum da sauri tace"Dr ta haihu yanzu an samu baby girl." Dr Da Amadu suka mike da sauri sai suka soma rige rigen shiga dakin Amadu sai washe baki yake kamar gonar audiga.......Ita kam rashida zubewa tayi a gurin tana sujjadar godiya ga Allah.....Dukaninsu suka shiga dakin, muryoyinsu ya sanya Wasila dan bude idonta tana kallonsu dishi dishi taga sai murna da farin ciki sukeyi suna dariya, rintse idanunta tayi tana ajiyar zuciya tabbas sai yau tasan tazo duniya ashe haka mahaifiyarta tasha wuya kafin ta haifeta.......Dr Nasir ya kalli Amadu dake kokarin zuwa gadon da take kwance yace."Yallabai ina ganin dole ayi mata karin jini saboda ta zubar da jini da yawa." Yace."Dr ayi komai idan da hali ma za'a iya daukar nawa idan zaiyi dai-dai da nata." Dr Nasir yace." okey to zan gwada yanzu." Kusa da ita ya tsaya yana dan kallon fuskarta lokaci kankani ta rame duk tayi zuru zuru, ya kama hannunta ya rike cikin nashi, idanunta ta bude tana kallonshi, a hankali yace."Sannu." Kanta ta daga mishi ta maida idanunta ta rufe.........Hajja da Rashida suka karaso gurin suna mata sannu ba tare data bude idanunta ba ta daga musu kanta.....Hajja ta kalleshi da fadin "Gaggawa ta sanya bamu dauko komai ba dole aje a dauko mata kaya t unda na jikinta sun baci." Yace."Bari na koma gidan yanzu." Hannunta ya saki da sauri ya fita daga dakin........Suna tsaye ita da rashida nurses din suka fito daga wani daki sun shirya baby tsaf da ita cikin kayan sanyi tana kamshin turare me dadi.....Hajja ta sanya hannu ta karbeta sai washe baki take tana musu godiya........daya daga cikin narses din ta tsaya kusa da Wasila tana mata magana......bude idanunta tayi tana kallon narse din da kyar tace."jiri ne kawai ke damuna sai bacci." Nurse din tace"To bari na taimaka miki muje toilet na gyara miki jikinki sai ki kwanta kafin Dr ya shigo." Daga kanta tayi narse din ta kama hannunta suka mike tsaye a hankali a hankali suka nufi toilet din dake cikin dakin.......ma dai-daicin ruwan dumi narse din ta hada mata ta zaunar da ita a jikin ruwan kana ta samu towel mai tsafta da wani ruwan d'umin tana dan danna mata jikinta.........Fitowa tay daga toilet din wanda yayi dai-dai da shigowarsa dakin hannunsa rike da ledoji Hajja tace"Yawwa kayan ne ko."? Yace."Sune Hajja ina take.'? ya fada yana rarraba idanunsa a dakin....Hajja tace "Tana bandaki." Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya dan tsaya kusa da rashida yana le'ka fuskar babyn tashi.....Hajja ce ta karbi kayan hannunsa ta mikawa nurse din ita kuma ta kar'ba ta daukar mata riga da zani na atamfa da pants da audiga guda biyu, ta juya da sauri ta koma toilet din Rashida ta mi'ka masa babyn tana murmushi tace"Yayana kamarku daya da yarinyar na dauka ma zata dauko kammanin anti na saboda wuyar data bamu kafin tazo duniya." Murmushi yayi ya karbi yarinyar yana kallonta yace."naji dadi da tayo kammanina rashida nima ai nasha wuya kafin na sameta." Rashida na cike da farin ciki tace"Ubangiji Allah ya rayata ya bawa mamanta lafiya." Ya amsa da "ameen lokacin da yake kara bakinsa kunnan yarinyar yana mata hud'uba gami da kiran sallah. Ganin nurse din ta fito da ita daga toilet din a kimtse gashi tana tafiya da kafafunta sai ya sauke ajiyar zuciya yana sake godewa Allah da ya sanya komai yazo cikin sauki.......Dr ne ya shigo yace." Yallabai zamuje yanzu a dauki jinin." Sai yay gaggawar mikawa rashida babyn dake hannunsa suka fita daga dakin tare da dr din.....Rashida da hajja suka nufi gadon da Wasila ke kwance suna sake yi mata sannu, kai kurrum take iya daga musu bakinta ya mutu murus har yanzu tana tuno irin bakar wuyar da tasha acikin awannin da suka gabanta, rashida ta dan zauna kusa da ita a hankali tace"Anti wasila baki dauki babyn ba." idanunta ta bude a hankali take kallon rashidan da babyn tayi murmushi a hankali tace "Rashida yarinyar na kama da babanta ko."? Rashida tasa dariya tana kallon Hajja tace" Eh mana nida hajja ma haka muka ce." Murmushi ta sakeyi ta rufe idanunta a hankali tace"Allah yayi mata albarka." Rashida da hajja suka amsa da "ameeen" Bacci me nauyi ne ya dauketa wanda tana baccin dr yazo yayi aikinshi ya gama ya fita Amadu kam fita yayi harabar asibitin ya dinga kiraye kirayen waya yana shaidawa 'yan uwa da abokanan arziki karuwar da ya samu. Karfe bakwai na safe Khalifa da matarshi suka shigo asibitin..........Khalifa ya dauki babyn ciki da farin ciki yake mata addua da fadin Afnan ta samu 'yar uwa dama kullum maganarta yaushe momynta zata siyo mata kanwa." Hajja da rashida suka saka dariya ya kalli Wasila dake dan murmushi yace "Sannu Wasila Allah ya kara lafiya kin iya haihuwa gaskiya kin biya mu tunda kika iya haifo mai kama damu." Murmushi tayi cike da kunya ta sunkuyar da kanta kasa, hafsa ta zauna kusa da ita tana mata sannu da jiki hafsa tayi sha'awar yarinyar wasila taji inama itace ta haihu ita yanzu cikinta watanshi hudu da sauran lokaci. Bayan sun koma gida misalin uku na rana sai ga mutanan garko Inna hajara da bitan da kuma matar kawu Habibu mai suna Saratu, mai allo ne yace maza maza suzo su gane masa abinda aka samu kafin yazo.......Su Wasila sunji dadin zuwansu sosai, nan inna hajara da bitan sukaga irin daular da Wasilan ke ciki dukaninsu mamaki suka shigayi babu shakka ba karamin mutum yarinyar ke aure ba, lalacewa sukayi gurin kalle kalle a gidan har gariba tayi gashi mai allo y ace su koma da wuri, Aikuwa Wasila tace ba xasuyi tafiyar dare ba sai da su bari sai gobe.....Inna hajara tace"Wai ni jama'a gidanan ba'a ganin fad'uwar rana ne? nifa tunda na shigo gidanan nake ganin yanayi daya baka gane ya yanayin gari ya yake wai ashe har magariba tayi bamu sani ba oh." Rashida ta dinga mata dariya tana fad'in "Nima lokacin da nazo gidan haka nayi ta sai da nasaba tukkuna nake ganewa idan lokacin sallah yayi zakiji kiran sallah ko kuma ki kalli agogo." Ina hajara tace"Yo duk cikinmu waye ya iya agogo ai kina sake baki sanar damu lokaci ba." Wasila dake zaune kusa da bitan tana shayar da babynta nono tace"Nifa Inna ba zaku koma da wuri ba dukaninku zaku zauna sai anyi suna nayi ar'ba'in tukkuna." Inna hajara tace"Ashe dai baki da hankali wasila yo ai idan wasu suka gamu rud'u rud'u sai su dauka kwadayi ne ya zaunar damu yanzu ma dan dare yayi ne shiyasa da tuni mun tafi." Wasila tace"Dan girman Allah inna ki zauna ko bitan ku taimaka min." Bitan tace"Idan banda abinki wasila wannan baiwar Allah na zaune tare dake tana iya bakin kokarinta a kanki ai idan muka zauna sai taga kamar mun raina kokarinta ne." Hajja dake kokarin 'karasowa inda suke tace"A'a bitan ni bazance komai ba wallahi ni kaina zanfi jin dadi ace wata daga cikinku ta zauna tare damu har yarinyar nan tayi ar'bain." Bitan tace"To sai dai ko Hajara amma dai sai abinda malam yace Hajja tace"malam ba zaice komai ba insha Allahu. Koda Amadu ya dawo gidan ya tarar dasu Inna hajara sai yaji dadi sosai ya shiga har inda suke suka gaisa a mutunce yana tambayarsu mutanan gida da malm mai allo, sukace kowa lafiya lau malam yace ayi maka barka kafin yazo.....Yace."Insha Allah gobe zan sanya Garba yaje ya daukoshi domin yazo yaga abinda aka samu. Kafatanin ma'aikatan gidan babu wanda bai shigo yaga baby ba, dukaninsu suna cikin farin ciki mussaman Garba da Abdulhadi aranar Amadu yayi musu kyatuttuka duk domin farin cikin da suka nuna bisa ga 'karuwar da ya samu. Wasila taga gata da kulawa gurin Hajja da inna hajara babu abinda takeyi sai aukin bacci idan kuwa kaga baby a hannunta to nono zata sha yarinyar na tsakanin hannun Hajja da inna Hajara watarana kuma rashida itake rainonta idan tana gida......Malam da Kawu Habibu sunzo sunga baby sun sanya mata albarka sosai nan Amadu ke shaida musu sunan yarinyar Fad'imatu sunan mahaifiyarshi kenan.....Malam da kawu suka sanya mata albarka da adduar Allah ya sanya ta zama mai taimakon addinin musulunci. Ranar suna Wasila ta fito tamkar wata amarya taci gayu sosai da wani uban les Hafsa ce ta dauko mata me make up tayi mata kwalliya sosai ta shiryata hannayenta da kafafunta sun sha jan lalle wanda yayi masifar kyau yayi jawur abun sha'awa, gold din dake jikinta kuwa abin kallo ne dan ana ya gobe suna ya shigo mata da kayan barka ita da baby set din akwatina shida shida makil da kaya iri daban daban wasu a dinke wasu kuma ba'a dinka ba ga uban gold kirar dubai da ya siya mata har kala uku yari da sar'ka da zobuna da abubuwan hannu ko ina na jikinta walwali yake yi.....Hafsa ta gayyaci kawayenta manya mata su kansu sai da suka raina kwalliyarsu ganin kwaliiyar mai jego din ta mussamance.......Zeey da Suhairat kam kasa zama sukayi a cikin gidan tsabar bakin ciki da yayi musu yawa ko wacce ta silale ta gudu ba tare da mutane sun fargaba. Amadu kam tun da safe kafin ya fita da yaga kwalliyar matar tashi hankalinsa yay bala'in tashi ganin tamkar an 'bare ta daga leda tayi wani 'bul-'bul ta cika ta batse tayi uban kwarjini irin na jego sai daukar ido takeyi, kafin ya barta ta fita daga d'akinsa sai da ya latsata iya son ransa ya tsotsi bakinta ya tayar wa da kansa hankali mutuka, sai da taga yana kokarin shige gona da iri ne yasa tasa masa kuka tilas ya kyaleta jikinsa na kyarma ya shiga goge mata fuska wai baya so ta 'bata kwalliyarta, da kyar ta samu ta kufce daga hannunsa, aikuwa bata sake komawa dakin ba har ya fito tana jinsa suna magana dasu Hajja taki fitowa daga daki sai bayan ya fita daga gidan ne ta fito ta cigaba da hidima da mutananta. ****** Bayan suna da kwana biyu gida ya dawo normal Hajja da Inna hajara suna zaune a palo bayan sun karya Wasila na cikin daki tana kimtsa kayanta irin wanda ta samu masu uban yawa turaman atamfofi babu adadi ga uban kudin da bata san iya adadinsu ba, dan abokananshi kyauta kudi suka dinga yi mata wanda takasa irgasu ballanta tasan adadinsu, shi kansa khalifa kyautar kusan dubu dari biyu yayi mata tare da sit din akwati cike da kayanta dana baby Zahra......Ya shigo dakin cikin farin yadi anyi masa dinki irin na zaman gida, idanunsa sakaye da farin gilashi, tana ganin ya shigo dakin sai gabanta ya fad'i! ciki ciki ta amsa sallamarshi tana dan gyara kafafunta, ya karaso ya zauna kusa da ita yana nani'karta, kamshin turaransa ya bugi hancinta, ajiyar zuciya ta sauke lokacin da taji saukar hannunsa a bayanta yana tattare gashin kanta daya sauka a bayanta, kafad'arta ya rike sosai ya matso da ita jikinsa murya a kasa yace."Laifin me nayi ne aka daina shigowa gaishe dani da safe."? Dan turo bakinta tayi gaba! Ya sanya dan yatsansa kan le'banta na 'kasa yana shafawa cikin wani irin salo, kallonshi tayi da idanunta da suka dan soma sauyawa, ya dan daga mata girarshi guda daya da munafikin murmushi a fuskarshi.........ta mai da kanta kasa gabanta na faduwa kadan kadan......Cikin wata irin murya yace." To tunda ke kin kasa zuwa inda nake ni gani nazo kin san hausawa nacewa garin masoyi baya nisa duk inda kika shiga kika 'boye sai na biki." Shuru tayi masa ba tace komai ba, ya sanya hannunsa ya tallafo fuskarta suka kurawa junansu ido.....Wani irin zallan sonta ta dinga hangowa cikin kwayar idanunsa, ta dinga kallon kyakyawar fuskarshi wacce annuri ke sauka akai a take taji wani masifar kaunarsa na ratsa ilahirin jikinta.....Lumshe idanunta tayi gabanta na wani irin bugawa da karfi da karfi.....Tana jin sanda yake lasar le'bunanta yana dan tura harshensa cikin bakinta ta wani makale a jikinsa tana sake ri'keshi a jikinta, harshensa dake wasa dashi saman le'bunanta tayi gaggawar sarkafoshi dana ta shiga tsotsa da sauri da sauri tana shafa wuyanshi da saisayyar sumar kanshi........... Littafin na kudi ne.......! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Wasap numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *74* Inna Hajara ce ta murd'a 'kofar dakin hannunta rike da baby zahra dake kukan yunwa tashinta daga bacci kenan tun bayan wanka safe da akayi mata bacci ya dauketa shine ta tashi tana kuka.....Inna hajara na fad'in "Ai dolene ki tashi da yunwa 'yar nan....kasa k'arasa maganar tayi ganin Amadu zaune a kusa da Wasila tayi fi'ki fi'ki da ido shi kuma ya sunkuyar da kanshi 'kasa kunyar duniya ta isheshi Allah yasa ma sunyi gaggawar sakin junansu lokacin da sukaji muryar Innan, to amma dai duk da haka inna hajara sai da ta fahimci wani abu tunda dai ai ita ba yarinya kankanuwa bace." A'lamarin ya bata mamaki sosai dan dukaninsu suna zaune a palo sam basu ga sanda har ya fito daga dakinshi ya shiga dakin ba, Karasawa tayi tana dan gyara fuskarta tace"Kar'beta ki bata nono kada ta soma wannan kukan nata kin san ba zakiji da dad'i ba." A sabu'le ta kar'bi yarinyar tana kokarin fito da nono.....Ya mi'ke tsaye yana dan gyara gilashinsa, ba tare da yayi kuskuran kallon innan ba yace."Inna antashi lafiya ya kwanan su Fad'ima." Inna Hajara itama dake ta iya duniyan ci sai ta maze kamar bata gane komai ba tace"Lafiyarsu kalau Alhaji ga Fad'imatu nan tayi wayo tubarkallah.'" Dan mirmushi yay yace."Allah yayi mata albarka." Inna ta amsa da "ameen." Yana fita daga dakin Inna hajara ta zauna kusa da ita fuskarta murtuk!!!! tace"Wallahi duk sanda na sake gani ya shigo dakin nan kin sakar masa fuska ya ta'baki sai ranki ya 'baci kwana tara da haihuwa har kin soma sakarwa miji jiki ke wace irin 'kwad'ayayya ce ne? ashe baki da wayo Wasila! ashe kin mance irin wahalhalun da kika sha kafin ki haihu shine sabida rashin kamun kai zaki saki jikinki har ya shigo yana tatta'baki ko." Wasila ta kama kuka tana kokarin kare kanta Inna Hajara tace"Rufe min baki ni bana son shashancin banza da wofi! kefa da kanki kike fad'a min anyi miki d'inki a matuncin ki to har yaushe ya warke da zaki komawa miji shashasha mara wayo kawai." Cikin kuka tace"Wai Inna me kika shigo ki kaga munayi kawai sai faman fad'a kike min ke baki shigo kinga munayin wani abu ba."! Inna Hajara ta kai bayan hannunta ta make bakinta tace"Dan Ubanki yarinya xaki mayar dani." Wasila ta kame bakinta tana hawaye.....Inna Hajara ta cigaba da sababi tana fad'i na shigo dakin na ganku makale da juna kuna tsotsa tsotse sannan ki raina min hankali."! Da sauri ta sunkuyar da kanta 'kasa tana mamaki ashe duk gaggawar sakin junansu da sukayi sai da ta gansu kai Inna hajara muguwar 'Yar sa'ido ce........Inna hajara tayi 'kwafa cike da takaici tace"Wallahi zan saka ido sosai a kanki duk ranar da na kara ganin kin sakar masa jikinki har kuna rungume rungume da tsotse tsotse to a ranar zan tattara nawa nawa nayi tafiyata tunda ke kin zama mara kamun kai da rashin kintsi.......Har yaushe akayi abun ? guri duk a d'anyace baiyi kwari ba amma saboda rashin hakuri irin naki ki biye masa ya cuceki a banza a wofi."!!! Cikin kuka tace"Ni Inna abar maganar dan Allah naji shikkenan zan kiyaye dan Allah kada ki tafi." Tsaki Inna hajara taja tace"Ai bana magana biyu na sake gani da idona sai dai ki nemeni ki rasa a gidanki." Tana gama maganarta ta fita daga dakin ranta dik a bace Wasila kuka taci ta 'koshi ta share hawayenta tana cigaba da shayar da babynta tana tunanin abinda ya faru tsakaninsu itama fa ta hango wautarta gaskiyar Inna hajara haihuwar fari tayi, ya kamata ace ta kame kanta a guri guda gudun azo a haifi dan da bashi da ido tasan ita dashi duk basu da hakuri a wannan fagen, gashi kuma bata so Inna hajara ta tafi tilas ne ta kama kanta ko ya shigo ta daina sakar masa fuska, wannan ce sha'awar data yankewa kanta. Hakance kuwa ta kasance kwata kwata Amadu ya daina ganin walwalarta ko ya shiga dakin ta dinga dauke dauken kai kenan idan ya zauna kusa da ita sai ta sauya guri idan ya dame ta tasa masa kuka tace dole sai ya bar dakin.....Abun da takeyi ya dinga bashi mamaki sosai ya soma jin haushinta yana dai daurewa ne, kawai baya so ya nuna mata fushinsa, ya kuma lura da yanda Inna Hajara ke zurga zurga a dakin duk sanda ta ganshi ya shiga da safe, dama da safe kawai yake shiga kafin ya fita da daddare baya dawowa da wuri kafin ya dawo sunyi bacci sai ya wuce dakinsa kawai, shi ba yaro bane tsaf ya fahimci akwai saka hannun Inna hajaran gurin abinda Wasilan ke masa duk sai yaji zaman matar a gidanshi ya isheshi tunda ba abun arziki take sa'kawa ba. ***** Yau kwanansu ashirin da shida kenan har ta soma sallah dan jinin biki da wuri ya dauke mata, tana kwance tana bacci dama 'ka'ida ne idan tayi wanka ta karya sai ta kwanta tayi bacci dan cikin dare ba sosai takeyi ba baby zahra na yawan tashi shan nono.........Cikin shirin fita ya fito daga dakinshi yana sanye da shadda fara 'kal da ita wacce kana ganinta kasan me tsada ce d'inki hannu ne na 'bakin zare wuya da hannuwa sai yay amfani da 'bakar Hula (dara) 'yar gasken mai gashi gashi a jikinta agogon dake hannunsa na dama shima 'baki ne na fatar damisa takalman kafarshi masu gidan ya tsa suma ba'kake sosai yayi kyau tamkar wani sauri dan shekara ashirin da takwas......Suka gaisa dasu Hajja da Inna hajara ya nufi dakin nata, Inna hajara idanunta a kansa tana so tagani idan taga ya jima bai fito ba tabi bayanshi. Yana shiga dakin ya tarar da ita tana bacci tana sanye da wani material roba roba dinki riga da siket ne dama can kayan sun matseta ballanta yanzu da ta sake cika da cikowa irin ta haihuwa......A hankali ya isa bakin gadon ya d'an tsaya a kanta yana 'kare mata kallo.....Cikin baccinta ta dinga jin 'kamshin turaransa, bud'e idanunta tayi sai taga inuwarshi tayi saurin daga kanta tana kallonshi. Mi'kewa tayi zaune tana mutsika idanunta, a hankali tace"Ina kwana."? Ya amsa babu yabo babu fallasa......mikewa tsaye tayi tana d'an jan rigarta da duk ta tattare tayi sama, ya bita da kallo tana kokarin wuce shi ya tari gabanta. Sai ta 'bata fuska tana kallonshi......Shima fuska a 'bace yace."Me yasa kika sauya halinki? wane dalili ne ya sanya duk sanda na shigo dakin nan kike 'bata rai idan na zauna kusa dake ki sanja guri idan na rike hannuki ki saka min kuka meke faruwa dakene."? Murya a sanyaye tace"Babu komai." Ya had'e ranshi sosai yace."Bana son 'karya ki fad'a min dalilin da ya sanya kike gudana ko zugaki akeyi ne."? Tayi saurin kallonshi......Yace." 'Kwarai kuwa ai da ba haka kike ba cikin 'yan kwanakin nan kika sauya d'abi'u dole ne nayi zargin ko zugaki ake." Sai ta tsargu! ta dinga kallonsa tana son tayi magana! Sam bata so ya zargi Innarta dan tana so ya cigaba da ganin mutuncinta kamar yanda yake gani ba zata so ya gane cewar Inna Hajara ce ke zugata ba........Tace"Ni babu wanda yake zugani kawai dai ina ganin kamar be dace ba ace muna had'uwa a d'aki ni da kai saboda banyi ar'bain ba." Ya dinga kallonta yana mamakin maganarta akwai kuruciya da rashin wayo a tare da ita, wannan maganar da takeyi sam bata da tushe ballanta makama kuma ba tunaninta bane, yasan innarta ce ke zugata. A d'an kausashe! yace." A cikin wane littafin addini ki kaji ance dan mace ta haihu shikkenan ita da mijinta sai ranar da tayi ar'bain? wannan magana da ki keyi irin ta jahilai ce ba'ace dan kin haihu shikkenn sai ki dinga gudun mijinki ba! Ni ba yaro bane na kuma gane abinda kike gudu shiyasa nace wannan abinda ki keyi ba tunaninki bane zugaki akeyi kuma duk me zugaki zata kaiki ta baro ne Ko yau idan nayi ra'ayi zan iya shigowa d'akin nan na kwana tare dake dama ba'ace lallai ki kwana da wata ba ni zan iya kula dake da yarinyata." Yanda yake maganar ne yasa ta gane ranshi a 'bace yake sosai to itama ranta ya 'baci sosai jin yana 'kokarin cin fuskar Innarta a gabanta zuwa yanzu ta gane ya gane cewar Inna hajara ce ke zugata. Murya na rawa tace"Inna Hajara kake kira da jahila kada ka manta fa a matsayin uwa take a gurina tunda kanwar mahaifina ce." Idanunsa tsaye a kanta yace."Ni da bakina kinji na zageta ko na ambaci sunanta nace da ita jahila." ? sunkuyar da kanta tayi tana kokarin mayar da kwallar dake kokarin zubo mata Tace."Ai ka gane itace shiyasa kake kokarin fad'a mata ba'kar magana a gabana to meye laifinta ai gyara kayan ka baya hana sauke mu raba." Murmushin takaici ne a fuskarsa ya bud'e baki kenan zaiyi magana zuruf Inna Hajar a ta turo 'kofar d'akin ta shigo kafad'arta sa'be da baby zahra tana fad'in ''Kina ina ne Wasila zo maza kar'beta ki bata nono kada ta fara wannan kukan nata." Duk suka juya suna kallonta tana tsaye a bakin 'kofar shigowa..........Jikinta ne kuma yayi sanyi ganinsu kamar suna cikin 'bacin rai dan ta lura da Wasilan ma kamar kuka take, sai tayi maza ta juya zata futa tana fad'in "A'a Alaji ashe baka fito ba." Yay saurin 'karasawa inda take yana fad'in "Yanzu zan fito Inna bani ita mu gaisa." Ya mi'ka hannunsa ya 'karbi yarinyarsa Inna ta bud'e 'kofar dakin ta fice da sauri duk kunya ta isheta.....Hannunsa ri'ke da babynsa suka 'karasa inda take tsaye tana shashshekar kuka Littafin na kudi ne! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: [8/24, 9:55 AM] .: 'Yr Bngr Sys *75* _Assalamu alaikum barkan ku da safiya da fatan kun tashi lafiya ya gida ya yara? madallah Jiya na fita anguwa tun safe ban samu nayi typing ba sai bayan na fita ne na kawo muku uzirina afuwa👏🏻 da yawa daga cikin ku nasan zasu dauka wani abu daban to nasan wad'anda suka san wacece binta baza su dauki rashin yin typing dina da wata manufa ba, amana d'aya ce kamar yanda na d'auki alkawari kuma na karbi kudin ku #600 domin ku dinga samun update na 'yar banga sau biyu a rana, to ku sani a cikin ku akwai wad'anda nayi wa uziri suna da yawa, kuma a rayuwa dole sai kayiwa d'an uwanka uziri mutum ba kullum yake samun abinda yake so ba, tinda na fara typing na 'yar banga ban tsaya ba ko hutun sallah ban tafi ba kullum sau biyu nake har 'yan normal gruop suna surutun hakan, ban ta'ba tsallake kwana biyu banyi typing ba inayi iya bakin kokarina duk domin na sauke nauyin dake kaina, Ni ina kokarin rike amanarku amma kuma wasu daga cikinku suna cin amanata to wannan be dameni ba saboda nasan kansu sukewa, watarana zan tashi bani da chaji watarana zan tashi bani da lafiya ko yarona, kunga typing ba zai yiwu ba, dole sai da nutsuwa nasan dai wad'anda suka san wacece binta zasu bada shaida a kanta ban kar'bi kudinku dan nayi wasa da hankalinku ba duniya dole sai kayiwa dan uwanka uziri, saboda haka dik sanda aka ga banyi typing ba to a fara tambayar lafiya tukkuna kafin aji bayani na, ku kar'bi uzirina kamar yanda nake kar'bar uzirinku...................Assalamu alaikum🙋🏻‍♀️_ Yana isa inda take tsaye sai ya rike hannunta ya jata suka zauna kan gado, baby Zahra ya d'ora mata a cinyarta cikin murya mai taushi yace."Ki bata nono kinga tana kuka bana so naga momyna na zubar da hawaye." Ma'kale kafad'a tayi tana goge fuskarta cikin shagwaba tace"Uhm!Uhum! wato momyka ko? to nima ai momyna ka 'batawa rai." Ya rike kafad'arta yana dan sansana wuyanta a hankali yace."Ayi min afuwa nima Inna Hajara mamana ce kuma kema ai kin san duk abinda na fad'a akanta hakane yanzu gashi data shigo kin tabbatar da maganata ko."? Shuru tayi masa kunyarsa takeji sosai.....Murmushi yay yana dan daga mata girarshi a hankali yace."Ai naga kin fara sallah saboda haka yau dakin nan zan kwana dan kwana biyun nan kokari da hakuri kawai nakeyi sha'awarki zata kasheni." Cikin wani irin voice ya'karashe maganar. Kallonsa takeyi tana d'an zum'bura bakinta tace"Ni wallahi A'a so kake ka sake farke gurin bayan kasan sai da aka yanka ni." Ya wani marairaice fuskarsa yana mata shu'umin kallo yace."Ai naji Likitarki tace gurin ya had'e ranar da mukaje asibiti." Hawaye ta share tana sake zu'baro baki gaba tace"Eh duk da ya had'e ai amma tace sai anyi wata uku sannan wani abu zai faru." Jikinta ya sake shigewa ya d'ora ha'barshi kan kafad'arta tare da zura hannunsa ya ri'ko kungunta ya rike sosai yace."Kina so na mutu kenan wata uku da kike magana tamkar shekara uku ce a gurina ai ni yau ma bazan iya hakura ba yanzu kafin na fita zanyi saboda nasan innarki zata hanani shigowa da daddare." Yana maganar yana cusa hannunsa cikin rigarta Zabura tayi baby zahra dake hannunta ta kusa fad'uwa yay saurin riketa yana dan kallonta yace.''Baki da hankali zaki yar min da momy ko."? Tana tureshi daga jikinta tace"To ka daina ta'bani ko kuma in maka ihu! Inna Hajara ta shigo taga abinda kake." Sai yasa dariya yana kallonta yace."Idan kin min ihu! Inna Hajara ta shigo taga abinda nake meye a ciki dama ni nafi so ta gani itace zataji kunya bani ba." Shiru tayi masa tana kokarin fito da nono domin bawa baby dake dan kuka......Taimaka mata yayi suka fito da nonon a tare, gabakid'aya idanunsa suka rufe ganin lafiyayyan nonon nata ya cika sosai gashi a tsaye nipple din ya sake tsukewa saboda tsotso, ya sauke ajiyar zuciya me zafi a hankali ya dora hannunsa saman brest din yana shafawa tamkar wani maraya ya d'ora kanshi a kafadarta......Wasila abu biyu ne suka dameta Yanda yake shafa fatar saman brest dinta shine ya sanya ta shiga wani irin hali gashi baby zahra ta kama nipple din tana ta tsotsa, sai tsigar jikinta ta dinga tashi duk ta rasa yan da zatayi sai mutsu-mutsu takeyi tana dan tureshi yana sake makaleta a jikinsa.....Kuka tasa masa tana fad'in "Dan Allah ka bari wallahi babu dad'i." Ya bud'e jajayen idanunshi da suka 'kankance yana kallonta kwata kwata ji yay bakinsa yay nauyi ya kasa magana a take jikinsa ya shiga kyarma wani irin sanyi ya dinga ratsa shi. Tunda taga ya shiga wannan yanayin sai gabanta ya tsananta fad'uwa domin tana gane duk sanda yake cikin tsananin sha'awa jikinsa rawa yake. Baby Xahra ya kar'be daga hannunta ya ajiyeta gadonta dake gefe, tana kallonshi yana kokarin 'balle botiran rigarshi da links....Sai tayi yunkuri barin gurin yay gaggawar rike hannunta. Bakinta sai rawa yake takasa magana....Murya a hard'e yace."Ki taimaka min na samu stysifiend ba dole sai na shiga wannan gurin ba tunda kince da matsala ke kin san irin dubarar da zakiyi min ko."? Yana wani lankwashe kansa yake maganar. A tsorace take kallonsa bakinta na rawa tace"Fita fa zakayi ka shirya tsaf kuma sai kace wani abu ni dai dan Allah ka mayar da rigarka ka tafi inda zakaje." 'Dan 'bata rai yay yace."Wai meyasa ne duk sanda zance miki ga abinda nake so sai kinyi min gardama meye a ciki dan kinyi min dabaru na samu biyan bukata kin san bana neman mata ko? kuma ke kadai ce matata to ki sani wannan halin naki zai iya janyowa na sake aure dan ni mutum ne mai yawan bukata da kuma san soyayya da kulawa." Jin maganar aure yasa ta soma kuka tana kallonshi tace"To ai inayi maka kokari duk sanda zaka zo da bukatarka ina kokarin ganin ka samu gamsuwa ko ranar da zan haihu ma hakane ya faru, yanzu kuma ai haihuwa nayi ba sai ka hakura nayi ar'bain ba." Kansa ya dafe cikin 'bacin rai yace."Ba zakiyi abinda na umarceki ba." Matsawa tayi gefe tana goge fuska...."Ni dai ka bari nayi ar'bain." ! Yaji kamar ya kwad'a mata mari! Yarinya mai shegen taurin kan tsiya wai meye manufar ar'bain d'in nan da malam bahaushe ya tsira! Tsaki! me kar'fi yaja ya mi'ke tsaye yana maida botiran rigarsa ya d'auki hularsa da gilashinsa da ya aje ya sanya, ya kama hanya ya fita daga dakin ba tare da ya kalli inda take tsaye ba. Yana fita ta nemi gefan gado ta zauna tana kuka ita tsoro takeji kada Inna hajara ta fahimci wani abun na faruwa a tsakaninsu ta tafi kwata kwata bata so ta tafi shiyasa kuma tana jin tsoransa kada yazo ya danneta ya lalata mata d'inki duk da likitan tace gurin yayi normal amma ai baiyi wani 'kwarin kirki ba. Inna Hajara ce kadai a palo ita hajja ta shiga daki domin daura alwalar sallahr walha to tana ganin wucewarsa ba tare da ya ko kalli inda take ba sai jikinta yay sanyi a hankali ta mike ta nufi dakin Wasilan.....Ta tarar da ita xaune tana kuka. Zama tayi kusa da ita a hankali tace"Goge hawayenki." Wasila ta goge hawayenta tana sunkuyar da kanta.....Inna Hajara tace"Ni banzo da niyyar na kashe miki aure ba Wasila, na lura mijinki bashi da hakuri ko kad'an, ni kuma ke nake tausayawa saboda irin wahalhalun da kika sha kafin ki haihu Uwa uba akazo aka yanka ki aka d'inke kamar 'kwarya, dole a sanya ido sosai a kanki domin ingantuwar lafiyarki! Bayan haka kuma dole ne kafin ki komawa miji sai an gyara miki jikinki domin haihuwar da kikayi duk wata ni'ima da kike dashi babu nida a tunanina ma ina so idan zan tafi gida muje tare dake can in gyaraki sosai da sosai to amma tunda naga take taken mijinki to zan tattara nawa nawa na tafi dama akan dole nake zaune a gidan, bana so yazo ya dinga jin haushina ko ya fahimci cewar nice nake hanaki biya masa bukata." Tun kafin Inna hajara ta 'karasa maganarta ta rike hannuwanta tamau! tana kuka sha'be!sha'be! "Wallahi Inna ba zaki tafi ba sai nayi ar'bain sai kace wata mara gata da galihu! ai haihuwar fari nayi kuma koda zanyi haihuwa goma a gidanan kina da damar da zaki zo ki zauna tare dani tunda ina cikin gidan.....Inna nasan abinda nakeyi nima bazan yarda ya haike min ba kawai ya cuceni bayan ban gama dawowa dai-dai ba, na amince zan jure ko wane irin fushin da zai dauka dani nasan idan ya gaji zai daina.." Inna hajara tace"A'a Wasila ni bazan so kullum ki dinga kwana da tsiniwar Allah da mala'ikunsa ba, kibi mijinki sau da ' kafa kiyi masa biyayya kan abinda yake so ni dai na fad'a miki yau yau zan tafi dan naga kamar haushina yake ji to zai dawo ya tarar na bar masa gidansa. Wasila ta dinga kuka tana bata hakuri Inna Hajara ta rufe idonta ruf ta fita daga dakin domun zuwa ta had'a kayanta.......Hannunta na kyarma ta d'auki wayarta ta shiga kiransa.....Lokacin yana cikin company sa tare da ma'aikatansa yaga kiran wayar tata ya'ki dauka har yanzu haushinta yake ji Ta kira ya kai sau biyar bai dauka ba sai kawai ta aje wayar ta fito palo tana goge fuskarta tasan haushinta yake ji shiyasa bai dauki wayarta ba, tana fitowa palo ta tarar Inna hajara da hajja suna fafatawa, Inna Hajara taurin kan tsiya ne da ita ta'ki sauraran hajja hannunta ri'ke da jakar kayanta ta kama hanya ta fita Wasila tabi bayanta har wajen harabar gidan......Garba ya iso gurin da sauri ya karbi jakar kayan hannunta shi baiyi tunanin wani abuba saboda ya dauka inna zata tafi gidane....Can parking ya nufa da jakar kayan ya fito da mota har inda suke tsaye Inna hajara ta bude ta shiga tana 'bata rai! Wasila kallonta kawai takeyi domin ita har ta gaji da magiya da bata hakuri, tana tsaye har garba yaja motar suka fita daga gidan, ta girgiza kanta ta juya domin komawa ciki tana kokarin mayar da hawayen dake so ya zubo mata. Tana shiga ta tarar da Hajja a tsaye a tsakiyar palon itama tana cikin alhini na tafiyar Inna hajaran Tace"Wasila kodai wani abu akayiwa hajara ne irin wannan tafiya haka da gaggawa, kuma na lura kamar dai ranta a 'bace yake."! Ta d'an d'auke hawaye a hankali tace"Haka kawai ta tubure wai gida zata tafi babu abinda akayi mata." Hajja ta zauna kan kujera jikinta a sanyaye tace"To ai shikkenan Allah ya sauketa lafiya." Ta amsa da "ameen tana kokarin shiga d'aki. **** "Haba Uwani wai dan Allah tun yaushe nake miki magiya kan ki kaimu muga d'akin yarinyar amma kin'ki kaimu kullum nayi miki magana sai kice zamuje to sai yaushe zamuje? kada fa ki manta da cewar kwanaki dani dake mukayi lissafin watannin cikin yarinyar har ki kecewa cikin ya isa haihuwa nace watakila ma ta haihu to kinga yana da kyau muje muga halin da ake ciki." Kuluwa ce zaune a gaban Uwani take wannan maganar cikin 'kas'kantar da kanta.......Uwani ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Kuluwan kamar ba itaba wai yau an wayi gari Kuluwa nayi mata magana cikin kalami mai dad'i lallai duniya kenan. Tace"Kuluwa ba wai bana so muje bane gaskiya bana so muje gidanan kiyi wani abu da zai sanya kima da mutuncinmu ya zube mutumin nan ba karamin mutum bane kuma kinga mu sirikai ne dole mu kama girmanmu ke kuma kuluwa baki da girma sai na jiki idan kin amince cewar xaki kiyaye kuma zaki nutsu sosai to shikkenan sai mu shirya idan Allah ya kaimu dani dake da Kawu da kuma su Inna mai waina muje muga abinda yarinyar ta haifa." Cikin kwantar da kai Kuluwa tace"Haba Uwani wallahi bazan aikata abin kunya ba zan kula sosai bazan baki kunya ba insha Allahu." Uwani tace"Shikkenan to yanzu zan tashi na shirya na nufi gidan Inna Tabawa domin na shaida mata halin da ake ciki." Kuluwa tace"To hakan yayi bari idan na sauke abinci sai na d'an d'umamaki ruwan wanka kafin ki tafi kiyi sai kinfi jin dad'i." Mikewa tayi ta nufi kicin........Uwani tabi ta da kallo cike da mamaki. Littafin na kudi ne! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *76* Koda Rashida ta dawo ta tarar Inna hajara ta tafi itama sai da taji rashin dad'i tayi ta tambayar Wasila dalili, kunya ta hanata fad'a mata kawai sai tace"Rashida kin san dai rigimar Inna hajara dama da kyar na samu ma ta zauna tayi wad'annan kwanakin amma babu wani abu da akayi mata wanda zai sanya ta tafiya kawai dai dama tayi ra'ayi ne." Rashida ta amince da maganar Wasila suka zauna suna jimamin tafiyar Innar tasu. To can 'bangaran su mai girma governor Lawan Rabo sun tada aiki sosai shida mu'karrabansa duk dan ganin yanda al'ummar jahar suka tashi hankalinsu gurin ganin sun rusa tafiyarshi da kuma jam'iyyar da yake ciki gabakid'aya jamiyyar da yake ciki dashi kansa sun daina power gabakidaya jama'a nata komawa jam'iyyar *CPC* jam'iyyar su Amadu kenan duk ta doke sauran jam'iyyun da suke adawa da junansu......Hankali mai girma governor yayi masifar tashi, babu shakka idan ya tsaya kallon ruwa to kuwa kwad'o zaiyi masa 'kafa, tuni ya kira 'yan fadarshi irin su As da mataimakinsa suka zauna zaman meeting inda suka yanke shawarwarin da suke ganin zasu taimaka musu gurin campaig, governor ya fitar da miliyoyin kudi ya rabawa 'yan gwangila irinsu As yace aje ayi duk abinda ya kamata a cikin jahar domin a jawo hankalin jama'a jam'iyyarsu........As suka fara aiki gadan gadan inda suka fara rushe rushen gidajan jama'a da masana'antu wai zasuyi babban titin da jirgin 'kasa zai dinga wucewa, jama'a da yawa suka shiga halin damuwa an rushe musu muhalli ba'a basu diya ba masu sana'oi suma an rugaza musu guri ba'a biyasu ba, a mai dasu gida an tsuganar, takaici ya ishesu sai kawai suka soma shiga gidan redio suna zage zage da fad'in Allah sai ya saka musu wannan zalincin da ake musu.....Mai girma governor ya tafi katsina gurin abokinsa ya samu labarin abinda yake faruwa a jahar tashi, a take ya kira As yace ya shirya da kanshi ya shiga gidan redio yayi bayani wanda zai dauki hankalin jama'ar gari su amince da manufarsu. As ya shiga gidan redio na salama ya dinga zabga 'karya da 'karairayi kan cewar mutukar jama'ar gari sun sake za'bar lawan rabo to babu shakka zasuji dad'i a wannan karon komai zaiyi sauki za'a samu sauyi na rayuwa sannan yace."Duk wanda aka rushe masa gida da gurin sana'arshi a gurin aikin titin da sukeyi to duk su kwantar da hankalinsu za'a biya su hakkinsu......Ashe jama'ar gari sunyi dafifi a wajen gidan redion koda su As suka fito dashi da 'yan rakiyarsa da 'kyar suka sha dan ma da akwai security a tare dasu amma dai dik da haka sai da sukayi raga raga da gilashin motocinsu suna tafad'in "bamayi! kano ta d'an musa ce." Ranar Amadu da Khalifa sun sha dariya hankalinsu kuma ya kwanta sosai ganin suna samun nasara a cikin tafiyar tasu kullum 'kara samun masoya sukeyi ta ko wane fanni. Tun ranar da Inna hajara ta bar gidan a tsakaninsu suka daina samun jituwa wanda gaisuwa ce kawai take had'asu daga haka shikkenan zai fice harkokinsa, kuma koda ya dawo gidan yaga bai ga Inna Hajara baice mata komai ba itama ba tace masa komai ba, dukaninsu sun shiga cikin damuwa mai tsanani babu kamar ya ita kullum sai tayi kuka, ita bata ga abin fushi da daukar gaba ba ta lura yana da hakuri sosai amma bai iya fushi ba dan haka sai ta yanke shawarar tunkararsa ta bashi hakuri idan ya hakura shikkenan idan bai hakura ba zata rabu dashi duk ranar da ya gaji ya sauko dan kanshi.............Yau da wuri ya shigo gidan dan goma ma ba tayi ba, sai da ta bari Hajja da Rashida sun bar palon tukkuna ta fito daga dakinta tayi kwalliya sosai sai 'kamshin turare take. Murd'a kofar dakin tayi ta shiga da sallama a bakinta.....Babu kowa sai dai tana jin alamun motsi a toilet dinshi ta dan zauna gefan gadon tana bin dakin da kallo yaushe rabonta da shigowa tun ranar suna gashi yau kwananta talatin da bakwai da haihuwa saura kwana uku tayi ar'bain......Tana zaune tana sa'ke-sa'ke ya fito daga toilet d'in 'kungunsa daure da towel da karami a hannunsa. Had'a ido sukayi tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na fad'uwa.....Kadaran kadahan ya kalleta ba tare da yace komai ba ya 'karasa bakin mirror ya dan tsaya yana sake goge fuskarsa.....A sanyaye ta mi'ke ta isa inda yake tsaye ta 'karbi towel din hannunsa tana so ta goge masa jikinsa, sai kawai ya bar mata gurin, Ta bishi da kallon mamaki yaje ya nemi guri ya zauna gefan gado yana shafa vasillin a jikinsa, ba tayi zuciya ba ta isa inda yake a hankali ta sanya hannunta ta 'karbu vasilin d'in tana marairaicewa, Ya mi'ke kawai ya barta a gurin........Wardrobe ya nufa domin daukar jallabiyarsa, da gudu taje ta rungume faffad'an bayansa tana shashshekar kuka tace"Kayi hakuri kaji." Ajiyar zuciya ya sauke yana dan jin sassauci cikin zuciyarsa, shima dik abinda yake daurewa kawai yake yi yana dai so ya nuna mata kuranta ne, amma ba dan ya cuzguna mata ba, idan da ta kwantar da hankalinta shima ai yasan abinda yake yi ba zai ta'ba cutar da ita ba, amma ranar nan ya kwadaitu da ita mutu'ka ya kuma nemi ta a gaza masa ta'ki! dashi d'in manemin matane to babu shakka a ranar sai yaje ya biyawa kansa bukata amma haka ya hakura ya cireta daga cikin ranshi duk dan ya nuna mata kuskuranta A nutse ya jiyo da ita suna fuskantar junansu, kasa hada ido tayi dashi ta sunkuyar da kanta 'kasa tana goge fuskarta, a hankali ya sanya hannunshi ya goge mata hawayen fuskarta ya tallafo fuskarta sosai cikin tafin hannuwansa ya kallonta. Takasa d'aga kanta ta kalleshi saboda kunya da kuma tsabar kwarjin da Allah yayi masa. Murya a kasa kasa yace."Me kikayi min kike bani hakuri."? Sai ta dago fuskarta tana kallonsa. Ya sanya d'an yatsansa saman le'banta na 'kasa yana shafawa a hankali a hankali shi dai yana masifar son le'bunanta. Kasa cewa tayi komai ta maida kanta 'kasa tasan yana sane yake tambayar ta yafi kowa sanin kan abinda yasa take bashi hakuri. Murmushi yayi a hankali ya cika fuskarta ya juya ya dauko jallabiya cikin wardrobe yana fad'in "Ina momyna ko tayi bacci."? A hankali ta d'aga kanta tace" Yanzu nan na lalla'bata ta kwanta.....Hannunta ya ri'ke yace."Muje parlo yau ke zaki bani abinci a gajiye nake." Taji dad'in yanda ya saki jikinsa sosai wannan ya sake tabbatar mata da cewar ya hakura da fushi da ita kuma ta lura dama kamar daurewa kawai yakeyi yana hakuri. Ya zauna kan kujera yana dan dubawa babbar wayarshi yace."Ki had'o abincin ki kawo min nan zanci." Da sauri ta nufi daining din ta had'a mishi abincin komai da komai ta kawo gabanshi ta ajiye......'Kasa ya sauko hankalinsa na kan wayarshi yana dan juya abincin da cokali, sai ta kar'bi cokalin ta fara d'ebo abincin tana sa masa a bakinsa.......Kar'ba ya din gayi ba tare da ya kalleta ba hankalinsa gabakidaya yana kan wani text da Zeey tayi mishi. Kafin ma ya gama karanta text din kiran wayarta ya shigo wayar tashi. Dama tuntuni ya goge number ta cikin test dinta ma dan tasa sunanta ne ya ganeta. Ganin numbarta tace ya sanya shi daga wayar a nutse yay sallama dake hands free ya bud'e Wasila najin muryar Zeey tana fada'in "Ranka ya dad'e barka da dare yau dai naci sa'a an d'auki wayata." Gabanta ne ya shiga fad'uwa sai hannnta ya soma rawa tana kokarin sanya masa a bacin a baki cokalin ya su'buce daga hannunta abincin ya zube a jikinsa sa kasan gurin. Dan dubanta yay yana dan gyarawa hankalinsa nakan maganar da zeey ke masa yace."Zainab ya kike ya gida ya kwana biyu." Zeey tace"Alhamdullhi yallabai Wallahi kwanaki nayi ta kiran wayarka domin nayi maka Allah ya raya baka dauka ba nace to ko wani laifin nayi.'"? Murmushi yay a hankali ya dan koma saman kujera yace." Ai ke bakya laifi Zainab mybe lokotan da kike kiran wayar ina da uziri ne shiyasa amma nagode kwarai kuma naji dadi da kulawarki." Zeey tace"Ai har taron suna nazo sai dai ban dad'e ba na tafi domin a ranar ana bikin wata friend dina ne." Yace."Masha Allah kema ai yana da kyau ki futar da miji kiyi aure Zeey kin kwana biyu fa." Zeey tayi dariya me shashshe'ka tace"Yalla'bai kenan aini da aure sai dai inga anayi namiji daya nake so a duniya amma ya'ki aurana." Yasan inda maganarta ta dosa sai ya nuna bai gane komai ba, Yace."Zeey meye abunki? kina da ilimi sosai kana kina da kyau dai-dai gwargwado me kuma ake nema."? Murmushin takaici Zeey tayi tace"Duk da ina da abubuwan da ka fad'a yanzu to shi banyi masa ba." Dariya yasa yana d'an sosa gemunsa yace."Haba dai sai kace makaho ni da ba dan nayi aure ba da kawai na shigo anyi dani." Zeey tayi wata dariya me shashsheka tana sake ma'kale murya tace"Ashe kasan inda maganata ta dosa tunda naga ka d'auko hanya, Yallabai ko yau kazo ni a shirye nake dama ai Ubangiji cewa yay kuyi Hud'u mutukar zakuyi adalci." Ya bud'e bakinsa zaiyi magana yaga ta jefar da cokalin hannunta ta mi'ke rai a 'bace ta bar gurun......Ya bita da kallo har ta bude daki ta shiga ta bugo kofar da karfin gaske.....sai kawai ya girgiza kansa ya cigaba da hira da Zeey inda take ta tsara masa kalamai ita dole sai ta samu shiga a gurinsa........Yace."Ki bari zan duba maganarki a tsanake zan kira ki a waya." Cike da farin ciki da jin dadi Zeey tace"Shikkenan Yallabai ina sauraranka." Kashe wayar yay ya ajiye ta kusa dashi ya gyara zamansa sosai ya cigaba da cin abincinsa. Koda ta shiga dakin kwanciya tayi kan bed taci kukanta ta koshi ta kuma dauki al'kawarin yi masa rashin mutunci tunda dai shi bai san hakkin d'an adam ba in bansa wulakanci da rashin mutunci ya rasa ma a inda zaiyi hira da budurwarsa sai gidanshi kuma a gabanta lallai zata nuna masa cewar ta san abinda takeyi duk da take jahila to tasan ciwon kanta. Sai da ya kammala cin abincinsa a tsanake tukkuna ya bita dakin, lokaci har tayi wanka ta kwanta tana bawa baby zahra nono ta tashi daga bacci, yazo ya tsaya kansu yana kallonsu, ganin yanda tayi bala'in shan kunu ne ya sanya ya kasa cewa da ita komai sai kawai ya tsuguna ya mannawa 'yarshi sumba a saman goshinta ya mi'ke ya fita daga d'akin. Da 'kyar bacci ya dauketa saboda tsabar bakin ciki da takaici, ta tashi da safe cikin rashin walwala har Hajja ta shigo dakin suka gaisa ta shirya zahra har taso ta fahimci wani abu amma dai ba tace mata komai ba itama so take ta cika ar'bain ta tafi ai tayi abinda tayi, Hajja na fita da Zahra ita kuma ta shiga toilet domin yin nata wankan. Kafin ta fara wankan sai da ta shiga cikin ruwan d'umi tayi minti goma sha biyar sannan ta fito tayi wankanta da sabulai masu kyau da kamshi ta fito daure da karamin towel iya cinyarta.........Ashe yana zaune a dakin ya shigo tana toliet sai ya zauna zaman jiran fitowarta.......Ganin ta a haka fatar jikinta na wani irin she'ki da sul'bi ga santala santalan cinyoyinta a waje dik sai ya rasa nutsuwarsa ya dinga binta da wani mayen kallo har ta wuceshi ta nufi mirror tana zum'buro bakinta tare da sauya salon tafiyarta. Kasa daurewa yay ya mi'ke ya nufi inda take......Tana sane ta bude towel din wai zata sake d'aurawa aikuwa ya hangota ta madubi hankali a tashe yaje ya ri'ke towel din yana kokarin fuzgewa daga hannunta. Ta dan tureshi kadan ta bar masa gurin......Matseta yay jikin wardorbe yana rarraba idanunsa a jikinta..........Ta dinga ture kirjinsa tana son yin kuka amma dai ta daure saboda bata so ya dinga raina mata hankali....."Wai dan Allah meye haka bafa girmanka bane hakan da kakeyi ka kyaleni ni nasa kayana, kuma gidan nan dole ne ma na barshi dan ba zan zauna a inda ba'a bukatar dangina ba.'' A kausashe take maganar tana tuttureshi daga jikinta Muryarshi ba sosai take fita ba yace."Wace irin magana kikeyi ne waye baya kaunar dangin ki da har kike ikirarin barin gidan auranki." Sai ta fashe da kuka tana wani irin bubbuga 'kafafunta ta tureshi da 'karfi tana haki ta matsa gefe tana kallonshi tace"Eh dama zaka fad'i haka mana yau kwanan Inna Hajara nawa da tafiya ka ta'ba tambayata dalilin tafiyar ta!? Sannan yau kwanana nawa da haihuwa me yasa baka ta'ba tunani koda sau d'aya ne kace bari ka tura d'aya daga cikin yaranka domin yaje ya dauko mahaifiyata kan tazo taga abinda na haifa, na sani dama tuntuni na san da cewar baka dauki Uwata a matsayin komai ba dan da ka dauketa da daraja to da duk inda take kaje ka gaisheta da kanka kuma ka shaida mata na haihu da abinda na haifa.....To nagaji ni ba shashasha bace nasan kuma inda ke min ciwo zanyi tafiyata in yaso sai ka auro wacce kake ganin Iyayenta sune dai-dai da kai da kimarka." Tana gama maganarta ta bude wardorbe ta duba kayanta t a dauki riga da sket na wani had'addan swiss less ta shirya jikinta duk yana tsaye kamar gunki yana kallonta da mamakin kalamanta, bude kofar dakin ce ta sanya shi dawowa hayyacinsa, yay gaggawar kallon bakin kofar sai ya hango ficewarta daga dakin tare da jan kofar da karfin gaske. Littafin na kudi ne! Idan kika futar min da book keda Allah! Idan kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *77* Ya jima a tsaye a tsakiyar d'akin yana mamakin irin maganganun da yarinyar ta watsa masa, ransa yayi masifar 'baci sosai ashe raini har ya soma shiga tsakaninsu tunda har zata iya d'aga masa murya! gurin magana tana fad'a masa duk maganar da tazo bakinta tana d'aga masa harshe kamar zata zageshi Idan tana so ta nusar dashi abinda ke zuciyarta ai sai tayi masa bayani cikin fahimta ba da irin wannan sigar ba, dole ne ma ya dauki tsatstsauran mataki a kanta, idan dan wannan abun na jikinta take kokarin zaginsa to taje ta ri'ke kayanta zai nuna mata shi d'an halak ne. Koda ya fito daga 'dakin bai kalli inda suke zaune ba ya wuce bedroom dinsa ransa duk a jagule. Wasila kuwa jin zuciyarta take wasai tunda ta samu ta fad'i abinda ke cikin ranta shikkenan itama ta dauki al'kwarin akan ba zata sake zama ya dinga raina ta ba ballanta har ya dinga d'aga wayar 'yan matansa a gabanta sai ta nuna masa itama macace wacce tasan abinda takeyi. A shirye ya fito da shirin fita, ya tsaya suna magana da Hajja, Hajja tace"Nima fa na kusa tafiya tunda dai Allah yasa ta haihu lafiya shikkenan zan koma gida." Yace."Kiyi hakuri kiyi zamanki tare damu." Tace"A'a dai gwara na kuma gidana bana dinga zama cikin yara ba." Yace."Hajja ai zaman naki cikin Yara gyara kike ba 'barna ba." Wasila da kanta yake sunkuye tayi saurin dago kanta tana kallonsa, sai taga kamar magana yake fad'a mata kan Inna Hajara oh! wannan mutum baya barin takwana! wato Yana nufin Inna Hajara itake aikata 'barna kenan......Mi'kewa tayi ta bar musu gurin ba tare da tayi kuskuran kallonshi ba, Hajja ce ta bita da kallo sosai ta fuskanci akwai matsala a tsakaninsu amma kuma ba za tayi masu magana ba sai ranar da zata tafi tukkuna idan kuma sun dai-daita kansu shikkenan. Yana fita Garba ya daukeshi a mota kafin ya ajeshi cikin ma'aikatarshi yake Umartarshi da cewar idan ya saukeshi ya nufi can garin su Uwani Patskum yaje ya sanar musu da cewar Wasilan ta haihu idan da me ra'ayi zuwa yaga abinda ta haifa sai ya dauko shi yazo dashi.....Hakan ce ta kasance Garba na saukeshi sai ya dauki hanya kamar yanda ya umarceshi. Suna zaune a palo bayan azahar dan uku ma ta kusa Rashida ma ta dawo daga makaranta, kawai sai sukaji sallamarsu su Uwani da Kuluwa dasu Inna Tabawa........Rashida ta mi'ke a guje taje ta bude musu kofar falon suka shigo ciki....Wasila ta mi'ke tsaye fuskarta cike da! walwala da farin ciki mara misaltuwa, Tabawa Iya mai waina da Uwani suka nemi guri suka zazzauna a nutse ita kuwa Kuluwa sai kalle kalle take tana ya'ke dafaffun ha'koranta da kyar ta zauna kan kujerar tana wani irin abu irin na marasa gaskiya......Hajja ta dinga fadin "Sannuku da zuwa kai masha Allah sannuku Wallahi ko jiya sai da mukayi zancenku ashe kuna tafe." Inna Tabawa tace"Aikuwa dai munata sa rana sai yau Allah ya nufa yau din ma Ai maigidan nan ne ya tura a ka dauko mu.....Kuluwa tayi saurin kar'be maganar tace"Wallahi kuwa ai rashin kud'in mota duk shine yayi mana cikas da tuni munzo anyi hidimar suna damu ace yarinya ta haihu babu danginta ai da kunya gashi duk muna raye a duniyar." Wasila taji kamar ta kwada mata mari jin abinda take fad'a shashashar mace kawai daga zuwanta har ta soma sakin layi....Ita kuwa Hajja murmushi tayi kawai ta mi'ke tana kallon Rashida tace"Kije ki kawo musu abinci tunda Rabe ya fita.'' Rashida ta mi'ke ta nufi kicin cike da takaicin Kuluwa da haukanta. Kuluwa sai washe baki take tana kallon baby zahra dake hannunta tace"Yarinyar tubarakallah kyakykyawa gata da jikin girma kamar tayi wata uku kai masha Allah." Uwani ta kalleta tana dan jan tsaki cikin ranta, shiyasa fa taki amincewa da zuwansu tuntuni saboda hauka da rashin kamun kai irin na kuluwan Inna Tabawa ta kar'bi yar tana sanya mata albarka kana ta mi'kawa 'Yar uwarta iya mai wani itama ta sanya mata albarka ta mi'kawa Uwani, kunya ta hana ta 'karbar yarinyar sai dai tace"Allah ya rayata tafarkin addinin musulunci." Ganin ta kasa kar'bar yarinyar yasa Kuluwa dashare baki tace"Uwani kunya ki keji ne ai dole jikar 'yar fari hahahahaha." ta karashe maganar tana dariya kamar sabuwa r mahaukaciya sai wani mutsu mutsu takeyi......Uwani girgiza kanta tayi tayi mata banza ba tace mata komai ba haka su Inna Tabawa dama suma haushinta sukeji.........Koda Rashida ta jere musu abinci kan daining Kuluwa kasa zama tayi kan kujerar sai kauyanci takeyi duk ta hargitsa musu guri.....Wasila tace"Rashida ki kwashe abincin daga dainnig din ki shirya musu shi kan daddumar can ta gefe sai sunfi jin dadin hakan." Da sauri Kuluwa tace"Aikam dan gaskiya zama kan wannan abun ba zaiyi dadin cin abinci ba gwara mutum ya zauna a 'kas yanda abincin zaifi tsirga masa. Cike da takaicinta tace"Dan Allah Kuluwa ki nutsu mana bafa a aljanna kike ba da kike ta wannan rawar jikin haba! ki daina haka dan Allah idan ba haka ba to ni kada ki sake zuwar min gida dan ba zaki zo ki bani kunya ba.'' Kuluwa ta hau ya'ke cike da kunya tace"Yi hakuri 'yar nan al'amarin ya rud'ar dani wallahi ban ta'ba shiga irin wannan daular ba sai yau gaskiya ke d'in 'yar baiwa ce Allah ya samu a danshin ku." Tsaki kawai Wasila tayi ta bar gurin, Uwani tace"Kuluwa kafin muzo gidan nan fa sai da mukayi magana dake wai me yasa kike hakane kada da mai gidan nan ya shigo ki bamu kunya a gabansa." Kuluwa tace"Kai jama'a wai ya kuke so nayi ne? to shikkenan bari nayi gum! da bakina na daina sanya albarka tunda dai itace bakwa so nasa." Rashida tace''Hakan shine yafi alkairi dake." Kuluwa taja bakinta tayi shuru sai dai muzurai kawai takeyi tana gyara zamanta, haka suka ci abinci mai cike da nama da lemuka masu sanyi Bayan sun gama cin abincin Hajja ta fito daga daki tana kallon Wasila tace"Yana da kyau ki kira mai gidan a waya yazo su gaisa tunda naji kamar suna cewa yau zasu koma." Ai kafi ma Wasilan tace wani abu Kuluwa tace"A'a ba yau zamu koma ba sai mun kwana biyu tukkuna dan haka malam yace mu zauna mu yauta tukkuna." Hajja tace"A'a to masha Allah hakan ma yayi kyau ai babu damuwa." Ita kanta Hajja ta fahimci matar kamar bata da hankali. Wasila jikinta yay sanyi ganin abin na Kuluwa naso ya wuce gona da iri babu shakka baza ta so zamansu a cikin gidan ba ba dan komai ba sai dan kada su zauna Kuluwa ta zubar musu da d'an sauran mutuncinsu da suke dashi a idon maigidan dama hakan ma ya aka kaya yana musu wani irin kallo to ballanta kuma yazo yaga irin haukan da Kuluwa takeyi ai raini ne zai sake shiga tsakaninsu......Ke'bewa sukayi da mahaifiyarta Tace"Uwani gaskiya gwara ku tafi ni bana so ku zauna a gidannan saboda waccan matar mara hankali kawai idan Kunyi sallah sai ku tafi." Uwani tace"Rabu da shashasha, ai dama mu ba zama zamuyi ba sai kace wasu marasa hankali yau din nan zamu koma tunda Allah yasa mun ganki lafiya da yarinyarki ai anyi barka ita idan zata zauna sai ta nemi guri kwad'ayayyar banza kawai." Wasila tace"Ai naga alama so takeyi ta zauna min a gida kuma baza ta zauna ba wallahi." Uwani tace"To yaushe ma ai 'kafarmu 'kafarta." Wasila ta shiga bata labarin irin zaman da sukeyi dashi da kuma dalilin da ya sanya Inna hajara barin gidan. Uwani tace"To in banda abinshi shikkenan daga an haihu babu wani gyara sai a koma masa ai ba zakiyi daraja a idonsa ba kada ki yarda ya kusance ki sai kin gyara kanki sannan kin tabbatar wannan d'inkin da akayi miki yayi dai-dai sannan idan kin koma masa a haka yazo yaji wani sauyi ai wulakanci ne zai biyo baya." Wasila tace"Nima abinda nake so ya fahinta kenan ya kasa fahinta." Uwani tace"Aikuwa ba zai ta'ba fahimta ba tunda idanunsa sun rufe kiyi kokari kawai ki san yanda zakiyi ki biya masa bukatarsa idan ta taso kuma kada ki dinga yi masa rashin kunya tunda kinga ba sa'anki bane ni da nake mahaifiyarki watakila ma ya girme ni." Hawaye ta share tace"Uwani nifa bana mishi rashin kunya sai jiya da yau da safe kuma duk shine ya jawo kin san dama can ni bana shiri da wanda ba zai ga darajar iyayena ba Uwani banta'ba jin kaunarki da tausayinki cikin raina ba sai da na haihu sannan na tabbatar da cewar Uwa uwace kuma dolene kayi kishinta koda mahaukaciya ce." Uwani tayi murmushi a hankali tace"Ai dama baka ta'bata sanin me duniya take ciki sai ka haihu tukkuna zakayi hankali Allah yay miki albarka, dake da d uk zuriar da zaki samu." Wasila ta amsa da ameen tana goge hawaye ta mike a nutse ta shiga janyo manya manyan akwatinan dake gefe a jere Manya manya atamfofi ta shiga fitowa dasu da mayafai masu kyau da tsada, ta zubesu gaban Uwani tace"Ki za'bi wad'anda sukayi miki sauran kuma sai ki bawa su Inna mai waina." Uwani ta shiga d'aga atamfofin tana dubawa tace"Masha Allahu mungode sosai Allah yayi miki albarka." ta amsa da ameen tana zuba mata kayan cikin sabuwar akwati.....Wani dan karamin akwati ta dauko ta bude kudi masu yawa ne a ciki ta tura gaban Uwanin tace"Ki d'ibi iya yanda kike so wannan kud'in da tarin atamfofin nan na samesu ne a haihuwar da nayi....Uwani ta tsorata da ganin Uban kudin dake cikin akwatin tace" Ki dai bani abinda kikayi niyya Wasila duk wannan kudin naki ne."? Girgiza kanta tayi tace"Uwani basu kadai bane ma kinga wad'annan takardun shaidar mallakar rumfuna ne cikin babbar kasuwar dake cikin gari (sabon gari) wanda maigidan ya mallaka min duk saboda ya sameni cikkakiyar budurwa yanzu haka ban san iya adadin kudin da ake samu ba cikin ko wace rana, yace dai zamuje a bude accont ya dinga sanya min kudin a ciki." Uwani ta fashe da kuka tana kallon 'yar tata tace"Nagode Allah da mazon Allah da Allah be sanya kun d'auki hud'ubata ba kun zubar da mutuncinku a titi nasan da mutumin nan be sameki cikkakiyar mace ba da ba zai miki wannan halaccin ba, kuma da tuni zamanku Baiyi nisa irin haka ba ('kalube gare ku 'yan mata kuyi tattalin budurcinku domun ku mi'ka shi ga wanda ya dace shine mijin auranku, koda namiji bai maka kyauta ba to abin alfahari ne ya sameki cikakkiyar mace) Wasila tace" Kinga dama abinda nake ta so ki gane krnan nima nasan da bai sameni da budurci ba da tuni ya sakeni wallahi." Uwani ta goge hawaye tace"A koda yaushe ina alfahari dake Wasila kuma kullum cikin shi miki albarka nake shiyasa kike ta samun cigaba a rayuwarki, nasihata zuwa gareki shine kiyi wa mijinki biyayya ku zauna lafiya da juna kada naji kada kuma nagani yanzu wannan mutumin shine uwarki da ubanki kuma shine gatanki duk wani umarni da zai baki kibi mutukar bai sa'bawa addinin Allah ba." Wasila tace"Insha Allah Uwani zanyi kokari nagode....... Wasila ta irgi kudi kimanin dubu dari biyu ta zuba mata cikin akwatin tace "Uwani gashinan ki siyi waya kiyi sana'a da sauran ga numbar wayata zan rubuta miki idan kun koma gida sai ki kirani mu dunga gaisawa duk kuma abinda kike so ki siya kici abinda baki dashi kiyi min waya insha Allah zamu zo nida rashida bada jimawa ba." Uwani tace"Kudin da kika bani basuyi yawa ba kuwa kada na aje Kuluwa ta sace." Wasila tace"Kada ki aje akwatin a gidanta ki kai kayanki kidan Inna Tabawa." Uwani tace"Yawwa to hakan zanyi." Mi'kewa sukayi a tare suka fito palo, suka tarar da Rashida da Kuluwa sai musayar yawu sukeyi Hajja na musu dariya Kuluwa da dai taga kowa nayi mata kallon mahaukaciya sai ta shiga taitayinta ta kimtsa kanta sai dai har yanzu ba ta daina mamaki da al'ajabi ba. Uwani tace"To Hajja mun fito mu zamu tafi." Hajja tace"A'a ba zaku tsaya maigidan yazo ba ku gaisa." Uwani tace"Ai yamma tayi." Hajja tace"Kuma da naji Kuluwa tace kwana biyu zakuyi." Uwani tace"Haba Hajja kamar wasu marasa hankali ai tunda munga lafiyar yarinya da abinda ta haifa zaman me zamuyi." Kuluwa tayi saurin kallonta tana so tayi magana, Uwani tayi bala'in shan kunu babu fuska, Kuluwa ta sunkuyar da kanta 'kasa ranta duk a 'bace! lallai idan sun koma gida sai ta shukawa Uwani rashin mutunci tunda tana ba'kin cikin su zauna suyi kwana biyu su dandali arziki. Hajja tace"To ke Wasila baki kira mijin naki a waya ba, ai be dace ba ace su zo baizo sun gaisa ba." Tace."Hajja kina ji fa Inna Tabawa tace shine ya tura aka d'aukosu ai yasan da zuwansu." Hajja tace"Eh 'kwarai kam amma kika sani ko wani abune ya dauke masa hankali tunda kinga kwana biyun nan abubuwa da yawa suna dauke masa hankali, yana da kyau ki sanar masa da zuwan nasu watakila ko mantawa yayi." Tace"Shikkenan Hajja." Daki ta nufa domun kiran wayarshi kamar yanda Hajjan ta umarceta sam bata so suyi ta jayayya da matar. Suna tare d a khalifa yaga kiran wayarta sai ya aje wayar suka cigaba da abinda sukeyi shi da Khalifan wanda har ya shiga mamakin ganin bai daga wayar ba ya sanya yace."Da alama dai 'yan mata da zawaran dake damunka ne tunda naga baka dauki wayar ba.'' ba tare da ya bawa maganar mahimanci ba yace."Wasila ce." Khalifa ya kalleshi cike da mamaki yace."Lefi tayi kenan ake hukuntata ta wannan hanyar." Murmushin takaici yay mai tafe da bacin rai yace."Khalifa na ta'ba ganin wanda ya samu damar da wannan yarinyar ta samu a kaina kuwa."? Khalifa ya girgiza kansa yace."Gaskiya ban ta'ba gani ba nima kana sonta sosai dan duk wasu alamu sun nuna." Ya girgixa kanshi cikin takaici yace."Nima nasan da haka khalifa wannan damar data samu ce ta sanya take takani yanda ranta yake so yarinya 'kankanuwa ta dinga nuna ni da yatsa tana daga mun murya gurin magana tamkar zata zageni." Khalifa yace."Subahanallahi! me ya janyo hakan." ?Tsaki yaja yace."Saboda kawai na nemi hakkina shikkenan cibi ya zama 'kari." Khalifa yace."Ban gane ba."? A nutse ya kalleshi ya dan gyara zamansa ya soma warware masa abinda yake faruwa tsakaninsu." Khalifa yace."Kai nifa shiyasa sam bana son wannan zaman jegon wallahi duk daga wannan zaman ake lalata maka mata , yanzu ita wannan matar abinda tayi shine dai-dai da girmanta da komai ta dinga d'ora yarinya kan turba mara kyau, idan bata sauke maka bukatarka ba gurin wa zakaje tunda kai ba manemin mata bane." Ya sauke ajiyar zuciya ransa a 'bace yace."Allah Khalifa yarinyar nan tayi wasa sai na 'kara aure bana son hauka da da'ki'kanci wallahi kuma zata gane bata da wayo." Khalifa yace."A'a kayi hakuri dai ka cigaba da rarrashinta kasan yarinya ce."Tsaki yaja yace."Allah ya sawa'ke khalifa bazan kuma zuwa gunta sa wata bukata ba taje ra rike kayanta nima na rike nawa zan kuma fara neman aure." Khalifa yace"Yanzu ka sauka daga kan ra'ayinka kenan."? Yace."Duk wani abu da zanyi itace ta jawowa kanta ni babu ruwana." Khalifa yace."To Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Ya amsa sa ameen." Lokacin kiran ta ya sake shigowa wayar tashi yana ganin sunanta ya kashe wayar yana jan tsaki. Cike da takaici da mugun ba'kin ciki ta fito daga d'akin murya na rawa Tace"Hajja bai dauki wayar ba watakila ko baya kusa da wayar ne." Hajja tace"E to hakan na iya kasancewa." Mikewa tayi ta shiga daki tana fad'in "Ku dan jirani na fito." Uwani dasu Inna Tabawa suka mike Wasila ta jagorace su suka fita Ita Kuluwa zama tayi har sai da Hajja ta fito daga daki ta mi'ka mata karuwar ledar dake hannunta tace"Gashinan turaman atamfofine da mayafai da sabulai sai ku kasafta a tsakaninku." Kuluwa ta kar'be da sauri jikinta na kyarma sai washe bakinta take tana ta zabga godiya, Hajja tace."Babu komai Kuluwa ku gaida gida mungode." Suna can parking spece Kuluwa takaraso hammatar ta ma'kale da ledar kayan da Hajja ta basu sai murna takeyi tace"To Wasila da Rashida mu mun tafi sai mun sake zuwa ke Wasila idan maigadan nawa ya dawo to ki mi'ka gaisuwata gurinsa tunda dai rowarsa kike mana." Wasila tana daure fuska tace"Zai ji ku gaida gida ku gaishe da Kawu Madu." Suka dinga amsawa da "ameen." Duk suka shiga cikin motar Garba yaja suka fita daga cikin gidan......Wasila da Rashida suka juya jikinsu a sanyaye suka koma ciki To itama Uwanin dai daurewa kawai takeyi amma zuciyarta babu dad'i sam! tana bala'in 'kaunar 'yayanta kamar yanda suke 'kaunarta. Littafin na kudi ne......! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *78* _*Sa'ko na mussaman zuwa gareka Amadu 'kawayen Wasila irin su Mumy Farhan, Bomis Zainab kankara Mrs Aliyu Nafisa Buhari Hauwa Chindo, Sakina Ummee da dai sauransu, sunce kayi hakuri dan Allah karkayiwa Wasila kishiya kayi mata uziri saboda yarinya ce, idan kuma ka kuskura ka 'kara aure to zaka gane baka da wayo dan duk wacce zaka aura ba zata kama 'kafar Wasila ba, zaka dawo inda kake salati kana kiran sunan Allah😅🤭 babu ruwana Sistar Sakina ce tafad'a🕺🕺 sannan Sistar Jamila tace duk wacce zaka aura sunanta salamatu salam dan ba zata iya da jarabarka ba🕺 babu ruwana! Jamila da Ummee ne suka fad'a ni dai 'yar aike ce......Momyna tace kayi auranka dan ba Wasila ce kadai mace ba, takwara Fatima Yakubu ma haka tafad'a Sai sistar Hadiza Shall itama haka tace ka more rayuwarka, Shafa'a S Yari da Bilba sunce kayi aure ka more rayuwarka💃🏼🔥 ni dai na isar da sa'kona Amadu sai ka yanke shawarar da zata fishe ka, nima nace ba Wasila ce kad'ai autar mat.......🙊😌*_ Cikin sanyin jiki suka koma cikin gidan Hajja ta gansu duk babu kuzari a tare dasu tace"Ai kam ni kaina naso su zauna su danyi kwana biyu ku samu sakewa da mahaifiyarku amma ace daga zuwa sai su tafi wallahi banji dadin hakan ba sai kace wad'anda ake kora." Rashida ta goge hawaye tace"Nima naso su zauna wallahi yanzu anti Wasila yaushe zamuje to." Wasila ta kalleta ranta duk babu dad'i tace."Sai an d'an kwana biyu baby tayi 'kwari zamuje insha Allahu." Hajja tace"Kwarai kuwa hakan yana da kyau, Allah ya kaimu ya bamu lafiya mai amfani." Duk suka amsa da "ameen." To har dai kusan goma da wajan rabi bai shigo gidan ba Hajja na kokarin shiga daki ta kwanta ya shigo da sallama a bakinsa......Dukaninsu suka amsa suna masa sannu da zuwa. Ya kalli Hajja yace."Ashe baki kwanta ba hajja ko kema kallon kike."? Tace"Oh!oh kai nake ta jira ka dawo ai." Yace."To Allah yasa lafiya."Ganin yana 'kokarin zama ya sanya ta mi'ke a hankali ta bar gurin, Rashida ma ganin 'yar uwarta ta tashi sai itama tayi yun'kurin mi'kewa yace."Rashida koma kiyi zamanki ya kina kallo zaki tashi kuma." Cike da kunya da jin nauyi ta koma ta zauna ta maida hankalinta kan tv.....Hajja tace" Dazu munyi ba'ki a gidanan na sanya Wasila tayi kiranka a waya kazo ku gaisa duk da nasan da cewar kasan da zuwan nasu, bai kamata ace suzo har su tafi baka zo kun gaisa da juna ba." Ya d'an dafe kansa yana girgixa kai ya kai minti uku a haka kafin ya d'ago kansa yana kallon Hajjan yace."Wallahi Hajja na manta shaf! ni da kaina na sanya Garba yaje ya daukosu amma kuma banyi tsammanin yau zasu koma ba shiyasa kwata kwata ban mai da hankalina gurin dawowa gida da wuri ba.'' Hajja tace"Aikuwa ko awanni uku basu cika ba suka tafi dan babu yanda banyi dasu su zauna su kwana biyu ba suka ki." Yace."Ashsha! nima ban so hakan ba naso mu gaisa dasu wallahi amma babu damuwa Insha Allahu zamu shirya muje idan momy tayi kwari." Hajja tace"To yawwa yanzu naji kayi magana dan haka naji ita Wasilan ma ta fad'a to dan Allah ka mai da hankali kada ka shiririce ka kai yaran nan su kwana biyu tare da mahaifiyarsu." Yace."Insha Allah Hajja." Mikewa yay yace."Bari na shiga nayi wanka." Hajja tace"To sai da safe dan nima shiga zanyi na kwanta." Yace."Hajja Allah ya tashemu lafiya." Hajja ta mike ta nufi daki shima ya nufi dakinsa. suka var Rashida ita kadai tana kallo. Wanka yay ya fito yana mamakin zuwan bakin da kuma tafiyarsu a gaggauce baiji dad'i ba gaskiya sai kace wad'anda ake kora ai sa bari su kwana tukkuna sai su koma gida, zuciyarsa ta shiga wasi-wasi kan Wasila yana tunanin kamar itace za tace su tafi tunda gashi tana fad'awa Hajja zasuje idan ankwana to kuwa idan hakane nufinta babu inda za taje duk wanda ke son ganinta daga can garin sai da yazo koda kuwa mahaifiyarta ce yana da inda zai sauketa, amma babu inda zataje masa da yarinya suje suyi kwana da kwanaki a wani guri. Cikin jallabiya ruwan madara ya fito palon....Shuru dan Rashida ma bacci yaci karfinta ta kashe kayan kallo taje ta kwanta.....Daning ya zauna yana kokarin zuba abinci, wai kamar mara mace shike hidima da kanshi illar auran ' kananun yara kenan ya tabbata yanzu inda Zeey ya aura lalla'bashi zata dinga yi tamkar 'kwai amma wannan 'kwalar ta sameshi a 'bagas tana masa abinda ranta yake so, abincin ya zuba duk ya 'bata daining din yana soma cin abincin Zeey ta kira wayarshi, koda ya duba yaga numbarta sai ya share ya'ki dauka, Zeey kuwa tun ranar da ya saurareta har yana cewa zaiyi shawara take jin tamkar an tsomata a aljanna gani take ma kamar har ya aure ta ya gama, Shine fa ta dingi kiran wayarsa babu ji babu gani, kuma tun jiya bai dauka ba, amma da ike bata da zuciya ba ta daina ba. Yanzu ta kira ya kai sau takwasa yaki dagawa abincinsa kawai yake ci hankalinsa a kwance, yana goge bakinsa wani kiran ya sake shigowa wanda yay dai-dai da fitowar Wasila daga dakinta, kafad'arta sa'be da baby zahra tana d'an kuka da harbe harbe......Yana ganin fitowarta yay saurin daukar wayar ya bude murya sosai ya mike daga daining din ya nufi palon yana magana da Zeey. Maganarsa ce ta sanya ta juyo da sauri dan ba tayi tsammanin yana palon ba, ta dan tsaya tana kallonshi lokacin da yake kokarin zama kan kujera yana dariya da fad'in "Zeey rigimarki yawa gareta yanzu yanzu na fito daga wanka naga kiran wayarki nima ban jima da shigowa gida ba." Taji gabanta yayi muguwar fad'uwa jin hannunta na rawa ya sanya ta ri'ke baby zahra da kyau! Yarinyar ta soma kuka tana cilla kafafu! da sauri ta dauke kainta ta juya ta cigaba da tafiya dakinsu Hajja ta nufa. Kukan momynsa ne ya sanya duk abinda yake yi ya fita daga ranshi dan a rayuwarsa ya tsani yaji tana kuka yay saurin datse wayar yana fad'in "Ki bari zan kira ki anjima yanzu ina da uziri." Mikewa yay yabi bayanta dakin. Sai ya tarar da babyn Zahra hannun Hajja tana duba cikinta da ya dan kumbura. Yarinyar sai kuka takeyi, Hajja tace"Kuma da kika bata nono ta kar'ba."? Murya na dan rawa tace"Eh mana bacci fa takeyi kawai ta tashi tana kuka nasa mata nono a bakinta ta'ki kar'ba shine nace to ko cikinta ne ke ciwo." Hajja tace"Da alama dai cikin nata ne ke ciwo dan gashinan ya nuna alama." Yakarasa kusa dasu dan har jikinsa ma na gogar nata ta kauce da sauri ta bashi hanya, ya tsaya gaban Hajjan yana kallon babyn yace."Hajja meke damunta ne."? Hajja tace"Cikinta ne ke ciwo da alama dan gashinan ya kumbura." Ya dan tsuguna yana duba yarinyar hannunsa ya sanya ya dan bubbuga cikin yaji dummm! hankali a tashe ya kalleta tana tsaye itama jikinta dik yay sanyi yace."Ina magungunanta."? Tace"Suna d'aki." Cike da bada umarni yace."Kije ki dauko." Fita tai daga daga d'akin, Ta dawo dakin hannunta rike da wani d'an kwando da kwalayen magunguna a ciki. Kar'ba yay yana duddubawa, kwata kwata babu maganin ciwon ciki a ciki. Hajja Tace."Ai duk ba wannan ba ke Wasila maza jeki kicin ki d'an had'a ruwan d'umi da gishiri kad'an ki kawo min na bata insha Allah ko yaya inda ya shiga cikinta za tayi gyatsa watakila kin bata nono a kwance ne." Wasila tace"Ina bata nono bacci ya daukeni sai kawai na kwanta ina kuma kwanciya ta fara kuka shine na bata nonon a kwance." Hajja tace"Ai kinji matsalar dama! dan Allah ku daina bawa 'yayanku nono a kwance yana janyo musu illah babba har 'kwa'kwalwa yana ta'ba musu idan suka 'kware a haka sai kiga an samu matsala." Ta bude baki kenan za tayi magana ya katseta, fuska a daure murya a kausashe yace."Ai rashin hankaline dama kawai ki kwanta kina bawa yarinya nono a kwance meye amfanin hakan, ke zaki iya cin abinci akwance ne? Abinda kika kasan ba zaki iya ba to kada ki sake kwatantashi kan yarinyar nan! gashinan kin jawo mata lalura." Ba tare da tace masa komai ba ta kad'a kanta ta fice daga d'akin zuciyarta kamar zata babbake saboda tsabar bakin ciki da takaici.....Koda ta shiga kicin din ma kasa kata'bus tayi dan tama manta abinda ya shigar da ita, zama tayi kan wata kujera tana kuka ya kufce mata. Wai shin dame zataji ne? a cikin gidanan kullum babu kwanciyar hankali abu kadan sai masifa daga kawai ta bawa yarinya nono a kwance sai ace taja mata lalura duk dai so da kaunar da yake wa yarinyar bai kai ya nata ba itace ta haifeta tasha wahalar daukar nauyin cikinta kafin tazo duniya kome za i nuna akan yarinyar bai kai ya ita ba............Jin shuru bata dawowa yabi bayanta a fusace! Ya lura sa yarinyar nan so take ta kashe masa 'yarsa....Sai dai me? yana shiga kicin din ya tarar da ita ta had'a kai da gwiwa tana kuka, sai kuma jikinsa yay sanyi a hankali ya shiga kicin din motsinsa ya sanya ta d'ago kanta da sauri! ganinsa ya sanya ta saurin mai da kanta, bai kalli inda take ba ya soma dube dube a kicin din kwalbar gushirin ya d'auko dake saman kanta ya bud'e ya samu cup karami ya zuba kadan kana ya tsiyayi ruwan d'umi dai-dai misali ya dan motsa ruwan da gishirin suka had'e sai da ya fara sawa a bakinsa yaji dai-dai sannan ya wuce ya fita daga kicin din hannunsa rike da cup din ba tare da ya kalli inda take raku'be ba. Yana shiga da'kin da ruwan gishirin a hannunsa Hajja ta kar'ba a hankali ta dinga dandala mata a bakinta tana tsotsewa sai da tayi mata sau uku sannan ta mike tana kokarin sata a kafad'a, Rashida tace"Hajja koma ki zauna kawo in dan zagaya da ita." Hajja ta zauna tana fad'in " A kafad'a zaki sanyata insha Allah yanzu za tayi gyatsa." Rashida ta kar'bi babyn tasa a kafada ta shiga zagaye da ita a dakin.....Cikin ikon Allah kuwa ta daina kukan da takeyi ta shiga sauke ajiyar zuciya tana sakin gyatsa. Hajja tace"Alhamdullhi yanzu zakaga tayi bacci." Yace."Ai gwara tayi baccin Hajja yarinya kankanuwa cikinta yay irin wannan kumburin wanda ko a gurin babba ma zaiji jiki ballanta yaro karami irinta." Hajja tace"Mafi akasari dama 'kananun yara kamarta sunayin irin wannan kumewar cikin, sai hankali suke dainawa wasu kuwa sai suyi kwana da kwanaki ma basuyi bayan gari ba." Yace."Idan hakane kuwa al'amarin akwai ban tausayi wallahi." Hajja tayi murmushi tare da gyara kwanciya tana fad'in " to nidai sai da safe jama'a ina baccina tsohuwa ta tasheni dan dai kawai sunan kishiyata ne da ita shiyasa na saurareta da badan taci darajar sunan Yafindo ba to da sai dai ta nemi wanda zai rarrasheta." Rashida tace"Kai Hajja ai yanzu ma bake kika rarrasheta ba Momynra ce." Hajja na hamma tace"Haka kika ce ko."? Rashida na dariya tace"Ai gaskiya na fada Hajja gani ina rarrashinta har tayi bacci kice kece kika rarrasheta." Hajja tace"Shikkenan dan dai ba'a fatan cuta ne da sai nace gobe ma rana ce." Rashida tasa dariya tana dan bubbuga bayan baby zahran wacce ke lumshe ido bacci na fuzgarta.....A hankali yace."Kawota nan Rashida kema kije ki kwanta an tasheku kuna bacci ko." Cike da jin nauyi ta mika masa yarinyar tace"Haba babu komai Wallahi kaga ma bacci zatayi." Ya kar'be ta tare da rungumeta a jikinsa, yace."Ki dinga yiwa yayarki fad'a har yanzu ta'ki hankali." Kanta ta sunkuyar tana d'an murmushi, ya kama hanya ya fita daga dakin rungume da yarinyarsa a jikinsa. Tana kwance a gado tana tunanin rayuwa ya tura kofar dakin ya shigo, rufe idanunta tayi taki yin kwakkwaran motsi mugun haushinsa takeji dan duk wani girma da 'kimarsa da take gani ada yanzu sun zube a idonta. A hankali ya kwantar da babyn a gadonta, ya dan tsaya a kan yarinyar minti biyar ya tofe mata jikinta da addua kana ya juya da niyyar fita daga dakin. Ja yay ya tsaya yana tunani, sai kuma ya bud'e kofar dakin ya fita, tana jin fitarsa ta bude idanunta ta mike zaune tana jan tsaki! Yarinyar ta dauko ta dawo da ita kusa da ita ta kwanta tare da rufe jikinta da bargo, bacci har ya soma daukarta taji an bude dakin an shigo shine dai ya kara shigowa, dake ta kashe fitilar dakin sai ya kunna wayarsa yana duba gadon babyn, wayam babu ita, da sauri ya kalli bed din ya gansu a lullebe! a jiyar zuciya ya sauke, ya kashe wayarsa ya aje saman bedside ya zare jallabiyar jikinsa dake akwai singlet a jikinsa da gajeran wando sai kawai ya shiga cikin bargon nasu yay kwanta rigingine fuskarsa na kallon rufin dakin, ya dora hannuwansa a kirjinsa, yana addua, sai da ya gama tukkuna ya tofe musu jikinsu gabad'aya kana ya rufe idanunsa, Wasila gabanta tun yana fad'uwa har ya daina fad'uwa ganin tunda ya kwanta baiyi kuskuran koda rik'e d'an yatsanta ballanta yay mata wani abun asali ma ya bada tazara mai yawa a tsakaninsa da ita sanda tayi dubarar juyawa ta fahimci hakan......Al'amarin yay masifar 'bata mata rai! da kyar ta samu bacci ya dauketa, saboda tsabar damuwa da 'bacin ran da take ciki. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *78* _*Sa'ko na mussaman zuwa gareka Amadu 'kawayen Wasila irin su Mumy Farhan, Bomis Zainab kankara Mrs Aliyu Nafisa Buhari Hauwa Chindo, Sakina Ummee da dai sauransu, sunce kayi hakuri dan Allah karkayiwa Wasila kishiya kayi mata uziri saboda yarinya ce, idan kuma ka kuskura ka 'kara aure to zaka gane baka da wayo dan duk wacce zaka aura ba zata kama 'kafar Wasila ba, zaka dawo inda kake salati kana kiran sunan Allah😅🤭 babu ruwana Sistar Sakina ce tafad'a🕺🕺 sannan Sistar Jamila tace duk wacce zaka aura sunanta salamatu salam dan ba zata iya da jarabarka ba🕺 babu ruwana! Jamila da Ummee ne suka fad'a ni dai 'yar aike ce......Momyna tace kayi auranka dan ba Wasila ce kadai mace ba, takwara Fatima Yakubu ma haka tafad'a Sai sistar Hadiza Shall itama haka tace ka more rayuwarka, Shafa'a S Yari da Bilba sunce kayi aure ka more rayuwarka💃🏼🔥 ni dai na isar da sa'kona Amadu sai ka yanke shawarar da zata fishe ka, nima nace ba Wasila ce kad'ai autar mat.......🙊😌*_ Cikin sanyin jiki suka koma cikin gidan Hajja ta gansu duk babu kuzari a tare dasu tace"Ai kam ni kaina naso su zauna su danyi kwana biyu ku samu sakewa da mahaifiyarku amma ace daga zuwa sai su tafi wallahi banji dadin hakan ba sai kace wad'anda ake kora." Rashida ta goge hawaye tace"Nima naso su zauna wallahi yanzu anti Wasila yaushe zamuje to." Wasila ta kalleta ranta duk babu dad'i tace."Sai an d'an kwana biyu baby tayi 'kwari zamuje insha Allahu." Hajja tace"Kwarai kuwa hakan yana da kyau, Allah ya kaimu ya bamu lafiya mai amfani." Duk suka amsa da "ameen." To har dai kusan goma da wajan rabi bai shigo gidan ba Hajja na kokarin shiga daki ta kwanta ya shigo da sallama a bakinsa......Dukaninsu suka amsa suna masa sannu da zuwa. Ya kalli Hajja yace."Ashe baki kwanta ba hajja ko kema kallon kike."? Tace"Oh!oh kai nake ta jira ka dawo ai." Yace."To Allah yasa lafiya."Ganin yana 'kokarin zama ya sanya ta mi'ke a hankali ta bar gurin, Rashida ma ganin 'yar uwarta ta tashi sai itama tayi yun'kurin mi'kewa yace."Rashida koma kiyi zamanki ya kina kallo zaki tashi kuma." Cike da kunya da jin nauyi ta koma ta zauna ta maida hankalinta kan tv.....Hajja tace" Dazu munyi ba'ki a gidanan na sanya Wasila tayi kiranka a waya kazo ku gaisa duk da nasan da cewar kasan da zuwan nasu, bai kamata ace suzo har su tafi baka zo kun gaisa da juna ba." Ya d'an dafe kansa yana girgixa kai ya kai minti uku a haka kafin ya d'ago kansa yana kallon Hajjan yace."Wallahi Hajja na manta shaf! ni da kaina na sanya Garba yaje ya daukosu amma kuma banyi tsammanin yau zasu koma ba shiyasa kwata kwata ban mai da hankalina gurin dawowa gida da wuri ba.'' Hajja tace"Aikuwa ko awanni uku basu cika ba suka tafi dan babu yanda banyi dasu su zauna su kwana biyu ba suka ki." Yace."Ashsha! nima ban so hakan ba naso mu gaisa dasu wallahi amma babu damuwa Insha Allahu zamu shirya muje idan momy tayi kwari." Hajja tace"To yawwa yanzu naji kayi magana dan haka naji ita Wasilan ma ta fad'a to dan Allah ka mai da hankali kada ka shiririce ka kai yaran nan su kwana biyu tare da mahaifiyarsu." Yace."Insha Allah Hajja." Mikewa yay yace."Bari na shiga nayi wanka." Hajja tace"To sai da safe dan nima shiga zanyi na kwanta." Yace."Hajja Allah ya tashemu lafiya." Hajja ta mike ta nufi daki shima ya nufi dakinsa. suka var Rashida ita kadai tana kallo. Wanka yay ya fito yana mamakin zuwan bakin da kuma tafiyarsu a gaggauce baiji dad'i ba gaskiya sai kace wad'anda ake kora ai sa bari su kwana tukkuna sai su koma gida, zuciyarsa ta shiga wasi-wasi kan Wasila yana tunanin kamar itace za tace su tafi tunda gashi tana fad'awa Hajja zasuje idan ankwana to kuwa idan hakane nufinta babu inda za taje duk wanda ke son ganinta daga can garin sai da yazo koda kuwa mahaifiyarta ce yana da inda zai sauketa, amma b abu inda zataje masa da yarinya suje suyi kwana da kwanaki a wani guri. Cikin jallabiya ruwan madara ya fito palon....Shuru dan Rashida ma bacci yaci karfinta ta kashe kayan kallo taje ta kwanta.....Daning ya zauna yana kokarin zuba abinci, wai kamar mara mace shike hidima da kanshi illar auran 'kananun yara kenan ya tabbata yanzu inda Zeey ya aura lalla'bashi zata dinga yi tamkar 'kwai amma wannan 'kwalar ta sameshi a 'bagas tana masa abinda ranta yake so, abincin ya zuba duk ya 'bata daining din yana soma cin abincin Zeey ta kira wayarshi, koda ya duba yaga numbarta sai ya share ya'ki dauka, Zeey kuwa tun ranar da ya saurareta har yana cewa zaiyi shawara take jin tamkar an tsomata a aljanna gani take ma kamar har ya aure ta ya gama, Shine fa ta dingi kiran wayarsa babu ji babu gani, kuma tun jiya bai dauka ba, amma da ike bata da zuciya ba ta daina ba. Yanzu ta kira ya kai sau takwasa yaki dagawa abincinsa kawai yake ci hankalinsa a kwance, yana goge bakinsa wani kiran ya sake shigowa wanda yay dai-dai da fitowar Wasila daga dakinta, kafad'arta sa'be da baby zahra tana d'an kuka da harbe harbe......Yana ganin fitowarta yay saurin daukar wayar ya bude murya sosai ya mike daga daining din ya nufi palon yana magana da Zeey. Maganarsa ce ta sanya ta juyo da sauri dan ba tayi tsammanin yana palon ba, ta dan tsaya tana kallonshi lokacin da yake kokarin zama kan kujera yana dariya da fad'in "Zeey rigimarki yawa gareta yanzu yanzu na fito daga wanka naga kiran wayarki nima ban jima da shigowa gida ba." Taji gabanta yayi muguwar fad'uwa jin hannunta na rawa ya sanya ta ri'ke baby zahra da kyau! Yarinyar ta soma kuka tana cilla kafafu! da sauri ta dauke kainta ta juya ta cigaba da tafiya dakinsu Hajja ta nufa. Kukan momynsa ne ya sanya duk abinda yake yi ya fita daga ranshi dan a rayuwarsa ya tsani yaji tana kuka yay saurin datse wayar yana fad'in "Ki bari zan kira ki anjima yanzu ina da uziri." Mikewa yay yabi bayanta dakin. Sai ya tarar da babyn Zahra hannun Hajja tana duba cikinta da ya dan kumbura. Yarinyar sai kuka takeyi, Hajja tace"Kuma da kika bata nono ta kar'ba."? Murya na dan rawa tace"Eh mana bacci fa takeyi kawai ta tashi tana kuka nasa mata nono a bakinta ta'ki kar'ba shine nace to ko cikinta ne ke ciwo." Hajja tace"Da alama dai cikin nata ne ke ciwo dan gashinan ya nuna alama." Yakarasa kusa dasu dan har jikinsa ma na gogar nata ta kauce da sauri ta bashi hanya, ya tsaya gaban Hajjan yana kallon babyn yace."Hajja meke damunta ne."? Hajja tace"Cikinta ne ke ciwo da alama dan gashinan ya kumbura." Ya dan tsuguna yana duba yarinyar hannunsa ya sanya ya dan bubbuga cikin yaji dummm! hankali a tashe ya kalleta tana tsaye itama jikinta dik yay sanyi yace."Ina magungunanta."? Tace"Suna d'aki." Cike da bada umarni yace."Kije ki dauko." Fita tai daga daga d'akin, Ta dawo dakin hannunta rike da wani d'an kwando da kwalayen magunguna a ciki. Kar'ba yay yana duddubawa, kwata kwata babu maganin ciwon ciki a ciki. Hajja Tace."Ai duk ba wannan ba ke Wasila maza jeki kicin ki d'an had'a ruwan d'umi da gishiri kad'an ki kawo min na bata insha Allah ko yaya inda ya shiga cikinta za tayi gyatsa watakila kin bata nono a kwance ne." Wasila tace"Ina bata nono bacci ya daukeni sai kawai na kwanta ina kuma kwanciya ta fara kuka shine na bata nonon a kwance." Hajja tace"Ai kinji matsalar dama! dan Allah ku daina bawa 'yayanku nono a kwance yana janyo musu illah babba har 'kwa'kwalwa yana ta'ba musu idan suka 'kware a haka sai kiga an samu matsala." Ta bude baki kenan za tayi magana ya katseta, fuska a daure murya a kausashe yace."Ai rashin hankaline dama kawai ki kwanta kina bawa yarinya nono a kwance meye amfanin hakan, ke zaki iya cin abinci akwance ne? Abinda kika kasan ba zaki iya ba to kada ki sake kwatantashi kan yarinyar nan! gashinan kin jawo mata lalura." Ba tare da tace masa komai ba ta kad'a kanta ta fice daga d'akin zuciyarta kamar zata babbake saboda tsabar bakin ciki da takaici.....Koda ta shiga kicin din ma kasa kata'bus tayi dan tama manta abinda ya shigar da ita, zama tayi kan wata kujera tana kuka ya kufce mata. Wai shin dame zataji ne? a cikin gidanan kullum babu kwanciyar hankali abu kadan sai masifa daga kawai ta bawa yarinya nono a kwance sai ace taja mata lalura duk dai so da kaunar da yake wa yarinyar bai kai ya nata ba itace ta haifeta tasha wahalar daukar nauyin cikinta kafin tazo duniya kome zai nuna akan yarinyar bai kai ya ita ba............Jin shuru bata dawowa yabi bayanta a fusace! Ya lura sa yarinyar nan so take ta kashe masa 'yarsa....Sai dai me? yana shiga kicin din ya tarar da ita ta had'a kai da gwiwa tana kuka, sai kuma jikinsa yay sanyi a hankali ya shiga kicin din motsinsa ya sanya ta d'ago kanta da sauri! ganinsa ya sanya ta saurin mai da kanta, bai kalli inda take ba ya soma dube dube a kicin din kwalbar gushirin ya d'auko dake saman kanta ya bud'e ya samu cup karami ya zuba kadan kana ya tsiyayi ruwan d'umi dai-dai misali ya dan motsa ruwan da gishirin suka had'e sai da ya fara sawa a bakinsa yaji dai-dai sannan ya wuce ya fita daga kicin din hannunsa rike da cup din ba tare da ya kalli inda take raku'be ba. Yana shiga da'kin da ruwan gishirin a hannunsa Hajja ta kar'ba a hankali ta dinga dandala mata a bakinta tana tsotsewa sai da tayi mata sau uku sannan ta mike tana kokarin sata a kafad'a, Rashida tace"Hajja koma ki zauna kawo in dan zagaya da ita." Hajja ta zauna tana fad'in " A kafad'a zaki sanyata insha Allah yanzu za tayi gyatsa." Rashida ta kar'bi babyn tasa a kafada ta shiga zagaye da ita a dakin.....Cikin ikon Allah kuwa ta daina kukan da takeyi ta shiga sauke ajiyar zuciya tana sakin gyatsa. Hajja tace"Alhamdullhi yanzu zakaga tayi bacci." Yace."Ai gwara tayi baccin Hajja yarinya kankanuwa cikinta yay irin wannan kumburin wanda ko a gurin babba ma zaiji jiki ballanta yaro karami irinta." Hajja tace"Mafi akasari dama 'kananun yara kamarta sunayin irin wannan kumewar cikin, sai hankali suke dainawa wasu kuwa sai suyi kwana da kwanaki ma basuyi bayan gari ba." Yace."Idan hakane kuwa al'amarin akwai ban tausayi wallahi." Hajja tayi murmushi tare da gyara kwanciya tana fad'in " to nidai sai da safe jama'a ina baccina tsohuwa ta tasheni dan dai kawai sunan kishiyata ne da ita shiyasa na saurareta da badan taci darajar sunan Yafindo ba to da sai dai ta nemi wanda zai rarrasheta." Rashida tace"Kai Hajja ai yanzu ma bake kika rarrasheta ba Momynra ce." Hajja na hamma tace"Haka kika ce ko."? Rashida na dariya tace"Ai gaskiya na fada Hajja gani ina rarrashinta har tayi bacci kice kece kika rarrasheta." Hajja tace"Shikkenan dan dai ba'a fatan cuta ne da sai nace gobe ma rana ce." Rashida tasa dariya tana dan bubbuga bayan baby zahran wacce ke lumshe ido bacci na fuzgarta.....A hankali yace."Kawota nan Rashida kema kije ki kwanta an tasheku kuna bacci ko." Cike da jin nauyi ta mika masa yarinyar tace"Haba babu komai Wallahi kaga ma bacci zatayi." Ya kar'be ta tare da rungumeta a jikinsa, yace."Ki dinga yiwa yayarki fad'a har yanzu ta'ki hankali." Kanta ta sunkuyar tana d'an murmushi, ya kama hanya ya fita daga dakin rungume da yarinyarsa a jikinsa. Tana kwance a gado tana tunanin rayuwa ya tura kofar dakin ya shigo, rufe idanunta tayi taki yin kwakkwaran motsi mugun haushinsa takeji dan duk wani girma da 'kimarsa da take gani ada yanzu sun zube a idonta. A hankali ya kwantar da babyn a gadonta, ya dan tsaya a kan yarinyar minti biyar ya tofe mata jikinta da addua kana ya juya da niyyar fita daga dakin. Ja yay ya tsaya yana tunani, sai kuma ya bud'e kofar dakin ya fita, tana jin fitarsa ta bude idanunta ta mike zaune tana jan tsaki! Yarinyar ta dauko ta dawo da ita kusa da ita ta kwanta tare da rufe jikinta da bargo, bacci har ya soma daukarta taji an bude dakin an shigo shine dai ya kara shigowa, dake ta kashe fitilar dakin sai ya kunna wayarsa yana duba gadon babyn, wayam babu ita, da sauri ya kalli bed din ya gansu a lullebe! a jiyar zuciya ya sauke, ya kashe wayarsa ya aje saman bedside ya zare jallabiyar jikinsa dake akwai singlet a jikinsa da gajeran wando sai kawai ya shiga cikin bargon nasu yay kwanta rigingine fuskarsa na kallon rufin dakin, ya dora hannuwansa a kirjinsa, yana addua, sai d a ya gama tukkuna ya tofe musu jikinsu gabad'aya kana ya rufe idanunsa, Wasila gabanta tun yana fad'uwa har ya daina fad'uwa ganin tunda ya kwanta baiyi kuskuran koda rik'e d'an yatsanta ballanta yay mata wani abun asali ma ya bada tazara mai yawa a tsakaninsa da ita sanda tayi dubarar juyawa ta fahimci hakan......Al'amarin yay masifar 'bata mata rai! da kyar ta samu bacci ya dauketa, saboda tsabar damuwa da 'bacin ran da take ciki. Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *79* Wajejen 'karfe uku da rabi ya farka ya lalubi wayarshi ya kunna haskenta yana dubasu Baby Zahra bacci take sosai da'alama kuma tana jin dadin baccinta, fuskar Wasila ya haske ya dan tsira mata ido sai yaga kamar fuskarta ta ta d'an kumbura mussaman fatar idonta alamu ya nuna kafin tayi bacci taci kuka ta koshi, ya jima yana kallon fuskarta yana jin wani irin tausayinta na ratsa jikinsa, ya girgiza kanshi a hankali ya mika hannunsa kan hannunta data dan kwanta akansa hakan zai iya janyowa hannunta data kwanta akai yayi mata tsami! gyara mata yake kokarin yi ta bud'e idonta tana dan mi'ke kafafunta, hakan da tayi sai ya dan rankwafo jikinta, tayi gaggawar mikewa zaune shi kuma yay saurin sauka daga bed din ya kama hanya ya fice daga dakin, Shuru tayi tana tunani to da me zaiyi matane? bata da mai bata amsa, sai kawai ta kunna fitilar dakin haske ya gauraye ta kalli agogo taga hudu saura minti ashirin har an soma kiran sallahr farko....A hankali ta dan gyarawa baby kwanciyarta ta mike ta nufi toilet Wanka ta soma yi kafin ta daura alwala ta fito ta shirya cikin duguwar riga da hijab mai tsayi ta hau kan dadduma, nafila tayi raka'a biyu bayan ta idar ta daga hannunta sama tana addua tana hawaye kan Allah ya za'ba mata abunda yafi alkairi dangane da zamanta da mijinta. Al'kurani ta dauka ta fara karantawa tun daga fatiha har sai dai tayi izifi biyar tukkuna ta rufe al'kur'anin ta tada sallahar asubahi.......Tana idarwa baby zahra ta tashi ta soma kuka da neman nono, Da sauri ta cire hijab din jikinta ta dauki yarinyar ta ciro nono tasa mata a baki. Yarinyar na tsotsar nono ita kuma tana share hawaye daga haihuwar fari har gishiri ya salamce daga jikin kaza ashe dama duk k'aryace ba wani sonta da yake tunda gashi tun ba'aje ko ina ba yana wulakanta kan abinda bai taka kara ya karya ba, ta tabbata jiya yana sane ya'ki daukar wayarta kawai saboda ya wulakanta, kuma tasan domin ya kuntata mata ne yake waya da budurwarsa a gida insha Allah ba zata sake kiransa a waya ba domin tana masifar jin ciwon rashin amsa mata da yakeyi. Gari ya dan soma yin haske ya shigo dakin ya sauya jallabiya yanzu ba'ka ce a jikinsa mai gajeran gannu da dogon wuya jallabiyar dai larabawa sunfi anfani da ita, hannunsa rike da cazbaha ya 'karaso gabanta. Kanta a 'kasa tace"Ina kwana."? Idanunsa kan baby zahra Ya amsa babu yabo babu fallasa." Shuru tayi fuskarta a cukune. Yace."Ya jikin Mommy."? Da sauki." tafad'a a takaice. Yace."Ki fito yau zamuyi zaman karatu." Shuru tayi masa, ya kama hanya ya fice daga dakin. Palon ta fito cikin hijab hannunta rungume da baby ganin Hajja bata a palon sai ta nufi dakinta, tana kokarin fitowa suka gaisa ta mi'ka mata yarinyar tace"Yau zamu koma karatu Hajja ga 'kawarki." Hajja tace"Dama yanzu nake shirin shiga ai nayi mata wanka." Wasila tayi murmushi tace" Ai kam da wuri ta tashi tayi ta tsotson nono ina shirin mata wanka Babanta yace zamu zauna karatu." Hajja tace"To bari nayi mata wankan anan na shiryata. Tace"Bari na dauko miki kayanta." Tana fitowa palo ta tarar dashi da Rashida sun soma karatu, ya dago kansa suka hada ido sai tayi saurin dauke kanta ta wuce dakinta. minti biyar ta fito rike da kayan a hannunta dakin hajjan ta nufa ta mika mata ta fito ta zauna gurin karatun. A'lkur'ani ta bude dai-dai inda suke ta cigaba da sauraranshi har ya gama musu karatun yace su biya mishi yaji. A nutse suka soma biya mishi aya goma yake musu da safe da dare shi kanshi yana mamaki da yanda Allah yayi musu kwakwalwar saurin daukar karatu sam basa bashi wuya gurin karatu nan da nan suke daukewa, mussaman Wasila. Sauran littafan ya biya musu yana musu bayanin yanda zasu fahimta sosai, bayan sun kammala ne ya kalli Rashida a nutse yace."Rashida ya karatunki na boko ina fatan komai yana tafiya dai-dai kina fahinta."? Tace"Eh ina ganewa wallahi dan mun kusa jarrabawa tunda ina cikin wad'anda zasuyi jarabbawar fita." Yace."Alhamdullhi Ya kalli Wasila da hankalinta ke kan littafin zaduzjaujen Yace."Kema ki shirya insha Allahu za'ayi yanza za'ayi ki shiga cikinsu kiyi jarrabawa tunda naga babu lefi kina ganewa i dan Allah jarrabawar tayi kyau xanyi magana da abokina Prof 'Dalhatu Nuhu dake jami'ar Bayaro a sama muku gurbin karatu a makarantar insha Allahu." A hankali tace."To mungode, mikewa yay ya nufi dakinsa, itama ta mike jikinta a sabule ta nufi nata dakin, ita kanta rashida jikinta yay sanyi ta lura kamar akwai matsala a tsakaninsu dan duk sanda suka zauna zaman karatun kafin su fara sai sunyi wasa da dariya a tsakaninsu, dan wataran ma idan sunayi ita har kunya suke bata, amma yanzu taga ita dashi sun bawa kansu tazara ko wanne fuskarsa a had'e. Mikewa tayi tabi Wasilan dakinta.....Lokacin tayi wanka tana shiryawa rashida ta zauna gefan gado tana kallonta so take tayi mata magana amma kuma tana jin tsoro kar tayi mata masifa.....Wasila ta shirya cikin atamda java ja da baka d'inkin fetted gwon yay masifar fito mata da sharp dinta dan har sai da ta d'an saki zuf din rigar ta baya dake ta kwana biyu bata saka kayan ba, yanzu rigar ta matseta ire iren d'inkunanta ne na fitsara lokacin tana harkar siyasarta, Rashida tace"Anti Wasila dama wannan kayan suna nan." Tace"Gasu kuwa kin gani." Rashida tace"Yanzu sun matseki ba kamar da ba." Tana fesa turare a jikinta tace"Eh na dan yi 'kiba shiyasa. Dankwalinta ta daura ta nannad'e gashinta dashi ya fito ta ciki ta danyi make up kadan a fuskarta tasa jan janbaki a le'bunanta, wani masifar kyau tayi tamkar ka sace ka gudu." Rashida tace"Anti Wasila atamfar nan nayi miki kyau sosai." Tace."Nima shiyasa nake sonta." Rashida tace"Anti Wasila dan Allah kada kice nasa miki ido wai me yake faruwa ne tsakaninki da maigidan naga tun bayan tafiyar Inna Hajara ke dashi kuka rage walwala magana ma da kyar kukewa junanku. Wasila ta dan kalleta tana mamakin maganarta, ashe dai duk yanda take kokarin 'boye al'amarin sai da aka gane, jikinta a sanyaye tace"Rashida abokin kuka shi ake fadawa mutuwa, ke 'kanwata ce kuma nasan kina da hankali kin kai munzali kuma kin san abinda ke faruwa, yanzu dan Allah kece ace ki haihu kisha wuya sannan ayi miki d'inki gurin be warke ba sannan mijinki yazo miki da bukatar yin sex dake shin zaki yarda ki amince dashi ya lalata miki aiki ko ba zaki yarda ba."? Rashida tayi shiru tana tunani tace"Gaskiya mutukar gurin be warke ba bazan yarda ba dan idan d'inkin ya lalace inaji ina gani za'a sake min wani kuma shima mijin nawa daga ranar ya daina ganin amfanina amma idan na tabbatar da gurin ya warke zan amince na biya masa bukatarsa tunda hakkinsa ne." Wasila ta sauke ajiyar zuciya tace"To abinda ke faruwa kenan a tsakaninmu lokacin Inna Hajara nan tana nuna kulawarta a kaina shine yake jin haushinta wai ita ke zugani, na nuna masa ba haka bane shine yake fushi dan da Inna Hajaran ma ta tafi baice komai ba ya nuna yaji dadin tafiyarta, Rashida ni ban hanashi hakkinsa ba da ya amince da sai na dinga biya mishi bukatarsa ta wata hanya har Allah yasa gurin ya warke amma sai ya nuna shi dole sai ya shiga gurin ni kuma na'ki amincewa saboda nasan halinsa, shine fa yake ta fushi na bashi hakuri yaki hakura, Ina ga ma neman aure yake dan kullum sai sunyi waya da budurwarsa." Ta'karasa maganar muryarta na rawa tabbacin abin na mutukar damunta daurewa kawai take.......Rashida tace"To anti Wasila kema kina da gaskiya dan gaskiya kika sakar mishi jiki bayan kuma kin san da ciwo a gurin aiki ya 'baci ke zai bari a ciki, amma ga shawara me zai hana ki koma asibitin su duba miki su tabbatar gurin yayi dai-dai idan hakane sai kawai ki shirya ki cigaba da kula da mijinki." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Rashida tun Inna Hajara na nan da mukaje asibitin suka tabbatar aikin yay kyau dan gurin ya dawo normal kawai ni ina jin ciwo kadan kadan ne wallahi kuma ina jin tsoro kada wannan abun ya sanya wani abun ya faru sannan kuma kinga banyi wani gyaran jiki ba na fiso na gyara jikina sosai kafin sannan gurin ya sake yin 'kwari yanda ake so." Rashida tace"Gaskiya wannan ba dubara bace anti Wasila to shi kuma sai yayi ta zama da lalura kawai dan biyan bukatarki, ai tunda an tabbatar miki da lafiyar gurin ki amince masa da bukatarsa." Shuru tayi tana tunani tace."Shikkenan na dauki shawarark i zan amince masa idan ya sake nema nima sam bana son irin wannan zaman da muke." Rashida tace"Nima abin Bayayi min dadi gashi kuma naga kamar ya damu wallahi daurewa kawai yake." Ta'be bakinta tayi tace"Ni idan ta nine magana ta wuce ko yanzu ya nema shikkenan idan kuma yayi zuciya shi ya jawo." Rashida ta mike suka fita palo a tare Shi kadai ne zaune a daning yana karyawa Hajja na zaune a kujera da baby zahra a hannunta tayi mata wanka tsaf ta shiryata cikin kayan sanyi kasancewar ranar an tashi da lillimi baby zahra sai kamshin turare masu dadi takeyi, sosai yarinyar take kara kyau da ki'ba saboda tana samun kulawa ta ko wane bangare. Tun sanda suka fito daga dakin ya dora idanunsa kanta ya rasa nutsuwarsa, dan idonsa ya tsurata yana binta da wani mayataccen kallo tana tsaye tsakiyar palon suna magana da Hajja! Ya 'kura bayanta ido da yake a d'an bud'e saboda ta saki zuf din rigar kadan dan har brexiyar ta ta fito daga ciki, ajiyar zuciya ya dinga saukewa gabanshi na wani irin fad'uwa ji yay yawun bakinsa ya tsinke! kwata kwata ya gaza dauke idonsa daga kanta idanunsa sunyi masifar galabaita gurin kallon d'uwawunka da suka fito dam! dam cikin rigar kamar zasuyi magana ga lafiyayyar fatarta dake she'ki da daukar ido lukwi lukwi da ita da wani irin kwantaccen gashi a kai. Tsigar jikinsa ta dinga tashi sanyi ya soma ratsa jiki da 'bargonsa.....Rashida tayi saurin daukar abinda zata dauka wanda zata karya dashi ta bar daining din dan ta lura hankalin Yayan nata nakan yayarta wanda ta fahimci kamar ma baya cikin hankalinsa dan har ta gama abinda za tayi a gurin be kalli inda take ba. Wasila ta juyo tana dariya da fad'in "Kai Hajja! idan kin tafi ai ba Kishiyarki ce kadai zatayi kewa ba har damu dan Allah ki zauna kada ki tafi wallahi ba zamuji dadi ba." Hajja tace"Tafiya kuwa ta zama dole gobe i war haka na sauka a gida." Tana tafiya domin isa dainnig din take''Gaskiya Hajja ba zaki tafi ba zamu shiga cikin wani hali na kew.......Kasa 'karasa maganar tayi ganin ya zuba mata ido yana mata wani irin masifaffan kallo tamkar zai cinyeta, a take ta dai-daita nutsuwarta ta dan rage walwalar fuskarta, ta dan gyara kujera ta zauna tana ya mutse fuska, ita sam bata lura ma dashi a palon ba, haba wannan kallo kamar mawuyanci." Tea take kokarin had'awa hannunta ya shiga kyarma! sakamakon idanunsa masu mugun dafi da ya zuba mata, ta dan kalleshi a sace sai taga hankalinsa gabadaya nakan jikinta yana kallon brest dinta da suka fito ta saman riga........Taji dad'in hakan dama yaushe zai iya daurewa tasan halinsa sarai! sai ta dinga d'an gantsaro 'kirjinta tana d'an motsa jikinta da sunan tana gyara zamanta.......Wayarshi tayi ta ringing yana ji ya kasa dauka. Ta dago a hankali tace"Ana kiranka a waya." Dan dauke kansa yay yace."Rabu da ita." Shuru tayi tana ta'be bakinta, ta had'a tea din zata fara sha yace."Bani wannan ki had'a wani." Mi'ka masa tayi ba tace komai ba ta had'a wani ta fara sha tana had'awa da bread, tana kallonshi ya kasa shan tea din sai auki tsaki da yake saki yana latsa wayarsa, ba tace masa komai ta gama break dinta ta mike ta bar masa gurin...........Tashinta da kamar minti biyar shima ya mike a maimakon ya fita kamar yansa ya niyyata sai ya shige dakinsa ya kwanta, zazzabi zazzabi na nema ya rufeshi. Ita kam Wasila taji dad'in yanda taga tarkonta ya kamashi, murmushi take saki lokaci da lokacin tana jin sanyi cikin zuciyarta, tasan ko bata kai masa kanta ba to tana da tabbacin shi da kansa xai kawo kanshi..........Tunda ya shiga dakinshi bai fito ba sai lokacin sallar la'asar Hajja na kokarin shiga ta dauro alwala taga fitowarshi shima da shirin zuwa masjid tace"A'a dama kana ciki baka fita ba."? A dan kasalance yace."Hajja ban fita ba wallahi zazzabi zazzabi nakeji a jikina."Tace."Ashsha! yana da kyau kasha magani." Yace."Yanzu idan na dawo daga massalaci zanci abinci nasha magani." Tace"Allah ya sawa'ke." Ameen yace ya fice daga gidan. Wasila kam bayan tayi sallah wani wankan ta sakeyi ta cancad'a kwalliyarta cikin kananun kaya, riga da sket ta gyara gashinta da mayuka sai sheki yake ta daure da katon ri bbon dankwalin abaya tayi rolling dashi, ta fito palo tana zabga kamshin turaranta mai dadi........Tana zama Hajja tace"Kinga kuwa mijinki bai da lafiya ashe bai fita yau kwata kwata yana daki a kwance sai yanzu da ya fito zai tafi massalaci yake min bayani." Ta danji gabanta ya fad'i kadan anya kuwa wannan rashin lafiyar ta gaskiya ce? maji ma magani dai." Abinda tafada kenan cikin zuciyarta.....Ya shigo palon gabakidaya jikinsa babu kwari ko ga yanayin tafiyarshi ma zaka fahinta har yayi nufi zama a gurin cin abincin sai kuma ya fasa ya nufi dakinsa. Hajja tace"A'a ya zaka shige kuma kaci abinci kasha magani dan Allah kada ka bari zazza'bin nan yay 'karfi a jikinka.....Ya dan Juyo yana kallon Hajjan dan ko da wasa baiyi kuskuran kallon Inda Wasila ke zaune dalili be san halin da zai shiga ba idan ya kalleta yace."Hajja bana jin zan iya zaman gurin nan Ke! Ki kawo min abincin daki." Yafad'a yana d'an hararar inda take zaune." Hajja tace"Allah y sawa'ke Wasila tashi maza ki kai masa abincin ki tsaya yaci sosai yasha magani." Wasila ta mike ta nufi dainnig bata da wata damuwa dan ta tabbatar da cewar cutar 'karya ce ya 'kir'kirarwa kansa. Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *80* Yana kwance rigingine idanunsa na kallon rufin dakin ta shiga dakin hannunta rike da karamin tire dauke da kayan abinci a kai, sallama tayi a nutse ta shiga dakin, ya amsa sallamar ba tare da ya kalleta ba, a hankali ta dan jawo wani karamin teble ta ajiye tire din abincin ta dan tsaya tana kallonshi, har yanzu guri guda yake kallo......Kamar za tayi magana kuma sai ta girgiza kanta a hankali ta juya zata tafi, Gyaran murya yay yana kokarin mikewa zaune yace."Dawo ki had'a min abincin." Ta dawo fuskarta babu wata cikakkiyar walwala....Kasan kafet ya sauka ya tankwashe kafafunsa, yana kallonta ta dan sunkuya tana hada mishi abincin Brest dinta duk sunyo waje tamkar ma batasa breziya ba, ajiyar zuciya ya sauke idanunsa kurrr akai yana shafa gemunsa, ta hada mishi abincin ta aje gabanshi, yace." dauko min ruwa me sanyi da lemo." Ta wuce can inda fridge yake nan ma ya bita da kallo, tana juyowa ya dauke kansa yana dan juya abincin da cokali da kyar ya kai loma guda bakinsa ya ajiye cokalin yana fad'an "Anya zan iya cin abincin nan zazzabin nan ya sanya bana jin dadin bakina." Ta lura magana yake nema da ita a takaice tace"Ka daure kaci kasha magani zakaji sassauci." Yace."Zan gwada ci yanzu." Ta ajiye masa lemon da ruwa ta kama hanya tayi ficewarta tana wata irin tafiya sassan jikinta na wani irin motsawa. Jingina jikinsa yay jikin katakon gadon ya langwabe kansa tare da lumshe idanunsa tamkar wani maraya yana sake jin wani irin feeling na taso masa. Da kyar ya iya cin loma biyar na abincin ya mike daga gurin Wayarsa ya dauka ya kirata lokacin suna palo suna hira, mamaki ne ya kamata ganin kiran wayarshi, Cikin wata 'yar iskar murya tayi mishi magana, ya sake shiga tashin hankali da damuwa, murya a sanyaye yace."Kizo ki kwashe kayan abincin." A hankali tace "To." Takashe wayar, minti biyu ta mike ta nufi dakin....Idanunsa tsaye a kofar shigowa so yake kawai ta shigo ya cigaba da kallon albarkatun jikinta masu rikirkitashi, ta shigo dakin, yabi fuskarta da kallo kamar tsohon maye, dan gyara bakinta tayi ta isa inda yake zaune ya wani mi'ke kafafunshi, abincin dake gabanshi ta kalla ta ganshi da yawa dan ko rabi be ciki ba.....A hankali tace"Ai baka ci abincin ba." Ya wani lumshe jajayen idanunsa ya budesu a kanta yace."Waye ya fad'a miki.!? Ta girgiza kanta da dan ya mutsa fuska tace."Ba kowa." Daga haka bata sake cewa komai ba dan ta lura neman shiri yake da ita ita kuma bata shirya ba tukkuna. Tana kokarin harhada kayan abincin yace."Idan zaki zauna ki bani a baki zanci kasala ce take damuna da rashin kwarin jiki shiyasa na kasa cin abincin." Tace."Allah ya sawa'ke!." Daga haka bata sake magana ba ta dauki tiren abincin ta futa daga dakin cikin zuciyarta tana fad'in "Nasan wayo kawai ka shirya idan waya da budurwa ne ai ba zakace kasala kake ba. Tana aje kayan abincin a cikin ta samu wani madaidaicin bokitin roba ta zuba ruwa me kyau, kaninfari ta zuba a cikin ruwan me d'an dama ta mayar ta rufe, sannan ta bud'e freezer mai dauke da kayan miya ta dauko wata madaidaiciyar kabewa ta feraye ta ta yanka dai dai misali ta zuba ruwa ta dora a wuta, tana tsaye ta dawu ta sauke ta samu ludayi ta murjeta tare da ruwanta, fridge ta bude ta sanya a ciki ta fita daga cikin din dai dai lokacin Rabe ya shigo domin ya fara aikinshi na abincin dare. ***** Camas da Silinda sabuwar yarinyar dasu As suka samu kenan wacce ta zama makwafin Wasila dan abinda Silinda takeyi wane Wasila, tunda Silinda tazo government house suke fad'a da Camas! dan ganin komeye za'ayi sai a turata gefe guda Silinda itace a kan gaba, ko yawonsu sukaje na campaign Idan sun dawo Silinda ake bawa kudi ita kuma ta bata abinda tayi niyya shiyasa kullum suke cikin fad'a da juna, Camas! ta kare mata dan duk 'yan kud'ad'en da take samu sun 'kare 'yan damfara sun damfareta kowa ya samu rabonsa yanzu motar kanta bata da ita manya sutturunta ta kwashe ta kaisu gurin mata na kasuwar rimi ta siyar a banza a wofi dan idan ba tayi shaye shayenta ba bata jin dadi, gashi governor kwata-kwata yanzu ya daina sakin kudi kamar da suma su As din lallabawa suke domi n governor Lawan Rabo ganin yanda jama'ar gari ke masa tawaye ta kowane fanni yasa yasha Jinin jikinsa yana ganin da wuya ya kai labari dan tuntuni ya sare da al'amarin saboda kusan kullum idan ya fita sai jama'ar gari sunyi masa ihu anyi fad'a da 'kona 'kone dan akwai wani matashi ma da yay kundumbala yayi tsale kan titi motar da yake ciki na gudu ya d'aneta sai da ya fasa gilashin motar da wata shar'bebiyar wukarsa wai sai ya kasheshi yayi masifar tsorata da al'amarin ya kuma fahimci cewar jama'ar jahar tashi a shirye suke da shirin ko ta kwana suna jiran lokacin za'be yazo yasan idan yace dole sai ya zarce to zasu iya halakashi, a take securities din da suke tare da governor din suka farwa wannan matashin da duka sai da sukayi masa jini da majina tukkuna suka daddaureshi suka kaishi suka kulle. Silinda ta kaiwa Camas! wani bahagon mari wanda ya sanya shatin hannunta suka fito rad'au! Camas ta rike kumatunta tana wani irin huci tace"Me nayi miki kika mareni."? Silinda ta hau cusa mata ashar tana fad'in "Waike wace irin dabbace shegiya kawai wane kudi kuma zan baki jiya da muka dawo ba na baki dubu goma ba shegiya kawai wacce babu abinda ta iya sai shaye shaye." Camas na 'kwallah tace"To ina ruwanki idan ina shaye shaye da kudinki nakeyi macuciya kawai tare fa muke tafiyar nan amma idan an bamu kudi mu raba sai dai ki bani abinda kikayi niyya jiya a gabana ina gani As ya baki dubu hamsin yace mu raba sai ki bani dubu goma saboda ke 'barauniya ce!." Silinda na cije baki tana hura katon hancinta tace"Wallahi Camas kika sake wata magana anan gurin sai na hanaki shigowa wannan gidan kin san dai yanda kusancina yake da governor zan iya tozartaki wallahi gwarama ki lallabani ki zauna lafiya kina gani duk taurin kai irin nasu kwage da Mada sun sallama min ballanta ke banza galli ga horo." Camas ta sha'ki hanci! tana jin wani irin takaici a ranta ta girgiza kanta ta wuce ta bar gurin tamkar kububuwa." Silinda taja tsaki tana tsartar da yawu ta wuce ta nufi inda motarta take tana karkad'a key. Ta fito daga cikin gidan ta hangi Camas na tafiya a 'kafa takalmin 'kafarta na gurd'eta, Dariya tayi hade da buga sitiyarin motarta tazo ta wuceta fuuuuuuuu! Camas! ta tsorata da sauri ta matsa gefe tana cizar yatsa(Hausawa na cewa idan zaka gina ramin mugunta to ka gina shi dai-dai da kai dan watarana kaine zaka fada ciki) ***** *Malam Mai allo* Yau kusan sati guda kenan yana irin mafarki guda daya, kawai sai ya yanke shawarar yin istahra domin yana so zuciyarsa ta amince masa da abinda yake gani cikin mafarkinsa, karfe daya na dare ya tashi ya daura alwalarshi a nutse ya gabantar da istahara kamar yanda annabi ya koya mana, ya nade dadduma ya koma ya kwanta bacci, cikin iko n Allah sai dai ya sake yin irin mafarkin da yake yi dai shi da ita wannan karon ma gashinan har da albarkar haihuwa dan yaro 'karami ya gani a tsakaninsu, zuciyarsa ta aminta da abinda Allah yake nuna masa cikin mafarkinsa tsayin sati guda, tabbas jikinshi na bashi alkari ne tartare da al'amarin, kawai sai ya yanke shawarar tunkarar inda take ya cire fargaba da shakku gami da tsoron kada tayi masa rashin kunya kamar yanda ta saba. *Allah ya tabbatar mana da Alkari* ****** Bayan ta idar da sallah isha'i ta nufi kicin, abinda ta ajiye a frdge ta dauko ta fasa madara gwangwani guda biyu ta juya kan damammiyar kabewar nan ta juya sosai ta hade jikinta sai ta zauna kan wata kujera a kicin din ta shiga sha a hankali a hankali tana lumshe idonta, za'ki za'kin kabewar da gard'in madarar na ratsata,( Macen dake yin irin wannan had'in tana sha to za tayi gard'i tayi za'ki sosai sannan gabanta zai ciko kuma zata dinga jin sha'awa a kai a kai zakiyi ni'ima wacce maigida zai dinga sakar miki ihu yana sa miki albarka) Sai da tasha sosai sannan ta mayar da ragowar fridge ta bud'e ji'ka'kken kaninfarin data ji'ka ta sanya cup madaidaici ta d'ebo ta xauna ta shanye tas ta ajiye Cup din ta fita daga kicin d'in. Tana 'kokarin shigewa bedroom dinta Hajja tace"Zo ki kar'beta ki bata nono tasha tin dazu take kusurkusur kin san idan ta fara tsandara ihu to ba zamuji da dad'i ba." Tace"Hajja da wanka nakeso nayi wallahi."Hajja tace"A'a kada a shiga hakkin yarinyar nan Wasila zo dai ki fara bata nono tasha." Sai ta zauna kusa da Hajjan tana fad'in "Gaskiya Hajja duk sanda kika tafi zanji jiki wallahi Allah yarinyar nan zata hanani komai da komai na rayuwa ita dai komai nono." Hajja tace"Aikuwa dai tafiya ta ta zama dole dan gobe i yanzu ina gida. Ta dan marairaice fuska tace"Yanzu Hajja da gaske dai gobe zaki tafi."? Tace"To me zan tsaya nayi gobe zan wuce insha Allah da safe zanje can gidana zanyi aikin wainar gero da za'ayi sadaka da ita, tunda Allah tasa kin yada ganye lafiya lau ai dole mugode Allah." Tace"Hajja meye amfanin yin sadakar.''? Hajja tace"Wasu na cewa al'adace amma ni yanda na dauki al'amarin ba al'ada bace dan kayi sadaka ranar da ka yada ganye hakan na nuna cewar kana farin ciki da abinda Allah yay maka kuma duk yaron da ka bawa sadaka yaji dadi zaice Allah ya raya ya d'ayyaba." Rashida dake danna wayar Wasila tace"Gaskiya kam ai sadaka maganin masifa ce ba laifi dan kayi sadaka lokacin da kake cikin farin ciki ko kuma ubangiji yay maka wata kyautar." Hajja tace"Ai kowane mutum da irin fahimtarshi wasu mutanan babu ruwansu da yin irin wad'annan abubuwan." Shigowarshi palon ce ta katse musu zance da suke, Hajja tayi mishi sannu da zuwa Rashida ma haka, ya amsa yana kokarin zama kujerar dake fuskantar Wasila, carbin dake hannunsa ya nannad'e a hannunshi Hajja tace."Jiki yay kyau kenan tunda gashi har ka iya zuwa massalaci.'' Yace."Alhamdullhi Hajja yanzu babu zazza'bin sosai sai dai ciwon kai kad'an kad'an! Tace"Allah ya sawa'ke." Amsawa yay da "ameen.' Yana mai da hankalinsa kan Wasila dake kokarin gyara rigarta tace" Hajja kinga bacci za tayi ma." Hajja tace"To ai sai a goyata dan yanzu tunda tayi bacci da wuri kika kwantar da ita to idan ta gaji da kwanciya zata hanaki bacci da daddare." Rashida tace"Kawo na goyata." Tana kokarin mika mata yarinyar yace."Bani ita nan." Ta mi'ka masa ya d'orata saman kad'arshi yana shafa bayanta......Hajja tace"Aikuwa ka sabawa da yarinyar nan da haka to zaka sha wuya dan idan taji dad'i to cewa za tayi ba zatayi bacci a ko ina ba sai a kirjinka." Yace."Hajja wannan goyon ne ni bana so sai naga kamar ana takure ta wallahi." Hajja tace."Babu maganar takurewa, da goyo na kisa da duk baku rayu ba, dan kai d'in nan da kake gani babu irin goyon da baka sha ba a bayana." Yace."Allah Sarki Hajja Ubangiji Allah y saka da alkairi ya kara miki nisan kwana." Ta amsa da "amee." Tana murmushi hade da tuno lokacin kuruciyarshi sai da ta share hawaye a fakaice data tuno mahaifiyarshi Yafindo mutuniyar kirki Allah dai ya jikan musulmi." Mikewa yay ya nufi bedroom din Wasilan da babyn a kafadarshi, shuru dakin sai Uban 'kamshin turaran wuta yakeyi Turaran Wuta ne dana tsuguno wanda Hafsa matar Khalifa ta kawo mata kwana uku da haihuwarta bata ta'ba amfani dashi ba sai yau, mafi akasari tafi anfani da air freeshnar da tirare na tsinke koda ta haihu da irinsu ta dinga amfani yau kawai tayi sha'awar sanya na gurin Hafsa tana sanya shi kuwa dakin ya game da 'kamshi mai dadin gaske, turare ne wanda yaji kayan hadi ya kuma ji madarar turare 'yar gasken had'e ruwan ji'ko turarene da manyan mata ke amfani dashi, shi na tsugono d'in nada bala'in kyau sosai yana sanya gaban mace ya tsuke! yayi ta masifaffan 'kamshi, Allah Allah take ta fito daga wanka domin ta tsuguna kan turaran domun Hafsa tayi mata bayani dallah dallah cewar idan ta tsuguna kan turaran sai ta goga miski a gurin idan tayi kwana uku tana yin haka ita kanta zataji sauyi sosai dan gurin zai nuna alamun tamkar ba'a ta'ba haihuwa ba. Tana fitowa kawai sai ta ganshi a zaune, gabanta ya fadi sosai gaskiya ita bata son haka to me kuma za tayi mishi da zai kama ya shigo mata daki......Ya dinga binta da kallo har ita isa gaban mirror towel din na 'bantarewa daga jikinta cinyoyinta na fitowa, rasa inda zai saka kansa yay sai kawai ya kwanta saman bed din hade da d'ora baby zahra saman cikinsa ya rintse idanunsa gam! yana sauke ajiyar zuciya yana jin yanda joystick dinshi ke wani irin harbawa......Ganin ya juya mata baya ya sanya tayi saurin saka dunkule d'aya na turaran a cikin wutar ta tsuguna akai haya'kin na ratsa jikinta, kusan minti biyar tayi a haka sannan ta mike da sauri ta gyara towel din jikinta wanda yay dai-dai da mikewarsa zaune yana kallon inda take, da sauri ta bude wardrobe ta dauki riga da wando na bacci ta saka a jikinta ta gyara gashinta sosai ta saka hula mai wani irin ado a gabanta, turare ta fesa sosai a jikinta, ta nufi bed din, Ta dan tsaya kansa, kamshin jikinta na fuzgarshi, kamar wani bugagge yake kallonta da lumsassun idanunsa, a hankali tace"Zan kwanta." Cigaba yay da kallonta ya kasa cewa komai." Ta sake maimaita maganarta nan ma be ce mata komai ba, sai kawai ta haye bed din tana dan turo bakinta, bargo taja ta rufe kafafunta dashi, Ya sauke ajiyar zuciya me zafin gaske, a hankali ya mi'ke ya fita daga dakin, ta'be bakinta tayi tace"Zaka gama salau! salau! d'in naka ka dawo ka bada kai, idan laifi ne ai bani kadai ce mai lefi har da kai dan haka duk sai mu taru mu bawa junanmu hakuri." Ta dauka, ba zai dawo dakin ba sai ta saki jikinta sosai bacci na kokarin daukarta taji alamun shigowarsa dakin yana kulle kofa, ta dan kalleshi ta ganshi cikin wasu pyjamas sky blue 'kirjinsa a waje dan be daure igiyar gaban rigar ba Tsigar jikinta ta mi'ke da sauri ta mai da idanunta ta rufe tana takure jikinta gabanta kuma na d'an fad'uwa kad'an! Ya jima kafin taji ya hayo bed din yana jan bargon jikinta......Sai kawai ta sakar mishi bargon dik ya janye ya rufe jikinsa dashi har da kanshi, shuru dakin yay na tsayin minti goma, ta bude idanunta a hankali sai taga dakin yay duhu, alamun ya kashe fitila, ta dan juyo a hankali tana kallonshi taga yanda ya wani takure jikinsa cikin bargo har da rufe kanshi, yau bai bada tazara mai tsayi ba a tsakaninsu, juyawa tayi a hankali ta dan dora hannunta kan babynta dake gabanta tana sauke ajiyar zuciya, Can wayarshi ta soma ringing, firgigit ta mi'ke zaune tana kallonsa ko zai tashi ya dauki wayar, taga ko motsi yaki yi, gashi sai kiran wayar ake. A hankali tace"Ana kiran wayarka." Shuru yay mata sai da ta sake magana tukkuna yace."Ki dauka ki kashe wayar wannan halin da nake ci yasa na manta ban kashe wayar ba." Murya a harhard'e yake magana." Ta dan rankwafa ta jikinsa ta dauki wayar tana dubawa taga Zeey ce. Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *81* Wani matsiyacin tsaki taja me karfi ganin sunan Zeey kan screen din wayar, tuni ranta yay wani mugun 'baci taji zuciyarta na wani irin tafarfasa tamkar zata tsaga kirjinta ta fito waje haka takeji, hannunta na karkarwa ta datse kiran tana kara jan wani tsaki!! idanunta har sun kada sunyi jawur ranta bai ta'ba 'baci ba irin yau! Wai me matar nan take nufi ne? Jin tana ta jan tsaki ya sanya ya bud'e fuskarshi yana kallonta,tana rike da wayar tashi a hannunta sai dubawa takeyi. Shuru yay mata dan shima jikinshi ya bashi Zeey din ce dama dai-dai wannan lokacin take kiran wayarsa shi abin ma mamaki yake bashi sam bata da zuciya ko kadan yana jin ko aure zaiyi ba zai aureta ba dan shi yafi son ya auri mace wacce tasan ciwon kanta ba me bibiyar maza da kanta ba. Zeey Sarkin 'yan naci aikuwa sai ta sake kira second guda bata 'kara ba ta d'aga wayar a fusace! murya a sama tace"Ke! mahaukaciya idan kina cin 'kasa to ki kiyayi ta shuri wallahi! saboda rashin kamun kai da iskanci da wulakanci zaki dinga kiran waya duk daran duniya kina damun mutane? wallahi to duk sanda kika sake kiran me wayar nan sai nazo har inda kike naci miki uwa! ni *Wasilatu 'Yar gaske!* na wuce da tunaninki bana d'aukar rainin hankali! idan auranki zaiyi yaje ya aureki ban hanaba amma kada ki kuskura na sake ganin kin kirashi a waya lokacin da yake cikin gidanshi, duk sanda kika kuskura kika sake kiran wayarsa a dai-dai wannan lokacin sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki wallahi."! A fusace! take maganar tana wani irin huci jikinta na kyarma tamkar wacce tasha tsumin 'yan bori sai faman hura hanci take.......Mi'kewa yay zaune da sauri yana 'kokarin fizge wayarsa, ta mike da sauri ta bar gurin tana cigaba da sauraran maganar da Zeey ke mata." "Ke har wata abace da zaki ce zaki dauki mataki akaina to mu zuba ni dake shege kafasa aure kuma nida governor kamar anyi an gama sai dai ki mutu dan babban mutum mai 'kima da mu'kami gami da mutunci bai cancanci! ya zama miji a gareki ba." A fusace! tace"Da Uwarki ya cancanta."! Zeey ta mike zaune da sauri tana mamaki! kafin ma ta dawo daga cikin mamakinta taji muryar Wasila na fad'in "Nace da Uwarki ya cancanta!? Shegiya dabba! wacce ta rasa mashinshini! tana bin mazan mutane a waje, zan nuna miki isa da mu'kamina a gurin shi wanda kike ganin ban isa na zama mata gareshi ba, zakiji da kyau wallahi zai za'ba a tsakaninmu ni ko ke! shashasha! mahaukaciya kawai."! Tana karashe maganarta ta kashe wayar tare da fashewa da wani irin kukan ba'kin ciki da takaici. Ya jima kanshi a 'kasa ransa yayi masifar 'baci! ashe dama yarinyar nan ba tayi hankali ba wannan ai shashanci da rashin hankali da zata tsaya tana gundume gudunmen ashar da wata ransa ya sake 'baci sosai da abinda tayi dan duk a ganinsa laifin ba na kowa bane nata ne tunda be ce ta daga waya ba cewa yay ta kashe masa waya.......A d'an kausashe yace." Kiyi min shuru kada ki tasar min da yarinya daga bacci."! Cikin 'kuluwa da tsabar bakin ciki ta kalleshi, tace"Sai me! idan ta tashi ai laifin ba na kowa bane naka ne ni wallahi tallahi nagaji nagaji! ana cutata kuma ace ba zanyi magana ba kawai ka za'ba ni ko wannan 'yar iskar mahaukaciyar matar dake kiranka a waya." Cikin tsananin bacin rai yace."Ranki zaiyi mutukar 'baci idan kika sake yi min irin wannan maganar kece zaki tsara min abinda nayi niyya idan nace Zeey na za'ba me Za kiyi.!? Aikuwa sai ta fusata sosai idanunta ya rufe shaf ta manta waye a gabanta ta dinga zazzaga masa rashin kunya da fad'in "To same? dan ka za'bi Zeey ka ajiyeni dama ai hausawa suna cewa duk wanda yaci moriyar ganga zai yada koranta dama ai nasan tuntuni bani kake so abinda ke jikina kake so, dan haka ko sakina ma kayi ni bazan damu ba dan nasan Allah yayi min baiwar da in na rabu da kai in auri wanda yafi ka komai da komai na rayuwa sai me? dama dole akayi min me zanyi da tsoho! (me saisayayyan kai Inji *Nafeest* Lol🤭) ta cigaba da cewa " ai dama kai d'in kwata kwata ba'asan aurena bane dama da Zeey din kafi dacewa." Kallonta yake wani irin gumi na tsiyaya a jikinsa, tunda yake ba'a ta'ba ci masa fuska irin y au ba, wannan yarinyar shi takewa rashin mutunci da d'ibar albarka? wai shin ma duk me ya jawo hakane? tambayar kansa da kansa yake da yaga bashi da amsa ga wani irin ciwo da kansa ke masa sai kawai ya mike zai fita daga d'akin! tayi gaggawar tarar gabanta tana kuka da fad'in "Sai ka sakeni tunda kace ka za'bi Zeey dani wallahi na gama zama da kai dama baka cancanta dani ba."! Cikin wani irin yanayi na tsananin damuwa da rud'ani! ya kifa mata mariku masu tsakanin shiga jiki, ta zube akasan dakin tana rirrike kafafunshi ihu! take sosai wanda ya tashi su Hajja daga bacci duk sukayo waje cikin tsananin tashin hankali da damuwa. Kafarsa yake janyewa tana sake ri'kewa duk tabi ta cikwiye masa a jikinsa Ga wani irin jiri da ciwon kai na nema su zautar dashi. Hajja ta dinga buga kofar d'akin tana fad'in " Innalilhi wa'ina ilaihi raji'un jama'a meke faruwa ne? Amadu Wasila ku bude kofar mana komai yayi tsanani maganinsa Allah." Jin muryar Hajja ya sanya Wasila tayi zumbur ta mike tsaye, saboda yanayin kwarin jikinsa har sai da ta tureshi ta bude kofa a guje ta fita daga dakin ta rungume Hajja tana wani irin kuka da shashsheka! "Hajja! nagaji da wannan zaman nagaji kullum sai ya dokeni ya sani kuka kullum cikin 'kuntata min yake baya kulani baya sakar min fuska nayi masa lefi na bashi hakuri yaki hakura, kullum sai muna kwance budurwa zata kirashi a waya suyi ta hira kuma a gabana bashi da lokacina ko magana nake masa baya saurarata, yanzu da bakinsa yace" Ya za'bi budurwarsa a kaina, dama nasan haka zata iya faruwa tunda dani da iyayena duk be dauke mu da mahimanci ba sabida muna talakawa, dama budurwarsa tace ni bancancani da na zama matarsa ba dan haka ni kawai ya sauwa'ke min na huta da wannan zaman."! Hajja tace"Subahanallahi Wasila daina irin wad'an nan maganganun sam basu dace ba, kiyi hakuri kinji ko ansan ba'a kyauta miki ba amma komai a sannu ake binsa dama ni tuntuni na fuskanci matsala a tartare daku dama kuma naso in zauna daku din gobe idan Allah ya kaimu kiyi hakuri kinji ko duk da kince anyi miki laifi amma ina so kiyi hakuri dan duk wacce kika gani a gidan mijinta hakuri takeyi, maganar saki ki daina yi tunda har Allah yasa kun fara haihuwa ke dashi ai babu maganar rabuwa shi kuma aure lokaci gareshi idan Allah ya 'kaddara mijinki zai 'kara wani auran babu wanda ya isa ya hanashi abinda kikeyi bai dace ba kin san bashi da lafiya amma a maimakon ki kwantar masa da hankali sai kuma tashin hankali haba Wasila." Hajja ta kare maganarta cikin damuwa da kuma tausasa harshe. Wani irin bala'in shaushin matar ya turnu'keta! hakan da tayi yana nuna mata cewar tana goyan bayansa kenan! A fusace! ta shige dakinta ta bugo kofar dakin da karfi!!!!! Hajja da rashida suka bita da kallo cikin mamaki, dama Amadu shi tuntuni ya shigewarsa dakinshi tsabar takaici bai tsaya ya saurari sharrin da take shirya masa gurin Hajja ba abinda bata sani ba kuwa Hajja ko kad'an bata son abinda zai 'bata masa rai! Wannan abinda tayi yay masifar 'batawa Rashida rai! bata ta'ba yin turrr! da halin 'yar uwartata ba sai yau, kamar ta fashe da kuka tace" Dan Allah Hajja kiyi hakuri."! Hajja tayi murmushi a hankali tace"Ai babu komai Rashida Wasila na cikin 'bacin rai a yanzu komai zata iyayi kishi ne ke damunta." Rashida ta girgiza kanta rai a 'bace! tace"To Hajja kishi hauka ne ni wallahi banji dad'in abinda takeyi ba." Hajja tayi hanyar daki tana fad'in" Rashida kenan wani idan kishinsa ya tashi mancewa yake da komai da kowa kada ki damu nayi mata uziri." Rashida ta girgiza kanta ta nufi dakin Wasilan.....Zaune ta tarar da ita had'a tagumi! hannu bibbiyu tana zubda hawaye duk ta wani firgice!. Rashida tace"Yanzu anti Wasila wannan abin da kikayi shine dai-dai? nifa dole na fada miki gaskiya saboda in kika kashe wannan auran ba kanki kawai kika cutar ba har damu! Ashe har kin manta da al'kawarin da kika d'aukawar su Mai allo, shin wai me mutumin nan yake miki? meye bai miki ba na jin dadin rayuwa? ina ruwanki da auransa! ya auri mata dubu mana kin san dai ba zaki ta'ba hana abinda Allah ya halasta ba, to duk wannan tashin hankalin da damuwa r da kikeyi na banza ne wallahi, wai har Hajja zaki zum'burawa baki ki buga mata kofa kawai saboda tana fad'a miki gaskiya meye laifinta dan tace ki bawa mijinki hakuri tana jin tsoro kada ki kwana cikin fushin Ubangiji duk macan da take furta kalmar saki ga mijinta Allah na fushi da ita! ni wallahi anti Wasila wani lokacin idan kina wani abun har mamaki kike bani." Murya na rawa rashida ta karashe maganar. Maganganun ne suka sanya ta dawo hayyacinta nutsuwa ta shigeta sai ta dinga tunanin abubuwan da suka faru ita dashi a baya, gabanta ya buga da mugun karfi! kada fa yayi zuciya ya kara sakina irin na baya! abinda ta ayyana kenan cikin ranta..... Ta goge hawayen fuskarta tana kallon babynta dake bacci, Rashin kunyar da tayi masa ta tuna, jikina yay sanyi duk taji tsoro ya shigeta tasan halinshi baya barin takwana idan anyi misho sai ya rama kuma ta lura ranshi ya baci sosai, tsoranta Allah tsoranta Annabi kada ya saketa da jego! gashi ta daukarwa su Mai allo alkawarin zama dashi har abada. Ta kalli rashida jiki duk a sanyaye tace"Rashida Wallahi raina ne ya 'baci shiyasa kuma nasan ko ke akewa irin haka ba zakiji dad'i ba, amma nima nagane ban kyautaba." Rashida tace"Nifa a ganina duk wannan abinda ke faruwa tsakaninku rashin bashi kulawa ne da tun farko da ya nemi agajinki kina agaza masa kina rarrashinsa da lallabashi da biya masa bukatunsa to da duk haka bata faru ba, wallahi laifin ba na kowa bane naki ne."! Murya na rawa tace"Rashida kema laifina kike gani ko."? Rashida tace" Wallahi laifinki ne kan me yasa ba zaki kwantarwa da mijinki hankali ba tunda dai kin san baida hakuri ta wannan 'bangaran." Hawaye ta goge murya na rawa tace"Kina so na mi'ka masa jikinta ya lalatani." Rashida tace"Nifa ba haka nace ba, kiyi masa dabaru ma ki biya masa bukata, kuma ni banga wani abu ba banda kin sanyawa ranki kinje asibiti an tabbatar miki da cewar gurin nan ya warke to kuma zaman me kikeyi ki bawa me hakki hakkinsa kawai kin tsaya wani abu wallahi kece mai babban laifi." Wasila tayi shuru tana sauraran 'kanwartata, tace"Naji shikkenan jeki dan Allah ni nagaji da wannan maganar na hakura idan na mika masa jikina ya fatattakani ya watsar dani shikkenan tunda haka kuke bukata." Rashida ta juya ta fita daga dakin ranta a 'bace! Wasila ta jima zaune tana sa'ke-sa'ke yanda za'ayi ta gyara kwa'bar da tayi dan jikinta yay bala'in mutuwa sosai tana jin tsoro kada gari ya waye ya shigo mata da takardar saki irin na farko........Jikinta a sanyaye ta dauki babynta ta nufi dakin nashi......A hankali ta tura kofar dakin ta shiga ta mai da kofa ta rufe, da haske kadan a dakin shima na karamar wayarshi ne ya kunna. Yana kwance cikin bargo zazzabin gaske ne ya rufeshi a d'azu dai zazzabi 'karya ya 'kir'kirarwa kansa amma yanzu tsabar tension d'in Wasila ya zuba masa zazzabi me zafin gaske. Jin zamanta kusa dashi ya sanya ya bude idanunsa da sukayi masa bala'in nauyi sunyi jawur yana haska fuskarta da hasken wayarshi Marairaice fuska takeyi tana kalato hawaye.....Ya 'bara rai mutuka yace"Tashi ki fitar min a d'aki." Hannunsa ta ri'ke murya na rawa jiki na rawa tace"Kayi hakuri."!!!!! Ya janye hannunsa yace."Kin shigo nan ma ki zageni ke ga mara kunya ko."? Girgiza kanta tayi tace"Ba haka bane wallahi nayi kuskure raina ne ya 'baci! dan Allah kayi hakuri bazan sake ba." Yace." Zaki hanani aure ne."? Shuru tayi gabanta na fad'uwa. Ya sake maimaita magabarshi, girgiza kanta tayi alamun a'a hawaye na sauka a kumatunta, yace."To cewa nayi ki d'aga waya ta ko kuma cewa nayi ki kashe."? "Cewa kayi na kashe." Yace." To me yasa kika d'aga min waya."? ''Babu komai." tafada tana dan matse hannunta da nashi dake game! Yace."Zeey ba sa'arki bace ta girmeki nesa ba kusa ba kuma da zan aureta da tun kafin na aureki na aureta bana son rashin arziki da rashin mutunci wallahi duk sanda wani ko wata ya sake kirana a waya kika d'auka kika zageshi sai na sa'ba miki kuma idan kikayi wasa sai nayi aure domin nagaji da wannan rashin hankalin naki." Hannunsa ta rungume a kirjinta tana shashshe'kar kuka tace"Dan Allah kayi hakuri na daina kada kayi min kishiya Allah bazan iya had'aka da ko wace mace ba ina sonka ina kishinka duk sanda naga kuna waya da Zeey ji nake kamar na mutu saboda bakin ciki da takaici." Yace."Kina yi min irin wannan d'abi'un zan zauna dake ke kad'ai ki sanja hali idan kina bukatar hakan." Tana sake matsowa jikinsa sosai tace"Na daina wallahi Yanzu kome kake bukata zanyi maka dama dan dai na haihu ne amma yanzu idan ka shirya nima a shirye nake.........Ya watsa mata wani irin kallo yace."Ban shirya ba tukkuna kije ki huta ba yanzu ba." Sai ta sake rungume hannunsa sosai a kirjinta tana marairace masa fuska....... _Namiji tamkar yaro 'karami yake duk ta inda kika tafiyar dashi zai tafi kuma ba zaki sha wuya dashi ba Namiji ba'ayi masa kutse! ba'ayi masa dole ba'a nuna masa iko idan kikace zakiyiwa mijinki wad'annan da'bi'un zakiyi masifar shan wahala.........Wasila itace babbar mai laifi dangane da wannan rikicin da sukeyi Team din Wasila Afuwa Amadu nada masifar sau'kin kai kuma yana son Wasila ni banga laifinsa ba idan ma yana da laifi bai ka nata ba, yanzu gashi lokaci 'kankani ta shawo kansa duk da rashin mutuncin da take masa amma tasirin son da yake mata ya hanashi daukar mataki a kanta ko yayi niyya ma baya iyawa saboda yana sonta dan haka Wasila kiyi kokarin ganin kin rike mijinki da kyau idan ba haka ba na kawo mishi santaleliyar mace wacce tafi ki komai da komai da kike ta'kama dashi🤭🤭_ Littafin na kudi ne....! Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262*alliya: 'Yr Bngr Sys *82* Yace."Me yasa a sanda na nema baki bani ba sai yanzu da naji kwata-kwata bana sha'awa, kawai kije ki kwanta duk sanda na keso zanyi miki magana." Taji kamar ya da'ba mata wu'ka a ma'koshi yau itace ke masa tayin yin sex da ita yana kaucewa lallai yayi fushi da ita sosai! Jikinta a sanyaye ta saki hannunsa ta juya masa baya tana goge hawaye, Shima juya bayansa yay saboda baya so ya tsananta gurin kallonta domin kada ta rinjayeshi dan ya lura da rigar baccin dake jikinta me futar da tsaraici ce yana so ya tabbatar da shin da gaske tuban da tayi na gaskiya ne ko na karya dan ya daina yi mata rawar jiki ballanta ta cigaba da raina masa hankali. Ganin ya juya mata baya yana jan bargon jikinsa ya sake sanyawa jikinta yin sanyi ta juyo tana kallonshi, wata zuciyar na bata shawara kawai tayi tafiyarta yayin da wata zuciyar ke cewa ki zauna dai ki cigaba da rarrashinsa kada kiyi fushi dashi. Sai ta dauke baby zahra dake kwance a gefensu ta kwantar da ita a gadonta tayi mata addua a hankali ta dawo gadon ta kwanta kusa dashi tana nani'karsa, cikin bargon ta shiga ta zura hannunta ta rungumeshi sosai a jikinta tana sauke ajiyar zuciya, Shima ajiyar zuciyar ya sauke yana dan sake takure jikinsa tsigar jikinsa na mikewa a hankali ya tura le'banshi na kasa a bakinshi yana dan cizawa shi kadai yasan abinda ke damunsa Hannunta ta zura cikin rigar baccinsa ta kwance madaurin ta soma shafa faffad'an 'kirjinsa tana sake goga jikinta a nasa, A dan fusace! ya juyo yana tureta yace."ba cewa nayi ki fita min a daki ba." Ta narkar da muryarta tana dan hura masa iskar bakinta a fuskarsa tace"Umm! Umm! ni anan zan kwana kuma ina bukatarka a kusa dani." Kamar ya kwada mata mari haka yaji wato tana so tasa shi yayi abinda baiyi niyya ba. Yace."Okey ni bari na baki dakin tunda bakyajin magana."Kokarin mikewa yake ta haye jikinsa tana danne kirjinsa wai ba zai tashi ba." Ji yay duk wani kuzari nasa ya kare dama ya yini cikin kasala da damuwa ga zazzabi sai kawai ya koma ya kwanta yana kallon ikon Allah. Faffad'an 'kirjinsa ta shiga shafawa tana d'an murza nipple dinsa tana dan ja a hankali a hankali! Ya saki wata iriyar hamma! wacce bai san sanda ta fito ba ya wani sake mi'kewa sosai kan bed din yana mi'ka! hakan da yayi sai ya sake tabbatar mata da cewar sa'konta na ratsa masa jiki A hankali ta soma lasar kirjinsa tana dan jan gashin kirjin da bakinta tare da tsotsar kan nononsa! A gigice ya dafe mazaunanta! ya rike sosai ya shiga matsawa yana sakin wani irin nishi, kafin kice kwabo jijiyaraa ta kumbura tayi fam! tana jinta a jikinta na harbinta. A gaggauce ta dam'ko wuyanta ya rankafo da ita jikinsa sosai ya kama bakinta cikin gigita da wani irin salo suka shiga tsotsar bakin junansu........Yanda suke sucking din junansu shi zai nuna maka da cewar lallai dukaninsu a bukace suke da junansu, duk sun wani gigice sai makale jikin jununsu suke suna sakin wani irin nufarfashi.....Sun jima cikin wannan yanayi kafin tayi dubarar zare bakinta ta dan gyara kafafunshi ta kwance igiyar dogon wandon dake jikinsa, ta zare wandon lokaci guda jijiyarsa tayi tsalle ta fito, ta sauke wata irin ajiyar zuciya tana lumshe idanunta tare da tand'ar baki, ji tayi wani irin ruwa na zuba a jikinta ganin joystick dinshi kawai ya sanya duk wata sha'awarta ta tashi, hannu biyu tasa kan joystick din ta shiga murzara a hankali a hankali tana shafa samanta ruwan dake fita a jiki na taimaka mata gurin wasa da ita. Allah Sarki Amadu wargajewa yay ya saki jikinsa sosai yana ta cije le'bansa, sosai yake jin dadin abinda take masa. Sanda ta soma shan joystick din kasa nutsuwa yay sai da ya bude idonsa ya kamo ta kamar mahaukaci ya yage rigar jikinta jikinsa sai kyarma yake yi ya soma mutsika nonowanta yana wani irin gurnani! Wasila tayi masa wasa sosai har sai da ta tabbatar da ya samu gamsuwa sannan ta saurara masa aikam tasha addua gami da sa mata albarka yanzu duk wani lefinta da yake gani ya gushe tunda ta dauke masa damuwar dake damunsa tsayin kwanaki masu tsayi. Tare sukayi wanka suka fito sai dai me? wani irin zazzabi ne me zafin gaske ya rufeshi wanda s ai da ta taimaka masa gurin saka kaya ta lallabashi yasha magani kana ta rungumeshi a jikinsa tana ji tamkar ta dawo da zazzabin jikinta Sai da bacci ya daukeshi sannan ta samu ta rintsa, aikuwa asuba nayi baby zahra ta tashesu, duk suka tashi a firgice shine yay gaggawar sakkowa daga bed din ya nufi gadon yarinyar yana dubata. ta saka hannunta a bakinta tana ta tsotsa da alamun abincinta take nema. Yace."Kizo ki dauketa ki bata nono tasha da alamu yunwa takeji." Ta cire bargon dake jikinta a hankali ta sakko daga bed din tazo ta dauki babyn shi kuma ya shiga toilet domin daura alwala. 'Karfe shida da rabi suna zaune a gurin karatu ita dashi suna dan hira sama sama koda rashida ta fito ta gansu haka sai ta shiga mamaki sosai! babu shakka duk wanda zai shiga tsakanin ma'aurata to kuwa watarana shine zaiji kunya......Hajja ma bayan sun gama karatun data fito ta gansu suna hira Wasila sai dariya takeyi sai ta shiga mamaki sosai, taji dadin hakan cikin ranta kuma dama tasan fadan nasu ba zaiyi tsayi ba tunda dukaninsu tasirin so na d'awainiya dasu. Wasila wata iriyar kunya ce ta lullu'beta ganin Hajjan yasa ta tuno rashin kirkin data yi mata dazu. Kai a kasa ta shiga gaishe daita, Hajja ta amsa fuskarta dauke da fara'a ta nuna kamar ma wani abu bai faru ba tace"Ina 'Kawata take."? Tace"Bacci take har yanzu bata tashi ba." Hajja tace"Ashe kuwa zan tafi bamu gaisa ba." Amadu yace."Haba Hajja da wuri haka." Tace."Ka manta da maganar da mukayi d'azu daka shigo gaisheni." Yace."Me zai hana anan ayi abun sadakar ko dole ne sai kin koma gida." Tace"Nafi so dai na koma gida nayi can kaga nan ko anyi babu makarantu da kuma 'yan 'kananun yaran da za'a bawa." Yace."Shikkenan Hajja Allah ya saka da alkairi. " Ta amsa da "ameen ya rabbi." Ta cigaba da cewa"Naji dadi sosai dana fito na ganku haka dan Allah ku dinga hakuri da junanku dama kwanaki naso na fahimci wani abu a tsakaninsu to sai banyi magana ba saboda nasan zaku iya shirya tsakaninku kamar dai yanzu dana dauka kamar abin zaiyi tsayi sai gashi har kun sasanta alhamdullhi dama haka akeso ku d'inke duk wata 'baraka da shaid'an zai samu gurbin zama a tsakaninku....Ke Wasila kece 'kasa dashi ke kanki kin tabbatar akwai tazara me tsayi a tsakaninku, a zamantakewar ku na lura dake kina da taurin kai wani lokacin dan Allah ki daina wannan d'abi'a domin ba hali ne mai kyau ba, duk abinda mijinki ya umarce ki dashi to kiyi kokari gurin ganin kinyi masa biyayya Ubangiji Allah ya cigaba da baku zaman lafiya gami da zuria mai albarka." Suka amsa da "ameen" Hajja ta kalleshi a nutse tace"Dan Allah tun da dai yarinyar nan tayi ar'bain to ka kaita taga 'yan uwanta 'bangaran uwa da uba wallahi mutanan suna da kawaici kuma suna da kirki sosai, ka dinga kokarin sadata da 'yan uwanta." Yace."Insha Allahu Hajja." To Hajja na karyawa Garba ya shigo ya dauki jakar kayanta, Wasila da rashida kamar suyi kuka saboda alhini ita kanta Hajjan jikinta duk yayi sanyi daurewa kawai takeyi tana fad'in "Ai zan dinga zuwa akai-akai ina dubaku." Amadu da kanshi ya kar'bi key d'in motar hannun Garba yaja domin kai Hajjan gida, su Wasila suka koma ciki da sa'bulallan jiki. Rashida kwanciya tayi kan kujera jikinta duk a sanyaye ita kuma Wasila cikin dakinta ta shiga tana goge hawaye, wanka ta shiga tayi ta fito ta shirya jikinta sosai tayi kwalliya cikin wani irin boyal me ruwan zuma d'inki irin buba akayi masa da wani uban sirfani a wuyan rigar da yaji stons sai sheki takeyi tayi amfani da gold dinta na fitar sunan Zahra ado taci tamkar wata amarya ta baza turarruka masu kamshi a jikinta, ta shirya Zahra suka fito palo, Rashida ta dinga kwarzanta kyawun da tayi tana fad'in kamata yay kafin kowa ya fara ganin kwalliyar nan Abban Zahra ne zai fara gani. Wasila ta wani d'ora ka'fa daya kan d'aya Rashida na daukarta a hoto da wayarta. Sai da sukayi pictures sama da ashirin wasu ita kadai wasu ita da Rashidan da baby zahra wani kuma ita da babynta sunyi kyau har sun gaji. Har wajen karfe hud'u da rabi na yamma bai dawo ba, tun bayan da ya tafi kai Hajja gida, kwalliyar da tayi duk ta tsufa! bayan ta idar da sal lah ta yanke shawarar kiransa a waya. Suna tare da Khalifa a guest house dinsa kiran wayarta ya shigo ba kasafai yake son amsa mata waya a ko'ina saboda tsaro dan ba Khalifan ne kawai a gurun ba su kusan hudu ne, sai kawai ya kashe wayar, Ranta taji ya 'baci jikinta yay sanyi tace"Kodai bai hakura bane? Whsap ta shiga dama numbarshi ce kadai da ita, tana dubashi sai ganshi a online! abinda bata sani ba shine Amadu datar sa sai tayi kwana da kwanaki a bude saboda ba sosai yake shiga whasap din ba ko ya shiga baya dadewa yake sauka, sai kawai ta shiga tuttura masa pictures dinsu ita da baby zahra tana gama turawa ta kashe datar ta mike ta fita daga dakin. Kicin ta nufa ta dauko had'inta na ni'ima cikin fridge ta zauna tana sha sai da tasha sosai ta mayar ta tsiyayi ruwan kaninfarin ta daya tsumu! har wani ja yayi tasha tana rinste ido saboda yaji da gafinsa da ya game mata baki, cup din ta ajiye ta fita daga kicin din. Ya d'an dauki wayar yana duba lokaci kawai yaga sa'kkoni na shigo masa ta whasap kuma da numbar ta, da sauri ya shiga yana dubawa, Pictures din yake kallon yana sakin murmushi gabakid'aya hankalinsa nakan hotonan wanda sukayi masifar kyau da dauke masa hankali.......Khalifa yace."Wai me kake dubawa cikin waya ne sai murmushi kake."? Alhaji Nura yace."Da'alama dai bazawararsa ce tayi masa text mai daukar hankali." Kashe wayar yay yana kallonsu da murmushi a fuskarsa yace."Ni zan koma gida dama kai Khalifa nace maka bana jin dadi dan jiya da zazzabi na yini na kwana, komai za'ayi ayi idan da yuwuwar A bawa Alhaji Munzali rance kud'in nan a bashi amma dai a tabbatar da cewar akwai shaidu sannan kuma kowa ya sanya hannu." Khalifa yace."Kafin ka tafi sai kasa hannu tunda kaina zaka bada kudin in yaso sai musa namu daga baya." A gaggauce ya 'karbi takardar ya saka hannu ya mika masa yana gyara babbar rigarsa ya mikawa Alhaji Nura Hannu yana fad'in "Alhaji Saduwar alkairi." Alhaji Nura yace."Mutumina da alama dai madam ce tayi kira irin wannan sauri haka." Khalifa na sane yace."Kasan yarinya 'karama ya aura shiyasa yake wannan rawar jikin." Alhaji Nura yasa dariya yana fad'in "Nima daf nake da na auri 'yar 'kankanuwar yarinya domun in more yanda ya kamata." Gabad'aya dariya suka saka, suna mi'kewa tare da yin musabaha ga junansu, suka sauka da bene kowanne yana baza babbar riga Garba yay gaggawar bude masa mota ya shiga ya zauna yana dagawa Khalifa hannu wanda shima ya shiga motarshi tare da direbansa, Kusan tare motocin suka fita daga gurin kafin ko wace mota ta dauki hanyarta. Cikin 'kananun kaya ta shirya jikinta ta matse sosai ta saki dogon gashinta ya kwanta a bayanta le'bunanta sun sha jan janbaki tayi kyau sosai Cike da wasa Rashida tace"Lallai yau anti Wasila amarci ake ci bari na koma daki kafin Abban Zahra ya shigo naji kunya." Wasila ta harareta tana kai mata duka, rashida ta kauce tana 'yar dariya tace"Ni wallahi wannan soyyayar taku mamaki take bani ayi fad'a a shirya humm! Murmushi tayi tace"Baby zahra a gurinki zata kwana yau tunda kin daure min gindi na mi'ka kaina gurin dadynta yau zamu kwana muna abu daya." Rashida tasa hannunta ta rufe bakinta tana dariya cike da kunyar yayar tata tace"A'a anti Wasila ni ban daure miki gindi ba dan Allah ki sassautawa Abban baby kada ya zauce! baby zahra kuma na amince zan rike miki ita har gari ya waye amma dan Allah ki sasaautawa abbanta." Wasila tasa dariya tace"Shi zaki fad'awa kice ya sassauta min amma bani ba." Rashida ta dinga dariya tana fad'in "Anti Wasila shifa salihi ne ke kam ai babu sauki! Allah ma yasa Zahra ta samu k'ani." Wasila ta kai mata duka tana 'bata rai tace"Ciki yanzu Allah ya kiyaye min rashida har yanzu ban manta wuyar dana shaba." Tana rufe bakinta ya shigo palon, idanunsu suka sarke guri guda wani irin kallo suke jifan junansu dashi. Rashida tayi masa barka da zuwa ya amsa yana me kauda idonsa daga kan Wasila, baby zahra ya kar'ba daga hannunta yana mata wasa. Cikin wata irin murya tace"Sannu da zuwa." Ya amsa da "Yawwa."! yana kokarin shiga dakinshi da baby zahra a hannunsa......Mi'kewa tay tabi bayanshi tana wata irin t afiya sasaan jikinta na wani irin rawa. Agogon hannunsa yake kokarin cirewa ta 'karasa da sauri tana karba tana cire masa, ya tsira mata ido bako kiftawa, murmushi tayi tace" Dazu nayi ta kiran wayarka baka dauka ba." Anutse yace."Ina tare da jama'a ne duk sanda kika kira waya kikaga ban daga ba ina wani uziri ne. Ta ajiye agogon kan drowar ta fara kokarin cire masa babbar rigar jikinsa, ta ajiye kan bed tana 'balle masa botiran rigar cikin, ya zauna da dogon wando da singlet a jikinsa, Tace."Ko na had'a maka ruwan wanka."? Yace."Bari naci abinci tukkuna." Tace."Tom bari na kawo maka." Juyawa tayi da niyyar futa daga dakin ya bita da kallo har ta fice ya sauke wawar ajiyar zuciya yana me lumshe idanuwansa. Da kanta ta bashi abincin yaci ya koshi tana masa hira sosai yake mamakinta, yana adduar Allah yasa zamansu ya dore a haka. Tun da ya gama cin abincin jikinsa ya mutu murus! bacci bacci wani irin feeling mara dadi ne yake taso masa, sai kawai yay kwance kan chanis carfet din dake gefan bed din, Ta shigo dakin taga yana kokarin yin bacci, zama tayi kusa dashi kamshin jikinta ya bugeshi, da sauri ya bude idonsa yana kallonta, hannunta ta dora a kirjinsa tace"Ko jikin ne ya dawo kada kayi bacci da yamma Annabi ya hana." Yaji kamar ya daure sai dai ya kasa! janyota yay ta fad'a saman 'kirjinsa ya rungumeta 'kam! yana sauke wata zazzafar ajiyar zuciya. Littafin na kudi ne...! Kika futar min da book keda Allah! kika karana baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE* *BINTA UMAR ABBALE*alliya: 'Yr Bngr Sys *83* Kwanciya tayi saman kirjinsa tana jin yanda yake shashshafa sassan jikinta yana sakar mata wasu zafafan kesses wanda ya sanya a take ita jikinta ya mutu ta langwabe a jikinsa tana so ta biye masa, gashi magariba ta gabato, sun jima a haka har sai da yaji ya dan samu sassauci a tare dashi kana ya cireta daga jikinsa ya mike ya nufi toilet domun daura alwala, Sai da yayi wanka sannan ya daura alwala ya fito har yanzu tana nan takure a kasan kafet, ya dan kalleta yana nazarinta ganin ta d'ago kanta sun hada ido ya sanya ya fahimci halin da take ciki, Yace."Lokacin sallah yayi ko bakyajin kiran sallah ne."? A sanyaye tace"Yanzu zan tashi nayi alwala." bai ce komai ba ya fita daga dakin. Ta jima zaune tana so ta dawo dai-dai abin ya faskara muguwar sha'awa ce ke damunta. Da kyar taje ta dauro alwala ta fito, ta tada sallah, tana idarwa, ta fita parlo lokacin Rabe har ya shirya musu daining Rashida na daki ita kadai kunyar zama take a palon gudun kada masu gidan suyi abin kunya a gabanta. Dakin ta shiga ta tarar da ita tana kallo da plate din abinci a gabanta tana ci. Tace"Rashida yau babu kallo kenan."? Rashida tace"Anti Wasila yau nan zan zauna nayi kallona ina kewar Hajja Wallahi da tuni muna tare. Wasila tace."Bake kadai ba nima kewarta nake! wallahi matar nada kirki......juyawa tayi da niyyar futa daga dakin Rashida tace"Sai da safe Anti Wasila." Tace"Allah ya tashemu lafiya." Amadu be shigo gidan ba sai bayan sallahr isha'i, lokacin tayi wanka ta sauya kaya wannan karon ma kananu ne wanda suka matse mata jiki gashi tayi amfani da turarrika masu kamshin gaske duk inda ta gifta kamshi ne ke tashi, Da kyar ya daure ya iya zaman cin abincin, a daddafe suka nufi bedroom ita dashi, duk sun d'okanta da junansu. wata iriyar rayuwa sukayi a ranar wacce ba zasu ta'ba mantawa da ita ba, sun mori kansu da kansu kuma dukaninsu sun biya wa junansu bukata, sukayi wanka tare kamar yanda suka saba kana suka kwanta rungume da junansu. Koda asuba tayi yaje masjid ya dawo sai da suka sake komawa ruwa basu saurarawa kansu ba sai da gari yay haske sosai san suka sarara sukayi wanka suka shirya tsaf! Wasila ta shirya babynta ya karbeta suka fito palo a tare sai wani kyallin goshi yakeyi....Rashida data gaji da zaman jiran fitowarsu gurin karatu sai kawai ta bar gurin ta koma kan kujera ta zauna tana duba wani littafin addini. Sai da ya ganta da littafi a hannu sannan ya tuna da karatu, suka gaisa a nutse yace."Yau bamuyi karatu ba ko."? dan mirmushi tayi tace"Ai baka jin dad'i." Yace."Lefin yayarki ne da bata tasheni a bacci ba." Wasila taji karshen maganarsa lokacin ta fito daga daki ta dan harareshi irin na soyyaya tace" Ni babu ruwana wane irin tashi ne ban maka ba mybe maganin daka sha ne ya sanya maka bacci." Da sauri yace."Nima nafi tunanin haka." Dainnig ta nufa ya bita da kallo cikin sha'awa shi dai ba zai ta'ba gajiya da ita ba a rayuwarsa, Rashida ta kar'be baby zahra dake hannunshi Shi kuma ya wuce dainig domin karyawa Ko a gurin break din ma sai da sukayi wassanin su iya son ransu sannan sukayi break din cike da farin ciki gami da annushuwa, da kwata kwata baiyi niyyar fita ba yaso ya zauna gida ya yini tare da iyalinsa to dole ne ya fita saboda akwai babban abinda zai sanya ya fita din, harda kuka da zai fita tana ta shagwaba da dire diren kafafu shi kuma sai biye mata yake yi, da kyar dai ta barshi ya fita daga gidan. **** Tsaf malam Mai allo ya shirya cikin manya kaya yayi wa matarsa Bitan sallama dama duk abinda ke faruwa ya shaida mata saboda ya yarda da ita da nutsuwarta Bitan macace mai hankali da sanin ya kamata, fatan alkairi tayi masa gami da dawowa gida lafiya. Mai allo bai sha wahala ba gurin zuwa gidan Kawu Madu dake Pataskum dan Wasila tayi masa kwance sosai kuma sai da ya tambayi Madu mai itace ya sake tabbatar da cewa shi d'in ba 'boyayye bane. Allah ya taimaka Kawu Madu nan bai fita ba yaro ya shiga gidan ya shaida masa yayi ba'ko......Kawu Madu na fitowa yaga fuska irin ta Yahuza me rasuwa. Yace."Hala dai kaine Yayan Yahuza mijin Uwani mahaifiyarsu Wasila ko." Mai allo ya washe baki nsa yana mi'ka masa sannu yace."E kwarai nine malam ashe ka shaida ni." Kawu yace."Haba malam ai duk wanda yaga fuskarka yasan kai dan uwan Yahuza ne ai kuna kama sosai. Mai allo yace." Masha Allah masha Allah! Kawu madu yace."Bisimillahi malam shigo ciki." Mai mai allo yace"Da mun zauna ma a zaure magana ce mai muhimanci nake tafe da ita. Kawu yace."To babu damuwa bari na dauko abun zama." Yay saurin shiga cikin gidan yana washe bakinsa, Mai allo ya shiga soron gidan ya tsaya yana jiran fitowarsa. Sai da suka sake gaisawa suka nutsu tukkuna kafin Mai allo yay gyaran murya yana fuskantar Kawun yace."Magana ce nake tafe da ita Malam Adamu ina fatan kuma zaka dauki maganar tawa da mahimanci." Kawu Yace."Ina sauraranka Malam Mai allo yace."Nazo nan ne da niyyar auran Uwani ina fatan amincewarka.". Kawu madu yace."Alhamdullhi! kai amma naji dad'i wannan magana da kake tafe da ita dama ko jiya sai da mukayi magana da ita dake nan d'in ma tana samun zawarawa sai nace to ta futar da miji tayi aure sai ta nuna min duk cikin zawarawan dake sonta babu wanda yay mata a cikinsu, amma jikina na bani kai ba zata watsa maka kasa a ido ba ko banza tasan "yayanta sun samu Uba nagartacce." Mai allo yace."Nayi istahara dangane da al'marin kuma alhmdullhi Jikina na bani akwai alkairi shiyasa nayi gaggawar zuwa domin na sameta mu tattauna kuma ku sani insha Allah gobe zanje in samu Kawunta na can kano idan mun tsaida magana da ita." Kawu Madu yace."Hakan yayi kyau malam babu shakka idan Al'amarin ya 'kullu ni zanfi kowa farin cikin hakan. Mikewa yay ya nufi cikin gidan yana fadin'"Bari na kira maka ita ku tattauna. Koda Kawu madu ya shaidawa Uwani zuwan Mai allo sai ta shiga mamaki sosai jikinta yay sanyi tun bataji abinda yake tafe dashi ba, hakika yanzu take nadama gami da dana sanin abinda ta dinga yi masa a baya. Ta dauki mayafi kalar atamfar dake jikinta ta yafa a jikinta ta fita zauran.....Cikin nutsuwa take masa barka da zuwa tana sunkuyar da kanta kasa, sosai Mai allo yayi mamakin nutsuwarta, zauran yay shuru na minti biyar kafin mai allo yay gyaran murya a hankali yace."Ina fatan Kawu Madu ya fada miki abinda yake tafe dani.'' Uwani ta dago kanta tana kallonsa, haiba da kwarjininsa ya sanya ta sunkuyar da kanta kasa a hankali tace"Bai fada min ba." Mai allo ya sakeyin gyaran murya a karo na biyu yace."Wata magana ce mai muhimanci nake tafe da ita ina fatan idan kikaji zaki aminci da ita.". Tace."Malam ka fad'i ko wace irin magana ce ina sauraranka." Mai allo yace."Nazo nan ne da bukatar auranki." Uwani gabanta ya yanke ya fadi sai ta kasa dago ido ta kalleshi. Mai allo yace."Nasan zakiyi mamaki ko? to ki sani ba'a mamaki da ikon ubangiji tabbas wannan auran namu akwai albarka a cikinsa a yanzu babu abinda nake bukata daga gareki sai amincewarki." Uwani ta jima kanta a kasa ta kasa cewa komai dan har Malam din ya cire tsammanin za tayi magana, sai kuma yaji tace"Babu komai malam na amince Ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkairi a ciki, sannan don Allah ka gafarce ni kan abubuwan dana dunga yi maka a baya. Mai allo yay murmushi farin ciki ya cika masa zuciya yace."Alhamdullhi Naji dadi sosai da kika aminci kai tsaye ba tare da mun kai ruwa rana ba, ni kuma nayi miki al'kawarin rike ki tsakani da Allah da manzon Allah dik wani abu da kikayi min a baya na yafe miki Allah ya yafe mana baki daya." Uwani ta amsa da ameen Yace."Sati biyu kacal nake so a daura aure ko ya kika ce."? Murmushi tayi cike da kunya gami da jin nauyinsa tace"To shikkenan Allah ya nuna mana." To kafin malam ya tafi sai da suka tsayar da magana shi da Kawu Madu kan cewa kafin cikar kwanakin da suka d'iba zai kawo sadaki da duk abinda ya sawwa'ka." Kawu Madu yace."Kada ka takura kanta malam kawai ka kawo sadaki a daura aure." Malam yace."A'a dole sai yayi mata suttura da sauran abubuwan amfani." Cike da girmama juna sukayi sallama Malam ya wuce ya tafi zuciyarsa wasai yana jin wani irin so da kaunar Uwanin na ratsa jikinsa. *** Masha Allah Addua bata bar komai ba kuma hausawa nacewa duk abinda hakuri bai baka ba to babu shakka rashinsa ba zai baka ba , alhmdullhi gidan Amadu yayi kyau komai na tafiya dai-dai dukaninsu sun kwantar da hankalinsu suna kula da junansu kamar zasu cinye kansu, mutukar na gida suna daki a kulle suna soyyaya baby Zahra kam har ta saba da Rashida in ba nono zata sha ba baka ganinta gurin Wasila, al'amarin Zeey kuwa tun ranar data kira waya ta haddasa musu rigima bata sake kira ba saboda sosai taji zafin zagin da Wasila tayi mata, tayi ta tsammanin ko Amadun zai kirata taji shuru bai kirata ba, nan ta gane ashe itace take haukanta dole tilas ta sanyawa zuciyarta dangana ta rubuta masa text wanda lokacin da ya karanta test din sai da ya tausaya mata so masifa ne, shi kam yana ganin ko ya aureta wuya zata sha ko bakin ciki ya kasheta dan ba zai iya kwantata da Wasila ba, kwata kwata yanzu babu wacce take gabansa sai Wasila da babynta. Yana tsaye tsakiyar daki yana fesa turare ta shigo dakin tana zum'bura bakinta, taki kallonsa ta wuce taje ta kwanta kan bed tana hawaye, tun jiya suke ta tafka rigima tana so taje su gaisa da Mai allo kana su wuce pataskum amma yayi biris da maganarta idan ta dameshi yace zasuje sai an kwana biyu har yanzu kwana biyun ba tayi ba. Ganin tana kuka sai yaji babu dadi yazo ya tsaya kanta yana tambayarta menene? cikin kuka da shagwaba tace"Lokacin da Hajja take nan naji tace maka ka dinga bari muna zuwa gaishe da mahaifanmu amma yanzu nayi nayi da kai ka'ki barinmu, ni wallahi gurinta zan kai 'kararka." Ya zauna gefan bed din yana dariya dan maganarta dariya ta bashi yace."Ke! ni zaki kai 'kara."? Tana goge fuska da turo baki tace"To ai kana jin maganarta watakila ita idan tayi maka magana ka amince." Ya sasauta fuskarsa yace."Ba hanaku zuwa nayi ba, kinga Rashida jarrabawa zasu fara ranar Monday kuma tare zakuyi keda ita shine dalilin da ya sanya na dakata tukkuna kuyi jarrabawar sai muje tare nima ai ina so mu gaisa da Malam d'in." Ajiyar zuciya ta sauke ta rike hannunsa tana shafawa tace"Shikkenan Allah muna gama jarrabawar nan ko kwana daya baza mu kara ba zamu tafi." Ya d'age mata gira yana dan kashe idonsa yace."Wai idan kin tafi ni ya zakiyi dani kin san dai kin saba min da abubuwa da yawa." dariya tayi mishi tace"Kayi zamanka ka huta dama ai wataran cewa kake na dameka." Yace."Ba wannan ba, kwana nawa zakiyi." Da hannunwanta tayi masa alama wai kwana ashirin zatayi." Yace."Bana jin zan bari ki kwana Madam muje mu dawo a rana daya......Rungumeshi tayi tana cikwikwiya masa shaddar jikinsa tana kuka tace."A'a wallahi ni kwana daya be isheni ba." Cikin mutuwar jiki da kasala ya cireta daga jikinsa yana duba jikinsa yace."Duba saboda sangarta nayi adona kin 'bata min jiki, ni dai na gama magana ba zaki kwana ba." Da gudu ta d'ane jikinsa tana kuka "Wallahi sai ka amince nayi sati daya." Abinda take fada kenan tana cusa fuskarta a kirjinsa. Jikinsa ne ya mace suka zube ita dashi kan bed din tayi kwance a saman kirjinsa tana masa dukan wasa sai kuka takeyi, rungumeta yay jikinsa na rawa ya shiga sumbatarta ta ko'ina... **** Cikin ikon Allah Wasila ta shige cikin 'yan mata 'yan ajinsu Rashida ta saje dasu ba zaka ta'ba cewa matar aure ce ba, kuma babu abinda ya gagareta gurin karatun dan dama kafin zuwan ranar jarrabawar yana dan koya mata wasu abubuwan dake kuma tana da saurin fahinta babu wani abu da shige mata duhu ko ya daga mata hankali sukayi jarrabawar fita daga secondary skull cikin narasarori masu yawa. ***** Ana ya gobe zasu tafi Garko Kawu Habibu ya kira wayar Amadu yake shaida masa halin da ake ciki, cewar malam mai allo zai daura aure ranar juma'a mai zuwa, kuma ba da kowa sai da mahaifiyar matarshi Uwani, Amadu yayi mamaki sosai da maganar Kawu Habibu daga karshe yayi addua gami da fatan alkairi ya kuma tabbatar wa da Kawu Habibun cewa insha Allahu suna tafe kafin zuwan ranar..........Kasa hakuri yay ya kirata a waya yace."Akwai albishir din da zan shigo miki dashi, amma meye tukwicina." Tana dariya tace"Ai kaima kasa ni." Yace."Nasan me? kawai ki fad'amin tukwicina." Tace."To zan barka kayi sau goma." Dariya ya 'kyal'kyale da ita yana sake rike wayar a hannunshi, yace."Kamar gaske ko? yarinyar daka amfara zaki hau ihu kina cewa na daina ke zafi kikeji." Ma'kale wayar tayi sosai ta wani lumshe ido tace"E mana ai kaine kakeyi da 'karfi shiyasa." Yace."To me yasa idan na bari ke kikeyi da 'karfin."? Kunya ce ta rufeta ta hau inda inda! Yace." Ai nagane wannan kukan da kikeyi na sharri ne dan dana bari ke kuma kikeyi da kanki kukan d'adi ne ko."? Sai ta soma shagwaba da sangarta tana fad'in "Ya bari ita bata so." Yana daiya yace."Na bari shikkenn idan na dawo gida bazan fada miki albishir din ba sai nayi sau goma kamar yanda kika fada kin amince." ? "Umm."! tace" Tana lumshe idonta wannan 'yar wayar da suke tasa gabakid'aya hankalinta ya tashi sha'awa duk ta taso mata...... Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys *84* Aikuwa da ya dawo gidan ta dameshi kan lallai sai ya fad'a mata albishir d'in shi kuwa yay ta ja mata rai, sai da suka gama komai na rayuwarsu sannan yake shaida mata abinda ke faruwa, farin ciki ya lulli'beta tamkar anyi mata albishir da gidan aljanna gaskiya taji dad'i sosai da wannan abu dama itama sam bata son zaman mahaifiyarta ta a haka tunda dai ba wuce auran tayi ba, koda Rashida ma taji labarin abinda ke faruwa tayi ta murna da farin ciki da 'kyar sukayi bacci a ranar saboda farin cikin da suke ciki. Gari na waye wa ta tashi da walwala da farin ciki sai shiri takeyi shi kam yana kwance yana kallonta kwata kwata baya son tayi nesa dashi dan dai bashi da yanda zaiyi ne kawai, ya shirya cikin manya kaya kamar dai yanda ya saba, duk ranshi babu dadi kawai dai yana kokarin daurewa ne amma duk da haka sai da fahimta to itama nata bangaran tasan tilas tayi kewarsa amma haka zata hakura dan gaskiya tana so taje ta gaisa da iyayenta sosai.....Kafin su tafi sai da ya fara kaisu gidan Hajja suka gaisa sosai Hajja tayi mamakin girman baby zahra yarinyar tayi wayo sosai sai kace wata 'yar wata biyar. Hajja ta ke'be da Wasila tace"Dama inata so inzo gidan naku Allah be nufa ba to tinda Allah ya kawoki sai ki tafi da ajiyar da nayi miki." Wani garin magani ne a cikin wani madaidaicin bokiti tace"Kullum ki dinga sha da madara ko nono daga can sakwatto nasa aka hada miki, ita kuma wannan zuma ce kada kiyi wasa da ita kullum kina shan murfi biyu safe da dare, idan kikaji dad'insu nasan da kanki idan sun kare zaki bukaci ayi miki wani." Wasila ta sunkuyar da kanta kunyar Hajja takeji sosai godiya tayi mata cike da kunya tana kara jin kaunar matar a cikin ranta. Hajja har mota ta rakosu tana fad'in "Su gaishe da mahaifiyar tasu insha Allah ranar daurin aure tare da ita za'azo."........Garba ne ke driving Rashida na kusa dashi da baby a hannunta....Ita dashi kuma suna bayan mota sai kalamai take mishi wai ya kwantar da hankalinsa insha Allahu sati guda kamar yau ce." Ya kalleta sosai yace."Ni nace miki sati guda zakiyi."? Ta kalleshi tana marairace fuska a langwabe tace"Hakafa kace dani shekaran jiya." Yace."Takura min kikayi shiyasa na fada miki haka, yau laraba ko."? Ta daga kanta tana kokarin mai da hawaye, yace."Zan iya daurewa kuyi kwana biyu shima dan dai babu yanda zanyi ne! Ranar juma'a idan na shigo daurin aure sai mu tafi." Murya na rawa tace"To baza muje pataskum din ba." Yace."Wane pataskum kuma Itama Momyn ai nan za'a kawo ta sai ku had'u kawai ku gaisa." Tace."Ai sai dare za'a kawota kuma lokacin nasan mun tafi." Yace."Ni zanyi magana da Malam d'in kancewa ana daura aure a tura mota a daukota ke Ni da kaina ma zan tura Garba ya daukota da sauran 'yan uwa sai ku gaisa da juna.' Shuru tayi masa domun ta fahimci duk dubarar da zatayi masa ba zai amince ba. Haka suka isa Garko kowa na jin damuwa cikin ranshi mussaman shi Uban gayyar da yake fargarbar dare yay yasan kuma shi da bacci sai dai yaga anayi. Amadu kafin ya tafi babu inda bai je sun gaisa ba cikin dangin Wasila yau kowa yaga mijin da take aure suka zama abun kallo a garin ba'yan uwansu kadai ba harda jama'ar gari fitowa suke suna kallonsu mussaman da wani matashin saurayi dake shiga kano sarin kaya ya gane fuskarshi sosai ya dinga watsawa mutane ai shine *Amadu Musa Ba.Iya.ka d'an takarar governor Kano* Aikuwa Jama'ar garin Garko tamkar an musu albishiri da gidan aljanna! suka fito kwantsinsu da kwarkwartasu suna ihu da fad'in "Allah ya baka mulki jahar kano fari mai farar anyi maliya mai ruwan 'kare kukanka." Ganin yanda Jama'a suka nuna masa 'kauna sukayi dafifi a jikin motarsa ya sanya ya koma cikin motar tashi ya bude wata ma'ajiya da yake aje kudi ya daukosu dami guda, ya wakilta mutane biyar yace."kowa a bashi abinda ya samu." Aikwa Jama'a sukayi layi suna ihu da 'kara yi masa kirari.....Wannan damar da ya samu ce ya sanya ya Umarci Garba da yayi maza maza yaja motar su bar gurin dan idan ba haka ba jama'a baza su bari ya tafi ba. Su Wasila na cikin gidan Malam mata dam'kam tamkar suyi mata sujjada ita abun ma mamaki yake bata sai wani bata girma ake kowa so yake yayi tozali da ita, wato tun mijin nata bai zama governor ba har sun soma kiranta da matar governor dariya kawai take musu itama ta fito da kudi daga jakarta ta shiga raba musu......Deluwa sarkin kanzagi tace"Hajiya Wasila ina fatan idan kun samu mulki a Hannuku baza ki manta da Kauyen Garko ba domin dai nan ne tushenki asalinki Karamar hukumar garko na bukatar hanyoyi masu kyau, na bukatar wuta da ruwa da kuma makarantu gami da asibitoci sannan muna bukatar tallafi domin mu inganta harkokin noma da sauransu." Wasila dukanin abinda Deluwa ta fad'a sai da ta rubuta a wayarta tace"Insha Allahu duk su kwantar da hankalinsu idan mijinta ya samu mulki a hannunsu Wannan karamar hukuma zata zama city za'a gyara sosai yanda kowa zaiyi sha'awarta. Sai bayan magariba suka samu sassaucin mutane a gidan, Bitan ta shigo dakin bayanta goye da zahra tace"Oh! ai shikkenan kuma gidan nan zai zama sansani na jama'a duba dai mutane sun kasa bari ki huta abincin ma sun hana kici cikin nutsuwa." Wasila tayi dariya tace"Bitan ai haka siyasa take dama zakiga mutum kwata kwata baida nutsuwa daga zarar na bar garin inace shikkenan kuma." Bitan tace"Aikuwa dai kuna kokari wallahi ga baiwar Allah nan itama an shiga hakkinta." Tafada tana kokarin kwance zahra daga bayanta. Tace"Ki bata nono tasha Rashida zata shigo muku da abinci."Yarinyar na ganin mamanta ta soma cilla kafafu tana b'angala dariya. Bitan tace"Ji ja'aira wai ta san uwarta." Wasila na dariya tace"Bitan wannan yarinyar wayo ne da ita ai." Bitan tay dariya tana kokarin fita daga dakin tace"Ai yaran yanzu dama da wayonsu ake haifarsu. Tana fita Inna Hajara ta shigo gidan tare da dan autanta da yake dauke da kwanukan abinci." Bitan tace"Yanzu Hajara sai da kika yi girki bayan komarwar ki gida." Hajara tace"Murhu biyu nayi shiyasa nayi sauri." Bitan tace"A gaskiya dai mana." Kicin ta nufa ita kuma Inna Hajara ta shige masaukin su Wasila. Wasila tace"Inna Hajara sannu bakya gajiya da zurga zurga koda yake babu nisa sosai ai.....Hajara ta zauna tana fad'in"Ke ni zurga zurgar da nakeyi kullum ai koda kudi aka hadaki ba zaki iya ba." Wasila tayi dariya tace"Ai kam wallahi bazan iya ba, tace"Inna hajara shine tun bayan tafiyarki baki sake zuwa ba ko." Inna hajara tace"Ke rabani da zuwa wannan gidan da ba'a bukatata a ciki." Wasila kamar tayi dariya sai dai ta daure tace"Haba Inna waye baya bukatarki." Tace"Rufe min baki kina so ki kare mijinki ko? bayan kin san shine ya koreni daga gidansa to me zai kaini ni ba kwad'ayayya bace." Wasila tasa dariya tace"Haba Inna yaushe zai koreki a gidansa Wallahi bakiji yanda yaji rashin dadi ba da ya dawo yaga bakya nan yayi ta fada wai nice nayi miki laifi shiyasa kika tafi." Tace"Oho! dai ni duk abinda nakeyi dominsa nakeyi da har zai dinga jin haushina dan nace ki gyara kanki ai shine zai mora shiyasa ai koda ki kayi ar'bain banyi gigin zuwa ba dan nasan dole zaki zo da kafafunki, in yaso sai nayi miki abinda nayi niyya ba don halinsa ba kome za'ayi ai shi za'ayi wa amma saboda tsabar rashin hakuri irin nasa yake ganin aibun mutune." Wasila tace"Dan Allah Inna kiyi hakuri magana ta wuce Yace a baki hakuri." Ta'be baki tayi tace."Uhmm! ni dama ai ba bakuwar zafi bace, Wannan kwanon da kike gani roman 'yan shilla ne mai had'e da maganin gyaran matantaka da kuma ni'ima ki cinye tas ki shanye roman duk wani abu da kika rasa gurin haihuwa idan kinsha wannan roman zai maye gurbinsa. Wasila tace"To shikkenan Innata nagode sosai babu shakka duk wanda ya rasa iyaye a duniya dole yayi kuka." murya na rawa ta 'kare maganar. Inna hajara tace"To meye abin kuka kuma mu dai kullum fatanmu ki zauna dakin mijinki lafiya kiyi masa biyyaya domin ki samu rabauta duniya da lahira, itama Rashida addua muke kan Allah ya kawo mata miji nagari kamar naki." Wasila tace"Ameen Inna insha Allah Rashida zatayi aure komai nada lokaci dama. Tace"Inna gaskiya bazan boye miki ba naji dadi sosai da faruwar wannan abu Kawuna Malam zai auri Uwani wallahi ji nake tamkar babu wanda ya kaini farin ciki da faruwar al'amarin. Inna Hajara tace" Shi al'amarin Ubangiji dama haka yake ai Allah ya kaddara akwai aure tsakanin Mahaifiyarki da Malam babu abunda zamuce sai dai muyi fatan alkairi shi kuma Yahuzu Allah ya jikansa ya gafarta masa." Tana goge hawaye ta karashe maganar, itama Wasila taji zuciyarta na kokarin karyewa tuno mahaifinta da tayi sai dai kawai ta daure ta cigaba da yi masa adduar samun rahamar Allah a cikin zuciyarta. Inna Hajara bata bar gidan Malam ba sai da ta tabbatar da Wasila ta shanye roman 'yan shillan nan sannan tayiwa Bitan Sallama ta tafi gidanta. Koda malam ma ya dawo suka ke'be suna sake gaisawa da tambayar bayan rabuwa Wasila tace"Malam ji nake kamar nafi kowa murna da farin cikin da kasantuwar wannan abu kai da Uwani Allah Ubangiji ya sanya alkairi a ciki." Mai allo ya dinga amsa cike da walwala da farin ciki, Yace."Hakan shine suttura da kuma mutumcin mahaifiyar taku." **** Sai bayan goma da rabi ya shiga gida a gajiye sosai dan bayan sun bar garin Garko can 'karamar hukumar *Gaya* suka Wuce shi da Khalifa da jama'arsu, sai yamma lis suka dawo saboda yasan masu gidan basa nan yasa ya yada zango guest house dinshi Khalifa ya zauna yana d'eba masa kewa Sai da Hafsa taga dare yayi mijinta bai dawo ba ta kirashi a waya, sannan ne suka rabu kowanne ya tafi gidanshi Yana sane ya'ki kiranta a waya sabida yana so yaga shin zata manta dashi ko a'a bini bini zai duba wayarshi babu text dinta babu kiran wayarta gashi sha biyu na dare har ta wuce........Allah sarki Wasila tana can network ya sakata a gaba tun bayan tafiyar Inna Hajara take ta kiran numbarshi tana 'kin shiga ko kuma data fara ringing sai ta katse har kuka tayi saboda bakin ciki kowa na kwance a daki cikin dare ta fito tsakar gida wai ko dakin ne babu network nan ma tayi tayi kiran baya tafiya, sai ta koma daki ta kwanta lamo tamkar mara lafiya bini bini ta duba wayarta ko zataga test dinshi shuru duk ta rasa abinda ke mata dadi da kyar bacci ya dauketa. To shima nashi 'bangaran hakane, da kyar bacci ya daukeshi wanda tun yana saka ran ganin test dinta ya cire ya rungume filo kamar wani maraya yana fizgo bacci da karfi, gabadaya gani yay dare yayi mishi tsayi, dan haka uku da rabi nayi ya tashi yaje ya dauro alwala ya hau dadduma yay nafila, kafin ta dauki cazbaha ya wuce masallaci. Da safe da kyar ta karya duk takaici ya isheta, ga mutane sai shigowa sukeyi wai sunzo gaisheta sai kawai ta koma daki ta kwanta tace da Rashida duk wanda yazo tace musu bacci takeyi. Haka kuwa Rashida ta dinga sallamarsu, da cewar bacci take wasu masu naci zama sukeyi wai sai ta tashi sun gaisa da ita Wasu kuwa sai suce bari su tafi sa dawo da yamma. Wasila na ciki tana ta famar kiran wayar tashi wannan karon tana shiga sai dai kuma bai daga ba, nan ma zuciyarta ta sake hasala ta goge hawaye tana mikewa zaune......Sake kiran wayar tayi a karo mara adadi dai-dai lokacin da ya fito daga toilet da alama wanka yay dan ga jikinsa nan duk ruwa, da sauri ya karasa inda wayar take ya dauka, ajiyar zuciya ya sauke ya zauna gefan bed kana ya daga wayar. Kuka ta fashe dashi harda shashsheka, yaji duk jikinsa yay sanyi gabakidaya a rayuwarsa ya tsani yaji tana kuka.... A tausashe yace."Menene."? Tace"Me yasa ka ki daukar waya zuciyata kamar zata fashe." Ya sauke ajiyar zuciya yana furzar da wani huci daga bakinsa, yace."Sai kuma kiyi kuka babu sallama da gaisuwa da tambayar yaya na kwana."? Tace."Duk hankalina ne a tashe wallahi zuciyata sai sa'ke sa'ke take min." Yace."Ina Mommyna." A hankali tace"Tana can gurin Bitan." Yace."Kun tafi kun barni da damuwa ko."? Tace."Wallahi nima da kyar nayi bacci ban san haka nake sonka ba sai da na kasa samunka a waya ji nake kamar nayi tsuntsuwa nazo inda kake." Yaji wani irin dadi na ziyartasa, yace."Nima haka naji na kuma gane kece mahad'in rayuwata." Dariya tayi tace"Nagode mijina, yanzu kayi break fast ko." Yace."Nakasa komai tunda na tashi kinga ni da kyar ma nayi wanka." Tace."Wayyo babyna da ina nan Wallahi ni zanyi maka wanka in rungumeka in shafa maka mai in saka maka kaya." Yayi wani killer smile kafin yace."Tunda ni baby ne idan kinyi min wanka kin shafa min mai kuma kin sa min kaya sai ki bani nono nasha ko." Ta saki dariya da shashsheka tace"Allah da ina kusa zan baka kasha." Yaji tsigar jikinsa ta tashi Yace."Mu bar wannan maganar kada kisa nazo inda kike yanzu." Ta 'kyal'kyale masa da dariya tace"Ai dama kaina ka fara maganar." Yace."Tom na daina maganar." ya cigaba da cewa yau zan tafi katsina amma kuma komai dare zan dawo insha Allah." Tace"Wayyo Habibi Katsina me zakaje kayi."? Yace."Zanje Gurin abokina mana mutumin da yazo dubaki lokutan da baki da lafiya." Jiki a sanyaye tace"To Allah ya tsare min kai ya dawo da kai lafiya." Ya amsa da "ameen." Yace."Kinga yanzu na dan samu sassauci zan iya cin abinci sabida kin bani kulawa duk da bakya gabana naji dadi sosai Allah yay miki albarka." A nutse tace"Ameen." Bari na bari ka nutsu kayi break sai na sake kiranka ko." Yace."Okey my Princess! Murmushi tayi ta kashe wayar tana fad'in "Nazama gimbiya kenan.....Cike da nishadi ta fito tsakar gidan gidan malam ta cigaba da hada hada da jama'a masu shigowa. Gangami!! da turnu'kun!! haya'ki!!! nake hangowa kan titin zuwa gidan gomnati wato government house, mutane sunfi dari biyu sun kashe titi sai 'kone -'kone sukeyi suna tada 'kura gami da 'kona tayoyi suna watsa fetur suna 'kyasta ashana, sai ihu sukeyi suna buga ganguna, guri ya hargitse da hayaniya gami da haya'kin! wuta, dan wasu ma har sun soma galabaita duk da sune suka saka kansu abunda sukeyi din basu sare ba so sukeyi su shiga cikin government house din domin su cimma manufarsu kan mai girma governor Lawan Rabo, mafi akasarin jama'ar da suka tada wannan tarzomar iri-iren wad'anda aka rusawa gidaje ne da masana'antu gurun aikin titin jirgin 'kasa wanda ko rabin aikin ba'ayi ba an dakata gashi su kuma anyi musu al'kawari za'a biya su diya shuru kakeji malam yaci shirwa kullum 'karya daban ta gobe daban sam basa gajiya da shiga gidan redio suyi karya, sukuwa suka ga rainin hankalin yay yawa kawai suka yanke wannan hukuncin duk da sun san wannan abun da sukeyi din xai iya barazana ga rayuwar wasu daga cikin amma dai duk da haka sukaji suka gani domin suna so su kwaci hakkinsu da'aka danne musu, Mai girma governor Lawan Rabo hankalinsa yay masifar tashi sosai ya lura Jama'ar Jahar kano suna so su ga karshen sa dan duk abinda ke faruwa a kan titin yana gani ta cikin CCTV Dan haka sai kawai ya umarci Securities kan suje suyi aman wuta da alburusai a gurun wanda kwanansa ya 'kare shi ya jawo kansa. Ba tare da 'bata lokaci ba kuwa, Police din gidan gomnatin suka shiga motocinsu suka durfafi kan titin suna sakin harbi ko ta ina! Littafin na kudi ne.....! Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE*alliya: *'YAR BANGAR SIYASA!!* *END🔚* *ALHAMDULILLAHI* *85* Gurin ne ya sake hargitsewa da hayaniya dalilin zuwan Securities din, kafin kice kwabo jama'ar da sukayi dafifi a kan titin sun soma gudu saboda gabakidaya harbin bindigar da Police din keyi yayi masifar razanasu, sai kowa ya soma kokarin ceton ransa, amma dai duk da haka sai da harbin ya samu wasu daga cikinsu suna kwance a gurin suna ihu jini tamkar yay magana kan titin yayi kaca kaca sai hayaki ne yake tashi a gurin gashi gari ya soma duhu magariba ta gabato.....Governor na ganin abinda ke faruwa ya kira d'aya daga cikin mutanan da ya tura yace."Maza a kwashi wa'inda suka jikkata akai su asibiti, Allah sarki mutum kusan bakwai sun mutu 'yan uwansu sai kuka suke suna d'ora hannu aka hade da tsinewa Lawan Rabo albarka suna tur da wannan mulki nashi....Amadu na katsina tare da Abokinshi Alh Muktari labari ya samesu dan sai da suka ga abinda ke faruwa a labarai, hankali a tashe sukayi sallama da abokinshi ya dauko hanyar dawowa gida.....Koda ya iso bai nufi gida ba kai tsaye gidan redio na *Salama* ya umarci Garba ya saukeshi, abinda bai ta'ba faruwa ba kenan wai ya shiga gidan redio dan ya yad'a manufarshi, Tashar redion Salama taji dad'i sosai da zuwanshi, kafin kice me sun fara sanarwa yanzu yanzu d'an takarar governor kano mai girma *Amadu Musa* zaiyi magana dangane da abubuwan dake faruwa a wannan jahar. Jama'a duk suka maida hankalinsu gurin sauraran jawabinsa.....Ya fara da bisimillah had'e da addua kamar yanda annabi ya koya mana kana yace." *Hak'ika banji dad'in wannan abunda ya faru ba a yau! hankalina ya tashi matuka! ganin yanda jama'a suka jikkata wasu har suka rasa ransu, Duk abinda wannan gomnati tayi muku bai kamata ku dauki irin wannan mataki ba, don yin hakan ba zai amfanar daku komai ba sai 'bacin rai gami da nadama da dana sani, na tabbata yau wasu daga cikinku suna nan cikin bakin ciki da damuwa rashin Iyaye da 'yan uwa mata na gida suna kuka saboda wannan tashin hankalin Wata mijinta ya mutu wata mijinta ya 'kone ko ya karya, duk saboda wannan hatsaniyar data afku, wannan abun da jama'ar wannan jaha sukayi bai dace ba shi wanda kukeyi dominsa din baza ku ganshi ba ballanta ku cimma burinku akansa, duk abinda hakuri bai baku ba rashin sa ba zai baku ba, kuyi hakuri ku barshi da Allah bisa ga zalintarku da yayi sannan kuma cigaba da yi mana addua kan Allah ya cika mana burinmu a cikin wannan tafiya, mutukar Ubangiji Allah ya dam'ka min mulki wannan jahar zan share muku hawaye zakuyi mamaki sannan dukanin wanda yay asarar gidanshi ko masana'antar sa wannan gomnatin insha Allahu Ni Amadu! na kar'bi wannan mulki nayi muku alkawarin biyanku hakkinku, wannan titin kuma da suka d'auko gadan! gadan! sunayi ni dama nasan ba iyawa zasuyi ba ku zuba musu ido, mu idan muzo namu salon daban yake da nasu, babu wani abu nasu da suka bari wanda zamu d'ora aikinmu akai komai sabo zamu 'kir'kira! babu algus babu almundahana a ciki, zamuyi mulki bisa amana da tsoron Allah Insha Allah! Daga karshe nake muku fatan alkairi al'ummar wannan jaha mai albarka ku cigaba da addua kan Allah ya kawo mana sauyi mafi alkairi sannan kuma na umarce ku da kada ku kara tada wata tarzoma, saboda yin hakan bashi ne mafita ba, mafita shine ku bamu had'in kai aranar za'be! kowa ya fito ya za'bi Jam'iyyar mu mai albarka tun daga sama har 'kasa, ku za'bi Jam'iyyar CPC Sa'a! Wasalamu alaikum."* Amadu na gama Jawabinsa gari ya dauka anata hayaniya kowa na fadar albarkacin bakinsa, haka can ma gidan gomnatin Governor Lawan Rabo da mataimakinsa da kuma mabiya bayansu hankalinsu yay bala'in tashi, governor Lawan Rabo ya dinga da ya sanin hukuncin da ya yanke na tura securities da yayi suka dinga harbi, yasan har duniya ta nad'e jama'a ba zasu ta'ba mantawa da zamaninsa, ba, aikuwa yana jikin wannan jimamin kiran mai girma shugaban 'kasa ya sameshi, lallai yau yake so ya nufi Abuja domin yana so ya zauna dashi. Lawan Rabo ya shiga rudani mutuka yayin da mataimakinsa yayi nasa guri dama shi d'an ba ruwa na ne tunda duk shawarar da zai bashi baya dauka yanzu data kwa'be masa sai y aje yaji da matsalarsa. As da sauran jama'arsa ne suka rakashi can fadar shugaban 'kasar. Duk da suna cikin karkara sai da labari ya samesu, dan Wasila har jawabin mijinta sai data saurara, hankalinta a tashe ta dinga kiran wayarshi domin taji lafiyarsa, wayar bata shiga da alama dai gidan Malam bai da network me kyau. Sai misalin goma shaura na dare ya shiga gidanshi, yay wanka ya fito palo wanda yay dai-dai da shigowar Khalifa suka zauna suna sake tattauna maganar.........A dai-dai lokacin ta sake gwada kiransa a waya a kaci sa'a wayar ta shiga, zazzafar ajiyar zuciya ta sauke tace"Habibi sannu da hanya ina fatan ka dawo lafiya." Yace."Na dawo lafiya lou har yanzu ban samu sukunin kiran wayarki ba." Tace."Nima tun dazu nake ta neman wayarka network yana hanawa, na saurari Jawabinka dazu kano babu lafiya ashe." Yace."Eh gashinan jama'a nata fama wai sai sun halaka governorn ku Lawan Rabo." Tace"Dan Allah daina cewa governor mu wallahi na tsaneshi mugu ne." Yace."A haba dai yanzu kin fita daga jam'iyyarsu kenan."? Kamar zatayi kuka tace"Ka bari bana so dan Allah." Ya dan shafa saisayayyar sumarshi yace."To na bari ina Mommyna." Tace"Tana goye a bayan Bitan." Yace."Wai ita wannan Bitan din bata gajiya da hidima ne."? Murmushi tayi tace."Mutuniyar kirki kenan." Yace."Ina kaunar matar sosai saboda tana kaunarki gashi yanzu tana gwadawa kan Mommyna." Mirmushi kawai tayi, yace."Kin san wani abu."? Girgiza kanta tayi tana lumshe ido yace."Gabad'ayansu Malam Kawu Habibu Inna Hajara Momynmu da ita Bitan! Dukaninsu zasuje Umara insha Allah sati biyu masu yawa." Wani irin farin ciki ne ya lullubeta kamar tayi masa ihu a wayar sai dai ta daure ta dinga zabga masa godiya da addua muryarta sai rawa takeyi......Yace."Babu komai ai dangina nayiwa meye abin godiya." Tace"Eh duk da haka nagode." Yace."Idan sun dawo zamuje namu umarar." Tace"Tom shikkenan yanzu kuwa zanje na fadawa Kawu wannan albishir din." Murmushi yay yace."Sai Allah ya kaimu gobe ko."? Tace"Tom Allah ya kawo ku lafiya." Kashe wayar yay yana murmushi, suka hada ido da Khalifa dake zaune ya zuba masa ido, hummm! Wai Amadu ne ke hirar soyayya wanda da idan ance zaiyi sai yace shi bashi da lokacin yin haka. Murmushi yay yace."Dama kana nan a zaune."? Khalifa ya murmushin takaici yana jan 'karamin tsaki yace."Ai baza ka gane ina gurin ko bana gurin ba tunda idanunka sun rufe." Ya dan shafa kanshi As'usel da murmushi a fuskarsa yace."Khalifa ina son yarinyar nan wallahi." Khalifa ya mike yana fad'in "Ai ba sai ka fada ba duk ga alamu nan sun nuna." Mikewa yay ya bashi hannu suka tafa suna dariya a tare suka fita daga palon. Wasila ta sanar da Malam alherin da Amadu yay musu, malam ya shiga tsananin farin ciki mara misaltuwa ya aika aka kira masa Kawu Habibu shima ya dawo gida saboda daurin auran ya tarasu ya shaida musu abinda ke faruwa, Inna Hajara ta dinga rangwada 'buda a gidan tana fad'in "Haihuwa mai rana Yau ni Hajara nice zanje wannan guri sai ta fashe da kuka tana fyatar hanci tace" Allah ya ji'kanka dan uwana insha Allahu kana aljannar furdausi, Bitan tace ta dinga rarrashinta da ta daina kuka domin yin hakan zai sanya su Wasilan hankalinsu ya tashi, da kyar Inna Hajara tayi shiru ta kama Wasila ta rungume a jikinta tana mata addua gami da hud'uba kan zamantakewar aure. **** Alhamdullhi an d'aura auran Uwani da malam a gidan Kawunta dake Tudun maliki, bayan daurin aurane sai suka kuma nufi can pataskum din domin gaisuwa sannan kuma da dauko amarya, malam sai washe baki yake yana baza babbar riga Shi kuwa Amadu kunya ce take kamashi wai daurin auran Uwar matarshi ake sai dai kawai ya girgiza kansa yana murmushi. Uwani tayi ado dai-dai gwargwado kuruciyarta ta sake fitowa tamkar bata haifi Wasila ba wani cewa zaiyi yayarsu ce anyi mata kitso da jan lalle tana sanye da sabuwar atamfa 'yar ingila jama'a sun cika gidan Kawu Madu sai hidima ake Kuluwa sai washe baki takeyi tana karbar baki, Kuluwa yanzu ta dan rage kazanta dan Kawu Madu ya soma dawowa hayyacinsa asirin da tayi masa ya karye dan da ya farga da irin kazantar da takeyi yace."Wallahi ta kuka da kanta idan ya tashi aure zai aure mace mai tsabta 'yar gayu tunda shi ba kazami bane." Aikuwa Kuluwa ta tsorata sai ta dage da wanka da wani had'e da kitso akai akai kuma garin Allah yana wayewa zata sa brush ta wanke bakinta tun yana futar da jini har ya daina, amma duk da wannan abun da takeyi Kawu Madu bai saduda ba yana nan da bazawarsa 'yar 'kwalisa har sun tsayar da ranar daurin auransu, Kuluwan bata sani ba sai dai jama'a da yawa sun sani shuru kawai akayi mata ana jiran ranar da amarya zata zo aga me zai faru. Amadu kasa shiga gidan yay sai ya zauna cikin motar.....Kunyar hada ido yake da mahaifiyar matar tashi, to itama Uwanin tunda taji jama'a nata surutu da amabatar sunan mijin 'yar tata sai ta kasa fitowa tsakar gida ta zauna cikin daki abinta Kawu Madu da kansa ya fita har bakin motar da yake ciki suka gaisa cikin mutuncin da karamci sannan fa mutane suka farga dashi sai suka dinga zuwa daya bayan daya suna gaisawa, ganin hakan kamar bai dace ba yasa ya fito daga motar yana gaisawa da jama'a cikin sakin fuska da dattako. Karfe shida sun iso gidan......Lokacin Rashida da Wasila sun saka turare mai kamshi a dakin mahaifiyar tasu wanda ya sha jere mai kyau kuma na zamani, katon gado ne da katifa mai kyau sai katuwar sif mai murfi shida akwatinanta akai sai mudubi da drowars guda biyu koran kafet ne malale a dakin labule koraye da net dinsu, dakin yayi kyau sosai. Su Kuluwa da Ina Tabawa da Ita mai waina suka rako Uwani dakinta Bitan ta karbesu hannu bibbiyu aka gaisa cikin mutunci da mutuntawa............Wasila bata samu sun ke'be da mahaifiyarta ba ya dinga kiranta a waya ta fito su tafi saboda dare ya soma yi....Uwani tace"Ki shige ku tafi daga baya sai ki dawo ina laifi ma da ya barki kikayi kwanaki biyu, Babu yanda ta iya haka tasa yara suka dauki jakar kayanta Rashida kam fujirewa tayi wai tunda babu makaranta ba zata bisu ba sai jarrabawarsu ta fito, Uwani kam bata ce mata komai ba itama zata fiso ta zauna a gabanta.....Wasila ta fito tana sallama da jama'ar dake gidan duk zuciyarta babu dad'i Inna hajara tasa yara suka fitar mata da kayayyakinta wajan motar......Ita Kuluwa fad'i take "Kice ina gaisheshi." Wasila ko kallonta batayi ba ta fice daga gidan, sukayi karo da malam zai shigo sai ta zube a kas tana kuka, Yace."meyasa kike kuka Wasila. Tace"Wallahi Kawu bana so na tafiya yau." Yace."Kiyi hakuri kibi umarin mijinki Allah yay miki albarka." Ta amsa da amin tana mikewa, Yace."Ina Rashidar."? Tace"Wai anan zata zauna sai sanda jarrabawarmu ta fito." Malam yace."Zancan banza zancen hofi! jirani anan na fito da ita."Ya shiga gidan yana baza babbar rigarsa, Rashida na dakin Uwani malam ya shiga gidan yana fadin"Ina Rashida. tace."Gani Kawu." Yace."Maza ki fito ku tafi ni bana son shashanci." Tace."Kawu Uwani ce tace."Na zauna." Sai ya daga labulen dakin yana fad'in "Uwani anya hukuncin nan yayi dai-dai kuwa."? Ta dago kai ta kalleshi tace" Malam ai ba cewa nayi ta zauna gabadaya ba idan jarrabawarsu ta fito zata tafi." Yace."To! to ai babu komai Allah ya kaimu." Labulan dakin ya saki Ya nufi dakin Bitan! lokacin ita kuma tana kicin tana ta kokarin raba abinci dan su Kuluwa suna nan basu tafi ba sai gobe tukkuna. Dama tuntuni Garba ya shigar mata da kayanta cikin motar daga ita sai baby zahra da jakarta ta nufi motar, wanda yana hangota ya bude motar yana kallonta har ta 'karaso ta shiga tana kumbura fuska, baice mata komai ba ya mayar da murfin motar ya rufe, Garba ya shiga da sauri yaja motar suka dauki hanya. Baby zahra ya kar'ba daga hannunta yana mata wasa sai kyalkyala dariya takeyi, Yace."Momyna nayi missing dinki da yawa amma na lura ke da momynki baku damu dani ba, kunyi ki'ba kunyi lafiya kwana biyu." Kallonsa tayi tana dan sassauta murya tace"Allah Habibi ka yanke min jin dadina ina tare da 'yan uwana kawai sai kace lallai sai mun tafi." Yace."Akwai wani jin dadi wanda ya wuce ace kina tare dani."? Shuru tayi masa tana gyara fuskarta, Yace."Ina Rashida."? A hankali tace"Wai ba zata dawoba sai jarrabawa ta fito." Yace."To karatun isilamiyyarmu fa." Ajiyar zuciya ta sauke tace."Ni na ma nta ma wallahi sabida bana cikin nutsuwa kuma dai Uwani ce tace dole sai ta zauna." Yace."To tunda Momy ce ta yanke wannan hukuncin bani da magana amma dai naso ta dawo yanzu domin mu had'a izifi talatin d'inmu da ita." Tace."Itace ta jawowa kanta, idan ta dawo na koya mata inda aka wuceta." Yace."To malama." Shuru motar tayi na minti biyar ya dan kalleta yana kashe ido yace."Wane tanadi kikayi min." ? A hankali yay maganar saboda Garba. Fari tayi da ido tace" Kabari muje zaka gani." Ya sauke ajiyar zuciya a hankali yana Allah Allah su sauka gida yayi masifar d'okanta da kasantuwa a tare da ita. A daran ranar sunyi soyayya sosai wacce ta sanya su zubar da hawaye dukaninsu suka tabbatar wa da kansu cewar idan babu d'ayansu a cikin rayuwarsu to babu shakka rayuwarsu tana cikin kalubale mai girma. Bayan dawowarta da kwana uku Hafsa ta haihu d'a namiji ta haifa A ranar data haihu sukaje ganin jinjiri Hafsa ta 'karewa Wasila tanadi sosai tace"Wallahi kinji kunya ace wai wannan zuwan da kikayi shine na farko gidana ai ina sane dake shiyasa nima bana zuwa inda kike koda yake laifin ba na kowa bane na governor ne gashinan ai yana jina. Amadu da yaga Hafsa ta fusata tana sakin maganganu sai ya fara kokarin kare kanshi da cewar shifa ba laifinsa bane nata tunda yana cewa suzo sai tace tana da uziri. Wasila ta dinga mamakinsa babba dashi da karya, Hafsa tace" Ai nasan kafad'a ne domun ka wanke kanka dama ina ciki da kai kaine ke hanata zuwa inda nake nagode. Sai ya shiga bata hakuri Wasilan na tayashi da kyar Hafsa ta sako ta basu jaririn suka dauka......Afnan ta samu abokinyar wasa, baby zahra ta makale jikin Wasila wai lallai sai ta bita su dinga wasa da babynta. Amadu yace."Kome zakiyu ba zamu tafi dake ba ki hanamu kwanciyar hankali....Khalifa na dariya yace"Afnan fa tayi wayo yanzu ta daina kuka.'' Yace."Kome zaka fada kan Afnan ba zan yarda ba ai ni yarinyar ta shani na warke...........Amadu da Khalifa suka fita sabida bakin dake zuwa, Cikinsu harda Zeey da sauran 'yan gidansu, Zeey tamkar ba gidan 'yar uwarta tazo ba ta kasa sakin jikinta duk dan ganin Wasila a gidan wani irin kunyar yarinyar takeji sosai sai yanzu ta gane cewar abinda tayi itama bata kyauta ba. Ana ya gobe suna wata 'kawar Hafsa tazo musu da lafiyayyan garin magani mai suna 'kare kukanka maganin na wahalar samu itama yayarta ce take can Ghana acan suke hadashi, maganin na kyau sosai sai dai tsada amma amfani daya zakayi dashi ka gane amfaninsa a jikinka, Wasila bata ji nauyin kud'insa ba ta dauki roba biyu dubu dari uku kenan duk roba daya dubu dari da hamsin....Tace zata bawa Hafsa kudin insha Allah. Ita yanzu mutukar magani ta tabbatar da kyansa da ingancinsa ko nawa ne zata iya sawa ta siya domin ta gyara kanta da mijinta. Saboda yawan 'Korafin da Matan Kawunsa Almu keyi masa na rashin zuwan Wasila gidansu ya sanya ya dauketa ya kaita gidan ta wuni tare dasu, sosai Wasila ta yaba da mutuncinsu gami da karamcinsu sun karbeta hannu biyu sun dauki Zahra sun rike wannan ya dauka wannan ya ajiye kamar zasu cinyeta wannan kadai ya sanya taji tana masifar kaunar su, basu tafi ba har sai da Kawu Almun ya dawo daga kasuwa suka gaisa ya dinga sa musu albarka gami da adduar samun zuria mai albarka, a gurguje sukaje gidan Hajja itama suka gaisheta, sai bayan goma na dare sannan suka koma gida. ******** *BAYAN SHEKARU HUDU* Abubuwa da yawa sun faru a cikin wad'annan shekarun da suka gabata masu dadi da marasa dad'i to masu dad'in dai sunfi yawa Inda Wasila da Rashida suka sauke al'kur'ani mai girma da sauran litattafan addini kana kuma suka samu gurbin karatu a jami'ar bayaro university Wasila na karantar harkokin kasuwanci wato business administration ita kuma Rashida tana so ta zama malam asibiti ne Wasila mijinta ne ya za'ba mata abinda yake so sai tabi ra'ayinsa domin a zauna lafiya, cikin shekara biyu da ta gabanta *Amadu Musa* Ya kar'bi mulki jahar kano daga hannun Lawan Rabo ya cigaba da tafiyar da mulki kan tsari babu cuta babu cutarwa yanzu al'ummar jahar kano hankalinsu ya kwanta basu da da wata fargaba tunda komai na rayuwa yay sauki! !!!! a jahar duk wani al'kawari da Amadu ya dauka ya sauke musu tare da taimakon mataimakin shi Sunusi Alhasan *Khalifa* Su Wasila ana gidan gomnati ana cin duniya sosai tayi wani uban kyau! da k'iba da kwarjini ta zama babbar mace, shekarun Zahra biyar, Wasila ta soma sha'awar haihuwa sai dai ta riga ta sanya inplan duk saboda karatunta wanda takeyin basaja, gurin shiga makarantar duk da ko bata rufe fuskarta da niqab ba babu wanda zaice ita matar governor ne sai dai kawai idan an duba yanayin fatar jikinta da hutu da kuma irin manya manyan motocin da ake kawota makarantar dan wataran ma harda securities suke tafiya, idan taga jama'a naso su fahimci wani abun sai kawai ta hana securities din binsu, tasa Rashida tajasu a mota. Senator Nura mai wakiltar kano ta tsakiya shine ya kwallafa ransa kan Rashida wanda tun tana janyewa har dai ta amince masa saboda ta lura da mutumin yana da kirki da mutunci kuma yana sonta tsakani da Allah, yanzu haka saura watanni Biyu daurin auransu. ***** Camas! Kuka wiwi takeyi gami da nadamar abinda ta shuka yanzu neman Wasila take ruwa a jallo ta nemi yafiyarta bata san yanzu ganin Wasila ma wani gagarimin aikine babba, kusan kullum sai taje government house din securities suka koreta dan babu wanda yake mata kallon mai hankali tana yawo da yaggagun kaya shaye shayen da ta dinga yi ya mai da ita shudu shudu! Ga mahaifinta ya dade da rasuwa, sai mahaifiyarta suke zaune a gida duniya gabakid'aya ta juya mata baya duk wanda suka buga harkar siyasa sun watse As da su Alhaji Ma'aruf suma takansu suke dan Amadu ya kama governor Lawan Rabo ya gar'kame! suma sai da yasa hukumar Efcc ta tuhumesu, duk wani satar kudi da sukayi da kadarorin da suka siya sai da suka fadi inda suke Amadu duk ya kwace komai yace kudi na talakawa ne......Dukaninsu da gidan da suke ciki suka dogara shima kawai ya bar musu ne albarkacin aure da Haihuwa. **** *BAYAN SHEKARU BIYU* Wasila ta kammala karatunta cikin nasarori da samun cigaba, a rayuwa yanzu Wasila tana da ilimin da zata iya gogayya da duk wani jinsin mutum ba'kar fata ko farar fata, tana jin turanci sosai dan watarana ma idan ba tayi ra'ayin yin hausawa ba da turanci take magana, a cikin shekaru biyun da suka gabata, akayi bikin auran Rashida ta tare a gidanta, Uwani kuma ta haifi tagwaye duk maza tare da malam mai allo, hakanan Hafsa ma ta sake haihuwa inda ya kasance tazararsu da kishiyarta Aysha babu yawa, dan tun bayan samun gomnatinsu Khalifa ya kara aure yanzu haka Khalifa nada yara hud'u inda Amadu keda 'Daya........Ganin ana barinsa a baya sai ya tashi hankalinsa, yace."Tunda an gama karatun aje a cire inplan d'in. To itama dama a dame take haihuwar take muradi, Rashida ce ta cire mata aikuwa aranar da aka cire yini tayi tana zubar da jini ga jikinta yay tayi mata ciwo, sai da ta kwanta jinyya na kwana biyu sannan ta dawo hayyancinta, Jini na daukewa Yallabai ya bud'e Wuta, kullum in bai fita ba yana aikin abu guda, Itama gwanar da yake kullum cikin gyara take bata damuwa, Cikin ikon Allah kuwa ciki ya bayyana a jikinta, sosai sukayi farin ciki ita dashi, ba tare da 'bata lokaci ba ya shirya musu tafiya zuwa 'kasa mai tsarki domin suje sununa farin cikinsu gurin Allah Subahanahu wata'alah!!! *ALHAMDULILLAHI* ```Jama'a nan na kawo 'karshen wannan littafi mai suna 'YAR BANGAR SIYASA! Ina ro'kon Ubangiji Allah ya yafe min zunubai na, Abinda na rubuta dai-dai Ubangiji Allah ka bani lada, abinda na rubuta na rashin dai-dai Allah ka yafe min👏🏻 Ku d'auki abinda yake da amfani ku watsar da mara amfani Nagode Jama'ata Allah ya 'kara kauna❤️ Sai mun sake saduwa daku a cikin sabon littafina mai suna``` *A KWAI WATA A 'KASA!!* ```Wannan littafin ba zance komai a kansa ba saboda ni nasan komai🤭amma kai/ke duk ina bukatar kusan meke 'kunshe cikin littafin! AKWAI WATA A 'KASA!! Kada ku sake a baku labari! yana nan zai zo bada jimawa ba.``` GA MASU BUKATAR PAID BOOKS 'DINA TO SAI KU TUNTU'BENI TA WANNAN NUMBARS D'IN. 👇🏻 *08089965176* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* LITTATAFAN MARUBUCIYAR: *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BAL