[9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷* _Bright pens of✍🏾_ Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya 1...... Saukar ruwan saman, bai hanashi tafiya da sauri a filin Headquarter, dake nan Abuja ba. Cikin izza, taƙama, da taurin zuciya irinta sojoji, yake taka ƙafafuwan nasa, ruwan na sauka da ƙarfi a jikinsa, da ka ganshi kaga ingarman namiji. Gaba ɗaya sansanin sojojin cike yake, da manya da ƙana nan sojoji. (Part of Nigerian Armed forces headquarters Abuja, Motto (s) victory is from God Alone!". Gaba ɗaya sojojin dake cikin Headquarter ɗin, basu damu da ruwan dake sauka kamar da bakin ƙwarya ba, wasu na tsaye, wasu na zaune wasu kuma suna abinda ya shafe su, wasu kuma suna in da babu ruwan suna shan Cigarettes (sigari). Tun yana tafiya da sauri har ya fara daidaita tafiyarsa ,wanda daman hakan al'adar sa ce, duk inda ya gilma cikin Headquarter ɗin hannu ake sara masa zuwa sama, alama dai shi ɗin Babban mutum ne, matsayi mai girma gareshi a cikin sojojin. Wani office ya nufa cike da nutsuwa, yana zuwa aka bashi hanya ya shige, yana shiga office ɗin ya ƙame!.. tare da ɗaga hannunsa sama alamar girmamawa da masu ɗamara kewa junansu.  Sojan da yake zaune sanye da kaaki, yayi Murmushi cikin sakin fuska yace "Have a seat.." yai Maganar yana nuna masa kujera. Kamar ba zai zauna ba, se kuma ya zauna saman Kujera. General Ibrahim A.M ya kalli matashin saurayin dake gabansa kafin yace "Munyi magana da Chief of Army staff, akan Operation da za'a fita, aiki ne mai wahala kuma bama son, Kidnappers ɗin su samu information na aikin nan, dan opretion ne me hatsarin gaske, yana da kyau ku kula, bamu da tabbaci kowa zai dawo da rai acikin ku, dan kun san komai dai" Matashin dai kansa yake a ƙasa, yana sauraren General babu alamar zai magana, ya tattara dukkan nutsuwarsa yana sauraren shugaban nasa. General Ibrahim ya buɗe wani file yana dubawa kafin ya kalli saurayin yace "Hope you are ready for it, and  kayi sallama da iyalanka?" . Sai a lokacin Matashin saurayin ya ɗaga idanunsa wanda sukai ja sosai ya kalli General Ibrahim, kallon da yake masa yasa General Ibrahim faɗin "Oh, I forgot  you just came back from Zamfara yesterday" Matashin dai bai ce komai ba, da Idanu kawai yake bin General. General Ibrahim yace "Zaka iya tafiya, jirgi na jiranku a airport, and airforce zasu rigaku zuwa ku kula da kyau akan dukkanin bayanan da zasu baku, da kuma umarnin da zaku samu daga garemu" Matashin saurayin ya miƙe tsaye yace "ok sir" tare da sake sara masa, sannan ya juya, yana tafiya a hankali har ya fice daga cikin office ɗin General Ibrahim. Cikin nutsuwa General Ibrahim ya ɗauki Wayarsa tare da danna wasu lambobi, babu jimawa aka ɗauki wayar daya kira, ƙasa ya yi da Murya yace "Akwai kyakykyawan labari" daga cikin wayar wata shaƙaƙƙiyar murya ta bayyana akace "Mene labarin?" General Ibrahim ya ce "Chief of Army staff, ya bada umarni ga Sojojin da suke Headquarter na nan Abuja zuwa Naija state, kai tsaye kuma cikin Dajin Zugurma in da kuke tsare da yaran nan, kuma a wannan karon sun samu cikakken ikon yin harbi,  umarni ne daga NAC. _Nigerian Army council_" Mutumin da General Ibrahim ya kira ya yi dariya kafin ya ce. "Ganganci haihuwa da damuna, a tunaninsu zasu Iya ƙwace ƴan matan da mukai  kidnapping ne? Bayan gwamnati ta hanamu abinda muka buƙata?" General Ibrahim yace "Na kira dai dan in sanar maka da zuwan su, a Kowane lokaci sojojin sama zasu tsinkayi dajin, nine zan tsara komai na Operation ɗin tare da jami'anmu na nan Naija state,  zan sanar maka da duk wani arrangement na yaƙin, kaga kuna da damar da zaku samu galaba a kansu, dan haka se ku shirya zuwansu"  Mutumin ya yi dariya yace "Daman ance da ɗan gari akanci gari, mune mutanan banza, kai kuma maci amanar ƙasa" General Ibrahim ya yi Murmushi yace "To Rayuwar sai da haka, in ba haka ba a banza za ka gama aiki Kai retire amma na abinci ya gagareka, ko a kashe ka a banza gurin kare ƙasar da ta gaza biyawa masu bata tsaro buƙatunsu, dan haka zan tura maka account number, ka bani share ɗina saboda na samu labarin wasu daga iyayen yaran sun baku kuɗi akan ku sakar musu yaransu" Mutumin  yace "Zanci kaza kazanka, a gidan uwar wa zanga pos ko Networkina cikin tsakiyar jeji?" Ibrahim yace "Haka ne, ka shirya min kuɗina  zan san yadda zan in karɓa, dan Ina da buƙatarsu" yana faɗin hakan ya kashe Wayarsa, yana jin akan kuɗi babu abinda ba zai ba. Tabbas da ɗan gari ake cin gari. Matashin na fitowa daga cikin office ɗin General ya nufi wani waje domin ɗakko jakarsa, tsaye ya yi ganin wata budurwa sanye da kayan sojoji ta nufu inda yake, hakan yasa ya ƙara haɗe ransa sosai. Budurwar mai suna Salima tace "Haba Captain at least yau kayi min Murmushi, saboda kai nabar Maiduguri nazo Abuja" Wanda aka kira da Captain ɗin, ya kalli Salima se kuma ya ɗauke kansa, Salima ta haɗe rai tace "Ban san me nayi maka ba, sama da shekaru biyar nake bibiyar ka, tun kafin kayi Aure" Captain ya gyara tsaiwa cikin tsare gira, murya a kaushashe yace "Bana harka da mutunan banza, ba zan mu'amala da karuwa kazar kowa ba" Yawo mai ɗaci Salima ta haɗiye tace "Yanzu har akwai mutumin kirki a cikin sojoji? Gashi nan kullum tara mata kuke, kuma mu matan dan mun nemi maza sai ya zama iftila'i, nifa a yau kace kana so na, zan zama iya taka kai ɗaya ban damu da matan da zakai harka dasu ba, indai zaka biya min tawa buƙatar" tsaki Captain yaja tare da ratsa wa ta gefenta ya shige.. duk inda ya gilma sai yaga mace da namiji manne da juna tare da sheƙe a yarsu, ko kunya babu.. Sanarwa aka fara yi, wanda ya Sanya Captain ɗaukan jakarsa, ya nufi filin wajan, Salima taso hadda ita za'ai posting zuwa Naija state. Farar safiya ce, A ranar  Asabar wanda yayi daidai ga 25 ga watan Mayu, shekara ta dubu biyu da goma sha ɗaya. Jirgin Sojoji ne (Helicopter). Yake shawagi a saman dajin Zugurma na jihar Naija state. Sosai jirgin yake zaga dajin ta sama, sautinsa ya cika ko ina a dajin, ya dinga bada wata irin amsa kuwwa. Ƙarfe 12 daidai, jirgin su Captain na sojoji ya sauka a filin tashi da saukar jirage na Niger state, cikin ƙanƙanin lokaci suka kammala duk wani shiri da za suyi, suka nufi cikin dajin.    Tafe suke a cikin manyan motocin yaƙi, ciki har da egwa yayin da wasu suke tafe a ƙasa, suna tafe suna 'yan iface ifacensu na sojoji, kafin samu umarnin cewar su tsaya su yada zango a wani guri, kasancewar sunyi tafiya me nisa, ba tare da jin wani ƙwaƙwaran motsi a dajin ba. Daga cikin ɗaya daga cikin motocin, Wani matashi ne zaune, a kujerar mazaunin direba, Zame abin kansa yayi a hankali,  yana fitowa daga cikin motar, Idanunsa akan wani matashi wanda yake gyara zaman bindigar sa, cikin rashin ko in kula na sojoji ya nemi waje ya zauna. Musulman cikin su na ƙoƙarin yin alwala suyi salla, wasu suna cin Abinci yayin da wasu suka keɓe suna shan sigari. Captain Denial ya buɗe jajayen idanunsa akan wani soja yace "Ka gama naka aikin, tun da ka kawo mu cikin wannan jejin" ya faɗa cikin harshen turanci.  ya shafa kansa yace "War is not mine" Captain Denial ya yi Murmushi yace "You go see" ma'ana zaka gani!. Duk sun sauka daga motar, se wani soja wanda tun da aka sauka cikin dajin bai ɗago kansa ba, balle yayi magana. Daniel ya kalleshi kafin yace "Captain Khamal" wanda aka kira da Captain Khamal ɗin, ya ɗago kansa a hankali, Baƙi ne shi sosai, irin baƙin nan mai kyau da kuma ɗaukan Idanu, ( _He's dark-skinned yet handsome_ ). Kana ganinsa kasan bashi da son wasa, zuciyarsa a tsaye take! Tsayyen mutum akan ra'ayinsa, fuskarsa nan tasa a ɗaure take koda yaushe. (But Friendly to his family). "Akwai matsala ne?" Captain ya Girgiza kansa, yana ƙoƙarin sanya rigarsa ta uniform ɗin soja. Ɗaya sojan ya nisa yace  "Wannan  yaƙi ne mai hatsari sosai, idan a kai nasara  zaka iya samun matsayi mai girma, saboda kana ƙoƙari sosai akan harkar tsaro ka san aiki sosai, akwai yiwuwar ka samu ƙarin matsayi me girma, amma naga kamar baka farin ciki?" Captain Khamal ya ware manyan idanunsa akan Jamil, cikin rashin damuwa yace "Ihu zan tayi ke nan? Saboda na fito yaƙi, za'a ƙaran girma? Ko mene?" Jamil ya ɗaga kafaɗa tare da watsa hannunsa yace "Kada ka gayan ba daɗi Malam, ƙilan masifa ka haɗawa kanka, rabonka da Matarka watanni wajan biyar kenan, dole ka rasa walwala ga matan nan birjik kawai ka rage zafi, gaba ɗaya duniyar nawa take daga kano sai Abuja fa, amma ka takure kanka kamar wani gunki" Taɓe baki Captain Khamal ya yi yana gyara zaman bindigar sa, ganin yayi masa banza yasa Jamil faɗin "I advise you, as you best friend, not as coulliqe". Captain yaja tsaki yace "Ko kaɗan, mahaukacin banza ba abunda kake tunani bane" Jamil ya ware idanunsa yana ƙoƙarin hana kansa dariya, ganin yadda Khamal ya hayyayaƙo masa, amma ya san tastuniyar gizo ba ta wuce ƙoƙi yace "Nine mahaukacin? Wallahi akwai wata yarinya tana zuwa gidana kullum, kawai zan bar baka ita, in mun koma Abuja" tsaki Khamal yaja yana yin waje yana faɗin "Dana aikata zina, gwara na mutu" yana faɗin hakan ya fita daga cikin motar. Jamil yabi bayansa da kallo yana Mamakin ƙarfin imani da haƙuri irin na Khamal, da yawan sojoji suna da hanyar ragewa kansu damuwa, amma banda Khamal da ya kasance me tsantseni. Captain babban matsayi ne a cikin sojoji. A rank in the military and maritime service, and the highest-ranking company officer. A Captain gets three vertically aligned silver stars on the shoulders. This is the highest rank among the tactical troop organization. Idan ka shige matakin Captain ka fara hawa babban matsayi  a Nigerian Army council (NAC). Captain Khamal yabi cikin dajin da kallo yana mamakin girman da yake dashi, ta ina zasu fara lalubar waɗan nan ƴan matan? Zasu koma gida duka da ransu ko yaya ne? Yana tsaye hannunsa zube cikin Aljihu gaba ɗaya jikinsa kayan yaƙi ne, Daga baya yaji an dafa shi da sauri ya juya yana zare Bindiga, Captain Denial yayi Murmushi yana busa hayaƙin sigari yace "Kai da kake a daji ai ba kai babu tsoro" Khamal dai ya taɓe baki yana jin warin Tabar na juya masa ciki, Denial ya ɗauki photo daga cikin aljihun Wandonsa ya miƙewa Captain Khamal photon yace "Ka ajjiye a wajanka" A hankali Captain yake bin photon da kallo ganin photon mace da kuma ƙaramar yarinya ɗauke a hannunta, cikin rashin fahimta yace. "me zan dashi?" Denial yace "Koda zan mutu a nan, ka bawa matata domin jikina yana bani ba kowa zai bar dajin nan da ransa ba a cikin mu, za'ai artabu duba da information ɗin da muka samu akan 'yan bindigar" Khamal kallon Denial kawai yake, ba tare da yace komai ba ya saka photon cikin aljihun Wandonsa. Tunda suka sauka cikin jejin basa jin motsin komai sai na kukan mugwayen dabbobi, A hankali Khamal ke tafiya yana zuwa wajan wata Bishiya ya yi saurin ɗauke kansa, saboda ganin Denial da yayi tsaye da wata Sojan mace suna murje jikin juna, ko tsoran a kawo musu hari basa yi. Ya bar gurin yana jin ɓacin rai akan abunda ya gani, ya koma in da sauran sojojin suke,  Jamil ne yace "Captain yanzu idan ka samu nasara shi kenan ka daina fita yaƙi?" Captain ya ɗaga kafaɗa alamar bai sani ba, waje suka nema suka zauna, suna kallon yadda ake ta haɗa kayan yaƙi da alama abokan harin nasu basu farga dasu a dajin ba, ko kuma suma duk cikin irin na su shirin ne ba wanda ya sani sai Allah. Jamil ya ɗauki Wayarsa zai vedio call da watsastsiyyar budurwarsa amma babu network gaba ɗaya cikin dajin, sai kawai ya ɗauki pen da paper ya fara Rubutu, yana tsaka da Rubutun suka fara jiyo ƙarar  bindigogi ta ko'ina. Garin sauri Jamil ya danƙawa Captain paper hannunsa. Kafin kace wani abu dajin ya ƙaraɗe da ƙarar Bindigu. Cikin azama suma zaratan sojojin suka fara maida martani, tare da fara sakin harsashi cikin ƙwarewa da dakiya irin ta aiki, kan kace kwabo amsa kuwwar sautin bindigogin ya karaɗe dajin gaba ɗaya. Sun kwashi dogon lokaci suna bata kashi, babu Sallah ga Musulmin cikin su babu abinci, hankalin duka sojojin a tashe ganin an fara kashe su ana neman aci galaba a kansu, ba tare sun kai ga in da 'yan mata suke ba. An raunata da dama daga cikin sojojin, bayan komai ya lafa nan likitocin cikinsu suka fara aikin ba su taimakon gaggawa. Cikin dare kowa ya ɓoye a inda yake, wayar Khamal ya fara haske da mamaki yake kallon wayar ganin screen ɗin wayar ya nuna sunan _My wife_ har zai katse sai ya tuna rabon da yayi waya da matarsa wata biyu kenan ciff. Bashi da tabbacin zai bar nan a raye, a nutse ya ɗaga kiran yana faɗin "Hey Beb..." Daga can Garin Kano matar Khamal mai suna Na'ima tace "Hankali na, yaƙi kwanciya Dear" shiru yayi mata saboda motsin da yaji a daf da in da yake, A hankali Na'ima tace "Nayi kewarka tare da Babynka dake cikina, gaba ɗaya hankalina a tashe yake, ga bana samunka a waya, bana son wani abu ya sameka" idanunsa ya lumshe cikin ƙasa da murya yace "I miss you, ki kula, ina aiki ne yanzu" yana faɗin haka ya kashe wayar baki ɗaya. A hankali ya fara tafiya a ƙasa, yana jan cikinsa a ƙasa zuwa inda yake hango mutum a kwance, mamaki ya kama shi ganin wata matashiyar yarinya kwance cikin jini se numfarfashi take, duk an yage suturar jikimta, da alamar fyaɗe akai mata, ba mutum ɗaya bama, saboda yanayin da take yafi ƙarfin ace mutum ɗaya ne yai mata. Yarinyar ta kama hannun Khamal ta riƙe sosai muryarta na rawa, ganin ta kasa magana gashi se rirriƙeshi take yasa Khamal ya ɗora kunnansa a bakinta, A hankali yarinyar tace "Ya...Ya... Yaaya" sai kuma tai shiru numfashinta na fisga da ƙarfi, tana ƙanƙame hannun Khamal tace "Basu da imani, basu da tausayi, kada ka barsu Yaya, kada ka barsu Yayaaa in ba kuyi sauri ba sauran ma haka za suyi musu, fyaɗe suke mana" ta ƙarasa maganar tana shaƙuwa. A kiɗime Khamal ya shiga girgiza yarinyar amma ina tuni rai yayi halinsa, wani irin numfashi ya fara fitarwa jikinsa ya ɗauki rawa, yana da tabbaci tana ɗaya daga cikin ƴan matan da aka sace, runste idanunsa yayi a hankali ya rufe mata Idanunta tare da jan zanin jikinta ya rufeta, har yanzu tana riƙe da hannunsa, wani irin baƙin ciki yana ratsa zuciyarsa, ace a ƙasarka amma ranka da mutuncinka ba a bakin komai yake ba, kai mutuwar wulaƙanci irin wannan saboda son zuciyar wasu tsirarun mutane. Cikin dare Khamal ya dinga bincikar dajin, yana zagawa da map ɗin da ke hannunsa, da yake akwai hasken farin wata. A haka Khamal ya gano suna daf da in da yaran suke, saboda hayaniyar da ya dinga jin tana tasowa nesa kaɗan da in da yake, dan haka cikin ƙwarewa irin ta aiki Khamal da jama'arsa suka ƙarasa in da suke, Nan da nan suma suka farga, suka fara musayar wuta, wasu daga ciki ga yara a hannunsa,wasu kuma jikinsu duk jini alamar ba'a jima dayi musu fyaɗe ba. Yaran suna a matuƙar galabaice. A daren su Captain basu iya bacci ba, duk yawan bataliyar nan ta sojojin, an kashe da dama daga cikinsu, an illata wasu, a daren suka kama wasu daga cikin 'yan ta'addan yayin da wasu daga cikin su suka samu nasarar tserewa zuwa cikin dajin. Sanyin safiyar yasa Captain Miƙewa yana tafiya a hankali, suka tattare 'yan matan guri guda, duk sun galabaita saboda wahala, wasunsu ba su da lafiya wasu babu suturar kirki a jikinsu, nan sojojin suka fara yiwa 'yan matan jagora dan fitar da su daga cikin sarƙaƙiyar dajin, yayin da wasu sojojin ke ta kwaso gawarwakin'yan uwansu da aka kashe. "Khamal" aka kira sunansa, da sauri ya juya ganin Jamil kwance cikin jini, anyi masa harbi kusan guda uku, jikinsa na rawa yace "Jamil" Jamil ya girgiza kai yace "Khamal ina maka fatan tsira da ranka, kaje wajan matata kace ta yafe min, wlh ban san adadin ƴan matan da nayi mu'amala dasu ba, yanzu haka ina ɗauke da Hiv, ina da tabbacin matata ma tana dashi, bata san hawa ba bata san sauka ba, na ɗora mata mugun ciwo" Khamal ya Girgiza kansa yace "Kayi salati" Khamal ya fara salati Jamil yana maimaita wa, a nan jikin Khamal Ubangiji ya ɗauki ran Jamil.... Kwanan su wajan uku, cikin dajin gaba ɗaya kuma sun kwashe ƴan matan an fita da su, a kwanaki ukun nan, kullum se sunyi musayar wuta da 'yan bindiga. sojojin duk sun ƙare, se wanda ba'a rasa ba, da gudu Major yake tafiya ganin wata budurwa yashe a ƙasa, kafin ya Ƙarasa wajanta yaji ance "Kaiiii" Aka daka masa tsawa da karfi, Juyawa yayi ya ware idanunsa ganin wani riƙe da bindiga zai harbeshi, Denial ya tare harbin hakan yasa aka harbi Denial a ƙirji... Captain ya zaro bindiga ya fara Harbin ɗan ta'addan , sai daya kashe shi sannan ya nufi wajan Denial yace "Mene yasa haka Denial?" Denial ya girgiza kai yace "Kai na musamman ne, gwara na mutu kai ka rayu, bana faɗa maka ba? Daman nasan mutuwa zan, kada ka manta da abinda na baka, a cikin mu akwai maciya amanar ƙasa, amma kai da gaske kake naka aikin, Khamal na baka amanar iyali na.. zaka iya, nasan zaka iya ka kula dasu" Yana faɗin hakan rai yayi halinsa, wani irin ihu Khamal ya saki mene yasa haka ke faruwa? Su sojoji a haka rayuwarsu zata ƙare ne? Sunyi shiri na gaske akan faɗan nan, amma kamar 'yan ta'addan sun san da zuwansuz duk sun samu nasarar kashe zaratan sojoji masu ƙoƙari, ciki har da makusantan abokansa, Miƙewa ya yi, gaba ɗaya jikinsa jini ne kayansa duk sun yage, ga yunwa, ƙishirwa. Yana zaune a ƙasa yaji shawagen Helicopter, da alamar General ne ya ƙaraso,yasan ɗauki gaggawa aka kawo musu, kasa Miƙewa yayi har sai da wani soja yazo wajansa ya ɗaga sa, yana faɗin "Komai yazo ƙarshe Captain" Sauran gawarwakin aka kwashe zuwa cikin wata babbar motar sojoji, raguwar 'yan ta'addan da sojojin suka kama suka ɗaure, suma aka zuba su cikin mota, suma sauran mutanen da suka tsitstsinto anyi garkuwa da su, a wata mota aka zuba su, Khamal ya miƙe ya na tafiya a hankali, kamar daga sama kunnansa ya fara jiyo masa kukan ƙaramin yaro,  tsaye yayi, yai shiruu, jin kamar ba kuka bane yasa ya cigaba da tafiya.  yana ƙoƙarin sanya ƙafarsa cikin mota, ya ƙara jiyo sautin kuka, a wannan karon kuma ya tabbatar gaskiya kunnansa ya jiyo masa, kuka ne da gaske, fasa hawa motar yai, sauran sojojin na kiransa amma be kula ba, a hankali yake tafiya jiki a sanyaye da ƙyar yake ɗaga ƙafarsa saboda wahala, ganin baiga kowa ba sai ya fara tunanin ko aljanu ne? Ko kuma kukan wata dabbar ce, wani kukan ya sake jiyowa da sauri ya juya zuwa inda yake jin kukan, ya ƙara nausawa cikin dajin, ware idanunsa yayi kan ƙaramar yarinyar dake zaune a ƙasa ta ƙanƙame jikinta waje guda, Idanunta rufe da alama gaba ɗaya a firgice take, Khamal ya ware idanunsa akan yarinyar gaba ɗaya ba zata shige shekara uku ba (3Years) fara ce sosai kamar buzuwa kamar kuma Balarabiya, tafi kama da ruwa biyu (Half-caste) domin gashinta wanda yafi ƙarfin kanta ya sauka har ƙasa kasancewar a zaune take, farar fatar jikinta tayi baƙi sosai, ga raunuka a jikinta.. Sosai Khamal ya girgiza da ganin ƙaramar yarinya a cikin jejin nan, sai ya fara tunanin ko dai Aljana ce?ko a cikin matan da akai kidnapping take, Samun kansa ya yi da cewa "Ke" shiru tayi masa sai kukanta take tana ƙanƙame jikinta, cikin rashin sanin cewa yarinyar nada ƙarancin ji a kunnanta yasa Khamal ƙara cewa "Kee" nan ma tayi masa shiru. "kada ka kuskura ka ɗauki yarinyar nan, ita ba kidnapping ɗinta mukai ba, ita tamu ce, rainonta za muyi, 'yar mu ce" Cewar wani mutum da ke tsaye, hannunsa riƙe da bindiga. Captain Khamal ya kalli mutumin sai kuma ya kalli Yarinyar, kana yaja baya kaɗan yace "To me zan da ita tun da taku ce?" Ya faɗa yana Juyawa, mutumin ya sunkuya zai ɗauki yarinyar kenan yaji saukar bullet a bayansa, ihu ya saki yana faɗuwa ƙasa, cikin zafin zuciya Khamal ya fisgo Yarinyar yace "Keeee...." Sai a lokacin taji saukar muryarsa a kunnanta, fararen idanunta ta ɗaga, wanda yasa zuciyar Khamal bugawa, Yarinyar ta washe bakinta ta nufi wajan Captain Khamal tace "Abbi..." Ta faɗi hakan tana ƙanƙame ƙafafuwan Khamal, “Abbi?” Khamal ya maimaita a zuciyarsa a fili kuma sunkuyawa yayi ya ɗauki yarinyar a kafaɗarsa, kai tsaye ya nufi in da motocin su suke da ita yana ƙoƙarin shiga cikin mota yaji saukar wani abu mai kama da kibiya ko mashi a gefen cikinsa, a hankali kuma yaji zafin  saukar abu a jikinsa tsananin azaba yasa sam bai kawo cewa harbinsa akai ba, ƙafarsa ya ɗaga da ƙyar yana sauke Yarinyar muryarsa na rawa yace "Shiga ciki" watsa hannunta tayi tace "Abbi" alamar bata gane zan can nasa ba, da hannunsa yayi mata alamar ta shiga cikin motar, sauran sojojin na ciki basu san meke faruwa ba, bayan ta shiga cikin motar Khamal ya ɗaga ƙafarsa da ƙyar zai shiga cikin Motar ya ƙara jin saukar wani harbin a gefen cikinsa... 😂😁 Ya kuka ji salon Bright pens?..... Daban ne... Share share share as so much as you can!. #Nimcyluv #Zee kumurya #Ayushercool [9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA HUDU ✷* _Bright pens of✍🏾_ Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya Ƙirƙirarren labari me, ba mu yi shi dan cin zarafin wani ko wata ba, idan yai kamanceceniya da rayuwar wani ko wata Arashi ne. Littafin DARE DA DUHU haƙƙin mallakar mu ne, bamu yar da a juya shi ta kowace siga ba, ko a sashi a wata kafa ba ba tare da izinin mu ba. BISMILLAHIRAHMANIRAHIM ELEGANT ONLINE WRITER'S P2..... Jin sautin harbin da ya sake tashi ne, ya sa yarinyar fitowa daga cikin Motar da sauri ta tsaya tana kallon Captain. Jini ne ya shiga zuba a gadon bayansa, ga na cikinsa da yake zuba shi ma, cike da jarumta irin ta soja yake ƙoƙarin tsayuwa kan ƙafafunsa, ya kuma ƙoƙarin ya yunƙura ya ɗaga ƙafarsa, sai dai yaji jikinsa yai masa nauyi, ga wani danshi da yake ji ya jiƙa masa kaya, sai a lokacin ya fuskanci harbi ne, a nan take duhu ya maye gurbin hasken ranar da ya haska dajin a idon Captain, a hankali yai baya ji kake timm ya faɗi ƙasa.    Sam ba ta san me ya faru da mutumin ba, wanda ya karɓo ta a hannun waɗan nan mutanen, sai dai ta zuba masa manya manyan idanunta, sai jujjuya ƙwayar idanunta take a kansa. Sautin Wani harbin ne ya kuma tashi, cikin azama wani soja ya fito daga cikin Motar, ya danƙi yarinyar ya kwantar da ita flat a ƙasa, ya shiga danna nakiyar ta sa bindigar shima a saitin in da ƙarar harbin ke tasowa.   Sautin Command ɗin Commander Land army ya jiyo nesa kaɗan da in da suke, yana bawa tawagar sojojin umarni, cikin dakakkiyar muryarsa dake amsa kuwwa a dajin, tare da ƙarar motocin sojojin na yaƙi, hakan ya tabbatar masa, da an turo wasu sojojin domin kawo musu ɗauki. Nan da nan ƙarar harbi ya sake cika dajin, tamkar za'a tsaga dajin. Tai lamoo a ƙasa, duk wannan ba ta kashin, da ƙarar bindigogin da ke tashi, can ƙasa ƙasa take jiyo sautin kaɗan kaɗan a cikin kunnenta. Gaba ɗaya hankalinta yana kan mutumin nan da ya ɗakko ta, da yake kwance a ƙasa, ba ya ko motsi. Ba tare da tunanin komai ba, ta miƙe zata nufi in da yake ƙasa a kwance, sojan nan da ya kwantar da ita flat a ƙasa, ya fizgota cikin tsawa yace "Lay down before they shoot you" shiru tai tana son gane me yake cewa. Ya sake kwantar da ita a ƙasa, hellcopter nan kuwa tuni ya tashi ya fara shawagi a sama, suna communicating da sojojin dake ƙasa. An kwashi kusan awanni biyu ana wannan musayar wuta a tsakanin 'yan ta'addan da kuma sojojin, wanda a ƙarshe Allah ya bawa sojojin nasarar fatattakar maharan, suka kashe na kashewa. Sai bayan da ƙura ta lafa, sannan Lieutenant Faruk ya migirna a hankali, saboda harbin shima da akayi masa a dantsensa. Cikin jarumta ya miƙe tsaye, sai dai jiri ne ke ɗibar sa, saboda jini da yake zubarwa a dantsen nasa, yana tashi ita ma yarinyar ta tashi tsaye, sannu a hankali ya ƙarasa in da Captain yake kwance a sume cikin jini, ya durƙusa ya ɗago shi, tare da kara kunnensa a saitin zuciyarsa, can ƙasa ƙasa yaji bugun zuciyarsa alamar yana da rai. Bin su kawai take da ido, tana sake zura kai tana kallon Captain da idanunsa ke rufe. Tawagar sojojin da suka shigo dajin kawo musu ɗauki ne suka fara ɓullowa, suna ta tattara gawarwakin 'yan uwansu, da wanda a kaiwa rauni. Cikin hanzari suka ƙaraso in da su Captain suke. Lieutenant Faruk na zaune rungume da Captain a jikinsa, Chief Commander yace "Are you ok?" Faruk yace "Yes sir, but Captain K Buba needs first aid, he is seriously bleeding" "Is he alive?" Ya sake tambayarsa. "Yes, but am not sure" Nan da nan aka ɗauki Captain zuwa inda aka kwantar da wanda suke buƙatar taimakon gaggawa, wanɗanda akaiwa rauni. Nan Army doctors, likitocin sojoji suka rufu akan Captain dan ceto rayuwarsa, aka fara ƙoƙarin cire bullet ɗin dake cikinsa. Sun yi nasarar cire na bayansa, amma na cikinsa ba su samu cire shi ba, sukace sai an koma can Barack za'a iya cire shi a Asibiti. Nan su kai ƙoƙarin tsaida jinin da ke zuba a jikinsa. Lieutenant Faruk ma an cire masa bullet ɗin da ke damtsensa, an saka bandage an nannaɗe masa hannun. "Hey, what this little baby is doing here?" Chief Commander ya faɗa yana nuna yarinyar da Captain ya tsinta. Faruk yace "Captain ne ya tsinto ta". "Is she among the victims?" Faruk yace "No, I don't think so, maybe she was kidnapped too, I don't actually knows where she belongs to" Ita dai bakunan su kawai take bi da kallo, Tare da son fuskantar me suke faɗa. Mota daban aka ware, aka tara gawarwakin sojojin da suka rasa rayukansu akan ceto wannan ɗalibai da akai garkuwa da su (may the gentle soul of the fallen heroes, rest in perfect peace). Aka samu wata motar aka saka wanɗanda suka ji rauni, tana ganin an ɗauki Captain ita ma ta miƙe ta bisu, dan kar su ɓace mata, aka saka shi a mota ita ma ta fara ƙoƙarin shiga Motar. "Hey, Carry this girl with you" Commander yai maganar yana nuna wani soja. Ganin ya danƙi hannunta zai shiga da ita wata motar ya sa ta fashewa da kuka. "Shut up!" Yai mata tsawa, duk da ba ta iya jin sautin abunda ya faɗa sosai amma ba ƙaramin razana ta yai ba, gaba ɗaya tsoron su ya shige ta, har ta fara tunanin ko irin mutanen da suka sato ta ne. Lieutenant Faruk ne ya ƙaraso, ya kamo hannunta suka shiga wata Motar, sai leƙa window take, tana nunawa Faruk motar da aka saka Captain a ciki, bai kula ta ba ya jingina da jikin kujera tare da lumshe ido. A daidaita sahu ce ta tsaya a ƙofar wani Babban Asibiti, mutane sai shiga suke suna fita, tare da salallami, fuskokinsu duk babu daɗi. A gigice wata mata ta sakko daga cikin adaidaita sahun, hannunta ɗauke da wani yaro da bai fi shekaru huɗu ba, jikinsa sai rawar sanyi yake, haƙoransa na datsewa. Bayan ta sallami mai a daidaita sahun, cikin gudu_gudu sauri_sauri ta shiga cikin Asibitin, ta nufi ɓangaren Accident and emmrgency, wato sashen bada taimakon gaggawa. Teburin Nurses ta nufa hannunta riƙe da yaron tace "Bayin Allah dan Allah ku taimaka min, yaro na kawo". Ɗaya ta ɗago ta kalleta tace "Ba mu da gado" Cikin tashin hankali tace "Dan girman Allah ku duba min yaron nan, kar shima in rasa shi, duk 'yan uwansa babu sai shi kaɗai ku temaka dan Allah" A fusace wata Nurse tace "kinji mace, muka ce miki ba mu da gado, ko ransa a hannunmu yake? In Allah ya ga dama karɓar shi zai yi, ko kina so ko ba kya so, waɗanda kike gani a kwance ma sallamar su za muyi, likitoci yajin aiki zasu tafi, in kina da kuɗi kuma zaki iya kai shi Asibitin kuɗi a duba shi" Cikin kuka tace "Wanne zan kai shi wanda zan samu likita a dubamin shi" Nurse ɗin tai murmushi ta ce "yanzun nan aka kira likitan da yake duba marasa lafiya a nan, duk ranar Talata yske zuwa, kuma awa uku kawai yake ya tafi, doctor G.Y ya tafi Asibitinsa, ki je ki same shi a can sai ya fi duba miki yaron yadda yakamata, a bashi duk abunda yake buƙata". "Au dama ba'a shiga yajin aikin ba?" Ta tambaya tana rarraba ido. Nurse ɗin ta ce "eh ba'a shiga ba tukuna, amma ai na gaya miki bamu da gado ko? Kuma ana shirye-shiryen tsunduma yajin aikin likitoci" "To shikenan, ina ne Asibitin nasa?" Suka kwatanta mata Asibitin, haka ta kuma fitowa da yaron, cikin tashin hankali ta tafi in da aka kwatanta mata. G.Y BULAMA HOSPITAL AND MERTERNITY, shine a rubuce a katafaren ginin, Manyan motoci na ta shiga suna fita a cikin harabar Asibitin. Tana rungume da yaron ta shiga cikin Asibitin, kai tsaye ta nufi in da wasu Nurses ke zaune tace "Sannunku, dan Allah mara lafiya muka kawo" tai maganar tana nuna musu yaron da ke hannunta. "Kuna da file a nan ne?" Wata Nurse ta tambaya. "A'a, Wallahi mun je Asibiti uku duk sai ace mana ba gado, a na ƙarshen ne aka ce mana wai yajin aiki likitoci za suyi, shine aka kwatanta mana nan" "To ai Hajiya sai kun buɗe file sannan likita zai ganku" Ta ce "To nawa ne buɗe file ɗin?" "Naira dubu biyar ne, single file" Turus tai, dan kuɗin hannunta dama dubu bakwai ne, sun ƙarar da biyu a yawon Asibitoci. Dubu biyar ɗin kenan ta rage a hannunta, a sanyaye ta ce "To a buɗe mana" Haka ta biya kuɗin nan, aka buɗe musu file, bayan an buɗe aka ce su biya dubu uku kuɗin ganin likita. Ta kalli Nurse ɗin ta ce "Wallahi suke nan a jikina, ki taimaka min baiwar Allah, kar in rasa ɗana, dan Allah ku duba shi" "Baiwar Allah, ba fa Asibiti na bane, kuma ba Asibitin gwamnati bane, haka ƙa'idar Asibitin take. Ta koma gefe kawai ta fashe da kuka. Wani dogon mutum ne fari sol, ya fito daga wani ɗaki jikinsa sanye da farar rigar likitoci, Nurses na biye da shi sun riƙo masa files, ganin mace ta saka ɗa a gaba tana kuka ya sa ya tsaya ya kalleta ya kalli yaron ya ce "Lafiya baiwar Allah, baki san akwai marasa lafiya a kwance ba kika ware murya kina wannan kukan?" Cikin kukan ta ce "dan Allah likita kai min rai, ka dubamin yaron nan, dubu biyar ɗin kenan na biya kuɗin buɗe file, kuma yanzu ance sai na biya na ganinka dan Allah ka dubamin shi". Ɗan shiru yai yana kallon ta, daga bisani ya durƙusa ya tattaɓa yaron, ya buɗe idon yaron, sannan ya miƙe tsaye yace "ku biya naira dubu hamsin, kwantar da yaron za'ai ya galabaita sosai" Daga haka bai kuma cewa komai ba, ya fara tafiya. Take hawayen idonta suka bushe jin an ambato dubu hamsin, dan basu da ita ba su da dalilinta, dan Mai_ gidanta ɗan acaɓa ne. Jiki na rawa ta ɗakko 'yar ƙaramar wayar ta mai madannai, ta nemi lambar mijin nata, cikin kuka tai masa bayanin halin da ake ciki. Yace "ki kwantar da hankalinki, kice su yi masa duk abun da ya dace, zan bada jinginar babur ɗina, in kawo kuɗin. Allah sarki uwa, kamar zata zare haka ta kuma tashi, ta nufi ofishin likitan nan, ta tarar yana duba wani mara lafiya, a hanzarce ta ce "likita dan Allah ka zo a fara bashi magani, babansa yace gashi nan zuwa zai zo ya biya kuɗin" Cike da ƙosawa da ƙufula ya ce "hajiya baki ga mara lafiya nake dubawa bane? Mu nan Asibitin bama haka, ki je idan kun kawo kuɗin a bashi maganin, kar ki sake shigo min office haka ba izini" Da ƙyar ta iya jan ƙafafuwanta da su kai mata nauyi, ta bar office ɗin, ta koma in da ta kwantar da yaron, sai jijjiga yake, jikinsa rauu da zazzaɓi, bakinsa se zubar da dafara yake, ta samu guri ta zauna ta ɗora yaron a kan ƙirjinta tana jin yadda zuciyar sa ke bugawa, kamar zata fasa ƙirjinsa ta fito. Ta lumshe ido tana zubar da hawaye tana kallon yadda kumfa ke fite a bakin yaron, amma cikin ma'aikatan ba wanda ya kalle su da idon tausayawa. Tana nan a zaune sai ga mijin nata kamar korarrare ya shigo hankali a tashe, ya ƙarasa in da take zaune da yaron yana faɗin "Zainabu, an duba shi kuwa?" Kasa Magana tai sai sake rushewa da kuka, yace "ki kwantar da hankalinki, na bada jinginar babur ɗina, na karɓo kuɗin a gurin maƙocinmu, a ina za'a biya kuɗin?" Ta nuna masa reception, in da zai je ya biya, ya je ya biya ya zo ya ɗauki yaron, ya rungume shi a jikinsa, da receipt ɗin biyan kuɗin a hannunsa. Aka nuna musu ofishin likitan, Ya shiga da yaron a jikinsa, likitan ya kalle shi ya nuna masa gadon da ke cikin Office ɗin yace ya kwantar da yaron ya je waje. Haka ya kwantar da shi ya fice, ya koma in da ya bar matarsa ya dinga rarashinta yana bata baki. Nurses ɗin jira suke suga doctor ya taso ya duba yaron, amma yace "This boy will not survive, da tun zuwansu sun ba da kuɗi ne, da maybe mu iya ceto shi, but for now, ba zai surving ba" "But doctor, da an jarraba dai ko Allah zai sa a ceto shi" wata Nurse tai Maganar cike da tausayawa. "Will you shut up, zaki koyamin aiki ne?" Yai maganar yana zazzare ido. Ta ce "No am sorry Sir" Wata matashiyar budurwa ce, sanye da uniform ta shigo hannunta da file ta kalli likitan ta ce "Doctor, 'yan uwan matar nan da za'aiwa CS a cikinsu duk babu me irin blood group ɗinta, Amma an samu mai O negative a cikinsu, wanda zeyi daidai da jinin Alhajin nan da aka rasa samun jinin da za'a saka masa" Ya ce "ok, yanzu abunda za'ai shine, ku ɗebi 2 pints of blood, a jikin shi mai O negative ɗin, sai kun ɗiba zuwa anjima sai ku ce musu kun sake gwadawa  jinin bai yi ba, su sake samo wasu mutanen, idan ya so a siyarawa da Alhajin jinin, 20thousands each pints, leda biyu 40 thousands kenan" Tace "ok Sir" Ya cigaba da sabgar gabansa, yayin da wannan yaro na kan gado ya cigaba da convulsing, ya kai mintuna talatin a haka, daga bisani rai yai halinsa. Sai da yaron ya rasu, Sannan Ya miƙe ya saka safar hannu, yai parking ɗin gawar, sannan ya fita daga office ɗin, cikin rige rige iyayen yaron suka ƙaraso suna tambayar ya jikinsa, cikin ko in kula doctor GY yace "He's gone, Allah yai masa rasuwa" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shi suka dinga maimaitawa, yayin da mahaifiyar yaron ta koma gefe tana zub da hawaye, shikenan guda ɗaya yaron, shima gashi ta rasa shi. Shi kuwa doctor G.Y yai gaba abunsa. Wasu daga cikin patient suka dinga bata baki, akan tayi tawakalli Allah ya bata wani. Cikin kuka ta kalli Nurses ɗin tace "Wataƙila da kun taimaka mana, ko da magani ne lokacin da muka zo yana suma, da wata ƙila bai rasu ba" Wata Nurse tace "ki ji min mata kamar jahila, maza kiyi saɓo kinji, mutane kamar ba musulmai ba ba tawakalli" Duk dauriya da jarumta irin ta namiji, sai da mahaifin yaron yai kuka, yace "ki dena faɗar haka Zainab, kinga hankalin mutane ya fara dawowa kan ki, ana gaya miki magana, Khalifa lokacinsa ne ya riga ya yi, Allah ya karɓe shi, Allah ya jiƙansa bari in je in samo adaidaita sahu, mu ɗau gawar". Haka ya fita dan neman adaidaita sahun da zata kai su gida. Bayan ya samu adaidaita sahun ya shigo Asibitin, ya koma reception ya tarar da wanda ya biya kuɗin Asibitin a gurinta ya ce "To, baiwar Allah tunda ba'a kwantar da yaron nan ba, Allah ya karɓi abunsa, ko ba duka ba dan Allah ku rago min kuɗin da na biya" Jinjina kai tayi tace "Ga doctor Bulama can, shine mai Asibitin wanda ya duba ɗanka, kaje ka same shi kai masa bayani". Bai yi ƙasa a gwiwa ba, yabi bayan doctor Bulama, tare da maimaita masa abunda ya gayawa receptionist. A wulaƙance ya dube shi sannan yace "Ka taɓa ganin wanda ya je ƙiyama ya dawo?" Ya girgiza Kai yace "A'a" "To nan Asibitin, no refundable after payment, kuɗi sun riga sun shiga asusun Asibiti, dan haka sai dai ka haƙura". Kamar zai shige cikin doctor Garba, haka ya duƙa yana cewa "Dan Allah ka taimaka min, Wallahi babur ɗina da nake neman Abinci na bada jingina, na karɓo kuɗin" A fusace doctor yace "kaga i have something to attend to, ka san ba ka da ƙarfi meyasa ka taho nan?" "Wallahi an rasa gado ne, kuma akace ma yajin aiki likitoci za su tafi shiyasa, dan Allah ka temaka mana..." Ai bai tsaya saurar sauran zancen ba, ya wuce a bar shi a gurin, ɗauke da baƙi ciki goma da Ashirin!. Kantagora Army barrack Naija state, nan ne in da aka kai gawarwakin sojojin da suka rasa ransu, da wanda a kaiwa rauni, kai tsaye aka wuce da su babban Asibitin da ke cikin barikin sojojin. Duk in da Faruk ya saka ƙafarsa, a nan yarinyar nan take mayar da tata ƙafar, ita kaɗai a cikin zaratan sojojin nan sai binsu take. Wani Babban soja yai umarni da a kaita cikin yaran da aka kuɓutar, ko itama a samu nata iyayen. Wani soja ya ce "To ai wannan yarinyar ba tai kama da 'yan Nigeria ba ma, ko ma dai daga maƙotan ƙasashen nan akai kidnapping ɗin ta?" Faruk ya ce "i have no idea about it, abunda na sani shine ba ta cikin wancan yaran da aka kuɓutar, dan haka ba cikin su Yakamata a haɗata ba, daban za'ai cigiyar iyayenta, abunyi Yanzu shine ko Madam Halima ce a bata ita ta zauna da ita, kan a san abunyi akanta". Su kai na'am da shawarar da Faruk ya bayar, akan ta zauna a gurin Madam Halima, itama soja ce a cikin tawagar, mijinta ma soja ne suna zaune a nan cikin barrack ɗin tare. Madam Halima ta kalli kyakkyawar fuskar yarinyar, wadda tai duƙun duƙun, 'yar rigar jikinta tai futu futu da datti, ga gashin kanta a hargitse duk datti da ƙasa. Cike da tausaywa yadda 'yar ƙanƙanuwar yarinyar tai rayuwa a hannun 'yan ta'adda babu kulawa ta ce "ya sunan ki?" Maimakon ta amsa sai tai ƙuri da ido tana kallon Madam Halima. "Ya sunan ki na ce?" Madam ta kuma maimaitawa, amma shiru ba tai responding ba. Faruk ya ce "ina ga fa ba ta Magana, da tunda aka tsinto ta banji tayi Magana ba". Madam ta ce "Allah sarki, Allah kaɗai ya san halin da iyayenta ke ciki, ai ita ma a Asibitin zamu bar ta a duba lafiyar ta tukunna" Faruk ya ce. "ok hakan ya yi". 'Yan matan nan ma da aka kuɓutar, duk nan Asibitin cikin barrack aka kawo su, dan binciken lafiyar su, kafin a miƙa su ga iyayensu. Gaba ɗaya ganinta take kamar a wata duniyar ta daban, Madam Halima taiwa yarinyar nan wanka tsaf, aka samo wata rigar aka saka mata, aka kwantar da ita akan gadon marasa lafiya, ba ta umm ba ta um'um, sai aukin rarraba idanu, babban burinta bai wuce ta ga wannan mutumin da ya ɗakkota daga hannun wannan mutanen ba. Sai dai ba ta san in da aka kai shi ba, wasu mutanen ne daban suke zuwa suna duba ta, suka dinga soka mata allura suna ɗibar mata jini, sai da suka saka ta kuka, dan haka gaba ɗaya tsoron gurin take ji. "Ashhadu alla ila ha illallah, Rabbana alaika tawakalna wa ilaika anabna wa ilaikal masir" shine abunda ya ke ta maimaitawa, tare da ƙoƙarin buɗe idanunsa a hankali. Dumm yake ji a kansa, ga shi dishi dishi yake gani, a hankali ya cigaba da lumshe idonsa yana buɗewa har Allah ya sa ya buɗe su yana ganin komai clearly. "Congratulations Captain, you survive" wani matashin likita ya faɗa yana murmushi. A hankali ya yunƙura zai tashi zaune, amma Likitan yai saurin cewa "No relax, ba'a daɗe da fitowa da kai daga tiyata ba, mun cire maka bullet a cikinka ne. Ajiyar zuciya yai yace "Alhamdilillah, yaran fa suna ina?" "Suna nan tare da mu a cikin Asibitin nan, ana musu gwaje gwaje kan a sada su da 'yan uwansu" Kamar dirar mikiya, haka yarinyar da ya tsinta ta faɗo masa, da sauri ya ce "There was one little baby, da na samo a cikin dajin, tana ina?" Likitan ya ɗan yi shiru sannan yace "kai gaskiya ni banga yarinya ƙarama a cikin yaran nan ba, duk 'yan makaranta ne" Da sauri ya ce "No, their is one little girl, ba tafi 3 years ba, wata fara haka" Doctor ya ce "Please calm down, kaga yanzu muka fito da kai, ka kwantar da hankalinka kar jininka ya hau". Captain ya girgiza kai yace "dole a nemo ta, she's not among the students, ba a cikin su take ba". "Shikenan is ok, za'a nemo ta insha Allah, bari inje in duba amma for now, dan Allah ka kwanta ka samu nustuwa" "Nutsuwata ɗaya, shine a ga yarinyar nan" "Ok, bari inje a duba". Captain ya koma ya gyara kwanciyar sa yana lumshe ido. Doctor da yaiwa Captain aiki ya cire masa bullet ya fita, dan neman yarinyar da Captain ya saka shi. Sai dai duk iya binciken da yai, babu wanda ya ga yarinyar, kowa ya tanbaya sai ya ce bai ganta ba, iya ɗaliban nan suke nan babu wata yarinya 'yar shekaru uku a cikin su. Har mutuary ya je, ya duba cikin gawarwakin yaran, amma babu wata yarinya ƙarama a cikin su. Komawa ɗakin da Captain yake yai, ya tarar an zaunar da shi, wani likitan ya kammala yi masa dressing ɗin in da ya samu rauni a bayansa. Ɗagowa Captain yai ya ɗan tsura masa idanu, yana jiran jin amsar da zai ba shi, duk da kasancewar likitan soja ne, amma sai da gabansa ya faɗi da irin kallon da Captain ke masa, saboda kasancewar sa mutum me matuƙar kwarjini. "Am.. duk cikin yaran nan an duba ba ta ciki, kuma har gawarwaki na duba amma babu ita a ciki, kowa na tambaya sai ya ce babu wata yarinya ƙarama a cikin yaran da aka kuɓutar duk matasa ne 'yan makaranta. "Impossible" Captain ya faɗa yana ƙoƙarin tashi. Saurin riƙe shi su kai suna cewa yayi haƙuri. "Ya za'ai yarinyar da na saka a Mota, ace ba'a ganta ba, a gabana fa ta shiga Motar?" "Ka yi haƙuri a sake dubawa za'a ganta". "No, zan duba da kaina" yai maganar yana ƙoƙarin miƙewa, sai dai jiri ya kwashe shi, da tsananin azaba da cikinsa ke yi, hakan ya tilasta masa komawa ya zauna. Comment and Share please Nimcyluv Ayshercool Zee kumurya. [9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷* _Bright pens✍🏾_ Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya *4.....* Elegant Online writer's _Kuyi following wannan acct ɗin a Arewabooks_ https://arewabooks.com/u/nimcyluv Captain Khamal ya yi saurin zame kan matarsa dake kafaɗarsa, idanunsa ya ware tare da sakin kwantaccen Murmushi, saboda ganin waɗanda suka shigo Room ɗin. Babbar mace ce, fara tas da ita zata iya yin shekaru hamsin a duniya. "Finally, my son survived Alhamdilillah" Hajiya A'isha ta ce, tana ƙarasawa bakin gadon da Major Khamal yake kwance. Lumshe idanunsa ya yi, He breathed slowly kafin ya ware idanunsa akan matar cikin ƙasa da murya yace. "First love" Ya Faɗi maganar yana ƙara sakar mata Murmushi. hannunsa ta kama tare dayi masa ƙuri da Idanunta, she tries to understand, if there is something wrong with him. A Hankali tace "Hankali na, ya tashi sosai Babana, na kasa samun nutsuwa bana son aikin nan naka, kullum cikin zullumi nake da tashin hankali" Captain Khamal ya kama hannun Hajiya A'isha wacce ta kasance Uwa a gare shi, ya ɗan yi murmushi yace "First love, ba gashi kinga lafiya nake ba? Zan warke insha Allah" "Tsoro take kada a kashe mata Jaruminta" Da sauri Captain Khamal ya ɗaga kansa, with so much surprise yake kallon mai maganar, Sai a lokacin ya kula dashi. "Baffa" Captain ya ce, yana ware idanunsa akan mahaifinsa dake tsaye cikin shigar manyan kaya, kamarsa da Major Khamal ta bayyana sosai, hatta baƙar fatar Captain irinta Baffa ce. Baffa ya harari Khamal, cikin wasa ya ce "An manta da Baffa saboda anga first love? Shine ni aka ƙi kulani" "It's not like that, Baffa" waje Baffa ya nema tare da zama cikin tausayin ɗan nasa ya ce "Ya jikin naka?" . "Jiki Alhamdilillah Baffa" Jinjina kai Baffa ya yi yana kallon wajan da aka harbi Khamal, cikin sanyin murya Baffa yace "I received a call on phone, from the military command in Abuja, sun gaya min Wanda suka rasa rayukansu a dajin, hankali na ya tashi sosai, mun ɗauka ko har da kai, Sai daga baya muka samu full information akan cewar kai raunuka ka samu" Captain dai murmushi yake, yana son iyayensa bashi da kamar su. "Yaya K, ya jiki?" Cewar wani matashin saurayi. Khamal ya kalli ƙaninsa Shureim yace "You?" Shureim ya kwaɓe fuska tare da faɗin "Duk na damu zan rasa Big bro, shine ya kula kowa banda ni" "Sorry Shureim" Shureim ya ce "Ya jikin Yaya K?" Captain ya rufe idanunsa A hankali ya ce "I'm good" surutun da yake yi, gaba ɗaya ya fama masa ciwon, yana jin yadda gurin yake masa zafi sosai. Na'ima dake gefensa, ji take kamar ta ɗauke mijinta su tafi gida haka take ji. Tayi kewarsa sosai, har tsanar aikin take saboda tsayin lokacin da suke ɗauka basa tare. Army Doctor ɗin daya shigo ne, ya kalli su Baffa cikin sakin fuska ya ce "Ana buƙatar ya samu nutsuwa, wajan harsashin bai warke ba haryanzu" Baffa ya miƙe tsaye, Yana faɗin "Daman da yaya aka barmu muka shigo ganinsa, tafiya za mu yi tunda kun mana fin ƙarfi" Dr ɗin dai murmushi ya yi, Baffa ya yi waje. Hajiya A'isha ta kalli Captain ta ce "Allah ya ƙara sauƙi Babana, Zuwa yaushe zaka dawo gida ka huta?". "First love ban sani ba, but Soon in sha Allah" ta ce "To, Allah ya tsare min kai" yunƙurawa ya yi zai tashi da sauri Na'ima ta kamashi tana faɗin "Be careful" Duk yadda yaso miƙewa kasawa ya yi, Dole ya koma tare da zama ya ce "Allah ya kiyaye hanya first love" fita duk sukai hadda Shureim. Na'ima ta kalleshi tace "My man, ni ina nan tare da kai ko?" Ya ware Idanu ya ce "Are You sure?" Kai ta ɗaga masa tana kama hannunsa tace "I really really miss you Man, Over eight months banji ɗumin ka ba" hancinta ya ja "I miss you both, i mean you and my unborn child" Lamo tai a kafaɗar sa, kewarsa na fisgarta, She misses every single thing about him, she wants to be with her husband. Madam Halima kuwa ta rasa ya ya zatai da Yarinyar kuka kawai take tana kiran "Abbi" cikin damuwa da kuma son rarrashin Yarinyar Madam Halima tace "Me kike so?" Yarinyar Taƙi cewa komai, domin bama ta gane me Madam Halima ta ce ba. Madam Halima tace "Jama'a na shiga Uku, wacce irin yarinya ce wannan?" Miƙewa ta yi tare da zama kusa da yarinyar cikin rarrashi tace. "Kin ga stop crying, A good child never cry." Ƙanƙame jikinta tayi, bata so ko taɓa ta ayi, She's afraid of everything. Babu wanda take son gani sai Mutumin daya ɗakko ta, Idanunta na hango mata shi cikin jini. Da hannu Madam Halima tai mata nuni irin Sign language ɗin nan tace. "Ke, kuka ki daina babu kyau". "Abbi..." Yarinyar Ta faɗa da ɗan ƙarfi, shiru Madam Halima tai, ko mahaifinta ne Abbi?. Kallon yarinyar tayi, fara ce sosai, irin farin nan ƙal, But she looks very similar to Arabs, her eyes, hair, almost everything. "ماذا تريد اين والدك" Ma'ana "me kike so, ina mahaifin ki yake?" Madam Halima ta tambayeta da larabci, a tunaninta tunda tayi mata kala da Larabawa, may be tana jin larabci, bata san cewa gaba ɗaya maganar ce ba sosai take jinta ba. Cikin rarrashi ta ce "Kee, yanzu zan kira Abbinki.. kina so?" Da sauri ta ɗaga mata kai tana mata ƙuri da Idanunta, ta fuskanci hakan ne saboda bakin Madam da ta kalla, Madam Halima tai Murmushi tana bata Teddy tace "sai Kinyi bacci Abbi zai zo, kwanta" tai mata alama da data kwanta, ganin ta sake ambatar Abbi yasa Yarinyar kwanciya ta sakin ajjiyar zuciya, kana ganinta kasan akwai ɓoyayyan abu a tattare da ita. Sai da Madam Halima taga tayi bacci, ta zare mata yatsarta dake baki, a firgice ta farka tana shirin sakin kuka Madam Halima ta mayar mata da yatsar bakinta. Duk a wahale take, ta jima Idanunta bai ga bacci ba, ihun dabbobin jeji, da kuma tsoro yasa bata wani baccin kirki. Girgiza kai Madam Halima tayi Ubangiji kaɗai yasan halin da Yarinyar ta shiga, ko ƴar ina ce? Su waye iyayenta, they are alive or dead, Ohho!?. Wayarta ta ɗauka tare da kiran Lieutanant Faruk, ta faɗa masa She wants to see him immediately. Faruk daya shigo yanzu, shima ya kalli yarinyar kafin ya juya ya kalli Madam Halima yace "what happened now?" Madam Halima ta ce "Honestly, Her memory may be impaired idan taci gaba da kasancewa haka, a Yanzu ma kamar tana da wata ɓoyayyiyar larura" Faruk kasa cewa komai ya yi, yana mamakin yadda ƙaramar yarinya ta kasance a cikin wannan jejin, ko me ya kaita oho? Ko iyayenta akai kidnapping tai escaping ko wani abun ne, Allah ne ya barwa kansa sani. Faruk yai ajiyar zuciya yace "I will speak to Captain Khamal, Whatever he said, I will get back to you, Amma Banga kyautatuwar zamanta a nan ba" Madam Halima taja numfashi kafin ta nemi waje ta zauna tace "you said she was not among the school children kidnapped?" "Haka yace" Faruk ya faɗa yana taɓe fuska. Madam Halima tace "Waye yace?" yace "Captain Khamal, kin san taurin kansa ai, bakomai ze tsaya yai maka bayani ba" Tace "To, Allah ya kyauta" Daga nan Faruk juyawa ya yi, tare da yin waje, yabar Madam da baki a buɗe. Wata matashiyar budurwa ce tsaye, da gajeren wanddo da farar shirt irin na sojoji, kanta ya sha a wigs, tai parking ɗin sa a bayanta, ta sarawa Lieutanant Faruk daya fito ta ce "Sir, Abu babu daɗi Allah ya tsare gaba. Amma nayi farin ciki sosai da nasarar da kuka samu" Faruk yace "Thank you,Salima yaushe kika shigo Naija state?" Tace "Not too long, Ina Captain ne?" Murmushi kawai Faruk ya yi mata, dan yasan tatsuniyar gizo baya shige koƙi Yace "Shi kika biyo ke nan?. Tace "A'a, za'ai posting ɗin mu zuwa wani waje ne, shine muka biyo ta nan zamu shige da sauran" Faruk yace "I see, yanzu Captain ba lallai ki ganshi ba, lokacin treatment ɗin sa ya yi" Salima tace "My be zuwa Dare" Faruk ya kalli Salima in a serious tone yace "Zan iya cewa wani abu, Salima?". "All ears. Sir Faruk" Salima ta faɗi hakan tana kallon Faruk sosai. "Meyasa ba zaki iya haƙuri da soyayyar Captain Khamal ba?" Salima was speechless. Bata san cewa Abinda Faruk zai faɗa mata ke nan ba. Cikin sanyin Murya ta ce "I can't stop thinking about him, I always want to be with him, Wallah Sir Faruk ban san me zan ba, nace masa koda bai auren ba, kawai mu kasance tare, duk abinda yake so zan masa, like how every woman takes care of her husband" Shiru Faruk ya yi ta kallon Salima, If he is not mistaken, bata da burin daya shige Captain ya kwanta da ita, ta ɓullo masa ta barikanci ya ƙi yarda, tace ya aureta nan ma yaƙi. Faruk yace "Captain daban yake a cikin mu, rashin matarsa kusa dashi bai sa yabi matan banza ba, Ni shaida ne, You are wasting your time Salima, ko Captain zai kula wata ai banda irinki,ke fa duk kusan mazan Barrack ɗin Abuja ba wanda bai san yaya kike ba, Among the men, including me" "Alright, kace kishi ka ke dani? Ya ware hannunsa tare da yin gaba yana faɗin " ko ɗan, it's just a suggestion"... The next day at night. Captain na zaune Sanye da vest fara ƙal, sai gajeren wando, ƙafarsa sanye cikin wani baƙin takalmi, Leutanant Faruk ne ya buɗe ƙofar ya shigo, cikin girmamawa ya gaida Captain. Sipping coffee Captain Khamal yake a nutse, a hankali ta dinga leƙo da kanta daga bayan Faruk tana leƙen Captain Sam Captain bai lura da ita ba, yaji a jikinsa akwai wanda ke kallonsa dai. "Abbi ɗin, kike leƙa kuma?" Faruk ya faɗa da ɗan ƙarfi yadda za taji abinda yake cewa. Captain ya ɗago kansa da sauri, farin hannunta mai ɗauke da Teddy ya hango. Gaba ɗaya ta ɓoye jikinta da fuskarta a bayan Faruk. Da sauri Faruk yaja baya yana murmushi ya ce "Ai baki isa ba, yadda kika ɗaga hankalin kowa shine yanzu zaki ɓoye a bayana?" Yarinyar ta rufe Idanunta tana ƙanƙame Teddyn da Madam Halima ta bata, riga da wando ne jikinta masu kyau, peach colour. An raba mata gashin kanta gida biyu ya kwanta har baya. A nutse Captain yake ƙare mata kallo, ko wanne kalar sauyin ta samu, ba zai mance kamanninta ba, duk yanzu tsaf take, saɓanin lokacin da ya tsinceta cikin datti. Zame Teddyn tayi daga kan fuskarta, tare da buɗe Idanunta. Idanu suka haɗa da Captain Khamal, ya ware mata manyan idanunsa, ƙara ta saki tana ƙanƙame Teddy. Sosai ya bata tsoro, bayan kuma shi take ta kuka za tazo wajensa. Murmushi Captain ya saki, yana ɗan rufe idanunsa, seeing how she was scared by what he did to her. "Come here". Captain ya ce mata, yana miƙa mata hannunsa, ƙuri tayi masa da Manyan idanunta, da suke farare ta tass, Ganin yadda ta kafeshi da Idanu, kamar bata taɓa ganinsa ba, yasa Captain ya ƙara ware mata manyan idanunsa yana sane. Maimakon yaga tayi ƙara, sai kawai yaga ta saki Teddyn tare da ta zuwa wajansa da gudu. Zamewa ya yi kaɗan yana gyara zamansa, saboda ciwon jikinsa. "Abbi" Yarinyar ta ce, tana tsayawa gaban Captain tare da leƙa fuskarsa, Murmushi ya sakar mata, itama ta washe white teeths ɗin ta, tana ƙara zura kanta tare da leƙa fuskarsa sosai. Faruk dai ikon Allah yake kallo, tunda aka kawo yarinyar take kuka, amma yanzu gata harda dariya. "Abbi" Ta kuma cewa tana nuna masa ciwon jikinsa sai kuma tace "Shhhhhh" tana kwaɓe fuska tare da Girgiza kanta, alamar bata son ganin ciwon gaba ɗaya. Musamman daya kasance a jikin Abbi ɗinta. Fuskarta ya tallafo, a zuciyarsa yana jinjina kyan da Ubangiji ya yi mata, mai fisgar Hankalin jama'a. Caraf yaji ta kama tafin hannunsa wanda yasa Captain saurin rufe ido, sai kuma ya buɗe lokaci guda!. "How are you?" Cewar Captain yana buɗe idanunsa akan innocent face ɗin ta, bata san mene yace ba, amma sosai taji sautin kamilalliyar muryarsa a kunnanta, ta samu kanta da ɗaga masa kai tana faɗin "Abbi" Ya fahimci kalmar “Abbi”. Ita kawai ta riƙe cikin bakinta, idan ba Captain ba, kallon kowa take matsayin wani abu daban. "Sir yanzu wanne suna za'a ce mata, tun da naga ko sunanta ba ta sani ba?" Gently Captain ya kalli Faruk, sai kuma ya kalli fuskar yarinyar kafin ya rufe idanunsa yace. “ABRA KHAMAL KHAMIS BUBA” "Abra...?" Faruk ya ɗan zaro ido ya maimaita a zuciyarsa, kafin yace "Allah ya raya, Abra.." "Amin, thank you" cewar Captain Faruk yace "Amma yallaɓai, naji ka haɗa sunan nata da naka, ba za'a nemo iyayenta ba kenan?" Shiru Captain yai, bai bawa Faruk amsar tambayar da yai masa ba. Abra kuwa ta ƙurawa tea ɗin dake gefen Captain Idanu, shima ya Kalli tea ɗin, da hannunsa ya yi mata alamar zata sha ne? Domin ba zai iya yin ihun magana ba. Ta ɗaga masa kai tare da faɗin "Abbi" hannunsa yasa tare da ɗaga ta Cak zuwa saman cinyarsa, a nutse yake bata tea ɗin tana sha, sai da tasha sosai ta janye bakinta, idanunsa akan Faruk yace. "Wannan kan nata, abuɗe kamar ƴar arna, kai kuma kamar maye ka zuba mata ido Mtwss" Murmushi Faruk ya yi, tare da ɗauke idanunsa daga kan Abra yace "Haka aka ban ita nima, idan maye ni me zan da Abra sai dai Abbin Abra" Murmushi kawai Captain ya yi, a hankali kuma yaji numfashi Abra na sauka alamar tai bacci kwance a nan jikinsa. Yatsarsa data saka a baki tana tsotsa ta ɗauka nata ne, shi ya zame a hankali yace. "She is sleeping, come and pick her up" ya faɗa yana hura iska sosai a kunnanta, Just to confirm abinda yake tunani, amma ko motsawa ba tayi ba, sai ma firgita da tayi tana riƙe hannunsa tace "Abbi" Captain bai ce komai ba, amma har zuciyarsa yake tsananin so da tausayin Abra. Faruk ya ɗauke ta, yana yin waje "Tell Madam Halima, that she should took a good care of her, ina tsoran Barrack.". Faruk ya jinjina kai. Babu jimawa da fitar Faruk, Na'ima ta shigo, hakan yasa ba taga Abra ba sam, tana zuba ƙamshi sosai ta Ƙarasa wajan Captain, tare da zama gefensa tace "Man" Hannunta ya kama tare da murzawa "Wife" ya faɗa a taushashe, ƙamshinta na ɗaukan hankalinsa, shi kansa dauriya yake sosai a kanta. "When will you be discharged?" Na'ima tayi magana tana bin Captain da wani irin kallo, mai kama da zallar buƙatar mata ga mijinta. "to tomorrow or the day after" yace yana kissing lip's ɗinta, ta rufe idanunta, ya yi mata side hug, tare da ƙurawa cikinta idanu, wanda ya girma sosai saura kaɗan EDD nata ya cika. Wayar Na'ima ta ɗauki ringing, ta yi wani kalar zabura tana tura baki gaba, Captain ya yi Murmushi, a hankali ta ɗauki wayar daga cikin wayar akace "Waye ne?" Na'ima tace "Nice Granny" tace "Kewa?" Ta ce "Na'ima" da sauri Granny dake cikin wayar tace "Auzubillah, wata abace Na'ima kuma? Kinga ba ruwana dake, cewa zan daman ki kirani, irin kiran nan mai motsi" kashe wayar Na'ima tayi dake akwai Wi-Fi sai ta kira number Granny a V.c Fuskar wata tsohuwa ta bayyana a screen ɗin wayar Na'ima, tana hakimce akan kujera ta lafta wani glasses a Fuskarta, a cewarta kwana biyu baki ke son kamata. Ganin fuskar Na'ima, yasa Granny runtse idanunta tace "A'a me zan da naki fuskar kuma? Maza kamo min fuskar Kamalu" Captain Khamal ya ɗura kansa a kafaɗar Na'ima, a sanyaye ya ce. "Granny" fashe masa tayi kuka sosai tace "Allah ya isa, Allah ya isa, Allah dai ya isa har sau uku" ya yi Murmushi ya ce "Ɗaya ta Isa" da sauri tace "Wlh bata isa ba, guda goma na su yi, amma na barta a guda uku, kuma gaba ɗaya da matarka Na'ima nake, ai ba uwata bace da zanji tsoranta" Captain dai ya kasa cewa komai, Granny tana matse Idanunta tace "Abinda matarka tai min, Allah kaɗai na barwa, shi yasan yadda zai da ita, banda haka mace bata san darajar ɗan fari ba, tai ta gantali da narkeken ciki a gaba, duniya duk ta lalace da ɓata gari, haka kurum ta haɗu da wani mayen ya lashe ɗan Tun a ciki? To ya bazan mata Allah ya isa ba? Nifa shi yasa tun farko nace kawai kayi mata huɗu ko wacce tayi ta kanta, amma yanzu zanta shela wacce taga Allah taga Ma"aiki ta aureka" Captain ya kalli Na'ima data haɗe fuska yace "Granny, Soon zan ƙara mata ai..." Granny ta waro Idanunta tace "kace Allah?" Ya ɗaga mata kai. Tayi ƙasa da murya tace "To ai kaga haka yafi? Nayi magana cikin azanci, kuma ka fahimcen, Amma wannan matar taka mai kama da sadaka yalla sam ba tai min ba, ƴar banza ce, tana kallon kuwa a wulaƙance" Haka tai ta surutu daga ƙarshe ta kashe wayar. Na'ima ta cika tai fam, Captain ya jawota yana matseta yace "Sorry, Wife... Zo kiji". Kwanan Na'ima huɗu wajan Captain a gidan da aka ware masa, shi kuma yana Hospital, kullum sai Faruk ya kawo masa Abra, amma basu taɓa samun Na'ima a wajan ba, hakan ya yi wa Captain daɗi, dan yasan rikicin Na'ima, Abra kullum da kuka take barin Wajan Abbi ɗinta. Yana zaune, cikin wasu ƙana nan kaya masu kyau, a hankali aka turo ƙofar tare da shigowa, tunda ta Shigo yake binta da kallo, idanunsa ya ɗauke cikin sanyin jiki Salima ta Ƙarasa tare da faɗin "Ya jiki dear?" Captain ya yi mata banza, wajansa ta Ƙarasa kafin ya tashi ta riƙe ƙafarsa tare da fashewa da kuka sosai tace. "Dan girman Allah, kaji tausayi na Khamal, ka daina azabtar dani da soyayyarka" Daka bakin ƙofa akace "Kutirin Ubanki zaici ba tausayi ba, Shegiya karuwa mai bin mazan mutane" Da sauri Salima ta miƙe tsaye, shi kansa Captain a rikice yake kallon Na'ima, tana zuwa ta ɗauke Salima da maruka tace "Wlh wlh sai naga bayanki, akan mijina sai na kashe mutum, mijina nawa ne kawai, da ƴa ƴan da zan haifa masa, karuwa kawai" Salima ta haɗe fuska tace "I am not a prostitute" Na'ima ta cire mayafinta, ko cikin jikinta bata gani ta shaƙo wuyan Salima tace "Na faɗa karuwa, idan ba karuwa ba gantalalliya wace za tana bin mijin wata tana cewa ya so ta? Wlh sai na kashe ki na kashe Captain na kashe kaina, gaba ɗaya mu tafi lahira ai mana hisabi a can, babu wata banzar data isa ta shiga rayuwar mijina, ina son mijina fiye da komai" da ƙyar Captain ya ƙwace Salima da ga hannun Na'ima, tare da daka mata tsawa yace "Stop this nonsense, Na'ima." With so much surprise Na'ima ke kallon Captain. Ya kalli Salima yace "Get out" Salima ta kalli Na'ima ta ce "Zaki gane da karuwa kike magana, Wlh sai na shigo gidan ki, sai na auri Mijinki, sai na rabaki dashi" Wani ihu Na'ima ta saki, ta shiga ƙundumawa Salima zagi, tana ƙoƙarin ɗaukan wata kwalba zata kwaɗa mata, Captain ya riƙe Na'ima yace "I Said Get out, Salima" fita Salima tayi. Na'ima ta fashe da kuka sosai, Captain ya kasa ce mata komai ya jata jikinsa sosai ya rungome ta yana faɗin "meyasa kike hakane? Matar nan soja ce ga ciki a jikinki ba kya tsoron tai miki illa?". "Wallahi in dai akan ka ne, bana tsoronta" ta ƙarasa Maganar tare da zame jikinta daga nasa tai waje. G.Y Bulama hospital and Merternity. Dr G.Y ya kalli mutumin dake gabansa kafin yace "ranka ya daɗe, zamu shiga tiyata da ita" Mutumin yace "Dr Ka taimaki matata, I don't want to lose her" yanayin yadda yai maganar zaka gane, tsohon ɗan boko ne. G.Y yace "Tunda ka kawo kuɗin aikin da wuri, Don't worry, she will be fine insha Allah". Yana faɗin haka ya nufi theatre room inda aka kai matar mutumin. Ƙyakƙyawan yaron dake kusa da Mutumin a ƙalla ze shekara goma sha ɗaya, kamarsa ɗaya sak da mutumin yace "Abu, Mami na" Mutumin ya shafa kan yaron nasa yace "Mami zata samu lafiya, stop crying My son" yanayinsu ya nuna suna da cikakken ilimi sosai. Both arabi da boko. Dr G.y ya kalli matar dake kwance akan gadon tiyata, cikin jikinta sai juyawa yake, duk abinda ke cikin nata shima wahala yake sha sosai, ya matso yazo duniya. Cikin ko in kula ya kalli wata Nurse yace "Ina wannan yaron mai ciwon Sikila?" Tace "Yana male Ward" "Shine wanda za'a ƙarawa jini, Iyayensa sune masu kuɗin nan?" Ta ɗaga masa kai. yyace "Ok a ɗauki 1 Pints of blood, da aka ajiye na wannan matar, naga irin jinin su ɗaya, sai a kaiwa iyayensa su bada 50k a sawa yaron" Nurse ɗin tace "Dr ita kuma matar fa? C.s za'ai mata fa,kuma zata buƙaci jini immediately in an fito da ita, ai bai dace a ɗauki nata ba" Dr G.y ya nemi waje ya gyara tsayuwarsa yana faɗin "Who is the boss between me and you?". Cikin girmamawa tace "kai ne Sir" yace "So do as i said, is hardly for her to survive" Kamar za tai kuka Nurse ɗin tace "Amma aka amshi kuɗin aiki har 180k, Dr? But You can still try to help her." Dr ya haɗe rai sosai ya ce "Ke nan, zuwa asibitin duk a banza? Ra'ayi na ne haka, har a gado aka kwantar da ita, and bance ba za'ai mata komai ba, za'a cire abunda ke cikin nata, but she's hypotensive and at the same time she has hyperglycemia, is hardly for her to survive". Nurse ɗin tai zuguum tana kallon cikin tiyatar in da matar ke kwance, take ta jujjuya kanta, alamar tana jin jiki. Wani likitan ne ya shigo cikin tiyatar, yana faɗin "an haɗa komai?" G.Y ysce "Eh an haɗa komai mu shiga" Suka je suka kewaye matar, sukai mata allurai aka kashe daga cikin ta zuwa ƙafafuwan ta, sannan suka fara ƙoƙarin yankata, GY ya samata ruwa da allurai a ciki sannan suka fara aikin. Suna tsaka da yi numfashinta ya fara sama yana ƙasa, SPO2 ɗinta was very low, ga PR ɗinta was very high. Da sauri ɗaya likitan yace "what's going wrong? GY wace allurar ka sa mata a ruwan nan ne?" GY ya gaya masa, ya duba ruwan ya ɗakko kwalaban alluran ya duba, a take ya zare ido yace "GY ka manta she's hypertensive ne? Kuma allurar ai ba ita bace". Da sauri GY ya duba tabbas yayi kuskure gurin saka allurar, na da nan suka tsaida ruwan, suka cigaba da ƙoƙarin ciro ɗan, amma yaron haka suka ciro shi babu rai. Tuni ta galabaita matar, ta fita hayyacinta ba ta gane koma, ga jini da ya ɓalle kamar an kunna famfo, da ƙyar su ka ɗinke cikin nata, Amma ta ƙasanta jini sai ambaliya yake, ɗaya likitan yai mata duk alluran da suka kamata, amma jini be tsaya ba, ya kalli GY Yace "maza maza da an kaita ward, a saka mata jini, sannan ƴan uwanta su sake kawo wani jinin". Mutumin nan da ɗansa suna tsaye aka fito da matar, gaba ɗaya abunda aka rufeta da shi, jini ya ɓata har ɗiga yake, aikuwa yaron ya bi bayansu da sauri GY ya kalli Nurse yace "maza aje lap, a ɗakko jinin nan a sakamata". Nurse tace "Doctor, har ka manta kace a siyarwa da iyayen yaran nan me sickler?" Ɗaya likitan yace "GY harƙallarka tayi yawa Wallahi, yanzu ya za muyi da matar nan, she needs blood urgently, naga ance she has hyperglycemia, a bani glucometer in sake gwadawa" Sai dai yana gwadawa ya ga sugan nata yai ƙasa sosai, ya duba file ɗinta, tun da tai awo a Asibitin, ba'a taɓa cewa tana da sugar ba sai yanzu. "Waye ya duba sugarn nan kan a shiga tiyata" Nurse ɗin dake biye da su tace "Nurse Bintu ce" "Yaushe ta zama Nurse? Ba food hygiene tai ba? Dan me za ta dinga aikin Nurses, gaskiya GY Asibitinka da gyara". Duk wannan mujadalar, yaron na tsaye a bakin ƙofa, yaji duk abunda suke faɗa. Ya ja da baya ya koma in da ya baro mahaifinsa, cikin damuwa yace "My son, kayi mana Maminka addu'a" Shiru Yaron yai bai ce komai ba, Su GY suka fito a tare ya kalli mutumin yace "Sai dai kuyi haƙuri, mun rasa ɗan da ke cikin ta, ita ma kuyi ta Addu'a muna kan ƙoƙarin ceto ranta ne" Ba su kuma yi musu wani bayani ba, suka wuce, yaron ya kama hannun mahaifinsa ya ja shi zuwa ɗakin da take ciki, tana kwance jini na ta ɗinga daga kan gadon da take! For seven days now, Captain is being treating in the military hospital, in Naija State military base. Chief of Army staff ne, da General Ibrahim, da Chief Commander tsaye a cikin Room ɗin, Chief ya kalli Captain yace "Congratulations Captain, we were confirmed that today you will be discharged " Captain yace "Thank you, sir" Chief ya ce "akwai Good news, but it will be surprising.." Captain ya ware idanunsa sosai, Chief Commander ya yi Murmushi kafin ya kalli Captain ya ce. "Jirgi na jiranka an gama komai, Allah ya ƙara sauƙi Captain, kai na musamman ne" General dai hararar Captain yake, yana tunanin yadda zai ga bayansa. Gaba ɗaya fita sukai waje. A hankali Captain ya fito cikin wata farar singlet irinta sojoji yana ƙarewa harabar Barrack ɗin kallo. Tunanin yadda zai tafi da Abra yake ga Na'ima, gashi Chief ya tilasta sai an bincka iyayenta. Yana tsaye yaga Faruk ya nufu wajansa, Captain ya ce "What happened?" Faruk ya Girgiza kai yace "Abra" a hargitse Captain yace "Abra What? Don't tell Anything mara kyau akan Yarinyata" Faruk yace "Abra was missing, tun safe babu Abra gaba ɗaya n duba cikin Barrack ɗin nan babu ita... Abra ta ɓata!. Bright pens Nimcyluv Zee kumurya Ayushercool✍🏾🤘🏼 'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm! BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE I'm selling MTN data with this cheap price MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month Airtel,9mobile and Glo also available. *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* Whatsapp OR Call *08066268951* [9/30, 8:55 PM] Abk: *✷DARE DA DUHU✷* _Bright pens of✍🏾_ Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya *3......* Elegant Online writers _Ƙirƙirarren labari ne, ba mu yi shi dan cin zarafin wani ko wata ba, idan yai kamanceceniya da rayuwar wani ko wata Arashi ne🫣_ _Littafin DARE DA DUHU haƙƙin mallakar mu ne, bamu yar da a juya shi ta kowace siga ba, ko a sashi a wata kafa ba ba tare da izinin mu ba_ Dafe kansa dake barazanar tarwatse masa ya yi, tare da taune lips ɗinsa na ƙasa cikin taurin zuciya. Likitan da ya je nemo yarinyar bai ganta ba ya dube shi, cikin girmamawa da son kwantar masa da hankali ya ce. "Ka kwantar da hankalinka Sir, Insha Allah, za'a ganta" Runtse idonsa ya yi, gently ya ƙara buɗe su yana kallon su ya ce. "Where is my phone?" Likitan ya ce. "Tana nan tare da uniform ɗinka, da za'a yi maka surgery ne aka cire su." Bai ce komai ba sai alama da ya yi masa da hannu akan ya kawo masa wayar. Likitan ya sara masa sannan ya fice. Gyara masa kwanciya ɗayan Likitan ya yi, shi ma ya fice. Lumshe idonsa ya yi yana tuna Jamil da Danniel cikin jini a kallon ƙarshe da ya yi musu, sosai mutuwar su take dukan zuciyarsa. Numfashi ya fesar mai zafi lokacin da ya tuno fuskar ƙaramar yarinyar da ya gani, bai san me yasa ya ji ya damu da ita ba a cikin zuciyarsa, ji yake yi kamar ya fizge drip ɗin hannunsa ya fita ya nemo ta da kansa. A fili ya furta "Where is She?What kind of situation is she in? who will take care of her?" Ya yi maganar cikin damuwa. he just felt worried about the little girl. General Ibrahim A.M ne yake ta kaiwa da komowa a cikin office ɗinsa, shi kaɗai cikin tsananin ɓacin rai. Lokaci ɗaya ya koma mazauninsa ya zauna yana fesar da wani numfashi mai zafi, duk da kasancewar office ɗin da A.c amma gumi ne kawai yake tsatstsafo masa ta ko'ina a jikinsa. Hannunsa dafe da kansa sai karkaɗa ƙafafuwansa yake yi. Da ƙarfi ya buga table ɗin gabansa tare da faɗin. "Damn it!" Wayarsa ce ta fara ruri tana neman agaji, tsaki ya ja har kiran ya katse bai bi ta kan sa ba, dan ba ta shi yake ba. Sai da aka yi masa 4 missed call sannan ya janyo wayar cikin ɗacin rai a fusace ya ɗaga ba tare da ya duba mai kiran ba. Daga cikin wayar wata shaƙaƙƙiyar murya ya ce. "An samu bacin rana!" Ajiyar zuciya General Ibrahim ya sauke yace "Har da na Inuwa ma duk an samu Gwaska." Gwaska ya ce "Ba a taɓa mun Ɓarna irin wannan ba tunda na fara harkan nan, ya akai haka ta faru?." Cikin ɓacin rai General ya ce. "Ba za ka gane baƙin cikin da nake ci da wannan Nasara da yaran nan suka samu ba, ban taɓa tunanin hakan za ta faru ba, a yanda na san ka na san taƙadirancinka ko rundunar sojoji million aka turo za ka iya gamawa da su, na baka komai a tsare, umarnin harbin da aka basu ne ya ɓata komai, kuma aka shirya wata rundunar aka tura ba tare da sanina ba,  shiyasa su suka yi galaba a kanku. Babban baƙin cikina da wancan yaron Khamal ya dawo a raye ba, kuma na san duk nasarar da aka samu sanadiyyar sa ne, dan ba ƙaramin jajircewa ce da shi akan aikinsa ba, yana aiki ne da jikinsa gami da zuciyarsa, He knows the value of his work, especially if he wears military uniforms on his body, he feels like he is carrying the whole country in his shoulder, gaba ɗaya yanzu idan manyanmu a kansa yake". Gwaska ya yi wata shegiyar dariya ya ce. "Indai kere na yawo, zabo na yawo wata rana za'a haɗu, Wallahi sai na ɗauki fansar kisan yarana da akai mun da kuma harsashin da ya huda jikina, zan yi ɓarnar da sena girgiza ƙasar nan girgiza ta gaske makuwa, kuma dole a sakarmin yarana da aka kama ko kuma aga abunda ba'a so" Cikin mamaki General ya ce. "What? You mean kai ma sun yi nasarar harbin k......," kiran da ya shigo cikin wayarsa ne ya katse masa abun da yake cewa. Janye wayar ya yi daga kunnensa ya duba, ganin Chief of Army staff ne yasa cikin sauri ya cewa Gwaska "Ina zuwa, I will call you later." Bai jira amsarsa ba ya ɗaga kiran Chief ɗin. Ƙamewa ya yi kamar yana gabansa with so much respect ya ce. "Morning Sir." Daga ɗaya ɓangaren Chief ya ce. "Morning General, ka shirya kai da sojoji kamar 20 anjima za mu zo mu je mu dubo yaranmu na Naija state, sanann mu jagoranci miƙa yaran nan ga iyayensu " "Done Sir." General ya faɗa tare da sara masa. Dungurar da wayar ya yi bayan ya katse kiran cikin tsananin takaici. Abun da yake ƙara baƙanta ran General idan ya tuna yanda Nigeria da duniya gaba-ɗaya ta ɗauka da zancen nasarar da su Captain Khamal suka samu akan ƴan ta'addan, duk inda mutum ya duba a social media zancen ake yi ana yaba musu da jinjina musu akan bajintar da suka yi. Kuma daga faruwar abun jiya har Chief zai je ya dubo su da kansa da sauran manyan muƙarabban gwamnati, duk kuwa da tarin sabgogin dake kansu. Tsaki ya ja a fili ya ce "Sai ka ce akansu aka fara fita operation, mu da duk da muke zuwa uban wa ya yi mana haka?" Sumar kansa ya yamutsa cikin rashin sanin abun yi, duk wannan abubuwan ba su wani dame shi ba kamar irin ace za'a ƙarawa Captain matsayi, domin ya san tabbas idan hakan ta faru gaba_gaba Captain zai kamo matsayinsa ko ma ya wuce shi tunda mutum ne shi jajirtacce akan aikinsa, kuma ze iya bankaɗo muguwar harƙallar da yake aikatawa. Table ɗin gabansa ya ƙara bugawa da dukkan ƙarfinsa idanunsa duka a waje ya ce "Impossible! Wallahi ko zan rasa aikina ba zan taɓa bari a ƙarawa yaron nan girma ba." Kamar mahaukaci ya ɗauki wayarsa ya fice fuuuu!! daga office ɗin tamkar zai tashi sama. A hankali ta buɗe idonta tana bin inda take kallo, kunnuwanta na jiyo mata sauti mai kama da maganganun mutane ƙasa_ƙasa. Hannun hagunta ta ji ya ɗaure mata, ga wani abu da take ji daga hannun yana shiga cikin jikinta a hankali. Yunƙurin tashi zaune ta yi, Madam Halima dake zaune a kujerar gaban gadon da take, ta yi saurin tashi tsaye tana faɗin. "Kin farka, sannu Dear." Da ido kawai take bin ta dan ba ta jin abun da take cewa sosai, kamar mai yin magana cikin raɗa haka take ji. Madam Halima ta mayar da ita ta kwanta, cikin kulawa ta ce. "Let me call the doctor" ta juya ta fara tafiya, Yarinyar dake kwance saman gado, ta bi ta ido har ta ɓacewa ganin ta, kalle-kalle ta shiga yi a ward ɗin da suke mai ɗauke da gadajen marasa lafiya guda huɗu, duk yara ne ƙanana kamarta sai masu jinyar su. Tare Madam Halima suka dawo da Doctor Zainab, dudduba jikinta ta yi bayan ta yi mata sannu, d Doctor ta dubi Madam Halima  ta ce "Madam a ba ta ko ruwan tea ne ta sha dan tana tattare da yunwa, anjima idan ruwan nan ya ƙare za'a iya discharging ɗinku, because gaba-ɗaya results ɗin gwaje-gwajen da aka yi mata ya nuna ba ta da wani ciwo mai illa a jikinta." Madam ta ce. "Masha Allah, Mun gode sosai fa Doctor." Doctor ta yi murmurshi ta ce. "Don't mind." Sannan ta shafa cukurkuɗaɗɗan gashin Yarinyar ta ce. "Cute Baby Allah ya ƙara lafiya." Da ido kawai yarinyar ta bita. Bayan fitar Doctor, Madam Halima ta bar ta a hannun wata Nurse ta tafi haɗo mata kayan tea ta dawo. Har lokacin idanunta biyu ba ta koma barcin ba. Bayan ta haɗa mata tea ɗin ta tashe ta zaune ta jingina bayanta a jikin pillow sannan ta ɗauko cup ɗin da spoon ta deɓo tea ɗin ta kai bakinta. Kawar da kai ta yi dan ba ta taɓa ganin irin wannan abun ba. Madam Halima ta kamo hannunta ta ce "What happen?" Duk da ba ta ji abun da ta ce sosai ba amma sai ta girgiza mata kai. Tsayawa Madam Halima ta yi tana kallon ta, har yanzu yanayinta ya nuna tana cikin tsoro, ba tare da ta yi zato ba ta ji cikin muryar yara  da ƙarfin sauti ta ce. "Zan yi fitsari." Madam Halima da ta yi tunanin duk  yanayin tsoron da yarinyar take ciki ne yasa ta yin maganar da ƙarfi, cikin farinciki ta ce. "Alhamdulillah, baki ya buɗe kenan?" Yana nan kwance Likitan da ya je ɗauko masa wayarsa ya dawo ya kawo masa. More than 50 missed call ya tarar, fiye da rabi duk na Family ɗinsa ne. Numbern Mahaifiyarsa da ya yi saving da First  love ya fara bin bayan kiran, amma har ya kira sau biyu not respond, numfashi ya sauke ya kira numbern My wife, still ita ma no respond. Tsaki ya ja ya ajiye wayar  a gefensa tare da lumshe idonsa yana sauraren bugun zuciyarsa, gefe guda kuma raɗaɗi da ciwon harbin jikinsa na ɗan damunsa, musamman da ya kasance sai dai ya kwanta ta ɓari ɗaya. Gently ya ji an turo ƙofar ɗakin an shigo tare da yin sallama, buɗe idonsa ya yi ya sauke akan wanda ya shigo. Lieutenant Faruk ne, da mamaki Khamal yake duban shi ganin hannunsa nannaɗe da bandage, alamar shima an harbeshi. Murmurshi Lieutenant Faruk ya sakar masa tare da sake yin sallama. Amsa masa ya yi a can ƙasan maƙoshi. Faruk ya ƙaraso tare da janyo kujera da hannunsa mai lafiya ya zauna a gabansa. "Good Morning Captain" Ya faɗa cikin respect. Ɗaga masa kai kawai Captain ya yi. Cikin kulawa Faruƙ ya ce "Ya jikin naka?" Cikin dakakkiyar muryarsa ya ce. "Alhamdulillah, and you?" Faruk ya ce. "Da sauƙi Alhamdulillah." Jinjina kai Captain ya yi tare da runtse idanunsa, lokaci ɗaya kuma ya buɗe idon kamar an tsikare shi ya ce. "Faruk I want to ask you something?" Faruk ya ce. "Okay Sir." Captain yana kallon cikin idonsa ya ce. "Akwai wata little Baby da na ɗauko jiya tana ina, ance ba'a ganta ba?" Faruk ya ce. "Tana cikin asibitin nan, ana bincikar lafiyar jikinta, Madam Halima ce tare da ita." Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi ya ce. "Ina fatan dai babu wani abu da ya same ta ko?" Lieutenant Faruk ya ce. "Babu Sir." Ajiyar zuciya ya ƙara saukewa, yana jin yanda nutsuwa ta fara mamaye zuciyarsa. Faruk ya cigaba da magana. "Muna jiran a tabbatar tana cikin ƙoshin lafiya ne kafin mu fara cigiyar iyayenta, su sauran yaran ɗazu aka kaisu gidan gwamnati, za'a miƙa su ga iyayensu, ita kuma ba wanda ya san daga ina take, za'ai cigiyar iyayenta" Da sauri Captain Khamal ya ce. " No, not now." Da mamaki Faruk yake kallon shi, da son jin dalilin da ya sa yace ba yanzu ba. gyaɗa masa kai Khamal ya yi ya ce. "A bar ta a hannun Madam Halima har zuwa lokacin da zan samu lafiya, da kaina nake son yin bincike a kanta." "But Sir...." Ɗaga masa hannu ya yi fuskarsa a haɗe, alamar ya ƙosa da maganganun Faruk, hakan yasa Faruk ya haɗiye maganarsa, amma cikin ransa fal mamaki ne akan abun da Captain ya faɗa. A sanin da ya yi masa mutum ne wanda babu ruwansa da shiga shirgin da ba nasa ba, komai zaka yi sai dai ya bika da ido amma ba zai tanka ba. But bai san dalilinsa na yin hakan akan yarinyar ba. Ɗan taɓe baki ya yi ya miƙe ya yi masa sallama ya fita. Ƙarfe ɗaya saura na rana tawagar su Chief of Army staff ta sauka a Kantagora Army barrack Naija state, direct inda Captain Khamal yake ya ce a fara kai su. Su uku suka fara shiga ɗakin da yake,  Chief da General Ibrahim sai wani Colonel, daga baya kuma Ministan tsaro da na sufuri da wasu jami'an tsaron suma suka shiga. Yana kwance idanunsa a lumshe kamar mai bacci, amma ba baccin yake ba, wani likita na tsaye a kansa yana dudduba shi. Ƙamewa Likitan ya yi ya sarawa su Chief of Army staff tare da welcoming ɗinsu. Hakan ya saka ya buɗe idanunsa ya waiwaya ya kalle su. Da sauri ya ɗago kansa tare da ƙoƙarin yin salute daga kwancen da yake. Chief ya ƙarasa kusa da shi ya kama hannunsa yana murmurshi ya ce. "No need, our Lion the king of the jungle, I salute you Captain Khamal Khamis" Ƙasa ya yi da kansa cikin respect ya ce. "Welcome Sir." Chief ya ce. "Thank you, How are you feeling now?" Ya ce. "Better Alhamdulillah." Chief ya ce. "Masha Allah, Allah ya ƙara lafiya, rundunar soja tana matuƙar Alfahari da samun jajirtacce kamar ka, shugaban ƙasa ma ya yabawa ƙoƙarin da ku kai, duk da baya gari amma ya turo wakilansa, muna tare da ministan tsaro da na sufuri, duk muka zo duba ku." Captain Khamal ya jinjina kai tare da faɗin "Thank you sir" General Ibrahim ya ƙaraso cikin ƙoƙarin ɓoye halin da yake ciki ya yi masa sannu ba yabo ba fallasa, shi ma ya amsa masa a haka. Minista kuwa cikin fara'a ya yi masa sannu tare da yi masa jinjina akan aikin da suka yi. Ta gefen ido General ya dinga hararar Khamal cikin tsananin baƙin ciki. Chief ya zauna a kujerar da Likitan ya kawo masa, yana duban Captain Khamal cikin jinjina ya ce. "Sannu da ƙoƙari Captain, tabbas kai ɗin na daban ne kuma mai sa'a ne ko a cikin sojoji. Irinku Jajirtattu masu aiki domin Allah ƙasar mu take buƙata, da ace ƙasar mu za ta samu kamar ka su fi rinjaye a cikin jami'an tsaro da ma mutane da  an samu sauƙin ta'addanci da duk wani criminals acts a cikin ƙasar nan. An daɗe ba'a samu Nasara a fita operation kamar wannan da kuka fita ba, hakan ya ƙara nuna mana jajircewarka Hukumar sojojin ƙasa ta yaba muku kuma ta jinjina muku." Captain ya ce. "Thank you Sir." Chief ya ce. "Allah ya ƙara lafiya, bari mu zagaya mu duba sauran soldiers ɗin daga nan zamu wuce government House na nan garin, dan miƙa yaran nan ga iyayensu. " Captain ya ce. "Okay Sir, a fito lafiya." Cikin yaƙe General Ibrahim ya ce masa. "Allah ya ƙara lafiya Captain" A ransa kuwa cewa ya yi. 'By the grace of God ba zaka tashi daga wannan ciwon ba sai dai a ɗauki gawarka daga gurin nan, ba dai ka taka da ƙafafuwanka ka bar shi ba.' Da ƙyar Madam Halima ta saka yarinyar, ta sha tea ɗin kaɗan bayan ta saka mata Fo ta yi fitsarin a ciki. Abun mamaki kuma mijin Madam Halima yana kawo  Banana ta karɓa ta fara ci cikin sauri-sauri, hakan ya ƙara nuna tana jin yunwa sosai. Cikin mamaki Madam Halima ta dubi Mijinta Captain Abdussamad ta ce. "Captain ka ga abun mamaki, yarinyar nan ɗazu daƙyar ta sha tea kamar zata yi kuka, amma ka ga yanzu yanda take cin Bananan." Captain dake kallon Yarinyar ya ce. "May be tana son ta ne that is why." Madam Halima ta jinjina kai ta ce. "She is so cute, amma har yanzu a cikin firgici take, ta ƙi sakin ranta ta nutsu, kamar ma a firgice take da environment ɗin" Captain ya ce. "Dole ai, tunda babu wanda ya san tsawon lokacin da ta ɗauka a hannun azzaluman mutanen can, kuma a cikin dokar daji" Numfashi Madam Halima ta sauke ta ce. "Allah Sarki, yanzu haka maybe iyayenta sun yi cigiyar ta har sun gaji." Captain ya ce. "Wa ya faɗa miki iyaye suna gajiya da neman ɗansu? Ai sai dai masu bincika musun su gaji." Madam Halima ta ce. "Haka ne, amma yarinyar nan ba ta mun kala da 'ƴan Africa ba, ko shi yasa idan muka yi mata magana ba ta ganewa, ko ba bahushiya bace? amma kuma ɗazu ta yi mun Hausa." Captain ya ce "Komai ma zai iya kasancewa, may be ba ta jin hausan ne sosai." Jinjina kai kawai Madam Halima ta yi Idanunta akan yarinyar, ita kam har cikin ranta take jin tausayi da k'aunar Yarinyar, ko dan ba ta Ƴaƴa ne ya saka? Gaba ɗaya ransa a dagule yake, yana cigaba da lissafin ta ina ze sake ɓullowa lamarin, dan wannan galabar da aka samu akan 'yan ta'adda kamar koma baya ne a gare shi, da samun raunin yadda a tsakanin sa da su Gwaska. Wayarsa ce ta fara ringing, kamar ba ze ɗauka ba, se kuma ya miƙa hannu ya ɗauka, cikin hamzari ya miƙe tsaye yana sarawa wanda yake Maganar da shi a waya, kamar yana gabansa. Daga cikin wayar aka ce "Mr. President ya dawo gari, ze yi zaman gaggawa da mu yau da daddare, akan harkar tsaro" General Ibrahim yace "ok Sir" ya sake ƙamewa, sannan ya ajiye wayar. Yana ajiyewa ya wani sake haɗe rai, tare da yin ƙwafa, ya daki tebur yai waje cikin sauri. Manya manyan masu ruwa da tsaki a harkar al'amuran tsaro duk sun hallara, kama daga Chief of Army staff, AVM General General na sojoji, babba da ƙaramin ministan tsaro, masu bawa shugaban ƙasa shawara akan harkar tsaro, da sauran manya masu bada shawara akan harkar tsaro, da shi kansa shugaban ƙasan, sun hallara a cikin katafaren ofishin da shugaban ƙasa ke ganawar sirri, babu ɗan Jarida babu masu saka ido, babu duk wata Camera ta ɗauka, saboda ganawa ce ta sirri. Shugaban ƙasa yai gyaran murya cikin harshen turanci yace "To nayi farin ciki matuƙa da irin nasarar da jami'an tsaron mu suka samu, akan ceto yaran nan da aka sace, dama gaba ɗaya idon duniya a kanmu yake, dan ganin ƙoƙarin da za muyi, to Alhamdilillah yaran sun kuɓuta kamar yadda na samu labari, duk da wasu sun rasa rayukansu, mun bada sanarwar jaje ga ahalin wannan yara. Yanzu abu na gaba shine, wane mataki zamu ɗauka akan kawo ƙarshen sace mana ɗalibai da ake a makarantun kwana da ma na jeka ka dawo? Ƙaramin ministan tsaro yace "Ai your Excellency, a nawa ganin a rufe Dukkanin makarantun sakandare da na primary na yankin gabashin ƙasar nan, tun da a nan rashin tsaron yake, zuwa a ga yadda hali ze yi" Baban ministan tsaro yace "A' wannan ba shawara bace ai, shikenan se mu ajiye yaranmu a gida ba makaranta? Wanan ai kawo koma baya ne da naƙasu ga ilimin al'ummar yankin" Ƙaramin ministan tsaro a ransa yace "wannan shine baban burinmu, al'ummar yankin suyi ta saun koma baya" Haka akai ta tattaunawa, har aka samu matsaya akan cewar, dole a rufe makarantun a dakatar da ilimin wannan yankin, har se zuwa lokacin da za'a samar da tsaro. Magana ta gaba kuma, shugaban ƙasa yai bayanin cewa, akwai ƙasashen da sukai alƙawarin tallafawa ƙasa da maƙudan kuɗaɗe dan siyo makamai da za'a bawa Sojoji dan cigaba da yaƙi. Nan suma sojojin suka faɗi ƙorafe ƙorafensu, abubuwan da suke buƙata, da yadda kuɗaɗen da ake warewa harkar tsaro ba sa isa yadda Yakamata. Shugaban ƙasa yai alƙawarin kafa kwamitin bibiya, akan yadda ake amfani da kuɗaɗen da ake warewa harkar tsaron. Aka tattauna batutuwa masu mahimmanci, da shawarwari akan yadda za'a shawo kan matsalolin tsaro. General Ibrahim yana komawa gida, ya samu wani keɓaɓɓen guri, ya fara kiran waya. Dashshiyar muryar Gwaska ta bayyana a cikin wayar "ya, dama kai muke dako, kunyi zama da shugaban ƙasa, me ake ciki?" "Dama kiran da nai maka kenan, yau me magana da yawun shugaban ƙasa ze sanar da rufe makarantun firamare da na sakandare na yankin gabashin ƙasar nan, har zuwa lokacin da za'a samu tsaro, Sannan akwai maƙudan kuɗaɗe da za'a bawa ƙasar nan tallafi dan siyo makamai da cigaba da yaƙar ku" gaba ɗaya ya kwashe Abinda aka tattauna ya gayawa Gwaska. Wata irin mahaukaciya dariya Gwaska ya saki, kai da jin wannan dariya ka san me ita ya samu rauni a imaninsa ya tsagaita da dariyar yace "Yankin mu na ta samun koma baya ta kowace siga, yayin da ta wani fannin hakan ya zama hanyar samawa ƙasa hanyoyin samun kuɗaɗen da manyan ƙasar suke kashe mu raba. Hakan yayi kya a satin nan zamu ƙaddamar da babban harin da yafi wanda mu kai a baya. Muna nan muna cigaba da saurarenka, duk yadda ake ciki game da shirin rundunar ku, muna sauraren ka, abunda ya shafi shirin gwamnati shima muna da masu kawo mana rahoto, ka huta.." daga haka Gwaska ya kashe wayarsa. Bayan Sallar la'asar Captain yana zaune yana shan coffee ɗin da ya saka aka kawo masa a hankali aka turo ƙofar ɗakin da yake da ƙarfi. Ɗaga kansa ya yi cikin sauri saboda ƙamshin da yaji ya ziyarci hancinsa, da mamaki yake kallon matashiyar kyakkyawar matar dake tsaye tana kallon sa hawaye na shatata daga cikin idanunta. Ajiye cup ɗin hannunsa ya yi cikin tsananin mamaki, duk da tsohon cikin da matar ke ɗauke da shi haka ta tako cikin gudu ta zo ta rungume shi tana sakin ajiyar zuciya mai ƙarfi tare da fashewa da kuka. Ɗan ture ta ya yi daga jikinsa a hankali saboda yanda take ƙoƙarin fama masa ciwukan jikinsa. Cikin dauriya ya kwantar da kanta akan kafaɗarsa, Gently ya shiga bubbuga bayanta alamar rarrashi cikin sauke ajiyar zuciya ba tare da ya ce komai ba. Lumshe idanunsa ya yi yana shaƙar ƙamshinta da ya yi bala'in missing ɗinsa. Tsahon 5 minutes suna haka sannan ya ɗago ta ya shiga share mata hawaye tare da girgiza mata kai. Ta gane me yake nufi, hakan yasa ta haɗiye kukanta. Cikin muryar da ta ci kuka ta ƙoshi ta ce. "My Man, sun kusa kashe mun kai ko?" Hannunta ya kamo ya shiga murzawa slowly cikin tsananin ƙaunarta ya ce. "Ba su kusa ba, tunda Allah bai yi ba gani a raye." Ta ɓata fuska ta ce. "Wannan manyan raunikan dake jikinka fa My Man? Na san ba dan Allah ya yi da nisan kwananka a gaba ba da tuni na rasa ka." Ta ƙarashe maganar tana sakin kuka. Cikin sanyin murya ya ce. "Aikin sojan kenan My Wife, kar ki manta sai da muka rantse za mu kare rayukan al'umma kafin mu fara aikin. Ki bar kukan nan haka, just pray for me." Ta ja hanci ta ce. "Allah ya baka lafiya My Man." Karan hancinta ya ja tare da ɗan yin murmurshi ya ce. "Ameen My wife, ya aka yi kika san ina nan har kika zo?" Ta zauna a gefensa tana kallon cikin idonsa ta ce. "Ta yanda labarin irin bajintar da kuka yi ya zagaye duniya, kafafen yaɗa labarai ko ina ana ta sanarwa, kuma an kira Baffa an sanar masa. Yana shafa cikinta a hankali ya ce. "How was My unborn Baby? I missed both of you so much." Kwantar da kanta ta yi akan kafad'arsa ta ce. "We missed you too, Baby yana lafiya, sai dai jiya na san yanda ban yi bacci ba shima bai yi ba, saboda yanda ya dinga wutsil-wutsil kamar zai fito duniya ya tarewa Dad ɗinsa harbin da aka yi masa." Murmurshi ya yi irin wanda shi kansa ya manta rabon da ya yi kamar sa ya ce. "Zai iya ai, tunda shi ma Jarumi ne kamar Babansa." Dai-dai nan aka turo ƙofar ɗakin aka shigo. Share, share share Please Nimcyluv Zee kumurya Ayshercool. 'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm! BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE I'm selling MTN data with this cheap price MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month Airtel,9mobile and Glo also available. *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* Whatsapp OR Call *08066268951* [9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷* Bright pens✍🏾 Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya *5.....* Elegant Online writer's _Domin samun Complete labaran mu, na littafai kala-kala, kuyi following wannan Acct ɗin a Arewabooks👇🏾_ https://arewabooks.com/u/nimcyluv Wani irin kallo Captain ya bi Faruk da shi, yana son gazgata abun da kunnuwansa suka jiye masa ya fito daga bakin Faruk. "Do you mean my Abra?" Yai maganar yana nuna kansa da yatsansa. Faruk cikin damuwa yace "eh, Abra ba'a ganta ba, na duba duk in da ya dace a cikin barrack ɗin nan ba'a same ta ba" "Shhhhhh, kar ka gayamin maganar banza mana Faruk, ya za'ai ace yarinyar nan ta ɓata how comes? Kaga, i have no option for now am going make sure you bring back my daughter" "Haba Captain, ta ya zan maka ƙarya, Wallahi a..... Be ƙarasa maganar ba Captain Khamal ya ɗaga masa hannu yace "na gama Magana, duk in da 'ya ta take ka tabbatar ka nemo ta ka kawo min a bata" daga haka ya cigaba da takunsa sannu a hankali me kama da na ƙasaita yaa bar Faruk a tsaye a gurin. Faruk yace "ya salam, Madam Halima kin kashe ni ina kika bar yarinyar nan ta tafi? Ya a kai ta ɓata?" ya ƙarasa maganar yana sauke wani irin nannauyan numfashi, kafin daga bisani ya juya cikin sassarfa ya nufi wani sashi na barrack ɗin. Zaune take a kan gwiwonwinta, ta zubawa kyakkyawar yarinyar me kama da 'yar larabawa idanu, hawaye ne kwance akan fuskar yarinyar, hannunta ɗaya riƙe da teddy bear, ta zura yatsanta ɗaya a baki tana tsotsa kamar me shan nono. "Hey look up, kina son chocolate?" Tai Maganar tana kallon idon Abra. Shiru Abra tai tana binta da kallo, dan sam ba ta ji me tace ba. "In baki chocolate, ai zaki sha ko?* Still Abra bata amsa ba, kallonta kawai take kamar wata gunki. Salima ta tashi ta ɗakko jakarta,ta ciro Chocolate ta miƙawa Abra, maimakon Abra ta karɓi Chocolate ɗin, se ta fashe da kuka tana kiran "Abbi, Abbi". "Shhhhhh, is ok i will take you to your Abbi, amma ki yi shiru, I have plenty chocolate and teddies, zan baki idan ki kai shiru" Ƙaro sautin kukan Abra tai, tana kiran sunan Abbi. "Ji min makirar yarinya zata ɗaga min hankali, will you shut up?" Babban abunda ya bawa Salima mamaki, be wuce yadda sam Abra ba ta responding ga Maganar da duk za tai mata ba, kukanta kawai take yi. Salima tace "what so ever, da ke zanyi amfani in cika burina, se na nunawa matar Khalid bariki iyawa ce, sena rusa gidan da mijin da take taƙa ma da shi. TWO DAYS BACK. Kwana biyu da suka shige! tun bayan faɗan nan da Salima sukayi da Naima, Salima ba ta sake komawa gurin Khamal ba, se ta fita waje ta kama Hotel tai zamanta, sakamakon rashin posting ɗin su da ba'a yi ba. Tun abun da ya faru a tsakanin ta da Na'ima matar Khamal, tace se ta ga abunda ya turewa buzu naɗi in dai akan Khamal ne, se ta gwadawa Na'ima kalar nata rashin mutuncin da iya barikanci. Khamal kuwa da ƙyar ya rarrashi Na'ima, kasancewar ta mace me tsananin kishin tsiya, ba ta da haƙuri ko kaɗan akan kishi, ita da ta zo dubiya ƙarshe se da su kai faɗa da Khamal akan Salima. Na'ima ta daɗe da sanin Salima na bibiyar Khmal, amma tafi kowa sanin halin mijinta, mutum ne kamili da be ɗau duniya da zafi ba, sam ba shi da wannan ɗabi'ar ta kule kulen mata, hasali ma mutum ne me tsare gida, wanda ba'a kawo masa wargi, amma Salima ke ta cusa kanta a wajensa. Tun kan ya Auri Na'ima, Salima take son sa, amma kasancewar Salima ba mutuniyar arziki ba ce ya sa ko saurararta ba ya yi sam, ya sha yi mata gargadi da jan kunne, akan ta fita daga rayuwar sa amma taƙi, se da ta ƙure shi ta kai ga ta sa ya gaya mata miyagun maganganu, amma still ta ƙi barin rayuwarsa, sannan tai alwashin se ta ga bayan Na'ima, se ta raba shi da ita. A ranar da Na'ima su kai faɗa da Salima, washegari ta shirya tace ba zata cigaba da zama ba, tafiya za tayi gida. Captain yace "dear, yanzu tafiya zaki ki barni a nan, nika ɗai?" "To zaman me zan cigaba da yi, ka san EDD ɗina ma ya kusa, gara ina gida haihuwa ta zo min, tun da suna kula da kai kuma an kusa sallamar ka" Haka ya ƙyaleta, tai shirinta ta juya Kanon dabo. Washegari da safe wajen ƙarfe sha ɗaya na safe, Salima tai wanka ta shirya ta koma gurin Khamal, a hanyar da zata sada ta da ward ɗin da yake, ta haɗu da Faruk hannunsa ɗauke da Abra. Ta tsaya suka gaisa, ta kalli Abra tace "ina ka samo wannan cute Babyn haka?" Nan Faruk yai mata bayani yace "a gurin operation Captain Khamal ya tsinto ta, tana gararanba a cikin daji, Kuma ikon Allah, Allah ya haɗa jininsa da ita sosai" Salima tace "ita ma kidnapping ɗin nata a kayi?" Yace "Sanin gaibu se Allah" Tace "ikon Allah, to an gano iyayenta?" Yace "A'a, ba'a gano su ba, tana gurin wata staff ɗin mu ne, Madam Halima matar Captain Abdussamad Goza" Tace "ok, Allah sarki shes cute Masha Allah, to yanzu ya za'ai da ita? Tun da ba'a samu iyayenta ba?" Faruk yace "Ai da kyar ne idan ba Captain ne ze ɗau yarinyar nan ba, dan kamar sun daɗe da sanin juna, yana son yarinyar sosai dan har ya raɗa mata suna, it ma Abbi take ce masa, kamar sun san juna,. Se dai be gayan abun da ya yanke ba amma nafi kyautata zaton da ita ze koma, ya riƙeta kan a ga iyayenta" Ɗan shiru Salimaa tai kan daga bisani tai ajiyar zuciya tace "thats good" daga nan ta wuce zuwa in da Khamal yake. A wannan karon ma bata samu kulawa daga Khamal ba, sema tijarar da yai mata ya koreta daga ɗakinsa. Idan da sabo ta saba da wannan abubuwan na wulaƙanci da hantara da yake mata, amma sam ba ta damuwa, ita dai burinta ya amsa yana sonta. Washegari ta koma cikin barrack, cikin ikon Allah ta bi ta compound ɗin su Madam Halima, abun mamaki ta ga Abra a tsaye hannunta da teddy ɗinta, tana rarraba manya manyan idanunta tana ƙarewa gurin kallo. Ƙarasawa in da take Salima tai, ta durƙusa a gabanta tace "cute baby, how are you?" Ɗan ja da baya Abra tai tana kallon Salima. Wani tunani ne ya faɗowa Salima, ta kuma matsawa kusa da Abrar tace "ina da sweet, ai zaki sha ko in baki?" Still Abra ba ta amsa ba, saboda ba ta iya jin abunda Salima ke faɗa. "Ok, zomuje in kai ki gurin Abbi" Bakin Salima ta ƙurawa ido, taga kamar Abbi tace. Ta miƙawa Abra hannu, aikuwa ba musu ta bita, saboda ganin laɓɓan Salima sun ambaci Abbi. Salima ta ɗauki Abra ta tafi da ita. Yadda a kai Abra ta fito kuwa shine Madam Halima ce t fita  tare da Abra, da suka dawo ne, taga Abra ta tsaya tana kallon murguza murguzan karnunkan da ke kaiwa suna komowa a compound ɗin, ta ɗauke Abra ta shiga da ita gida, a zatonta ko tsoronsu take ji, sedai bayan shigarta wanka, Abra ɗin ta sake fitowa tana kallon karnukan, wanda a nan ne Salima tai awon gaba da ita, tare da ƙudurce wani abu a ranta. Tun da Madam Halima ta farga Abra ta ɓata ta shiga cikin tsananin damuwa da tashin hankali, saboda Abra ta shiga ranta matuƙa, sannan da ya zata fara bayanin yarinyar da aka bata ajiya ta ɓata?. Captain Khamal kuwa ji yake tamkar zuciyar sa zata fashe, maimakon yai murna ze koma garinsa da yai wata da watanni baya nan, amma ya kasa farinciki saboda ɓatan Abra, ji yake kamar 'yar cikinsa ce ta ɓata, haka nan yaji yana ƙaunar yarinyar, dan har a wani sashi na zuciyar sa yana jin idan iyayenta suka bayyana be san ya zeyi ba, sakamakon tsananin ƙaunar yarinyar da yake yi. Shiru yai yana tuna innocent face ɗinta,tana kiransa da Abbi, wanda har cikin ransa yake jin sunan da take kiran na shi da shi. Tunani yake akan how taje Wannan dajin? Waye ya kaita? A yaya ta rayu? Suwaye iyayenta? Gashi tun da ya tsince ta shi dai be ji tai wata magana ba, da zata ba shi haske game da ita ba, Abbi kawai shi ne abun da yaji bakinta yana faɗa. Wata zazzafar iska ya furzar daga bakinsa, yana jin tamkar ya koma Naija State, tabbas ba dan an riga an gama shirya dawowarsa ba, da ba in da za shi se an nemo masa Abra ɗin sa, amma a yanzu ma ba ta ɓaci ba, nan da 'yan awanni idan ba'a ganta ba, dole ya koma Naija state, jikinsa ya na ba shi Akwai wani al'amari me girma game da Yarinyar. Faruk kansa ya shiga damuwa da tashin hankali, akan ɓatan Abra, balle Madam Halima da megidanta, sun fi ɗaga hankalinsu akan kowa, nan da nan aka baza cigiyarta a cikin barrack ɗin. Salima kuwa Abra ta addabeta da kuka, fafur yarinyar nan ta ƙi jin rarrashi, gashi maganar duniya ta ƙi sauraron Salima. Salima ta ɗauketa ta fita da ita, wani babban shop ta kai Abra tai mata siye siyen, kayan ci da na wasa, se dai duk da hakan Abrar ta ƙi sakin jikinta da Salima, yadda take nunawa ma kamar tsoronta take ji. Salima ba ta damu da hakan ba, burinta kawai take fatan ya cika, ta tafi da Abra gurin wasan yara, ta din ga yiwa Abra ɗin hotuna. Sai magariba Sannan suka koma masaukin Salima, sedai  suna komawa Abra tace ba ta san zace ba, ta ɗora da kukanta a in da ta tsaya tana kiran "Abbi" Salima tace "Ohh God, this pikin want spoil ma plans" Ta kaɗa ta raya, amma Abra ta ƙi bacci, kuma taƙi yin shiru, tai rarashin tai shouting ɗin, amma kamar ta na yi da gunki. Ba shiri ta ɗau Abra ta nufi cikin barrack ɗin, kai tsaye ba tare da shakkar komai ba, ta nufi gidan Madam Halima, ai kuwa ta tarar da su a ƙofar gida tare da Faruk, da wasu sojoji, Faruk ya rasa in da ze sa kansa, saboda yadda ya sha kiran waya a gurin Captain Khamal akan Maganar Abra. "Wa nake gani haka kamar Abra?" Yai maganar yana kallon in da Salima ke tahowa. Duk da dare ne amma ko ina da hasken fitilu. Salima ta ƙaraso tace "lafiya na ganku a tsaye haka?" Faruk yace "wacce irin magana ce wannan, kin ɗagawa mutane hankali, a zatonmu Yarinyar nan ɓata tayi". Salima cikin ko in kula tace "No, na zo wucewa ne na ganta, na ɗauke ta mukaje na sai mata ice cream, that's all" Mijin Madam Halima yace "amma haka akeyi, ki ɗau yarianya ba excuse ba wanda ya sani, duk kin ɗaga mana hankali, yarinyar nan fa ajiyar ta aka bamu" Salima tace "to ai ni banga wani laifi da nayi ba, yanzu ba gashi na dawo da ita ba" Abrar kuwa Faruk take miƙawa hannu, tana maimaita Abbi. Ya karɓeta tare da rungumeta a jikinsa yana faɗin "Am sorry dear" se jera ajiyar zuciya take. Ban da Allah yasa Faruk da mijin Madam Halima na gurin, da se sun bawa hammta iska, dan ba ƙaramin haushin abunda Salima ta aikata ba Madam ta ji, yadda ta ɗaga musu hankali da yawa. Faruk kuwa ya dudduba Abra ya ga ba abunda ya sameta, dan haka ya ƙudurce, a gobe zuwa jibi ze gaggawar zuwa Kano, ya danƙawa Khamal Abra, idan ya so koma ya ze da ita yayi, tun da Salima ta fara ɗaukarta ba wanda ya sani, nan gaba be san me za tai mata, saboda ya san Salima farin sani, sun taɓa aiki tare, ya san irin yadda take faɗi tashin samun abunda zata samu shiga a gurin Khamal. Labarin da aka tashi da shi yau ne, yai matuƙar girgiza al'ummar ƙasar, 'yan ta'adda sun tare manyan motocin cike da ɗaliban jami'a masu zuwa excution, sun yanka wasu daga mazan ciki, sun yi awon gaba da 'yan matan da malaman su zuwa cikin daji, a can Jihar Kaduna.    Lamarin ya girgiza al'umma da dama dake ƙasar Nigeria, kasancewar ba a warke daga jimamin, ɓatan ɗalibai 'yan makarantar Sakandire da aka kwashe ba, wanda sojoji suka ƙwato su da kyar, katsam se ga wannan mummunan labari ya sake cika gari. A ranar da aka sace 'yan makarantar washegari 'yan ta'addan suka saki video suna demanding 200millon as a ransom, a cikin kuɗin da gwamnatin tarayya za ta karɓa na tallafi daga ƙasashen turai, suka bada sati guda cewar idan ba'a biya kuɗin ba, za su dinga yiwa matan Fyaɗe suna yanka su ɗaya bayan ɗaya, kuma muddin aka tura sojoji za su kashe su baki ɗaya, Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Tun bayan dawowar Khamal, 'yan dubiya da 'yan Sannu da zuwa suka cika gidan, aka dinga tururwar zuwa duba Khamal, Na'ima se rawar kai take gami da taraiyar sa, da yi masa hidima iya iyawarta, dan a duniya ba ta da burin da ya wuce ganin ta sanya Khalid farinciki, saboda tsananin soyayyar da take masa. Duk da tsufan da cikinta yai, shima da raunin da ke jiinsa, da batun ɓatan Abra da yake damunsa, be hana su nunawa juna tsantsar soyayya da yadda su kai kewar juna ba. Faruk kuwa se farinciki yake, akan yadda ze  mayarwa da Khamal amanarsa, ya san ze farinciki ƙwarai.   Cikin tsananin tashin hankali da kaɗuwa, Captain Khamal yake kallon labarai, da tashin hankalin da al'ummar wannan ƙasa suka tsinci kansu a ciki, su gasu da su kai wannan opretion ko warkewa ba suyi ba, an kuma kai wani harin, wanda wasu sojojin za'a kuma ɗiba suje fafutukar karɓo su, babban abunda ya sake ɗaga masa hankali be wuce yadda ya shiga tunanin ya akai 'yan ta'adda suka san za'a bawa gwamnatin tarayya tallafi? Bayan ba aji hakan daga bakin gwamnatin ba, anya babu haɗin bakin wanda suke jikin gwamnatin? Yanzu iyalan su Jamil da aka kashe, babu wani tartibin abu da Gwamnati za tai wa iyalansu, da ze rage musu raɗaɗi, wanda gwamnati zata nuna damuwarta da rasa ɗan ƙasa da akai, a bakin aikin kare ƙasarsa, haka za'a kuma kwasar wasu a kai su daji. Wani mugun sarawa kansa yai, tare da tunanin meye mafita akan wannan lamari da ya ƙi ci, ya ƙi cinyewa. Ƙarfe huɗu daidai, Faruk yana cikin garin Kano tare da Abra, shima ya warke daga harbin da ke hannunsa. Khamal yana kwamce akan 3seater, Na'ima na jikinsa a kwance tana rarrashinsa, ganin yadda ya shiga damuwa, saboda wannan abu da ya sake faruwa mara daɗin ji, se ƙoƙarin kwantar masa da hankali take, saboda ya shiga damuwa sosai. Knocking ɗin ƙofar falo aka fara yi, Na'ima tace "Baby bari in buɗe ƙofa" Khamal yace "No dear, zauna inje in buɗe ki huta, kar ki wahal da kan ki da babyna" Murmushi tai tace "My sweet, kar ka damu dama ance in dinga exercise, bari in buɗe" Ya jinjina mata kai, ta miƙe tsaye tana tafe sannu a hankali, cikin salon tafiya irin ta masu juna biyu. Tana buɗe ƙofar ta ga Faruk tsaye, cikin ƙananan kaya, murmushi yai tare da sara mata. Ita ma murmushin tai tace "kai ne a tafe ba sanarwa? Ya jikin naka?" Faruk yace "Alhamdilillah" Ba shi hanya tai ya shigo, se yanzu ta lura da ƙaramar kyakywar yarinyar da yake tafe da ita. Abra na hango Khamal, ta ruga da gudu ta nufe shi tana kiran "Abbii" Da azama ya tashi zaune, duk da haryanzu yana jin ciwo a in da aka harbe shi. Abrar ta faɗa jikinsa ta ruƙunƙume shi, Captain ya rungumeta sosai a jikinsa yana faɗin "My daughter, i missed you" ta ɗago tana bin idon Khamal da kallo, tana murmushi. Faruk ya sarawa Khamal sannan ya zauna yana faɗin "Yallaɓai ya jikin?" Khamal yace "jiki Alhamdilillah" Na'ima kuwa kallonsu take cike da rashin fahimta, ina Captain ya samo 'ya har ta ke kiransa da Abbi, ta daɗe da sanin sa kenan?. Khamal ya kalli Na'ima yace "Madam, a kawo musu ɗan abun taɓawa" Ta miƙe ta nufi hanyar kitchen, zuciyarta fal wasi wasi da tambayoyi. Khamal ya kalli Faruk yace "ya akai aka ganta?" Nan Faruk ya gayawa Khamal duk abunda ya faru, Captain Khamal yai shiru tare da jinjina kai yace "Salima again?" Shiru ya ɗanyi yana nazari, sannan yai ƙwafa, yana sake rungume Abra a jikinsa. Ya nisa yace "Faruk, ashe abunda ya kuma faruwa kenan, an kuma kwashe ɗaliban jami'a?" Faruk ya girgiza kai yace "bari kawai Captain, abun akwai tashin hankali, kullum abun ƙara worst yake, matsalar sake yawa take, kalli uban wanda muka kashe, da wanda muka kama, amma bayan ransom ɗin da suka buƙata har da se an sakar musu yaransu da muka kama, within seven days" Khamal ya cije laɓɓansa na ƙasa, yana wani irin huci yace "Why? And When? Yaushe zamu samu 'yan ci, hankalinmu ya kwanta na 'yan ƙasa ya kwanta, har ɗan ta'adda yasan za'a bawa gwamnati tallafi, ya buƙaci wani abu a ciki, wannan wane irin abu ne, idan da gwamnati suke faɗa meye laifin innocent souls da suke sacewa suna cin zarafin su, yaushe hankalinmu ze kwanta? Gwamnatin mu na iya ƙoƙarin ta, mu kanmu jami'am tsaro muna namu ƙoƙarin, to a ina matsalar take? Waye me laifin?" Ya ƙarasa maganar yana huci. Faruk yace "hakane, kowa yana ƙoƙari, amma akwai buƙatar mu gyara mu sake zage damtse gaba ɗayanmu, mutanen nan 'yan uwanmu ne, a cikin mu suke, meyasa za su zage su dinga kashe mu? Me mu kai musu? Akwai wani abu a ƙasa da yake buƙatar dogon Nazari". Captain yai ajiyar zuciya yace "hakane, kuma idan aka tsaida hankali guri ɗaya, za'a a iya samo bakin zaren" Faruk yace "hakane, Allah ya iya mana" "Ameen" Khamal ya amsa. Na'ima ta dawo Falon ta kawowa su Faruk snacks, da ruwa da lemo me sanyi. Abra tai ta bin abunda ta kawo ɗin da kallo, Captain ya ɗakko donut ya miƙa mata. Ta karɓa maimakon ta kai bakinta, se ta hau leƙa ɗan ramin nan na jikim donut ɗin tana dariya, a zatonta abun wasa ne. Sai da Khamal, ya ɗauka ya ci sannan ita ma ya nuna mata yadda za ta ci, sannan Abra ita ma ta fara ci. Faruk da Khamal suka shiga hira abunsu, suna cigaba da tattaunawa akan matsalar tsaro, Abra na jikin Khamal tana ta kaɗa ƙafa tana ciye ciyenta. Faruk ya miƙe tare da cewa "to Yallaɓai, ni zan tafi and Alhamdilillah na dawo da amanar da aka bani, ina fatan Ubangiji Allah ya taya riƙo, sannan ya ƙara maka lafiya" Captain yace "Ameen ya hayyu ya ƙayyum, nagode ƙwarai Faruk, ka gaida gida". Faruk ya juya ze tafi, Na'ima tace "a'a ya na ga kuma ze tafi ya bar yarinyar?" Khamal yace "karki damu zan miki bayani" Faruk ya juya tare da ɗagawa Abra hannu, itama ɗaga masa hannu tai tana masa murmushi. Na'ima ta dawo da dubanta kan Khamal tace "Nifa ban gane ba, bayanin me za kai min?" Khamal yace "Calm down baby, ki zauna mana" Zama tai tana tura baki tace "Gaya min, meye ma'anar wannan abun? Wacece wannan yarinyar?" Khamal ya gyara zamansa, ya gayawa Na'ima komai, tun daga tsintar Abra da yai har zuwa yanzu, sannan ya ɗora da cewa "A hukumance ma, hukumar mu sun san da zaman Abra a hannu na, za'a cigaba da neman iyayenta, in Allah yasa an samesu shikenan, idan ba'a same su ba ina son Abra ta cigaba da zama tare da mu a nan, mu riƙe ta tamkar 'yar da mu ka haifa". "Dan Allah ɗan saurara mana Khamal, wai shekaruna nawa ne yanzu a duniya da har kake tunanin zaka iya raina min hankali? Wato ka mai da ni ma wata nusarar mahaukaciya, wadda ba ta san me take ba, kaje karuwa ta haifa maka 'ya, kuma ka ɗakko kace in riƙe kana cikin hayyacinka kuwa? Kai ina zaton sautin ƙarar bom da ka saba ji a daji ya taɓa maka ƙwaƙwalwa ba ka sani ba. To bari kaji in gaya maka, wannan 'ya Wallahi ba zan riƙeta ba, ka mayarwa da uwarta can da kuka haifeta tare ta riƙeta, dama aiku sojoji ba wanda za'a bawa amana bane, wato uwarta na gudun abun kunya ba zata riƙe ba se ni, karkatacciyar bishiyarka me daɗin hawa, ni zan riƙe 'yar karuwa to Wallahi da sake" "Shut up Na'ima!" Tsawar da Khamal yai mata se da ɗan cikinta ya juya, saboda tsabar razana da ta yi. "Ni kike cewa na haifi 'ya da karuwa a waje? Na'ima yanzu shedar da zaki bayar a kaina kenan? Kin fi kowa sanik ni ba mutumin banza bane" Cikin tsiwa tace "Abu na ɗan Adam kowane lokaci ai yana iya canzawa, kuma in da kake zuwan tunda ba wani ne yake binka ya ga me aikata ba, ai Allah kaɗai ya san me kake yi, dan haka Wallahi ba zan riƙe 'yar karuwa ba, ka maida ita gurin uwarta tun da wuri". Khamal yace "Na'ima, nan gidana ne, kuma ko 'yar karuwa na kawo nace ta zauna, gida na ne ba naki ba, idan ba zaki iya riƙe Abra ba, zaki iya tattara kayanki ke ki koma in da kika fito". A razane ta kalli Captain Khamal tace "yanzu zaka iya rabuwa da ni, da ɗanka na sunna da zan haifa akan 'yar da karuwa ta haifa maka Khamal?" Yace "yes of course, idan ba zaki zauna da Abra ba, ni zan iya rabuwa da ke, kuma ko ki yadda tsintar Abra nai, ko kar ki yadda ki cigaba da zama akan bakanki cewar 'ya ta ce da na haifa a waje, wannan ke ta shafa amma Abra a nan zata zauna tare da mu". Fashewa Na'ima tai da kuka, ta wuce bedroom ɗinta, ta cire wayarta da ke caji, ta shiga neman lambar Ammi, wato mahaifiyar Khamal, Ammi na ɗagawa Na'ima ta sake fashewa da kuka tace "Ammi dan Allah ku zo gidanmu akwai matsala, Khamal yaiwa karuwa ciki a waje, ta haihu tace ba zata riƙe ba, shine ya kawomin ita wai in ban riƙe ba ze sakeni" Ammi tace "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Khamal ɗin?" "Wallahi Ammi da gaske nake, dan Allah kuzo, kar baƙi ciki ya kasheni, dan Wallahi se da ya zaɓa ko ni ko ita, ba zan zauna da 'yar zina in raineta ba!". COMMENT AND SHARE BRIGHT PENS NIMCYLUV AYSHECOOL ZEE KUMURYA Domin ƙarin bayani, ku tuntuɓe mu akan 07063065680 09047871750 m selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm! BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE I'm selling MTN data with this cheap price MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month Airtel,9mobile and Glo also available. *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* Whatsapp OR Call *08066268951*[9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷* Brigh pens✍️ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya *6.....* Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. IDAN KATIN WAYA NE #500 NE. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. *_Masu son Littafin MIJIN MALAMA... Kuyi following Acct ɗin nan a Arewabooks👇🏾_* https://arewabooks.com/u/nimcyluv Cikin kaɗuwa Ammi ta ce. "Subhanallahi, Na'ima kin san me kike cewa kuwa? Baban nawa ne zai aikata wannan mummunan aikin?" "Wallahi Ammi dagaske nake, kin san dai ba zan yi masa k'arya ba, ki zo ki ga yanda suke yi da Yarinyar, zaki tabbatar Ɗa da Mahaifi ne." Jiki a sanyaye Ammi ta ce. "Wannan maganar ba ta waya ba ce, bari na kira Alhaji, za mu zo yanzun nan insha Allahu, amma dan Allah kar ki tayar da hankalinki da yawa, kin san a yanayin da kike ciki ba'a buƙatar ki saka damuwa a cikin ranki." "Toh Ammi sai kin zo" Ta faɗi haka cikin kuka, zuciyarta na yi mata wani irin suya saboda tsananin kishi. Khamal ya shayar da ita ruwan mamaki, ba ta taɓa zaton haka daga gare shi ba, she trusted him over, ashe ya ce zai nuna mata halinsu na sojoji. Cillar da wayar ta yi ta fito daga ɗakin kamar mahaukaciya, ko nauyin cikin jikinta ba ta ji. Zaune ta tarar da Captain a parlour kan kujera two seater, Abra na jikinsa ta yi bacci abinta. Kallon Television yake yi hankalinsa kwance tamkar babu wani abu na ɓacin rai da yake damun shi. Hakan ya ƙara k'ular da Na'ima, ta tsani wannan maziyar tasa, abu ya faru ya mayar da kai mahaukaci shi kuma ya dinga pretending like everything is okay. Kamar zautacciya ta fara cillar da pillows ɗin kujera cikin kuka tana faɗin. "Wallahi Khamal ba ka isa ka tozarta ni ba, sai na kashe ka na kashe yarinyar in yaso nima a kashe ni!" Khamal dake bin ta da wani irin kallo cikin tsawa ya ce mata. "Na'ima! Wallahi kika sake wani abun ya samu Yarona da ke cikinki garin haukanki sai na nuna miki ɓacin raina, wanda baki taɓa ganin irinsa ba." "Ya mutu ma ina ruwana Ni, kuma ɓacin rai ka daɗe baka nuna mun shi ba, ƙarƙari dai ka ce ka sake ni in tafi in bar maka gidanka, to idan ka sake nin sai me? Na ce sai me?" Tai maganar tana zazzare idanunta da sukai jawur, saboda azabar kishi da kuma kukan da tai. A firgice Abra ta farka daga baccin saboda hargagin Na'ima, fashewa ta yi kuka tare da ƙanƙame Captain tana kiran sunan "Abbi". Cikin tsana Na'ima ta wurga mata wani kallo tana huci kamar zata ci babu, ji take tamkar ta fizgo Abra daga jikin Khamal. Tsaki Captain ya yi ya miƙe tare da Abra a jikinsa ya shige bedroom ɗinsa yana rarrashin ta. Ganin haka yasa Na'ima fashewa da kuka tare da zama daɓas akan kujera, ganin yadda ya maida ita mahaukaciya. "Khamal why? Me yasa zaka mun haka? Ban cancanci haka daga gare ka ba, kar ka saka mun tukwicin k'aunar da nake yi maka da cin amana." Ta faɗi haka cikin sheshshek'a. Ƙarfe biyar da mintuna su Ammi suka ƙaraso gidan, har lokacin Na'ima tana zaune a inda take, ta ci kuka ta gode Allah, sai wani irin haki take yi saboda tsabar ɗorawa kai masifa, ga nauyin ciki. Tana jin ana knocking ta miƙe da sauri ta buɗe ƙofar, zatonta ya zama gaskiya su Ammi ne tare da Baffa. Granny ce a gaba, baki buɗe take kallon Na'ima bayan sun shigo, tafa hannuwa ta shiga yi ta ce. "Na shiga uku ni Mari, wannan fita hayyacin naki da kika yi Na'ima na mene ne? Ko waya aka yi miki aka ce tsohuwa ko tsoho wani ya mutu?" Na'ima ba ta bi ta kanta ba ta yiwa su Ammi sannu da zuwa cikin dauriya. Kama hannunta Ammi ta yi cikin lallami ta ce. "Na'ima ba ki ji abun da na faɗa miki ba ne na cewa ki kwantar da hankalinki? Kin ga yanda kika koma kuwa?" Sake fashewa tai da kukan tace "To Ammi ya zan yi? Ba ki ji yanda zuciyata take mun wani irin zafi da suya ba ne." Baffa ya yiwa kansa mazauni ya ce. "Ina shi Khamal ɗin yake?" "Yana ɗakinsa tare da Yarinyar." Na'ima ta faɗa cikin ɗacin rai. "A'a, wacce yarinyar kuma? Me kuke zance akai ne? Me yake faruwa ne?" Granny ta tambayi haka tana bin su da kallo. Ganin babu mai shirin ba ta amsa cikin fusata ta ce. "Yau na ga jaraba, ya ina tambayar ku, kun mun shiru kun mayar da ni wata gantalalliya? Ni dama tun da na ga Buba ya dawo gida hankali a tashe na san da wata a ƙasa, na tambayi me ya faru kuma saboda ba'a ɗauke ni da muhimmanci ba an ce mun ba komai, duba jikin Khamalu kawai za'a zo yi, na zo kuma na ji ana wani zance na daban da ban gane masa ba." Cikin girmamawa Ammi ta ce. "Hajiya ki zauna zaki ji komai yanzu." "Wanne irin in zauna kuma kamar wata ruɓaɓɓiya? Ƴarki ce ni da zaki ba ni wannan umarni haka?" Ammi ba ta kuma magana ba ta nemi guri ta zauna, Na'ima da take jin kamar ta tsinkawa Granny mari saboda takaici ta nufi ɗakin Captain ta fara yin knocking da ƙarfi. Lokacin yana kwance idanunsa a lumshe, raba Abra ya yi daga jikinsa a hankali wadda ya samu ta koma bacci da ƙyar sannan ya miƙe a fusace ya je ya buɗe ƙofar. Ganin haka yasa Na'ima ta juya ba tare da ta yi masa magana ba, kamar ya share ta ya koma sai dai ya daure ya bi bayanta. Cikin mamaki yake duban su Ammi ganin su zaune a parlour ba tare da ya san da zuwan su ba. kallon Na'ima ya yi cikin ɓacin rai, akan wannan 'Yar maganar shine ta ɗaɗɗako iyayensa suka zo? Siririn tsaki ya ja a hankali ya ce. "Sannun ku da zuwa." "Granny ta ce. "Yawwa, ya jikin naka ɗan albarka? Na ga jiki ya yi kyau Masha Allah." "Da sauƙi Alhamdulillah." Ya ba ta amsa ba yabo ba fallasa. Baffa ya ce. "Nemi guri ka zauna mu yi magana." Bai yi musu ba ya zauna a saman carpet. "Wacce yarinya ka kawo gidanka Khamal?" Baffa ya jefa masa wannan tambayar. A nutse ya fara magana cikin ladabi. "Baffa a wannan operation ɗin da muka fita na tsinci wata yarinya k'arama daban ba'a cikin yaran da aka yi kidnapping ɗinsu ba...." Bayanin komai ya yiwa Baffa har yadda suka yi da Na'ima bayan an kawo Abra. Cikin zuzuta Granny ta ce. "Huhuhu, yau na ga ƙarfin hali, Na'ima ashe dama ke ba matar rufin asiri ba ce ba mu sani ba? Na ɗauka ko dabba Khamalu ya kawo gidan nan baza ki ce uffan ba sai dai ki karɓe ta hannu bibbiyu. To gidan naki ne ko nasa? ban da jaraba irin taki mutumin ba shi da lafiya amma ki saka shi a gaba da fitina, kina fama da narkeken ciki haihuwa ko yau ko gobe maimakon a gan ki da carbi a hannu kina lazimi akan Allah ya sauke ki lafiya, amma ke ta neman bala'i kike? Tirrr da wannan abu." Na'ima ta saka kuka ta ce. "To kuma a rasa mai riƙon yarinyar sai shi kaɗai? Cewa fa ya yi idan ba'a ga iyayenta ba a nan za ta cigaba da zama tare da mu." Baffa yana duban ta ya ce. "Ki kwantar da hankalinki Na'ima, a yanayin da kike ciki ba'a son kina saka damuwa har haka a cikin ranki." Ammi ta nisa ta ce. "Amma Khamal daga tsintar yarinya sai ka ce kana son ta zaka riƙe ta? Mene ma'anar yin hakan?" "Wallahi first love ba da wata manufa nake son riƙe Yarinyar nan ba, tun kallon farko da yi mata na ji ina jin tausayinta sosai a cikin raina. Ni fa ban ga abun ɗaga hankali a wannan abun ba, me yarinyar za ta tsare mata in ta zauna a gidan? Ammi ke uwace ya rayuwar wannan yarinya za ta kasance idan ta faɗa hannun ɓata gari?" Na'ima ta e "Ai dama dole ka ce haka tun da Ubangiji ya toni asirin ka, to wallahi sai dai ka zaɓa ko ni ko ita, amma ni dai ba zan zauna da ita a cikin gidan nan ba." "Sai ki san inda dare ya yi miki, gida dai nawa ne kuma abun da na gama zan yi a cikinsa." Ya ba ta amsa cikin haɗe rai. Tsawatar musu Baffa ya yi ya ce. "Ya isa haka! Ba zuwa muka yi mu saka ku a gaba kuna sa'insa ba." Ya mayar da duban sa ga Na'ima ya ce. "Ki yi hak'uri ki bar yarinyar ta zauna a nan ɗin kafin Allah ya bayyana iyayenta, kar kuma ki saka a ranki na goyi bayan Khamal ne, a'a ko kaɗan, na san halin Khamal na san waye shi, ba'a shaidar ɗan mutum amma zan yabi Khamal akan ba ya aikata zina, tun daa da ba shi da mata bai yi ba balle yanzu da yake da ke. Taimako ne zai yi na riƙon yarinyar, domin idan ya bar ta ba'a san yanda rayuwarta zata kasance ba, duk da gwamnati za ta kula da ita tare da ba ta kariya amma nan ɗin sai ya fi safe." Granny dake bin su da ido ta fashe da kuka ta ce. "Allah wadaran naka ya lalace, yanzu Na'ima saboda tsabar baki da ta ido mijinki kike dangantawa da zina? To ki je dan kanki, Allah kuma ya saka mana akan wannan k'azafi da kika yiwa jikana." Ta share hawayen fuskarta tana mitsi_mitsi da ido ta ce. "Kin ci albarkacin cikin dake jikinki, amma wallahi da yau a bazawara zaki kwana a gidan Ubanki, domin kuwa ke ba matar mutunci ba ce, ja'ira da ido kamar an soya Aya." Baffa ya ce. "A'a Hajiya a dai bi komai a sannu.." Bai gama rufe baki ba ta hayayyaƙo masa da faɗin. "Na ƙi na bi a sannun, Sharrin zina fa ta yiwa jikana, ku kuma yana ɗanku kun zauna kuna yin abu wani lako_lako kun ƙi yin abu da jiki ki ɗauki mummunan mataki a kanta." Ta ƙasan ido Na'ima ta dinga wurga mata harara. Nasiha mai ratsa jiki Baffa ya yi musu akan su ƙara hak'uri da juna, sannan ya yiwa Na'ima faɗa akan zargin da ta yiwa Captain, ya nuna mata hakan ba daidai ba ne, musamman da already dama ta riga ta san halin Captain, bai kamata daga ta gan shi da yarinya ta ce ƴarsa ba ce. Sannan ya ba ta hak'uri akan riƙon Abra da ya ce su yi, dan ya gani baro baro a fuskarta ba ta ji daɗin hakan ba ko kaɗan. Shi kuma Baffa haka Ubangiji ya yi shi, mutum ne mai faɗar gaskiya komai ɗacinta, ko da ba za ta yi maka daɗi ba sai ya faɗa, sai dai ka ji haushin sa. Ammi ma ta ɗora da ta ƴar nasihar da ban baki a gare su gaba-d'aya. Na'ima kawai jin su take yi amma ba ta fahimtar me suke cewa, ita kawai gani take yi sun goyawa ɗansu baya ne. "Sai masifa da wasu surutai ake yi, amma ko yarinyar da ake jarabar a kanta ba mu gani ba." Cewar Granny tana yatsina fuska cike da rikicin tsufa. Captain da hankalinsa gaba-d'aya yana kan Abra, ya miƙe ba tare ya yi magana ba ya nufi ɗakinsa, Na'ima ta bi shi da kallo hawaye na zuba daga cikin idonta, wani irin haushinsa cunkushe a cikin zuciyarta. Yana shiga ya tarar Abra ta tashi daga baccin, tana ta kuka tare da kiran sunansa. Rungume ta ya yi tsam a jikinsa ya shiga rarrashin ta. Ajiyar zuciya ta saki tana kallon fuskarsa cikin maganarta da ƙarfi ta ce. "Abbi" "Na'am My daughter, I'm sorry na tafi na bar ki ke kaɗai ko?" Ya yi maganar yana shafa kanta. Duk da ba ta ji me ya ce sosai ba sai ta tura bakinta gaba. Kissing kuncinta ya yi cikin murmurshi sannan ya ɗauke ta suka fito parlour. Kallon Abra kawai su Ammi suke cikin mamaki. Ammi ta ce. "Ikon Allah, wannan yarinya haka kamar Balarabiya?" Wani salati Granny ta rafka tare da miƙewa tsaye tana gyara ɗaurin zaninta ta ce. "Huhuhu, mutanen duniya babu gaskiya da tsoron Allah, ban da tsabar sharri ina Khamalu zai haifi wannan kyakkyawar yarinyar mai zubi da turawa, yana ɗan baƙi da shi? A gaskiya wannan mata babu abun da za mu ce miki sai dai kawai Allah ya shiga tsakaninmu da ke, haka kawai kina daga kwance ki narkawa jikana sharri, bayan kuma kina zaune a cikin gidansa kin gama cin abincinsa kin yi ƙat dake, kin murmuro daga ramar da kika zo da ita." Ammi ta ce. "Hajiya wannan maganar fa an wuce ta, ɓacin rai ne ya saka Na'ima ta yi haka." Baffa da ya kasa ɗauke idonsa daga kan Abra ya miƙa mata hannu, ba ta yi musu ba ta je gurinsa, ko dan ta ga suna kama da Abbinta ne. Baffa ya ce. "Allah Sarki, sannu yarinya, Allah ya bayyana iyayenki." Ammi ta amsa da Amin. Granny ta zo zata ɗauki Abra ta ƙi yarda da ita, da ta takura sai Yarinyar ta saka kuka ta koma gurin Abbinta ta lafe a jikinsa. Riƙe haɓa Granny ta yi ta ce. "Yau na ga yarinya da jaraba, dan ma zan taimaka in ɗauke ki ba tare da na san daga inda kike ba shine zaki mun tijara, ban da ma zuciyar musulunci irin tawa mene haɗina dake? Aba jawur a koɗe kamar ƙosai" Ta taɓe baki tare da komawa ta zauna tana cigaba da mitocinta. Baffa ya miƙe yana duban su Captain ya ce. "Mu za mu wuce, sai a daɗa hak'uri da juna, ɗa kuma na kowa ne, idan ka riƙe na wani kai baka san wa zai riƙe maka naka ba." Na'ima ta danne zuciyarta ta ce. "Insha Allahu Baffa, mun gode Allah ya ƙara girma." "Baffa ba za ku jira a yi Sallah ba sai ku tafin, kuma ko ruwa fa ba ku sha ba." Cewar Captain. Baffa ya ce. "Alhamdulillah, wucewa za mu yi, na ga sauran lokacin da ya rage a kira sallah zai kai mu gida insha Allahu." Granny ta ce. "Dama ba'a yi niyyar ba mu ruwan ba, sai yanzu za'a wani ce mu zauna mu sha." Captain ya dube ta ya ce. "Kin taɓa zuwa gidan kafin yau an hana ki ruwan ne?" Ɗaure fuska ta yi ta ce. "Ni dai ba zan biye ka mu yi tashin hankali ba tunda ba halina ba ne kowa ya shaida, ato." Sannan ta mayar da duban ta ga Baffa ta ce. "Sai dai in ce ku gaishe da gida, dan ni anan zan zauna in kula da wannan zabiyar yarinyar mai ƙwala ƙwalan idanuwa kamar na kakata haulatu, tunda ita wannan asararriyar ta yi nauyi ba iya kula da ita za ta yi ba, tana juyi da ƙyar tana mirgina uban ciki amma se jaraba, gobe idan Allah ya kai mu Shureim sai ya kawo mun kayan sakawata." Baffa ya ce. "A'a tare za mu wuce da ke yanzu, Iman ta zo ta zauna a nan ɗin tunda sun kusa yin hutu a school." Bai jira cewarta ba ya yi gaba. Granny ta bi shi da wani irin kallo sannan ta miƙe ba tare da ta yi magana ba ta yi waje fuuu. Ɗan murmushi Captain ya yi ya bi bayansu. Ammi ta miƙe tana duban Na'ima ta ce. "Ki yi hak'uri, na san zaki ga kamar ba'a kyauta miki ba, amma ba rashin kyautawa ba ne, hakan shine dai-dai. Ɗa na kowa ne, sanadiyyar riƙon yarinyar sai ki ga Ubangiji ya baki wani abun da baki taɓa zo ba a cikin rayuwarki, dan Allah ki riƙe yarinyar nan saboda da Allah, kar ki cutar da ita. Kema ba ki san me gaba zata haifar ba" Na'ima ta share hawayen fuskarta cikin dakiya ta ce. "Insha Allahu Ammi, ɗazun ma ɓacin rai ya saka na yi hakan, ku yi hak'uri, insha Allahu komai ya wuce. Ammi ta ce. "Yawwa, Allah ya yi albarka, ya sauke ki lafiya." Ta amsa da Amin tare da miƙewa ta raka Ammi bakin ƙofa. A haukace ta dawo cikin parlour ta shiga bedroom ɗinta ta kulle ta ɗauki wayarta ta kira lambar Yayarta, tana jin ta ɗaga ta fashe da kuka ta ce. "Na shiga uku Aunty, ina cikin damuwa, Khamal ya zo mun da wata masifa cikin gidana." A rud'e Aunty ta ce. "Subhanallahi! Mene ya faru?" "Yarinya ya kawo mun cikin gidana wai za mu riƙe ta, a cewarsa wai a operation suka tsinto ta, ni kuma na san wallahi k'arya yake yi ƴarsa ce suka haifa da wata karuwar a waje." "Ya aka yi kika san hakan? Ke da kullum cikin yabon Captain kike akan kamewarsa da rashin bin matan banza?" "Aunty ba ki ga yanda suke yi da yarinyar ba ne, shak'uwarsu ta fi ƙarfin a ce a cikin abun da bai 1 month suka yi kamar ta ba, kuma baki ga shegiyar Yarinyar ba, kyau kamar ita ta yi kanta, irin kyawun nan dai na ƴaƴan shegu, dan dama a gurin aikin nan nasu akwai mata masu bibiyarsa. Na kira iyayensa kuma domin su zo a yiwa tufkar hanci amma sun goyi bayan ɗansu, ni na yi kara ban kira nawa iyayen ba dan kar ace sun zo sun goyi da bayana, ashe su ma son kai za su yi. Wallahi Aunty ba ki ji yanda zuciyata take mun zafi ba, ni dai ba zan zauna da wannan yarinyar a gidan nan ba, ki bani mafita Please." Aunty ta ce. "Shi Captain ɗin ya kuka yi da shi?, ki nuna masa bakya san riƙon yarinyar mana." Cikin sheshshek'a Na'ima ta ce. "Aunty cewa fa ya yi sai dai in zaɓa ko in riƙe ta ko in bar masa gidansa, ya zaɓe ta a kaina, duk irin tarin soyayyar da Khamal yake mun amma yau ni yake faɗawa haka? ba dole in ji na tsani Yarinyar ba tunda a kanta ya faɗa mun haka." Cikin mamaki Aunty ta ce. "Shi Captain ɗin ne ya faɗa miki haka?" "Wallahi Aunty shine." Nan ta kwashe labarin duk abun da ya faru ta faɗawa Aunty. Cikin ɓacin rai Aunty ta ce. "Lallai ma Khamal, yanzu akan wata banza can shine zai nemi ya wulak'anta ki? Ya fifita ta a kanki? To amma idan ya san wata ai bai san wata ba, ki k'yale shi ki taushi zuciyarki, ki nuna masa kin amince zaki riƙe yarinyar, taa k'ark'ashin ƙasa za mu biyo masa, a gabansa ki dinga nuna duk duniya babu wanda ya kai ki k'aunar Yarinyar, a bayan idonsa kuma ki dinga cin ubanta son ranki kina gallaza mata, yanda komai ƙanƙantarta da kanta za ta nemi ta bar gidan, koma ta gudu da ƙafafuwanta." "Ta yaya Aunty? Yarinya ce fa k'arama, ba tafi shekara uku ba, ni fa kawai damuwata yarinyar nan ta bar gidan nan a yau. Dan ba zan raini 'yar haram ba in ci kashinta in ci fitsarinta ba" "Daɗina dake gajen hak'uri, ki yi yanda na ce miki kawai, da kissa da makirci zaki kori yarinyar daga gidan ba tare an yi tunanin ke kika aikata hakan ba, amma fa dole sai kin danne zuciyarki kin ajiye wannan masiffaffen kishin naki a gefe, in kuma ki kayi dalilin kashe Auren naki ai kin huta." Haka Aunty ta dinga tausar Na'ima da koya mata irin abubuwan makircin da za ta yi, har aka yi Sallar Magriba suna wayar, sai da ta ji shigowar Captain gidan sannan ta yi mata sallama ta share hawayen fuskarta ta tashi ta fito parlour. A tsugunne ta tarar da shi yana cirewa Abra takalmin ƙafarta wadda ke shan choculate hankali kwance. Wani abu ne ya soki zuciyarta, wato masallacin ma da yarinyar ya tafi saboda tsantsar k'aunar da yake yi mata. Danne baƙin cikin da ya taso mata ta yi ta kakalo murmushi ta ce. "Sannu da zuwa My Man." Ko d'agowa bai yi ba balle ya ba ta amsa. Ƙarasawa ta yi ta tsugunna a gabansa cikin kissa ta ce. "Magana nake maka fa." Nan ma banza ya yi da ita. A hankali ta kamo hannunsa cikin marairaicewa ta ce. "Dan Allah ka yi hak'uri My Man, na tuba na gane gaskiya, wallahi ɗazun ma sharrin shaidan ne." Ta ƙarashe zancen idanunta cike da ƙwalla. Ba tare da ya kalle ta ba ya ce. "Ya wuce." Yana ƙoƙarin janye hannunsa daga nata ta riƙe shi gam tare da sakar masa kuka. Numfashi ya sauke ya ce. "Mene haka kuma? Ba na ce na hak'ura ba?" "Ai na san ba ka hak'uran ba, Please My Man ka san ba zan juri fushinka ba." Sakin fuskarsa ya yi ya ce. "Komai ya wuce ki bar kukan nan haka." Sannan ya saka hannu ya shafi cikinta cikin k'aunar Unborn ɗinsa." Ajiyar zuciya ta sauke ganin da gaske ya hak'uran. Hannu Abra ta kama ta ce. "Zo nan Daughter." Ƙin zuwa ta yi ta lafe a jikin Major tare da kwab'e fuska za ta yi kuka. Duk da haka ba ta yi zuciya ba ta shafa fuskarta ta ce. "Ya sunanki?" "Abra." Captain ya ba ta amsa idanunsa akan Abra. "Wow nice name, Allah ya raya mana ke" "Amin" "Bari na je na yi Sallah." Na'ima ta faɗa tana miƙewa, dan dauriyarta ta kusa ƙarewa akan pretending ɗin da take yi, ji take tamkar ta janyo Abra ta shaƙe ta ta mutu saboda tsanarta dake ƙara cika mata zuciya. Bai ce komai ba sai bin ta da ya yi da wani irin kallo, darajar cikin cikinta ta ci, da kuma nasihar da Ammi ta yi masa bayan sun fita, akan ya yi hak'uri ya mayar da komai ba komai ba tun da Na'iman ta yi nadamar abun da ta aikata, shi yasa kawai ya haƙura, amma da ya yi niyyar sai ya hukunta ta akan hauka da ƙazafin da ta yi masa. LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. 'Yan uwa da abokan arzkin wanda aka sacewa 'yan uwa hankalinsu yaƙi kwanciya, gani suke babu wani yunƙuri da gwamnati take yi, dan karɓo musu yaransu, musamman masu 'ya'ya mata a ciki. Suka dinga kira ga gwamnati, akan Lallai a biya su wannan kuɗi, a karɓo musu yaransu. Yayin da gefe guda, gwamanti na ta ƙoƙarin ganin yadda za'a karɓo yaran, ba tare da an illata wani ba, kuma ba tare da an biya wannan kuɗi ba, idan aka kwashi wannan zunzurutun kuɗi aka bawa 'yan ta'adda hakan ƙarara ze ƙara nuna gazawar gwamnati, wanda babu gwamnatin da zata so ace ta gaza. Taro aka gabatar cikin dare, in da aka siyo manyan makaman yaƙi, da za'a rabawa Sojoji, cikin sirri aka kawo makaman aka saye su, a in da tsirarun da aka yadda da su a harkar tsaro ne kawai suka sani. General Ibrahim ne tare da ƙaramin ministan tsaro, suka ɗai a wani ɗaki suna tattaunawa cikin harshen turanci. Ƙaramin minista ya kalli General Ibrahim yace "ai mu wannan abu gaba ta kaimu, ka saka amintattun yaranka su fita da wasu daga cikin kayan da na gaya maka, aka kaisu wannan mararrabar, masu shi za su zi su karɓa, kuma akwai ƙishin ƙishin tun da gwamnatin tarayya ba zata karɓo su ba, Gwamnan jihar ze rage wani abu ya basu ya karɓosu, wanda muna da kaso me tsoka a ciki". General Ibrahim yace "an gama ranka ya daɗe, duk yadda kace haka za'ai, sannan akwai wasu sojoji, da aka kora suke ta ragaita a gari, cikin sirri zan janyo su cikin harkar nan, zasu bada gudunmawa sosai da sosai". Minista yace "ni dai fatana kar a samu matsala, dan idan aka samu matsala na san yadda zan zame kaina in barka". General yace "ba za'a samu wata matsala ba, za'a fitar da makaman a siyar musu da wasu" "Good" suka cigaba da tattaunawa akan yadda za su yiwa harkar tsaro zagon ƙasa dan gina kawaunan su. Yau kuwa gidan Captain Khamal, bayan Sallar isha'i suna zaune a kan carpet suna yin dinner da Pride rice with chicken ɗin da Na'ima ta yi musu, Abra dai ta ƙi ci dan har yanzu ta kasa sabawa da irin abinciccikan nan, sai fruits Captain ya bayar aka siyo mata masu yawa take shan abun ta, hakan ba ƙaramin ƙara ƙonawa Na'ima rai ya yi ba. Suna cin abincin amma hankalin Captain gaba-d'aya yana kan Abra, da ta yi motsi zai ce. "What happen Daughter? Ko, What do you want?" Ko Abincin ya ƙi maida hankali ya ci, ya lalace akan Abra. Imagining take da babu wannan shegiyar yarinyar, da tuni yanzu tana jikin Mijinta tana zuba masa shagwab'a yana tattalinta, yana ririta ta kamar ƙwai. Gashi ƙarin abun takaicin yarinyar ta ƙi yarda da ita ko kaɗan, duk irin wayon da ta yi mata amma yarinyar ta ƙi zuwa gurinta. Bayan sun gama cin abincin da kansa ya yiwa Abra wanka ya kwantar da ita ya tofe ta da addu'a, sai da ya ga ta yi bacci sannan ya baro ɗakin da take. Sai a wannan lokacin Na'ima ta samu ya ba ta full time ɗinsa a kanta, ya nuna mata soyayya kamar yadda ya saba, tamkar babu wani abu na ɓacin rai da ya faru a tsakaninsu. Washegari da safe Captain yana bacci Abra ta yi kashi a ƙasa a cikin toilet ɗinsa, duk da zaman da ta yi a gidan Madam Halima, amma har yanzu ba ta saba da hawa kan toilet seat ba idan za ta yi kashi. Na'ima tana ɗakinta a lokacin suna waya da mahaifiyarta tana ba ta labarin abin da ya faru, ba ta san me Abra ta aikata ba. LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU* _Brigh pens✍️_ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya P7 Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗin a Arewabooks https://arewabooks.com/book?id=6220842688e1ec3a0410329f https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949 https://arewabooks.com/u/nimcyluv Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Cikin wani irin ɓacin rai, Na'ima ke bin Abra da kallo! Wacce ke tsugune a toilet ɗin Captain, tayi kashi a ƙasa gaba ɗaya ta ɓata toilet ɗin da jikinta. Bata taɓa jin, akwai wani data taɓa tsana a duniya kamar ABRA KHAMAL ba, ta tsani Yarinyar tsana mai yawan gaske. Gani take shigowarta rayuwarsu gaba ɗaya matsala ce. Wannan dalilin ke sa wa Na'ima ta ƙara jin ranta ya ɓaci akan Abra. Kishin Abra ya kama Na'ima, irin kishin nan na tsakanin Kishiya da kishiya (crazy jealousy) mussaman yadda ta ga Khamal ɗin ya na bawa Abra kulawa. Rai ɓace, Na'ima ta ja hannun Abra zuwa Part ɗin ta, Abra na tirjewa tana ƙoƙarin ƙwala kiran sunan “Abbi” Na'ima ta hankaɗa ta zuwa cikin toilet ɗin dake nata part ɗin. Wannan shi ne dama ta Farko, Da Za tai amfani da ita wajan cin Uban Abra, ta san idan tace a part ɗin Captain Khamal Khamis zatai Punishing ɗin ta, Tabbas zata ɓata rawar ta da tsalle, wanda zai sanya Captain Khamal Khamis ya din ga yi mata kallon Munafuka mai Fuska biyu, ita kuma bata son duk wani abu da zai shafi mu'amalar ta da Khamal. "Zaki ci Ubanki, ƴar banza mai siffa irin ta sadaka yalla!" Na'ima ta faɗa tana murɗe kunnen Abra cike da mugunta, zafin da Abra taji ya sa ta saki wata siririyar ƙara mara sauti, saboda rufe mata baki da Na'ima tayi. A fusace kuma ta shiga zarewa Abra, kayan jikinta tare dayi mata tsirara. Ficewa Na'ima tayi, daga cikin toilet ɗin ta nufi ƙofar part ɗin nata, cikin sauri ko lura da cikinta ba tayi, taja ƙofar ta rufe, ta sa mata key, saboda kada Khamal ya jiyo sautin kukan Abra. Tana komawa toilet ta nemi wayar chaji, Abra na durƙushe in da ta ajiyeta, babu zato ta ji saukar bulala akan fatar gadon bayanta. Ihu ta saki da dukkan ƙarfinta tana kiran sunan Abbi, bata taɓa tunanin akwai azaba irin wannan ba, saukar bulalar ya gigita Abra Khamal Khamis ƙwarai, har wani irin shiɗewa take na rashin sabo!. Na'ima tace "Yadda ki ka rabani da farin ciki na, ki kai sanadiyyar shiga tsakani na da mijina, haka zaki dauwama cikin gidan nan ina gana maki azaba kala kala, wacce zata saka da ƙafarki ki fice ki bar min gida na, Gidana nawa ne, da ga ni, sai Mijina sai kuma yaran da zan haifa masa, bana buƙatar kowa cikin rayuwarmu, zuwanki ya ruguza min dukkan wani  burina, ba zaki taɓa jin daɗi ba in dai a gidan nan ne, mufuka, Algungumin". Tai Maganar Kamar ta na yi da sa'arta. Yadda Na'ima ke kumfar baki zaka ɗauka da wata ƙatuwar mace, sa'arta take wannan ihun, ba da little Abra da ba ta wuce a goyata. A. Abra kasa kuka tayi sai sakin ajjiyar zuciya kawai take, bayanta yayi kwance da zanan bulala, ta kasa ko ɗaga kai ta kalli Na'ima. Tana bala'i da kumfar baki ta wanke wa Abra kashin, tare dayi mata wanka. Na'ima ta kalli Abra kafin da ɗan ƙarfi tace "Tsinanniyyar yarinya, Allah ya isa tsakani na dake, wlh da ƙafarki zaki bar gidan nan" Abra bata san me Na'ima take faɗa ba, hakan yasa bata ma fahimta ba, wani irin tsoron Na'ima ya kama Abra, tsoran dake neman sanyata cikin mugun hali, da son raunata mata ƙaramar ƙwaƙwalwarta. Kama gashin kanta tayi da ƙarfi, cikin tsanar Yarinyar tace "Keee!!" Abra ko motsi ba tayi ba, sai jikinta kawai take tsuma da karkarwa na azaba. "Kika sake, naji kin faɗawa Abbi wannan maganar sai na yanka ki" Na'ima ta faɗi maganar cikin kunnen Abra, tana nuna mata wuyanta da hannu. “A...Abbi jani" cewar Abra wanda ilahirin jikinta rawa yake, Na'ima ta figi hannunta zuwa bedroom tana faɗin "Abbin uwarki, ko na Ubanki? Baki da Uba a gidan nan Wallahi zan tabbatar dana gurɓata wannan muguwar fuskar taki. Kura da fatar Akuya!" Abra bata fahimta, da alamar yarinyar ta gama gigita da Na'ima, a haka Na'ima ta shirya Abra cikin Pria shirt short dress. Red colour, ta ɗaure mata tulin sumar kanta da ribbon. Yadda Na'ima taji ana knocking ƙofar ta, yasa tayi saurin Miƙewa tare da gogewa Abra Fuskarta tas, ta nemi perfume ta fesa mata, hannunta ta saka ta ɗauki Abra tana gasa mata mintsini a haka ta nufi ƙofa da ita. Tana buɗe ƙofar taga Captain Khamal tsaye sanye cikin ƙana nan kaya masu kyau, sai ɗaukan idanu yake. Na'ima tai murmushi, tace "Man, ina son yarinyar wallahi ta shiga raina daka jiya zuwa yau" tai maganar dan kar ya fahimci wani ab7 Ganin Khamal yasa hankalin Abra tashi, ta shiga miƙawa Abbinta hannu tana son zuwa gareshi. "Haba Daughter, nifa Mami ce mene yasa kike gudana" Na'ima ta faɗa tana rungome Abra. Kafin ta ɗaga idanunta zuwa ga Khamal tace. "Ina jin babu daɗi, yadda Abra bata son na ɗauke ta, ba na jin daɗin ƙyuyar nan ta ta." kwantaccen Murmushi Khamal ya saki tare da saka hannunsa ya amshi Abra dake hannun Na'ima, Abra ta ƙanƙame Khamal kamar zata shige jikinsa sai ajjiyar zuciya take saki. A nutse Captain Khamal ya kalli Na'ima yana kashe mata idanunsa yace "Bata da yarda, kin san Uba yafi gaban wasa, shiya sa tafi yarda dani akan kowa" “Uba yafi gaban wasa?” shine kalmar da ya nemi zautar da tunanin Na'ima, tunanin da ya sanya ta ƙara ninka ƙudirinta akan Abra, cikin fuskewa tace "I see, ka fahimtar da ita cewa nice mahaifiyarta, bana son yadda take guduna ina son yi mata riƙo irin na uwa da ƴa, ina nufin A good mother, who stands by her child, ba zan ji daɗi abinda yake cikina ya fito duniya har ya girma ba, ace Abra na guduna ina son nunawa, Ɗa na ko Ƴa ta cewa Abra ita ce babba" Kalman Na'ima sunyi tasiri a zuciyar Kham, wani farin ciki ya kamashi cikin nuna kulawa ya bawa Na'ima side hug yace. "Kada ki damu, rashin sabo ne da kuma yadda ta tsinci kanta, zan yi ƙoƙarin fahimtar da Ita" Murmushi Na'ima tayi da saurin kuma tace. "Oh, i almost forget bari naje na haɗa mata something Liquid, tai breakfast" Yace "thats good, I don't want my girl to starve" yai maganar yana sake rungume Abra tare da juyawa zuwa part ɗinsa. Na'ima tace "Yanzu ta fara zama da yunwa" Khamal dake ƙoƙarin buɗe ƙofa, ya juya gaba ɗaya yace "magana ki kai?" Na'ima ta buɗe idanunta tace "Nace bani 10 minutes" ta faɗa tana saurin shigewa cikin kicthen. A hankali Khamal ya fara ƙoƙarin sauke Abra, wata gigitacciyar ƙara ta saka tana ƙanƙame shi tare da ɓoye fuskarta a jikinsa, jikinta na rawa tace "Abbi" Kallonta Khamal yake, He is trying to understand, what scared her. Zama ya yi da ita saman Royal bed ɗin sa, cikin nuna kulawa yace "Daughter" ya faɗa yana kallon Fuskarta, ganin Idanunta ya yi jaaa sosai, Fuskarta ta kumbura alamar tayi kuka yasa, da sauri Captain ya kamata a jikinsa yace "Mene ya baki tsoro? Waye ya saki kuka Abra Khamal?" Yai maganar yana ɗaga muryarsa dan ta ji me yake faɗa. Abra babu damar magana, sai ɓoye jikinta take a jikinsa tana ajiyar zuciya, Tsam-tsam Khamal ya rungume ta a jikinsa, yana jin tausayinta na kamashi. Bai yarda da ƙwaƙwalwar Yarinyar ba, baya son ta samu  “Depression” saboda alamu duk sun nuna a firgice take, Kamar ma wani abu ne ke tsorata ta, ƙara rungumeta yayi a jikinsa jin yadda take ta sauke ajjiyar zuciya! "I'm sorry Daughter, Abbi is here with you" ya faɗa yana shafa kanta. Kwanciya tai lamooo, a jikinsa bayan wani ɗan lokaci, ya ji Saukar numfashinta  a ƙirjinsa, hakan yasa ya ɗan ɗagota sai a lokacin ya lura bacci tayi, gaba ɗaya a firgice take, kwantar da ita yaso yi, amma Abra taƙi sai ma sa ka masa kuka da tayi. Kwanciya ya yi saman gadon, ya ɗora ta a jikinsa yana bubbuga bayanta alamar rarrashi, a nutse ya yi kissing cheeks ɗinta, Muryar can ƙasa yace. "Ba zaki taɓa kukan rashin iyaye ba, zan baki kulawa, Soyayya, tattali, zan yi maki dukkan abunda Uba na gari ya dace ya yiwa yaransa, zan bada ke ga miji na gari wanda zai so ki Love forever, love without deception insha Allah." Ya faɗi Maganar yana shafa sumar kan Abra, wata irin soyayya ya kewa yarinyar, wacce  baya tunanin ko ɗan cikinsa zai iya yi masa irin wannan Soyayyar.  Ya kuma fahimci cewa haɗuwar jini ce Abra ta kasance kyauta a gareshi ( A gift from God). Zameta yayi daga jikinsa yana gyara mata kwanciya tare da ja mata duvet ya lulluɓe mata jikinta, ya jima yana kallon yadda take sauke numfashi a wahale kafin ya juya zuwa waje. A dinning area, ya samu Na'ima tsaye, tana shirya breakfast, tayi adonta kamar kullum cikin doguwar rigar Abaya, fuskarsa babu walwala yaja Kujera ya zauna, without looking at her direction. Murmushi tayi cikin ƙasa da murya tace. "Ya na ganka kai ɗaya? Where's my Daughter?" A kasalance yace "Mene ya samu Abra Khamal?" Dam! Zuciyar Na'ima ta buga, bata ƙaunar yadda Khamal ke maƙala sunan Abra da nasa, gani take babu wanda ya cancanci wannan sunan irin (Biological Child) ɗin sa. "Wani abu ya samu Abran bayan na kawo maka ita?" gaba ɗaya ya ɗaga kansa ya kalli Na'ima kafin yace. "Na fuskanci ta yi kuka, a launin Idanunta na gane" Na'ima taja Kujera bayan ta kammala haɗawa Captain breakfast ta du be shi sosai kafin tace. "Oh, ina son faɗa maka daman, ɗazu tayi kashi a ƙasa kasan daman ba yarda take dani ba, saboda na ɗauke ta zuwa Part ɗina, na wanke mata tare dayi mata wanka shine take ta kuka" Jinjina kansa yayi tare da fara yin breakfast, ba tare da yace komai ba, sai da ya kammala ya miƙe tsaye, a tare suka dawo Main Parlo shi da Na'ima, tana ta faɗa masa how she loves Abra. Murmushi kawai Captain keyi, feeling so happy  ƙasa tayi da Murya tace. "Ya kamata ai mata shopping, na kayan sawa masu kyau sosai" "Nawa zai isa?" Captain yace kai tsaye idanunsa akan plasma yana kallon News. "200k, zai Isa komai da komai Man" Kallonta kawai yayi ba tare da yace komai ba. iya satin biyun nan da Abra tai a gidan Captain Khamal, tas ha Wahala sosai wajan Na'ima, bata barin alama guda ɗaya wanda Khamal zai fahimta, kasancewar  baya gari yaje bada Wasiyyar da Captain Denial da Jamil suka bari. Hakan yasa Na'ima ta samu full  Chance na azabtar da Abra Khamal Khamis. Da Yamma misalin 4:15 Motar Khamal ce ke tafiya akan titin Railway Quarters Nasarawa kano, kai tsaye motar a gida mai number 15 ta tsaya aka fara danna Horn, cikin sauri  Mai gadi ya buɗe musu gate ɗin, ana yin parking da Motar, Captain Khamal Khamis ya fito, saboda yadda yaji zuciyarsa na bugawa, da sauri ya nufi cikin gidan, gaba ɗaya hankalinsa ya tashi tun daka Main Parlo kunnansa ya fara jiyo masa sautin Muryar Abra. Tsaye ya yi yana son sanin inda kukan ke tasowa, da sauri kuma ya nufi kitchen  a gigice yace. “Na'ima!!!!” Khamal ya dakawa Na'ima tsawa, tsawar daya sanya tayi saurin sakin cokalin hannunta, wanda ya yi jajir saboda gasa shi da tayi a jikin Gas! Yadda jikin Captain Khamal ke rawa, haka na Abra ke rawa, Na'ima kam hatta ɗan dake cikinta sai daya motsa, bata taɓa tunanin zai dawo cikin wannan satin ba, ko ɗazu sun yi waya amma bai ce mata yana hanya ba. Dawowar ta sa tazo mata unexpected, wanda yasa Na'ima ta kasa controlling kanta, tsoro ya kamata musamman yadda taga idanun Khamal na fitar da wani irin ruwan Masifa. Da gudu Abra ta Ƙarasa wajan Khamal, tana saka wani irin kuka tare da zaro harshenta waje wanda ya yi jaa sosai, Khamal ya durƙusa tare da saka hannunsa ya ɗauki Abra, Gam! Gam! Abra ta riƙe Khamal tana sauke numfashi a wahale, cikin taƙaici Captain yace. "Na'ima? Abun da na gani, gaskiya ne Ƙona mata harshe ki kai With spoon? Ke mahaukaciya ce? Me wannan yarinyar tayi Miki? ashe ƙarya ki kai baki shirya amsar Abra matsayin ƴa ba?" Shiru tayi masa, gaba ɗaya Khamal yayi kanta cikin hargaginsu na sojoji yace "Ba magana nake maki ba?" Tace "Na faɗa maka bana sonta, bana sonta yaya zan kuma.....," Marin daya sauke mata ya tilasta wa Na'ima haɗiye sauran maganganun, cikin fusata yace. "You are evil, Na'ima!... Nayi nadamar bar maki Abra, Whatever happened to her ke ce sila, ba zan yafe Maki ba" Cikin kuka Na'ima tace "Dama na san wannan shegiyar yarinyar 'ƴar kace, wacce karuwa ta haifa maka, wallahi sai na kasheta ba zan taɓa zama da ƴar karuwa a cikin gida na ba" Tana faɗin hakan ta nufi inda wuƙa take ganin hakan yasa Khamal ya  goya Abra a bayansa, ita kuma ta ƙanƙameshi, bai tsaya jiran komai ba ko tunanin cikin dake jikin ta ya sake ɗauke ta da mari, sai da ya jera mata mari har uku cikin ɗaga murya yace. "Abra ƴa ta ce, jina ce, nina na haife ta, nina samar da cikinta tare da karuwar da kike magana, tun da baki da hankali ba ki san me kike ba, Abra Khamal Khamis is my biological Daughter! Kuma zan kawo karuwar da ta haifa min ita a matsayin mata taci gaba da riƙe ta..." Yana faɗin hakan yayi waje, kai tsaye motarsa ya nufa Driver na ganinsa ya buɗe masa mota ya shiga ɗauke da Abra wacce take ta sauke ajjiyar zuciya na azaba. Wani irin ciwo ne ya tasowa Na'ima, ba tare data shirya zuwansa ba, wata irin ƙulewar mara, da ciwon baya ne taso mata gadan gadan.  ba tare da zato ko tsammani ba, nan take kuma wani ruwa ya fara bin ƙasan ƙafarta, idanunta har rufewa suke saboda kalman ƴa, da karuwa da suke mata kai kawo a kunne! Da gaske Khamal yake Abra 'yar sa ce? Wani gefe na zuciyar Na'ima ya tambayeta. Tuna shaƙuwa mai ƙarfi dake tsakanin Abra da Khamal yasa, marar Na'ima ƙara ƙullewa wayarta ta ɗauka a kiɗime jin kamar abin cikinta zai faso ta cikinta ya fito, cikin kuka tace. "Na shiga uku, zan mutu wallahi ƴarsa ce" Aunty daga can cikin wayar tace. "Meke faruwa kuma yanzu Na'ima?" Na'ima na durƙushe dafe da cikinta tace "Duk abinda kika ce min nayi, na ƙona mata hannu na ƙona mata harshe da cokali, yau ma ina shirin ƙona mata harshe sai ga shi ya dawo" Aunty ta buɗe idanunta With shock tace "mene yasa wani lokacin daƙiƙiyar ƙwaƙwalwa ce take Na'ima? Ba nace idan yana nan babu ruwanki da yarinyar ba?" Na'ima na kuka tace "Baya nan, ban san yau zai dawo ba..." Ƙara Na'ima ta saki ba tare data ƙarasa maganar ba, Anty tace "Lafiya kike ihu kuma?" tana yarfe hannu tace "marata ce za ta fashe Antyy, please Anty kizo na shiga uku...." Jifa tai da wayar  jikinta na rawa tana haɗa gumin azaba, da wani irin ciwo da ba ta taɓa jin irinsa ba, da ma kwana kusan biyu mararta na mata ciwo, amma da yake ta saka bala'i a ranta ba ta damu taje Asibiti ba. Mintuna talatin da wayar da su kai, Anty Suwaiba ta ƙaraso cikin gidan hankali tashe, tun daga tsakiyar Main Parlo ta fara jiyo kakarin Na'ima tana nishi. Hankali a tashe tace  "Ina kayan haihuwar suke, mu tafi Asibiti wannan ai kin kusa haihuwa?" Da ƙyar Na'ima tace "Cikin ɗakina, kan mudubi" da sauri Anuty ta nufi ɗakin Na'ima bata sha wahalar ganin kayan ba, tana ɗakko wa suka ci karo da Granny a Parlon. Kallon tsaf Granny ta yiwa Anuty Suwaiba kafin tace "Ya na ganki duk a hargitse kamar wata taɓaɓɓiya Suwaiba?" Kafin Suwaiba tace komai Ammi dake bayan Granny wanda zuwansu kenan tace "Badai haihuwa Na'ima tayi ba Suwaiba?" "Haihuwa za tayi, Asibiti zamu tafi" Anty ta faɗa a gajarce tana nufar kitchen ɗin. Granny ta buɗe baki sosai tana girgiza kai tace "To mene ya kawo Bazawara gidan Kamalu kuma? Ina da labarin baƙin halin matar nan, yaza tazo tayi kane kane a gidan jikana kamar ita yake Aure?" Ammi dai ba tace komai ba, tabi bayan Anuty Suwaiba zuwa kitchen ɗin. Se dai miƙewar da Na'ima za tai, tai nishi se ga jariri. Ammi tace "Iko se Allah, tun farko be kamata ta zauna a gida ita kaɗai ba ga watam haihuwa ya kama". Ammi ta amshi jaririn hannun Subawai wanda yake ta tsala ihu, tai waje ta ba su guri, cotton da zaiton ta ɗauka ta shiga goge masa jiki, cikin ikon Allah kuma mahaifa ta faɗo, Anuty ta gyara wajan tass, Na'ima ta haihu a kitchen saboda 5sabar jaraba.. a ranta tana jinjina rashin kirki irin na Khamal Khamis. Na'ima wacce ta fito wanka yanzu ta shirya cikin atamfa sai kuka take tana faɗin "Ammi kin gani ko? ya gwammace ya ɗauki yarinyar yayi waje da ita, akan ya kai ni asibiti, Duk abinda muka tsara a rayuwar mu amma Zuwanta ya fara lalata komai, wlh ba zan iya ba" Ammi da take riƙe da kyakykyawan jaririn Na'ima wanda ya kwashe kamarta tas, babu abinda ya ɗauka na khamal sai kyawawan fararen idanunsa, amma kamar yaron da Na'ima ta ɓaci. Ammi tace "kiyi haƙuri, bani da bakin baki haƙuri Na'ima, amma bai dace ki dinga danganta Abra da Khamal ba, Khamal da ya iya riƙe kansa  tun lokacin samartaka, tsayin shekaru mene zai sa kice wannan yarinyar ƴarsa ce? Da Khamal zai ajjiye shege da tun yana saurayi zai ajjiye ba yanzu daya yi Aure ba. Ba ina kare Khamal ba ne, Saboda rayuwa ta sauya Mutane na iya canzawa a kowane lokaci, balle rayuwa irinta sojoji d suke cuɗanya da mutane daban daban. Naima tace "Har mari na yayi akan gantalliyyar yarinya da babu wanda yasan Wacece ita, yanzu fa kiransa akai aka ce masa na haihu, haihuwar da yake ta burinta kalli yadda yayi watsi da komai? Bai damu da ɗan sa da yanzu duniya yake buƙatar jin ɗumin jikinsa ba, Nasan Khamal sai ya nuna bambanci tsakanin Shegiyar da ɗan daya haifa Wallahi ba zan iya ba" Na'ima ta ƙare maganar cikin kuka, Granny dake zaune tun ɗazu baki saki tana kallon Na'ima na tatala rashin mutunci, ko nauyin Ammi ba ta ji, ta runste idanunta tace. "Ki ga gantali a kanki, mace babu Tawakkali, nan nan fa naji ana cewa ƴar uwarki wacce ta mutu cikin Shege tayi, amma ke baki duba wannan ba? Kiyi ta zabga Masifa da wannan yammaci yanzu da kin mutu wajan haihuwa kice me?, to kawai a kiramin Khamal yaje ya nemo mace ya aura tun da ita wannan ba macan rufin asiri bace,  wallahi Na'ima ke ba abokiyar zama bace ban taɓa jin haka ba" Anuty Suwaiba dai na zaune tana ayyana irin yadda zata saka Na'ima taci Uban Abra, hankali kwance.... Ammi ta sake kiran number Khamal amma bai ɗauka ba. Khamal Khamis dake zaune gaban likita Abra na jikinsa wacce ta samu yin Bacci, a hankali yace "Pardon! Ban gane mene kake cewa ba" Likitan ya gyara zama bayan ya miƙawa Khamal scanning ɗin da akai ma Abra, tare da X-rays da kuma teses yace "Binciken da mukai duk sun nuna lafiyarta ƙalau, amma akwai yiwuwar ta kamu da depression, gaba ɗaya yarinyar kamar wani abu na tsorata ta. “Depression?" Khamal Khamis ya maimaita. Likitan yace "ka kwantar da hankalinka mana" Khamal ya girgiza kai yace "I can't, kayi min bayani menene Depression ɗin ma na kasa fahimta gaba ɗaya" Murmushi kawai likitan ya yi kafin yace. "It's normal for kids to feel sad, act grouchy, or be in a bad mood at times. But when a sad or bad mood lasts for weeks or longer, and when there are other changes in a child's behavior, it might be depression" Major ya ƙanƙame Abra cike da tausayi a hankali yace. "To me ze sa Abra ta kamu da depression" Likitan ya kalli Captain cike da kulawa kafin ya girgiza kai yace " Yana iya faruwa, a dalilin gado idan suna da shi a family, ko yanayin environment ɗin da suke zaune, ko wani abu da yake damunsu ko yake takura su". "Innalillahi wa'inna ilaihir rajiun!" Khamal ya faɗa sannan  yace "Abra tai ƙanƙanta ta kamu da irin wannan ciwon" Likitan yace "Ba abun mamaki bane ba, a wasu yaran akan iya identifying ɗin sa da wuri, kamar a shekarunta idan iyaye suka kula suka je Asibiti da wuri," Kallon Abra Khamal kawai keyi idan yace baya son yarinyar ya yi ƙarya, cikin kulawa ya kalli Dr yace. "What Should I Do if My Child Is Depressed?" Kan Likitan a ƙasa yana duba abu ya bawa Khamal amsa da faɗin. "A dinga bata isashen lokaci, a zauna da ita a tattauna a ji meye matsalolinta, a gane meyasa take takure kanta daga cikin mutane, kuma ba ta magana, tunda shekara uku a yara ai sun fara kiran sumaye da sauran surutu, amma ita kace sunanka kawai take iya kira, sannan kuma a cigaba da haƙuri za ta warke insha Allah" Khamal yai ajiyar zuciya, Bayan samun cikakken bayanai, hankalinsa ya ɗan kwanta, kuma yayi imani zaluncin Na'ima ne yake ƙara tsorata ta, ya jefata cikin firgici, amma duk da haka abun na damunsa na yadda Abra ba ta magana. Ɗaukan Abra ya yi zuwa waje, a hanya ya tsaya tare da siya mata kayan wasa kala-kala wanda zai ɗauke mata kewa. Kai tsaye gidansa ya nufa, yana zuwa ya samu Ammi a Parlo da Granny sai few people ƴan uwan Na'ima. Yadda Ammi ke kallonsa yasa ya ɗan shafa kai a hankali yace "First love" Da sauri Granny tai farat tace "Kaga ƙadaddararriyar matar da Ubangiji ya haɗaka da ita? Mace babu rufin asiri ko kaɗan?" Murmushi kawai Captain yayi domin ganin jariri da mutane a zazzaune, ya tabattar masa da haihuwa Na'ima tai. Ganin jaririn ya sanya ya mance da ɓacin ran da yake ciki... A hankali ya sauke Abra zuwa gefensa ya ɗauki Baby boy ɗin yana rungume shi. "Abinda kayi ka kyuta yanzu? Kasan illar abinda hakan ke nufi?" Ammi tai maganar tana kallonsa. Idanunsa akan Baby boy yace "I'm sorry first love ba zan sake ba" "Uhm bana son Fitina, bana son zuwan yarinyar nan ya kawo sauyi tsakanin ka da matarka" A hankali yace "In sha Allah, hakan ba zata sake faruwa ba" baki Granny ta taɓe tana faɗin "yanzu wanne suna ka sakawa Yaron?" A hankali yace "SALMAM KHAMAL KHAMIS" Ammi tace "Allah ya raya mai gidana Salman" A ranar Khamal ya lallaɓa Na'ima ya yi, tare da bata haƙuri, gaba ɗaya ya manta da abunda tai masa, saboda murnar haihuwar Salman, yai ta mata faɗa akan abunda ta aikatawa Abra, da bayanin likita tare da misalta idan akan Salman haka ke faruwa ya za ta ji?. Ta ce In sha Allah ba za ta sake ba, maganar iya baki ce domin bata kai zuciya ba, tana nan tana tunanin ta ina za ta sake ɓullowa lamarin. Duk da tarin munafunci da zagon ƙasa, haɗi da almundahana da makaman da gwamnati take bayarwa saboda a bawa jami'an tsaro, amma su General Ibrahim  suke ha'inci akan su, anyi nasarar kuɓutar da 'yan makarantar, bayan tafka uban gumurzu, suka kashe sojoji sosai a wannan karon ma. Wannan karon babu Captain Khamal, a wanda suka je opretion ɗin, amma shima anyi Nasara. Wannan Nasarar da aka yi, ta raunata alaƙar da ke tsakanin Gwaska da General Ibrahim, har yake tunanin ko General Ibrahim ke ƙoƙarin juya musu baya. Se da ƙyar sannan suka sasanta suka cigaba da yi wa harkar tsaron ƙasa ɓarna. Shekarar Salman Biyu a duniya, lokacin Abra nada shekaru biyar, a lokacin aka ƙarawa Captain matsayi zuwa Major. A lokacin kuma bincike ya tabbatar Abra bata da ƙarfin ji, ba sosai take jin magana ba kuma idan zatai magana da ɗan ƙarfi take.... (Conductive hearing loss) Likitan ya shaidawa Captain wanda yanzu ya dawo Major, ya tabattar masa da idan aka sa mata hearing aid za ta da din ga ji. Dan da fari Khamal ya zaci abun daga ƙwaƙwalwarta ne, se da ga baya suka gane, idan akai magana a hankali ba ta ji, se an ɗaga murya ko ta kalli bakin mutum, sannan take gane me yace. Aka samawa Abra hearing aid, wanda Abbin ya bada kuɗi masu yawan gaske, aka siyo shi daga Germany dan yi mata amfani da shi. General Ibrahim ya cigaba da cin karansa babu babbaka, tare da samun goyon baya, da ga manya manyan muƙarraban gwamnati, suka dinga kawo tarnaƙi ga matsalar tsaro, sannan ya cigaba da takun saƙa  da Khamal, mussaman da aka ƙarawa Khamal ɗin matsayi zuwa Major, tunaninsa kawai shi ne, yadda ze kawo ƙarshen Khamal, yayin da Khamal shi ma ya ɗora alamar tambaya akan General Ibrahim ɗin. Bayan shekara Goma! (MAFARIN ƘADDARAR ABRA). KAR KU BARI AYI BA KU, AKWAI TARIN SARƘAƘIYA DA BAN MAMAKI A GABA. BRIGHT PENS ZEE KUMURYA NIMCYLUV AYSHECOOL LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷* Brigh pens✍️ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya              *P.....8* Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗin a Arewabooks https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949 https://arewabooks.com/u/nimcyluv Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Abra ta sha wahala sosai zamanta a tare da Na'ima, samun sauƙinta kawai shine idan Major Khamal yana gari, ko kuma idan sun je gidan Ammi, ko idan ta na tare da Faris, wato Salman. GY BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY. MD ne wato Doctor GY a office ɗinsa, tare da wani mutum, GY ya gyara zaman glass ɗinsa ya kalli mutumin yace "wannan harƙallar ana samu sosai, zamu tura musu wannan mutumin da za suyi masa aiki, zasu turo mana da namu share ɗin". Mutumin ya gyara zama yace "amma doctor baka ganin zasu iya ganewa, dan mu ci kuɗinsu za'a tura su india?" "Ba zasu gane ba, ai ba yau muka fara wannan harkar da doctor Aman ba, shine shugaban Asibitin Darman Shakti, wannan ne karo na huɗu ina tura masa mutane, muna wannan harka" Mutumin yace "Amma in balli ya tashi akwai damuwa fa" GY yace "kar ka damu, ba wani balli da ze tashi, normal ne" Mutumin yai ajiyar zuciya yace "Shikenan doctor, Allah yai mana jagora". "Wallahi ranka ya daɗe, gaba ɗaya ji na ke aikin nan ya fita daga kai na, bana ƙaunar aikin nan yanzu gaba ɗaya". "Subhanallah, amma meyasa ka ke jin aikin ya fita da ga ranka ba ka so?" Cike da damuwa yace "Yanzu fisabilillahi abun da ake ya dace? Muna sadaukar da rayukanmu saboda ƙasarmu, amma manyanmu sun mai da ranmu ba a bakin komai ba, ƙirƙiri ga Nasara mu na kallo, amma se a dinga dakatar da mu?". Major Khamal ya gyara zamansa, ya kalli matashin saurayin da ke ta mita yace "kai min bayani sosai yadda zan gane" Matashin yace "Ranka ya daɗe, yaƙin da mu ka je ɗin nan, just recently, an gama shirya Komai mu ka shiga dajin nan, sedai ƙiri ƙiri aka hanamu harbi, su kuma kamar sun san dabarun da za mu yi amfani da su gurin yaƙin, su ka far mana da harbi, muna ji muna gani haka su ka far mana da harbi, se ɓuya mu kai Kamar wasu sakarkaru ba sojoji ba. Shekaranjiya mun biyo ta wani ƙauye, an turamu wani aiki, ga mu ga 'yan ta'adda muna kallonsu, su na ta wucewa akan babura, sun rako wani Babban ƙusa a cikin su, wanda da ina gabda Allah ya sa mun kama wanda suka ɗakko ɗin, da mun karya alkadarinsu, dan a lokacin mun fi su yawa da kayan aiki a hannu, mu kai waya mu kace a bamu umarnin harbi, gamu gasu, amma se cewa a kai ba ruwanmu da su, kawai mu wuce. Dan Allah ya rayuwa za ta yuwu da haka? Muna sanye da uniform amma ya zama aikin banza, sedai mu saka mu ɗau tsofaffin bindigogi muna hura hanci, idan munje yaƙi a fito a kashe mu, ba mu da kataɓus". Ɗan shiruu Major Khamal ya yi Sannan yace "waye kwamandannku, lokacin da kuka je yaƙin?" Cikin damuwa sojan yace "Captain Alex ne" Ai yana cewa Captain Alex, a hankali Major Khamal yace "General Ibrahim" A fili yace "Komai ze wuce insha Allah, idan irinku zaratan matasan sojoji na rasa karsashi suna ajiye aikin ya goben ƙasarmu ze kasance?" "Yallaɓai to mu ya ta mu goben za ta kasance, da mu da iyalan mu da iyayenmu, idan an tura mu daji an hanamu kare kanmu balle ƙasarmu, in mun mutu wa ze kula mana da su?" Major Yace "Allah yana tare da ma su zuciyar taimako, wadda ta ke aiki dan Allah". Yai ajiyar zuciya yace "to shikenan Yallaɓai, Allah ya wuce mana gaba". Major yace "Ameen, amma kar a karaya Please" jinjina kai yayi, ya gyara zaman bindigarsa ya fice. TWO YEARS LATER.... Tsaye yake a ƙofar kitchen, ya zuba mata idanunsa, tana sanye cikin riga da skirt na English wears, ta na gaban sink ta na wanke wanke, gefe kuma ta ajiye littafi tana yi tana karantawa. Murmushi ya yii tare da gyaran murya, duk da ya san ba jinsa za tai ba, saboda a hankali ya yi, cikin sanɗa ya je bayanta ya tsaya, ba zato ba tsammani ta waigo ta ganshi a bayanta, "Abbiii" ta faɗa a tsorace. Dariya Salman ya shiga yi mata ya ɗan ɗaga murya yace "Matsoraciya kawai" Ɗan tura baki tai tare da kai masa dukan wasa tace "shine zaka bani tsoro?" Yace "Sorry Uktyna, Abran Abbi, kina aiki kina karatu?" Tace "Eh mana, kasan from now, anytime our timetable can be fixed, amma kai kana yawon ball ko?" Ɗan sosa kai Salman yai yace "don't mind me, dan Allah ki dafa min indomie mana". Ɗan buɗe baki tai da mamaki tace "Ohh God, Faris kafin ka fita fa almost kai ka cinye Abincin rana fa" "Eh, to ai ball nai gaba ɗaya ji nake kamar ban ci komai ba" Abra tace "to yanzu dai kana gani aiki nake, bari in gama se in dafa maka" Salman yace "let me help you with the dishes, bari in wanke se ki dafa mana" Abra tace "ni a ƙoshe nake, kai ne dai sarkin ci gashi nan kafi kowa girma a gidan nan" Salman yace "ke ma da za ki dinga cin abinci sosai kamar ni ɗin nan, da kin yi girma sosai, amma yanzu kalli ba wanda zece kece yayata, amma na ji daɗi gara a dinga cewa nine yayanki" Dariya Abra tai tace "Koma dai menene nice Babba" "Ba wani nan, in aka duba girma na fi ki girma, baki fi in goyaki in ta gudu da ke a cikin GRA ba" Haka ya cigaba da tsokanar ta, ya karɓi wanke wanken, ita kuma ta ɗora tukunyar dafa masa indomie. "Kai Salman meye haka? Me kake yi a kitchen?" Salman ya waiga ya kalli in da Mami ke tsaye a ƙofar kitchen ɗin, ita ma Abra waiwayawa tai tana kallon Mamin. "Nace me kake a kitchen?" Salman yace "Mami wanke wanke na ke ta ya Sister" "Uban me ya haɗaka da wanke wanke, mace ne kai? Me ma kake yi a kitchen ɗin ba ka da aikin yi ne?" Cikin sanyin halinta da son bawa ɗan uwanta kariya Abra tace "Eyya, Mami yi haƙuri ni nace ya tayani" "Dalla rufemin baki da ke nake?" Abra ta ja bakinta tai shiru, Sam Salman baya jin daɗin yadda Mami ke treating ɗin su da banbanci, yana mamakin yadda Mami ke banzatar da Abra kamar ba ita ta haifesu ba, ko da yake ya ga Abbi ya fi son Abra, shi kuma Mami tafi son sa, amma duk da haka ai shi Abba baya hantararsa kamar yadda Mami kewa Abra. Salman yace "Mami, ba Yaya ce ta sani wanke wanke ba, aiki take nace ta dafa min noodles, shiyasa na karɓa nake tayata". "Dalla ajiye kwanukan nan ka zo ka fita ka bar kitchen ɗin" cikin tausayin yadda yayartasa tai kasaƙe tana binsu da ido, ya ajiye kwanukan, yace "to bari in karɓi girkin" "Salman kana so in zageka ne ko? Ba zaka zo ka bar kitchen ɗin nan ba?" haka Salman ya bar kitchen ɗin jiki a sanyaye. Idan da sabo Abra ta saba wannan halin ko in kula da Mami take nuna mata, amma sam hakan ba ya mata daɗi, tana son kasancewa da mahaifiyar ta ita ma, ta ji ɗuminta su yi hira, amma hakan yana faruwa ne kawai idan Abbi yana gari, da zarar baya nan, shikenan za su koma yadda su ke. Salman yana nan Falo a zaune, Abra ta fito da plate a hannunta, sai tururi taliyar take, murmushi yai yace "Yawwa ƙanwata, Allah yai miki albarka" haɗe rai tayi tace "idan ba zan mayar ba" Salman yace "Am sorry sweetheart, tuba nake babbar yaya, uwar son girma" Ta ƙaraso ta ajiye masa plate ɗin abincin, ta ɗakko masa ruwa da kofi ta ajiye masa, ya ɗau plate ɗin yana cewa "tun da na fara jin ƙamshin Abincin nan nake salvating, Ko restaurant zamu buɗe ne?" Abra tace "in dai zaka dinga girkawa shikenan, and please my bro, a ɗan tsagaita da yawon ball ɗin nan, ka ga exams zamu fara fa, amma baka da aiki se dai kaci Abinci, kai video games, se yawon ball wanda be dace ba, kaga Abbi yadda yake ta ɗawainiya da mu akan harkar karatunmu, ba sa jin daɗin result ɗin da kake kawowa a 'yan kwanakin nan. And bana jin daɗi inga ana maka faɗa bana so, dan Allah ka mai da hankali akan karatun ka ka ji dearna, You are brilliant before ban san meyasa ka dena son karatu ba yanzu, performance ɗin ka ya yi baya" maimakon yai mataa magana seya ɗage mata gira ɗaya. "Ina maka magana kana ɗagamin gira" Yai dariya yace "dariya ki ke bani ne, wai ke a dole ga babba kina faɗa, Sannu Mami" Filon kujera ta jefa kwaɗa masa a ka tace "ina maka magana ka mai dani abun dariya ko?" Cigaba da yai da dariya yai yana " 'yar ficikar Abbi, don't mind me, insha Allah zan baki mamaki this time around, ki mana timetable, zamu din ga karatu tare, in dai hakan ze saki farinciki". "Wace irin jarabace ne wai Wannan? Na koro ka da ga kitchen, shi ne ki ka kuma biyo shi nan, meye hakane Abra, waike wace irin mara hankali ce ne?" Salman yace "Ohh my goodness, Mami idan ban hira da 'yar uwata ba da wa zanyi? Mami idan ba ku ba wa muke da, wanda zamuje mu sake da shi haka? Meye laifin Yayata ne? Haba Mami? Yanzu haka faɗa takemin akan karatu, in mutum be shaƙu da ɗan uwansa ba to gurin wa zeje?" Hajiya Na'ima tace "Ikon Allah, Au Salman har mun kai gaɓar da zan dinga faɗa kana mayar min akan wannan yarinyar? Kaga Salman ka kiyayeni" Abra tace 'Mami kiyi haƙuri dan Allah..... "Dalla rufemin baki, da anyi magana yenyen ayi haƙuri, ba yau ba gobe kuna liƙe da juna, ba ku san kun girma bane, kusancinku da juna ba shi da wata fa'ida ba?" Kai tsaye Salman ya gane in da maganganun mahaifiyarsa suka dosa saboda haka yace 'haba Mami, ya zaki dinga Wannan maganar? She's my biological sister, meyasa zaki dinga kawo wannan tunanin?" Ji tai kamar ta fasa ƙwai a gurin kowama ya huta, Salman ya ji Abra ba yayarsa bace, dan ba zata manta lokacin da ta taɓa gaya masa ba, befi 3yrs ba, dan haka baze iya riƙewa ba, amma da ta tuna kashedin Major, wanda  se ta haɗiye ba ta faɗa ba, dan haryanzu ba ta ƙaunar Abra, ko kaɗan. Abra kam tuni ta bar falon, hawaye fal idonta, ta rasa meyasa Mami ba ta sonta, kuma ba ta san ta dinga zama da ɗan uwanta, tana son Salman sosai, da shikaɗai take sakewa se Abbi, dan ita ko ƙawaye ba ta da su, saboda ba ta son hayaniya sam, hayaniyar Salman kawai take iya jurewa. Ta koma ɗaki tai shiru tana tunanin menene laifinta a gurin Mamainsu?. Mami ta cigaba da zazzagawa Salman faɗa, kamar za ta dake shi. Sallamar da akayi ne ta sata yin shiru tare da amsawa. "Ke da waye ne kike ta wannan ɓaɓatu haka?" Cewar Anty suwaiba. "Bari Anty suwaiba, ni da wannan sakarkarun mana, kullum yaron nan yana liƙe da wannan yarinyar sekace jaraba, na rasa irin wannan abu, nayi nayi amma yaƙi ji, abu kamar jaraba". Anty suwaiba cike da duniyanci tace "ban da abunki idan be zauna da 'yar uwarsa ba, da wa ze zauna? Tsakanin ɗa da mahaifi ai se Allah". Salman dai ko Anty suwaiba be samu kulawa ba, ya tashi ya fita tare da jin tausayin Yayarsa. Suwaiba ta kalleta tace "Ke Na'ima meyasa baki da wayo ne? A garin wannan zafin ran da masifar taki wataran zaki faɗa abunda ake ta ɓoyewa, idan kuwa kika kuskura kika gayawa yarinyar nan ba ke kika haifeta ba, kin san mijinki baya Magana biyu ko? Kuma muddin ya sakeki ba ke kaɗai ya saka ba, har mu ya saka, dan Allah ne gatanmu Khamal ne gatanmu, duk asirinmu a lulluɓe a ƙarƙashin inuwar arzikinsa". Hajiya Na'ima ta zauna tace "ni Wannan lamarin ya isheni, yau shekaru nawa yarinyar nan tana gidan nan, amma babu abunda ya canza, shawarar ki ba wadda ban amfani da ita ba, amma babu alamar zata bar gidan nan, yanzu na dena jin tsoron Khamal yace ze Aureta, amma Wannan shishshigin da yaron nan yake mata ne bana so". Anty suwaiba tace "to ke ika ruwanki? Shekara uku fa ta bashi, ta ina ze Aureta kuma Khmal dai baze taɓa cewa ze aurawa ɗansa Ita ba, in dai ba ya so gayamata ba shine mahaifinta ba" Na'ima tace "kin san wani abu kuwa?" "A'a sekin faɗa" 'yadda Kamal yake fifita ta akan Salman ne ya ƙona min rai, ga ɗan da ka haifa ta sunna, amma ka maida shegiya 'ya kana nuna naka bakomai bane" "To ya zaki yi, taki ƙaddarar kenan" Tsaki Na'ima tai dan ji take kamar ta kori Abra daga gidan daurewa kawai takeyi. Abra na ta jin daɗi gobe Abbi ze dawo, idan ya dawo zata tambayeshi tana son zuwa hutu gidan Ammi, dan Ammi tafi sonta akan Mami, babban abunda yake sake bawa Abra mamaki be wuce yadda ake cewa dangin mahaifiya sun fi son ɗa, akan dangin mahaifi ba, amma ita a nata dagin, dangin mahaifinta da mahaifinta sunfi sonta fiye da mahaifiyarta da dangin ta. Domin ƙauracewa ire iren wannan tunanin, se Abra ta ɗaura alwala ta fara haddarta ta Alqur'ani me girma. Saboda sanin halin Salman, na rashin jure yunwa yake sa Abra ta tashi da wuri ta ɗora breakfast, gashi kuma Abbi ze dawo gari, dan haka bisa al'adarta ita ke shiryawa Abbin nata Abincin da za'a karɓe shi, amma a wannan karon har gari ya waye ƙarfe tara Abra ba ta fito ba. Hakan ya bawa Salman mamaki, dan haka ya wuce ɗakinta, dan jin ba'asi. Yana zuwa ya tarar da ita ta dunƙule a bargo, se kuka take kamar wata 'yar yaye. Cikin hanzari ya ƙarasa gaban gadonta yana faɗin "Yaya, menene? Kukan me kike?" Abra ta riƙo hannunsa tace "Salman cikina ciwo" "Subhanallah, sannu ciwo yake miki?" Ta jinjina masa kai tana kuka. "To kiyi shiru, ko dai cikin ki ne ya ɓaci, ina da maganin gudawa" Kasancewar ta shagwaɓaɓɓiya cikin shagwaɓa tace "Um, Um ni ba gudawa nake ba" Salman yace "to bari in kira Mami" "A'a ni karka tafi ka barni a nan" Salman yace "to, bari in kirata a waya" Abra ta riƙe hannun Salman gam, tana cigaba da rintse ido. Falo yaje ya ɗakko wayar gida, ya dawo ɗakin Abra ya zauna Wayar Mami ya kira, ya sanar mata da halin da Abra ke ciki, se dai amsar da ta bashi sam be ji daɗin ta ba, na ya kira mata likita ita tana da abun yi. Haka Salman ya nemo lambar doctor Habib, wanda yake Family doctor ɗinsu ne, kuma soja ne, doctor Habib yace gashi nan zuwa. "Faris" ta kira sunansa. Yace "Na'am Yaya" "Har amai fa nake yi, da ciwon kai" Yace "to kiyi haƙuri, doctor yana hanya" Tace "Ina Mami?" Salman ya ɗanyi jimm sannan yace "tana zuwa, kiyi haƙuri" yai maganar cike da kulawa. Yana nan zaune tare da Abra, Doctor ya kira wayar gidan Salman ya ɗaga, ya ce "gani nazo, tana wani ɗakin ne?" Salman ya kalli Abra, kayan bacci ne a jikinta, ya ɗan tsuke fuska kamar yana gaban doctor yace "jiramu a falo" Ya kalli Abra yace "tashi muje likitan ya zo" Abra ta yunƙura ta tashi, se dai Salman ya zare ido yace "Yaya, meye wannan a jikinki?" Da sauri ta waiwaya, jini ne duk ya ɓata mata shimfiɗa da jikinta. Aikuwa ta fashe da kuka tace "Na shiga uku, meya sameni Faris mutuwa zanyi?" Salman yace "Innalillahi ba zaki mutu ba, ki canza wasu kayan, semu gayawa doctor, ai normal ne" Salman yace "to shiga ki canza kaya, bari in jiraki a falo" Haka ya koma falo shi da likita suka jira Abra, ta fito tana ta tsantsame jikinta, likitan yai mata tambayoyi, nan ya tabattar da period ta fara, se dai ya zo mata da wahala, dan haka ya sakamta drip, tare da bata magunguna da shawarwari. Salman yaje ya samu mahaifiyarsu kwance a ɗakinta, ta haɗa abinci ta karya, Salman yace "Mami Yaya ba lafiya fa" "To ni na saka mata ciwon da zan cire mata?" Salman ya girgiza kai yace "A'a, doctor yace wai idan da wannan Pad ɗin da mata ke amfani da ita wai ki bayar". "Me za'ai da ita?" Ta tambaye shi. " ukhty ce za tai amfani da shi" Hajiya Na'ima ta ɗanyi jimmm, sannan tace "jeka toilet ka ɗauka" Salman yaje ya ɗakko ya fice, dan abun kunya, Hajiya Na'ima na gidan, amma se doctor ne ya nunawa Abra yadda ake amfani da pad ɗin, hakan ba ƙaramin ciwo yai wa Salman ba, duk da yana da ƙarancin shekaru amma yana matuƙar kishin yayar ta sa, he is always protective to her, ko a Makaranta ba ya son yaga wani ya raɓeta, wanda tun suna yara sosai baya son ko baƙi sukai yaga yara sun fiye zuwa in da take, se ya dinga ganin kamar zasu cutar da Ita kasancewarta ba me hayaniya ba. Tana nan kwance, doctor yana jiran ruwan ya ƙare ya samata wani, Salman yaje ya ɗakko bargo ya rufe Abra, yaje kitchen ya dafo mata tea ya ɗakko bread ya zo ya haɗa mata. Shi kansa doctor yanayin gidan Khamal yana burge shi, kan yaransa a haɗe yake, suna son juna sosai, sai dai yana mamakin yadda matarsa bata bawa lamarin 'yar ta ta mahimmanci. Da drip ɗin farko ya ƙare, Salman da kansa ya din ga bawa Abra abinci, har ta ɗan ci sosai, sannan ta kwata aka kuma saka ɗayan, ya nunawa Salman yadda zata sha magungunan ta, da yadda ze cire mata ruwan idan ya ƙare, sannan ya fita saboda yana da in da za shi. Salman se jera mata sannu yake, ya ga ta kai hannu tana shashshafa gashin kanta, cikin kulawa yace "Ukty ya dai?" "Ni kitson nan ne ya dameni, ƙaramin ciwon kai yake" ta faɗa har da ƙwalla. Salman ya kalli kitson, manya guda shida, ga gashin nan baƙiƙirin, kwance a farar fatar kanta, yace "ko a tsefe ne?" Tace "eh" ya tashi ya tafi ɗakinta, ya ɗakko comb da kibiya, ya dawo ya zauna ta ɗora kanta akan cinyarsa, ba'a jima ba ya tsefe kan nan tas, dama Salman ya saba da tsifa, shi yake tsefewa Abra kai wasu lokutan. Ya shiga taje mata a hankali dan kar taji zafi, gashin ya baje a jikinsa, ya rufe mata fuska. Hajiya Na'ima ce ta buɗe ƙofar part ɗinta ta fito, turus ta tsaya tana kallon Salman, "meye haka kamar wani ɗan daudu?" Mami tai maganar tana nuna su. Salman yace "Mami ba kiga ba ta da lafiya ba, tsefe mata nake" "Au bayan kurumtakar kuma, kuturwa ce ita da ba zata iya tsefewa ba, kai yau nina ke ganin tsiya, tsifar ma se kayi mata namamajo" Abra tace "Faris bar shi haka, nagode sosai". Salman yace "tsaya in sa miki ribbon ɗin, sai a mai da hular" "Ina maka magana kana cewa seka sa mata hula, ina ga nan gaba kuma shagon kitso da lalle zaka buɗe, sai kuma suyar doya da ƙwai tunda ka zama ɗan daudu" Shi Salman ma dariya Mamin ta bashi yace "haba Mami, in ba gashin ki kona Ukty ba, gashin wa zan iya taɓawa, Mami ki mata sannu mana ba kiga ta rame ba?" "Ba zan mata sannun ba, a kanta aka fara haila da za ta wani langaɓe ta na numfarfashi?, dalla tashi ka bar gurin nan, in ban yi da gaske ba ina ga nan gaba maƙale hannu zaka fara irin na 'yan daudu" Jiniya ce ta cika layin, zuwa cikin gidan, wanda hakan ke almta cewar megidan ya dawo. Wani murmushi ne ya bayyana a fuskar Abra, tare da murna tace "Abba ya sauka a gids, se dai Wannan karon ban masa girki ba". Kan su gama maganar Abbi ya shigo falon tare da sallama. Yana ganin Abra a kwance a gigice ya ƙarasa yana faɗin "sweetheart what's wrong? Ya na ganki a kwance? Har da drip haka?" Hajiya Na'ima ta hau yaƙe tace "Yallaɓai barka da sauka" "Yawwa Madam, meya sami Abra na?" Salman yace "Abbi ba ta da lafiya ne" Hajiya Na'ima tace "yanzun nan doctor ya bar gidan nan, she start first period today, shine take ta shagwaɓa da koke koke" Abbi yace "Eyya, sorry my dear, dole ta damu sosai, this is her first day is not easy for her, sannu Sweetheart". Baƙin cikin yadda Salman da Khamal suka lalace akan Abra, kowa yana mata Sannu kamar za su maida ita ciki ya sa wani baƙin ciki ya turnuƙeta, gashi se wani shagwaɓa Abran take, har da hawaye, Hajiya Na'ima ji take Kamar ta ɗura musu Ashar su duka ta huta. Haka Hajiya Na'ima ta shiga hidimar dole, da yaƙe ta samar musu da Abinci, kasancewar me girkin gata kwance ba lafiya. Abba da kansa ya din ga bawa Abinci, Salman kuma yana ɓallo magani yana bata. Hajiya Na'ima baƙin ciki ya sa ta koma ɗakinta tana huci, tana jin kamar ta ɗakko muciya ta saukewa Abra muƙamuƙi kowa ya huta. Haka Abbi ya wuni ririta Abra, tare da yi mata nasiha akan yadda zata kula da kanta da Addinin ta. Sakkowa take daga kan bene, hannunt a riƙe da waya ƙirar iPhone, se taune taune take. "Meenal" ya kira sunanta. Ƙarasa sakkowa tai daga kan benen, cikin siririyar muryarta tace "Daddy i miss You" Yace "I miss You too, ya school ɗin?" "School Alhamdilillah, mun kusa gamawa, ya aiki ya fiɗa" Yai murmushi yace "fiɗa sekace wani mahauci?" Tai murmushi tace "Daddy ai banbancinku ku mutane kuke fiɗewa" Yace "Meenal kenan? Ina fatan zaki gajeni ai" Cikin sauri Meenal tace "No, no, Daddy, ka manta Art class nake yi, ni bana son ganin jini, is so iiritating to me, ni masscom zanyi" "Yanzu shikenan Daddy baze samu magajiya ba?" Tai dariya tace "Daddy ba shi da magajiya" Yai murmushi yace "To shikenan, Allah ya ida nufi". "Aku me Magana, tun da kika dawo gidan nan kowa se yasan kin zo, se surutu kike masa ki bar shi ki huta mana" cewar matar da take sakkowa daga kan step me tsananin kama da Meenal. Meenal tace "Mummy I have to show him how much I miss him" Doctor yace "And i miss you too dear, yau tare ma zamu ci Abinci ma, banda ma ke kike son boarding ɗin nan, ai da ni ba in da zaki matsa daga kusa da ni". Abra ta ji sauƙi sosai, dan har ta koma makaranta, Salman se nan nan yake da ita yana bata kulawa, duk da ita tana art class shi kuma yana science, amma buni buni se yaje ajinsu ya ga ko tana Lafiya. Kasancewar Khamal yana nan, hakan yasa Abra ta samu sauƙin hantara da zagi daga gurin Mami. Wani mummunan labari ne ya iske Major, kasancewar an kama manya manyan 'yan ta'adda, al'umma na ta murna, cewar ko ba komai an rage mugun iri, ku ma za'a samu sassauci dan za su bada wasu bayanan, idan aka hukunta su ko ba komai, wasu za su ɗan rage raɗaɗin rashin 'yan uwansu da 'yan ta'addan su ka kashe, da wanda aka raba da mahallansu, da wanda aka sace musu 'yan uwa, da kisan da aka din ga yiwa mutane ba dalili. Se dai bayan zama da shugaban ƙasa yai da manyan jami'an tsaro, labari ya cika gari cewa, gwamnati za tai afuwa ga waɗan nan 'yan ta'adda, za ta mai da wasu Makaranta wasu kuma a ba su aikin yi.   Hakan ba ƙaramin cece kuce ya janyow ba, mutane na ganin ya za'ai wanda ya kashe mutum ɗaya an kama shi an ɗaure an yanke masa hukunci, amma wanda suka kashe dubban mutane, suka girgiza tattalin arzikin ƙasa, su za'ai musu afuwa har da ma samun wani tagomashi da ga gwamnati, nan mutane suka dinga sukar wannan hukunci na gwamnati. Labari ya iske Major Khamal, shi kansa ya sa rai tare da zuba ido akan matakin da gwamnati za ta ɗauka, dan sun sha baƙar wahala tare da tsananta bincike, kan su samu nasarar kamo wasu daga cikin manya manyan mutane da ke cikin ƙungiyar ta'addanci, amma katsam ya samu labarin matakin gwamnati akan lamarin. A hankali ya miƙe tsaye yana zagayawa yace "lokaci ya yi, da zan yi wasan kura da duk wanda suke da hannu cikin lalacewar tsaro a ƙasar nan! Sedai hakan ba ze yuwu ba se da goyom bayan manya, amma suwaye manyan? Su ne dai wanda sukewa harkar zagon ƙasa.   A hankali ya nemi guri ya zauna tare da dafe kansa, da yai masa wani irin nauyi. Hajiya Na'ima na ta shiri da daddare, zata tafi ɗakin Yallaɓai Khamal, sai dai wayarta ta fara ringing, ta amsa wayar tare da sata a kunnenta. "Barka da dare Hajiya Na'ima, mrs Khamal" Cike da rashin fahimta ta amsa da "yawwa barka wake magana?" "Garajen me kike? Zaki ji ne, ya 'yata take ina fatan tana lafiya?" "Wace 'yar kenan?" "Abra Khamal Khamis, na kiraki ne dan jin ya 'yata take, fatan kina riƙemin ita da amana, sannan ina miki albishir da cewa daga yanzu zuwa kowane lokaci zan iya shigowa gidanki, domin cigaba da rainon 'ya ta da kaina!. LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU* _Brigh pens✍️_ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya                                P9 Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗin a Arewabooks https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949 https://arewabooks.com/u/nimcyluv Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Wata irin bugawa zuciyar Na'ima ta yi, cikin ƙaraji ta ce. "What? Wacece ke?" Dariyar rainin hankali wadda ta kira wayar ta yi ta ce. "Ko ba ki ji abun da na faɗa dai-dai ba ne in ƙara maimaita miki?" Wata Uwar ashariya Na'ima ta ƙunduma ta ce. "Wallahi k'arya kike matsiya, Shegiya karuwa, Khamal nawa ne ni kaɗai babu wacce ta isa ko da rab'ar shi ne ta yi balle har ta aure shi, ba'a halicci mace ba wallahi." Cikin murmurshi ta ce. "Za kuwa ki gani, ganin idonki, ki cigaba da kular mun da my Daughter yanda ya kamata." Sannan ta ja tsaki ta kashe wayar. A haukace Na'ima ta sauke wayar daga kunnenta ta shiga bin screen ɗin wayar da kallo, tamkar za ta ga matar da ta kira ta a cikinsa, babban baƙin cikinta sai da aka b'oye numbern sannan a kira ta. Wani irin tuƙuƙwin baƙin ciki zuciyarta take mata, cikin takaici ta cillar da wayar, Allah ya taimaka ta faɗa kan gado. Hannunta ta ɗora akan goshinta tana bubbuga kanta ta fara magana ita kaɗai. "Impossible! Wallahi ba zai yiwu ba, sai na gano ko wace ce ke na kashe ki, sai dai ki auri Khamal a lahira ba dai a duniya ba, matuƙar ina numfashi babu macen da ta isa ta shigo cikin gidana a matsayin matar Mijina. Wayarta da ta cillar ta ɗauka ta fice daga ɗakin a matuƙar fusace ta nufi part ɗin Khamal. Salman dake zaune a parlour yana kallon Ball ya bi ta da kallo cikin mamakin ganin yanayin da ta fito kamar wadda ba ta cikin hayyacinta. "To Macuci, mayaudari, azzalumi, mugu, yau Allah ya toni asinka, dama an ce rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya tal ta mai kaya." Abun da Na'ima ta faɗa kenan bayan ta tura ƙofar ɗakin Khamal da ƙarfi ta shiga. Da mugun mamaki Khamal dake zaune yana operating system yake kallon ta, kasa cewa komai ya yi saboda tsananin mamaki. Cikin kuka ta ce. "Ka cuce ni, na yarda da kai Khamal, amma ban san me ya rud'e ka, ka ci amanata ba." "Na'ima, wannan maganar banzan da kike yi duk na mene ne?" "Na cikin shegen da kika yi aka haifi waccan shegiyar yarinyar ne." Fauu! Fauu! Khamal da ya miƙe cikin sauri kamar wanda aka hankad'a ya saukewa Na'ima tagwayen maruka a fuska. Cikin tsananin ɓacin rai ya fara magana. "I told you Na'ima, duk abun da zaki yi ki yi amma kar ki ƙara danganta mun ƴa da Shegiya, na faɗa miki ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba." Na'ima dake riƙe da kuncinta wanda take jin kamar ba ya jikinta saboda tsananin azaba, idanunta na zubar da hawaye ta ce. "Ni ka mara Khamal akan waccan yarinyar mara asali?" "Yes, kuma idan kika ƙara maimaita abun da kika faɗa, abun da ya fi mari ma zan miki wallahi!" Yana gama faɗar haka ya fice ya bar mata ɗakin ya tafi other room dake part ɗin ransa a matuƙar b'ace. Da wani irin kallo ta bi shi har ya fice, wani irin ɗaci take ji tun daga zuciyarta har zuwa bakinta. Zama ta yi a bakin gado tare da fashewa da kuka, a ranta tana faɗin, 'Komai zai faru sai dai ya faru, amma wannan karon ba za ta hak'ura ba, ba za ta cigaba da zama da Shegiya a gidanta ba, sai a yi duk wacce za'a yi.' Sai da ta ci kukanta ta ƙoshi sannan ta lalubo wayarta dake gefenta, dan ko gani ba ta yi sosai saboda masifar ciwon da kanta yake mata. Numbern Aunty Suwaiba ta kira, ringing biyu ta ɗaga tare da ambatar sunanta. Kuka Na'ima ta sakar mata cikin rashin abun yi. "A'a, Lafiya? Me ya faru? Wani abun ne ya samu Khamal ko Salman zaki kira ni a daren nan ki saka mun kuka?" Aunty Suwaiba ta tambaye ta cikin kid'ima. Cikin kukan ta ce. "Na shiga uku na lalace Aunty, ta tabbata Abra ƴar Khamal ce ta cikinsa, duk abubuwan da ya faɗa mun a baya ashe duk k'arya ne, shashasha wadda ba ta san abun da take yi ba kawai ya mayar da ni." "Ke wa ya faɗa miki? Mene hujjar ki na cewa hakan?" "Wadda ya yiwa cikin ta haifa masa ita ce ta kira ni ta tabbatar mun da zargina." Kwashe duk yanda suka yi da wadda ta kira ta, da yanda suka yi da Khamal ta yi ta faɗawa Aunty, ta ƙara faɗin. "Ni kam yarinyar nan ta zame mun bala'i da masifa a gidan Aurena, da ina rayuwata da mijina hankali kwance amma yanzu ta shigo duk ta wargaza mana farincikinmu." "Na rasa yaushe zaki yi hankali Na'ima, shegen kishi ya rufe miki ido kin kasa ganin dai_dai, idan ma ta tabbata mahaifiyar Abran ce ta kira ki sai ki yi masa wannan haukan? Ke sai ka ce ba jinin Mama ba? Yaushe zaki ko yi kissa ne. "Aunty wannan abun fa ba zancen wata kissa ba ne, ba za ki gane yanda nake ji ba ne a cikin zuciyata, kamar ana rura garwashi haka nake ji, ni yanzu kawai ki faɗa mun yanda zan yi Yarinyar nan ta bar gidan nan, dan wallahi ba zan cigaba da zama da ita ba." Numfashi Aunty Suwaiba ta sauke ta ce. "Na ji zan faɗa miki, amma sai kin mun alƙawari zaki je ki bawa Khamal hak'urin maganganun da kika faffaɗa masa." "A saboda me zan ba shi hak'uri? Shi fa ya mun laifi, har da mari fa, abun da tunda nake da Khamal bai taɓa mun ba. Ki bar ma wannan maganar, kawai ki faɗa mun yanda zan yi, abun fa bana sanyi ba ne, na ga baki ɗauki abun serious ba, ko dan bake aka yiwa haka ba?" Ta yi maganar fuskarta na nuna tsantsar ɓacin ran da damuwar da take ciki. Aunty Suwaiba ta ce. "Ba haka ba ne Na'ima, kin san bayan ke babu wanda ya kai ni baƙin cikin zaman Yarinyar nan a gidanki, amma bana son ki yi abun da zaki zo kina da na sani ne." "Babu wani da na sanin da zan yi, wallahi sai dai mu rabu da Khamal, matuƙar ya zaɓi cigaba da zaman yarinyar nan a gidan nan, haba abun ya ishe ni haka, hak'urina ya ƙare." Ta ƙarashe maganar cikin kuka, wani irin kishi na nuƙurƙusar zuciyarta. Daƙyar Aunty Suwaiba ta rarrashi Na'ima ta yarda za ta je ta bawa Khamal haƙuri, shi ma dan ta ce idan ba ta je ta bashi ba, baza ta faɗa mata yanda za ta yi Abra ta bar gidan cikin sauƙi ba, ba tare da an yi tunanin da saka hannunta ba. Ita kuma Na'ima gani take Aunty Suwaiba ba za ta gane halin da ta ciki ba ne, a ganinta ita aka cuce ta, kuma an hana ta kuka. Aunty Suwaiba ba kuwa tsoron kar Auren Na'ima ya mutu su shiga uku take, dan ita suka dogara ita da sauran ƴan'uwansu. Domin ta fuskanci babu abun da Khamal ba zai iya ba akan Abra. "Amma fa Aunty daƙyar in zai hak'ura, dan yanda ya hasala ko su Ammi na zaga sai saka." "Zai hak'ura mana, kamar kin manta halinsa ne, yana da zafi amma kuma yana da sauƙin kai wani lokacin, ki nuna kin damu kin yi nadamar maganganun da kika faɗa masa, duk taurin ransa zai hak'ura. Su Maza suna san ka yi musu laifi ka amsa ka yi, kuma kar ki bari sai gobe, da zafi_zafi ake dukan ƙarfe, ki je yanzu yanda zai gane da gaske kin yi nadamar, in ya so cikin nutsuwa sai ki faɗa masa komai na kiran wayar da aka yi miki." Numfashi Na'ima ta sauke ba don son ranta ba ta ce. "Shikenan Aunty, zan yi duk yanda kika ce." "Yawwa, ki fa yin fa, dan na san halinki sai ki amsa ki kuma ƙi yi." "Zan yi fa da gaske." "Shikenan, sai mun yi waya da safe, ki kwantar da hankalinki, na miki alƙawarin zaman Shegiyar yarinyar can a gidanki ya zo ƙarshe." Duk yanda take jin tsananin zafi da k'una da baƙin ciki gami da takaici a cikin ranta, haka ta taushi zuciyarta ta miƙe tana goge hawayen fuskarta bayan sun gama wayar ta nufi ɗakin da Khamal yake. A hankali ta tura ƙofar ɗakin, ta yi sa'a ƙofar a buɗe take, a zaune ta tarar da shi akan bedside drawer ya riƙe kansa da hannayensa, alamun ransa ya kai ƙololuwar ɓaci. Jin ƙamshinta ya saka shi ɗago kansa da sauri tare da miƙewa yana kallon ta. Kafin ta ce uffan ya nuna mata ƙofa da hannunsa cikin ɗaga murya ya ce. "Get out!" Marairaicewa ta yi ta buɗe baki za ta yi magana amma ya ƙi ba ta damar hakan. "I said get out from this room." Ya faɗa a tsawace kyakkyawan idanunsa da suka rine zuwa ja duka a waje. Jikinta ne ya ɗauki ƙyarma, ba ta yi tunanin ya ɗauki zafi haka ba, tsugunnawa ta yi akan ƙafafuwanta ta fashe da kuka ta ce. "Please My Man listen to me, ka saurari abun da zan faɗa maka." "Me kuma ya rage baki faɗa mun ba Na'ima? Me zaki ce mun? Duk yanda nake danne zuciyata akan kar mu matsala amma ba kya gani? To tunda haka kika zaɓa mu zuba ni da ke a gidan." "I'm sorry, dan Allah ka saurare Ni, wallahi na yi nadamar maganganun da na faɗa maka, amma ka mun uzuri raina ne a matuƙar ɓace a lokacin." Numfashi ya sauke ganin yanda take kuka sosai sai zuciyarsa ta fara karyewa, ya yi tunanin da gaske ta yi nadamar ne har cikin zuciyarta. Fuska a ɗaure ya ce. "Ba na son jin komai daga gare ki a yanzu, maganganun da kika faɗa mun ɗazu ma sun ishe ni." Wani yawu ta haɗiye mai ɗaci ta shiga girgiza masa kai. "Dan Allah Khamal ka saurare ni ka ji bayanin da zan yi maka." Zama ya yi a gefen gado ya ce. "Ina jin ki." Ajiyar zuciya ta sauke ta bashi labarin kiran wayar da aka yi mata. Kallon ta kawai yake har ta miƙo masa wayarta tana nuna masa kiran da aka yi mata da Private Number. Karɓa ya yi ya duba amma bai ce komai ba, ita ma ba ta ce komai ba sai idanu da ta zuba masa, imagine kawai take yi a cikin ranta ƙaramin yaƙin da za'a yi idan ya amsa laifinsa. "Ba zance k'arya kike yi ba, amma gaskiya ban yarda da wannan abun ba, babu wanda zai kira ki ya faɗa miki haka, because ban da Family na da naki da wasu daga cikin abokan aikina, babu wanda ya san ta yanda muka samu Abra da matsayinta a gidan nan." Wani malolon baƙin ciki ne ya ƙara cika zuciyarta, wato ma maƙaryaciya ya mayar da ita? Ita ta shirya hakan nufinsa ko kuma cigaba da raina mata hankalin da yake yi tun lokacin da ya kawo Abra zai yi? Ji take kamar ta tsinka masa mari dan baƙin ciki, amma dai ta daure ta yi kalar tausayi ta ce. "Wallahi da gaske nake, akan me zan ƙirƙiri wannan abun? Kar ka manta tun lokacin kawo Abra gidan nan na yiwa abun mummunar fahimta har muka samu saɓani ban ƙara tayar da hankalina ba, na cigaba da rainon ta cikin kulawa da zuciya ɗaya, to me zai saka yanzu kuma in yi haka?" "Duk da haka, amma ko da hakan ne, daga kiran ki an faɗa miki wannan maganar sai ki zo ki dinga jifa na da waɗannan miyagun kalaman? Why Na'ima? Idan rai ya ɓaci sai kuma hankali ya gushe?" Shiru ta yi ba ta ce komai ba, cigaba da magana ya yi idanunsa a cikin nata. "Baki yarda da kanki ba, ba kuma ki yarda da ikon Allah ba, da kin yarda da baza ki dinga wannan abubuwan kamar wata illiteracy ba, ki saka a ranki Ubangiji ne ke yin komai, kuma shi ya nufa sai Abra ta yi rayuwa a gidanmu. Sannan kuma k'arya fure take ba ta ƴaƴa, ki saka a ranta komai daren dad'ewa gaskiya za ta bayyana, idan ma ƙarya nake miki Ubangiji ba zai barni ba, dole watarana sai ya toni asirina." Na'ima ta kwantar da kanta ta dinga nuna masa ta yi nadama, sharrin shaiɗan ne da kuma tsananin kishin sa da take yi, amma Insha Allahu haka baza ta kuma faruwa. Ganin yanda take kuka da kalar tausayin da ta yi yasa Khamal ya janyo ta jikinsa ya ce. "Shikenan Wifey komai ya wuce, amma kar ki ƙara mun irin haka, ban ji daɗi ba, raina ya ɓaci sosai, yanzu fa ba da ba ne, mun girma mun zama iyaye, ya kamata irin wannan abubuwan duk mu daina su." "Insha Allahu bazan kuma ba." Ta yi maganar cikin sanyi tana ƙare shigewa jikinsa kamar ba Uwar ɗan saurayi Salman ba. Bayanta ya shafa ya ce. "Allah yasa, bana son muna samun saɓani, musamman akan Abra, dan watarana yaran nan za su iya ji su gane halin da ake ciki. Ke Mace ce mai daraja a idona, ko dan yanda kika riƙe mun Abra da amana ba zan so wani abu na ba dai-dai ya shiga tsakaninmu ba." Ƙwafa ta yi a cikin ranta tsanar Abra na ƙara cika mata zuciya, wato saboda ita ne ma yake ragwanta mata? Lallai dole ta san abun yi, dan gaba zai iya cewa ma saboda Abran yake zaune da ita. A fili kuwa murmurshin yaƙe ta yi ta ce. "Na gode Mijina, Abra kuma she is my Daughter, ka daina danganta ni da mariƙiya a gare ta, ni mahaifiya ce a gurinta, dan kallo ɗaya nake yi musu ita da Salman, matsayinsu ɗaya a cikin raina." Murmurshi ya yi yana jin ɓacin ransa fiye da rabi ya tafi. Washegari Bayan an idar da Sallar Asuba Abra ta yi lazimi da karatun Alƙur'ani kamar yadda, ta saba kullum ta nufi kitchen dan haɗa breakfast. Sai da ta fara tsaftace kitchen ɗin duk da ba ya tare da wani datti sannan ta fara aikin. Around 6:40 Salman ya shigo kitchen ɗin fuskarsa na nuna alamun tashin sa kenan daga bacci. "Sleeping sickness, an tashi kenan?" Abra ta faɗa tana kallon sa. Yamutsa fuska ya yi ya ce. "Baccin ma ko isa ta bai yi ba, na tashi ne kawai saboda school." "Ba dole ba, tunda jiya ka raba dare kana ta aikin kallon Ball." "Baza ki gane daɗin kallon Ball ba ne Yaya, na ce ki zauna muna yi tare amma ƙin ki." "Wannan sai ku, ni ina zan iya." Irish ɗin da take soyawa ya ɗauki yanka ɗaya ya ci ya ce. "Sannu da aiki, ke kullum ba kya gajiya da yi mana daɗaɗan abinci masu motsa kunnen mutum, kuma gashi ke ba ci kike yi sosai ba." Murmurshi ta yi ta ce. "Yanda kake da cin nan Salman idan ban zage na yi girki ba a gidan nan ai sai a samu matsala." Murmurshin ya yi shi ma ya ce. "To Allah ya biya ki, bari na taya ki mu samu ladan tare." Da sauri ta ce. "A'a ban ce ba, ka je ka shirya school kar mu yi late, nima na kusa gamawa." Ƙi ya yi ya ce shi dai sai ya taya ta, ita kuma ba ƙi take ba, tsoron kar Mami ta zo ta gan shi ne, duk da Abbi yana nan baza ta ce komai ba a yanzu, amma yana tafiya duk sai ta fanshe mata masifarta. Tare suka kammala aikin suka kai komai dinning, suna aikin suna hira cikin nishaɗi da ƙaunar junansu. Bayan sun gama kowa ya nufi ɗakinsa dan yin wanka tare da shiryawa. Salman ya riga ta fitowa, dan dama ita yanda take da sanyi haka take yin komai a sanyaye. 5 minutes da zaman shi ita ma ta fito sanye cikin uniform ɗinta mai kyau riga da skirt gami da ɗan ƙaramin hijab iya ƙirji. Salman ya bi ta da kallo. Tana duban sa ta ce. "What are you waiting for? ka zauna kana kallo na baza ka zuba abinci ka ci ba." "Ke nake jira mana Yayata, kin san ai ba zan iya cin abinci ni kaɗai ba kya nan ba." Ya yi ƙarashe zancen tare da jan kujerar kusa da ita ya zauna. Dai-dai nan su Khamal suka yi sallama a parlour'n, Hajiya Na'ima ta ci kwalliya sai ƙamshi take zubawa, kamar babu wani abu na ɓacin rai dake damun ta, Salman ya bi ta da kallo yanayin da ya gan ta jiya ya faɗo masa a cikin rai. "Good Morning Abbi and Mami" Abra ta faɗa fuskarta ɗauke da murmurshi. "Morning Daughter, da fatan kin tashi lafiya?" "Lafiya ƙalau Abbina." Cikin murmushin munafurci Na'ima ta ce, "Uhm, ƴar gidan Abbi, wato shi kaɗai kika gani ko?" Sunkuyar da kai kawai Abra ta yi, mamakin halin mahaifiyarsu na yanda take nuna mata a gaban Abbi yana cika mata zuciya. Khamal ne ya bawa Na'ima amsa da faɗin. "Me kuma ya faru? Yau ma zaki ce ta nuna bambancin ne? Na ga dai a tare ta gaishe mu." "Amma ai sunanka ta fara kira kafin ni." Murmurshi ya yi ya ce. "Mr Jealousy, ga naki ɗan nan ai kema, yanda yake kallon ki na san ke zai fara gaisarwa. Salman ya murmusa sannan ya gaishe su a tare. Bayan sun zauna Abra ta yi serving ɗinsu, Khamal sai saka mata albarka yake yi tare da yaba mata. Hakan ba ƙaramin ƙona ran Na'ima yake yi ba, ji take kamar ta ɗauki ruwan tea ɗin dake tururi ta sheƙa mata a fuska, ƙarin abun takaicin Salman sai taya shi yabon Abra yake yi. Babu yadda ta iya ita ma haka ta dinga yaƙe tana taya su. Bayan sun gama suka ɗauko school bags ɗinsu suka yiwa iyayen nasu sallama suka fice. Kafin su ƙarasa parking space Salman ya ɓata fuska ya ce, "Uniform ɗin nan kamar ya matse ki sosai Yaya." "Ba bu abun da ya mun, me ka gani?" "Kawai ni dai haka nake gani, haushi ma nake ji kina yawo a school a haka." Cikin mamaki Abra ta ce, "Me yasa? Duk sauran students ɗin dake yawo a haka fa?" "Ni ke kaɗai na sani, gaskiya zan cewa Abbi duk ya sauya miki uniform ɗinki, ba na son ganin ki da waɗannan." Tace "Sannu Yaya." "Ai dama ni ne Yayan ko ba ki faɗa ba." Dai-dai nan suka ƙarasa parking space inda direban sojan da zai kai su yake jiran su, hakan yasa Abra ba ta kuma magana ba. Masha Allah, an samu sauyin gwamnati, bayan shafe dogon lokaci waccan jami'iyya ta na mulki, duk ta yi iyakar bakin ƙoƙarin ta, gurin kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro, amma abun ya ci tura, a wannan karon sabuwar gwamnatin ta zo da sabbin tsare tsare, ciki har da yiwa harkar tsaro garan bawul, aka kawo sauye sauye da dama. Sauyin gwamnati da aka samu ya sa da yawa daga cikin iyayen gidan General Ibrahim da suke harƙallar su tare ba su koma ba, sedai a hakan gwamnatin ta sake ɗibar kara da kiyashi a tafiyar, dan an kuma kitso da kwarkwata gurin zaɓen muƙarraban gwamnati, dan akwai sauran ire iren wanda su ka yiwa waccan gwamnati aiki, suka hanata cigaba suka hana ƙasa cigaba. Amma duk da haka a wannan karon, jami'an tsaro ma su cike da son ganin zaman lafiya ya wanzu a ƙasa, suna cike da farincikin sauye sauyen da aka samu a harkar tsaro, kuma suka sa ran cewar alamu sun nuna ƙarshen harkar ta'addanci a ƙasa yana kusantowa. Sabon shugaban ƙasar ta bakin me magana da yawunsa, ya fitar da sanarwar cewar babu yafiya ga duk wani wanda aka kama da laifin ta'addanci ko yi wa harkar tsaro zagon ƙasa. Sannan duk wanda aka kama da laifin mallakar makami ba bisa ƙa'ida ba musanman bindiga, to hukuncinsa ki sa ne, ba tare da wata Shari'a ba. Haka zalika duk wanda aka samu da fitar da sirrin rundunar tsaro, shi ma ze zama a cikin 'yan ta'adda kuma hukunci ɗaya za su karɓa da 'yan ta'addan. Se dai an kai ruwa rana akan wannan ƙuduri na gwamnati kan majalissa su amince, kasancewar shugaban ƙasa a tsaye yake, ya sanya shi tsayawa kai da fata akan dokokin, tare da ba da umarnin bincikar duk wani ɗan majalisa da ya soki wannan ƙudurin. Da yawa cikin marasa gaskiya ya ɗuri ruwa, dan wannan gwamnati da gaske ta ke, irinsu General Ibrahim kuwa, ciki ya ɗuri ruwa gashi akwai yiwuwar ai musu retire, kuma shugaban ƙasa ya kafa kwamiti na musamman, dan bincikar yadda akai da maƙudan kuɗaɗen da aka dinga sawa a harkar tsaro, gwamnatin baya. Yau ta kama Saturday, da rana bayan su Abra sun dawo daga Tahfiz suna zaune a parlour suna game ita da Salman, Na'ima tana kallon wani program a tv, Khamal kuma yana karanta News paper. A shagwaɓe ta ɗago fuskarta tana kallon Salman dake ƙunshe dariyarsa, dungurar masa da Game ɗin ta yi ta ce. "Ni dai ban yarda ba wayo kawai kake mun." Dariyar da yake ƙunshewa ya saki ya ce. "Akan me zan miki wayo, ki yarda kawai na fiki iyawa." Turo ɗan ƙaramin bakinta ta yi tare da kawar da kanta gefe. Murmurshi ya yi ya ce. "Shikenan mu sake yin wani, ke zaki ci insha Allahu." "Ba zan yi ba ɗin, girki ma zan tafi in ɗora." "Haba ƴar ƙanwata ki tsaya mu ƙara ɗaya Please, ƙara koya miki nake son yi yanda gobe zaki winning a kaina." Na'ima dake sauraren su ta harare shi ta ce, "Ka bar ta, ta je yi aikinta, kai tunda ba ka da abun yi sai zama a cikin gida tare da mace sai ka yi ta yi ai." A hankali ta yi maganar yanda Khamal ba zai ji ba, kasancewar ta fi shi kusa da su. Jiki a sanyaye Abra ta miƙe da niyyar zuwa kitchen. "Daughter ku shirya ku je ku gaishe da su Mama yanzu." Muryar Abbinta da ya faɗi haka yasa ta tsayawa cak ƙirjinta ya faru dukan uku_uku, domin ko kaɗan ba ta ƙaunar abun da zai kai ta gidansu Mahaifiyarsu ko gidan wani nata, saboda tsana ƙarara da suke nuna mata. Salman da shi ma ba son su je yake ba saboda kar a ɓata ran Yayarsa ya ce. "Abbi akwai Islamiyya fa, ƙarfe huɗu za mu koma." Khalmal ya ce, "Za ku iya zuwa ai ku gaishe su kafin time ɗin, tunda yanzu ko 1:30 ba ta yi ba, weekend ɗin nan shi kaɗai time ɗin da kuke da shi na ziyara, dama suna ta complain ba kwa zuwa sosai." Jiya Mama ta kira Na'ima a waya ta bawa Khamal dan su gaisa, shine bayan sun gaisa ɗin cikin kissa take ce masa su Abra ba sa zuwar musu sosai, shi yasa ya ce su je yau su gaishe ta. "Abbi to ai girki Yaya Abra za ta yi." "Salman! Gidan namu ne ba ka san ku je ko me? Dan girki idan kun tafi ba sai in yi ba?" Cewar Na'ima cikin haɗe rai. "Allah ya baki haƙuri Mami, ba haka nake nufi ba." Ya yi maganar tare da miƙewa tsaye. Numfashi Abra ta sauke ta ce. "Bari mu shirya sai mu je yanzu Abbi." "Yawwa ƴaƴan albarka, Allah ya albarkaci rayuwarku." "Amin." Suka amsa gaba-ɗaya. Salman yana duban Abra ya ce. "Ki yi sauri ki shirya kar ki tsayar da ni, dan na san hali." Murguɗa masa baki ta yi ba ta ce komai ba ta shige ɗaki. Kasancewar sun yi wanka kafin su tafi Tahfiz, kaya kawai ta sauya ta saka wata doguwar rigar abaya mai kyau da tsada purple colour, ta yi kyau sosai dan rigar ba ƙaramin haskakata ta yi ba. Ta fashe jikinta da turaruka masu sanyin ƙamshi sannan ta ɗauki handbag ɗinta ta fito parlour. Sallama ta yiwa iyayen nata ta fice bayan Abbi ya ba ta kuɗi ya ce su tsaya a hanya su siyawa su Fruits, tare da addu'ar Allah ya tsare. Na'ima ta bi ta da wani irin kallo tare da sakin wani munafukin murmushi. Suna tafe Salman na yaba kyawun da ta yi kamar yadda ya saba yi mata kullum idan ta yi kwalliya, murmushin yaƙe kawai take yi masa amma ta gaza cewa komai, saboda tsoro da fargabar abun da za ta tarar a gidansu Mama na cin mutuncin kamar yadda suka yi mata kodayaushe. Duk yadda ta kai ga ɓoye damurta sai da Salman ya gane halin da take ciki, tausayin ƴar'uwar tasa ne ya cika masa zuciya. Ya rasa laifin da ta yi da ya saka Mami da danginta ba sa ƙaunar ta. Mintuna goma sha biyar ne ya kai su Unguwarsu Mama, kasancewar ƙaramin gida ne a ƙofar gida Driver ya yi parking Motar. Salman dake gaba ne ya fara buɗe Motar ya fita, ya zagaya ya buɗewa Abra Motar wadda da zuciyarta ke bugawa da sauri da sauri, cikin matuƙar sanyin jiki ta fito, ledar fruits ɗin da suka siyo Salman ya ɗauka, ba tare da ɗayansu ya yi magana ba suka nufi cikin gidan. LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUN GODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *✷ DARE DA DUHU ✷* Brigh pens✍🏾 Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya *P 10.......* Elegant Online writer's Akwai complete littatafanmu a Arewabooks, da wanda kuka karanta da wanda baku karanta ba, kuyi following wannan Acct ɗin domin sabbin littafai kamar *MIJIN MALAMA* da *RUƊIN ƘURUCIYA* https://arewabooks.com/u/nimcyluv👇🏾 https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949. _Littafin DARE DA DUHU na kuɗi ne akan ₦300 kacal, zaku tura kuɗin ta wannan acct ɗin 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. Ko kuma ku tuntuɓi wannan Numbers ɗin 09047871750.. idan katin waya zaka tura ₦500 ne. Transfer ne ₦300. Kuyi Mgn whatsapp kai tsaye 07063065780/09047871750. Bright pens na gdy😊_ Marairaice fuska Abra tayi, lokacin da suka isa ƙofar da zata kaisu zuwa parlourn gidan kakarsu wacce ta haifi Na'ima. Salman ya kalli yayar ta sa kafin a hankali yace "Mene Yaya?" Muryar ta na rawa tace "Faris tsoro na keji" Salam ya buɗe ido sai kuma ya yi dry yana faɗin "Yaya ba gani ba, ki daina tsoro idan ina tare dake" Shiru tayi masa, gane cewa da gaske tsoran ta keji yasa Salman kama hannunta suka shiga cikin parlourn bakinsu ɗauke da Sallama. Muryar Salman ita ta danne siririyar muryar Abra, hakan yasa Mama dake zaune, ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya zaton iya shi kaɗai ne yazo. Cikin farin ciki ta ɗaga Idanunta tana faɗin. "Maraba, lale da Mai gidana" Salman ya yi Murmushi yace. "Ƴar Tsohuwa" "Wace Tsohuwar Salmanun Faris? Kabar ganina a haka auren naka sai nayi niy....," Maganar Mama ta tsaya lokacin da Idanunta ya sauka akan Abra, wacce take ɓoyewa bayan Salman sai ka rantse shine gaba da ita. Mama ta haɗe fuska, tare da ɗauke kanta gefe guda, sam bata ƙaunar ganin Abra da jikan nata Salman, tsoro da fargaba da tunanin wani abu, yana kawowa Zuciyarta farmaki. Anuty Suwaiba tunda suka shigo take bin Abra da wani irin kallo, musamman ganin yadda lokaci guda Abra ta zama cikakkiyar budurwa kamar ita ta yi kanta sbd tsananin kyau, zubi, diri, na tsarin da Ubangiji ya yi wa jikin na ta. Cikin sakin fuska, Salman ya ƙaraso cikin parlourn still holding her hands, Abra tayi saurin zame hannunta daga cikin na Salman, ta zauna ƙasan carpet muryarta na rawa tace. "In...Ina...Inna...," Gaba ɗaya ta nemi gaisuwar ta rasa a cikin bakinta, Sbd Mama data murje mata yatsun hannunta da ƙafa. Zafi da azaba yasa Abra sakin ajjiyar zcy, gomi na tsastsafo mata daga tsakiyar goshinta. A fusace Mama ta juya inda Abra take zaune tace. "Kinga riƙe gaisuwar ki, munafukar yarinya mai mugun nufi a zuciya, ire-iren wannan baƙin halin naki yake sawa wani yayi zaton cutarki muke, ban taɓa yin jika mai mugun hali irin naki ba, KURMA kawai!" "Wlh Mama mugun halin yarinyar nan yafi ƙarfin ta, na samu labarin ita take hana Salman zuwa gidan nan, Allah na tuba mene haɗin kashi da kiyashi ma? Shegiyar yarinya ke dai wlh Allah wadarai da halinki" Anuty Suwaiba ta ƙarashe zan can tana Miƙewa tsaye, ita ta yadda ta tsani mutuwarta haka ta tsani ganin buɗe idanunta ta ga Abra a cikin gidan Na'ima, musamman yanzu yadda duniya ta lalace ka gama kiwata yarinya ka waye gari Uban riƙon ya aureta. Abra tayi ƙasa da kanta, cikin damuwa Salman yace "haba Mama! haba Mama!! haba Mama!!!.. laluran nan fa Allah ne ya ɗorawa Yaya, babu wanda ya shige haka fa, kuma ni Anuty ki daina cewa yaya ta hanani zuwa gidan nan, ni yaro ne da za'a hanani abinda nai niyya? I don't want to go to your house since you don't like to see my sister" Anuty Suwaiba ta saki baki kafin tace "your fifteenth year in the world, ban fa manta time ɗin da akai maka kaciya ba, yanzu nan kai har jinka kake wani babba?" Wani irin baƙin ciki ya ziyarci zuciyar Salman, babu abinda ya tsaya masa a rai irin maganar kaciyar da Anuty Suwaiba ta yi, idanunsa har wani ruwu ruwa ya tara sbd zafin zuciya. Mama ta riƙe baki tace. "Salmanu! Akan wannan mowar kake faɗa mana Mgn? Kalli yadda ta gagara gaishe ni balle ta gaida Suwaiba? is this is what Na'ima train to you?" Mama tayi mganar tana bugawa Abra tsawa, wacce ta sanya tayi saurin fashewa da kuka muryarta na rawa tace. "Kiyi hqr Mama" Miƙewa Mama tayi, domin idan taci gaba da zama a nan, zata iya lakaɗawa Abra dokan mutuwa!. Salman yabi Grandma ɗin su da kallo, zuciyarsa nayi masa wani irin zafi baya ƙaunar duk abinda zai sanya yayarsa kuka, duk abinda ake wa Abra shine ya kejin zafin abin a zuciyarsa (Heartache) yana tsanin so da ƙaunar farin cikinta He is jealous of his sister, he sympathizes with her. "Ki daina kuka Yaya" Salman ya faɗi mganar a raunace, idanunsa ya kaɗa ya yi wani irin jaa na zafin zuciya, kallonsa kawai Abra take. "Salman mene mowa? Ni na haifi kaina ko Mami ce ta haifan? Wanne laifi na aikata mai girma haka Faris? My mother's relatives do not love me at all, ina tsoran kada su rabani da kai Salman zan jure komai banda rabuwa dakai" Kuka ta fashe da shi, jikinta na rawa da ɓari, gaba ɗaya tayi kan Salman sbd duhun da take gani a cikin idanunta. Salman ya yi mata masauki a ƙirjinsa, ya riƙeta Tsam-tsam yana shafa kanta tare da jijjigata a jikinsa yana faɗin. "Kin gani ko yaya? Kinga abinda zaki jawa kanki sbd damuwa? Idan kinga na rabu dake yaya Kice Ubangiji ne ya ɗauki raina" Muryarta na rawa tana riƙe Salman ta ce. "Salman ka maye gurbin Mami don Allah,Ina jin zuciyata na yi min zafi Salman" Kasa Mgn Salman ya yi, sun jima a haka kafin ta zame jikinta tana goge Hawayen idanunta zuwa Fuskarta. Shiru ya biyo baya babu wanda ya sake Mgn, Salman da ya tuna zan can kaciyar nan sai ransa ya ɓaci. A hankali ya zauna gefenta cikin ƙasa da murya yace. "Ina jin babu daɗi Angel.. bana son ganin Yayata cikin damuwa, please please ki daina Stop crying" Ya faɗa yana sanya hannunsa saman Fuskarta, slowly ya shiga goge mata hawayen da yaƙi tsaya mata, yana jin yadda take sauke ajjiyar zuciya, da Idanu kawai yake binta sai kuma ya girgiza kai. Gyara zamansa yyi very close to her yana ɗaukan remote ya ce "Yaya na tambayeki?" A hankali Abra tace "Uhm" Kansa ya shafa sbd Mganar da ta yi masa nauyi, Abra ta haɗe fuska tace "All ears, kasan ban son haka ko?" Juyawa ya yi suka haɗa idanu yana sakin Murmushi yace "I knw, Yayata nada tsari" idanunta akan T.v tace "Faɗi?" Salman idanunsa gaba ɗaya akan Abra wacce ita kuma hankalinta yake kan T.v yace. "The stomach ache you had a few days ago Yaya" Shiru ya yi mata, ta juya tace. "To ina jinka ai, mene ya faru?" Sumar kansa ya shafa, shifa tunda ya yi niyyar Mgn bai ga kuma abinda zai hanasa yin shiru ba, fisgewa ya yi yace. "The blood, i mean shine al'adar da ake Mgn mata su nayi?" Abra ta juyo da sauri tana buɗe daradaran Idanunta waje tace. "Jini? Injiwa? Yaushe kuma?" Duk ta daburce da tambayar da ƙanin nata ya yi mata. Murmushi ya yi ya ce "Why are you answering my questions with a question Yaya..?" Abra dai ta haɗe fuska tace "To ban gane ba ai" Salman ya yi Murmushi kawai yana girgiza kai sai kuma yace. "Our biology teacher told us" Attention ɗin Abra yana wajan Salman, amma idanunta na kan t.v, kamar ba zatai Mgn sai kuma tace. "Ya ce muku me?" Salman yace. "Adolescent period mana Yaya, and you know what Hadda wannan blood ɗin acikin alamun fa" shiru kawai Abra tayi tana Mmkin yadda Salman baya jin kunyarta, ko dan su biyu suka taso a cikin gidan nasu?. Bai damu da yin shirun nata ba yace. "Kinga yace, idan maza suka balaga fa, muryarsu na zama ƙatuwa, Chest hair, armpit hair, and pubic hair suna fitowa maza sosai, da kuma gemu, Man's bottom is getting bigger....," "Faris...!!!" Abra ta faɗa da ƙarfi tana rufe bakinta tare da zaro idanu waje, ita kanta Mgnar ƙanin nata Kunya yake bata. Salman ya tura baki gaba cikin ko a jikinsa yace. "Kefa Yaya matsala ce dake wani lokacin, ba gwara na faɗa maki ba tunda ke baki sani ba, ko kinfi so Kullum Dr sai yaga Sirrin ki?" Tai masa banza yace. "Nida dole na faɗa maki, I don't want anyone to hear your secret" Kallonsa kawai Abra take tana ji yace. "A woman's maturity is different from a man's, mace tana balaga za kiga tana ƙara kyau, muryarta daɗi Kullum kamar Algaita, ita mace bata da gashin ƙirji, sai armpit and public hair, sai Development of breast zai ta girma saɓanin shekarun baya, zasu fara Developing feelings towards opposite sex, komai na mace mai kyau ne, kyansu, Murya, diri, zasu iya attacking opposite sex ɗin su..." Shiru ya yi yana kallon yayar ta sa sai kuma ya yi ƙasa da murya yace. "Sai Menstruation or period, Duk wata wata mace keyi kuma shima yana cikin alamomin girma na mace, kuma shine abu mafi hatsari fa Yaya, Ance a wannan gaɓar mace na iya samun ciki da wuri, Shi Haila is normal vaginal bleeding that occurs as part of a woman's monthly cycle. Every month, your body prepares for pregnancy. If no pregnancy occurs, the uterus, or womb, sheds its lining. The menstrual blood is partly blood and partly tissue from inside the uterus, Shi ya sa time ɗin da naga Dr na dubaki naji babu daɗi Yaya, kuma naga Mami bata faɗa maki shi ya sa ni kuma na ƙara research akan haka" Shiru kawai Abra tayi, kafin tayi Mgn yace. "Islamiyya tashi mu tafi, tunda babu wanda ya kulamu" tana ƙoƙarin tashi wani ƙanin Na'ima mai suna Faisal ya shigo idanunsa akan Abra kafin ya zauna saman Kujera yana kallon Salman. Salman yace "Ina yi ni Uncle?" Faisal yace "Lfy, ke jeki dafa min indomie yanzu" Da sauri Salman yace. "Uncle Islamiyya zamu koma gida mu tafi" Faisal haɗe fuska sosai yace. "You will go, until she finishes cooking indomie" A sanyaye Abra ta miƙe ta nufi kitchen, ƙilan ita bata da ranar hutawa a duniya, ɗan uwanta Shine farin cikinta, sai kuma Abbinta. Miƙewa Salman ya yi zai bi bayanta, cikin sauri Faisal yace. "Jeka mota akwai kaya na kwaso min" ya faɗa yana bashi key ɗin motar, amsa Salman ya yi tare da yin waje yana surutai. Faisal na ganin Salman ya yi waje, ya miƙe da sauri yana sakin Murmushi kai tsaye kitchen ɗin ya nufa, Abra na tsaye tana yanka albasa, gaba ɗaya a firgice take, taji motsi a bayanta sai dai bata ɗauka na mutum bane. Cikin sanɗa Faisal ya Ƙarasa inda take tsaye, wani irin kallo ya bita dashi, idan ba zai manta yanzu shekarar ta 18 Salman kuma 15, gaba ɗaya suna matakin secondary schl Ss 1, Salman Science class, Abra art class, amma girma da tunanin Salman haɗi da wayonsa yafi ƙarfi na ɗan Shekara 20 zuwa sama, domin babu abinda Abra zata nuna masa dan gane da wayo, dalilin hakan yasa ya korasa zuwa waje. A hankali Faisal ya matsa dab da bayanta har yana sauke mata numfashi, Saukar numfashi da taji yasa jikinta fara rawa wuƙar hannunta ta yanke ta, amma saɓar tsoro bata yankan take ba, Tana ƙoƙarin kurma ihu yyi saurin rufe mata baki da hannunsa. Ganin yanayin Faisal ba ƙaramin gigita Abra Khamal Khamis ya yi ba, cikin wani yanayi Faisal yace "Shhhhhh" Ya faɗa yana bin jikin Abra da kallo, har lokacin hannunsa yana bakinta ya hanata yin ihun cikin rawar Murya yace. "I want to talk to you,If you yell at me, I will surprise you". Kai kawai ta ɗaga masa burinta ya saketa, sai a lokacin kuma maganar Salman ya faɗo mata na ɗaukan ciki. He's still holding onto her ya ce. "Ina son muyi wani deal dake" shiru kawai tayi kanta a ƙasa zuciyar ta na harbawa, Faisal ya zame hannunsa daga bakinta yace. "Zan baki kuɗi, ki bani wani abu" da sauri Abra ya kallesa ya ɗaga mata kai yace. "Zan iya forcing naki akan abinda nake so, amma zan baki dama, ki saka a ranki duk abinda nayi Maki babu uban wanda ya isa ya yi taking action akai balle ki Tsammaci za'a kulleni, I want to sleep with you, I really want you, Ina son yin wasanni dake i mean _“Romance”_ baki da gata baki da ƴan ci, ki tsaya na moreki na tara maki dukiya Abra!" Jikinta ne ya fara rawa tama kasa cewa komai, Faisal ya ɗaga mata kai yace. "Yes Abra, just like that" Ya faɗa yana shafa ƙirjinta wanda ya Sanya Abra saurin runste idanunta, muryarta na rawa tace. "Uncle kai ƙanin mahaifiyata ne, babu kyau abinda kake haramun ne, bana son dukiya ka cika ni" Faisal ya yi Murmushi yana ƙara shafar ƙirjinta dake mugun burgesa yace. "And so what? Gaba ɗaya duniyar nawa take Abra, kawai muji daɗin mu, zan riritaki" Abra could not understand what Faisal was saying to her. gani take babu yadda za'ai ƙanin Maminta yace haka, daman ance yana shaye-shaye Maybe shiyasa yake abu kamar Mahaukaci. Dagewa tayi ta kurma ihu! Iya ƙarfinta tare da faɗin. "Salman!!!!!" Jin hakan yasa Faisal saurin sakinta yana zame hannunsa daga jikinta, da sauri kuma ya juya ya fita, yana fita Salam daya shigo yanzu jikinsa na rawa ya dubi Uncle ɗin nasa, Da sauri kuma ya yi kitchen ɗin yana faɗin. "Yaya.. Yaya... Angel" Cak ya tsaya yana kallon yadda jikinta ke rawa, ga bleeding ɗin da take a hannunta, muryarsa na rawa yace. "Angel" Da sauri ta ɗago kanta ganin Salman yasa ta nufi inda yake, gani take har lokacin Uncle Faisal na nan, tana zuwa ta faɗa jikinsa tana ƙanƙame sa, Her whole body is shaking, she was very scared. Shiru Salman ya yi, domin yasan halin Yayar tasa, a duk lokacin data tsorata wajansa kawai take zuwa ta ɓoye, idan tsoro ya yi mata yawa numfashinta har ɗaukewa yake. "Shhhhh, I'm here Yaya" Ya faɗa a sanyaye yana ɗan bubbuga bayanta alamar rarrashi, sun jima a haka kafin ta fara sauke ajjiyar zuciya har lokacin yana rungome da ita. Tunani fal cikin ransa, ita da wa? what is she afraid of? Sai ya tattara komai ya alaƙan tashi da Uncle Faisal. Ɗago kanta tayi, suka haɗa Idanu da Salman daya kafeta da Idanu, wanda cikin few minutes suka sauya launi tace. "Faris muje gida" Ta faɗa tana zame jikinta, ganin yaƙi ce mata komai tace. "Salman" Idanu ya buɗe sai kuma yace. "Ke da wa Yaya? Uncle Faisal right?" Ta girgiza kai tace. "you misunderstood, I'm just saw a cat in the kitchen, naji tsoro" Tana faɗin hakan tayi waje da idanu ya bita a fili yace "Liar" Lokacin da Salman ya fito parlour Abra har tayi waje, Uncle Faisal da Mama ya samu zaune, Mama tace "Mai gidana ba kaci abinci ba" A fili yace "No thanks" sai kuma ya juya ya kalli Uncle Faisal ya yi ƙwafa kana ya yi waje. A entrance na gidan ya samu Abra yana zuwa driver ya buɗe musu suka shiga kana suka nufi, Railway quarters. Washegari ya kama Monday, cikin sauri Salman ya fito sanye da Uniform yana faɗin. "Yaya we getting late, kiyi sauri ni ba zan breakfast ba" daidai nan Abbi ya fito yana gyara zaman I watch ɗin sa, Salman ya yi murmushi yace. "Mrng Abbi" "Mrng, how are you My son" Salman yace "I'm good Abbi" Abbi ya duba time yace "Laa! Zaku makara where is she?" Salam yace "she's in her room" Gaba ɗaya suka nufi bedroom ɗin Abra, a tsaye suka sameta tana ƙoƙarin saka baby hijab ɗin jikinta, Abbi ya yi Murmushi tare da ƙara sawa wajanta, ya amshi hijab ɗin ya saka mata yana faɗin. "My dear san yin jikinki ya yi yawa" Salman yace "Wlh Abbi, kamar mai shawara, And Yaya bata son cin abinci" Kama hannunta Abbi ya yi yace "Mene yasa kuka makara yau" kafin Abra tayi Mgn Salman yace. "Abbi ita tayi breakfast, tayi shara, wanke kwanuka, tayi mopping" Abbi ya ware Idanu waje ya ce. "Why My dear? As from today kada ki sake yin komai Tun da akwai shcl, amma weekend kina free sai islamiyya, zanwa Maminku magana a samo Maid ko?" Waje sukai yana musu hira, da kansa ya kai su makarantar, time ɗin ana Assemble. Bayan an gama Assemble aka kira Abra Khamal Khamis ta yi addu'a, daman ta saba kanta a ƙasa take karatu kafin ta ɗura da addu'a, tana gamawa kowa ya nufi class ɗin su. 5 Subjects sukai attending kafin a fita break, tana zaune tare da wasu class mate ɗin su, wata Khairy tace. "Abra Khamal Khamis, U looking so worried what's up?" Murmushi tayi tace "Noting Khairy, kawai tunanin exam nake, kinga yanzu duk revision ake" Khairy tace "you're right, Keep trying, I know you will pass the final exam" Wata Jannat tace. "Ai ko ba kiyi karatu ba, dole kici exam Abra, Duk team kece 1st position fa" Khairy tace "Wlh idan nice Abra ba wani karatu da zan" Murmushi kawai Abra tayi har beauty point ɗin ta suka loma tace. "Malam yace a cikin sira, wata rana a kogon hira, an saukarwa da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama wahayi, cikin suratul Alaq, Sura ta 96 a cikin Alkur'ani, wacce take da ayoyi 19, surar data sauka a Makkiyya, kalma ta farko cikin Alkur'ani ita ce “IƘƘIRA” aka cewa Manzon Allah s.a.w kayi karatu, wannan kalma ita ce ta farko cikin Alkur'ani kafin cikakken bayani yazo a Suratul Alaq, kinga ke nan karatu wajibi ne, ya zama dole tunda har aka fara yiwa Manzon Allah Sallallahu alaihi wahayi dashi, Yace shi ba mai karatu bane, amma Mala'ika Jibril ya matse sa yace IƘKIRA.. yace Laa ana bi ɗalik, kinga karatu ana nufin samunsa da wahala Khairy komai akwai wahala idan ka dage ya zama sauƙi a gareka.. do what is right not what is easy" Khairy da Jannat Kallonta sukai, this is the first time that Abra spoke a lot in the class. Khairy ta buɗe baki tace. "Wow! So interesting, gsky Abra ki gode Allah, I have never seen someone as knowledgeable as you" Jannat ta taɓe baki tace "Amma karatun na yawa, data rage dai" Khairy tace "Ta ya ya karatu zai yawa Jannat Yusuf?" Jannat ta watsa hannunta tare da Miƙewa tsaye tace. "It's just a suggestion" "Oh, i see" cewar Khairy. Da ga nan Jannat office ɗin staff ɗin makarantar ta yi, domin ya ce ta zo yana son ganinta idan har tana son passed all her exams, a hanya ta tsaya ta fesa turare a jikinta. Abra Idanunta a ƙasa suna zaune Salman ya shigo hannunsa riƙe da takeaway da rubber ice cream, idanunsa akan Abra. "Salman, you are not seen unless you bring Abra something to break" Khairy tayi Mgnar tana dry, Murmushi kawai yyi yana girgiza kansa can kuma yace. "To ɗan matsa, aku Sarkin surutu" Khairy tace "Oh, haka zaka ce ko?" Bai ce komai ba ya zauna kusa da Abra dake Murmushi tana buɗe littafin English na gabanta yace. "Yaya ya zaki karatu ne?" Ta buɗe masa Idanunta tace "like how?" Ya kalleta ya kalli littafan gabanta yace "kamar dai haka" lumshe idanunta kawai tayi, yabi zara zara eyes lashes ɗin ta da kallo kafin yace. "Me za kici? Meat pie? Cake? Dunot? Shawarma? Pizza? Hamburger? Me za kici Yaya tell me" Kamar zatai kuka tace "Please Faris surutun yana yawa" shima ya marairaice mata yace "kefa kawai na kewa, yanzu me za kici" Tace "I'm full, ina karatu yanzu..." Kafin ta Ƙarasa maganar taji hannunsa cikin bakinta ya sanya mata cake a baki, da sauri ta amshi cake ɗin tana zaro idanunta waje, bayan ta ciye ta kallesa muryarta na harɗe wa tace. "Faris" "Angel" Salman ya faɗa yana kashe mata Idanunta ɗaya tace "but kasan ban fiya son zaƙi ba ko?" Yace "i knw Yaya, ni wlh karatun nan yana yawa, nifa ina mace ba ruwana da wani karatu tunda aure zan" Shiru tayi masa, a hankali yace "nifa ba zan fita ba Yaya, sai kin faɗa min abinda za kici" ta girgiza kai tace. "Bani da appetite, kuma ban san ɓata hannu" Kallonta ya yi sai kuma ya girgiza kansa, a hankali ya dinga bata cake ɗin tana ci, yana bata exotic tana sha har taci sosai. Kallonsa tayi sai kuma ta saki murmushi tace. "Thank you Ɗan ƙanina" "Uhm" yace kawai kafin ya miƙe har yaje waje sai kuma ya tsaya da ƙarfi yace. "Angel" da sauri ta ɗago kanta tace "What happening Salman?" Gira ya ɗaga mata tare da kashe mata idanu yayi waje da gudu. Ta girgiza kai tace "Allah ya shirya" A sati na gaba su Abra aka fara exam, Salman sam bai damu da karatu ba, ita kam ta dage tana fata ace wannan karan Mami ta sanya mata albarka idan ta ɗauki 1st position, Salman yana sane yaƙi mai da hankali sbd ya faɗi wanwar ta inda position ɗin Abra zai fi nasa. Yau ma a gajiye Abra suka dawo daga Islamiyya ko kayanta bata cire ba ta faɗa saman bed sai bacci. Har aka kira magrib tana bacci. Salman na zaune da Abbi wanda ya dawo gari a ranar cikin kulawa Abbi yace "Salman ina yayar taka?" Salman ya ajjiye handle ɗin game ɗin da yake yace "Tun da muka dawo islamiyya bata fito ba" Abbi ya yi shiru sai kuma yace "is she alright?" Salman yace "not sure Abbi" yace "ok jeka kirata, zamu je shopping daga nan Granny na son ganinku sai mita take fa" Salman ya miƙe daga shi sai farar vest wacce ta kama cikinsa wanda ya buɗe alamun zama saurayi, sai 3Qauter a jikinsa kai tsaye ya nufi bedroom ɗin Abra. Abra na tsaye gaban mirror ta fito daga wanka, tana ƙoƙarin saka lace rapped bra a jikinta taji Salman na faɗin. "Yaya.. Yaya..Yaya" Gaba ɗaya ruɗewa tayi gashi ƙofar a buɗe take bata saka mata key ba, Ruɗewar da tayi yasa bra ɗin kwacewa daga hannunta ta faɗi, daidai nan kuma Salman ya shigo yana faɗin "Angel..." Bai ƙarasa faɗa ba yaji ta fasa wata ƙara tace "No!! Salman get out I'm naked....... *We are still in free pages.... A koda yaushe zamu iya tsayawa... Ka hanzarta biyan kuɗin ka domin a dama dakai.. littafin daban yake.. kada ku manta marubuta uku ne suke rubuta muku wannan Labarin Nimcyluv🤘🏼 Ayushercool🍷Zee kumurya💘* [9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU* _Brigh pens✍️_ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya                                P11 Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗin a Arewabooks https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949 https://arewabooks.com/u/nimcyluv https://arewabooks.com/book?id= Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Cak ya tsaya kamar wanda aka dasa shi a gurin cikin rashin sanin abun yi, shi kansa ya rud'e balle kuma ita, cikin rawar murya ya ce. "I'm .so.. sorry Yaya." Juya masa baya ta yi da sauri tare da ƙanƙame jikinta guri guda, kamar za ta yi kuka ta ce. "Salman! I said get out please!" Bai ce komai ba ya juya ya fice daga ɗakin cikin wani irin yanayi na sanyin jiki. "Ya dai? Ko wani abu ne ya same ta?" Abbi dake duban sa bayan ya dawo ya zauna, ya faɗi haka. Daidaita nutsuwarsa ya yi ya ce. "Nothing Abbi, tana wanka ne." Gyaɗa kai Khamal ya yi ya cigaba da latsa wayarsa. Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi jin ƙarar buɗe ƙofa tare da fitar shi, kamar mai tsoron wani abu ta juyo a hankali, saurin ɗaukar brar ta yi ta saka ta ƙarasa shiryawa, cikin wani hadadden less wanda aka yi masa ɗinkin tea bubu. Ta yi kyau sosai duk da ba wata kwalliya ta yi ba, bayan ta feshe jikinta da tsadaddun turaren da Abbinta yake siyo mata, ta ɗauki medium vail ta yafa sannan ta fice, bayan ta ɗauki Small handbag ɗinta. Tunda ta fito Na'ima ta kafe ta da ido wanda hakan yasa ta jin kamar za ta faɗi, Salman ma jin ƙamshinta ya ɗago kansa a hankali yana kallon ta, a ransa yana yaba tsananin kyawun Yaya tasa. Ita kuwa Na'ima baƙin ciki ne ya cika mata zuciya, na kyawun da Abra take shi da kuma takaicin yanda Khamal yake siya mata suturu masu kyau da tsada, gami da duk wani abu na kwalliyar ƴa mace. Duk abun da ya gani indai na gayu ne sai ya siyo mata, idan ta yi magana ya ce, ai ita ƴa mace ƴar kwalliya ce, idan bai siya mata ba wa zai siya mata? Ita ma babu yanda ta iya haka take siya matan saboda gudun kar ya gane har yanzu ba ƙaunar Yarinyar take yi ba. "Kai Masha Allahu laƙuwwata illabillah, ƴata tafi kowa a kyau da iya ɗaukar kwalliya, gaskiya sai ɗan Sarki ko ɗan gwamna zan bawa, dan Ƴata mai tsada ce." Na'ima ta faɗi haka cikin murmushin da bai kai zuci ba. Sai a lokacin Khamal ya ɗago ya dubi Abra, cikin murmushi ya ce. "To Allah ya kawo mana na gari." Lumshe ido kawai Salman ya yi ya buɗe bai ce komai ba. "Sannu da hutawa Mami." "Yawwa Daughter, kun dawo daga islamiyya ina sama ina shiryawa, sai yanzu na sakko, ya makarantar?" "Alhamdulillah." Ta faɗa cikin siririyar muryarta. Mayar da duban ta, ta yi ga Abbinta ta yi masa sannu da gida, ya amsa cikin fara'a sannan ya miƙe ya ce su huce. Abra da ba ta inda za su je ba ta yiwa Mami sallama ta fara fita, ita wannan shiryawar da ta yi da niyyar ta tambayi Abbinta za ta gidansu wata friend ɗinta, dan su yi totorial akan last paper ɗinsu da za su yi ranar Monday ta literature. Amma kasancewar ba ta saba musu ba sai ta hak'ura ta fasa zuwan, tunda Abbi ya ce za su fita. "Kai kuma lafiya kake ta bin mutane da ido?" Cewar Na'ima tana duban Salman. "Lafiya Mami, bari mu wuce sai mun dawo." Ya yi maganar tare da miƙewa ya fice. Na'ima ta ce. "To Allah ya kiyaye, sai kun dawo ɗin." "Yaya! Angel." Salman ya faɗa bayan ya fito cikin ƙoƙarin cire moment ɗin ɗazu daga cikin zuciyarsa, na ganin ta nicked da ya yi. Abra dake tsaye ta ɓata fuska ba ta ce komai ba. Ya ƙaraso ya tsaya a gabanta ya ce, "Kin yi kyau sosai." Tana ware manyan idanunta a kansa ta ce. "Ko? Kai da ba ka gajiya da faɗar haka as always." Ya ce. "Ai hakan ne shi yasa, kullum fa ƙara kyau kike yi da wani irin fresh kamar sabuwar amarya." Ta ce. "Kai kuma fa? ai kai ma haka Handsome ɗin Mami." Murmurshi ya yi cikin jin daɗin yabon shi da ta yi. A haka khamal ya fito ya same su suna hira gwanin sha'awa. Wani haɗɗaɗen gurin sayar da snaks da ice_cream dake cikin Nasarawa Khamal ya kai su, ya yi musu order na abin da kowa yake so. A hankali Abra take shan Vanilla ice cream ɗin dake gabanta, duk da ba wannan ne first time da suka saba zuwa irin guraren nan ba, amma duk a takure take jin kanta. Sai gyaggyara mayafinta take ta kasa zama guri ɗaya. Salman dake gefenta yana lura da yanayin da take ciki ya ce. "Ko in baki a baki ne, na ga kamar ƙiwar sha kike yi?" A hankali ya yi maganar yanda Khamal ba zai ji ba. Tura masa baki kawai ta yi ba ta ce komai ba. Murmurshi ya yi ya cigaba da cin meatpie ɗinsa, lokaci ɗaya murmushin ya ɗauke daga fuskarsa sakamakon four eyes da suka yi da wani matashin Saurayi da yake pacing ɗinsu, wanda ya ƙurawa Abra ido kamar zai lashe ta. Wata Uwar harara ya galla masa ya ce. "Yaya tashi ki je Mota ki ƙarasa sha, kafin Abbi ya gama mu wuce." Ya ƙarashe zancen tare da ajiye meatpie ɗin hannunsa, dan ji ya yi gaba-d'aya ya fice masa daga rai. Da mamaki take duban shi amma ba ta ce komai ba, Khamal da ya ji abun da Salman ya faɗa, ya dube shi ya ce. "Me yasa zaka ce ta tashi?" "Abbi na ga sai kallon ta ake yi a gurin nan, kar ido ya yi mata yawa ta je ta ƙware." Ya yi maganar da iya gaskiya. Murmurshi Khamal ya yi, cikin ransa yana jinjina al'amarin Salman, yanda yake acting akan Abra sai ka ce shine sama da ita. "Ki tashi Please." Ya faɗa yana narkar da idanunsa a cikin nata. "Ka fiya takura Faris, mu jira Abbi ya gama mana, sai mu fita gaba-d'aya." Ɗan ƙaramin tsaki ya ja idanunsa akan Matashin nan da ya kasa ɗauke idonsa daga kan Abra, wani irin kallo yake wurga masa. Har suka bar gurin mutumin nan bai daina kallon Abra ba, Salman kuwa sai cika yake yana batsewa. Sai da Abbi ya yiwa Mami da su Ammi take away sannan suka tafi. Suna hanya aka yi Sallar Magriba, hakan yasa Abbi tsayawa a wani Masallaci suka yi Sallah shi da Salman sannan suka wuce. "Wai kai lafiyarka kuwa kake ta ɓata rai?" Abra ta tambayi Salman cikin kulawa, bayan sun fito daga cikin Mota lokacin da suka ƙarasa gidan Ammi." "Babu komai, Ni ma kawai a haka na ji ni." "Ka fiya rigima kai dai" "Na kai ki?" "Ka ma fi ni, Ni dai bana son ganin ka a haka, Please ka saki ranka ka ji ɗan ƙanina." Ta ƙarashe maganar cike da shagwab'a. "Sai kin ce mun Yaya gaskiya." Ya yi maganar yana wani shan kunu. Dariya ta yi ta ce. "Ba zan faɗa ba ɗin, Sarkin son girma." Ba ta jira amsar shi ba ta wuce cikin gidan. Murmurshi ya yi tare da shafa sumar kansa ya bi bayanta. Da sallama suka shiga main parlour'n gidan, Ammi tana tsaye a dinning area tana yayyankawa Baffa fruits, Hajiya kuwa na kame akan kujera tana jan carbi mai dubu, da alama ba ta jima da idar da Sallah ba dan sanye take cikin Hijabi, ta ƙara tsufa amma har yanzu bakin nan nata yana nan bai mutu ba. Cikin fara'a da murnar ganin su Ammi ta amsa musu tare da yi musu sannu da zuwa, Ƴaƴan Shureim guda biyu da suka zo Weekend suka taho da gudu suna faɗin. "Oyoyo Yaya da Ya Salman." Abra ta ajiye ledar hannunta ta rungume su a jikinta cikin murmurshi. Salman ya shafi kansu ya ce. "Oyoyo ƴaƴan gidan Ammi, kodayaushe aka zo gidan Ammi a gan ku." Granny dake bin su da kallo ta cikin White medicated glass ɗin dake idonta ta ce. "Su masu zumunci kenan ai, ku kuwa uwarku saboda baƙin hali ba ta barin ku zuwa, ita ba ta zo ba ku ba ta bar ku kun zo ba." Ta taɓe baki ta ce. "Ba ruwana ma dai, lazimi nake yi bazan ce uffan ba sai na gama tunda babu kyau ana yi ana surutu." Salman ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, ya ce. "Ai kin ɓata lazimin tunda kin riga kin yi maganar, sai dai ki sake daga farko." "Ka ci kanka, ni ba zan biye maka ba, sunan Allah nake ambata bana wani garɗi Khamalu ba ko na wata garɗiya Nai'ma ba, ato, a sarara mun a bar ni in yi abuna cikin nutsuwa." Abra ta ƙaraso cikin parlour'n hannunta riƙe da na Fadeela, Fadil kuma ya ɗauko ledar da ta ajiye, zama ta yi a kusa da Granny ta gaishe ta, ɗaga mata hannu ta yi tana ƙara fito da carbinta daga cikin hijabi tana ɗaɗɗaga shi, ita a dole a ga lazimi take yi ba za ta yi magana ba. Murmurshi Abra ta yi ta miƙe ta ƙarasa gurin Ammi ta gaishe ta, Ammi ta rungume ta tare da amsa masa mata. Daga nan ta wuce bedroom ɗin Ammi dan yin Sallah. Sai wajen goma da wani abu suka bar gidan, kamar kar su tafi saboda yanda ake tarairayar su, da yanda suke cin dariyar Granny, har Baffa ma ya sakko anata hirar da shi tare da Khamal wanda ya shigo daga baya, bayan sun gama gaisawa da mai gadi. Granny sai mitar rashin zuwan su gidan akai_akai take yi, idan Khamal ya ce makaranta ce ta sa ba sa zuwan sai ta ƙanne ido ta ce. "To ni ina ruwana ma da zuwansu da rashinsa, tunda ba wata tsiyar suke mini ba in sun zo? Sai dai ma su sace mun ɗan tsirena da kilishina, da ɗan Albarkana yake siyo mini ban sani ba." Da za su tafi ta ce kar su tafi su zauna su kwana, Khamal ya ce gobe Monday akwai school sai dai in an yi hutu za su zo su yi hutunsu a nan insha Allahu. Sai ta tsuke fuska ta ce, "Allah ya raka taki gona." Abra tana son su je gidansu Ammi sosai, saboda nishaɗi da farincikin da take tsintar kanta a ciki, gashi ai ta nan_nan da su ana nuna musu ƙauna da kulawa. Washegari da sassafe Khamal ya wuce Abuja gurin aiki. G.Y BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY. A hankali take tafiya cikin sanyin jiki, tana sanye cikin fararen uniform na Nurses. Ƙofar wani office ta tura a hankali ta shiga bakinta ɗauke da sallama. Wani baƙin likita dake zaune a mazauninsa shi kaɗai a cikin office ɗin, yana operating system ya amsa mata Sallamar ba tare da ya ɗago ba. Ƙaraso ta yi ta zauna a ɗaya daga cikin kujerun dake gaban table ɗin. "Barka da safiya Doctor." Sai a lokacin ya ɗago tare da yin murmurshi ya ce. "Kin tashi lafiya Jamila? Ya su Mama?" "Lafiya ƙalau, na zo ai Sister Basira ta ce mun ka zo kana nema na." Ya ce, "Eh, me yasa yau baki zo akan lokaci ba?" "Abun hawa ne ban samu da wuri ba." "Da kin kira ni ai, da na biyo na ɗauke ki." Yaƙe kawai ta yi ba ta ce komai ba, ɗan ƙura mata ido ya yi na sakanni, cikin kulawa ya ce. "Kamar wani abun yana damun ki Jamila." Numfashi ta sauke ta ce. "Babu komai Doctor." Ya ce. "Ban yarda ba, ga damuwa nan ƙarara a fuskarki." Cikin yanayin damuwa ta ce. "Akwai abun da yake damu na, amma bazan iya faɗar shi ba." "Saboda me? Please Jamila tell me, har kin saka hankalina ya fara tashi." "Ba fa wani abu ne, kawai dai ina tsoron yin maganar ne." "Oh My God! Tsoron me? Ni ne fa? You are free to tell me everything da yake ranki, ko baki yarda da ni ba ne?" Ɗan jim ta yi kamar mai nazari sannan ta ce. "Yardar da na yi da kai ne yasa zan faɗa maka abun da yake raina, wani abu ne ya daɗe yana damu na, amma na rasa da wa zan yi sharing ɗinsa, Doctor! Abun da yake faruwa a cikin asibitin nan ya yi yawa, zaluncin ya yi yawa, Matar nan da Doctor Bulama ya hana ka, ka duba ta jiya mai naƙudar nan da ta matuƙar galabaita akan ba su biya kuɗin gado ba ta rasu, bayan ƴan'uwanta kuma sun yi fafutuka sun kawo kuɗin, wallahi jiya da ita na kwana a cikin raina, lokacin da ta zube a cikin reception ɗin nan tana mu taimaka mata kawai nake tunawa, ga ɗa ya kawo kai zai fito amma ya hana mu, mu taimake ta." Ta ƙarashe maganar kamar za ta yi kuka. Doctor Lukman ya sauke numfashi ya ce. "In dai Doctor Bulama ne abun da ya fi haka ma zaki ga ya yi, ke baƙuwa ce a asibitin nan shi yasa abun da yake damun ki, amma mu mun riga mun saba da irin waɗannan abubuwan." "Gaskiya idan aka cigaba a haka ba zan iya zaman asibitin nan ba Doctor, dan watarana sai zuciyata ta buga, a ce mutum babu abun da ya sani yake bawa muhimmanci a rayuwarsa sai kuɗi? Kuɗi abun banza da zaka mutu ka bar su, a yanda aka san likitoci masu tausayi da jan patients ɗinsu a jiki gami da kwantar musu da hankali, amma shi ko kaɗan bai san hakan ba. Abun da yake bani mamaki kuma yanda har yanzu asibitin nasa yake ƙara haɓaka, mutane suke ta yabon sa suna ƙwararrun likitoci ne a ciki waɗanda suka san aikinsu." Murmurshi Doctor Lukman ya yi ya ce. "Ai komai da iyawa ake yi Jamila, ma'aikatan cikin asibitin nan kawai suka san halin da ake ciki, amma sauran mutane gani suke yi ana yin iyakar bakin ƙoƙari dan ganin an kula da mutum da yi masa abun da ya dace. Kuma kar ki manta, shi fa Doctor Bulama indai zaka cika masa ƴaƴan banki to zaka ga aiki yanda ya kamata, zai kula da kai tamkar ɗan cikinsa." "Kai amma abubuwan nasa sun yi yawa, ya kiyayi ƙarshen sa, dan ba zai masa kyau ba, matuƙar bai tuba ya daina abun da yake yi ba." "Ke dai kawai Allah yasa mu dace, amma ana abu a ƙasar nan, gashi shuwagabanninmu babu ruwansu, tunda ba su ko Ƴaƴansu ake yiwa ba, su in dai zaka ba su Haraji mai tsoka to duk ma abun da zaka yi ka je ka yi." "Akwai Allah." Jamila ta faɗa cikin rauni da damuwa. Sha biyu da ƴan mintuna na rasa su Abra suka dawo gida, yau sun yi final exam gaba-d'ayansu. Na'ima tana zaune a parlour ita da wata ƙawarta da ta kawo mata ziyara, suka yi sallama suka shigo, ta amsa musu tana bin Abra da wani wulaƙantaccen kallo, ƙasa ta yi da kanta gabanta na fad'uwa, ta san watan shan wahalarta ya kama tunda Abbi ba ya gari. Cikin girmamawa ta gaishe da baƙuwar tare da yiwa Nai'ma sannu da gida, sannan ta wuce ɗakinta. Salman kuwa zama ya yi ya gaishe da baƙuwar tare da faɗin. "Mami yau mun gama exam ɗinmu ta third semester Ss 1, ranar Saturday ɗin nan za mu yi speech in Allah ya kai mu. Na'ima ta ce. "Masha Allah, Allah ya nuna mana ya bayar da sa'a." Ya amsa da Amin sannan ya tashi ya nufi ɗakinsa. Ƙawar Mami mai suna Maryam ta dube ta cike da munafurci ta ce. "Na'ima kar dai ki ce mun har yanzu kina riƙe da wannan Shegiyar yarinyar?" "To ya zan yi, tunda mai gidan ya dage." "Taɓ kin ga zaki iya ne, amma da ni ce da tuni ta bar mun gida wallahi, yanda take da kyan nan ai sai ta raba ki da mijin naki ma." "Khamal ba zai taɓa son yarinyar nan ba na sani, dan a matsayin ƴa ya ɗauke ta, kuma ba ya son ta san ba shi ya haife ta ba, dan haka ki ma bar wannan zancen kar zuciyata ta buga, dan wallahi idan hakan ta kasance sai na kashe ta na kashe kaina na kashe khamal! Damuwata a yanzu yanda Khamal yake nuna mata ƙauna shi da ƴan'uwansa, dan a yanda suke nunuwa sun fi ƙaunar ta akan Salman, abun nan yana ci mini tuwo a ƙwarya ba kaɗan ba." "To ai ke kika zauna komai yake faruwa, ta ƙarƙashin ƙasa zaki bi ki yi yanda dole ta bar gidan, azabtar da ita zaki na yi bana wasa ba idan baya nan." "Hakan nake yi ai, dan kin ga bana komai a gidan nan ita take yi." "Dan girki da su wanke_wanke ai mai sauƙi ne, aiki zaki na ba ta wanda sai ta kwanta ciwo dan wahala, idan wuya ta ishe ta da kanta za ta gudu." Na'ima ta ɓata fuska ta ce, "To su girkin da nake ba ta ma cewa ya yi aikin ya yi mata yawa, a samo masu aiki suna yi, sai dabara na yi masa na ce ai ita ƴa mace dole sai an yi treating ɗinta a gidan iyayenta, kar ta je gidan Miji a ce ba ta iya komai ba, sannan fa ya hak'ura ya bari take yin aikin." Maryam ta ce. "Ai idan baya nan zaki na ba ta ayyukan wahalar." "Idan baya nan ai akwai mai yi masa c.i.d Salman, wannan yaron kamar cingum kullum yana naniƙe da ita, shaƙuwarsu da soyayyar junansu har tsoro take ba ni." "Ke fa Na'ima idan kika yi wani abun kamar ba wayayyiya ba, yanzu komai sai an koya miki, ai da dabara zaki yi. Bari in faɗa miki yanda zaki na yi." Shawarwari kala_kala na mugunta da azabtarwa Maryam ta bawa Na'ima akan ta dinga yiwa Abra, ai kuwa ta ji daɗin su sosai ta ce a yau ba gobe ba za ta fara. Fitowar ta kenan daga wanka ta zira riga mara nauyi da niyyar ta kwanta ta huta, saboda ciwon da kanta yake mata, dan jiya ba ta yi ishasshen bacci ba, ta tsaya karatun Nobels ɗin da za'a yi musu question a exam ɗinsu ta Yau. Mami ce ta banko ɗakin ta shigo ba tare da ta yi sallama. "Ubanki kike yi a ɗakin da ba za ki fito ki ɗora mana girki ba? Ba ki ga rana ta yi ba ne?" Na'ima ta faɗi haka cikin masifa tana wurga mata uwar harara. Ƙasa ta yi da kanta ta ce. "Ki yi hak'uri Mami, ban san baki girka ba." "Tunda ga baiwar Ubanki ko? In girka miki ki zo ki ci?" Ta ja ƙwafa sannan ta juya ta bar ɗakin. Ba ta ce komai ba, ta ɗauki hijab ɗinta ta zira ta bi bayan Na'ima, ta san da Abbi yana nan kafin su dawo daga school Mami ta yi girki, shi yasa yau ma ta ɗauka ta yi. "Salman! Salman!" Firgigit ya farka daga baccin da ya fara ɗaukar sa, Mami ya gani tsaye a kansa. "Ka tashi zan aike ka?" Idanunsa dake cike da bacci ya lumshe ya ce. "To Mami ina zuwa." "Kamarya kana zuwa? Hajiya Maryam ce fa za ta tafi, zaku bi ta gidanta kai da driver za ta ba ka saƙo ka kawo mini, saƙon kuma na gaggawa ne ina buƙatar shi yanzu." Duk da baccin dake cin shi haka ya tashi zaune ya amsa mata, bayan ta juya ta fita ya tashi ya shiga toilet dan wanke fuskarsa. Ƙarfe uku da mintuna Abra ta gama lunch, tana ƙoƙarin shiga ɗakinta ta kwanta ta ɗan yi bacci kafin lokacin islamiyya ya yi, amma Na'ima ta hana ta, umarni ta ba ta akan ta biyo ta ɗakinta, babu musu ta bi ta. Zannuwan gado farare tass wanda Na'ima ta wawwatsa musu manja da gayya ta nunawa Abra ta ce. "Kwashe waɗannan kayan ki je ki wanke su tass yanzun nan, akwai sabulu da omo a cikinsu." Abra ta kalli kayan ta kalli mahaifiyarta, ta ce. "Mami ba zan iya ba wallahi, sun mini nauy..." Ba ta ƙarasa Maganar ba Na'ima ta ɗauke ta da wani gigitaccen mari. "Dan kaza_kazanki in ce ki yi abu ki ce mun a'a? Wato kin fara riƙa ko? ina magana kina musa mun saboda kin raina Ni, kina ganin kin girma yanzu kanmu ɗaya." Abra dake dafe da kuncinta tana hawaye ta ce. "Ki yi haƙuri Mami, zan yi." "Kar ma ki yi, yanzu in saka ki tsallen kwado a gidan nan, ba ke mayya ba, kin nace sai kin zauna, wahala yanzu kika fara shan ta a gidan nan, kaɗan ma kika gani." Abra da ba fahimtar abun da take cewa ta yi ba saboda gigitar marin da ta sha, ta sunkuci bedsheets ɗin ta nufi bakin tap. Tana kuka sosai ta tara ruwa a cikin bucket ta fara wankin. Har kusan Magriba ba ta gama ba, sai gurza su take yi da sabulu amma manjan ya ƙi fita, ga shi zanin gadon ya ƙara nauyi saboda ruwan da ya sha, ta rasa ma ta yaya za ta jujjuya shi ta wanke ko'ina, gashi abu ba guda ɗaya ba har uku. Hannayenta kamar ba'a jikinta suke ba saboda ciwon da suke mata, bayanta ya ƙame saboda sunkuyo, haka ma wuyanta, ga yunwa dake addabar cikinta. Matsalar kuma ita ba iya wanki sosai ta yi ba tunda ba sa yi, daga socks sai undies ɗinta kawai take wankewa, suna da masu yi musu wanki a gidan. Bayan su Salman sun kai Hajiya Maryam gida ta dage sai ya shiga ciki ya karɓi saƙon, ba dan son ransa ba ya bi bayanta. Ta zaunar da shi a parlour ta ce bari ta shiga ɗaki ta ɗauko masa, ta yi kusan mintuna talatin sannan ta fito, Salman har ya gaji da jira. Ta zauna akan kujera ta ce. "Salman na duba ban ga saƙon da zan baka ba, amma bari na yi waya yanzu a kawo wani sai na baka ka, ka kai mata." Cikin ƙosawa Salman ya ce. "Bari kawai mu koma Aunty, wani lokacin na zo na karɓar mata, yanzu lokacin islamiyya ya kusa." Hajiya Maryam ta ce. "Ka ɗan jira dai, yanzu fa za'a kawo, Mamanka tana buƙatar saƙon yanzu_yanzu shi yasa." Bai ƙara cewa komai ba, amma kallo ɗaya zaka yi masa ka san bai so hakan ba, Hajiya Maryam ta tashi ta kawo masa drinks da snaks. Wasa_wasa har ƙarfe uku ba'a kawo saƙon ba, sai ƙarairayi Hajiya Maryam take yi masa, ta ce mai kawo saƙon ne Motarsa ta samu matsala, amma ya kusa ƙarasowa. Ganin la'asar ta kusa Salman ya ce zai tafi gida, sai Hajiya Maryam ta kira Na'ima ta sanar mata, Na'ima ta ce ta ba wa Salman wayar, yana karɓa ta balbale shi da faɗa, ta ce kuma ko dare zai kai ya jira ya karɓar matar saƙon. Sai shida na yamma saura aka kawo saƙon aka ba shi suka taho gida. Sai da Na'ima ta ji shigowar Motar su Salman gidan sannan ta fito bakin tap ɗin cikin sauri, tana zuwa ta hand'aka Abra gefe ta ce. "Makirar yarinya, tun ɗazu Uwar me kika zauna baki gama ba? Sai ki wuce mu tafi ciki." Ba ta ce komai ba, dan idan ta ce za ta yi magana kuka ne zai kufce mata. Mami ta tasa ta a gaba suka shiga ciki, saboda gudun kar Salman ya zo ya tarar da ita a gurin ya sanar da mahaifinsa. Kamar za ta faɗi haka take jin kanta, daƙyar take iya taka ƙafuwanta, haka ta daure ta ƙarasa ta shige ɗakinta ta faɗa kan gado tare da sakin wani marayan kuka, ko'ina a jikinta ciwo yake mata, amma ita ba wannan ne ya fi damun ta ba, tsanar da mahaifiyarta take nuna mata ya fi komai damun ta, a kodayaushe cikin tambayar kanta dalilin da yasa take mata hakan take. Bayan Salman ya shigo ya ba wa Nai'ma saƙon sai ya wuce kitchen ya ɗebi abinci ya ci, saboda yunwar da yake ji, dan ƙin cin komai ya yi a gidan Hajiya Maryam tsabar takaici. Yana Allah_Allah ya gama cin abincin ya je ya ga Yayarsa dan ba ƙaramin kewar ta ya yi ba yau, amma kafin ya gama aka kira Sallah, hakan ya sa yana gamawa ya wuce masallaci. Da ya dawo Na'ima ta tare shi a bakin ƙofa ta aike shi ya kai mata saƙo, bai dawo ba sai bayan isha'i, a lokacin kuma Abra ta gama cin kukanta bacci ɗauke ta, hakan ya sa ba su haɗu ba sai washegari. Misalin ƙarfe sha ɗaya na safe bayan ta gama ayyukan gida wanda duk tare suka yi da Salman, suna yi yana ba ta labarin yanda ya yi missing ɗinta jiya tare da yi mata mitar ta yi bacci ba ta jira ya dawo ba, haƙuri ta ba shi ta ce masa kanta ne yake mata ciwo a lokacin, shi ya saka ta sha magani ta yi bacci. Suna zaune a parlour suna hira da tsokanar juna kamar yadda suka saba cikin nishaɗi Na'ima ta shigo parlour'n. Fuskarta ɗauke da fara'a ta cewa Salaman. "Son yau na cika maka burinka na nacin son driving da kake yi, jiya na saka an yi maka bucking a wani guri da ake koyarwa, yau zaka fara zuwa, sai ka tashi ka shirya ka tafi, direbanku zai kai ka. Salman ya fasa ihu ya ce. "Wow, thank you Mamina, na ji daɗi sosai." "Sai ka tashi ka tafi, kar su yi ta jiran ka." Cikin murnar Salman ya miƙe ya ce, "Amma har da Yaya ko Mami?" "Sai dai Kakan Yaya ba Yaya ba, tana macen zan yi asarar kuɗina in biya mata ta koyi wata Mota, sai dai ta mutu ba ta iya ba." Ɓata fuska ya yi bai ce komai ba, sam ba ya jin daɗin abun da Mami take yiwa Yayarsa. Murmurshi Abra ta yi ta ce, "Congratulations Bro, Allah ya bayar da sa'a ya taimaka." Murmurshin ya mayar mata ya ce, "Ina ƙwarewa ke zan fara kaiwa unguwa Yayata." "To Allah ya nuna mana lokacin." Ya amsa da Amin sannan ya fice bayan ya yi musu sallama. A rayuwar Salman yana son ya ga yana driving, tun da ya so ya koya amma Mami ta hana ta ce Ya yi ƙanƙanta sai ya ƙara girma. Na'ima tana jin Motar su Salaman ta fita ta wurgawa Abra wani wulaƙantaccen kallo, cikin tsawa ta ce. "Tashi ki je ɗakina zaki ga labulaye a ƙasa ki ɗauka ki je ki wanke, saura yau ma ki zauna laƙai_laƙai irin na jiya, wallahi idan baki wanke su ba tass sai na lahira ya fi ki jin daɗi." Jikinta a matuƙar sanyaye ta miƙe ta je ta kwaso labulayen, hannunta har yau bai daina yi mata raɗaɗi ba na dirzar zanin gadon da ta dinga yi jiya, ga jikinta ba wani jin daɗinsa take yi ba. Jiya ta yi fashin islamiyya yau baza ta so ta kuma yi ba, hakan yasa cikin sauri ta jiƙa kayan a cikin ƙaton baho ta zauna ta fara wankin zuciyarta babu daɗi. Ko 5 minutes ba ta yi da zama ba ta ji alamun ana kallon ta, juyawa ta yi suka yi ido huɗu da wanda ba ta taɓa tunanin ganin shi a wannan lokacin ba, sai da ta juyo ɗin ne kuma ƙamshinsa ya cika mata hanci. LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU* _Brigh pens✍️_ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya                                P12 Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗinkin a Arewabooks https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949 https://arewabooks.com/u/nimcyluv https://arewabooks.com/book?id= Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Salman ta gani a tsaye yana bin ta da kallon mamaki, cikin hanzari ya ƙara so in da take durƙushe, yana faɗin "Yaya, me kike haka a durƙushe?" Yana ƙarasowa ya kalli tulin labulayen da ke gabanta tana murzasu da ƙyar. Salman yace "Yaya? Waye ya sa ki Wannan aikin haka?" A wannan karon kasa jurewa ta yi, ta fashe da kuka. Ɗagota Salman yai yana cewa "Am sorry, de na kukan gayamin waye ya saki Wannan aikin haka?". Ta share hawayenta tace "labulayen ɗakin Mami ne, da na guest room" "To waye yace ki wanke?" "Mami ce" Salman yace "What? Mami kuma, duk almajiran da ke gidan nan, a rasa wanda za'a saka wannan aikin se ke? Ba ta ganin ko ƙwarin kirki ba ki da shi, kalle ki fa, ajiye kayan nan muje ciki" yai maganar yana jan hannunta. Riƙe shi tai ta girgiza masa kai tace "No Faris, please ka zo ka tayani mu wanke, saboda ina son zuwa Islamiyya, kaga jiya ban je ba, kuma ana screening na saukar Alqur'ani". "What, jiyan ma ba ki je Islamiyya ba, why?" Abra tace "a'a mantawa nai, naje ai ya nake nufi" Salman yace "kin ga wuce muje". "Faris please, Mami ce fa ta sani, ni dai kawai ka tayani mu gama". Banza yai mata ya cigaba da jan ta zuwa cikin Falo, Mami na zaune tana kallo tana kaɗa ƙafa, ta tsikaro ɗauri gaban goshi, tana danna remote. Babu tsammani Hajiya Na'ima ta ɗaga kai, ta ga Salman riƙe da hannun Abra, sai da ta sha jinin jikinta amma ta maze tace "Ya na ga ka dawo?" Salman be amsa mata Maganar ba yace "Mami, wai ke kika saka Yaya wankin wannan manyan labulayen?" "Eh, ni ma sata ko ban isa bane?" "Mami kin isa mana, amma kina ganin yana yinta ba ta da ƙwarin kirki, ni Yakamata ki saka in ma wankewar ne, ga lokacin islamiyya yayi". "Sannu ubana ka gama? Nace ka gama?, Ba mace bace? Idan ban sata aiki ba sai yaushe gidan wani fa zata, tana da tabbacin in da zata zata samu masu wanke mata ne, shine ki ka kai masa ƙarata?, algunguma kin wuce kin ƙarasa wankin nan ko sai na zo na kakkarya ki a gurin nan, shegen ido Kamar Magen mayu" Jikin Abra a matuƙar sanyaye ta zare hannunta daga ma Salman tai waje. "Haba Mami, dan Allah meyasa kikewa Yaya Abra haka?, a duniya ban taɓa ganin uwar da takewa ɗanta haka ba, kinga ba ta da cikakkiyar lafiya, dan Allah Mami kar abunda kike mata ya kuma illata lafiyarta" A hasale tace "Ka rufen baki ko se na ta so kanka, uban me ma ya dawo da kai gidan nan, bayan ga in da na turaka?" Ransa haɗe yace "lokacin Islamiyya ne yayi" yana gama faɗin haka ya bar Falon, in da Abra take ya koma, ya tarar da ita a zaune akan labulayen, tana ta uban kuka, farar fatar fuskarta tai jawur. Be ce mata uffan ba, ya matsar da ita gefe, ya tattara labulayen wankesu tsaf, har ya kammala kuka take ba ta dena ba. Se da ya gama wankin sannan yace "tashi muje ki ci Abinci ki shirya mu tafi Islamiyya". Jiki ba ƙwari ta bi bayan Salman, se dai a wannan karon Mami ta bar Falon. Ɗakinta ta wuce, Salman kuma ya wuce ɗakinsa, dan ya yi shirin islamiyya, sai dai gaba ɗaya ransa babu daɗi, sai ƙoƙari yake ya gano dalilin da yasa Maminsu ba ta son Abra, Abunda take mata ya yi yawa, ya wuce ace kara ce ta ɗan fari, ƙiyayya ce kawai, to amma ya za'ai mutum ya haifi ɗa kuma ya dinga ƙin sa. Haka ya dinga tunani daban daban a ransa, har ya kammala shirin makarantar. Dining ya tafi dan cin Abincin rana, sedai Abra ta faɗo masa a ransa, ya san babu tabbacin ta ci Abincin, wata ƙila tana can tana laƙai laƙai koma kukan ta cigaba. Ya miƙe da plate ɗin Abinci a hannunsa, ya nufi ɗakinta da sallama a bakinsa ya shiga, ya tarar da ita a zaune a gefen gado, ta saka uniform ɗin Islamiyya, se dai ta takure tana ta uban kuka. Cikin damuwa Salman ya ajiye Plate ɗin Abincin akan dressing mirror, ya ƙarasa kusa da ita ya zauna, yace "Haba Abbis Fav, why? Dan Allah ki dena kukan nan haka ya isa". "Faris, Meyasa Mami ba ta sona ne?" Tai maganar kamar za ta shiɗe. Salman yace "tana sonki mana, kema ba kiga Abbi yafi sonki ba, nima tafi sona ne amma tana sonki kema" Abra ta girgiza kai tace "No, she hates me, kai meyasa Abbi ba ya maka abunda take min? I so much Love my Mum, i have no one like her, ina son Mamina Faris, but why is she treating me like this? Ni aikin da take sani baya damuna, ta isa ta sani ne, amma meyasa take kyarata, ba ta son inje in da take? I so much Love her, dan Allah in laifi nai mata ka tayani bata haƙuri, amma dan Allah ta din ga sona nima" Jikin Salman yai sanyi ƙalau, ji yai kamar ya taya Abran kuka, tabbas abunda Mami ke nuna mata ƙiyayya ce, amma shima ya rasa dalilin hakan. Cikin hikima Salmn ya fara Magana "Haba Yaya, ke fa jaruma ce, kamar yau kika fara jin faɗan Mami, ai idan da sabo ya ci ace mun saba da wannan faɗan nata, watarn ma fa ba mu mu kai laifin ba, amma seta huce a kanmu, Yanzu ma karki raba ɗayan biyu, wani ne ya ɓata mata rai, let's forget about it, muci Abincin nan and hope kin yi shirin screening ɗin nan, dan shi ne na ƙarshe, ko ai sauka da kai ko kuma ka faɗi, ko kuma ai be kamata ma in tambaye ki ba, ku da kuke 'yan gaban goshin sheik Nurain, ai dole kiyi sauka" yai maganar ƙoƙarin basar da waccan Maganar. Murmushi ta yi lokaci ɗaya fuskarta ɗauke da hawaye tace "Alhamdilillah, ai ni na kammala shiri, se addu'a Allah ya sa muyi nasara, dan Allah Faris kaima ka dage gobe in Allah ya kaimu ku za'ai wa screening ɗin". Yace "yanzu in ban ci ba ya zaki?" Yai maganar yana kallonta. Tace "zama ka ci, in baka ci ba haƙura zan da saukar nima" murmushi yai yana jin son yayar ta sa a ransa, tana matuƙar son sa da son ganin cigabansa, shiyasa shima baya son ganin hawayenta. Da haka ya lallaɓata suka ci Abinci tare, yana yi yana tsokanar ta, wai idan a gidan yawa take, se an dinga cinye Abinci ana barinta saboda ɗan abunda take ci kamar wasan yara. Suka kammala ci, ta saka hjjabinta suka fice Islamiyya tare. G.Y Bulama Hospital and Maternity. Bainu ba kya tsufa, shine kirarin da wasu ka yiwa MD na Asibitin, wato mamallakin Asibitin GY Bulama Hospital and Maternity, babu alamar shekaru a tare shi, kullum cikin gayu da tsafta yake, ga kyawunsa na nan farin bafulatani jawurr da shi, kamar ba ya jin hausa.   Daga abokan aikinsa zuwa ma'aikatansa mata, da yawa na nuna suna sonsa, sedai ba fuska ga shi ba wanda ba shi da labarin masifar Matarsa da yadda ta kasa ta tsare akan Mijin nata. Yana zaune a Office ɗin sa, yana aiki a Computer ɗin sa, Nurse Basira ce ta shigo, tace "Sannu da aiki Sir" Yace "Yawwa Sister, ya aikin" Tace "Alhamdilillah Sir sai dai...." Ya ɗago ya kalleta yace 'ina jinki meyafaru?" "Nace da ma, kaga muna da patient a ward a kwance, ga out patient ga wanda aka ajiye for observation, amma naje pharmacy given set ɗin da za'a saka musu ruwa be fi uku ya rage ba, an tafi kawowa me kawowar haryanzu be dawo ba, wasu sun fara ƙorafi, nace ko gurinka za'a samu? Ko a bawa security yaje Sarauta Pharmacy ya siyo a fara sa musu, tun da duk sun biya kuɗi". Yai ajiyar zuciya yace "Basira, do you forget this is an business organization, muna aiki ne dan neman kuɗi, Pharmacy sun je siyo abunda babu, and still you are asking for another money a siyo kan su kawo, wannan ai asara ce, wanda ze jira ya jira, wanda ba ze jira ba ya tafi, amma kuɗin mutum baze dawo ba. And must i teach you everything a Makaranta ba a koya muku use of available resources ba? Ki yi 'yan dabaru ki musu amfani da guda ukun, idan na wannan ya ƙare, sai ki wanke shi ki kuma yiwa wani amfani da shi". Seda Basira ta buɗe baki sannan tace "Amm Doctor, ai this can be a means of transmission disease, mutane with different health status ai musu using one giving set, is a risky". "Basira get out of my Office, if you can't do it, i will do it myself". Cikin girmamawa tace 'am sorry sir" daga haka ta bar Office ɗin ranta a ɓace. A Nursing station ta tarar da Jamila tana jiranta, Jamila na ganinta tace "yaya ku ka da shi? Ayi a sallami Mutanen can na Emergency, relatives ɗin su sun fara complain" Basira ta kwashe mata yadda su kai da doctor. Zare ido Jamila tai tace "ke kuma yanzu yi zaki?" Basira tace 'idan ban ba to ya zanyi?" "Caɓ, to gaskiya Wannan rashin gaskiyar ba dani ba, wannan ai zalunci ne, mutum ya biya maƙudan kuɗi dan neman lagiyarsa amma a ƙara masa ciwo, Tiirrr da wannan abu, idan mu kai haka ilimin da mu kai be amfane mu da komai ba" Basira tace "to ya zan yi, idan ban hakan ba ze iya korata" Jamila tace "Allah ya temaka, amma ba da hannuna ba kam, ba zan iya wannan gangancin ba". Cike da farinciki da annashuwa Abra da Salman suka taho gida, sakamakon nasarar da Abra tai, na tsallake screening ɗin sauka, suna tafe ya na zigata yana cewa "dama na san zaki iya, Yayata ba dai hazaƙa ba". Suna gida a falo suka tarar da Mami, gaba ɗaya har Abra ta manta da abunda Mamin tai mata, Salman ya kalli Mami yace "Mami, Yaya ta ci screening ɗin sauka, a yanzu haka babu me makinta" Wata uwar harara ta watsa masa tace "to sai me? Kai kuma fa, kana nan kana gayamin taci screening kai kuma fa?" Abra tace "Mami ai shi ma ya ci zagayen farko zuwa na biyu, gobe in Allah ya kaimu za'a gama yi musu suma, kuma nasan ze ci insha Allah" "Rufen baki da ke nake?" Tai mata Maganar cikin tsawa. "Kai kenan kana ɓare ɓare, ita tayi abun arziki a makaranta amma kullum kai ne koma baya" Salman yace "to Mami ai naga ni da Yaya ɗaya ne, nasararta tawa ce banga..... "Shut up! Sakarai ba zaka taɓa gane me nake nufi ba, namiji ne kai ita rayuwarta taƙaitacciya ce a gida zata ƙare tata rayuwar, kai ne namiji kai ne ɗan gwagwarmaya, amma kullum ana nuna maka kana shirme" Abra ba ta kuma tankawa ba, ta wuce ɗakinta rai ba daɗi. Ƙaton ɗakin taro ne wato event center, cike da manyan mutane, tun daga harabar gurin irin Manyan motocin da akai parking, za ka san taron ya haɗa da Manyan mutane. Wani sashi na ɗakin taron, ɗalibai ne 'yan makaranta sanye da uniform a jikinsu, kowannen su fuskarsa ɗauke da walwala.   A dukkan bangon ɗakin taron, ƙatuwar banner ce da tambarin makarantar, daga ƙasa an rubuta speech and prize given day. Kiɗa ne ya ke tashi, kaɗan kaɗan a cikin manyan speakun da ke ɗakin taron. Can aka sanar da fara gudanar da taro, in da ɗaliban makarantar za su gabatar, da abubuwa domin nishaɗantarwa da kuma nunawa iyayen su irin ilimin da suke samu a wannan makarantar. Kasancewar makarantar haɗaka ce ta musulmi da kiristoci, akace za'a gabatar da Addu'a, daga bakin ɗalibai, kan a fara taron. ABRA KHAMAL KHAMIS, aka fara kira domin buɗe taro da Addu'a. Cikin nutsuwa ta fito, ta nufi in da zata karɓi mic, gaba ɗaya ido ya koma kanta, saboda farar fatarta da ke ɗaukar ido. Haushi ne ya kama Salman, ganin yadda aka bi Yayar ta sa da ido, kamar wasu mayu, wasu ko ƙiftawa ba sa yi, komai na ta a nutse. Abbi kuwa se murmushi yake, yana kallon 'yar ta sa. Cikin zazzaƙar muryarta ta fara kwararo Addu'a, yayin da hall ɗin ake amsawa da Ameen. Mami kuwa kamar tai bindiga, dan haushi komai sai dai ace Abra, maimakon Salman. Bayan ta idar ta koma mazaunin ta, aka kira wani kirista shi ma yai Addu'a, aka saurari jawabin maraba daga bakin shugaban Makaranta, daga nan aka kira debate. Debate ɗin akan rashin tsaro da ake fama da shi, laifin waye? Gwamnati ko jami'an tsaro?. Abra na cikin masu kare Jami'an tsaro, yayin da Salman ke cikin masu kare gwamnati. Masha Allah, yaran sun yi bajinta, yadda suke zubar da turanci, da hujjoji. Ko da Abra ta fito domin yin nata, Subhanallah, sai da ta sanya idonta a cikin na Abbinta, tai murmushi sannan ta fara kwararo kirari ga jami'an tsaron, ta ƙame tare da sarawa, san nan ta fara sauke sanka-sankar hujjoji, wadda take jin su daga ƙarƙashin zuciyar ta, saboda yadda take jin Abbinta da yadda yake bawa ƙasarsa gudunmawa. Sai da Abbi yai ƙwalla, yana tafa mata yana jin ƙaunar yarinyar ta sa a cikin ransa. Ku san duk wani abu da aka gudanar a gurin, akwai Abra ko Salman a ciki, amma Abra ita ce akan gaba a Komai. A ƙarshen taro da aka fara raba kyaututtuka, Abra ce ke da rinjayen grade a kaf makarantar, sau ɗaya kacal aka taɓa samun wanda ya taɓa samun irin grade ɗin ta, Salman ne na uku, a ɓangaren tsafta sai da ta samu kyauta, haka ladabi da biyayya, sakamakon debate ɗinsu ma su ne na ɗaya. Abra tafi kowane ɗalibi samun kyaututtuka, duk da Salman ma ya samu sosai, amma ba kamar Abra ba. Shi kansa Abbi sai da Makarantar ta karrama shi, akan jajircewaesa akan yaransa, aka karrama Familyn su gaba ɗaya, aka gayyace shi dan ya tofa albarkacin bakinsa. Shima a nan ya dinga koɗa Abra, yana jinjina ƙoƙarinta da jajircewarta. Salman ko a jikinsa, murmushi ya dinga yi yana tafi, Ammi kuwa ji take da da madoki, sai ta zanewa Salman jikinsa dan sam ba ya kishin kansa. Daga ƙarshe aka dinga hotuna, ba yadda Hajiya Na'ima ta iya, haka ta dinga yaƙe ana hotuna, sannan suka nufi gida. Suna tafe a hanya Salman na sake wasa Abra, yana mata kirari tana murmushi, Haka Khamal ma, ya biyewa Salman suna koɗa Abra. "My favorite, yadda kika dinga wasa jami'an tsaro da gudunmawarsu ga ƙasa, da yadda kika dinga blowing English da points masu kyau, i almost cry". Abra tace "Abbina, yabon gwani ya zama dole, idan ba'a jinjina muku ba be kamata a zage ku ba, day and night, rain and sun you never off duty, Tun tasowarmu kuke tsaye akan ganin ƙasarmu ta samu zaman lafiya, Salute to our brave soldiers" ta ƙarasa Maganar tana sarawa Abbin nasu. Salman wata shewa yai yana tafawa Abra, yayin da Abbi yake ta murmushi yace "Allah ya rayamin ku da imani, haƙiƙa Ku ababen alfahari na ne, ina fatan ku zama wani abu a rayuwa, yadda al'umma da ƙasarku za suyi alfahari da ku, sannan insha Allah zamu shirya walima tayaku murna" Abra tai farat tace "Abbi, ka manta saukar mu saura sati biyu, kawai a bari semu haɗe kar kashe kuɗin yai maka yawa" Abbi yace "Masha Allah, Allah ya albarkaci rayuwar ku, ya raya mana ku da imani". Salman yace "Ameen Abbinmu, maganin kukan mu" Abbi ya kalli Hajiya Na'ima yace "Madam ba kice komai ba, ba ki ga irin bajintar da yaran naki su kai bane, gaskiya kin iya haihuwa da kika haifa min 'ya'ya masu ƙwazo". Murmushin dole Na'ima tai kamar be basir, kai da ganin fuskarta ka san be kai zuci ba murmushin tace "Aikam ina jin ku, Allah ya ƙara musu basira" Haka suka ƙarasa gida, su Salman na ta nishaɗinsu su da Babansu, Hajiya Na'ima kuwa tana tunanin me za taiwa Abra ta huce, saboda yadda take jin tsanar Abra na sake ninkuwa a zuciyarta, kullum Abra ce gaba akan komai, gashi daga Salman har Babansa gaba ɗaya sun maida hankali akan Abra, kamar ba su da sauran abun yi a doron ƙasa sai akan Abra. "Daddy" "Na'am Babyn Daddy ya akayi ne?" Cewar GY Bulama, da ke kallon 'tilon yar sa cike da tsananin ƙaunarta. "Daddy na kusa shakara goma sha takwas fa" Yace "wow, Masha Allah babyna ta girma, we most celebrate your birthday" Tai murmushi tace "that's my Dad, amma fa guri za'a kama ai shagali sosai" Yace "Insha Allah, shagali za mu yi na gaske". "Kai kam doctor kai ta biyewa wannan yarinyar ta na maka shirme, har Abincin na ka ze sanyi bak ci ba" Doctor yai murmushi yace "to idan ban biye mata ya kike so a Yi? She's the only daughter i have alive". Meenal ta kalli Babanta tace "Wai Daddy ni bani da 'yan uwa ne? Nifa ina son in ga nima ina da siblings, I like big family" Ya ɗan murmusa yace "Babyna kenan, Allah shi ke tsara komai, lokuta da dama ba ma samun abunda muke so, se Abunda Allah ya shirya mana, ke kaɗai Allah ya bamu, ina fatan Allah ya sa ke mu samu jikoki masu yawa daga gareki". Rufe idonta Meenal tai tace "Ohh Daddy, har ka bani kunya" Yai murmushi yace "Yau kuma ni ake jin kunya?" Tace "Ka san wani abu Daddy?" "A'a sai kin faɗa" Cikin gaɓunta tace "Wani brother ɗin ƙawata ne ya zo mata visiting, yace ya na so na wai ze kawon ziyara ma" Yace "Wow, Masha Allah, amma naji daɗi sosai, ɗan ina ne?" "Nima ban san a unguwar da yake ba, amma dai brother ɗin ƙawata ne" "Masha Allah, to Allah ya kawo shi lafiya". Girgiza kai Mummy tai tace "Allah ya kawo ranar da zaki hankali, da babanki kike hirar saurayi?". Doctor yace "to ya ranki, idan ba tai hira da Daddy ba da wa za tai?" Mummy tace "lallai 'yar gidan Daddy". Tsaye yake a gaban dressing mirror yana kallon kansa, lokaci guda kuma yana ɗaura agogo a hannunsa, sanye yake da dogon wandon jeans, da jar riga long slip, ya taje sumar kansa sai ƙyalli take, saboda yadda ta ji mai. Dogo ne sosai, with Caramel skin complexion, masha Allah balck beauty ne, sedai kallo ɗaya za ka yi masa ka gano yadda yake da matuƙar kwarjini. Ya gama sanya agogonsa, ya ɗau turare ya dinga fesawa, ya fesa wannan ya fesa wancan, sai da ya gama Sannan ya ɗau mukullin motarsa da wayoyinsa yai waje. Wata babbar mace zaune a kan ɗaya daga cikin manya manyan kujerun falon, idonta sanye da gilashi ta na duba littafin azkar. Ƙamshin da ya karaɗe ɗakin ne ya sa ta ɗago ta dube shi, ta ɗanyi tari tace "Kaii Adnan wannan turarukan na ka sun fiye ƙarfi, wannan ai sai Asmata ta tashi" Yai murmushi yace "Hajiya Mama kenan, ba za su tayar miki da komai ba" Ta ɗan gyara zama tace "wannan kwalliya haka, hala taɗi za'a je?" Ya ɗan tsuke fuska yace "taɗi kuma?" Tace "Eh mana, wato na faɗi maƙiyin naka, shine zaka haɗe rai, haba ɗan Maman, ga kyau, ga kuɗ, ga aiki Alhamdilillah komai kana da shi, sedai haryanzu ba ka cika kamili me kima ba a idon duniya, saboda ba ka da abokiyar Rayuwa, shekaru tafiya suke ba sa jira" Adnan yace "to Hajiya Mama, za'ai insha Allah, yanzu dai wani ɗan aiki za muje wani guri" Tace "haka dai, aiki aiki ba hutu, to Allah ya dafa" Yace "Ameen Maman Adnan" ta bi shi da kallo tana murmushi. Sannu a hankali yake tuƙin motar, yana tafe sautin waƙar Eminem am not afraid, na tashi daga Radio motar tasa. A ƙofar wani ƙaton gida yai parking, rage Radio yayi, ya ɗakko wayarsa ya kira wata lamba, sai dai aka ce me layin yana waya. Tsaki yai ya ajiye wayar, ya kashingiɗa da jikin motar, tare da lumshe idonsa. Can yaji an buɗe gaban motar an shigo, ya buɗe idanunsa ya kalli wanda ya shigo ɗin yace "Wai da wa kake waya ne? Na kira ka amma user busy" Murmushi wanda ya shigo ɗin yayi yace "Kai dai bari, wato wata new catch na yi, Babyn ta yi Wallahi da ita nake waya, da ƙyar na iya fitowa ma gurinka" Tsaki Adnan yai yace "Shirme kawai" "Wallahi ba shirme bane, ai Soyayya duniya ce, wanda yake yinta shi ze gane" Adnan yace "Please Usman, let's keep this aside, mu je muyi abun da ya kamace mu" Usman yace "to muje, amma ina gaya maka, Soyayya duniya ce Adnan, kai ba kaga yarinyar ba, ina ga next week insha Allah za ka rakani, muje in kai mata ziyara, da na jewa Ameera Visiting na ga babyn, ba ka ga yadda ta tafi da ni ba" "Amma ba ni Adnan ɗin ba ko?" Yai maganar ba tare da ya kalli in da Usman yake ba. Usman yace "Eh ba kai Adnan ɗin ba, aljaninka, ɗan rainin hankali kawai, sai ka rakani". Adnan be kuma cewa komai ba suka cigaba da tafiya. Taro yai taro, gidan Khamal ya cika da mutane, domin taya su Abra murnar saukar Alqur'ani me girma, da kuma haddar izufi Arba'in ga kowannensu, ga nasarorin da suka samu, a makarantar boko. Alhamdilillah, an ci an sha sun samu kyaututtuka daga Manyan mutane, abokan Abbinsu da kuma sauran 'yan uwa da abokan arziki. Har Bayan sallar isha'i gidan cike yake da mutane, se wajen tara zuwa goma na dare Sannan aka watse. Tuni Abra ta kwanta bacci, saboda yadda ta gaji tiƙis saboda zirga zirga, da kuma hayaniya. Mami kanta a gajiye take, tai wanka ta samu tana cin Abinci a ɗakinta, dan ba ta samu ta nutsu ta ci ba. Wayarta ce ta ɗau ruri, ta miƙa hannu ta ɗauka, ba tare da ta duba me kiran wayar ba. "Na kira ne domin jin lafiyar 'ya ta, da kuma miƙa saƙon taya murna na saukar Alqur'ani da tai" "Wace ke? Wai wacece haka ne?" Hajiya Na'ima tai maganar cikin ɗaga murya. "Meye na ɗaga murya kuma? Uwar Abra ce". "To in ke uwarta ce ki zo ki ɗauki 'yar ki mana". "Me ze sa in zo in ɗauketa? Alhalin tana zaune Lafiya a gidan ubanta, Khamal na cigaba da raina miki hankali, amma a zahirin gaskiya Abra 'yar da muka haifa ce ni da Khamal, da ma na gaya miki bariki na ya fi naki, tsayin wannan lokaci ina nan ina bibiyar ki, idan kuma kina musu ki buɗe what's app ɗin ki, na ajiye miki saƙo". Jiki na rawa Hajiya Na'ima ta katse kiran, ta buɗe what's app ɗinta, saƙo ne ya shigo, ta buɗe ta shiga dubawa, hotunan Abra ne da shiga kala kala, da kuma wasu hotunan Salima tare da Abra, lokacin tana ƙarama sosai, daga ƙasan hotunan aka rubuta thank you for adopting my Child. Zaro ido tai tace "What? Khamal ni zaka cuta?" Hannunta ya hau rawa ta saki wayar a ƙasa. Khamal ne ya shigo ɗakin yana faɗin "My dear, har kin kwanta ne? Gajiyar ce ta hana a zo in da nake yau" Ya ƙara so yana ƙoƙarin riƙo hannunta, saurin ja baya tai tace "kar ka kuskura ka taɓa ni, tsawon shekaru kana raina min hankali, da na yunƙura zan magana se ka dan kwafar da ni, ka cika ni da daɗin baki, yau ƙarya ta ƙare na gaji" Cike da rashin fahimta yace "to ai ni sam ban gane akan me kike magana ba" "Ai dama ba zaka gane ba, tun da ka daɗ kana munafunta ta, meye wannan?" Tai maganar tana miƙa masa wayarta. Ya karɓa ya kalli hotunan, sannan ya ɗan taɓa baki yace "naga hotuna, sedai ban san daga in da aka samo su ba, na gaji da yi miki bayani, wannan ba ze wuce makircin Salima ba, ni na gaji da yi miki bayani". Ya ƙarasa maganar yana ajiye wayar. "To Wallahi a wannan karon na gaji da wannan wasan kwaikwayon, ka ɗau 'yarta ka mayar mata, ba zan cigaba da riƙe 'yar Zina ba, se ta bar min gidana" Khamal yaji tamkar ta soka masa mashi a ƙirjinsa yace "kar ki sake kiran 'ya ta da 'yar Zina, alamu sun nuna min Abra ba ta jin daɗin zaman gidan nan, a gabana ki nuna kina sonta, amma Allah kaɗai ya san me kike mata idan ba na nan, Wallahi Na'ima na kama ki da wani abu na rashin gaskiya akan Abra, Aurena da ke ya ƙare" "Eh ya ƙare ɗin, se ka Auro Salima ku cigaba da rainon Abran, ko ka kai ka Auri Abran" Khamal ya ga idan ya tsaya, yana cigaba da sauran Na'ima, za suyi ba daɗi dan haka ya fice ya bar mata ɗakin a fusace. Salman ne ya shiga ɗakin Mami, ya tarar da ita tana ta bala'i. Cike da rashin fahimta yace "Mami, wai akan me kike maganganun nan? Kamar fa ji nai kina cewa Babar Abra" "Eh, Abra ba 'ya ta bace ba ni na haifeta ba? Shekarun baya babanku ya zo min da ita, ya raina min hankali akan cewa tsintar ta yai a daji, ashe haifarta yai shi da wata karuwa, amma ya dinga rainamin hankali, to Wallahi se ta bar gidan nan". Jikin Salman ya ɗau rawa yace "Maa....ma...mi, kin san ko me kike cewa? Abran ta wa ce karuwa ta haifa? Impossible Mami, Abra 'yar ki ce, mu biyu kika haifa". "Shut up, ni ban haifeta ba, kai ka ɗai na haifa!!! LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU* Brigh pens✍️ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya                 *P.....13* Elegant online writers Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗinkin a Arewabooks https://arewabooks.com/u/nimcyluv https://arewabooks.com/book?id= *Albishir ga Makarantar littafan Hausa, ga masu buƙatar bugaggen littafin TSINTACCIYA wato hard copy a satin nan zai fita kasuwa... Wato ya keson mallakar nasa Bugaggen na takarda ya yi magana a wannan number 08119237616* LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Kafin Salman ya gama tantance abunda Mami ke faɗa masa, ya ji saukar muryarta cikin tashin hankali tana faɗin. "You are my son, not Abra. Abra karuwa ce ta Haifawa Ubanka, ya zo ya ke ci mana amana, Salman, believe me ya fifita son da ya ke maka akan Abra, yarinyar da babu wanda yasan asalin wacce Shegiyar karuwar ce uwarta, Khamal ya raina min hankali Your father hurt us, deceived us" Ta ƙare maganar tana sakin kuka da ƙarfi, ita kanta bata san lokacin da maganganun suke fitowa da ga cikin bakinta ba, wani irin zafi Zuciyarta ke yi mata, wanda ya sanya ta kasa controlling kanta, har ta kai ta dayin Revealing secrets tonan asirin shekara da shekaru. Salman zama ya yi kamar wani gunki, ya kasa tantance abunda Mami ke faɗa masa, his thoughts stopped. Komai nasa ya tsaya, ya kasa yadda ko fahimtar abunda ta ke faɗa akan Abra, shi tsoran Mahaifiyar tasu ne ma ya fara kamashi, ta ya ya zaka haifi ɗa a cikin ka kace wai karuwa ce ta haifa? This is impossible. Juyawa ya yi a hankali zai fice da ga cikin ɗakin, Mami tayi saurin Miƙewa tsaye, jikinta na rawa ta fisgo Salman baya tare da sanyawa ƙofar key. Salman ya ɗaga idanun shi wanda su kayi jajur, a hankali kuma ya ce. "You are too tired Mami, za ki samu headache fa, ki kwanta ki huta" Girgiza masa kai ta yi ta ce  "listen to me Salman, at least listening to your mother Salman, Wlh Allah Abra ba ƴa ta bace, I have nothing to do with her, ban taɓa shayar da ita nono na ba, Everything that happens is your Father's plan, I'm just pretending, na gaji da yadda ya ke fifita ta akanmu da mu ke dolensa" Tuni jikin Salman ya fara rawa, tunaninsa ya rabu kashi-kashi kowanne da abunda yake faɗa masa, "Salman Mahaifiyarka ce, ba zata yi maka ƙarya ba" wata zuciyar ta gaya masa. "Salman kada ka yarda daman can Mami ba son Abra take ba, tana nuna masa rashin so irin na ɗan fari ne kawai" A raunane yace "Mami ke fa Uwa ce? Ta ya ya zaki dinga sheganta ƴar da ki ka haifa? Me Yaya tayi maki Maki? You don't love her, that's all, but stop harassing her ki dai na sheganta ta don Allah" Da Mamaki Mami tace. "Salman kana tunanin zan maka ƙarya? Mene yasa kai ban ce bani na haifeka ba? Mene yasa bance ban shayar da kai nono na ba? Mene yasa ban sheganta ka ba? Because you are my son, my blood, biological son. Kai na ɗauki cikin ka, naji zafin haihuwar ka, na raineka. kasan akan Abra nayi haihuwar da ban shirya ba? Na haifeka saboda bala'i a kitchen, Gaba ɗaya Abra ta ɗauke min wani jin daɗin rayuwa da farin ciki? Tun kana cikin cikina na fara samun matsala da mahaifinka, shiyasa na ke ta ƙoƙarin nesanta ka da ita, kai ɗan sunna ne ka daina haɗa kanka da ƴar karuwa.....," "Mami!!!!!!" Salman ya faɗa jikinsa ko'ina rawa yake, ya kasa ɗaukan maganganun ta wanda suke neman haukata masa ƙwaƙwalwa, saboda muninsu. Cikin rawar Murya ya ce. "Ba zan yarda ba, Yaya ƴar kice kamar yadda nake ɗan ki, that's all" Mami ta kalli Salman sosai ta ce "Kana nufin zan maka ƙarya Salman?" Shiru ya yi mata kansa a ƙasa amma idanunsa sunyi jaa sosai sai numfashi yake fitarwa, ji yake kamar mafarki ya ke. "Kana tunanin zan maka ƙarya, kaf dangina da na mahaifinka da wa ka ga ta na kama? Akwai me irin siffarta?" Salman dai ya yi shiru, kansa na ƙasa bawai bai yarda bane, gaba ɗaya bashi da nutsuwar fahimtar Maganar tata. A zafafe Hajiya Na'ima tace "Answer my questions Salman Khamal Khamis?"  Salman ya ɗaga kansa tare da kallon Mami a hankali ya ce. "Ban ƙaryata ki ba Mami, na kasa yadda ne kawai...," Ɗauke shi tayi da ƙyakƙyawan mari tace "Ni nayi kuskure tun farko, to kaje duk uban wanda zaka tambaya kaje ka tambaya Abra Shegiya ce, Abra TSINTACCIYA ce, Abra ƴar karuwa ce...!!" Tana faɗin haka ta koma saman gado ta zauna, Da sauri Salman ya nufi ƙofa zai fita. "Salman" Mami ta kira sunansa da ƙarfi, kiran da ya sanya ya yi saurin juyawa tare da kallon direction ɗin da take zaune, da hannu tai masa nuni da ya zo. Bai mata musu ba ya Ƙarasa wajanta kansa a ƙasa, hannunsa ta kama muryarta na rawa tace. "This is an secret between us, ba wai dan ba ni da gaskiya ba, saboda ina son in kasance da kai da kuma Mijina, idan ka faɗawa wani ko wata cewa ni na faɗa maka, Mahaifinka zai datse igiyar auren dake tsakaninmu, I don't like that Salman, I love my husband, i so much love your father shi ya sa nake ta zaune har yanzu, sannan ina fatan za ka nesanta kan ka da ga wannan yarinyar" Kallonta kawai Salman ke yi, bai taɓa ganin Mami na kuka ba sai yanzu, mene gaskiyar Al'amarin? Ta shi ya yi jiki a sanyaye sai da ya je bakin ƙofa Mami ta ce. "Ka saka a ranka, ba zan taɓa so da ƙaunar Abra ba, ina kishinta sosai kishin kuma akan ka ne, duk wani plan da muka shirya da Khamal akanka ta wargatsa, She take away my happiness, she destroyed my house, to the extent ta fini kima a idon mahaifinka" Tana faɗin haka ta saki kuka sosai, gaba ɗaya matar data kirata a waya ta gama wargatsa mata lissafi. Da sauri Salman ya bar cikin ɗakin jikinsa na ɓari, ko Kallon gabansa ba ya yi tashin hankali ya bayyana akan fuskarsa, yana zuwa ɗakinsa ya faɗa kan gado tare da jan duvet ya lulluɓe jikinsa, wani irin zazzaɓi mai zafi ya rufe shi, he can't believe cewa Abra ba ƴar Mami bace, har yanzu ya kasa yarda ko kuma fahimtar hakan. Shiru ya yi haƙoransa na haɗuwa waje guda, ya zama kamar wani zautacce, ya kasa yadda, bacci ya ƙauracewa idanunsa how could he believes that Abra ba sister ɗinsa ba ce, yadda ya ke jin ta a ranshi, ya sa maganganun Mamin su ka kasa tasiri a zuciyar sa, sai dai kuma ko me za'ayi ba zai taɓa yadda Abra karuwa ce ta haifawa Abbi ita ba, bacci ɓarawo shine ya sace Salman cikin dare. Gefen Hajiya Na'ima kuma, daren black night ya zame mata, Babu wanda ya yi baccin kirki sai Abra. Wacce ake ta Masifa a kanta, she slept peacefully, ba ta san me yake faruwa ba. Gajiyar da Abra ta yi, bai hana ta tashi tun 7 na safe ba ta fara gyara gidan, ba tai Mamakin yadda ta ji gidan shiru ba, Faris ne kawai ya tsaya mata a rai, domin tasan da wuri yake fitowa ta yata aiki. Tana tsaye a kicthen, sanye da pech ɗin pyjamas ta ɗora hijab akai, wuƙa ce a hannunta tana yanka Onion  With red pepper wanda Zatai using da shi, wajan yiwa Abbi ƙosan da yake so. Few minutes ta gama haɗa ƙullin ƙosan da ya sha kayan ƙamshi da Egg. Tana gama soya ƙosan, ta ɗakko malkaɗɗan ƙullinta na kunun gyaɗa, wanda ya sha haɗin, Danyar gyaɗa, Dafaffiyar shinkafa, sugar, madara, Leman tsami, Filawa. 15 minutes to 20 ta kammala kunun gyaɗar, tana gamawa ta haɗawa Salman Smoothies. Haɗa komai ta yi akan dining table, zuciyarta fal tunanin abinda ya hana Salman fitowa. Cikin sanyin jikin nan nata, ta yi wanka ta shirya cikin wata blue ɗin Abaya mai stones, ta yi rolling kanta da Vail ɗin, Oval shape face ɗin ta, ya sake fitowa kyanta na ƴan matanci, ya bayyana a fili da Wahala mace ta kalli Abra bata sake Kallonta ba, balle kuma namiji. Ƙyakƙyawan idanunta ta ja ta rufe tana jin yadda hearing aid ɗin nan sometimes yake damunta. Flat shoe ta saka ta nufi Main Parlour, amma ga Mamakin ta har zuwa lokacin babu kowa a parlourn, da fararen idanunta take bin cikin wajan dining table da kallo, a nutse ta nufi bedroom ɗin Salman domin tabbatar da lafiyarsa. A hankali ta tura ƙofar ɗakin, Salman na kwance har lokacin idanunsa biyu, bawai barci ya ke ba, Ƙamshin turarenta kawai ya shaƙa wanda ya tabbatar masa Yayarsa ce, da sauri ya rufe idanunsa yana ƙara narkewa jikin bargon daya rufe jikinsa da shi. Abra ta kalli Salman, cikin sanyin murya ta ce."You haven't woken up yet?" Ƙara rufe idanunsa Salman ya yi. "Faris" Abra ta ƙara kiran sunansa tana yaye bargon daya lulluɓe jikinsa da shi, Shiru ya sake yi ma ta baya son ko haɗa idanu ya yi da ita. Kamar Abra za ta yi kuka ta ce. "Please Faris wake up, It's already morning" Ta faɗa a sanyaye kamar mai raɗa. Tana ƙoƙarin zare bargon da ga jikinsa baki ɗaya, Salman ya yi saurin riƙewa tare da juyowa baki ɗaya zuwa inda Abra take zaune. Kallon juna su kayi, shi dai bai Magana ba, sai bin ta da ido da yake. Abra ta ce. "Barcin me kake haka?" Idanunsa ya mayar kan hannunta data riƙe bargon, sai kuma ya ware idanun shi ya ce. "Yaya.." Abra ta kwaɓe fuska ta ce "Ba wani yaya, kawai ka je kayi wanka sai muyi breakfast, ka ga yau har Smoothies na yi maka" Salman ya Girgiza kai idanun shi a ƙasa yana kallon hannunta ya ce. "Ba wannan ba yaya" "to mene?" Abra ta faɗa da ɗan sauri ganin gaba ɗaya Salman baya cikin mood ɗin sa, langwaɓar ma ta da kai gefe ya yi cikin ƙasa da murya ya ce. "Have you forgotten?" Ta ware idanunta, sai kuma ta ce "Na manta" Murmushi kawai ya yi ma ta yana Girgiza kansa da ke masa ciwo. Ganin ya yi shiru kuma ba shi da alamun mgn Abra ta ce "Kayi shiru?" "A'a ba komai yayata" Ta ce "to tashi ka yi wanka" ya dafe kansa ya ce "Ke yaya wannan wankan kamar ibada, kai na kemin ciwo sosai, sanyi-sanyi na ke ji" Jikin Abra na rawa ta ce. "You're sick Faris? Me ke damunka? Kayi wanka bari na kawo maka breakfast nan, sorry ƙanina" ɓata fuska Salman ya yi "Yaya wai dame kika fini ne?" Abra ta ce "kamarya?" Ya Girgiza ma ta kai yana rufe idanu Calmly ya ce "Nothing!!" Shiru gaba ɗaya suka yi, Abra har ranta take jin babu daɗi, bata so ko kaɗai Faris ya yi ciwo musamman yanzu da taga idanun shi ya yi jaa, ta ƙara tabbatar da ciwon kai ya ke sosai. "massage my head Angel" Zama ta yi a gefen gadon idanunta a kansa tana kallon fuskarsa mai kama data Maminsu sak, a hankali Salman ya kwanta yana ɗora kansa a cinyar Abra, cikin nutsuwa Abra take masa massage ɗin yatsun hannunta gaba ɗaya a cikin sumar kansa wanda ya ke saman cinyarta, bayan ciwon kai hadda zazzaɓi. "Faris" "Uhm Angel Abbi's daughter, alfaharin Faris" A sanyaye Abra ta ce. "I love my mother Faris, I want to be with her" Da sauri Salman ya tashi zaune ya ce. "Mene yasa kike son damun Kan ki ne har haka yaya? Nifa idan kina cikin damuwa wlh na fi ki shiga damuwa, na faɗa maki komai lokaci ne, ita fa Mami karar ɗan fari take maki, amma kullum muka haɗu da ita sai tace min tana sonki, tana alfahari dake.. Mami loves you more than me" Idanun Abra na cika da hawaye ta ce "da gaske ka ke Faris? da gaske Mami tana so na?" Kai kawai ya ɗaga ma ta, yaƙi yarda ya kalleta, yana tuna maganganun Mami na jiya, masu ɗaci da tsayawa a rai. Miƙewa ta yi ta ce "to kayi wanka ka fito yanzu ko?" Kai ya ɗaga ma ta kawai, ita kuma ta fita a hankali yabi bayanta da kallo. Abbi ta samu zaune saman dining table hannunsa riƙe da mug yana shan kunun gyaɗa, da idanu ya bita a kullum mmki da girman Abra yake, har tsoran kyanta ya ke. "Good morning Abbi" "Mrng Abbin's daughter" Zama ta yi tana haɗa tea ta ce "Abbi yau kun makara, Mami bata fito ba?" Murmushi ya yi mata yana ajjiye mug ɗin hannunsa ya ce. "Na tashi, ina duba wani abu a system, Mami bata jin daɗi. Ina ƙanin naki?" Abra ta marairaice fuska kamar zatai kuka ta ce. "Abbi Faris ma baya jin daɗi, ka kira masa doctor ya duba sa shi da Mami" Abbi ya ɗan yi Murmushi ya ce "My dear, Salman namiji ne, ba mace kamarki ba. Shi ya sa yake raina ki komai na kuka ne a wajanki?" Abra ta ce. "Abbi da Salman kawai nake hira fa, idan ya kwanta ciwo bana jin daɗi sai na ji zazzaɓi ya kamani" cike da tausayawa Abbi ya ke kallon Abra. Kafin ya yi magana Salman ya fito cikin tattausan farin yadi mai kyau irin na Abbinsa, sai ƙamshi yake abinka da farin bafulatani ya yi wani irin kyau. "Mrng Abbi, yaya haɗa min tea pls cikina" Da sauri Abra ta shiga haɗa masa tea ɗin tana faɗin "Sorry Faris, sorry" Abbi ya kalli Salman ya ce "Ya jikin?" A hankali ya ce "felling much better Abbi" amsar tea ɗin hannun Abra ya yi ya fara sha, sai da ya shanye tas. Kana ya sha Smoothies ɗin da dankali. "Abbi bari na duba Mami" Abbi ya ce "a'a kiyi zamanki, ta sha magani barci ta ke" Salman dai bai ce komai ba. Da ga ƙarshe ya miƙe tsaye Abra ta ce "ina zaka?" Ya ɗan kalleta ya ce "Yaya ki koyi zama ke ɗaya fa, ni da ba mace ba nayi ta zama a gida" ta marairaicewa ta ce "Abbi ka ji shi ko?" Abbi ya ce "Ina jinsa, but he's right kada ya zama namamajo" nan da nan idanunta ya cika da hawaye Salman ya matsa kusa da ita yana ma ta dariya ya ce. "To kawai ki yadda ni ne babba sai in dinga zama kullum a gida" da sauri ta ce "Na.... Na yarda pls Faris gidan babu daɗi fa" ya ɗaga ma ta gira yana gyara zaman hular kansa ya ce "Sorry Angel, yanzu zan dawo wani abokina zan duba" Miƙewa tayi ta ce. "To zan rakaka, kaga sai ka rakani Saloon ko?" Ya ce "kada muyi haka dake yaya, ke ba matata ba, ke ba ƙawata ba, duk inda zani kice zaki yanzu zan dawo" Abra ta saki kuka kamar ita ce ƙarama ta ce. "Pls Faris ai ba zan bika ciki ba, kawai a waje zan tsaya sbd kada ka daɗe" Salman ya ce. "Ki zauna a waje yaya? Kuma ke sai ki zauna ɗin baki san mace sirri ba ce?" Sai a lokacin Abbi ya saka baki cikin maganar ya ce. "Ƙyaleshi Daughter, ranar da zaki yi aure ki bar masa gidan sai yafi kowa maraici" da sauri Salman ya kalli Abbi ya ce "Aure kuma?" Abbi ya kama hannun Abra ya ce. "E, Aure. Zata bar maka gidan ka cinye" kasa cewa komai Salman ya yi da sauri kuma ya fice da ga cikin Parlour ya bar gidan ba ki ɗaya. Abbi kuma ya ja Hannun Abra yana faɗin "Wallahi shi ya sa Salman ya raina ki, kece babba amma kina maida kan ki ƙarama, gashi nan shi ya zama ƙatoto ya kusa kamani ke gaki nan kamar tsinke, banda shagwaɓa ba abunda ki ka iya". Da sauri-sauri Salman ya fito da ga cikin motar bayan driver ya yi parking a entrance ɗin gidan su Ammi. Kai tsaye ciki ya nufa hankali ta she .Granny dake zaune a parlour hannunta riƙe da ƙatoton carbi ta yi saurin runste idanunta ta ce. "Wa'innahu sulaimanu wa'innahu bisimillahir rahim, wanne ɗan asarar ne haka ya faɗo mana gida kamar kidnapa?" Salman ya nemi waje ya zauna, ba tare da ya kalli Granny ba, infact hankalinsa ba ya jikinsa. Granny ta miƙe tsaye jiki na rawa tace. "A'isha! A'isha! A'isha ki fito, fito maza Allah ya yi wa Na'ima rasuwa, Allahu Akbar Na'ima sa'i ya yi" Kallonta kawai Salman ya yi jiki na rawa Ammi ta fito ta ce. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wacce Na'ima? Daman bata da lafiya ne?" Granny ta girgiza kai ta ce. "Huhu ina zan sani, bari dai muji ko mutuwar ce?" Ammi ta ce "A'a, Hajiya ba shi ne ya faɗa ba?" Granny ta haɗe fuska ta ce "A'a kawai sai gani nayi ya faɗo mana gida hankali ta she, idan ba Na'ima ce ta rasu ba Uban mene zai saka ya faɗo mana gida kamar ɗan fashi ko irin kwartayen layin nan?" Ammi ta zauna kusa da Salman ta ce. "Mai gida ya ya akai ne?" Salman ya ce. "Ammi da gaske Yaya ba ƴar Mami bace?" Granny ta dafe ƙirjinta ta ce. "Masifa ta sauka a gidan Kamalu tirrr da halin Na'ima, ban taɓa gani ko jin labarin gantalliyyar mace mara rufin asiri irin Na'ima ba, Ubangiji ka ɗai ya san yadda zai da ita" Kasa Magana Ammi ta yi hankalinta gaba ɗaya ya tashi har wani gumi ke tsastsafo ma ta. "Ammi wajanki na zo domin ki faɗa min gaskiya, don Allah ka da ku barni a duhu, gani na ke har yanzu dare ne ban farka ba, gani nake kamar mafarki nake, Pls Ammi ka da ku barni cikin DARE DA DUHU" Salman ya ƙare maganar yana kama hannun Ammi. A sanyaye Ammi ta ce. "Naima told the truth, Abra is not her daughter, You and Abra are not siblings" Kai Salman ya shiga girgizawa Ammi ta ce. "Khamal ne ya tsinto Abra lokacin da suka je wani jeji...." She told him everything in a nutshell. Da yadda aka samu Abra, da kuma matsalar da Na'ima ta bayar kafin ta amince da riƙe Abra! Kasa Magana Salman ya yi a lokacin na farko ya fashe da kuka yana ɗora kansa a cinyar Ammi, yana wata irin sheshsheƙa kamar ba namiji ba, wani irin tausayin Abra na ratsa zuciyarsa, ya na ji tamkar zuciyarsa ce zata bar tsakiyar ƙirjinsa sbd tsabar tashin hankali. Hankali tashe Granny ta yi waje wajan gatekeeper tana faɗin. "Huhuhu idan bai kai Na'ima kotu ba Shegiya uwata ta haifan, Allah shi kaɗai ya san yadda zai da Na'ima ni da zan bawa Kamalu shawara kawai ya Aure yarinyar muga tsiya..." Sai kuma ta yi shiru tana zazzare idanu ta ce. "A to ai ba wani abu ne, uban kowa ya san ba shi ne ya haifeta ba, wlh Na'ima za ta ga yadda ake tsiya da iya bariki idan ban saka Kamalu ya auri Babura ba a gantale a na zo duniya to" Gatekeeper ya ce. "Hajiya lafiya kowa?" ta yi ƙasa da murya ta ce. "Ashe matar Kamalu mahaukaciya ce?" Shi dai Ya yi shiru, dan sun saba da wannan rikicin na ta na tsufa. Sai Yamma Salman ya bar gidan bayan Ammi ta ba shi amanar Abra akan ya kula da ita, kada ya bari ta san Maganar ya share mata hawaye, Abbinsu baya zaman gida sosai.. ya ajjiye girmansa da Abra ta yi a gefe ya kula da kimarta. Kaduna North. Police station. Ya na zaune a cikin office ɗin sa, jikinsa sanye da farar singlet sai ɗaukan idanu ta ke, ta kama faffaɗan ƙirjinsa fuskar nan tasa, a Kame kamar kullum babu alamar fara'a. Fararen idanunsa maƙale a jikin keyboard ɗin system wacce ke gabansa a saman table, cikin zafin nama yake operating system ɗin yana taune laɓɓansa. Baka ganin komai a fuskarsa sai jan laɓɓansa da farin Eyeballs ɗin sa, sumarsa tai kwance luff a kansa. Tsaki ya ja kaɗan, sbd hayaniyar da ke ta shi da ga cikin police station ɗin zuwa office ɗin. He doesn't like noise, ciwon kai take sa shi. Tsaki ya ƙara ja a karo na biyu, cikin zafin nama kuma ya miƙe tsaye yana tura hannunsa cikin sumar kansa idanunsa ya yi jaa sosai sbd ciwon kan da ya fara. Hannunsa zube cikin Aljihu ya nufi wajan office ɗin, da ga shi sai farar singlet da dogon wando na police uniform Wanda ya ƙara haska ɓakar fatarsa. Tsaye ya yi a bakin wajan hannunsa ɗaya cikin Aljihu ɗaya kuma ya riƙe ƙugu da shi. Cikin tsawa S.p Adnan Aliyu Matawalle ya ce. "Heyyy!  What's going on here?"  Wani da ga cikin police ɗin wajan ya tsarawa S.p Adnan ya ce. "He was arrested for raping a three-year-old girl" S.p Adnan ya ware manyan idanunsa, idan akwai abinda ya tsana a cikin  main crime that people are found with shi ne ”fyaɗe” He hates the word and doesn't like it at all. Cikin ɗaga murya S.p ya ce "What? Reped  three-years old? Police officer ɗin ya ce "Yes sir, wlh abin is so boring The girl died too" Nan take idanun S.p Adnan ya ƙara yin jaa fiye da baya jikinsa na ɗan rawa kasancewar sa Mutum mai zafin zuciya, yana zuwa wajan Mutumin da ya yi fyaɗen ya kama hannunsa yana faɗin. "You're mad, How can you rape a little girl like that? Ehh? you killed her!" S.p ya faɗa yana fesar da iska da ga cikin bakinsa, idan ransa ya ɓaci bai iya controlling kansa ba, gaba ɗaya Police Officers ɗin suka shiga hankalinsu. Cikin ɓacin rai S.p Adnan Aliyu Matawalle ya damƙi Hannun mutumin ya ce. "An old man like you is the one who will rape her?" Ƙass!!! Sauti Hannun tsohon ya bada ƙara sakamakon ƙarya hannunsa da S.p ya yi, wanda shi kansa bai san ya aikata ba. Rai ɓace ya koma Officer ɗin sa ya ɗauki key car ya nufi waje. Police Officers ɗin suka faɗawa D.o.p, abinda ya ke faruwa shi kuma D.p.o ya faɗawa presquito, presquito ya miƙa tsohon zuwa Court. Tun da ga bakin gate ya fara danna Horn babu saurarawa, da sauri gatekeeper ya buɗe masa gate ɗin, cikin zafin nawa ya tura kan Benz ɗin sa cikin entrance ɗin babban gidan na su. Murfin motar ya buɗe ya fito kansa a ƙasa hannunsa zu be cikin Aljihu ya nufi cikin gidan da ɗan sauri domin babu abinda ya ke bashi tsoro irin hadari. Gashi garin dab ake da fara ruwan sama. Hajiya Mama dake zaune a Parlour tana kallon News ta ce. "Wlcm My son"  wajanta ya Ƙarasa yana ɗora kansa a cinyarta idanunsa ya rufe, kalmar fyaɗe na yi masa yawo a cikin kansa. Hajiya Mama ta ce "what happened? as if you are worried" Mirginawa ya yi a saman cinyarta ta tare da yin shiru, a hankali ya ke saukewa numfashi a nan cinyarta barci ya ɗauke sa tana shafa masa kai. Da idanu Hajiya Mama ta ke bin Adnan har tsoron zafin ransa ta ke, ga taurin kai. Tana jinjinawa matar da zata iya zama da shi matsayin miji. Burinta a yanzu bai shige ta ga aurensa ba. Washegari ya kama weekend. Driving ya ke kamar zai tashi sama, Usman dake gefensa ya ce. "Wlh ka zubar damu Allah ya isa" S.p ya ja tsaki ransa a ɓace Usman ya ce "ka daɗe ba kayi tsaki ba, zance ne dole ka rakani kayi ta zama a haka mu soyayya yanzu muka fara" Adnan dai yaƙi cewa komai, kuma babu alamun zai ce Usman ya gyara zama ya ce. "You don't understand, but love is love, it changes a person, ban taɓa tunanin zan so farar mace ba, burina na auri baƙar mace, When I saw Meenal for the first time, I couldn't help myself, yarinyar classic ce very educated ƙyakƙyawa ce sosai, A beauty I have never seen before" Usman ya wani lumshe idanunsa ya ce. "Kuma a photo kawai na kanta,  ina ta imagine yadda zan ganta reality, Uhm anya zan iya controlling kai na? Ƙiiiiii!! S.p Adnan Aliyu Matawalle ya ja burki cikin zafin zuciya ya damƙo Usman ya ce. "Banza, lion mayen mata zaka fice min da ga mota" Usman ya zare idanu ya ce "Goodness, zaka yiwa Meenal asarata let go of me pls my dear friend" hankaɗasa gefe S.p ya yi cikin ɓacin rai yaci gaba da driving har suka isa unguwar su Meenal wacce take da ɗan nisa da tasu sosai. Kaf unguwar babu gida mai kyau da girma irin gidan Dr G.y Bulama, mai gadi ya buɗe musu ƙofa kasancewar Meenal ta sanar masa da zuwan guests ɗin ta. S.p ya gama parking Usman ya fara fita Adnan ƙin fita ya yi sai ma ƙira'ar Mishary Rashid Alafasy. A hankali ya ke bin ƙira'ar idanunsa rufe, cikin jin haushi Usman ya ce "Wannan dai wulaƙanci ne, ka ga idan zaka wulaƙantani a gaban Yarinyar nan ka koma kawai Nagode" Adnan ya yiwa motar key, ganin da gaske tafiya zai Usman ya ce "Amma da ga ɗan iska sai kai S.p kaga ni wasa nake Please get down ga yarinyar nan" kashe motar ya yi tare da fitowa yana ƙare haɗe fuska nan na tasa, jikinsa sanye da maroon ɗin voyel mai kyau idanunsa maƙale da glasses mai kyau sai sumar kansa kwance da ita. Idanunsa ya ɗauke lokacin da Meenal ta ƙaraso wajan Usman ya shafa kai ya rasa me zance tayi musu Welcome ta ce "shall we...?" Ta faɗa ta nayin gaba. Usman ya kama Hannun S.p suka nufi guest Room ɗin da Meenal tayi. Few minutes ta cika musu gabansu da kayan motsa baki, S.p ko amsa gaisuwarta bai ba, saboda rsai zufa data yanko masa, ganin yanayin S.p yasa Usman faɗin "Are You Okay Adnan?" A karo na farko Meenal ta ji Muryar Adnan mai tsananin daɗi ya ce "Headache.. i think I'm going now" ya faɗi hakan yana ɗauke idanunsa daga kan photon dake maƙale a jikin bango, Waje ya yi yana dafe kansa, yana fita Usman ya ɗan tattauna da Meenal ya na jin kamar ya ɗauke ta su tafi kawai tun yaushe, a nan tayi inviting na su zuwa birthday party ɗin ta, kana sukai sallama. Kasa driving S.p ya yi, hakan yasa Usman ya amshi driving ɗin suka nufi gida. A nan garin Kano. Salman ne ke biye da Abra cikin Ado Bayero mall, bayan ya rakata Saloon suka biyo yin shopping tare da shan ice cream. Bill ɗin kuɗin kayan akai masu Salman ya bada a.t.m aka cira, shi kuma ya ɗauki kayan ya ce "Angel muje" Abra ta bi bayan Salman cikin sanyin jiki, musamman da wani mutum ya kafeta da idanu. "Yaya idan ki kai aure ba'a gidanki zan tare ba, sbd na dinga tayaki aiki,  wannan sanyin jikin naki ya yi wa, kalleki wata rana dai zan goyaki naji nauyinki, dan na tabbatar jariri sai ya fiki" Abra tai Murmushi ta ce "Allah ya shiryaka Faris" da sauri ya ce "Amin Yayata, ina buƙatar shirin Ubangiji kiyi min addu'a kwana nan bana gane kai na" Da sauri ta ce "Meke damunka Faris? Gaya min Pls" ya girgiza ma ta kai ya ce "Wlh ban sani ba Angel" suna ƙoƙarin fita daga cikin wajan mutumin dake kallon Abra ya yi saurin riƙe ma ta hannu. A razane Abra ta juya sukai idanu biyu da saurayin mai kyan gaske, fari tas ƙyakƙyawa ajin farko. Jiki na rawa ta fara ƙoƙarin  ƙwace hannunta. Saurayin mai suna Abdullah ya ƙara riƙe hannun Abra gashi Salman ya yi mata nisa yana can yana surutu ya ɗauka suna tare, cikin razani Abdullah ya ja numfashi ya ce "Who are you?" Ya faɗa yana ƙoƙarin shafa fuskarta, kafin ya Ƙarasa ɗora hannunsa akan fuskarta ya ji an sauke masa wani irin mari, da sauri ya dubi Salman dake tsaye yana huci kamar zaki ya ce "How dare you slap me like that?"  Salman ya ce "An marake, kasan jikin waka taɓa? Wlh kamar an soka min  ma shi a zuciya,  mutum ɗaya keda mallakin jikin Angel wlh na ƙara ganin ka shiga harkata sai nayi maka illa" A wannan lokacin Salman har Abra ya ji haushi,  ko inda take bai kalla ba ya juya tare da yin waje, yana ƙoƙarin ficewa Abra ta ƙwala masa kira "Faris...!!!" Zubewa ta yi a waje jikinta na rawa numfashinta na ɗaukewa ƙirjinta na ɗagawa kamar mai Asthma, hannunta riƙe da cikinta, a kiɗeme Abdullah dake tsaye ya durƙusa zai kama Abra Salman daya ƙaraso wajan ya hankaɗe Abdullah yana zubewa gaban Abra yana faɗin "Yaya mene ya sameki? Yaya menene I'm here ga ƙaninki a wajanki, Angel open your eyes" ya ƙare maganar yana jijjigata amma tuni numfashinta ya yi sama yana ƙoƙarin ɗaukewa. Cikin tashin hankali Salman ya jawo Abra jikinsa yana ƙanƙameta kamar wani zai ƙwace masa ita. Ganin numfashi na ƙoƙarin ɗaukewa, ga shi duk mutane sun zagaye su yasa Salman warware rolling ɗin kan Abra ya rufe mata fuska can kuma ya tuna da maganar wani malamin su daya faɗa musu a lap, cikin sauri jikinsa na rawa da ɓari ya ɗaga mayafin nata tare da zura ƙansa ciki, a hankali ya tallafo fuskarta a hannunsa tare da ɗora bakinsa akan nata... LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU* _Brigh pens✍️_ Nimcyluv Ayushercool Zee Kumurya                                P14 Domin samun complete litattafanmu, ku yi following ɗin wannan accounts ɗinkin a Arewabooks https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949 https://arewabooks.com/u/nimcyluv https://arewabooks.com/book?id= Elegant online writers LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Kamar wanda aka tsikara ya yi saurin janye fuskarsa ya fasa yin abun da ya yi niyya, gyara mata mayafin jikinta ya yi ya ciccib'e ta ya miƙe tsaye da ita a jikinsa. Mutumin nan da Salman ya hankaɗe shi bai daddara ba ya ƙara matsowa da niyyar ya taimaka masa su riƙe Abra tare, a matuƙar kufule Salman ya kai masa duka da ƙafa, saurin ja baya ya yi cikin mamakin ƙarfin halin yaron da taurin zuciyarsa. Wata muguwar harara Salman ya cilla masa tare da yin ƙwafa sannan ya yi gaba da sauri ya nufi Motarsu. Driver na hango su ya fito daga mota da sauri, cikin al'ajabi ya fara tambayar Salman abun da ya faru. "Please buɗe mun baya na saka ta mu tafi asibiti." Salman ya faɗa masa haka cikin damuwa da ɓacin rai. A hanzarce Driver'n ya buɗe masa Motar, kwantar da Abra dake sume tamkar babu numfashi a jikinta ya yi, sannan shi ma ya shiga bayan, akan cinyarsa ya ɗora kanta ya ƙurawa fuskarta ido cikin tsananin damuwa da fargabar kar ya rasa ta, a hankali ya ɗora hannunsa akan fuskarta yana shafawa cikin rashin sanin abun yi, addu'a kawai yake a cikin ransa akan Allah ya tashi ƙafaɗun Yayarsa. Cikin mutunen da suka biyo su suna musu Allah ya kiyaye gaba, wani ya miƙa masa handbag ɗin Abra da ledar siyayyar da suka yi. Ko kallan shi bai yi ba dan ba ta su yake ba, sai driver ne ya karɓa ya saka a front seat. Matashin saurayin nan kuwa (Abdallah) ya kasa ɗauke idonsa daga kansu, sai da Motarsu ta bar gurin sannan ya sauke numfashi ya shiga tasa motar cikin sanyin jiki, zuciyarsa cike da tsananin mamakin wani al'amari. Asibitin Isyaka Rabi'u nan Driver'n ya kai su, saboda yanda Salman yake azalzalar shi akan ya yi sauri, asibitin kuma shine asibiti mafi kusa daga nan Ado Bayero mall ɗin. Ko gama daidaita parking driver bai yi ba Salman ya buɗe Motar tare da fitowa ya nufi cikin asibitin cikin sassarfa. After some minutes suka fito tare da wasu Nurses dake ɗauke da kujerar ɗora marasa lafiya. Cikin sauri Salman ya fito da Abra daga cikin motar aka ɗora ta akan wheel chair, Nurses ɗin suka tura ta zuwa ciki Salman na biye da su. Emergency suka nufa da ita. Har ɗakin da aka shigar da ita Salman ya so bin su, amma aka dakatar da shi aka ce ya jira waje. Numfashi ya sauke mai zafin gaske saboda yanda zuciyarsa take yi masa ƙuna, hoton saurayin nan a lokacin da ya riƙe hannun Abra tare da ƙoƙarin kai hannunsa fuskarta ya kasa b'acewa daga cikin zuciyarsa, ganin abun yake tamkar yanzu yake faruwa. Ga kuma damuwar halin da Abra ta shiga lokaci ɗaya, zuciyarsa sai bugawa take saboda fargaba da tashin hankali. Dafe kansa da gumi ke kwance akai ya yi, innalillahiwa'inna'ilaihirra'un kawai yake maimaitawa a cikin zuciyarsa. "Allah ka tashi ƙafaɗun Yaya ka ba ta lafiya." Ya faɗi hakan a fili cikin tsananin damuwa. "Me ya same ta ne wai ƙaramin Alhaji?" Driver da ya biyo bayansu ya tambaye shi a rud'e. "I don't know, ƙara kawai na ji ta yi, shikenan sai ta faɗi." "Subhanallahi, to Allah Ubangiji ya ba ta lafiya." "Ameen." Ya amsa a ƙasan maƙoshi. Zarya ya shiga yi a reception ɗin cikin tashin hankali, dan ya rasa a ina ma zai saka ransa ya ji daɗi, sai kallon ɗakin da aka shigar da Abra yake, ji yake kamar ya tafi ya faɗa cikin ɗakin ya ga halin da take ciki, danne zuciyarsa kawai yake yi, tunda ya san dokar asibiti ne hakan. Daga baya sai ya koma bakin window'n ɗakin yana leƙawa, amma babu abun da ya iya gani saboda glass ɗin window'n a zuge yake, kuma da akwai labule ta ciki. Sai a lokacin ya tuna da ya kamata ya kira gida ya sanar musu halin da ake ciki. Wayar driver ya karɓa da niyyar kiran Abbi, sai kuma ya tuna baya nan, hakan yasa ya kira number Na'ima. Tana zaune a parlour tana karkaɗa ƙafa, idanunta akan ƙofa tana jiran shigowar su Abra ta ji dalilin da yasa su ka je suka zauna, alhalin Abran ta san za ta yi girki. Wayarta dake kan cinyarta ce ta fara ringing, ɗan tsaki ta yi sannan ta ɗauki wayar ta duba, ganin Number Driver ya saka gabanta fad'uwa. A fili ta ce. "Wayyo, Allah yasa ba wani abun ne ya samu My Son ba." Ta ɗaga wayar cikin sauri tare da karawa a kunne, a hanzarce ta ce. "Hello, driv...." "Ni ne Mami" Salman ya katse ta da faɗin haka. Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi ta ce. "Salman a ina kuka tsaya ne har yanzu ba ku dawo ba?" "Mami Yaya ce ta faɗi a cikin mall ɗin, yanzu haka muna asibiti." "Kamar ya ta faɗi? Aljanu ne da ita ko me?" Ta yi maganar cikin yamutsa fuska. "I don't know, ban san me ya same ta ba Mami, dan Allah ki zo asibitin yanzu." Ya yi maganar cikin tsantsar damuwa. "In zo in mata me?" "Haba Mami, ki ga jikin nata mana, ƴarki ba lafiya amma ki ce me zaki zo ki mata." Cikin tsawa ta ce, "Ƴar karuwa dai, kar ka ƙara danganta ni da ita, na faɗa maka." "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, Mami dan Allah ki daina wannan maganar, ba ki san yanda nake jin ba daɗi ba a cikin raina idan kika faɗa." "Tunda na taɓa Uwarka ba? Ka kiyaye ni fa Salman! Ka fita daga cikin idona in rufe." "Shikenan ki yi haƙuri, yanzu dai Please ki daure ki zo, wallahi Yaya tana cikin mawuyacin hali, numfashinta fa gaba-d'aya ya ɗauke." "Ta mutu ma ina ruwana? Idan na zo shi ne zai saka ta warke ko me?" "Amma zuwanki yana da muhimmanci, kin ga Abbi ba ya nan." "To ba zan zo ba ɗin, Salman ka kiyaye ni fa!" Mtss, ta ja tsaki tare da kashe wayarta. Bin wayar da kallo kawai Salman ya yi cikin matuƙar sanyin jiki, damuwar dake cikin ransa na ƙara yawaita, ya rasa wanne irin hali ne da mahaifiyarsa, ya rasa waccen irin ƙiyayya take yiwa Abra, har yanzu jin al'amarin yake kamar a mafarki, Yayarsa a bar soyuwa a gare shi ba ƴar'uwarsa ba ce ta jini! Zuciyarsa ta kasa ɗaukar wannan al'amarin, don ya yi mata girma da nauyi. Numfashi ya sauke mai zafi, wani irin sarawa kansa yake yi masa, tunanin kiran wayar Ammi ya yi, sai dai ya san Driver ba shi da Numbern ta, shi kuma ba shi da ita a kansa, kuma ba ya son ya kira Abbi ya sanar masa ya tayar masa da hankali. Wani tunani ne ya faɗo masa, hakan yasa shi fita waje da sauri, driver ya bi shi da ido. Motarsu ya buɗe ya ɗauko handbag ɗin Abra, cikin sa'a ya ga abun da yake nema. Numbers ɗin relatives ɗinsu ne Abra ta rubuta a cikin wata ƴar ƙaramar jotter, duk inda za su da ita take tafiya a cikin jakarta, saboda rana irin wannan, tunda su har yanzu Abbi bai ba su damar riƙe waya  ba. Ajiyar zuciya mai ƙarfi ya sauke, Numbern Aunty Iman ƴar Autarsu Abbi ya yi copy a wayar Driver sannan ya yi dialling, ringing kaɗan ta ɗaga tare da yin sallama. Bayan ya amsa ya ɗora da faɗin. "Aunty muna Hospital Yaya Abra ba ta da lafiya, na kira wayar Mami tun ɗazu ba ta ɗauka ba." A kiɗime ta ce, "Subhanallahi, me ya same ta? Kuna ina yanzu? Wanne asibitin ne?" "Ban san me ya same ta ba, mun fita shopping ne kawai ta faɗi." "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, ka tura mun address ɗin asibitin, yanzu zan biya na ɗauki Ammi sai mu taho tare, bari na kira baban Nu'aim na sanar masa." "Toh Aunty sai kun ƙaraso." Juyawa ya yi ya koma ciki, daidai lokacin Doctor's ɗin da suka rufu akan Abra suka fito daga ɗakin da take. Kamar zai tashi sama ya ƙarasa gare su yana faɗin. "Doctor ya jikin nata? Me ya same ta? Ta farfaɗo? Tana numfashi yanzu?" "Ka kwantar da hankalinka, ba wata matsala ba ce, mun samu numfashinta ya daidaita, yanzu haka ta samu bacci ne sakamakon allurar da muka yi mata." Cewar ɗaya daga cikin likitocin cikin son kwantar wa da Salman hankali. "Doctor me ya same ta to? Please ka mun bayani." Ya yi maganar a rikice. "Ina Mahaifiyarku ko wani babba?" "Suna hanya sun kusa ƙarasowa." "Ok, idan sun ƙaraso ka ce musu ina neman su a office ɗina." Ya ƙarashe zancen tare da nuna masa inda office ɗin nasa yake da hannunsa." Da to kawai ya amsa masa, dan ba ma wani fahimtar shi yake sosai ba, dan zuciyarsa na gurin Yayarsa cike da son ganin ta da halin da take ciki. Ko jiran a ba shi umarni bai yi ba ya tura ƙofar ɗakin ya shiga. Ita kaɗai ce a ɗakin mai ɗauke gadajen marasa lafiya biyu, tana kwance akan ɗaya idanunta a rufe numfashinta na fita a hankali a hankali, an ɗaura mata drip a hannun hagunta. Tsayawa ya yi a kanta cikin dokawar zuciya, after some seconds ya tsugunna tare da kama hannun damanta ya ɗora shi akan kirjinsa, idanunsa a kanta cikin tsananin tausayi da ƙaunarta. A hankali ya saka ɗayan hannunsa ya shiga shafa fuskarta yana faɗin. "Alhamdulillah, zuciyata ta fara samun nutsuwa daga fargabar rasa ki, Allah ya baki lafiya My Angel!" Kamar ta ji me ya ce sai ta ɗan motsa hannunta dake kan ƙirjinsa, ƙara ƙanƙame hannun nata ya yi cikin irin wani yanayi, a hankali ya kifa kansa a kan cikinta ya lumshe idonsa tare da sakin ajiyar zuciya, sassayan ƙamshinta mai daɗi yana ratsa ƙofofin hancinsa. A haka su Ammi suka shigo ɗakin hankali a tashe suka tarar da su. Aunty Iman da ta yi tunanin kuka Salman yake ta ƙaraso ta dafa kafaɗarsa cikin lallami ta ce. "Salman ga mu mun ƙaraso, ka kwantar da hankalinka, Insha Allahu za ta samu lafiya, cuta ai ba mutuwa ba ce." Ɗago kansa ya yi ya dubi Aunty Iman da idanunsa da suka rine zuwa launin ja, cikin damuwa ya ce. "Aunty me yasa Mami ta tsani Yaya tsana mai tsanani? Ko da ba ita ta haife ta ba bai kamata ba, wannan tsanar ta yi yawa, me ta yi mata? Me ne laifin ta? Ko da abun da take tunani haka ne ai ba ita aikata ba, me yasa take huce haushinta a kanta?" Kallon shi kawai su Ammi suke yi ba su ce komai ba, cikin ƙarfin hali Aunty Iman ta ce. "Ka yi haƙuri Salman, yanzu ba lokacin yin wannan maganar ba ne, ta lafiyar ƴar'uwarka muke yi, me ya same ta har ta faɗi ta suma?" Labarin duk abin da ya faru Salman ya ba su, lokaci ɗaya Aunty Iman da Ammi suka kalli juna kamar wanda suka fahimci wani abu. Cikin mamaki Ammi ta ce. "Wani kuma? Wane ne wanin?" Gyaɗa mata kai kawai Salman ya yi dan ba ma ya san zancen mutumin, saboda wani irin zafi yake ji a cikin zuciyarsa idan ya tuna riƙe wa Abra hannu da ya yi. Aunty Iman ta ce. "Ikon Allah, yanzu kuma kafin mu shigo nan mun haɗu da wani Doctor, ya ja mu ofis ɗinsa ya yi mana bayanin abun da yake damun ta bayan ya tambaye mu mu ne iyayenta, ya sanar mana firgici ta shiga, shi ne ya jefa ta a wannan halin, may be ta ga wani abu da ya firgita ta ne ko ya tsora ta over." Salman ya yatsina fuska ya ce. "Wa ya sani ko maye ta haɗu da shi." Ammi ta ce "Allah ya kiyaye, ba ma fatan haka, kar ka kuma faɗar haka Salman, na san daƙyar in ka yi Sallar la'asar yanda na gan ka agigicen nan, ka je ka yi yanzu tunda mun zo." Salman ya ce. "To, tare da muke da driver kuma na ga bai shigo ba." Ammi ta ce. "Mun haɗu da shi, na aike shi can gida ne ya karbo mana ruwan zafi da kayan tea a wajen Matar Shureim, saboda kiɗimewa mun manta ba ba mu ɗauko ba." Salman ya miƙe ya fice, Aunty Iman ta bi bayansa dan zuwa ta siyo magungunan da aka rubutawa Abra, ta kuma biya kuɗin charges ɗinsu da aka yi. Na'ima tana kwance akan gadonta tana chatting da ƙawayenta hankali kwance Major ya kira wayarta, bayan ta ɗauka sun gaisa ya ce. "Ina Daughter da Salman? Na kira general phone ɗin gidan na ji ba su ɗauka ba." Jim ta yi na wasu sakanni sannan ta ce. "Suna islamiyya, ni kuma ina ɗaki ban ji kiran ba." "Wacce Islamiyyar? Yau fa Thursday." "Oh sorry na manta, ka san na saba kafin su yi sauka suna zuwa har Alhamis da Juma'a, sun je shopping ne." "Na'ima wannan wacce irin magana ce? Yarana sun fita amma saboda careless baki san takamaiman inda suka tafi ba, sai kin yi kame_kame kafin ki sanar mun? Shopping ɗin kuma da aka fita tun 12 shine har yanzu ba su dawo ba?" Ɓata fuska ta yi ta ce. "Haba Khamal, ya kake so in yi, duk ƙoƙarin da nake akan yaran nan baka gani, dan yau ɗaya ka tambaya na yi mantuwar inda suka je sai ka kama faɗa, ni fa ɗan Adam ce ajiza kamar kowa, zan iya mantuwa. Kuma da kake cewa sun tafi tun ɗazu ba su dawo ba, nima ina zaune ni kaɗai faɗan da nake yi kenan, amma na kira driver ya ce mun suna hanya sun kusa ƙarasowa." Ajiyar zuciya Khamal ya sauke ya ce. "Shikenan Allah ya dawo da su lafiya, in sun dawo na san za su kira ni, ina zaune ni kaɗai a office kawai na ji hankalina bai kwanta ba, kamar something bad happen to you." "No..no babu komai, muna lafiya dukanmu." "To Allah ya ƙara muku lafiyar, ya cigaba da ba ku kariyarsa a kodayaushe." "Amin ya Allah Mijina, tare da kai." Ya amsa da Amin sannan suka yi sallama. Tsaki Na'ima ta ja a fili cikin takaici, wato har jikinsa ya ba shi babu lafiya, saboda waccan shegiyar yarinyar ba ta da lafiya. Taɓe baki ta yi ta cigaba da chat ɗinta. Sai da biyar ta wuce Abra ta farka, lokacin su Ammi suna tattaunawa akan abun da Na'ima ta yi na ƙin zuwa asibiti, da yake Salman ya ba su labari saboda yanda abun ya tsaya masa a rai. "Salman! Faris!" Da abun da ta farka a bakinta kenan cikin sanyin murya irinta marasa lafiya. A tare Salman da Ammi suka yi kanta, Ammi ta riƙe ta hannunta tana ambatar sunanta. Idanunta a lumshe amma sunan Salman kawai take kira. Wata sassanyar ajiyar zuciya ya sauke amma bai ce komai ba. Fita Aunty Iman ta yi dan kiran likita. Cikin kulawa Ammi ta ce. "Sannu Abra, Allah ya baki lafiya, ciwon lokaci ɗaya amma har kin faɗa." A hankali ta buɗe idonta ta sauke su akan kyakkywar fuskar Salman, idanunta a cikin nasa ta amsawa da Ammi da Amin. Ba yabo ba fallasa ya ce. "Sannu Yaya." Gyaɗa masa kai ta yi tana ƙara narkar da idanunta a cikin nasa. Lumshe idonsa ya yi ya buɗe wani baƙon al'amari na yawo a cikin zuciyarsa, bai kuma magana ba sai zama da ya yi a gefen gadon. Ammi ta gyara mata kwanciya tana jera mata sannu. Tare Aunty Iman suka dawo ɗakin da Doctor, ya dudduba jikin Abra tare da yi mata tambayoyi sannan ya tabbatar musu babu watar matsala, drip ɗin da aka saka mata yana ƙarewa za a sallame su. Kulawa sosai Ammi da Aunty Iman suka ba wa Abra, Salman ma ya nuna mata kulawa sosai amma ya ƙi sakar mata fuska, sai ta yi masa magana yana ji ya fuske kamar bai ji ba, duk sai ta ji ta damu, ta rasa sukuni a cikin zuciyarta. Bayan Magriba aka sallame su, Alhamdulillah jikin Abra ya yi sauƙi, kamar ba ita ce awanni uku zuwa huɗu da suka wuce take kwance cikin mawuyacin hali ba. Gidan Ammi Salman ya ce su wuce, dan ya san sai ta fi samun kulawa a can akan gurin mahaifiyarsa. Na'ima na jin shigowar Motar da su Abra suka fita ta yi saurin saukowa falon ƙasa, a tunaninta su ne suka dawo, ba ta san driver ne kaɗai ba. Jin shiru-shiru ba su shigo ba yasa ta ɗaukar mayafinta ta fita compound ɗin gidan. Kiran shi ta yi a waya ya zo inda take, cikin mamaki ta tambaye shi ina su Salman ta gan shi ya dawo shi kaɗai? A ladabce ya ce, "Hajiya Babba ta zo asibitin, daga nan suka wuce gidanta." "Wacce Hajiya Babban?" "Mahaifiyar Sir Khamal?" Jinjina kai ta yi ta ce. "Alright" Sannan ta juya ta koma ciki ranta a matuƙar ɓace. Abra tana kwance akan gadon ɗakin Ammi, idanunta akan Salman wanda har lokacin ya ƙi sakar mata fuska ta ce. "Faris cikina ciwo yake mini." Cikin kulawa ya ce. "Sannu Allah ya ƙara sauƙi, bari na karɓo miki magani a gurin Ammi." Ɓata fuska ta yi ta ce. "Me ya faru na gan ka a haka? Kamar kana cikin damuwa, tun ɗazu kuma ina tambayar ka, ka ƙi ba ni amsa." "Nothing." Ya faɗa yana ƙara haɗe rai. Cikin marairaicewa ta ce. "Please Faris tell me, ko so kake ka ganni a cikin damuwa ni ma? Ka san bana son na gan ka a cikin damuwa" Bai ce komai ba ya miƙe da niyyar fita, kukan da ta fashe da shi ne yasa shi dakatawa. Da sauri ya koma ya zauna a kusa da ita tare da kama hannunta, a rud'e ya ce. "Mene ne Yaya? Jikin ne ko ciwon cikin ne?" Cikin shagwab'a ta ce. "Kai ne Salman, ka ƙi faɗa mun abun da yake damun ka, ka san kuma ba zan jure ganin ka a haka ba, cikin ɓacin rai." Numfashi ya sauke ya ɗauki kanta ya ɗora akan cinyarsa, hawayen fuskarta ya fara share mata ya ce. "Babyn Abbi, zaki karyar mini zuciya da wannan shagwab'ar taki, har kin sa hankalina ya tashi, na ɗauka wani abun ne ya same ki." "To ai kai ne" "I'm sorry na daina My Angel" ya yi maganar yana shafa kuncinta. "To faɗa mun me yake damun ka, me ya ɓata maka rai?" "Tsayawar da kika yi har wani banza ya riƙe miki hannu, maimakon ki tsinka masa mari sai kika tsaya kina kallon shi." Ya yi maganar cikin ɓacin rai da takaici. "To ya zan yi Faris? Ni ma abun a bazata ya zo mun, amma ka yi haƙuri insha Allahu hakan ba zai kuma faruwa ba." "Allah yasa, dan bana fatan hakan ta kuma faruwa akan wani mai tsautsayin, dan tsaf zan karya hannun duk wanda ya kuma gigin taɓa mun jikinki." Da mamaki take kallon shi, yanda ya dage yake magana iya gaskiyar shi. Murmurshi ta yi ta ce, "To ka saki ranka mana in ji daɗi a cikin raina, ka ji ɗan ƙanina." Karan hancinta ya ja tare da yin murmurshi bai ce komai ba. Ƙarfe goma da ƴan mintuna na dare Salman yana zaune a parlour suna magana da Ammi Khamal ya kira wayar Ammi, bayan ta ɗauka sun gaisa ya ce ta bawa Salman wayar. "Hello Abbi." "Na'am Salman, me yasa kuka wuce gidan Ammi daga shopping ba ku sanar da Maminku ba?" Kallon Ammi ya yi sannan ya ce. "Abbi na kira wayarta zan sanar mata da wayar Driver ba ta shiga ba." "Duk da haka da kun koma gida kun fasa zuwa gidan Ammin, yanzu gashi duk kun ɗaga mata hankali, ta kira ni tana ta faɗa wai sai driver ne ya sanar mata, har yanzu ku ba ku kira ta ba." Shiru Salman ya yi dan ya rasa abun cewa, Khamal ya ce. "Kar ku sake haka, ba daidai ba ne." Cikin ladabi ya ce. "Insha Allahu Abbi za mu kiyaye." "Yawwa ɗan albarka, ina Yayar taka?" "Ta yi bacci." Daga haka suka yi sallama, zai faɗawa Ammi abun da ya faru ta dakatar da shi da faɗin. "Na ji komai ba sai ka maimaita mini ba, ka yi haƙuri Salman, mahaifiyarka ce Na'ima amma abubuwan da take yi ba ta kyautawa, ban yi tunanin duk shekarun nan har yanzu ba ta ƙaunar yarinyar nan ba, na ɗauka ta haƙura komai ya wuce, ashe da sauran rina a kaba. Abun da nake so da kai kar ka bari mahaifinku ya ji wannan maganar, kamar yadda na faɗa tun ɗazu kar a sanar masa wannan ciwon da Abra ta yi, to ko nan gaba kar ka faɗa masa, saboda ba na son ya san da batun ƙin zuwa duba Abra da Nai'ma ta yi." Jiki a sanyaye Salman ya ce. "Insha Allahu, wai ina Granny ne?" "Ta je gidan Gwaggo tun safe, a can za ta kwana, sai gobe za ta dawo." Salman ya ce. "Shi yasa na ji gidan tsit, ba ta zo ta cika mu da magana da karaɗi ba." "Uwar tawa ce mai karaɗi Salman?" Bai ce komai ba ya miƙe yana dariya ya shiga ɗakin da Abra take. Ya tarar da ita a zaune ta ƙurawa guri ɗaya ido. "Yaya kin tashi? ko cikin ne?" Kamar za ta yi kuka ta kalle shi ta ce. "Ina Mami? Me yasa ba ta zo ba?" Kama hannunta ya yi ya ce. "Ba'a faɗa mata baki da lafiya ba ne, saboda kar hankalinta ya tashi, that is why muka taho nan." "Mami ba ta damu da ni ba, babu yanda za'a yi hankalinta ya tashi saboda ba ni da lafiya." Ta yi maganar cikin tsantsar damuwa. "Wa ya faɗa miki? Ki bar wannan maganar, Mami tana son ki sosai na faɗa miki." "Soyayya ba ta ɓoyuwa Faris, ƙiyayya ma haka, ban san me na yiwa Mami ba ta so na ba, ba ta saurare na, ba ta jana a jiki ta kula da ni kamar kowacce Uwa da ɗanta!" Ta ƙarashe maganar cikin kuka. Cikin damuwa ya ce. "Dan Allah Angel ki bar wannan maganar, kin ga baki da lafiya, kar ki ƙarawa kanki wani ciwon." Daƙyar Salman ya rarrashi Abra ta yi shiru, dan sosai ta birkice take kuka, ba ta yi tunanin tsanar da Mami take mata ta kai haka ba, ba ta da lafiya har kwanciya ta yi a asibiti amma ba ta je ta duba ta ba, a matsayinta na mahaifiyarta, dole abun ya taɓa zuciyarta sosai. Sai da ta yi bacci sannan ya bar ɗakin, zuciyarsa cike da damuwa, shi kansa abun da Mami take yana damun shi ba kaɗan ba. Washegari bayan su Abra sun karya Ammi ta haɗa su da driver ya mayar da su gida, saboda kiran wayar Ammi da Khamal ya yi da sassafe ya ce su koma gidan, Na'ima ta gan su ta ji daɗi dan duk ta damu, shi ma yana hanya yau zai dawo. kasancewar jikin Abra ya yi sauƙi sosai sai Ammi ta bar su suka tafin. Duk da ta so su zauna su kwana biyu ko dan ta kula da Abra sosai, kuma gidan ita kaɗai ce Baffa ma baya nan ya yi tafiya. A parlour suka tarar da Na'ima hakimce akan kujera tana karkaɗa ƙafa, ta ci kwalliya kamar wadda za ta wani gurin, ƙamshinta ne kawai yake tashi a cikin parlour'n. Salman ne a gaba Abra na bin shi a baya, kanta a ƙasa suka yi sallama. Ba ta amsa musu ba sai bin Abra da ta yi da wani mugun kallo. Cikin sanyin murya Abra ta ce. "Sannu hutawa Mani, Ina kwana?" "Yana gidan Ubanki!" Ba ta kuma cewa komai ba ta nufi ɗakinta da sauri cikin sanyin jiki, Salman ya bi ta da kallo. "Sannu Salman, Na mamajo, bita zai_zai, cingum, maƙale mata duk sunayenka ne, abun da ka yi kuma ka kyauta na tafiya gidan kakaninka ku kwana, saboda ka ja mun baƙin jini a gurinsu ko? a ce bana kula da ita, wannan jarababbiyar tsohuwar ta zo ta cinye ni da masifaffen surutunta mara ma'ana." "Ki yi haƙuri Mami don Al.." "Ba zan yi ba, kullum kai kenan daga an yi magana a yi haƙuri a yi haƙuri, wallahi Salman ba dan a gida na haife ka ba sai in ce canza mini kai aka yi, na rasa me yasa kodayaushe ina ƙoƙarin raba wannan Shegiyar shak'uwar taku da waccan mayyar yarinyar amma shaƙuwar taku sai ma ƙara gaba take yi, ba ka jin maganata kwata_kwata Salman, ba ka bin abun da nake faɗa." Tsugunnawa ya yi cikin raunin murya ya ce. "Ki yi haƙuri Mami, ba na son in ga kina ɓata ranki a kaina ko akan Yaya, kin san fushinki masifa ne a gare mu, don Allah Mami ki yi haƙuri." "Idan ba ka son fushina da ɓacin raina ka daina shigewa waccan shegiyar yarinyar." "I'm sorry to say Mami, ba zan iya fita daga sabgar Yaya ba, ita ɗin wata aba ce mai matuƙar mahimmanci a cikin RAYUWATA, tana da matsayi mai girma a cikin zuciyata, bayan ke da Abbi ba ni da kamar ta a cikin faɗin duniyar nan, dan Allah Mami ki daina yunƙurin raba mu, domin ɗayanmu ba zai iya rayuwa ba idan babu ɗaya." "Ko kashin awaki ne ku wallahi sai na raba ku Salman, kai ɗa ne tsaftatacce mai ƴanci kamar ko wanne ɗa, ita kuma SHEGIYA ce Ƴar Zina, wadda ta fito ta haramtacciyar hanya! Dan haka kar ka ƙara haɗa kanka da ita, idan kuma......." Buɗo Kofar parlour'n da aka yi aka shigo ya katse wa Na'ima maganarta, a tare suka juya suka kalli mai shigowar cikin tsananin mamaki da kaɗuwa. LITTAFIN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE.[10/1, 2:40 PM] Abk: LITTAFIN DARE DA DUHU NA KUƊI NE, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Da sauri Abra ta ɗauke idanunta saboda kwarjinin da mutum ya yi mata, amma har yanzu jikinta rawa yake na rashin sabo da kallon da jama'ar wajan suke mata. A hankali ta yi ƙasa da kanta tana mai jan idanunta ta rufe ruf sai ƙanƙame hannunta take. Taɓe baki ya yi yana mai zame idanunsa daga kallon tsautsayin da ya yi mata, cikin takun nan nasa na natsuwa da kamala fuska ɗaure yaci gaba da tafiya yana mai gyara zaman bluetooth ɗin kunansa a hankali kuma a fili ya ce. "I am not a child, Abba, I will take care of myself" A sanyaye yake maganar yana shafa sumar dake kwance a kansa, a nutse yake tafiya yana waya da mahaifinsa. Abba dake sauraran S.p Adnan Aliyu Matawalle ya ja numfashi ya ce. "Me yasa ba zan damu da kai ba Son? Ina tsoron matsala ta haɗaka da wani, You are stubborn and hard-hearted. Baka son cin abinci ina kasan yanayin Olser ɗin ka idan ya tashi?" Adnan ya marairaice fuska tamkar yana gaban Abba cikin ƙosawa da kallon da ƴan matan wajan ke masa ya ce. "I am thirty-two years old, but you still look like a child to me, Abba. Don mind me nasan yadda zan kula da kai na" Da sauri ta cikin wayar Abba ya ce. "Baka sani ba Adnan, idan ka sani ba zaka dinga hora kanka da yunwa ba, sai wife ta takura ka kake cin abinci, naso ace tare da Usman kuka tafi, da iya takurar Usman dole ta sanya ka kaci abinci ko da something liquid ne haka" Adnan dai ya yi shiru yana sauraran faɗan da Abba yake masa, sai da ya gaji da faɗa ya ce. "Ina da meeting bye take care of yourself ok" "I'll. Love You Father, please ka sha maganinka ok" ya faɗi hakan yana yatsuna fuska tare da rufe idanunsa ya ɗan buɗe a lokaci guda, a hankali ya fara ƙarewa cikin B.U.K ɗin kallo yana ƙara tuna rayuwar makarantar da ya yi a ciki. Ba tare daya lura da cewa ya ƙaraso inda Abra Khamal Khamis take zaune ba, sai ji ya yi ta miƙe da sauri har tana yin tuntuɓe da ƙafarsa, ko ta kanta bai bi ba, ya nemi waje ya zaune tare da sauke ajjiyar zuciya mai ɗan ƙarfi wacce take nuni da zallar gajiya da ya yi. A karo na biyu ya ƙara rufe idanunsa yana sauke numfashi, jin mutum kusa da shi ya sanya ya buɗe ido da sauri. With so much surprised yake bin mutumin da ya zaune kusa dashi da kallo, kafin kace me ɗalibai sun rufe Sp Adnan Aliyu Matawalle, kasancewar ya riƙe muƙamin _“The student president of the university”_ a nan Cikin B.U.K. Ya sanya da yawan ɗaliban sun san shi, suna da labarin komai ance ba'a taɓa student mai farin jinin Sp Adnan Aliyu Matawalle ba. Kallonsu kawai yake But he could not hide his surprise. Fayyad ya saki dry yana ware hannunsa yace "Surprised, Surprised Our ex- president" murmushi ba ɗabi'ar Adnan bace hakan yasa da idanu kawai yake binsu, Fayyad wanda ya kasance Class mate ɗin Adnan tun daga secondary har zuwa University da sukai Department ɗaya ya ce "yau dai ka ziyarci makarantar mu bayan wasu shekaru, You are Welcome." Sauran Students suka ce "We appreciate your visit, Sir" kai kawai ya jinjina musu Fayyad ya ce musu "You can go, yana godiya" gaba ɗaya suka bar wajan. Fayyad ya miƙe tsaye yana faɗin "mu ƙarasa office ko?" Nan ma kai Adnan ya jinjina yana ƙoƙarin Miƙewa daga kan kujerar da yake idanunsa ya sauka akan wani I.d card fari tas dashi. A nutse ya miƙa hannunsa ya ɗauki I.d card ɗin a hankali ya duba sunan da yake jiki. ABRA KHAMAL KHAMIS. Shine Abin da idanunsa suka fara gani a jikin I.d card ɗin. Gently ya fara bin Information ɗin dake cikin I.d card ɗin kamar haka: Name: Abra Khamal Khamis Reg No: .................. Program me: Mass communication Department: Department of Mass communication Phone number: ............. Sai ƙyakkyawan photonta dake maƙale jiki, black ɗin Abaya ce jikinta tayi rolling kanta da veil, dimples ɗinta ya loma dalilin Murmushin da ta yi. Cikin wasu ɗakiƙo ya ƙare wa photon kallo kafin ya taɓe baki daidai nan Fayyad ya matso inda yake yana faɗin. "What are you waiting for?" Girgiza kai Adnan ya yi a karo na farko cikin sautin Muryarsa ya ce "Nothing" "Ok.... Shall we?" Fayyad ya faɗa yana nunawa Adnan hanyar zuwa office ɗinsa, kasancewar a cikin University ɗin yake koyarwa. Kai tsaye suka nufi cikin office ɗin. Tafiya kawai take kanta a ƙasa, gaba ɗaya hankalinta baya jikinta, jinta take wata uncomfortable ta saba duk inda zata suna tafiya tare da Salman, a yanzu kuma ita kaɗai ce gani take kamar mutumin ɗazo ne zai biyota, tana tafe kuma tana cin karo da Old Students na University ɗin, sai faɗin Sir S.p Adnan Aliyu Matawalle suke suna nufar hanyar data baro. Ita dai ba wanda ta kula balle ta san meke faruwa, ji tayi yunwar ma ya tsaya mata. Caraf taji an riƙe mata hannu, a gigice ta ɗaga idanunta wanda ta gani kuma yasa ta saki ajjiyar zuciya tana kwaɓe fuska tare da ƙanƙame hannunsa daya riƙe ta da shi. Salman ya ware idanunsa akan Abra yace. "Ya na ganki a hargitse?" Ta girgiza masa kai, nan da nan mood ɗinsa ya sauya a tunaninsa wani ya biyota, bai ce mata komai ba sai manyan idanunsa daya kafesa da ita. "Let's go Faris" Ta faɗa kamar zatai kuka tana mai sake damƙe hannunsa, Salman ya haɗe fuska a kaushashe ya ce "Ban gane mu tafi ba, you told me you are hungry" "yanzu kuma na ƙoshi, mu tafi gida tunda mun gama abinda ya kawo mu" ta faɗa tun kafin Salman ya sauke numfashi da ga maganar da ya yi. Kasa ce mata komai ya yi, ya daɗe da sanin halin ya yar tasa, a hankali ya kama hannunta tare da nufar ƙasan wata Bishiya da ita, zaunar da ita ya yi saman Kujera a hankali Shima ya zauna cikin rarrashi ya ce. "Kina jin yunwa sosai Yaya, ki fara cin abincin sai mu yafi ba zan barinki da yunwa har muje gida ba, kuma ba lallai Mami tayi abinci ba" Abra ta haɗe rai, tama ƙi yarda ta kallesa baki ɗaya, ta lura akan buƙatar ta Salman baya jin mgnarta sam. "Angel" tai masa banza, tare da ɗauke kanta gefe guda a hankali ta shiga wasa da yatsun hannunta. Salman ya zame ƙasan qwiwoyinsa hannunsa ya ɗora a cinyar Abra, yana leƙa fuskarta dake ƙasa, haɗa idanu sukai tai saurin rufe nata tare da ɗauke kai zuwa gefe. Tashi zaune ya yi tare da zama gefen ta, takeaway ɗin daya kawo mata ya buɗe, wainar shinkafa ce mai zafi, da miyar agoshi ta sha nama sai ƙamshi take, bayan ya buɗe takeaway ɗin ya ɗauki ruwa faro tare da wanke hannunsa. Muryarsa bata fita sosai yace "Yaya" tai masa banza ya ƙara cewa "Angel" still taƙi kulasa, gyara zama ya yi yana tura hular kansa baya saboda damunsa da tayi, kamar da ga sama taji yace "Abra...!!!" Da sauri ta juya baki buɗe saboda Mmkin jin sunanta a bakin Salman wanda bata taɓa ji ba, suna haɗa idanu ya ɗauke nasa idon, shima fuska a haɗe. Ganin sauyin nasa yasa ta marairaice fuska tace "Faris muje gida" bai bari ta sake magana ya kama Fuskarta da tafukan hannunsa ya tallafo haɓatar sosai, baki ta buɗe Zatai magana ya yi saurin ɗora yatsarsa a bakinta ya ce "Shhhhhh" shiru ta yi wanda ba tai niyya ba, a karo na farko wani kwarjinin Salman ya ziyarci ƙwayar idanunta, ƙasa tayi da ganinta. "Hahhhh" Salman ya faɗa a sanyaye, ba tare da ta yi musu ba, ta buɗe cute small mouth ɗin nata wanda yake ɗauke da red ɗin laɓɓan masu taushi a hankali ya saka mata naman daya ɗakko har lokacin yana riƙe da Fuskarta yana ƙare mata kallo, ita kuma idanunta a ƙasa. Tana cinye naman ya fara bata wainar shinkafar bata wani ci da yawa ba, ta girgiza masa kai ya ce "Sai kin cinye fa" Kamar zatai kuka tace "wallahi na ƙoshi, ka cinye sauran" shima ya ce "Ni ai bance ina jin yunwa ba, karatu zaki fara dole kici abinci ƴar nan" yana faɗin hakan ya ƙara tura mata wainar a baki. Da ƙyar ta haɗiye tana zare Idanunta tace "Zanyi amai fa" yana haɗe fuska ya ce "ba wani amai yaya, na fahimci sai nayi maki da gaske ba ruwana da girmata da kikai" Ba zato yaji ta fashe masa da kuka sosai, da gudu kuma ta miƙe tsaye tana kakarin amai amma sam yaƙi zuba, kakari take sosai jikinta na rawa, da sauri Salman ya kama hannunta ganin zata faɗi yayi saurin yi mata side hug ruwa ya bata tasha yana bubbuga bayanta "Sorry Angel, I'm so sorry" ƙin kulasa tayi sai shassheƙar kuka take, ganin da taƙi kulasa duk ya rikice daidai nan ƙawarta Khairy ta ƙaraso itama an bata admission a B.u.k. Cikin rashin damuwa da yadda ta gansu tace "Wow yau nayi Sa'ar zuwa B.u.k Wlh" Shiru Abra ta yi Salman ya ware idanunsa yana faɗin "Sbd kin samu course ɗin da kikeso?" Ta girgiza masa kai tace "Is not like that Salman, I have never seen a man so beautiful as him" daga Abra har Salman ba wanda yace mata komai, Salman hankalinsa na kan Abra ita kuma ta haɗe fuska tana kallon Wani wajan. Khairy baki na ƙaiƙayi ta kalli Abra tace "Wai ashe a nan shcl ɗin ya yi karatu, ya riƙe muƙamin shugaban ɗalibai, ba kiga yadda aka rufesa ba kowa na son ganinsa, kai Ubangiji ya yi halitta a nan" Abra ta taɓe baki tace "who asked you? We have nothing to worry about... let's go Faris" dry khairy ta saka tana tafa hannayenta cikin farin ciki tace. "Ba lallai ki yarda da kyansa ba, tunda baki gansa ba, ni da har kallon sexy eyes ɗinsa na yi, gashi wani babba mai kyan sura, irin namijin da nake so mai baƙar fata" Haka kurum Salman yaji baya son jin maganar, duk da bai san Who is she talking about ba, amma yaji ransa ya ɓaci. Abra ta kalli Khairy tace "kuma sai ya zama dole na sani Ummulkhairy?" Khairy na ƙoƙarin magana Idanunta ya sauka akan Sp Adnan shi da Fayyad suna tahowa, jikinta na rawa tace "Look Abra, wlh shine wanda nake maki magana" daga Abra har Salman babu wanda ya juya balle suga wanda Khairy ke magana akansa. Fayyad ya yi Murmushi yana dokan kafaɗar Adnan yace "You're kidding, it's just your pride that prevents you from finding a wife" Ya ƙare maganar yana ƙara kaiwa Adnan doka, kafin ya ɗora da faɗin. "Aure duniya ne, ma'aurata sune kaɗai zasu fahimci abinda nake cewa, Let's keep the joke aside, you have education, money, health, you are handsome Adnan, babu macan da za tace bata sonka I'm still wondering akan abinda ya hanaka aure, Shawara nake baka tun kafin lokaci ya ƙure maka wallahi rayuwa bata da tabbas gwara ka Ajjiye masu yi maka addu'a kafin lokaci tsofa ya riske ka" A karo na farko Sp Adnan yai wani irin Murmushi daya sanya fararen haƙoransa bayyana, wanda shi kansa Fayyad ya yi mamakin Murmushin nasa. A hankali yace. "Thank you Alhaji Aliyu Matawalle" Fayyad ya ware idanu ya ce "it's just a suggestion. Ba lallai ka amince ba" Su Adnan na zuwa daidai inda su Abra suke ya lumshe idanunsa kana ya buɗe ya ce "I don't believe in true love, mata sai a hankali there is no Promise in their hearts" Da sauri Abra ta matsa kusa da Khairy ganin Adnan na ƙoƙarin take mata ƙafa, amma yana zuwa inda take ya janye ƙafarsa zuwa wani gefe ko inda suke bai kalla ba, yana ji Khairy na cewa "Bye sir" amma ko amsawa bai ba. Salman ya nufi motarsu ganin Drivern gidansu, Abra tabi bayansa. Kusan lokacin ɗaya dasu da Adnan suka bar cikin B.u.k. Washegari ya kama Weekend. Abra na tsaye a kicthen sanye cikin wata fitted gown ɗin green ɗin lace sai Stones masu ƙyalli, tayi simple ɗauri gashinta har baya, tattara carrot ɗin data yanka tayi, tare da green, yellow, and red pepper ta Ajjiye gefe guda. Green beans ta ɗauka wanda ta ɗan dafa, bayan ta kammala komai ta ɗauki shinkafar da tayi pi bowling ta juye ta zuwa cikin wata pot ɗin, another pot tai using wajan zuba mai mara yawa, ta zuba kayan miya, kana ta zuba su magi da spices in few minutes ta haɗa fried rice with chicken kabab. Tana gamawa ta haɗa salad wanda tai using lemon kaɗan a ciki sai pineapple juice. Salman dake shigowa kitchen ɗin yai saurin tsayawa a bakin ƙofa yana jan numfashi tare da rufe idanunsa, na ƙamshin daya daki hancinsa. Idanunsa ya ware a kanta tun daga kan fararen yatsun ƙafarta ya fara Kallonta, zuwa hips ɗinta da gadon bayanta, a hankali ya maida idanunsa kan baƙin dogon gashinta. Cikin rashin sani ya furta. "Rest of my life.... Angel na" Abra ta juya da sauri suka haɗa idanu ya kashe mata ido ɗaya tare da ɗaga mata gira. "like you said something?" Ta tambayesa bayan ta gama wanke hannunta a jikin sink. shiru ya yi mata sai idanu da yake binta dashi, ganin ta ɗauke kanta zuwa ɗaukan warmers ɗin data zuba abinci ciki a nutse ya ce. "Sweetheart" Juyawa ta kuma yi suka haɗa idanu, ta wani haɗe fuska tace "Wai me kake cewa ne,It's like calling someone's name?" Hannunsa da yake saƙale a ƙirjinsa ya zame tare da zuba su cikin Aljihu, a hankali ya ce "wane suna zan kira wanda ya shige Angel" tana miƙa masa warmers ɗaya tace "ba haka naji ba, kadai ce wani abu nada ban" Murmushi kawai ya yi mata yana girgiza kansa, shi kansa bai san lokacin da yace hakan ba. "Kada ki manta kina using Hearing aid ne Angel" ta kallesa tace "And then?" Ya ware shoulder irin Nothing ɗin nan. A tare suka jera kayan abincin akan dining room suna kammalawa Salman ya zauna yana faɗin "zuba min abincin" hannu tasa ta dungure masa kai tana faɗin "Food, food, food. stop eating too much" Salmanun-faris girgiza kai ya yi yana tsiyaya Juice a cup a hankali yake sipping Juice ɗin kafin ya ce "gwara na zama ƙatoto yadda za kifi yadda da abinda zan zo maki da shi" Abra tai shiru can kuma tace "like how?" Yana ɗaukan spoon ya ce "With time" Kafin wani ya ƙara magana a cikinsu Mami ta ƙaraso wajan hannunta riƙe da waya cikin wani dakakken lace idanunta akan Abra tace. "Ok zan turo ta yanzu, kada ki damu kawai ki Ajjiye min aini nace ina so kuma wannan haɗin ya yi" jim tayi sai kuma tace "Ni bani da damuwa, kuma nasan Man zai amince so kada ki damu kici gaba da tsara komai" shiru ta sakeyi alamar tana sauraran mai maganar daga cikin wayar tace "Shi ke nan, ki ɗan jira yanzu ne in sha Allah" tana faɗin hakan tayi hanging up na kiran Idanunta still akan Abra tace. "Daughter" Ba Abra ba hatta Salman sai da ya ɗaga idanunsa ya kalli Mami, abin yazo musu unexpected ya zama wani extraordinary a gare su, ko sunan Abra da wahala aji Mami ta faɗa amma yau ita take kiran Abra da Daughter? Tsananin murna yasa Abra har wani hawaye Idanunta ya tara muryarta na rawa tace "Na...n... na'am Mami" Mami tai Murmushi ta kama Hannun Abra tace "Be patient my dear, zan aikeki gidan Hajja Amina yanzu kinji" Abra ta ɗaga kai da sauri tace "Ok Mami bari na shirya" da sauri Salman ya miƙe tsaye. "Mami aike kuma? Yaya zaki aika bayan Abbi yace kada ta dinga fita, kuma ba gani ba ki faɗa min aiken yanzu naje na amsu maki" Mami tace "ai na ganka ko ka taɓa ji ance ni makauniya ce, bana kula Abra ace bana sonta idan na nemi kusanci da ita kuma a fara wani zance, kada ka sake ina magana kana saka min baki Salman it will be the last time da zakai min haka" Salman ya buɗe baki zai magana Abra ta girgiza masa kai tace "No Faris,stop arguing with your mother. Ka bari yanzu zanje na dawo" idan ran Salman ya yi dubu to ya ɓaci idanuna tuni ya yi jajur sbd saɓar abinda yake ci masa zuciya, a fusace kuma ya nufi waje zai fita ganin haka yasa Mami faɗin "kada ka kuskura kabar gidan nan, tunda ni Matsayin Shasha ka ɗauke ni" juyawa yayi daga inda yake zuwa bedroom ɗin sa, ganin hakan yasa Mami kallon Abra tace "Kaya zaki amsu min wajan Hajja Amina, kada ki sake ki dawo ba kayan saura ki tsaya a hanya" "Yanzu zan dawo, bari na ɗakko mayafina driver ya kaini" "A'a ba wani driver, ka kuɗi zan baki ki hau napep ok?" Ta ɗaga kanta 1k ta miƙa kuɗin napep tana bata ta nufi dining room. Abra kuma ta juya zuwa bedroom ɗin ta. Tana tsaye gaban mirror zata ɗauki turare ta fesa a jikinta ya yi saurin riƙe hannunta mai ɗauke da turaren, kallonsa tayi sai da gabanta ya faɗi ganin irin kallon da yake binta da shi. Wardrobe ɗinta ya buɗe ya ɗauki wani ƙaton hijab har ƙasa bakinta na rawa tace "Ni ba zan saka hijab ba gsky" idanuna cikin nata ya ce "Ni kuma nace sai kin saka" murguɗa masa baki tayi tace "Ni ba zan saka ba, kana wani abu kamar kaine yanae, shekara uku na baka yaro sai son girma da manyan can Masifa" Salman na warware hijab ɗin ya ce " say whatever you want to say, but kada ki sake ce min yaro age is just a number ba'a goshi ake rubuta su ba" "Idan na kuma faɗa me zakai min? Kwana biyun nan naga ka fara raina ki ko? Sbd kana kallonka ƙato babu mai cewa nice babba shine kake son faɗa min abinda kayi niyya" bakinta dake ta motsawa yana zuba masifa yake bi da kallo sai da ta kama faɗan ta ce "kuma sai ka faɗa min abinda zakai min idan na sake faɗa" girgiza kai kawai ya yi ba zato taji gaba ɗaya ya ɗaga ta cak ya dire ta a gabansa tare da kama ƙugunta ya saka mata mayafin. Yana gamawa kamar sai saketa sai ya ɗora bakinsa a saitin kunnanta ta cikin hijab ɗin ya ce. "Yaa Subuhanallah! جعلنا الله معًا إلى الأبد" Wato “Ubangiji ya Sanya mu kasance tare har abada” Abra hankalinta baya jikinta murna take yau Mami ta aiketa dan haka bata tsaya tantance maganganun na Salman ba tayi waje sanye da ƙaton hijab. Abra na barin gidan motocin Major Khamal Khamis suna shigowa, wani soja ya buɗe masa ƙofa ya Fito dake gaba ma'aikatan gidan sojoji ne. Cikin nutsuwa Abbi ke tafiya zuwa gidan yana shiga Mami ta miƙe tsaye, da ɗan sassarfa ta nufi wajan Abbi tare da rungomesa tana faɗin "Wlcm Back Yallaɓai na" Murmushi ya yi yace "Thank you Madam" Jin shiru yasa yace "Ina Daughter,ina Salman?" Tace "Salman na nan baya jin daɗi, Abra na aiketa tun ɗazo naji shiru amma nasan tana hanya" Shiru ya yi yana son fahimtar zan can nata sai kuma ya ce "Ok, lemme take a shower" bayansu tafi har zuwa sashinsa ta haɗa masa ruwan wanka. Bayan ya yi wanka yana cikin cin Abinci yaga ta zabga tagumi yace "Meke faruwa Madam?" Ta girgiza kai ya kama hannunta ya ce "please" ajjiyar zuciya ta sauke ta ce "Ko Abinci yau Abra bata samu yi maka ba, jiya da yau idan na aiketa sai ta shafe wasu lokuta bata dawo ba" Ajjiye spoon ɗin hannunsa ya yi cikin damuwa ya ce "ita Abra? To ina take tsayawa?" "I have no idea. Bari na kira Hajja Amina" wayarta ta ɗauka ta kira Hajja Amina tana ɗauka tace "Hajja Amina me Abra take har yanzu shiru?" Hajja Amina tai salati da ga cikin wayar kasancewar a Speaker Mami ta saka tace "Wacce Abra kuma ni Amina, yarinyar da ko minti biyar ba tayi ba ta amshi kayan ta fita tace akwai inda zata daga nan gidan" kashe wayar Mami tayi ta ce "To ina yarinyar nan tayi?" Kasa cewa komai Abbi ya yi sai miƙewa kawai da yai tare da nufar sashinsa. Ana ƙwala kiran Sallar Magrib Abra na shigowa cikin Main Parlour sai da gabanta ya faɗi ganin Abbi tsaye fuskarsa babu walwala wani irin kallo yake binta da shi, musamman da yaga leder shopping a hannunta. Bakinta na rawa tace "Sannu da dawowa Ab..." Tau!!!!! Abbi ya ɗauke Abra da mari wanda ya sanya tayi baya zata faɗi cikin sauri Salman ya tareta ta faɗa jikinsa, Wani marin Abbi ya ƙara saukewa Abra daya sanya ta saki wata gigitacciyar ƙara tare da saka hannu gaba ɗaya ta ƙanƙame Salman. Wani irin kukan Abra ta fashe dashi bakinta sunan Faris yake faɗa akan ya taimaketa daga dokan Abbi. "Wato har kinyi girman da za'a aikeki ki tsaya yin shopping da wani? Yaushe kika zama haka Abra? Ina tarbiyyar da nayi maki kuma yanzu yanzu ki haɗiye kukan nan ki faɗa min Shegen daya kaiki shopping Wlh yau a ɗaure zai kwana, ba zai taɓa yiyuwa ina tufka wani yana warware min ita ba, ba zai taɓa yiyuwa ba" bakinta na rawa jikinta na ɓari tace "Abbi kayi haƙuri, wlh babu wanda nabi ɗan gidan...." "Shut up" Mami ta daka mata tsawa tare da faɗin "tun ɗazo na kira Hajja Amina tace ko minti biyar baki ba a gidanta, shine yanzu zaki shirya ƙarya domin kare kai fita a nan kiban waje" da gudu ta saki Salman ta nufi bedroom ɗin ta, Salman kallon Mami kawai yake domin har ransa bai yarda da wannan zan can ba akwai abinda yake faruwa. Juyawa ya yi zuwa masjid ɗin domin yin sallar Magrib. Kuka kawai Abra take lallashin duniya Salman ya yi amma taƙi yin shiru, da ƙyar ya lallaɓata tai sallah ya faki Idanunta ya saka mata maganin bacci cikin ruwa tana sha bacci ya yi gaba da ita. Da Subhi bayan ta tashi da ƙyar saboda nauyin da Idanunta ya yi mata, bayan tai wanka tare da yin tana zaune saman sallaya aka turo ƙofar ɗakin tare da shigowa. Ƙamshin turarensa da taji yasa bata ɗago kanta ba, haka kurum ta tashi da ƙuncin zuciya. Zama Salman ya yi a gefen inda take zaune Murya a ƙasan maƙoshi yace. "Sabahul khair Angel" Ba tare data kallesa ba Idanunta akan Azkar ɗin da take tace "Ka tashi lafiya?" Bai amsata ba domin shi kaɗan yasan yadda yake bacci kullum shiru ne ya biyo baya kafin Salman ya kau da tunanin zuciyarsa ya ce. "Wane ya yi maki shopping?" Sai a wannan lokacin ta ɗago kanta suka haɗa idanu ita kanta tai Mmkin yadda fuskar Salmam tai jajur idanunsa ya kumbura Sbd rashin bacci. "Ina tambayarki kin tsaya kallo na kamar baki sanni ba?" Juyowa tayi baki ɗaya tare da kallonsa cikin sakin fuska tace "Maybe bana ɗaya daga cikin mutanan da za su yi farin ciki a duniya, ƙilan rabona sai bayan bana numfashi Salman" tana faɗin hakan ta miƙe tsaye hannunta riƙe da Alkur'ani bayan ta Ajjiye ta juya zata fita zuwa kitchen. da sauri Salman ya rufe ƙofar tare da murɗa key a jiki. Hannayensa ya harɗe a ƙirji idanunsa akan Abra da tayi tsaye tana binsa da kallon Mmki. "If I am alive, you must be happy" a hankali ya matsa inda take idanunsa cikin nata ya ce "Ki faɗa min wanda ya yi maki shopping da kuma yadda kika daɗe a waje" banza tayi masa. "Ki faɗa min" a hassale tace "Salman ka barni dame zanji ne pls? Ka barshi a wani nabi shi ke nan....," gigitacciyar tsawar da Salman ya daka mata ya sanya tayi sauri rufe bakinta jikinta ya ɗauki rawa da ɓari, shi ne karo na farko da ya ɗaga mata Murya harda tsawa bata san lokacin data fashe da kuka ba tana durƙoshewa a wajan. Ran Salman a ɓace gaba ɗaya ta gagara fahimtarsa, idan har bai Ajjiye girmansa da tayi ba, to ba zai iya kulawa da ita ba kamar yadda ya yi zuciyarsa Al'ƙawari, durƙosawa yyi tare da ɗago ta tsaye muryarsa babu wasa ya ce. "You will not cry for me. Amsa zaki bani Abra amsa nake buƙata" muryarta na rawa tace "Bayan naje gidan Hajja Amina muka gaisa tai shigewarta ɗaki a nan naita zama, sai dab da magrib ta saka ɗan ta ya ɗauke ni wai shine zai ban saƙon, ganin Aiken Mami ne ban damu ba, shine ya kaini Sadaraki store yai shopping tare da bani wai shine aiken...," Kukan da yaci ƙarfinta ne ya sanya ta kasa ci gaba da magana wani irin kuka take wanda ta daɗe ba tayi kamarsa ba. Ganin yadda take kuka har tana shiɗewa kamar numfashinta zai fita ya sanya a fusace Salman ya jawota jikinsa tare da rungometa Tsam-tsam a jikinsa, zuciyarsa na wani irin bugawa kamar zata faso ƙirjinsa ta fito idanunsa ya yi wani masifar jaa kamar gauta jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa saman goshinsa numfashi kawai yake fitarwa. "You shouted at me,after I am innocent" ta ƙare maganar tana sakin wani irin kuka tana ƙara ƙankame jikin Salman, domin a wajansa kawai take samun sauƙi. Faɗa masa ne kawai ba tayi amma tuntuni ta yarda cewa shine ragamar rayuwarta da babu shi ta tuni Zuciyarta ta buga. Muryarsa bata fita sosai ya ce "I'm sorry Yaya" yana faɗin hakan ya zareta daga jikinsa kamar walƙiya haka ya ɓace daga ɗakin yana zuwa bedroom ɗin sa, Wayarsa ya ɗauka tare da kiran number Ammi bayan sun gaisa ya faɗa mata dake faruwa. Granny dake gefe hankali tashe tace. "Huhuhu idan ban kaɗa Na'ima gidansu ba yau to wlh kuce ƴar banza ce ni, Ubangiji ya yi gutsi gutsi da Zuciyar Na'ima. Zan aurawa Kamalu Babura sai naga ƙaryar iskanci" tana faɗin hakan ta miƙe tsaye yana ɗaukan mayafi tace "A'isha kike kowa masa kira salamamman drivern can ya kaini gidan Kamalu a yau shima shi ya gane cewa ni ba tsohuwar banza bace duk yadda ka ke da kiyaye harshenka sai an saka kayi saɓon Ubangiji" sai kuma ta fashe da kuka tace "Da ƙyar Na'ima taga Ubangiji da ƙyar ne ta kansa". Tahir guest palace. Room 36. Yana kwance sanye da red ɗin Armless wacce ta bayyanar da faffaɗan ƙirjinsa. A hankali ya mirgina tare da yin rufda ciki yana ɗan lumshe idanunsa. Ta cikin system ɗin dake gabansa Muryar Abba ta fito yace "Na faɗa cewa zani England,Follow the flight today and come back to Kaduna" Sp Adnan ya ware idanunsa dake cike da bacci a hankali ya Kalli fuskarsa mahaifin nasa ta cikin vedio call ɗin da suke "Abba ba yau zan dawo ba, kuma akwai mota tare dani" cike da damuwa Abba ya ce "How many times do I have to tell you that I don't like long car journeys" Murmushi Adnan ya yi cike da so da ƙaunar mahaifin nasa ya ce "Abinda Ubangiji ya ƙaddara zai samu bawa dole ya samesa ko a jirgi ne, just pray for me" "Ok I'll, When will you come back?" Adnan na hargitsa sumar kansa idanunsa rufe ya ce "Ni ọsẹ kan tabi meji" Murmushi Abba ya saki yana kallon Hajiya Mama dake gefensa ya ce "Yau ɗanki ya tuna da yaran mahaifiyarsa" Hajiya Mama tayi dry tace "kyan ɗana daman ya gado mahaifiyarsa" Abba yana kallon Adnan ya ce "Idan ɗan ya kasance mace ko? Ɗa namiji kam Ubansa yake kwaikwayo" Murmushi kawai Adnan yake wa iyayen nasa "Me zaka zauna yi a Kano har bako guda?" Miƙewa zaune Sp ya yi cikin kwaɓe fuska ya ce " "An investigation brought me to Kano, who I suspect is in the University" Abba ya ce "Ikon Allah. To Allah ya taimaka ya yi maka jagora please My son is rage zafin zuciya" da idanu kawai Sp yabi Abba "yanzu yaya za'ai ka kama criminal ɗin?" Adnan ya ɗan yatsuna fuska ya ce "I have a plan Abba.. bye take care of yourself" yana faɗin hakan ya kashe system ɗin tare da Miƙewa ya nufi bathroom, wanka ya yi ya shirya cikin wasu ƙana nan kaya Sleeveless tank top da tracksuit trousers ya ɗora white p.cap a saman sumar kansa, sai Ƙamshin Pur oud yake. Wayarsa ce ta fara ringing ganin sunan Fayyad ya Sanya bai ɗaga ba, hannunsa ya miƙa ya ɗauki I.d card ɗin dake gefen gado, ƙyakkyawar Fuskarta yabi da kallo kafin a hankali yaja idanunsa ya rufe yana sauke numfashi. I.d card ɗin ya saka cikin Aljihu kana ya fita daga Room ɗin cikin sassarfa ya fara sauka daga kan strains ɗin 3 floor. Ganin zai ɓatawa kansa lokacin ya tsaya ya shiga elevator tare da danna 1floor. Yana sauka reception Wayarsa ya fara ƙara ganin sunan Abba yasa ya tsaya tare da ɗaga kiran. "Son ka kula da kanka, ka rage zafin zuciya. Shine Abinda zaka faɗa ko Abba na riga na haddace fa" ta cikin wayar Abba ya yi Murmushi ya ce "ba zaka gane ba, Allah ya yi maka albarka" Adnan ya ce "Amin, Bye." Motar gabansa ya buɗe tare da shiga yana ji Fayyad ya daki kafaɗarsa ya ce. "Ban taɓa sanin baƙar fata duniya bace sai a kanka Adnan, kaga yadda kayi kyau" Adnan dai bai ce komai ba. "Jiya ka kirani kana son magana dani" Adnan ya jinjina kansa yana rufe idanu, Fayyad ya ce "Ok bari muje gidana muyi magana, da ga nan sai ku gaisa da Madam" Adnan dai bai ce komai ba, Fayyad ya ƙarawa motarsa wuta babu jimawa suka kawo cikin estate ɗin Motar Fayyad na shigowa ciki Motar Granny da driver ya kawota na danno kai cikin estate da sauri Fayyad ya daka burki ganin motar dake bayansu ta tawo da sauri ta nufi gidan dake kusa da nasa. Adnan ya buɗe idanu da sauri yana jan tsaki. Fayyad ya ce "Wannan driven mahaukaci ne" Adnan ya ƙara jan tsaki ya ce "Ƴan Nigeria ke nan" kafin Fayyad ya yi Magana sunga wata tsohuwa ta tsaya gaban motarsa ta fara Masifa. "Wani gantallan ne wanda bai san darajar rai ba ke neman salwantar da tawa rayuwar? Kasan nawa ɗana ya sai motar nan kowa? Mutane suyi ta abu daka kamar marasa wadataccen ilimi. Nifa daidai nake da ko wanne ɗan kwalta Alkur'an sai na kwaɓe mu daku kawai kowa ya yi ta kansa" Salman da ya fito daga cikin gidansu ya yi saurin kama hannun Granny sukai cikin gidan. Adnan dai idanunsa a ƙasa Fayyad babu abinda yake banda dry yana buga cinya. Adnan ya ɗaga idanunsa ya ce "Old version ce fa motar masifaffiyar Tsohuwa" kamar ya faɗa a kunan Granny sai gani sukai ta fito daga cikin gidan a guje ta ce "Kaga masifa akanka wallahi li'ilafi qurash" tana faɗin hakan tai cikin gidan tana Masifa son ranta. Shi kansa Sp sai da abin bashi Murmushi kasancewar ba ɗabi'arsa bane sai kawai ya Girgiza kai. Fayyad ya Ƙarasa shigar da motarsa cikin gidan nasa gaba ɗaya suka nufi ciki. Tunda daga bakin ƙofa Granny ta gyara zaman ɗan kwalinta. Kai tsaye Granny ɗakin Na'ima ta nufa babu jimawa ta dawo hannunta riƙe da mayafi, cillawa Na'ima tayi ta koma ta ƙara ɗakko hand bag itama ta cillawa Na'ima. "Maza maza kama gabanki wlh Wlh yau koni ko ke, ke babu ruwana ni ba ƴar banza bace dole ki yi yaji yau" Abbi ya ce "Mene ya faru Granny?" Granny ta runste idanunta ta ce "Ni da Ubangiji na kawai muka san abinda ya faru, kuma a satin nan zanwa Kamalu aure. Idan ki kaga banwa Kamalu aure ba cikin satin nan kice ni ba haifaffiya bace cikin uwata".... LITTAFIN DARE DA DUHU NA KUƊI NE, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. [10/1, 2:40 PM] Abk: LITTAFIN DARE DA DUHU NA KUƊI NE, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750 DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750 MUNGODE. Cikin mamaki Khamal ya ce. "Subhanallahi! Granny wai me ya faru ne?" "Mene ma bai faru ba Kamalu? Wannan matar taka mai kama da bayi ba matar arziƙi ba ce, mugunta ce fal cikinta da kake ganin ta haka, munafuka mai fuska biyu." Granny ta a faɗi haka tana hararar Nai'ma. Salman dake tsaye ya juya tare da ficewa daga parlour'n, dan bai ɗauki maganganun Granny da mahimmanci ba, a soki burutsunta ya ɗau abun, dama fitar da ya yi gidan Aunty Iman zai je ya ɗauko Abra, tana can tun safe ta kai mata ziyara. Nai'ma da zuciyarta ke bugawa da ƙarfi ta dubi Granny tare da faɗin. "Haba Granny, wai me na yi miki kika tsane ni haka?" Kama baki ta yi ta ce. "Au ba ki san me kika yi ba? To ba za ki taɓa sani ba kuwa, tashi maza ki ƙara mai ki bar mini gidan jika, takardarki kuma na nan tafe zan kawo miki da kaina, as'as'as." "Wai dan Allah Granny mene haka? Ya zaki zo ki ɗaga mana hankali." "Abun da ya fi hankali ma zan daga muku, kai da ba ka gane mai ƙaunar ka saboda Allah, wannan matar da ka ji abun da ta aikata wallahi da tuni ka sallame ta kafin ma wani ya ji." "Me ta yi toh?" Khamal ya tambaya cikin ƙosawa da hargagin Granny. "Ban sani ba Ubana! Wato ƙarya nake yi kenan, tsofai-tsofai da ni amma kake ƙaryata ni Kamalu? akan wannan makirar matar taka?" Sai ta fashe da kuka tare da faɗin. "Da A'isha ce ai ba za ka ƙaryata ta ba, to wallahi yau sai matar nan ta bar gidan nan, idan kuma ka ƙi in saka direba ya kira mun Hamisu da A'isha in sanar musu na saka abu ka ƙi yi." Cikin sauri Khamal ya ce. "Ki yi haƙuri abun bai kai haka ba." Sannan ya kalli Nai'ma ya ce. "Ki ba ta haƙuri." Kafin ya gama rufe baki Granny ta ce. "Kamalu mahaukaciya ka mayar da ni ko me? Uban haƙuri za ta ba ni ba haƙuri ba, to ba zan haƙuran ba, wallahi in dai ƴar halak ce ni sai wannan abar ta bar gidan nan a yanzun nan, munafuka ta san ba ta da gaskiya ai, sai fiƙi_fiƙi take da ido." Marairaicewa Nai'ma ta yi ta ce. "Dan Allah Granny ki yi haƙuri, duk da ban san laifin da na aikata ba." Mitsss, ta ja dogon tsaki tare da ƙanƙance ido tana jefawa Nai'ma wani irin kallo ta cikin glass, ba tare da ta yi magana ba ta fice daga parlour'n fuu tana faɗin. "Ka nuna mini ban isa da kai ba, bari na saka a kira mini wanda ya isa da kai, shi ai bai isa ya ƙetarewa umarnina ba." "Oh My God, rigimar Granny ta yi yawa, mene fa'idar wannan abun da ta zo ta yi?" Hawayen munafurci Na'ima ta fara ta ce. "Ban san me na yiwa Kakarka ba Khamal ba ta so na, kullum zancenta za ta ƙaro maka Aure, ko kuma ta ce ka rabu da ni." Cikin rarrashi Khamal ya ce. "Halin Granny ne ba ki sani ba Wifey ko me? Rikicinta ne kawai ba wani abu ba, idan ya tashi kowa ma yi masa take babu wanda ta ƙyale." "Wannan ba rikici ba ne Khamal, tsana ce kawai." Daidai nan Granny ta dawo hannunta riƙe da wayar Driver ta miƙawa Khamal. Ba tare da ya karɓa ba ya ce. "Me zan yi da ita?" "Huhuhu, yau na ga jaraba, to wacce ta yi cikinka ta tsuguna ta haife ka ce take son magana da kai." Granny ta faɗi haka kamar za ta ki fa masa mari. Karɓar wayar ya yi ya kara a kunnensa. Kafin ya yi magana muryar Ammi ta doki kunnensa a kausashe da faɗin. "Khamal ka yi abin da Granny ta ce." "Amma Ammi..." "Ba na son jin komai, ka yi ko mene ne, daga baya ma yi magana." Jiki a sanyaye ya ce. "Shikenan." Tare da katse wayar. Kallon Nai'ma ya yi ya ce. "Ki je gidan, I will come tomorrow." Fashewa da kuka ta yi ta ce. "Yanzu Khamal yau ni kake kora daga gidanka? Ni Nai'ma uwar Ƴaƴanka kake cewa in bar maka gida?" "Babu yadda zan yi ne Nai'ma, umarnin mahaifiyata na bi, but don't worry, everything will be okay insha Allahu." Daga haka ya miƙe ya nufi part dinsa. "A tashi a tashi da Allah, gida ne tunda ba na Ubanki ba ne sai kin bar shi wallahi, kuma a cikin satin nan zan aurawa Kamalu zankaɗeɗiyar budurwa, kuma ta cikin gida ce ba bare ba, bari uban nasa ya dawo." A zuciye Nai'ma ta goge hawayen fuskarta tare da miƙewa tsaye ta nufi ɗakinta kamar za ta tashi sama. Tafa hannuwa Granny ta yi ta ce. "Au da bangaje ni za ki yi? To Uwarki kika yi niyyar bangajewa ba ni ba, kuma gidan jikana yau dole a bar shi." Guri ta samu ta zauna ta kunto goro dake ɗaure a jikin zaninta ta basga tana karkaɗa ƙafa, idanunta akan ɗakin Na'ima." Sai da Granny ta ga fitar Nai'ma daga gidan sannan ta tafi, zuciyarta fess yau ta kawo ƙarshen iskancin Na'ima. Fayyad na gaba Adnan yana bin shi a baya suka shiga parlour'n gidan, wata farar matashiyar matar dake zaune akan kujera ta amsa musu sallamar da suka yi cikin fara'a. "Wow Masha Allah, yau ga Sp Adnan a gidana, kullum ana mini hirar ka, yau ma tun safe ake maimaita mini zaka zo, welcome." Ta faɗi haka tana miƙewa tsaye. Murmurshi Adnan ya yi bai ce komai ba, gurin zama Fayyad ya nuna masa ya zauna. A hankali ya ce. "Yana yi miki gulmata kenan Maman Boy?" Still tana murmurshi ta ce. "Sosai ma, kai dai a yi shiru kawai." Fayyad ya zauna a gefensa ya ce. "Ai bana gulamar tuzurai sai ta Ma'aurata." Ko kallon shi Adnan bai yi ba. Dariya Maman Boy ta yi ta haye upstairs. Tare suka dawo da wata budurwar yarinya, wadda da alama K'anwarta ce saboda kamar da suke. Tunda suka sauko ta zuba wa Adnan na mujiya, har plate ɗin da ta ɗoro drinks a kansa ya kusa suɓucewa daga hannunta, cikin son burge shi ta gaishe shi, ba tare da ya ɗago ba ya amsa mata. Maman Boy ta miƙa masa Boy sannan suka koma saman. Suna shiga ɗaki K'anwar Maman Boy ta ce. "Wow amma Aunty guy ɗin nan ya haɗu, ga kyau ga aji, yanda kika san irin Black Americans ɗin nan, ni na taɓa ganin baƙin mutum mai kyan shi kuwa?" "Kai Ramlah uwar zuzuta, daga ganin mutum sau ɗaya har kin ƙare masa kallo?" "Aunty ba za ki gane ba ne, amma guy ɗin ya haɗu over, Matarsa ta more." Murmurshi Maman Boy ta yi ta ce. "Ko dai kin ƙyasa ne?" "Rufa mun asiri, kar Matarsa ta ji ta mun duka, kawai dai na faɗi abun da yake da akwai ne, kin san ni ba na gani in yi shiru." Maman Boy ba ta kuma cewa komai ba, Ramlah kuwa cigaba ta yi da yaba kyawu da zubin halitta irin na Adnan. "Ka sha juice ɗin mana, ka wani lumshe ido ina magana ka mun shiru, tunanin me kake?" Fayyad da ya gama zuba drinks a cikin glass cup ya faɗi haka. Ba tare da ya buɗe idon ba ya ce. "I'm okay, thank you." "Wannan ai wulaƙanci ne, Matata ta kawo maka abu amma ka ce ba za ka sha ba." "I will drink, amma ba dan kai ba." "Na ji ɗin, Malam ka faɗi gaskiyar abin da yake damun ka, ka zo ƴanmatan Kano sun ruɗa ka shine kake wani babbasarwa, wannan yanayin da kake daga gani na fall in love ne. "Ka fi kowa sanin ba ni da time ɗin shirme ko?" Ya yi maganar yana gyara kwanciyar Boy da ya yi bacci a jikinsa. "Allah ya nuna mun ranar da ka zo kana cewa, dama Fayad haka so yake, lokacin zan ci dariyata in more, wai wa ya ga su Adnan ana Baby please sorry, you know I love you more." Ya ƙarashe maganar cikin dariya. Taɓe baki kawai Adnan bai ƙara magana ba. Abra ba ta nan Granny ta zo, kuma har ta tafi ba su dawo ba, saboda sun biya siyo school bag ita da Salman bayan sun baro gidan Aunty Iman, saboda normal handbag ba za ta ɗauki tarkacen school ba. Ba su farga Nai'ma ba ta gidan ba sai da daddare lokacin dinner, saboda sun saba idan Khamal yana gari kodayaushe tana part ɗinsa. Ganin Khamal ya fito shi kaɗai yasa Salman ya ce. "Abbi Mami fa? Tunda muka dawo ban gan ta ba, na je ɗakinta ba ta nan." "Ta je gidan Mama." Ya ba shi amsa "Mama kuma? Lafiya?" Ya tambaya cikin mamaki. "Lafiya ƙalau." "Yaushe za ta dawo?" "Gobe." "Me ake yi a can Abbi?" "I don't know, Mama ce ta kira ne za su tattauna akan something important." "Me ne abun?" "Na ce maka ban sani ba, Family issue ne, ka zama ɗan jarida ne Salman da za ka titsiye ni da tambayoyi haka? ka ci abinka, kar na kuma jin bakinka." Khamal ya faɗi haka cikin faɗa. Ƙasa Abra ta yi da kanta tana wasa da cokali a cikin abincinta, amma ta kasa ɗiba ta kai bakinta. "Ki ci abinci Malama, ba wasa za ki tsaya ba." Khamal ya faɗa mata haka ba yabo ba fallasa. Gyaɗa masa kai ta yi a hankali ta fara cin abinci. Kaɗan Khama ya tsakuri abincin ya ci ya miƙe, shi ma dan kada yaran nasa su yi tunanin da wata matsalar ne, musamman Salman da yake da saurin fahimtar abu. Daga dinning area ɗin ɗakinsa ya wuce ya dauko car key ya fice zuwa gidan Ammi. "Yaya, ba ki yi tunanin wani abu ya faru ba da bama nan?" Salman ya tambayi Abra cikin nazari. Ajiyar zuciya ta sauke ta ce. "Like what?" "Ko Mami sun samu matsala ne da Abbi shi yasa ta tafi gida? dan yanayinsa ya nuna yana cikin damuwa." "I don't think that gaskiya Faris, kuma insha Allah ba haka ba ne." "To Allah yasa." Ya yi maganar tare da cigaba da cin abincinsa. ita kuwa kasa cigaba da cin abincin ta yi, don tana cikin damuwa, ɓoyewa kawai take dan kar Salman ya fuskanta. Ta damu sosai akan fushin da Abbinta yake da ita, na makircin da Nai'ma ta shirya mata, ta ba shi haƙuri ya ce ya haƙura amma ya ƙi sakar mata kamar da. Khamal ne zaune a ɗakin Ammi yana zayyane mata abun da ya faru, bayan ya gama ta ce. "Yanzu ya kake so ayi?" Ya ce. "Toh Ammi, na rasa ma me zance, rigimar Granny ta yi yawa, haka kawai ta zo ta kora yar mutane gidansu, babu wani dalili." Ammi ta ce. "Ka kira Baffa ka sanar masa, zai yi mata magana kuma na san za ta haƙura." Numfashi ya sauke cikin damuwa ya ce. "Zan kira shi insha Allahu, amma ni Ammi ban so kika biyewa Granny ba, yanzu Nai'ma sai ta ga kamar na wulaƙantata ne." "Hakan shi ne solution da kwanciyar hankali, ko so kake yau Granny ta hana ni bacci da mitar na ƙi bin umarninta, saboda ba ita haife ni ba?" Girgiza kai kawai Khamal ya yi, zuciyarsa cike da takaicin halin Granny, amma abu ɗaya da ya daure masa kai shi ne, ya san duk jarabar Granny ba ta yin ta ba tare da dalili ba ko an taɓo ta, idan haka ne kenan Na'ima ta yi mata laifin da gaske, amma wanne irin laifi ne? Ko dai rikicin tsufan nata ne ya ƙaro? Hankali a tashe Nai'ma ta ƙarasa gidansu, Mama tana ganin ta, ta san ba ƙalau ba. "Ke lafiyarki kika faɗo mana gida babu ko sallama?" "Ina fa lafiya Mama? Allah ya haɗa ni da matsiyaciyar ƙaddararriyar kakar miji, ƴar kaza_kaza." Nai'ma ta faɗi haka tana hawaye. A ruɗe Mama ta ce. "Yanzu me ya faru, na gan ki a hargitse?" Labarin abun da ya faru ta sanar mata. Cikin takaici Mama ta ce, "Wannan mata akwai bala'i, mata kawai ki ɗorawa kanki jaraba a rayuwa?" "Shegiya ga shi ta ƙi mutuwa." Jinjina kai Mama ta yi ta ce. "To ta je dan kanta, aniyarta ta bi ta, zama gidan Khamal ne yanzu kika fara, sai dai ta mutu dan baƙin ciki. Ki kwantar da hankalinki, na san Khamal ɗin zai zo ya mayar da ke cikin ruwan sanyi." "Hmm, Mama babban tashin hankalina kullum cikin cewa za ta yi masa Aure take, tsorona kar zancenta ya tabbata, dan sai abun da ta ce iyayensa suke bi, idan ta dage amincewa fa za su yi." Ta yi maganar cikin tsantsar damuwa. "Ba zai yiyu ba, wannan tatsuniya ce, ki daina damun kanki akan wannan soki burutsun tsohuwar mara ma'ana, ki ɗauki zancenta shirme kawai. Tashi ki wuce ciki ki huta, bari Suwaiba ta dawo ta dafa miki abin da zaki ci." Zuciyar Nai'ma fal baƙin ciki ta miƙe ta shige ciki, wata irin tsanar Granny na cika mata zuciya, shegiyar mata ta yi sanadin da yau za ta kwana a cikin zafi ba a cikin AC ba, ita da ko taro ake a gidansu ba ta kwana, sai dai ta zo da sassafe saboda ba ta iya baccin cikin kwanciyar hankali. Babban takaicinta ba ta san abun da ta yi Granny ta yi mata haka ba, don ko kusa ba ta yi tunanin Salman ne ya sanar musu abun da ta yi wa Abra jiya ba. Abra na ɗakinta tana zuba abubuwan school a cikin new bag ɗinta, sai a time ɗin ta farga da rashin ganin I.d card ɗinta. Ƙara checking tsohuwar jakarta ta yi ko za ta gan shi amma ba ta gani ba, parlour ta fito inda Salman yake zaune yana kallon Ball. "Faris school i.d card ɗina yana gurinka?" Ba tare da ya ɗago ba ya ce. "No." Cikin damuwa ta ce. "Na duba ban gani ba, Allah yasa ban yar da shi ba." Yana duban ta ya ce. "Ki ƙara dubawa dai sosai Yaya." Kamar za ta yi kuka ta ce. "Na fa duba ko'ina ban gani ba." "To mene abun damuwa? Kar ki mun kuka ni akan ɗan wannan abun." "Dole in damu Salman, idan aka hana ni shiga school fa saboda babu shi." "Babu mai hana ki, wasu ma ba a ba su ba, ki bari gobe idan muka je school sai mu yi report a sake miki wani, kafin a sake sai ki dinga nuna admission latter ɗinki in za mu shiga." Ajiyar zuciya ta sauke ta ce. "Amma na yi mamakin rasa abun nan, ko garin ya na yar oho?" "Yarinya ce ke, shi ya sa komai naki sai addu'a, kuka, shagwaɓa, everything." Dariya ta yi ta faki idonsa ta ja dogon hancinsa da ƙarfi ta ce. "Tazarar shekaru uku ba wasa ba ce yaro." Tana faɗin hakan sai Salman ya yunƙura kamar zai kamo ta, ƙara ta saki tare da yin baya da sauri tana dariya. Ƙwafa kawai ya yi bai ce komai ba. Dawowa ta yi ta zauna a kusa da shi ta ce. "Please kar ka faɗa wa Abbi na yi loosing i.d card ɗina, ya ce daga fara zuwa har na fara yarda abubuwa." "An gama My Angel, zo ki taya ni kallo." "Maƙe kafaɗa ta yi ta ce. "Bacci zan yi, ka san gobe 8 muke da lecture, kai ma haka, saura kuma ka makarar da mu." "Uhm, su Yaya ƴan University, inyee." Ya yi maganar cikin dariya." "Na ji, ka kira Mami kuwa?" "Na kira ta ba ta ɗauka ba." Jinjina kai kawai Abra ta yi ta miƙe ta koma ɗakinta. Washegari da sassafe Ammi tana kitchen tana haɗa breakfast Granny ta zo bakin kitchen ɗin ta tsaya ta fara magana. "Kai jama'a, mutane babu Allah a ransu, ɗana yana can gurin neman halak amma saboda rashin tsoron Allah an kira shi an haɗa mu, jiya har na fara bacci kiran wayarsa ya tashe ni, to ni dai ba ruwana kowa ya haifa, kuma duk abun da mutum ya mun sai an yi masa shi ma, ato." Murmurshi Ammi ta yi tare da juyowa tana duban Granny, cikin girmamawa ta tsuguna ta ce. "Ina kwana Hajiya?" "Lau." Granny ta ba ta amsa cikin ɓata fuska. "Bari na kawo miki abincin Granny, yau na makara ban tashi da wuri ba ne. "To ba yunwa ce ta taso ni ba, a ƙoshe nake, kin san ni ƴaƴana ba sa cewa in yi abu in ƙi yi, tunda ni ma suna mun biyayya daidai gwargwado, abun da Hamisu ya faɗa mun ne na kwana da shi a raina, yau kuwa ina tashi na ce ba zan yi sanya ba, gidansu waccan gantalalliyar matar kamalun zan je in dawo da ita." "Hajiya da kanki kuma? Da kin bari Khamal ɗin ya je ya ɗauko ta." "Bar ni in je da kaina ɗin, ni yanzu ba dogon surutu na zo mu yi ba, kira direba ya zo ya kai ni." Ammi ta ce. "Toh, amma dan Allah ki tsaya ki karya Hajiya." Granny ta ce. "To na tsaya, kuma fa da gaskiyarki A'isha, dan waɗancan ruɓaɓɓun idan na je babu abun da za su ba ni, sai dai su bar ni yunwa tai ta sakaɗa ta, Allah na tuba ma ko sun ba ni ba ci zan yi ba, yo me zan yi da kayansu?" Takwas da mintuna a ƙofar gidansu Nai'ma ta yi wa su Granny, tana zaune a bayan Mota take bin gidan da wani irin kallo. Tsaki ta ja ta ce. "Tirrrr, ban da ƙaddara me zai haɗa Kamalu da ƴar wannan gidan? Gida ɗan tsurut haka kamar kabari, don ma Allah ya yi mu masu ilimi, mun san Talaka da mai kuɗi duk Allah ne ya yi su." Ta ƙarashe maganar tare da buɗe Motar ta fita, fuskar nan babu fara'a ko kaɗan, sai fama take da ƙatuwar jaka a hannu. Murmurshi kawai driver yake. Aunty Suwaiba tana tsakar gida tana alwala Granny ta rafka sallama, cikin mamaki take kallon ta, lokaci ɗaya ta haɗe rai ta cigaba da abun da take yi. "Ba mutane a gidan ne ko gidan na arna ne? Ana ta sallama an ƙi amsawa." Hararar ƙasan ido Suwaiba ta wurga wa Granny, cikin raini ta ce. "Me Idonki ya gane miki?" Tafa hannuwa Granny ta yi ta ce. "A'a fa, kar ki mun fitsara da farar safiyar nan, wallahi jibguwa zaki yi, kin san jikana soja ne, yanzu sai in kira shi ya turo sojoji mota-mota a tafi dake a ɗaure, don haka ki kiyaye ni. Kodayake ba laifinki ba ne, zafin zawarci ne, dan shi babu abun da ba ya sakawa." Ba ta jira cewar Suwaiba ta shige ciki tana baɓɓata fuska. Mama ta tarɓe ta ba yabo ba fallasa, Granny ba ta damu ba ta zazzage musu abun da yake cikinta tass, sai da ta ƙare musu cin mutunci akan mugun halinsu sannan ta dubi Nai'ma dake ta banka mata harara a sace ta ce. "Kya iya kwaso jiki ki biyo ni mu tafi, ba kuma don halinki na zo bikon nan ba, don ɗanki Salman na zo, yaron kirki kar ya ƙullace ni akan abun da na yi miki." Nai'ma ba ta tanka mata ba ta miƙe ta shige ɗaki. Taɓe baki ta yi. "Ko ba komai yau an yi kwanan gidan gyatumi cikin sauro da zafi ba cikin raɓa gidan jikana da aka saba ba." Tsaki Aunty Suwaiba ta yi ta miƙe ta bi bayan Na'ima. Around 12 na rana su Abra suka fito daga lecture, lecture biyu gare su kawai yau. Za ma ta yi a ɗaya daga cikin rumfunan department ɗinsu dan jiran Salman, shi sai 1 za su tashi. Khairat ce ta ƙaraso ta kama hannun Abra ta ce. "Zo mu je ki kira ni in duba wani abu kafin twin brother ɗin naki ya fito." Ƙin tashi Abra ta yi ta ce. "Kai khairy kin fiya yawo." "Please ki taso mu je." Yamutsa fuska Abra ta yi ta ce. "Ina za mu?" Khairy ta ce. "Can ne fa ba wani da nisa ba, daɗina dake ragwanta, yanzu ɗan zaman lecture ɗin nan sai ki ce kin gaji, ana ganin ki an ga fresh student." Murmurshi Abra ta yi ta miƙe suka tafi. Office ɗin Fayyad suka je, Khairy ta duba ko za ta ƙara ganin Adnan yau ma, sai dai ta yi rashin sa'a, yana tafiya suka zo." Cikin rashin jin daɗi ta ce. "Oh My God, kar dai yau ban zo school a sa'a ba?" Abra da ba ta san akan me take magana ba ta ce. "What happened?" "Guy ɗin da nake ba ki labari jiya na zo gani, daƙyar na iya bacci daren jiya saboda tunaninsa, na ci burin sake ganin shi yau, kuma kin san muna zuwa nan na ji ƙamshinsa." Khairy ta ba ta amsa cikin rawar jiki. Jinjina kai Abra ta yi ta ce. "Kin gamu da wahala amma, daga ganin mutum duk kin wani burkice, har kin gane wani ƙamshinsa?" "Ba za ki gane ba ne Abra Khamal Khamis, guy ɗin ya haɗu ƙarshe, kin san bana son baƙin Namiji, amma ganin guy ɗin nan jiya gaba-d'aya ya canza mini ra'ayi, ban yi tunani cikin baƙaƙen maza akwai masu kyau haka ba." Taɓe baki Abra ta yi dan totally shirme ta ɗauki batun, a ganinta wannan wahala ce da ɗora wa kai jidali. Komawa gurin zamanta ta yi ta bar Khairy da dube_dube, dan ƙin haƙura ta yi ta ce ita ba za ta tafi ba sai ta gan shi. Bayan sun koma gida suka tarar Nai'ma ta dawo, ba ta nuna musu komai ba da za su gane akwai dalilin da ya sa ta tafi gida jiya ba. Kasancewar Abbi yana nan ba ta nuna wa Abra komai na kyara ba, har girki ta yi kafin su dawo, a cewarta ƴarta ta kwaso gajiyar school ba za ta dawo ta yi girki ba. Abra tana cin abinci ta yi Sallah ta watsa ruwa ta kwanta, tunda babu abun da za ta yi. Da yamma Abra na zaune ita kaɗai a main Parlor tana duba lecture note ɗin da aka yi musu yau. Salman ya fito daga ɗakinsa cikin shigar kayan Ball. A hankali ta ɗago ta kalle shi jin ƙamshinsa, ɓata fuska ta yi tare da ɗauke kanta. Ƙarasowa ya yi ya zauna a gefenta ya ce. "Angel Sarkin karatu, ba ga bokon ba, ba ga islamiyya ba." "Ina zaka je?" Ta tambaye shi a shagwaɓe. Idanunsa a cikin nata ya ce. "Ball, amma bazan jima ba zan dawo." "Ball kuma Faris? Maimakon ka zauna ka yi karatun abun da aka yi muku yau? Ko dan ka ga Abbi ba ya nan ne?" "Idan na dawo zan yi, kar ki damu Babyn Faris da Abbi." Turo baki ta yi ta ce. "Ni dai kar ka fita ka bar ni, ni kaɗai Please." "Ki yi haƙuri Yaya, ba zan jima ba fa." Ya ƙarashe zancen tare da kamo hannunta. Kamar za ta yi kuka ta ce. "To zan bika." Shafa sumar kansa ya yi ya ce. "Angel rigima, gurin ball ɗin zan tafi dake? ai ta kalle ki ana tanka ki raina yana ɓaci a banza, ban yarda ba gaskiya." "To mene abun ɓacin ran?" "Ke ba za ki gane ba ai." Ya faɗi haka tare da miƙewa tsaye ganin lokacin fara ball ɗin har ya wuce. Kallon shi kawai take ba ta ce komai ba, ganin yanayinta ya san yana fita za ta iya yin kuka, shi kuma ba ya son hakan. Cikin rarrashi ya ce. "Mene wai? Yanzu fa zan dawo, ki yi kallo ko chat ko game kafin na dawo, zan taho miki da favourite thing ɗinki, choculates and sweets, I promised." "Ba na so, tunda kai always sai dai ka fice ka bar ni." Da ƙyar ya samu ya lallab'a ta, ta bar shi zai tafi, amma sai da sharaɗin ba zai wuce one hour ba, ya ce ya amince. Har bakin gare ta raka shi, sai da ta ga fitar shi sannan ta koma cikin gida. Kasa cigaba da karatun da take ta yi, tunanika kala-kala ne suka shiga yi mata yawo a cikin kai, tunanin rayuwarta da ƙalubalen da take fuskanta daga gurin mahaifiyarta, da kuma yanda yanzu take ƙoƙarin shiga tsakaninta da Abbinta. Knocking ɗin ƙofar parlour'n da aka yi ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi. Numfashi ta sauke tare da miƙewa cikin sanyin jiki ta je ta buɗe ƙofar bayan ta tambayi waye. Gabanta ne ya yanke faɗi ganin Uncle Faisal, ba ta ƙaunar abun da zai na haɗa ta hanya da mutumin nan ko kaɗan a rayuwarta. Baya ta yi da sauri ganin irin kallon da yake bin ta da shi, cikin rawar murya ta ce. "I...ina ...kwana?" "Lafiya ƙalau, Aunty Nai'ma fa?" "Tana sama tana bacci, bari na kira ta." Wani ɗan murmushi ya yi yana bin parlour'n da kallo kamar mai neman wani abu, cikin ransa kuwa faɗi yake. 'Wannan wata dama ce da ka samu Faisal, ka yi amfani da ita wajen cimma burinka na shekara da shekaru ba tare da kowa ya san kai ka aikata ba." Ajiyar zuciya ya sauke tare da lumshe idonsa, ya tuno lokacin da ya shigo gidan yanzu bai gamu da kowa ba, dan yana ta horn mai gadi bai zo ya buɗe masa gate ba, hakan yasa ya yi parking Motar a waje ya shigo babu ita, ya yi sa'a kuma ƙaramar ƙofar gidan a buɗe take. Ya san Salman ba ya gidan yanzu, dan da yana nan dole tare zai gan su da Abra a parlour, tunda ba sa iya rabuwa idan ba lokacin bacci ba, tamkar HANTA DA JINI haka suke. Abra ganin yanda ya yi shiru ta san ba Alkhairi yake kitsawa a cikin ransa ba, hakan yasa ta juya da sauri don guduwa ɗakinta. Ko taku biyu ba ta yi ba ya damƙi hannunta, ƙara ta saki tare da faɗin. "Please Uncle leave me, me na yi maka kake bibiya ta da wannan mummunar manufar, na roƙe ka da girman Allah ka bar ni, kai fa ƙanin mahaifiyata ne, ni tamkar ɗiyar ka ta cikinka nake." "Na bi ki ta lallami kin ƙi yarda, dama na faɗa miki idan ba ki yarda ta daɗin rai ba, za ki yarda ko ta halin ƙaƙa. Babu abun da zai hana ni cika burin raina a yau, ko dan na rama tijarar da Babanki ya mini akan na nemi wata alfarma a gurinsa." Fashewa ta yi da kuka tare da ƙoƙarin ƙwace hannunta tana kiran sunan Abbi da Faris, saurin toshe mata baki Faisai ya yi da hannunsa ɗaya, ta ƙarfin tsiya ya ja ta suka fice ta ƙofar kitchen wadda za ta kai ka ga ƙofar bayan gidan, Abra tana ji tana gani ya fice da ita daga gidan ta ƙofar baya ba tare da an gan su ba. Wani irin kuka take yi tamkar za ta shiɗe, don ta gama saddaƙarwa Faisal ya ci galaba, zai tafi da ita ya ɓata mata rayuwa kamar yadda ya sha furtawa. [10/1, 2:40 PM] Abk: Ihu Abra take yi, tana turjewa amma ya dinga janta, idanunsa gaba ɗaya sun rufe, ya manta da irin abunda ka iya biyo bayan ɗanyan aikin da yake ƙoƙarin aikatawa, ba abunda makauniyar zuciyarsa ke raya masa, illa cikar muradin sa akan Abra. Har waje ya janyota, tana tirjewa tana kuka, amma ya cigaba da janta har waje, layin shiru babu kowa. Ba zato ba tsammani sai ga wani daga cikin masu gadin gidansu Abra, wanda ya kasance soja ne ya nufosu akan babur, take Faisal ya tsaya cak yana wuri-wuri da ido. Cikin mamaki sojan, mai suna james yace "Hey Oga lafiya kuwa?". Faisal yace "eh lafiya ƙalau". James yace "to ya naga kana janta, kuma tana kuka, ga jikinta ba ko mayafi". Faisal ya haɗe rai yace "Eh laifi tayi mini, zan je in hukunta ta". Ɗan waro idanu Abra tayi, tana kallon Faisal. James yace "koma me tayi maka, ai be kamata ka dinga janta haka ba, da Oga na gari kaima ka san ko me tayi maka, ba ka isa ka fitar da ita daga gidan nan ta ƙarfi haka ba, koma me tayi maka kayi haƙuri" Wani irin baƙin ciki ne ya cunkushe zuciyar Faisal, na tarnaƙin da ya samu gurin cinmma mummunan burinsa akan Abra. Abra kuwa tana ganin Allah ya ƙwace ta, ta koma gida da sauri tana cigaba da kuka. James bai kawo komai ba, saboda ganin Faisal ƙanin matar gidan ne, bai kawo wani abu na cutarwa yayi niyyar yi mata ba. Ɗakinta ta koma ta cigaba da kuka, ta rasa wannan wace irin rayuwa ce, yanzu wa zata gayawa abunda Uncle Faisal yake yunƙurin yi mata, ai wannan ba abunda ma za ta iya faɗawa wani bane, ta yaya ma zata faɗi wannan mummunar magana haka. Tana cikin kukan ta jiyo muryar Salman, yana ƙwala mata kira, nan da nan tai sauri ta ja bargo ta rufe idonta, dan ba ta son ya zo ya sakata gaba da tambayoyi. Yana buɗe ƙofar ɗakin nata, ya hangota kwance ta juyawa ƙofa baya, dan haka sai yayi tunanin bacci take, dan haka ya rufe mata ƙofar ya koma ɗakinsa. Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750 A duk wani motsi da zai yi, tunanin Abra yake yi, lokaci-lokaci ya kan tsinci kansa da ɗaukar ID card ɗin ta yana kallo. Yanzu hakama zaune yake akan gado, hannunsa riƙe da ID card ɗin nata, ya zuba masa idanu, ya tattara dukkan wata nutsuwarsa a kallon ɗan ƙaramin hoton passport ɗin ta da yake jikin ID card ɗin.   Wata irin ajiyar zuciya yayi, ya ɗan lumshe idanunsa tare da damƙe katin sosai a hannunsa a hankali ya furta "Abra Khamal Khams" sai kuma ya ajiye shi akan gadon, ya tashi yana tafiya a hankali, zuwa banɗakin da yake cikin ɗakin. A department ɗinsu, sukayi parking ɗin motar, Abra ta kalli Salman tace "Faris" "Yaya" ya amsa. "ID card ɗina, ban ganshi ba" "Kiyi haƙuri, za'a ganshi insha Allah, saura kije kiyi ta kuka dan bakiga ID card ba, rainaki za'ayi" "Mhmm, to ka bani naka" Ware ido Salman yayi yace "Namiji kika koma?" "To kowa yana da nasa, amma ni bani da shi". Salman yace "to waye yace ki ɓatar da naki?" Tura baki tayi tana ƙoƙarin fita daga motar. Salman yace "ayi lectures lafiya My Angel ki kula da kanki Please,ba ruwanki da kowa kinji?" Murmushi kawai tayi masa, ta nufi hall ɗinsu, duk da hijjabi ne a jikinta, da facemask a fuskarta ba'a rasa msu binta da kallo ba, saboda hatta tafiyarta cikin nutsuwa takeyi gwanin ban sha'awa. GY BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY. GY Bulama ne ya haɗa gumi, yana yiwa wani matashi ɗinki, a ƙafarsa sakamakon faɗan daba, an ƙi karɓarsa a Asibitin gwamnati ance sai da 'yan sanda, shine suka taho Asibitin Bulama. Gaba ɗaya Emergency room ɗin sai ƙarnin jini yake, dan har a lokacin jinin be fasa zuba ba , haka Bulama yayi ɗinkin nan, da taimakon Nurses. Bayan ya kammala, ya cire safar hannunsa yace a kai mara lafiyan male ward, a biyo shi Office a karɓi takardar gwaje-gwaje da za'ayi masa. Haka akayi, Nurse Jamila ta bishi Office, ya rubuta gwajin ya bayar yace a kai lap, suje su ɗibi jininsa ayi wannan gwajin akawo masa. Bayan ya Sallami Nurse Jamila, wasu 'yan mata suka shigo su uku, suka samu guri ta zauna suka gaisa da Bulama. Ya kallesu yace "'yan Makaranta ya school ɗin?". Ɗaya daga cikin su tace "Lafiya ƙalau doctor, ya aiki?". Ya amsa da "Alhamdilillah" Tace"Yawwa doctor, kaga Wannan ƙawayena ne, to an samu matsala ne, nace bari in rakosu Asibitinka, ɗaya 4months, ɗaya 5Months". Bulama ya ɗan kallesu yace "to ku ya akai kuka bari haka ta faru?" Ɗayar tace "wallahi doctor tsautsayi, bamu san kan abun bane" Yace "Well, gaskiya Yakamata ku dinga kulawa, iyayenku karatu suka turoku, irin wannan rayuwar ba in da zata kai ku, mussaman kasancewar ku mata, Aure ko karatu shine ya dace da ku, duk abunda Namiji zai yi ado ne, yanzu Gashi nan su suna can hankalin su a kwance, ku kuma kuna wahala, ai haka ba daɗi" su kayi shiru kamar gaske. Yace "dubu ɗari ne kowacce, amma saboda wannan ƙawartaku patient ɗin gidan nan ce, ku bada 80k each of you". "Masha Allah, mun gode sosai doctor, Allah ya saka da alheri". Yace "Bakomai Allah ya kiyaye gaba,idan a shirye kuke, kuje ku biya kuɗin, za'ai aikin yanzu insha Allah" su kai tayi masa godiya, sannan suka bar Office ɗin. Suna fita ɗayar tace "Beb amma doctor nan ɗan rainin hankali ne, shi ba aikin zunubin ze yi ba, amma yake mana nasiha ya fara yiwa kansa mana" "Ke, nifa hankalina a tashe yake Wallahi, kar inje wani abun ya faru, tsoro nake ji". Cewar ɗaya daga cikin su. Wadda ta yi musu rakiyar ta kwaɓe baki tace "kina jin tsoro, amma kin iya kwanciya da namiji, mu biya kuɗi a cire cikin, mu koma in ci uban gayen nan, dan daga nan Abuja zan wuce, dan baze tonan Asiri ba, sai ya biya kuɗin aikin nan da zan biya, tijara zamu yi masa, kuma kar ki mana wannan sakacin naki Ke Ihsan, ki buɗe baki ki tatse shi". Wadda aka kira da Ihsan tace "Baby to ta yaya?". Baby tace "Au tambayata ma kike? Waye be sanshi a ƙasar nan ba, babban sojane da ƙasa take ji da shi, idan ya musa biyan kuɗin, vidoen tsiraicinsa zakiyi mana, mu saka a YouTube wallahi" Jannah ta kwashe da dariya tace "kai Baby baki da dama". Ihsan kamar za tayi kuka tace "Baby soja ne fa, idan ya harbeni fa?". Baby tace "Sojan me? Ina ruwan wani da aikinsa? Ya san sojan ne amma yayi iskanci, Wallahi kika ƙyaleshi, ya cuceki a banza" Da wannan hirarrakin nasu, suka ƙarasa reception dan biyan kuɗin. Nurse Jamila ce ta koma ofishin MD, hannunta riƙe da file, ta shigo Office ɗin, taje gaban teburin Bulama tace "doctor ga file ɗin nasa, an yi masa gwajin sakamakon yana ciki". Ya karɓa ya duba sannan yace "Ki turomin 'yan uwan patient ɗin" Ta amsa da to, sannan ta fita suka dawo tare da wasu maza guda biyu. Suka sake gaisawa sannan yace "yawwa duba da yadda mara lafiyan ya rasa jini sosai, akwai buƙatar mu ƙara masa jini, kamar leda uku haka, kuma muna buƙatar jinin da gaggawa kar ya rasa ransa". Sai da mamaki ya kama 'yan uwan nasa, ganin mara lafiyan nasu yana hayyacinsa, kuma ana ta hira da shi, amma ance wai sai an ƙara masa jini, kar ya rasa ransa, amma suka ɓoye manakin nasu, duba da aikinsa me ba nasu ba, ɗaya yace "to nawa ne jinin?" Bulama yace "eh to, duba da yadda kuka kashe kuɗaɗe sosai, zakuje lap a duba wanda jininsa zai yi, a ɗiba a saka masa, zaku biya dubu Arba'in, idan muma ba'a samu wanda jininsa yayi ba, zaku biya dubu saba'in, jini leda uku". Ɗayan yace "doctor babu ragi, naga baku karɓe mu bama, sai da muka ajiye dubu hamsin?". Bulama yace "Amma da bamu karɓeku ba kamar yadda Asibitin gwamnati sukayi, ai da wani zancen ake ba wannan ba, nan fa ba Asibitin gwamnati bane". Ɗayan yace "shikenan, bari muje mu biya". Bayan fitarsu, cikin damuwa Nurse Jamila tace "doctor, PCV ɗinsa fa 31%, meye amfanin jinin da za'a ƙara masa?" "Jamila ban hanaki yi mini shishshigi a aikina ba? Shekarata nawa ina aiki? Dan kinyi Nursing shekara uku shine zaki dinga min shishshigi a aikina, banda ina duba wani abu, da tuni na salamemeki, get out from my sight" yayi Maganar yana nuna mata hanyar fita. Tabbas Jamila akwai aiki, kamar jaka sam bata da son jiki, aiki take tsakani da Allah, yana jin daɗin aikin da ita, shikuma yana kyautata mata, dan Bulama akwai kyauta, mussaman ga ma'aikatansa masu ƙwazo, idan ya bushi iska, sai yasa a dire katan-katan na taliya da makaroni a raba musu, ko haka nan tsakiyar wata ya bisu me dubu ɗaya mai ɗari biyar ya raba musu, shiyasa ya samu masu goyon bayansa a harƙallar da yake a Asibitin nasa, kuma Asirinsa yake a rufe. Sai ƙarfe biyu sannan su Abra suka samu sukunin fitowa daga lectures, dan yin salla suci Abinci, su koma ta 2_4. A gajiye take sosai, sam Abra ba ta son takura, ita da Khairy suka fito, suka tafi masallaci dan yin salla. Bayan sun idar Khairy tace "Abra muje Cafeteria mu samu Abunda zamu muci". Abra tace "A'a ni ba zani ba" "Me yasa, ba kya jin yunwa ne?" "Zuwa zan in jira Faris, idan ya fito daga lectures maje muci Abincin" Khairy tace "Ikon Allah, ko kashin awaki kuka fito da Faris ɗin nan, wataran zaki Aure ku rabu, ai se kije ki tayi me ɗan uwa, nikam na tafi cin abinci bana iya ba". Abra gyara zaman facemask ɗinta tayi, ta miƙe tare da ɗaukar jakarta ta nufi hanyar barin masallacin. Wani guri ta samu can nesa da ɗalibai, ta zauna ta cire mask ɗin fuskarta, ta ɗakko wayarta tana trying lambar Faris. Jikinta ne ya bata ana kallonta, lokaci ɗaya kuma wani irin ƙamshi ya mamaye ilahirin gurin nan, duk da ba ta samu ɗaga kai taga waye ba, amma wani irin tsoro ya shigeta, a jikinta taji cewar kowaye yake ƙamshin nan ma'abocin kwarjini ne. Ba ta gama tunanin ba taji mutum ya zauna a kusa da ita, a razane ta fara bin ƙafafuwansa da kallo, sai dai ta kasa ɗaga kai ta kalli waye. Kamar an masa dole yace "Abra Khamal Khamis" Dam ƙirjinta ya buga, jin yadda ya ambaci sunanta, bata san lokacin da ta buɗe manyan idanunta, ta kalleshi ba, sai dai kallon nasa ya sake jefata cikin wani rikitaccen al'amari da ita kanta ta kasa gane wane irin yanayi ne haka?. "Is that not your name?" (Ba sunanki bane?) Ya tambayeta. Sunkuyar da kai tayi, ta ƙi yi masa Magana. "Are You deaf?" (Ke kurma ce?) Da sauri ta jinjina masa kai alamar eh. Yace "And how do you heard what I said this time?" (Ya akayi ki ka ji abunda nace, a wannan karon?) "Am using aid to hear" ta faɗi Maganar ba tare da ta shirya ba. Jin maganar ta ta yayi, tamkar rainin hankali, amma ya basar yace "Yaushe kuka fara lectures?" Ji tayi gaba ɗaya ya takura mata, ita ba ta sani ba malami ne ko ɗalibi, to yama za'yi malami ya zo ya sakata a gaba haka. Wayartace ta fara ringing, tayi sari ta ɗaga ta kara a kunneta tace "Hello Faris". "Angel kina ina ne? Na zo department ɗinku ban ganki ba, ko kinje cin abinci ne?". Tace "Aa banje ba, dama kai nake jira, bari yanzu zaka ganni" ta ƙarasa Maganar tare da miƙewa tsaye, Caraf ya sa hannu ya riƙo hannun Abra, wanda ya koma ɗan ƙarami a cikin nasa hannun, sai laushi hannun nata tamkar ya riƙe audiga. Zare ido tayi, tana bin hannunta dake cikin nasa da kallo, take hawaye ya taru a idonta tace "ka cika mini hannu na". Sai da ya ƙurawa kyakywar fuskarta ido sannan yace "Ina miki magana zaki tashi ki tafi?" Da ƙyar ta iya cewa "Brother na ne yake jirana, zanje muci Abinci". "Saurayinki dai ko?" Yayi Maganar ba tare da ya saki hannunta ba. Tayi sarin girgiza kai tace "A'a ni bani da surayi, ƙanina ne". Kallon Abra yake, tare da jinjina rainin hankali irin na Abra, wai duk wannan kyan nata take ce masa bata da saurayi, dan ta raina masa hankali. Hannunsa ɗaya ya sanya a cikin aljihunsa, ya ciro ID card ɗinta, ya danƙa mata a hannunta. Ɗan buɗe idanunta ta kuma yi, tan juya ID card ɗin ta kalleshi, amm ta kasa ce masa ta gode. Wayarta ce ta sake ɗaukar ruri, tana ɗaga wayar cikin shagwaɓa tace "Faris, gani nan yi haƙuri" Ta katse kiran, ta kalli Adnan tare da ƙoƙarin zame hannunta daga nasa, amma yaƙi sakin hannun, sai ƙara riƙe shi da yayi gam. "Dan Allah ka sakar mini hannuna, jirana ake". "Baki iya godiya bane?". "Yi haƙuri nagode" a hankali ya sakar mata hannu, cikin hanzari ta bar gurin ko waiwayawa baya ba ta yi. A ƙofar ajinsu ta tarar da Salman, aikuwa tana zuwa ya fara mita "Wai ina kika je ne haka?" A ɗan dirirce tace "Can gurin naje karatu, mu tafi kawai" Ya ɗan dubeta yace "meye wannan a hannunki?" Ta duba hannunnata tace "ID card ɗina ne" Yace "Hmm, a ina kika ganshi?" "Wani ne ya tsinta shine ya kawomin" Tsuke fuska Salman yayi yace "Wani kuma?" Tace "eh" Ya yi tsaki yace "wataƙila ma zama yayi yaita kallon hotonki da yake jiki". Murmushi tayi tace "Faris Allah ya shiryeka" Ƙara tsuke fuska yayi yace "Ki mai da mask ɗinki, har an fara binki da kallo". Ta sa hannu ta ja mask ɗin, ta rufe fuskarta sosai tace "Shikenan?" "Muje" yai maganar cikin bada umarni. Adnan kuwa yana nesa da su Abra kaɗan, yana hangota ita da Salman, kallonsu yake sosai yana ƙoƙarin tabattar da abunda Abra ta gaya masa na cewar Salman Brother ɗin ta ne. Salman ma dai Fari ne sosai, sai dai babu ta in da suka haɗa kamanni da Salman ɗin, kamanninsa daban nata daban. A hankali ya juya, ya bar department ɗin gaba ɗaya. Hajiya Na'ima ce ta shiga sashen Abbin Abra, ta tarar da shi yana ta shiri, ta kalleshi tace "Yallaɓai ya naga haka? Jiya fa ka dawo kuma na ga kana haɗa kaya, ina zaka kuma?" Ba tare da ya kalleta ba ya cigaba da haɗa kayan yace "lamarine na gaggawa, akwai buƙatar inje Abuja a yau ɗin nan" Tace "Amma meyasa?". "Sojojin da ake bincike akansu ne, wai sunci guba sun mutu". Tace "ta yaya? Waye ya basu gubar?" Yace "Nima ban sani ba, abunda zanje inji kenan, ya akai suka ci gubar suka mutu, ba tare da an samu wani cikakken bayani a bakinsu ba". "Kai amma ban so ba, daga dawowarka jiya ko gama ganinka ba muyi ba zaka juya?". Ya ɗago ya kalleta yace "Am sorry, nima ba hakan na so ba, amma kuyi haƙuri ya zama dole in tafi, lamarin akwai alamar tambaya". Tace "Shikenan, Allah ya tsare bari in ƙarasa haɗa maka kayan". Ta cigaba da haɗa masa kayan, shi kuma ya shiga wanka. Successfully, GY BULAMA ya cirewa 'yan matan nan ciki, bayan tafe masa uwar kuɗinsa da suka yi, ya rubuta musu magunguna tare da kafa musu dokokin da za su bi, dan gudun kar Matsala ta biyo baya. Suna tafe a mota, Baby na driving tana cigaba da shirya musu yadda zasu damfari Alhazan dake mu'amala da su kuɗi, Mussaman wanda yai mu'amala da Ihsan, wanda ya kasance babba ne sosai. Tace zasu koma gidan da suke su huta, idan suka warware zasu tafi Abuja, aje ayi wadda za'ayi dan su zasu biya kuɗin cire cikin da aka yi. Yauma a gajiye Abra suka koma gida, duk ta gaji jikinta har wani ciwo yake, Wanka kawai tayi, tai sallar la'asar,ta hau gadonta dan ta ɗan huta, ta lumshe idanunta sai dai gabanta ya faɗi, a lokacin da tuno da mutumin da ya tsinci ID card ɗinta, Mutumin da ko sunansa ba ta sani ba. Guntun tsaki ta ja, tare da ƙoƙarin gyara kwanciyarta, amma wayarta tai wata 'yar ƙara, alamar saƙo ya shigo. Ta miƙa hannu ta ɗau wayar, ta fara duba saƙon. *Sky is beautiful, especially when the millions of Stars appears in the dark, but is not that beautiful if the Moon doesn't appear. You are always that Moon that make the Sky beautiful, Stay bless my Angel. Murmushi Abra tayi tare da furta "Allah ya shiryeka Faris" Ta gama hutawarta, ta tashi ta shiga kitchen, a Wannan karon akai sa'a Mami tayi girki, ta shiga kitchen ta zuba ta fito falo, dan taci. Hakan yayi daidai da fitowar Salman falon shima, yana ganin Abra yace "Alhamdilillah, thank God dama nima banci Abincin ba, let's eat together". Ya ƙarasa kitchen, ya ɗakko spoon ya dawo ya zauna a inda Abra take, yasa cokali suka fara cin Abinci. Abra tace "Wai nikam ina Abbi? Naga motarsa a gida, kuma banga alamar yana nan ba". Salman yace "Mami tace mini aikin gaggawa ne ya kama shi, ya koma ɗazu muna school". Abra tace "Amma be bari mun dawo ba, ban gama ganinsa ba fa". "To ga hanya nan, maza bi shi" Salman yayi Maganar yana saka lomar Abinci a bakinsa. Mami ce ta fito daga sashinsa, cikin faɗa tace "Salman meye haka? Wai ba hanaka wannan abun ba, ka zauna kuna cin abinci tare, kai kaga dacewar hakan? Ko da duk ka nunamin ban isa bane?". Salman yace "Mami, Yaya ce fa ba wata ba, banga aibun haka ba". "Ai dama ba zaka gani ba, tashi ka bar gurin nan kafin in ɓata maka rai". Kan Salman ya yunƙura, Abra ta miƙe, ta bar masa Abincin, ta koma ɗakinta rai a ɓace. Wayarta na hannunta, taji tayi vibrating. I want you in my life for today, tomorrow and forever, have a cool evening my Moon. Ɗan shiru Abra tayi, Salman dai gashi can a Falo Mami na yi masa faɗa, to waye ya turo mata wannan saƙon? Sai yanzu ta duba labar taga baƙuwar lamba ce. Ɗan taɓe baki tayi, tana tunanin kawai mistake ake gurin turo mata saƙon. Kafin lokacin da zata kwanta bacci, aƙalla an tura mata messages kusan biyar. Haushine ya fara kamar Abra, ta replying da wrong number.   Daga haka ba  a kuma turo mata message ɗin ba, kan ta kwanta bacci sai da ta kira Abbi, sukayi hira, ta yi masa Adduoi da fatan Alkhairi. Haka nan ta samu kanta da jujjuya messages ɗin da aka dinga turo mata yau, sai ta samu kanta da tunanin ko yaya masu soyayya suke ji oho, ita dai Allah be sa ta taɓa yin saurayi ba, balle taji me ake ji. 'to ke meye naki na soyayya, ke da kike karatu, ki maida hankali akan karatun ki, ko dan ganin Farincikin iyayenki' wata zuciyar ta gargaɗeta. Ta ture tunanin komai, ta cigaba da karatun ta, ƙarfe ɗaya ta tashi, tayi alwala tayi sallar nafila, sannan ta nemi guri ta kwanta bacci. Da Asuba ƙarar shigowar saƙo ne, ya farkar da ita, ta ɗau wayar ta sake dubawa. "I pray Allah Khair for you now and always, include me in your prayers dear, you will always be in mine, have a wonderful Morning, i will be in your department to". "Ikon Allah" shine abunda ta faɗa, ta ajiye wayar. Abu kamar wasa kusan kwanaki uku, Ana turowa Abra ire-iren wannan saƙonnin, ba tare da ta san waye ake turo mata ba, da fari abun haushi yake bata, daga bisani kuma har Alla-Alla take, me turo saƙon ya turo, sai dai be taɓa kiranta ba. Tayi saving ɗin lambar a wayarta da Mr. Unknown. Ko da ta duba what's app ɗinta, labar ta bayyana a contact ɗinta, amma dp ɗin lambar babu hoto. Ji tayi tana son yiwa lambar magana amma kasa, kuma gashi tunda ake turo mata saƙon, tunda tayi reply da wrong number, ba ta sake replying ba. A wannan karon sai taji tana son yun replying, a message ɗin da aka turo mata, wanda yake cike da Adduoi da kuma koɗa ta. Tayi Replying da "Ameen, Nagode sosai, amma da Allah ko zan iya sanin waye?". Tun safe da tura message ɗin be mata reply ba, haka ana lectures amma hankalinta na kan wayarta, tana jiran ayi mata reply. Sai bayan da ta koma gida, sannan akayi reply "Is someone, who want a chance to be with you for ever". "May i know you please?" Ta kuma tanbayarsa. "Sai kin sanni sanni sannan zaki so ni? Bana iya komai a rana idan har ban ganki ba". Sai da ta ɗan ware idonta, sannan tace "A ina kake gani na, bayan bana zuwa ko ina sai Makaranta". "Zan ajiye miki saƙo a what's app, wanda zai tabattar miki da hakan, aini bana ƙarya sai bisa kuskure". Cikin hanzari ta shiga what's app ɗinta, aikuwa saiga saƙo a what's app ɗin, hotonta ya turo mata, tana tsaye a ƙofar ajinsu, saye da doguwar rigar abaya, wanda sam ba ta san an ɗau hoton ba". Mamakine ya sake kamata tace "A makarantar mu kake kenan?". "Neither No, Nor Yes" Kamar tana gabansa ta tura baki ta tura masa "Please tell me". "Me kike so in gaya miki?" Abra ta tura masa da "Ka gaya mini idan a makarantar mu kake, sannan ka turomin hotonka" "Idan na turo miki hotona na san ba zaki yadda ki soni ba" "Meyasa?" "Saboda ni mummuna ne, muni me ban tsoro, ke kuma kyakykyawa ce Masha Allah, kyawu mai ɗaukar hankali". Abunka da farin shiga, Abra ta ture litattafanta gefe, ta gyara zama tana cigaba da hira da wanda ba ta san kowanene ba. "Ni koma a ya kake, dan Allah ka turomini hotonka in gani". "Gaskiya ina tsoron bayyana miki kaina, kar Major ya sa sojoji su zane ni, bani da ƙwari zasu iya yi mini illa". Tayi reply da "Eyya, ai ba haka Abbi na yake ba, ba abunda zai sa ayi maka, ko hotonka ka nuna mini". "Ba zan turo miki hotona ba, amma zaki ganni very soon insha Allah, ina Faris?" Saida t buɗe baki da mamaki tace "Ya akayi ka san Faris, ko a Makaranta ba kowa ya san ina gaya masa wannan sunan ba". "Yanzu idan nace miki da Faris kike magana me zaki ce?" "Kaiiii Faris kuma, i dont think Faris will prank me with this". "Are you sure my Angel?" Gaba ɗaya Abra ta rikice, banda Abbi da Salman, ba wanda yake kiranta da Angel. Da sauri ta ajiye wayar, ta fita falo, aikuwa ta tarar da Salman a kwance a ka kujera, yana danna wayarsa. Da sauri ta ƙarasa, ba tare da tayi masa magana ba, ta miƙ hannu zata ƙwace wayarsa, caraf ya riƙe hannun, ya kalleta yace "Ya dai?" "I want see your phone" ta faɗa tana tsare shi da ido. "For what?" Abra tace "I just want to see it". Salman yace "aikuwa ba zaki gani ba". "Please Faris, ka bani in gani". "Me zaki yi da ita?". "Kai dai kawai ka bani". Miƙewa Salman yayi yace "tun da ba zaki faɗa mini me zaki da ita ba, na hanaki". Diddira ƙafarta ta shiga yi, cikin shagwaɓa tana cewa "dan Allah Faris ka bani in gani" Dariya yake yi yace "sai kin gaya mini me zaki da ita". Shagwaɓa take sosai, wanda hakan ba ƙaramin burge Salman yake ba, ganin za ta yi masa kuka, ya sanya ya miƙa mata wayar ta sa. Sai dai duk wani bincike da tayi, ba ta ga wani abu makamancin saƙonnin da ake tura mata ba a wayar ta Salman. Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/1, 2:40 PM] Abk: Ƙara rikicewa Abra tayi, ganin yadda ya tayara da motarsa ya bar gurin. Gaba ɗaya ta rasa abunda yakamata tayi a gurin nan, ihu za tayi ko kuka za tayi? Bata koma gurin cin Abincin nan ba, ta nufi department ɗin su, tana zuwa ta tarar da Salman da waya a hannunsa yana lelleƙawa  yaga ta in da zai hango Abra. Yana waiwayowa ya sukai ido huɗu da Abra da take ta tsuma. Da sauri ya ƙaraso in da take yana faɗin "Wai ina kika shiga ne? Over 15 missed calls, amma baki ɗaga ko ɗaya ba. Shiru tayi tana rarrraba ido, ta kasa ce masa uffan. A ɗan hasale yace "ki yi mini magana ma, kin tsaya kina kallona". "Wani lecturer ne ya ƙwace mini waya" "Me ki kayi masa da ze ƙwace miki waya?". "Wayata ce tayi ringing a aji, shine ya ƙwace mini wayar" tai maganar tana tsilli-tsilli da ido, saboda ƙaryar da tayi. Salman dai kallonta kawai yayi, yace "to yanzu daga ina kike?". "Cafeteria naje inci Abinci". "To Yanzu kinci Abincin?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Wai meke damunki ne, gaba ɗaya kamar a tsorace kike fa" yai maganar yana kallonta. gaba ɗaya tunaninta da hankalinta yana kan yadda za tai ta karɓi wayarta, tare da jinjinawa ƙarfin hali irin na Adnan. 'yanzu idan da gaske yake ya tafi da wayata Kaduna ya zanyi?' wata zuciyar ta tambayeta, nan da nan wank irin gumi ya shiga tsastsafo mata, na tashin hankali da damuwa. A haka suka nufi mota suka kama hanyar gida, Salman ya lura gaba ɗaya akwai abunda yake damunta, amma ganinaa yayi-yayi ta gaya masa taƙi, kawai sai ya ƙyaleta. Tafe suke a mota, Baby na sake gwadawa Ihsan yadda za suyi da Sojan nan idan sunje Abuja, Ihsan tai shiru tana sauraren Baby kamar 'ya da uwa. Baby  tace "Maza ki ɗakko waya, ki sanar masa gamu nan". Jiki a sanyaye Ihsan ta ɗakko waya ta kira wata lamba, wadda tai saving da Yallaɓai. Sai data kusa tsinkewa, sannan ya ɗauka "Hello beb ya?" Tai ajiyar zuciya tace "Ya kake? Ya aiki?" Yace "Alhamdilillah, nayi missing ɗinki sosai fa". Ihsan tace "gamu nan zamu shigo garin Abuja". With so much excitement yace "Wow, are you sure?". Tace "Quiet sure" Yace "Can't wait to see you Baby, sai kin zo, ki sauka a guest house ɗina, za'a samar maku da komai". Tace 'Alright, sai mun zo". "Ok bye". Baby tace "hmm zaka ga tsiya, ko ka saki kuɗi ka ƙwaci kanka, ko muyi maka bariki irin ta yaran zamani". Gaba ɗaya Abra jinta take kamar mara lafiya, saboda rashin wayarta, gashi gefe guda tana ta tunani unknown ɗinta, da yake turo mata saƙonni. Allah sarki ta san yanzu zai tayi mata Magana yaji ta shiru, ba ta reply. Da magariba, Abbi ya dawo daga masallaci suna hira shi da Na'ima, gefe Salman yana duba wayarsa, Abbi yace "Hope dai karatu kake ba shirirta ba?" Salman yace "eh Abbi, ina duba wani abu ne". "Ai nasan hankalinka ne, kafi maida hankali a kan, shirita fiye da karatu". Na'ima tace "Eh amma ai Abra ka yadda karatu take a waya, amma shi kace ba karatu yake ba" wani mugun kallo da yayi mata ne, ya sanya ta haɗiye Maganar ba shiri. Abbi yace "Ni ban ma ganta ba gaba ɗaya, me take yi a ɗakine iya kaɗai?" Salman yace "I don't know what's wrong with her today, gaba ɗaya kamar wani abu yana damunta". "Kira mini ita". Salman ya miƙe ya nufi ɗakinta, ko da ya shiga ya tarar tana zaune, ta zube littattafai a gabanta, amma tunani takeyi, ba karatun ba. Yayi ajiyar zuciya sannan yace "Idan kin gama tunanin kizo Abbi yana kiranki". Ta ɗaga kai ta kalli Salman, wanda tuni ya juya zaia bar gurin. Jiki a sanyaye ta miƙe ta biyo bayansa,  ta tarar da su gaba ɗaya a falo. Ta ƙarasa gaban Abbi ta zauna yace "Gani Abbi". "Daughter na, meke damunki ne? Duk muna nan a zaune, amma kin keɓe kanki a ɗaki, gashi fuskarki ta nuna, kina cikin damuwa". Abra tace "Abbi bakomai, na gaji ne kawai" Abbi yace "Anya kuwa? Ki gaya mini gaskiya". Salman yace "Wayarta akai seizing a Makaranta" Abbi yace "Subhanallah, how comes?" Salman yace "Wai ringing tayi a aji, shine aka ƙwace, shine take ta wannan ƙuncin". Abbi yace "Ki dena damuwa, in basu baki ba a canza miki wata". Na'ima da tun ɗazu ba tace komai ba tace "Wane irin a canza mata wata, ka sani ko ana musu karatu tana wasa da waya ne?". "No ba haka 'yata take ba, koma mene zanga abunyi, a canza wata idan be baki ba, amma ki dena damuwa kinji?" Tace "to Abbi". Salman ne ya miƙe ya nufi hanyar kitchen, ganin Kamar Salman yana fushi da ita, yasa ta miƙe itama ta nufi kitchen ɗin". "Ina zaki?" Na'ima tayi maganar tana zazzarewa Abra ido. Abra tace "Mami banci Abinci ba, zanje in zuba ne". Ba dan ta so ba, tai shiru saboda Abbi yana gurin. Da sauri Abra ta ƙarasa cikin kitchen, ta tarar da Salman a tsaye yayi shiru, da alama ma ba wani abu ya shiga yi a kitchen ɗin ba. Yana ganin ta shiga, shi kuma ya nufi hanyar fita, da sauri tace "Faris" Ya waigo ya kallta ba tare da yayi magana ba. "Fushi ka ke dani?". "Me ki kai mini da zan fushi dake?". 'ga alamu nan a fuskar ka, me nayi maka? Kuma ina shigowa ka juya zaka fita". "To ya kike so inyi, ina ta binki ki gaa mini me ke damunki amma kin ƙi". Abra tace "Haba Bloody na, rashin wayata ne kawai duk ya dameni, You know am so much attached to my Phone, am sorry" Ta yi maganar tana murmushi tare da jan dogon hancinsa, ji yayi yana neman shiga wani hali, kasancewar kusacinsu da Abra yayi yawa, gashi sai ƙamshin turare take yi. Cikin shagwaɓa ta ce "to kace mini ka haƙura mana". Lumshe ido yayi, yana kallon yadda take cigaba da shagwaɓa. "Talk mana". "Ta yi maganar tana girgiza shi". "Tom na haƙura" ya faɗa a taƙaice. Ta girgiza masa kai tace "See how you frown your face, gaskiya ba kaa haƙura ba" "Na haƙura Angel, let me go and rest please" "Wai to ya na ga duk ka wani canza ne?" Yace "Stress ne kawai na school, see you later" yayi maganar yana kashe mata ido ɗaya, ya fice daga kitchen ɗin. Murmushi tayi a hankali ta furta "Faris sarkin rigima, am imagining ma life without you, you are so much caring bro, Allah ya biya ka" ta ƙarasa Maganar da ajiyar zuciya. "Kai yanzu Adnan, fisabilillahi daga cewa zakaje wani Assigment a Kano ka dawo, sai kaje ka yi zamanka, kullum kana gaka nan gaka nan, mahaifinka duk ya damu". "Am sorry Hajiya, ni kaina ban yi zaton aikin zai ja mini dogon lokaci haka ba, amma Alhamdilillah an yi Nasara a aikin ai". "To barka, haka ake so dama, amma aikin na ku ne sai a hankali, yau mutum yana nan gobe yana can, ga ƙasar nan babu cikakken tsaro sam". Yace "Hakane Hajiya, dama aikin ɗamara kasada ne, amma gara a rasa rai ɗaya idan har zai silar rayuka da yawa su samu kwanciyar hankali". Hajiya tace "A'a Adnan, ai duk rai rai ne, mai shi yana son abunsa, Allah dai ya tsare mana ku". "Ameen, uwata ta kaina, baki mini Addu'a ba yau". Ta yi murmushi ta ce "Addu'a kullum cikinta muke ai, yanzu haka ma ai na yi maka". Yayi murmushi yace "Allah ya ja kwanan Hajiya Mama" "Ina, ai mu mun kai gangara, fatan ƙarshe mai kyau muke, ku muke yiwa Addu'a, Allah ya raya mana ku". Ja yayi kamar ta zuba masa wuta abunda ta faɗa, life without his Mum, haka kurum ya ji jikinsa yayi sanyi, miƙewa ya yi daga in da yake zaune yace "Sai da safe" "To Allah ya tashe mu Lafiya, kar ka manta kayi Addu'a" Bai amsa ba, kuma bai waigo ba ya wuce ɗakinsa. Ya shiga banɗaki ya watsa ruwa, ya fito yayi shirin kwanciya bacci, gefen pillow ɗin sa ya kalla, wayar Abra ce da aka ishe shi da ringing ya sakata a silent. Ya danna wayar, kusan 25missed calls, wanda duk daga Bloody sai Faris. Sliding ɗin screen ɗin wayar yayi, saiga hoton Abra akan screen lock ɗin wayar, kanta babu ɗan kwali, ta saki gashin kanta, da ya rufe mata gefen fuska, ta turo laɓɓanta gaba, wanda suka kasance pink. Shiru yayi ya zubawa hoton nata ido, kamar mai nazartar wani abu, daga bisani yayi wata nannauyar ajiyar zuciya, ya kashe wayar gaba ɗaya ya ajiye, ya kwanta. Duk da zuciyar Ihsan cike take da fargaba, amma haka ta ɓoye tsoronta, ta dake dan karta ɓata musu shiri, ta dube shi tace "Nifa Yallaɓai babban dalilin zuwana nan shine, ciki ne a jikina har watanni huɗu dan haka nazo ka bank kuɗi inje in cire shi, ka san dai babu da wanda na taɓa mu'amala sai kai. Haɗe rai yayi yace "Na sani ko bayan na buɗe hanyar, kin cigaba da leƙe-leƙenki, kuma wace irin sokuwa ce ke, da zaki bari ciki ya shiga jikinki har Wannan lokacin?" "Kar ka sake ce mini sokuwa, kawai ka bani kuɗi inje in zubar, kar Asirina ya tonu". Gajeren tsaki yayi Yace "Naji, zan baki 20k kije a cire shi". Wani banzan kallo ta yi masa tace "sai kace cikin jikin Akuya? Dubu ɗari aka ce zan ajiye, sannan a cire cikin ya zanyi da wata 20k". "Kina da hankali kuwa, a wannan marrar ne zan baki har 100K?". "A Arziƙin da Allah yayi maka mecece 100K? Ko nice a bar banza?" "Kinga zan bani 50K, daga haka ba zan ƙara ba". "Gaskiya ba zan karɓi 50K ba, a ina zan samu sauran?". Yace "Wannan ya rage naki kuma" wani irin baƙin ciki ya turnuƙe mata zuciya da tarin nadama da dana sani, ba yadda ta iya, haka ya tura mata 50K. Ba kunya kuma bayan ya tura mata ya fara lalubarta, abun mamaki sam ba ta masa musu ba, suka gama sheƙe ayarsu, Sannan ta kintsa jikinta, ta koma masaukin su. Baby ta dinga jinjina mata, domin kuwa duk abunda suka yi, ta naɗo tsaf a video ba tare da ya san tayi haka ba. Nan Baby ta sake shirya mata abunda zata yi masa, dan wanda ya yiwa Janna, sai da ya ajiye mata dubu ɗari biyu da hamsin, dan haka suma sai sun wanki wannan Yallaɓai. Dan haka suka tsara message tare da videon nan nasa, suka tura masa!. Innalillahi wa Innalillahi raji'un, tashik hankali da ba'a sa masa rana, Yana gurin aiki, amma haka ya miƙe jikinsa na tsuma, yaran nan sun san waye shi a cikin ƙasar nan kuwa? Yayi harka da manyan karuwai, amma wannan da ba su fi 'ya'yan cikinsa ba, sune za su ƙulla masa wannan tsiyar? Dole ya ɗauki mummunan mataki akan yarinyar nan, wanda nan gaba idan aka ce ta yiwa wani haka ba za tai ba. Abra tun tana kewar rashin wayarta, har ta saba ta haƙura da rashin wayar, gefe guda haka kurum take jin ta yi missing ɗin me turo mata messages ɗin nan a wayarta, ko ba komai wani mutum na musamman ne da ya shigo rayuwarta, ta wata siga da babu wanda ya taɓa shigowa ta haka. Guntun tsaki ta ja, bayan tuna Adnan ya tafar mata da wayarta. Sosai ta maida hankalinta kan karatunta, tun daga ranar da Adnan ya tafi da wayarta, ba ta sake ganinsa ba, tun tana tunanin zata kuma ganinsa ya bata wayarta har ta dena, ta cigaba da al'amuranta, sai cewa ma take wa ya sani koma ɓarawon wayane, wayar yake son ya sace shiyasa yake ta binta. Yau ba lokaci ɗaya Abra za su tashi da Salman ba, dan haka akwai snacks a jakarta, ta tafi department ɗin su Salman, domin suci sai ta jira har ya gama lectures, Sannan su tafi gida, dan ta san idan taje gidan ma, ba daɗinsa za taji ba. Ajin Su Salman ta nufa, ta ɗan leƙa ta window, taga ana yi musu lectures, Malmin ya raba ajin gida biyu, yana yi musu kacici_kacici, yace duk rukunin da suka ci, suna da maki goma-goma dukaninsu, amma sai ya kammala lectures ɗinsa na yau za'ayi. Ajinsu Faris Maza sunfi yawa akan mata, dukkansu suna sanye da fararen lapcoat akan kayansu, sun tattara nutsuwarsu akan malamin. Ba wanda ya ganta, tana nan tsaye aka gama lectures ɗin, aka fara Quiz. Anayi tana ta murmushi, abun yana burgeta sosai da sosai. Can aka yiwa rukunin su Faris wata tambaya, abunka da manyan professors, sai da ya rikita tambayar, yadda ba za su fahimta ba. Sai ya basu option yace su zaɓa, ganin sunyi shiru suna mazari ya sa Abra tai farat tace "Faris Ba ne amsar fa" gaba ɗaya ta manta a jikin window take, tana leƙe. Aikuwa gaba ɗaya suka waigo suna kallonta, sai kuma tayi shiru tana rarraba ido. Prof ɗin nan yace "Zo nan" jiki a sanyaye ta zagaya ta shiga ajin, tana sunkuyar da kai, saboda ba ta son kallo. Ya kalleta yace "Me kike yi a jikin window?". "Brother na nake jira mu ci Abinci" ta faɗa kai tsaye. Yai murmushi yace "Sai kace a Nursery? Waye brother ɗin naki?" Tace "Faris ne" "Waye Faris?". Ta kalli Salman da ido, Salman wata kunya ta kama shi, Sam Abra bata da wayo wasu lokutan. Prof ɗin yace "iyee, cire facemask ɗin nan". A hankali ta sauke face mask ɗin, tana sunkuyar da kai, harda masu cewa wow, tubarkallah abunda ya sa Salman sake tsuke fuska. Prof Jibiya yana da barkwanci sosai, dan haka yace "Salman, is she your sister?". Salman yace "Eh ƙanwata ce". Zaro ido ta yi, za tai magana, amma Salman ya harareta, hakan ya sata yin shiri. Jibiya yace "Masha Allah, to yanzu yi mana bayanin, meyasa kika zaɓi B a matsayin Amsa?". A nutse Abra tayi masa bayani, wanda in ba me kaifin hankali ba, babu wanda zai iya gano amsar. Ya jinjina kai yace "Kai Masha Allah, Madalla da basira irin taki, me kike karanta ne?" Ta gaya masa, ya jinjina nai, gaba ɗaya ba science tayi ba, amma ta iya bada wannan amsar. Prof yace "Yanzu kiyi tafiyarki, kije ki ci Abincin ki, dan wannan ba yanzu zai fito ba". Tace "To, amma zan iya ba shi nasa kan su fito?" Ya jinjina mata kai, 'yan ajin sai dariya sukewa halin ƙuruciya na Abra. Taje gaban seat ɗin Faris, ta ɗakko wata leda ta ajiye masa tace "zanje inyi karatu in kun gama sai mu tafi". Faris ya kalleta, a hankali yace "Dan Allah Angel yaushe zaki girma ne? Yarinya ba wayo gaba ɗaya". Tace "Ni ba zan kulaka a nan ba, sai munje gida". Daga haka ta yiwa lecturer godiya, ta fice, prof ya cigba da koɗa Abra da baiwarta, har da tambayar Salman anya uwa ɗaya uba ɗaya suke? Ko dai su larabawa ne, sai da Salman ransa ya ɓaci, ya tsuke fuska. Tana tafe tana ƙoƙarin samun gurin da zata zauna, ta ci Abincinta tayi karatu. Wani irin mahaukacin parkig aka yi a gabanta, wanda sai da ta razana, ta runtse idanunta. Jin shiru ba'a bugeta da motar bane ya sa ta buɗe idanunta a hankali. Ido huɗu suka yi da shi, wanda sai da ya fuskanci halin firgici da ta shiga. Juyawa tayi za ta canza hanya, amma cikin zafin nama ya fito daga motar, ya danƙo hannunta, ya jefata a cikin motar ta sa, ya rufe motar ya zagaya ya shiga, ya fizgi motar da gudu, ya bar makarantar. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ina zaka kai ni, na shiga ukuna, wayyo Abbina, Faris dan Allah a temake ni" "Shut up, ki dena yi mini ihu" yai mata wata razananniyar tsawa. Abra cikin kuka tace "dan Allah kayi haƙuri, ka ƙyaleni dan Allah" shiru yayi Mata ya cigaba da tafiya. Wani gurin cin Abinci yaje, yayi parking ya kalleta ransaa a haɗe ya ce "Fito" Cikin tsoro da fargaba ta fito tana zare ido, gurin ba mutane sosai suka shiga cikin gurin cin Abincin. Yayi mata umarnin ta zauna, haka ta zauna tana cigaba da waige-waige, tsoronta Allah tsoronta kar wani wanda ya santa ya ganta yaje ya gayawa Abbi. "Me za'a kawo miki?" Yayi Maganar yana kallonta. Ta girgiza masa kai alamar babu. "Ba sace ki nayi ba, Cin Abinci kika rako mijinki, dan haka You Are safe, ki saki jikinki, bana sace mutane" Kallonsa take, kamar ba shi ne ya gama yi mata tsawa ba. Yayi musu order Abinci, amma taƙi ci. "Nifa Mutum ne ba dodo ba, stop looking at me, like this" "Dan Allah ka mai da ni, dan Allah kayi haƙuri" Wani irin kallo yake mata, wanda sai da ta ji tsigar jikinta na tashi. Sauke idanunsa yayi, ya cigaba da cin abincinsa. "Ki dena kallona kar in ƙware". "Ai ba kallonka nake ba" ta faɗa a raunane. "Ya maganarmu ne?". "Wace Maganar?" Ya ɗago ya kalleta yace "ina tambayar ki, ki na tambayata?" Ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Abra talk" yayi Maganar in a cool voice, kamar ba shi ba. Shiru tayi bata amsa ba. Adnan yasa hannu ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna. Ya ɗan kashe mata ido yace "Yaushe zan zo gidanku in ga Major? Kinga ni ba ƙaramin yaro bane, ki dena mini wasa da hankali, ina ta binki amma kina mini wasa da hankali?" Tace "bakomai" A hankali ya saki haɓarta yace "muje mota, in baki wayarki, sai muje in ga gidan naku". "Za'ai mini faɗa a gida" "Ba za'ai miki faɗa ba, tashi muje". Gaba ɗaya Abra tsoron sa take ji, duk da tayi mamakin yadda yake Magana yanzu kamar ba shi ba. Haka ya sata gaba, zuwa cikin mota, a motar ya bata wayarta. Har bakin layinsu ya kaita, ya kalleta yace "Ranar Saturday zan zo insha Allah, ki shirya karɓa ta" Ba tace Komai ba, ta fara ƙoƙarin buɗe motar ta fita. "Wai ke ba ki iya godiya bane? Ko nace na sallameki ne?" "Nagode" ta faɗa tana tsoron kar wani ya ganta, dan ma motar tint ce. Yace "Well, a sauka lafiya Angel" da sauri ta waiwayo tana kallonsa. "In baki gama kallon nawa ba, sai in juyo" ba shiri ta buɗe motar ta fice, tana waige-waige kar taje wani ya ganta. Ihsan ce tai wani ɗan ihu tace "Janna, Baby kunga Mutumin nan ya rikice, wai Zai zo ya sameni, ko nawane zai sai videon in goge shi". Baby tayi dariya tace "A siyar masa a farashi mai tsada, sannan ki goge amma muna nan da shi ai, zai gane kuskuren sa, duk da ya saki kuɗi, da ba'ai haka ba, yanzu mu dai zamu fita, ki janyo shi nan, ya zo ki tatse mana shi. Haka suka cigaba da shewa, suna shawarwarin nawa zasu tatse shi. Suka shirya tsaf suka tafi nasu guri, suka bar Ihsan kawai tana jiran zuwan Yallaɓai. Su Janna basu koma ba sai bayan la'asar daga nasu gantali, Sai dai abunda suka gani ne ya girgiza su, cikin tashin hankali Janna ta ƙwala ihu, gawar Ihsan ce kwance a cikin jini! Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/1, 2:40 PM] Abk: jiki a sanyaye ta koma ɗakimta, tana zuwa ta zauna a bakin gado cikin confuse, kanta ya kulle gabaɗaya ta rasa tunanin ma me za ta yi. Salman kuma? Girgiza kai ta yi cikin sauri tare da faɗin. "Impossible! Faris ba zai taɓa mini wannan wasan ba, amma ko ma wanene ya san ni sosai." Latsa wayarta ta yi ta ƙura wa last message ɗinsa ido, kamar ta yi reply sai ta fasa ta ajiye wayar ta kwanta tare da lumshe idanunta. A hankali ya turo ƙofar ɗakin ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, bai jira amsarta ba ya ce. "Angel me ya faru ne?" Buɗe idonta ta yi tare da tura baki ba ta ce komai ba. Idanunsa a cikin nata ya ce. "Ko shagwaɓar ce ta motsa?" Harararar shi ta yi, ɗan murmushi ya yi ya ce. "Mami ce ta ce na kira ki." Da sauri ta tashi zaune ta ce. "Ni kuma?" Ya ce. "Eh, girki za ki ɗora." Ajiyar zuciya ta sauke tare da miƙewa suka fice tare. Zaune take akan ɗaya daga cikin royal chair ɗin dake parlour'n tana latsa wayarta, ta ci kwalliya cikin wani tsadadden farin less, idan ba faɗa maka aka yi ba za ka ce ta haifi Meenal ba saboda gayunta. Ɗaya daga cikin masu aikin gidan mai suna Asabe ce ta fito daga kitchen hannunta riƙe da plate, cikin sauri take tafiya har ta ƙaraso ta zube a gaban Hajiya. "Ranki ya daɗe Barka da yamma, ga wainar nan na kammala." Asabe ta yi maganar cikin ƙanƙan da kai. Wani wulaƙantaccen kallo ta ɗago ta wurga mata, cikin izza tamkar wata sarauniya ta ce. "Ubanki na ce ki dafa ne tun ɗazu ba ki gama ba sai yanzu?" Cikin kyarmar jiki Asabe ta ce. "Ki yi hak'uri Hajiya Saudat." "Dalla Malama tashi daga gabana, kafin ki kashe ni da warin ƙashi, Idiot kawai." Ta faɗa mata haka cikin tsawa. Ko gama rufe baki ba ta yi ba Asabe ta miƙe jiki a saɓule ta bar parlour'n. Ajiye wayar ta yi ta miƙe ta ɗauki plate ɗin ta haye upstairs. Meenal tana kwance akan gadonta na alfarma suna chatting da Usman Mahaifiyarta ta shigo ɗakin. Ɓata fuska Meenal ta yi ta ce. "Mommy sai yanzu?" "Sorry Daughter, tashi ki ci, ke ma da tsifa kike wallahi, duk abubuwan da ke gidan nan amma ki ce sai wata wainar fulawa za ki ci?" A shagwaɓe ta ce. "Ita kawai nake sha'awa ne Momy." "Ai gata nan." Hajiya ta faɗi haka tana ajiye plate ɗin akan bedside drawer, sannan ta juya ta fita ta koma ƙasa. Zamanta babu jimawa wani mai aiki a gidan ya shigo parlour'n, cikin respect ya gaishe ta, a wulaƙance ta amsa masa cikin yatsina fuska, sanar mata ya yi tana da baƙi. "Maza ne ko Mata?" Ta tambaya kamar ba ta san magana. "Mata ne." Ya amsa mata. Da hannu ta yi masa alamar ya shigo da su. Idanunta akan ƙofa bayan fitar Ilya ta ga waɗanda ba ta yi tsammani ba sun shigo, miƙewa tsaye ta yi da sauri cikin shouting ta ce. "What! Su waye waɗannan a cikin parlour na?" Iliya da ya yi musu jagora ya ce. "Su ne baƙin Hajiy...." Bai ƙarasa ba ta dakatar da shi cikin tsawa da faɗin. "Shut up! Wannan abubuwan za ka shigo mini da su har cikin parlour? Ubanwa ma ya ba su damar shigowa gidan nan har suka ƙetare main Parlor su shigo mini nan?" Kansa a ƙasa yana sosa kai ya ce. "Am Haji..." "Hajiya me? ashe ba ka da hankali Ilya ban sani ba? Tunda kake a gidan nan ka taɓa ganin mutane irin waɗannan sun zo gurina? Ko a bakin gate ɗin gidana ka taɓa ganin talaka yana shawagi?" Shiru Ilya ya yi bai ce komai ba, ƙwafa ta yi tana ƙara bin tsoffin matan da kallo cikin yatsina fuska kamar ta ga kashi. Ɗaya daga cikin Matan ne ta tsuguna akan gwiwoyinta cikin kuka ta ce. "Hajiya dan Allah ki yi haƙuri, neman taimako muka zo, ki taimaka mana kamar yadda Ubangiji ya taimake ki." Kallon sama da ƙasa ta yi mata cikin raini ta ce. "Nan ba gidauniyar taimako ba ne Malama, don haka ku tattara tsummokaran ƙafafuwanku ku bar mini parlour, kafin ku gama cika shi da wari da tsami. Mutane sai mutuwar zuciya, ba za ku fita ku nema ba sai yawon maula." Mtss ta ja tsaki tare da ɗaukar wayoyinta. Cikin gargaɗi ta kalli Ilya ta ce. "Ka fitar mini da su daga parlour kamar yadda ka shigo da su, ka jirayi hukunci kuma na shigo mini da matsiyata cikin gida da ka yi." Ba ta jira amsar shi ba ta shiga ƙwala kiran sunan Asabe da sauran abokan aikinta, jiki na rawa suka fito daga wani ɗaki dake cikin parlour'n, umarnin sake tsaftace parlour'n gami da saka masa turare ta ba su sannan ta haye sama, cikin izza da ɗagawa tamkar wata matar Shugaban ƙasa. Baby ce ta kalli Ihsan, da har zuwa wannan lokacin, tana kwance akan gado. A ɗan hasale Baby tace "waike Ihsan meye haka ne? Ki tashi ki shirya Abuja zamu tafi yanzun nan, cin uban wancan ɗan iskan". Ihsan ta yamutsa fuska tace "Wallahi Baby, haryanzu jikina na yi mini ciwo sosai, kin san na zubar da jini sosai". "To ai shiyasa dan ki fanshe wahalar ki, ya sa nace ku shirya mu tafi Abuja, bana jin Alhajin Janna Sosai, yana da sakin hannu, Amma shi wannan sojan nake son ki wankar mana, tunda mutumin banza ne shi, ga rowar tsiya, Wallahi ko mu ɗau tsiraicinsa muyi blackmailing ɗinsa". Ihsan tace "Wallahi tsoro nake ji Baby" "Au tsoro, kwanta zaki ga tsoro, dalla ki tashi ki shirya ba zaki sha wannan wahalar a banza ba, kuma idan muka je kar ki gaya masa an cire cikin nan kice kuɗi zai baki kije ki cire" Haka Baby ta sata a gaba, ta tashi tai wanka ta shirya, su uku suka hau motar Baby, suka nufi garin Abuja. Major ya kasa ya tsare, akan Lallai a tsananta bincike a gano, dalilin mutuwar sojojin nan da ake tuhumar yadda hatsaniya ta ɓarke, har sukai faɗa a tsakaninsu, amma abubuwa gaba ɗaya sun cakuɗe, an hargitsa abubuwan, yadda Binciken zai bada wahala, wanda duk plan ɗin General Ibrahim ne. Ba tare da an samo bakin zaren ba, a dole Abbi ya shirya komawa gida. Washegari ya kama Saturday, around 3pm bayan Abra ta gama ayyukan gida tana kwance akan kujera 3 seater tana browsing wani assignment da aka ba su a wayarta, Na'ima da Khamal suka shigo cikin parlour'n. Idanun Abra akan wayarta ta amsa musu sallamar da suka yi tare da gaishe su, saboda hankalinta gaba-d'aya yana kan assignment ɗin, so take ta yi ta gama dan yana da wahala, gashi kuma da yawa. Dinning area su Na'ima suka ƙarasa, Khamal ya zauna ta fara zuba masa lafiyayyen abincin da Abra ta girka. Bayan ta gama ta saka masa spoon ta saci kallon Abra ta ce. "Man, ban san me yake damun Daughter ba, yanzu ta koma always busy with her phone." Cikin rashin damuwa Khamal ya ce. "Kin manta yanzu yar jami'a ce ita? Ai dole sai tana fama da browsing da karatu kodayaushe." "To me yasa Salman shi ba ya haka?" Ta tambaye shi tare da zama a kusa da shi." "Ta fi shi serious ne." Cikin takaicin abun da Khamal ya faɗa ta ce. "Gaskiya ban yarda ba, yarona ma babu lefi, abun da na fi tunani kawai ita da akwai abun da take yi a wayar bayan karatun." Khamal ya dakata da cin abincin da yake ya ce. "Ban fahimce ki ba, me kike nufi?" Duk da Na'ima ta tsorata da yanda ya tsare gida amma ta dake zuciyarta ta ce. "Ni nake zaune da yaran nan kodayaushe a gida, kuma duk wani motsin su a kan idona yake, ta haka na gane yawan amfani da waya da Abra take yi, koda yaushe waya tana hannunta, har cikin dare idan na je duba ta ina hango hasken screen ta cikin blanket ɗinta, alamun ba bacci take ba waya take latsawa. Yanzu ma ka lura fa da muka shigo, ko ɗauke idonta daga kan wayar ba ta yi ba." "Shi ne me? Ba ki ga papers ɗin dake gabanta ba, may be tana discussing something important related to her study ne, wanda yake buƙatar full attention ɗinta akai." Cikin baƙin cikin rashin sanin haɗin kai Na'ima ta ce. "Haka ne, ni ma ba wani abun nake nufi ba, kawai ina so a bincika ne in ma wanin abun ne a yiwa tufkar hanci tun wuri." "Babu ma komai, na san tarbiyyar da na bawa yarana, na kuma yarda da su, dan haka ki daina irin wannan tunanikan, just pray for them, Allah ya kare mana su daga aikata dukkan wani abu mara kyau." Cikin yaƙe ta ce. "Ameen Mijina." Khamal ya cigaba da cin abincinsa, yayin da Na'ima ta shiga saƙe_saƙen yanda za ta ƙara ɓullo masa, akan makircin da take son ƙulla wa Abra. Ba ƙaramin baƙin ciki ta ji ba a yanzu da ya ƙi bawa maganarta muhimmanci, ta so ya karɓi wayar ya ga abubuwan da ta tura a ciki, ba tare da ita kanta Abran ta san da su ba, ta san idan ya gani kashe Abra ne kawai ba zai yi ba, saboda yanda ta san shi da takatsantsan da tarbiyya akan Ƴaƴansa. Cikin kwanikan nan da suka wuce mai turawa Abra text na love messages bai fasa ba, duk da ba kowanne take reply ba, saboda ta yi ta yi ya faɗa mata wane ne shi ko ya tura mata pics ɗinsa amma ya ƙi. Sai dai ta rasa me ya sa idan ta ga message ɗinsa take jin nishaɗi a cikin zuciyarta, ba ta gajiya da karanta messages ɗin nasa ko kaɗan, har ta haddace lokutan da yake tura mata, idan ya ƙara mintuna bai turo ba ta dinga duba wayarta kenan, tana jin vibrate za ta duba da sauri, idan shi ne ta buɗe ta karanta cikin sauri, idan kuma Company ne ta yi tsaki ta ajiye wayar. Yau Monday, misalin ƙarfe bakwai da rabi Abra ce tsaye a gaban mudubin ɗakinta tana gyara rolling ɗin mayafin abayar dake yane a kanta. Wayarta dake kan mudubin ta yi vibrate alamar shigowar saƙo. Ɗauka ta yi ta duba, ganin Mr unknown ya sa ta buɗe da sauri ta fara karantawa. "God Morning My Angel, da fatan kin tashi lafiya? Na san yanzu kina shirin tafiya school, Allah ya kiyaye hanya ya ba da sa'a, have a nice day Princess!" Murmushi ta yi a saman leɓɓenta tare da lumshe ido ta buɗe, zuciyarta cike da son ganin Mr unknown ɗinta. "Yaushe zan gan ka? A ina zan gan ka? Mutum ne kai ko Aljan da kake sanin duk wani moment ɗina?" Ta tambayi kanta a hankali tana kallon fuskarta ta cikin mudubi, still tana murmurshi. "Angel!" Muryar Salman da ba ta san time ɗin da ya shigo ɗakin ba ta doki kunnenta. "Na'am Faris." Ta amsa tare kallon shi. Wani irin kallo yake bin ta da shi bai ce komai ba. "Wannan kallon fa? Mu je in ka gama shiryawa, dama kai nake jira." "Kin yi kyau sosai kamar na sace ki." Ya faɗa cikin siririyar murya. Tana murmurshi ta ce. "In ka sace ni Salman ka kai ni ina?" "Gidana." Ya ba ta amsa cikin confidence. Jinjina kai kawai ta yi ba tare da tunanin komai akan maganar tasa ba, ta ɗauki jakarta tana shirin fita Salman ya ce. "Where is your facemask?" "Yau ba zan saka ba gaskiya, damu na yake yi." Dan haɗe rai ya yi ya ce. "Ki saka, yana ina in ɗauko miki." Cikin shagwaɓa ta ce. "Ka fiya takura Faris, don Allah ka ƙyale ni." Bai kula ta ba ya janyo drawer inda ya san tana ajiyewa ya ɗauko sabo ya miƙa mata. Da farko ƙin karɓa ta yi, sai da ta ga kamar ransa ya ɓaci sannan ta karɓa, cikin marairaicewa ta ce. "Ka yi haƙuri Bro zan saka." Ɗauke kai ya yi alamun he is angry with her. "Zan saka fa, Please kar ka yi fushi, ka san bana iya jurar fushinka." Ta yi maganar kamar za ta yi kuka. Sakin fuskarsa ya yi ya ce. "Ya wuce cry cry Baby, kawo in saka miki ma da kaina, sai ya fi yin kyau." Ba ta yi musu ba ta miƙa masa. Idanunsa a cikin nata yana narkar da su ya saka mata, bayan ya gama ya kashe mata ido ɗaya tare da sakar mata wani tattausan murmushi. Turo baki ta yi ta ja karan hancinsa da ƙarfi, ta ce. "Gashi nan ka lalata mini rolling ɗina." "I'm sorry the best among the best." Ya faɗa cikin kulawa. Na'ima ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, cikin faɗa ta ce. "Ba za ku makarantar ba ne? Kun tsaya kuna shiririta ko? Tun ɗazu driver yana jiran ku." "Ga mu nan fa Mami." Cewar Salman. Harararar shi ta yi ba ta ce komai ba ta juya ta fita. Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. Kamar kowacce Monday yau ma around 12 su Abra suka tashi, ta zauna a inda ta saba jiran Salman tana tsimayin shi. Shiru-shiru har 1 ta wuce bai zo ba, wata irin yunwa Abra ta ji tana ƙwaƙular hanjin cikinta. Cikin ƙosawa da zaman gurin ta ɗauko wayarta ta kira shi, har 3 missed call ta yi masa amma bai ɗaga ba. Miƙewa ta yi dan a yanda take jin yunwa ba za ta iya jiran har ya zo ba tare da ta ci abinci ba, Cafeteria ta nufa direct cikin tafiyarta mai tattare da nutsuwa da ɗaukar hankali. Bayan ta zauna ta yi order'n abun da take so ta ɗauko wayarta ta fara latsawa kafin a kawo mata. Haka kawai ta ji ta a takure tunda ta zauna a gurin, gyara mask ɗin fuskarta ta yi, ya rufe mata har saman hancinta, kyawawan idanunta ne kawai a waje. Duk da haka ba ta ji ta daidai ba, ɗago kanta ta yi a hankali tana kallon mutanen gurin, Cafeterian da ɗan jama'a amma kowa sabgar gabansa yake yi. Duk yadda ta so daurewa amma ta kasa, wani irin ido mai kaifi ta ji yana yawo a cikin jikinta alamun akwai wanda yake kallon ta. Slowly ta juyar da kanta gefe, lokaci ɗaya wani irin daddaɗan ƙamshi mai saukar da nutsuwar zuci ya ziyarci hancinta, ba ta san lokacin da ta lumshe idonta ta buɗe ba, ƙamshin ya yi mata kamar ta taɓa jin shi. Wata irin faɗuwar gaba ce ta ziyarce ta, lokacin da ta tsinci idanunta a cikin mutumin da ba ta taɓa tunanin sake ganin shi ba, ta ma manta da shi gabaɗaya a cikin rayuwarta. Cikin sakanni ƙwaƙwalwarta ta tuno mata inda take jin ƙamshinsa, a jikin i.d card ɗinta ne, tun ranar da ya ba ta har yau ƙamshinsa yana nan manne a jikinsa. Sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tare da saurin janye idanunta daga cikin nasa, wani irin abu ta ji yana yi mata yawo a jinin jikinta, gabaɗaya sai ta rasa nutsuwar zuciyarta ba tare da ta san dalili ba. Juyar da kanta ta yi daga ɓarin da yake, cikin ƙoƙarin daidaita nutsuwarta gudun kar a gane yanayin da take ciki. Wayarta dake hannunta ce ta fara vibrate, dubawa ta yi ta ga Salman ne yake kiran ta. Jikinta ne ya hau rawa, ta kasa ɗaukar wayar, saboda wanda ta gani ya ja kujerar gabanta ya zauna. Kamar kullum, yau ma kasa ɗaga idanunta tayi ta kalleshi, sai wani irin bugu da zuciyarta keyi, tamkar zata tsaga ƙirjinta ta fito. Dubansa ya kai kan screen ɗin wayarta, yaga sunan Faris akan screen ɗin. Ɗan taɓe baki yayi, a daidai lokacin kuma aka kawo mata Abincin da tayi order, aka ajiye a gabanta. Sai dai haryanzu ta kasa ɗago kanta, sai wasa da take da yatsun hannunta. "Eat your food, i have something to discuss with you" yai Maganar yana tura mata plate ɗin Abincin gabanta. Kamar gunki haka Abra ta zama, gashi da ƙyar take numfashi, saboda tsoro ga uban facemask a fuskarta, gefe ga Salman na ta rangaɗa mata kira, ba ƙaƙƙautawa. "I said you should eat your food, zamu yi magana sauri nake". Ɗago fararen idanunta tayi ta kalle shi, karaf ta sanya idanunta cikin nasa, saurin janye nata ta yi daga nasa. Yayin da shi kuma ya cigaba da kallon ta yana nazartar ta. Ya ɗan fesar da iskar bakinsa ya ce "Well, tun da ba zaki ci Abincin ba, ni bari inyi abunda ya kawo ni, ina da abun yi." Abra a ranta ta ce "Ikon Allah". "I am Sp Adnan Aliyu Matawalle, so na san maybe na takura miki, saboda yawan bibiyar ki da nake yi. So ni ba yaro ne ƙarami, ba shiririta ce ta kawo ni gurinki ba. Amm ina tunanin ina son mu kasance ƙarƙashin inuwa guda dake, duk da bai kamata in tunkare ki kai tsaye in sanar da ke ba, sai na nemi iznin mahaifinki, ina son zan Aure ki ne, idan ba damuwa ina son ki bani Address ɗin gidanku, zan zo". Zaro ido ta yi, tare da jin wata mummunar faɗuwar gaba, ta ina zata fara kai shi gidansu? Tukuna ma haka ake neman Aure ba soyayya ba komai, sai kace dole?". "Kin yi shiru" In a cracking voice ta ce "Ni karatu zan yi, Abbinmu zai mini faɗa". "Kina nufin ba zaki yi Aure ba kenan?". "Ni dai gaskiya Abbi zai mini faɗa". "Ai Abbin naki zan fara samu, ni zan same shi". Shiru Abra ta yi, ba ta sake cewa komai ba. "Bana son ina magana ayi banza da ni, ki bani Address ɗin, ina sauri zan koma Kaduna ne". Shiru ta kuma yi, ba tace komai ba. Kallon wayarta dake sake vibrating ya yi, ya miƙe tsaye ya sa hannu ya ɗau wayar da ID card ɗinta, ya watsa su a aljihunsa yace "Idan kin shirya, kya iya nemana, sai ki karɓi wayarki" "Dan Allah ka bani wayata" Banza yai mata ya nufi hanyar fita daga gurin. Miƙewa ta yi domin ta bishi, tana bin shi tana masa magiya, amma ko waiwayowa bai yi ba, ya buɗe motarsa ya shige, ya ja ya bar gurin. Abra ji tai kamar ta ɗora hannu a ka ta kurma ihu, ita yanzu ina zata sake ganinsa? Gashi ta ji yace Kaduna zai tafi. A hankali tace "Wayyo Allah wayata, me zance a gida?". Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/1, 2:40 PM] Abk: A gigice Baby ta cillar da jakar hannunta, cikin waro ido ta kurma wani uban ihu tare da ficewa daga ɗakin hotel ɗin a ruɗe. Ƙarasawa Janna ta yi ta shiga girgiza ƙafar Ihsan cikin kuka da tsananin tashin hankali. Ɗaya daga cikin ma'aikatan hotel ɗin ne ya hawo sama da sauri jin kururuwar Baby. "Hey, Lafiya kike mana wannan kwakwazon?" Kasa magana Baby ta yi, nuna masa ɗakin kawai take yi da hannu tare da toshe bakinta. Shiga ɗakin ya yi cikin sauri, cak ya tsaya tare da dafe ƙirjinsa cikin firgici. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un!" Abun da ya furta kenan a fili idanunsa akan gawar Ihsan dake kwance cikin jini malel-male. Da sauri ya juya ya fita ya je ya sanar da Manager na hotel ɗin abun da yake faruwa. After some minutes Su Janna ne zaune a police station mafi kusa da hotel ɗin, idanuwansu sun yi luhu-luhu alamun sun ci kuka sun gode Allah, sai zazzare idanuwa suke yi cikin firgici. D.p.o dake bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya ya dubi wani jami'i ya ba shi  umarnin ya shigar da Janna cikin cell, kuka ta fara tare da yi masa magiya tana ba shi haƙuri, tsawa ya daka mata wanda ta sa su duka suka razana, ba shiri ta yi shiru ta shiga jujjuya kai. Tasa ƙeyarta jami'in ya yi har cikin cell. "Ki nutsu, tambayoyi zan miki, kuma ki faɗa mini gaskiyar abin da kika sani, domin idan ma kin mini ƙarya zan gano daga baya, kuma hakan ba zai haifar miki da ɗa mai ido ba." Cewar D.p.o yana kallon Baby da jikinta ke tsuma. "In...insha Allahu zan faɗa maka gaskiya yallaɓai." "Good." Ya faɗa cikin gyaɗa kai. "Mene ne alaƙarki da wacce aka kashe?" "Ƙawata ce." Jinjina kai ya yi ya ce. "Tsawon wane lokaci kuka ɗauka tare? Kuma a ina kuka haɗu?" "4 Years back, a makaranta muka haɗu, A.b.u Zaria, course ɗinmu ɗaya da ita." "Okay, shi ne aka haɗa baki dake kenan aka kashe ta?" Cikin kuka Baby ta ce. "Wallahi ba haka ba ne Yallaɓai, ba ni da masaniya akan kisan Ihsan, ta yaya ma za a haɗa baki da ni a kashe ta? Ƙawata ce fa." D.p.o ya ce. "Ku ƴan wanne gari ne?" "Dukanmu ƴan Kaduna state ne." "Kaduna? Amma me ya kawo ku Abuja?" Shiru Baby ta yi ta fara sosa kanta tana rarraba idanuwa. "I'm toking to you my friend." Ya faɗa cikin tsawa. Zabura ta yi ta ce. "Mun zo ganin wani mutumi ne?" Ya ce. "Wane wanin? Daga Kadunan kuke yanzu?" "A'a, muna zaune a school hostel ne, daga can muka zo nan." Jinjina kai ya yi cikin nazartar ta ya ce. "Okay, cigaba da bayani, gurinwa kuka zo?" Cikin rawar murya ta ce. "Wani tsohon Soja ne, ita ƙawar tamu da aka kashe muka rako nan Abuja, don ta gana da shi akan wani abu." Tattara hankalinsa gabaɗaya D.P.O ya yi a kanta ya ce. "Wanne abu ne wannan da kuka taho tun daga Kaduna har Abuja saboda kawai su yi magana a kansa?" Baby tana hawaye ta ba shi labarin duk abun da ya faru tsakanin Ihsan da General Ibrahim, ganin ba ta da mafita, kuma tana son ta kuɓuta daga zargin su da ake yi. D.P.O ya ce. "Kin tabbata abun da kike faɗa mini gaskiya ne?" "Wallahi gaskiya ne ranka ya daɗe, kuma dalilin da ya sa ma ba mu fita tare da ita ba saboda zai zo su haɗu a lokacin." D.P.O ya ce. "Kuna da tabbas ɗin ya zo sun haɗun bayan kun fita? Kuma menene shaidar ku akan abun da kika faɗa." A raunane Baby ta ce. "Eh, lokacin da ya zo ta kira mu ta sanar mana zuwansa cikin murna, dan muna tunanin ya zo ya ba ta kuɗin da muka nema ne daga hannunsa, shaidar kuma akwai short video na tattaunawarsu ita da shi akan cikin jikinta a cikin wayoyinmu, wanda muka yi masa barazanar da shi." Numfashi D.P.O ya sauke tare da shafa kansa ya ce. "Ya sunan shi Sojan?" "General Ibrahim A.M" "What? General Ibrahim A.M? Are You sure?" Ya tambaya cikin shock. Gyaɗa masa kai ta yi cikin tabbatarwa. Girgiza kai ya yi ya ce "Oh My God!" Duban jami'in da ya kai Janna cell ya yi ya ce. "Officer." "Yes sir." Ya faɗa tare da ƙamewa. "Ka shigar da wannan ciki ka fito ɗayar." A ruɗe Baby ya ce. "Yallaɓai dan Allah ka sallame ni tunda na faɗa maka gaskiyar abin da ya faru, wallahi ba mu muka kashe ta ba, ba mu.." "Shut up, tashi mu je." Officer ya buga mata tsawa da faɗin haka. Kuka ta fashe da shi tare da miƙewa ta yi gaba. Exactly abun da Baby ta faɗa shi Janna ta faɗawa D.O.P, bayan ta gama yi masa jawabin ya bayar da umarni aka kawo masa wayoyinsu da aka karɓa, ya cewa Janna ta ɗauki tata ta cire key ta nuna masa videon tattaunawar Ihsan da General Ibrahim. Da wannan damar Janna ta yi amfani ta ɗora videon a social media in seconds, sannan ta miƙawa D.P.O wayar. Bayan ya gama kalla ya dubi wani police dake tsaye a gabansa ya ce. "Inspector, a cigaba da tsare yaran nan har zuwa lokacin da za mu gama bincike, sannan a je a taho da General Ibrahim A.M, yarinyar da aka kashe kuma a san yanda za a yi iyayenta su samu labari, and lastly aje a zo mini da Manager na hotel ɗin da abun da ya faru a ciki yanzu, a kuma bincika CC TV camera domin a tabbatar da General Ibrahim ya je hotel ɗin a yau ko akasin haka." "Done Sir." Inspector ya faɗa tare da sara masa. Bayan ya fita D.O.P ya dubi Janna dake ta kuka ta ce. "Wannan ya isa ya zama izna a gare ku da masu hali irin naku, yara ƙanana da ku iyayenku sun tura ku karatu amma kuna irin wannan rayuwar, yanzu wa gari ya waya? A misali idan General ɗin ne ya kashe ta hakan ya isa ku gane ba ku da wata daraja da ƙima a idanun irin waɗannan Mazan da kuke bi, ba su ɗauke ku a bakin komai ba, sun mayar da ku kamar ledar pure water saboda yawan da kuka yi a gari. Ya kashe ta ne saboda ya tsira da mutuncinsa kar abun da yake aikatawa ya fito fili, kuma a lokacin da ya kashe tan yana fita idan ya haɗu da wata ɗaukarta zai yi ya je ya sheƙa ayarsa da ita hankali kwance, ita kuma wannan ya gama da ita, da ita da Dabba duk matsayinsu ɗaya a gurinsa. Ina baki misali ne kawai ba wai ina faɗa dan ya aikata ba, dafatan kin fahimta?" Janna da kanta ke ƙasa tana hawaye ta gyaɗa masa kai. Girgiza kai ya yi cikin takaici ya ce. "Allah ya shirya." Sannan ya bayar da umarnin a mayar da ita ciki. General Ibrahim A.M ne zaune a gaban kujerar gaban table ɗin D.O.P, cikin shiga ta kamala, ba zaka taɓa cewa shi yake aikata baɗala da Ƴaƴan cikinsa a bayan fage ba. Bayan sun gaisa cikin ƙwarewar aiki D.P.O ya ce. "General, muna son za mu yi maka wasu ƴan tambayoyi ne a kan kisan wata yarinya da aka yi mai suna Ihsan Sadam Malali a Aminci Hotel."  Damm zuciyar General Ibrahim ta buga, amma da yake cikakken ɗan duniya ne kuma ya san ta kan harkar bincike sai ya ce. "D.P.O ni kuma? Wacce yarinya ce wannan? Me ya sa kuka gayyato ni akan kisan ta? Ba na jin ko a cikin familynmu akwai mai sunan da ka ambata balle na yi tunanin ko ina da wata dangantaka ta jini da ita, Ihsan ka ce ko wa?" Cikin nazartar shi D.P.O ya ce. "Bari ka ga hotonta, na san idan ka gani may be ka shaida ta." Bai jira cewar shi ba ya ɗauki wayarsa ya latsa sannan ya nuna wa General Ibrahim pics ɗin fuskar Ihsan da ya cika screen ɗin wayar. Ƙarɓa ya yi ya duba, cikin ɓoye razanin da zuciyarsa take ciki ya ce. "Gaskiya ban san wannan yarinyar ba D.P.O." "Ko?" D.P.O ya faɗa tare da karɓar wayarsa. "Ina jin mistake kuka yi ba ni za ku kira ba." "Kai kuwa za mu kira, saboda bincikenmu ya tabbatar mana da a guest house ɗinka yarinyar ta sauka ita ƙawayenta shekaran jiya." Cikin maziya General Ibrahim ya ce. "Eh hakan zai iya yiyuwa, saboda akwai abokaina da dama da suke saukar baƙinsu a gidan ba tare da na sani ba, because mun zama ɗaya na yarje musu hakan. Cikin gyaɗa kai D.P.O ya ce. "General please kar ka wahalar da mu ka wahalar da kanka, ka amsa kawai ka san yarinyar nan, in yi maka tambayoyin da zan yi maka, that is all." "A'a fa, ban san ta ba zan amsa na san ta ne? Da kuka kira ni in zo akan abun da ban sani ba na yi muku musu? Na taso na zo duk da ina gaba da ku a matsayi da miƙami, amma saboda ina girmama kaki da mahukunta ya sa na zo cikin salama ba tare da jayayya ba." General ya faɗa cikin harzuƙa. "Akan aikina nake General, kuma sanin kanka ne babu ruwan doka da wani muƙami ko matsayi, idan abu ya biyo ta kan mutum ko waye shi dole a tuhume shi, but ba wannan ne a gabanmu ba yanzu, let me show you something." D.P.O ya faɗi haka tare da ƙara ɗaukar wayarsa a karo na biyu. A ɗarare ta shiga gida zuciyarta cike da tsoron Na'ima, kasancewar Major ba ya gari. Allah ya taimake ta Na'ima ba ta main Parlor tana ɗakinta, ajiyar zuciya ta sauke ta shige ɗakinta. A bakin gado ta zauna tare da ƙurawa wayarta ido, sai dai a zahiri ba wayar take kallo ba, tunanin wanda ya ba ta wayar da kasancewar da suka yi tare na wasu mintuna take tunawa. Har yanzu zuciyarta ba ta daina bugawa ba, ta tsorata sosai da farko, dan wannan ne karo na farko da ta taɓa daɗewa tare da wani Namiji bayan relatives ɗinta. Sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tare da kai wayarta kan hancinta ta shaƙi ƙamshinsa, tun a jikin i.d card ɗinta ta ji tana son ƙamshin, sometimes idan za ta kwanta bacci sai ta ɗauko ta shinshina. Mr unknown ne ya faɗo mata a rai, da sauri ta latsa wayar ta cire password tare da cire ta daga Flight mode ɗin take, kamar jira ake messages suka dinga shigowa. Hannunta har rawa yake wajen dannawa ta buɗe ta karanta. Messages ɗinsa ya kai 15 ta gani, duk na yanda yake tsananin son ta ne da missing ɗinta da ya yi, a ƙarshe kuma sai ya roƙe ta akan ta taimaka ta yi masa reply koda da "Okay" ne, dan ya ji daɗi a cikin ransa. Murmushi ta yi ta tura masa da. "Hey, How are you." Message ɗin yana tafiya kira ya shigo cikin wayar da sabuwar Number, kallon special Numbern ta tsaya tana yi, sai da ta kusa katsewa sannan ta yi pick. "Assalamu alaikum." Wata murya mai cike kamala da daɗin sauti ta doki kunnenta. Sai da gabanta ya faɗi jin muryar wanda ba ta za ta ba, lumshe ido ta yi a hankali tare da gyara zama ta amsa masa cikin sassanyar muryarta. "Na kasa cigaba da driving a dalilin kyakkyawar fuskar matata dake ta mun gizo gami da tunaninta da ya addabi zuciyata, shi ya sa na kira ki don na samu nutsuwa, i hope kin shiga gida lafiya?" Ya yi maganar cikin wani irin salo da ya ratsa zuciya gami da ko'ina a jikinta. Shiru ta yi ta rasa me za ta ce, jin al'amarin take wani mai girma a kanta. "Ba na son ina magana ana ji na a yi shiru" Ya faɗi haka a ɗan kausashe kamar ba shi ya gama magana cikin kulawa yanzu ba. Turo baki ta yi kamar yana gabanta ta ce. "I'm sorry, ban san me zan ce ba ne." Murmushi ya yi mai sauti ya ce. "Just say I love you My husband." Waro ido ta yi ba ta ce komai ba. Ya ce. "I'm waiting for you Madam." Nan ma shiru ta yi sai sauke numfashi kawai take yi. Murmushi ya ƙara yi ya ce. "Okay bye, thank you, take care of yourself." Bai jira amsar ta ba ya kashe wayar. Ajiyar zuciya ta sauke tare da zare wayar daga kunnenta. sai ta tsinci zuciyarta da blaming kanta, kamar ba ta kyauta masa ba da ta yi shiru, to amma me za ta ce masa? Ita fa jinta take duk a takure, ga wani kwarjinin da yake yi mata, ga kunyar shi da take ji duk ita kaɗai. _Adnan_ ta ambaci sunansa a cikin zuciyarta, sunan ya yi mata daɗi ba kaɗan ba. Lumshe idanunta ta yi tana hango yanda yake magana cikin nutsuwa yana motsa ƙananun lips ɗinsa kamar ba ya son maganar ko wanda aka yiwa dole. Murmushi ne ya kufce mata ba tare da shirya yin sa ba, saboda tuno kyawawan fararen idanuwansa da yake tsare ta da su. "Angel!" Salman ya faɗa da ɗan ƙarfi lokacin da ya shigo ɗakin yana ƙare mata kallo. Da sauri ta buɗe idonta cikin ƙoƙarin daidaita nutsuwarta. "Me ya sa kika taho ba tare da kin sanar mini ba?" Kalar tausayi ta yi ta ce. "I'm sorry bloody, bayan na baro class ɗinku na ji ina son shiga toilet, kuma ka san i can't use toilet ɗin school, that is why na taho gida." Ajiyar zuciya ya sauke ya ce. "Shikenan, amma kin ɗaga mini hankali sosai, kin san irin neman da na yi miki kuwa?" "Sorry sweet Bro, ka je ka huta bari na tashi na haɗa maka delicious yanzun nan." Murmushi ya yi ya ce. "Baby girl, shi ne kika zo kika ba ni kunya a class." Cikin shagwaɓa ta ce. "Kunyar me kuma Faris?" "Ba ta komai, ni abun da ya fi ba ni haushi yanda ake ta tanka ki, bayan mun fito harda masu cewa in ba su contact ɗinki wai kin burge su." Ya ƙarashe zancen tare da jan tsaki. Murmushi kawai ta yi, ta rasa me ya sa Salman yake mata haka? Ba ya so ya ga maza suna kallon ta ko su yi mata magana, yanzu zai shiga ɓaɓɓata rai da jan tsaki. Lallaɓa shi ta yi ya sauko daga kumburin da yake, ta nuna masa an ba ta wayarta yau, taya ta murna ya yi sannan suka fita tare, ta shiga kitchen shi kuma ya yi ɗakinsa. Ba ƙaramin firgicewa General Ibrahim ya yi ba da ganin wannan videon, wani irin gumi ya shiga tsatstsafowa a jikinsa. D.P.O dake karantarsa ya ce. "Zaka ce ba kai ba ne wani ne ya yi amfani da fuskarka? Wannan ƙaryar da ka yi ta ƙara sanya mini zargi a kanka." General dai kasa magana ya yi, sai goge zufa yake yana zare ido. D.P.O ya janyo laptop ɗin dake gabansa ya yi yan danne-danne sannan ya juya ta yanda za ta fuskanci General Ibrahim, bai ce komai ba sai wani kallo da yake bin sa da shi. General Ibrahim ya ɗaga ido daƙyar ya dubi laptop ɗin, videon lokacin da ya shiga reception ɗin Aminci Hotel ne. "Wannan ma ko za ka musa ne? Ka saka facemask a lokacin dan ka yi badda kama, ma'aikacin hotel ɗin ya buƙaci ka buɗe fuskarka ya gan ka, sai ka ba shi cin hanci na 20k dan ya ƙyale ka wuce ka je ka kashe ƴar mutane. A matsayinka na babban jami'in tsaron ƙasa, wanda ƙasa take alfahari da kai." "Haba D.P.O ya zaka dinga alaƙanta ni da abun da ban sani ba? Ni fa ba ni ba ne wannan da kake magana akansa." General Ibrahim ya faɗi haka cikin borin kunya zuciyarsa na tsananta bugu. Miƙewa D.P.O ya yi ya ce. "Idan mun je gaba ka yi musu duk wannan bayanin." Bai jira cewarsa ba ya ƙwallawa Inspector kira, bayan ya shigo ya ce masa. "Ku tafi da shi headquarter tare da ƴan'matan nan, I.G yana jira, ya ce a mayar da case ɗin can, i will fallow you back. Kafin dare labarin kisan Ihsan da videon da ta ɗauka nasu ita da General Ibrahim ya gama zagaye ƙasa da kewaye, duk inda ka je zancen ake yi. Al'amarin ya girgiza manyan ƙasa da Sojoji waɗanda suka san General Ibrahim, saboda yadda yake nuna shi na Allah ne akan komai, da yawa ba su yi tunanin zai aikata hakan ba. Kwance yake akan gadonsa ya mimmiƙe baƙaƙen ƙafafuwansa, wata mata wadda da alama Matarsa ce tana yi masa tausa. Taba ce a hannunsa yana ƙarawa sama hazo daga kwancen da yake. Wayarsa dake gefensa ce ta shiga ruri, tsaki ya yi cikin maganar riƙaƙƙun ƴan daba ya ce. "Ba za a taɓa barin mutum ya huta ba." Ɗaukar wayar ya yi ya ɗaga ya kara a kunne, sai da ya zuga ya fesar sannan ya ce. "Ina jin ka ya aka yi ne? Kira da sakaliyar yammar nan?" "Ban gane in hau WhatsApp za ka tura mini abu ba, kawai ka faɗa mini, ka san ni yanar gizon nan ba wani gane mata nake ba." "To na ji, tunda ka dage zan hau." Ya ƙara jan tsaki sannan ya katse wayar. Yana ƴan mintocinsa ya siyi data ya kunna ya shiga WhatsApp. Wani uban ihu ya kurma tare da yar da wayar a ƙasa, cikin zafin zuciya ya cillar da tabar hannunsa tare da narka wani uban ashar ya ce. "Yata Ihsan ɗin aka kashe? Sannan kuma wancan tsohon matsiyacin gajeren Sojan ake zargi? Bayan ya gama lalata da ita? Taɓdi jan, Ibrahim ya deɓo ruwan dafa kansa, wallahi, wallahi, wallahi sai na ɗauki fansar jinin ƴata." Aruɗe mahaifiyar Ihsan ta miƙe cikin ƙaraji ta ce. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Mai gida me kake cewa ne? Ban fahimta ba, wacce Ihsai ɗin aka kashe? Ba dai yata ba?" "Ita fa Rabi, wai tun rana abun ya faru, ana ta kiran wayarmu daga ni har ke ba a same mu ba. An taɓo tsuliyar dodo Rabi, za a yi yaƙin da ba a taɓa yin kamar shi ba a duniya wallahi." Rabi da ba fahimtar abun da yake cewa take ba ta ɗauki wayar da ya cillar cikin rawar jiki ta latsa, videon gawar Ihsan da bayanin abun da ya faru ya bayyana, ƙara ta fasa tare da zubewa a ƙasa sumammiya. Na'ima na zaune a parlour ita kaɗai tana kallo wayarta ta fara ringing, murmurshi ta yi tare da ɗagawa. "Hello Hajiya Maryam ya ake ciki ne?" Daga ɗaya ɓangaren Hajiya Maryam ta ce. "Komai ya kammala ƙawata, ba dai level 1 take ba department of Mass communication?" Da sauri Mami ta ce. "Nan ne." "To ki kwantar da hankalinki tamkar tsumma a cikin randa, wanɗanda na bawa aikin nan ba ni da haufi a kansu, gwanaye ne, ba su taɓa aiki an samu matsala ba, ke dai kawai da zarar aiki ya cika ki cika musu aljihunsu da ƴaƴan banki." "Ba su da matsala da wannan, kin san kuɗi ba damuwata ba ne, ni dai kawai buƙatata ta biya, tsinanniyar yarinyar nan ta bar mini gida ko na huta, haba na gaji, na yi makircin na yi amma har yanzu ban ci nasara ba?" "To daga wannan karon kin gama cizan yatsa ƙawata." Murmushi Na'ima ta yi ta ce. "Da kuwa na zuba ruwa a ƙasa na sha." Maryam na dariya ta ce. "Ko acikin kwata ne ma ki zuba ki sha, duk a cikin celebration ne." Dariya suka yi a tare cikin tsananin farinciki. Washegari 8 Salman yake da lecture, Abra kuma sai 10 hakan ya sa ba su tafi tare ba. Ƙarfe 1 Salman ya fito daga lecture, bayan ya yi Sallah ya nufi department ɗin su Abra, ya jira har ƙarfe biyu suka fito daga lecture. Yana tsaye a bakin class dinsu yana zuba idon ganin ta, amma har kowa ya gama fitowa bai ga ko mai kama da Abra ba. Cikin mamaki ya shiga dudduba cikin department ɗin nasu amma bai gan ta ba, ya kira wayarta ya fi sau 20 ba a ɗauka ba. Hankali a tashe ya kira Na'ima ya tambaye ta ko Abra ta dawo gida? Sanar masa ta yi tana zaune a main parlour tun 12 amma ba ta ga shigowar Abra ba, direbansu ya kira ya tambaye shi ko Abra ta kira shi ya zo ya ɗauke ta? shi ma ya ce masa ba ta kira shi ba. Hankalin Salman idan ya yi dubu ya tashi, duk inda yake tunanin zai ga Abra ya duba amma bai gan ta ba, ya tattambayi classmates ɗinta amma duk amsar ɗaya ce ba su gan ta ba, majority ma ce masa suke yi ba su san ta ba, tunda kullum cikin facemaks take. University ba secondary school ba, balle ya yi report ya ce bai ga Abra ba, to wa ma zai yiwa report ɗin? Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/1, 3:01 PM] Abk: Ƙara rikicewa Abra tayi, ganin yadda ya tayara da motarsa ya bar gurin. Gaba ɗaya ta rasa abunda yakamata tayi a gurin nan, ihu za tayi ko kuka za tayi? Bata koma gurin cin Abincin nan ba, ta nufi department ɗin su, tana zuwa ta tarar da Salman da waya a hannunsa yana lelleƙawa  yaga ta in da zai hango Abra. Yana waiwayowa ya sukai ido huɗu da Abra da take ta tsuma. Da sauri ya ƙaraso in da take yana faɗin "Wai ina kika shiga ne? Over 15 missed calls, amma baki ɗaga ko ɗaya ba. Shiru tayi tana rarrraba ido, ta kasa ce masa uffan. A ɗan hasale yace "ki yi mini magana ma, kin tsaya kina kallona". "Wani lecturer ne ya ƙwace mini waya" "Me ki kayi masa da ze ƙwace miki waya?". "Wayata ce tayi ringing a aji, shine ya ƙwace mini wayar" tai maganar tana tsilli-tsilli da ido, saboda ƙaryar da tayi. Salman dai kallonta kawai yayi, yace "to yanzu daga ina kike?". "Cafeteria naje inci Abinci". "To Yanzu kinci Abincin?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Wai meke damunki ne, gaba ɗaya kamar a tsorace kike fa" yai maganar yana kallonta. gaba ɗaya tunaninta da hankalinta yana kan yadda za tai ta karɓi wayarta, tare da jinjinawa ƙarfin hali irin na Adnan. 'yanzu idan da gaske yake ya tafi da wayata Kaduna ya zanyi?' wata zuciyar ta tambayeta, nan da nan wank irin gumi ya shiga tsastsafo mata, na tashin hankali da damuwa. A haka suka nufi mota suka kama hanyar gida, Salman ya lura gaba ɗaya akwai abunda yake damunta, amma ganinaa yayi-yayi ta gaya masa taƙi, kawai sai ya ƙyaleta. Tafe suke a mota, Baby na sake gwadawa Ihsan yadda za suyi da Sojan nan idan sunje Abuja, Ihsan tai shiru tana sauraren Baby kamar 'ya da uwa. Baby  tace "Maza ki ɗakko waya, ki sanar masa gamu nan". Jiki a sanyaye Ihsan ta ɗakko waya ta kira wata lamba, wadda tai saving da Yallaɓai. Sai data kusa tsinkewa, sannan ya ɗauka "Hello beb ya?" Tai ajiyar zuciya tace "Ya kake? Ya aiki?" Yace "Alhamdilillah, nayi missing ɗinki sosai fa". Ihsan tace "gamu nan zamu shigo garin Abuja". With so much excitement yace "Wow, are you sure?". Tace "Quiet sure" Yace "Can't wait to see you Baby, sai kin zo, ki sauka a guest house ɗina, za'a samar maku da komai". Tace 'Alright, sai mun zo". "Ok bye". Baby tace "hmm zaka ga tsiya, ko ka saki kuɗi ka ƙwaci kanka, ko muyi maka bariki irin ta yaran zamani". Gaba ɗaya Abra jinta take kamar mara lafiya, saboda rashin wayarta, gashi gefe guda tana ta tunani unknown ɗinta, da yake turo mata saƙonni. Allah sarki ta san yanzu zai tayi mata Magana yaji ta shiru, ba ta reply. Da magariba, Abbi ya dawo daga masallaci suna hira shi da Na'ima, gefe Salman yana duba wayarsa, Abbi yace "Hope dai karatu kake ba shirirta ba?" Salman yace "eh Abbi, ina duba wani abu ne". "Ai nasan hankalinka ne, kafi maida hankali a kan, shirita fiye da karatu". Na'ima tace "Eh amma ai Abra ka yadda karatu take a waya, amma shi kace ba karatu yake ba" wani mugun kallo da yayi mata ne, ya sanya ta haɗiye Maganar ba shiri. Abbi yace "Ni ban ma ganta ba gaba ɗaya, me take yi a ɗakine iya kaɗai?" Salman yace "I don't know what's wrong with her today, gaba ɗaya kamar wani abu yana damunta". "Kira mini ita". Salman ya miƙe ya nufi ɗakinta, ko da ya shiga ya tarar tana zaune, ta zube littattafai a gabanta, amma tunani takeyi, ba karatun ba. Yayi ajiyar zuciya sannan yace "Idan kin gama tunanin kizo Abbi yana kiranki". Ta ɗaga kai ta kalli Salman, wanda tuni ya juya zaia bar gurin. Jiki a sanyaye ta miƙe ta biyo bayansa,  ta tarar da su gaba ɗaya a falo. Ta ƙarasa gaban Abbi ta zauna yace "Gani Abbi". "Daughter na, meke damunki ne? Duk muna nan a zaune, amma kin keɓe kanki a ɗaki, gashi fuskarki ta nuna, kina cikin damuwa". Abra tace "Abbi bakomai, na gaji ne kawai" Abbi yace "Anya kuwa? Ki gaya mini gaskiya". Salman yace "Wayarta akai seizing a Makaranta" Abbi yace "Subhanallah, how comes?" Salman yace "Wai ringing tayi a aji, shine aka ƙwace, shine take ta wannan ƙuncin". Abbi yace "Ki dena damuwa, in basu baki ba a canza miki wata". Na'ima da tun ɗazu ba tace komai ba tace "Wane irin a canza mata wata, ka sani ko ana musu karatu tana wasa da waya ne?". "No ba haka 'yata take ba, koma mene zanga abunyi, a canza wata idan be baki ba, amma ki dena damuwa kinji?" Tace "to Abbi". Salman ne ya miƙe ya nufi hanyar kitchen, ganin Kamar Salman yana fushi da ita, yasa ta miƙe itama ta nufi kitchen ɗin". "Ina zaki?" Na'ima tayi maganar tana zazzarewa Abra ido. Abra tace "Mami banci Abinci ba, zanje in zuba ne". Ba dan ta so ba, tai shiru saboda Abbi yana gurin. Da sauri Abra ta ƙarasa cikin kitchen, ta tarar da Salman a tsaye yayi shiru, da alama ma ba wani abu ya shiga yi a kitchen ɗin ba. Yana ganin ta shiga, shi kuma ya nufi hanyar fita, da sauri tace "Faris" Ya waigo ya kallta ba tare da yayi magana ba. "Fushi ka ke dani?". "Me ki kai mini da zan fushi dake?". 'ga alamu nan a fuskar ka, me nayi maka? Kuma ina shigowa ka juya zaka fita". "To ya kike so inyi, ina ta binki ki gaa mini me ke damunki amma kin ƙi". Abra tace "Haba Bloody na, rashin wayata ne kawai duk ya dameni, You know am so much attached to my Phone, am sorry" Ta yi maganar tana murmushi tare da jan dogon hancinsa, ji yayi yana neman shiga wani hali, kasancewar kusacinsu da Abra yayi yawa, gashi sai ƙamshin turare take yi. Cikin shagwaɓa ta ce "to kace mini ka haƙura mana". Lumshe ido yayi, yana kallon yadda take cigaba da shagwaɓa. "Talk mana". "Ta yi maganar tana girgiza shi". "Tom na haƙura" ya faɗa a taƙaice. Ta girgiza masa kai tace "See how you frown your face, gaskiya ba kaa haƙura ba" "Na haƙura Angel, let me go and rest please" "Wai to ya na ga duk ka wani canza ne?" Yace "Stress ne kawai na school, see you later" yayi maganar yana kashe mata ido ɗaya, ya fice daga kitchen ɗin. Murmushi tayi a hankali ta furta "Faris sarkin rigima, am imagining ma life without you, you are so much caring bro, Allah ya biya ka" ta ƙarasa Maganar da ajiyar zuciya. "Kai yanzu Adnan, fisabilillahi daga cewa zakaje wani Assigment a Kano ka dawo, sai kaje ka yi zamanka, kullum kana gaka nan gaka nan, mahaifinka duk ya damu". "Am sorry Hajiya, ni kaina ban yi zaton aikin zai ja mini dogon lokaci haka ba, amma Alhamdilillah an yi Nasara a aikin ai". "To barka, haka ake so dama, amma aikin na ku ne sai a hankali, yau mutum yana nan gobe yana can, ga ƙasar nan babu cikakken tsaro sam". Yace "Hakane Hajiya, dama aikin ɗamara kasada ne, amma gara a rasa rai ɗaya idan har zai silar rayuka da yawa su samu kwanciyar hankali". Hajiya tace "A'a Adnan, ai duk rai rai ne, mai shi yana son abunsa, Allah dai ya tsare mana ku". "Ameen, uwata ta kaina, baki mini Addu'a ba yau". Ta yi murmushi ta ce "Addu'a kullum cikinta muke ai, yanzu haka ma ai na yi maka". Yayi murmushi yace "Allah ya ja kwanan Hajiya Mama" "Ina, ai mu mun kai gangara, fatan ƙarshe mai kyau muke, ku muke yiwa Addu'a, Allah ya raya mana ku". Ja yayi kamar ta zuba masa wuta abunda ta faɗa, life without his Mum, haka kurum ya ji jikinsa yayi sanyi, miƙewa ya yi daga in da yake zaune yace "Sai da safe" "To Allah ya tashe mu Lafiya, kar ka manta kayi Addu'a" Bai amsa ba, kuma bai waigo ba ya wuce ɗakinsa. Ya shiga banɗaki ya watsa ruwa, ya fito yayi shirin kwanciya bacci, gefen pillow ɗin sa ya kalla, wayar Abra ce da aka ishe shi da ringing ya sakata a silent. Ya danna wayar, kusan 25missed calls, wanda duk daga Bloody sai Faris. Sliding ɗin screen ɗin wayar yayi, saiga hoton Abra akan screen lock ɗin wayar, kanta babu ɗan kwali, ta saki gashin kanta, da ya rufe mata gefen fuska, ta turo laɓɓanta gaba, wanda suka kasance pink. Shiru yayi ya zubawa hoton nata ido, kamar mai nazartar wani abu, daga bisani yayi wata nannauyar ajiyar zuciya, ya kashe wayar gaba ɗaya ya ajiye, ya kwanta. Duk da zuciyar Ihsan cike take da fargaba, amma haka ta ɓoye tsoronta, ta dake dan karta ɓata musu shiri, ta dube shi tace "Nifa Yallaɓai babban dalilin zuwana nan shine, ciki ne a jikina har watanni huɗu dan haka nazo ka bank kuɗi inje in cire shi, ka san dai babu da wanda na taɓa mu'amala sai kai. Haɗe rai yayi yace "Na sani ko bayan na buɗe hanyar, kin cigaba da leƙe-leƙenki, kuma wace irin sokuwa ce ke, da zaki bari ciki ya shiga jikinki har Wannan lokacin?" "Kar ka sake ce mini sokuwa, kawai ka bani kuɗi inje in zubar, kar Asirina ya tonu". Gajeren tsaki yayi Yace "Naji, zan baki 20k kije a cire shi". Wani banzan kallo ta yi masa tace "sai kace cikin jikin Akuya? Dubu ɗari aka ce zan ajiye, sannan a cire cikin ya zanyi da wata 20k". "Kina da hankali kuwa, a wannan marrar ne zan baki har 100K?". "A Arziƙin da Allah yayi maka mecece 100K? Ko nice a bar banza?" "Kinga zan bani 50K, daga haka ba zan ƙara ba". "Gaskiya ba zan karɓi 50K ba, a ina zan samu sauran?". Yace "Wannan ya rage naki kuma" wani irin baƙin ciki ya turnuƙe mata zuciya da tarin nadama da dana sani, ba yadda ta iya, haka ya tura mata 50K. Ba kunya kuma bayan ya tura mata ya fara lalubarta, abun mamaki sam ba ta masa musu ba, suka gama sheƙe ayarsu, Sannan ta kintsa jikinta, ta koma masaukin su. Baby ta dinga jinjina mata, domin kuwa duk abunda suka yi, ta naɗo tsaf a video ba tare da ya san tayi haka ba. Nan Baby ta sake shirya mata abunda zata yi masa, dan wanda ya yiwa Janna, sai da ya ajiye mata dubu ɗari biyu da hamsin, dan haka suma sai sun wanki wannan Yallaɓai. Dan haka suka tsara message tare da videon nan nasa, suka tura masa!. Innalillahi wa Innalillahi raji'un, tashik hankali da ba'a sa masa rana, Yana gurin aiki, amma haka ya miƙe jikinsa na tsuma, yaran nan sun san waye shi a cikin ƙasar nan kuwa? Yayi harka da manyan karuwai, amma wannan da ba su fi 'ya'yan cikinsa ba, sune za su ƙulla masa wannan tsiyar? Dole ya ɗauki mummunan mataki akan yarinyar nan, wanda nan gaba idan aka ce ta yiwa wani haka ba za tai ba. Abra tun tana kewar rashin wayarta, har ta saba ta haƙura da rashin wayar, gefe guda haka kurum take jin ta yi missing ɗin me turo mata messages ɗin nan a wayarta, ko ba komai wani mutum na musamman ne da ya shigo rayuwarta, ta wata siga da babu wanda ya taɓa shigowa ta haka. Guntun tsaki ta ja, bayan tuna Adnan ya tafar mata da wayarta. Sosai ta maida hankalinta kan karatunta, tun daga ranar da Adnan ya tafi da wayarta, ba ta sake ganinsa ba, tun tana tunanin zata kuma ganinsa ya bata wayarta har ta dena, ta cigaba da al'amuranta, sai cewa ma take wa ya sani koma ɓarawon wayane, wayar yake son ya sace shiyasa yake ta binta. Yau ba lokaci ɗaya Abra za su tashi da Salman ba, dan haka akwai snacks a jakarta, ta tafi department ɗin su Salman, domin suci sai ta jira har ya gama lectures, Sannan su tafi gida, dan ta san idan taje gidan ma, ba daɗinsa za taji ba. Ajin Su Salman ta nufa, ta ɗan leƙa ta window, taga ana yi musu lectures, Malmin ya raba ajin gida biyu, yana yi musu kacici_kacici, yace duk rukunin da suka ci, suna da maki goma-goma dukaninsu, amma sai ya kammala lectures ɗinsa na yau za'ayi. Ajinsu Faris Maza sunfi yawa akan mata, dukkansu suna sanye da fararen lapcoat akan kayansu, sun tattara nutsuwarsu akan malamin. Ba wanda ya ganta, tana nan tsaye aka gama lectures ɗin, aka fara Quiz. Anayi tana ta murmushi, abun yana burgeta sosai da sosai. Can aka yiwa rukunin su Faris wata tambaya, abunka da manyan professors, sai da ya rikita tambayar, yadda ba za su fahimta ba. Sai ya basu option yace su zaɓa, ganin sunyi shiru suna mazari ya sa Abra tai farat tace "Faris Ba ne amsar fa" gaba ɗaya ta manta a jikin window take, tana leƙe. Aikuwa gaba ɗaya suka waigo suna kallonta, sai kuma tayi shiru tana rarraba ido. Prof ɗin nan yace "Zo nan" jiki a sanyaye ta zagaya ta shiga ajin, tana sunkuyar da kai, saboda ba ta son kallo. Ya kalleta yace "Me kike yi a jikin window?". "Brother na nake jira mu ci Abinci" ta faɗa kai tsaye. Yai murmushi yace "Sai kace a Nursery? Waye brother ɗin naki?" Tace "Faris ne" "Waye Faris?". Ta kalli Salman da ido, Salman wata kunya ta kama shi, Sam Abra bata da wayo wasu lokutan. Prof ɗin yace "iyee, cire facemask ɗin nan". A hankali ta sauke face mask ɗin, tana sunkuyar da kai, harda masu cewa wow, tubarkallah abunda ya sa Salman sake tsuke fuska. Prof Jibiya yana da barkwanci sosai, dan haka yace "Salman, is she your sister?". Salman yace "Eh ƙanwata ce". Zaro ido ta yi, za tai magana, amma Salman ya harareta, hakan ya sata yin shiri. Jibiya yace "Masha Allah, to yanzu yi mana bayanin, meyasa kika zaɓi B a matsayin Amsa?". A nutse Abra tayi masa bayani, wanda in ba me kaifin hankali ba, babu wanda zai iya gano amsar. Ya jinjina kai yace "Kai Masha Allah, Madalla da basira irin taki, me kike karanta ne?" Ta gaya masa, ya jinjina nai, gaba ɗaya ba science tayi ba, amma ta iya bada wannan amsar. Prof yace "Yanzu kiyi tafiyarki, kije ki ci Abincin ki, dan wannan ba yanzu zai fito ba". Tace "To, amma zan iya ba shi nasa kan su fito?" Ya jinjina mata kai, 'yan ajin sai dariya sukewa halin ƙuruciya na Abra. Taje gaban seat ɗin Faris, ta ɗakko wata leda ta ajiye masa tace "zanje inyi karatu in kun gama sai mu tafi". Faris ya kalleta, a hankali yace "Dan Allah Angel yaushe zaki girma ne? Yarinya ba wayo gaba ɗaya". Tace "Ni ba zan kulaka a nan ba, sai munje gida". Daga haka ta yiwa lecturer godiya, ta fice, prof ya cigba da koɗa Abra da baiwarta, har da tambayar Salman anya uwa ɗaya uba ɗaya suke? Ko dai su larabawa ne, sai da Salman ransa ya ɓaci, ya tsuke fuska. Tana tafe tana ƙoƙarin samun gurin da zata zauna, ta ci Abincinta tayi karatu. Wani irin mahaukacin parkig aka yi a gabanta, wanda sai da ta razana, ta runtse idanunta. Jin shiru ba'a bugeta da motar bane ya sa ta buɗe idanunta a hankali. Ido huɗu suka yi da shi, wanda sai da ya fuskanci halin firgici da ta shiga. Juyawa tayi za ta canza hanya, amma cikin zafin nama ya fito daga motar, ya danƙo hannunta, ya jefata a cikin motar ta sa, ya rufe motar ya zagaya ya shiga, ya fizgi motar da gudu, ya bar makarantar. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ina zaka kai ni, na shiga ukuna, wayyo Abbina, Faris dan Allah a temake ni" "Shut up, ki dena yi mini ihu" yai mata wata razananniyar tsawa. Abra cikin kuka tace "dan Allah kayi haƙuri, ka ƙyaleni dan Allah" shiru yayi Mata ya cigaba da tafiya. Wani gurin cin Abinci yaje, yayi parking ya kalleta ransaa a haɗe ya ce "Fito" Cikin tsoro da fargaba ta fito tana zare ido, gurin ba mutane sosai suka shiga cikin gurin cin Abincin. Yayi mata umarnin ta zauna, haka ta zauna tana cigaba da waige-waige, tsoronta Allah tsoronta kar wani wanda ya santa ya ganta yaje ya gayawa Abbi. "Me za'a kawo miki?" Yayi Maganar yana kallonta. Ta girgiza masa kai alamar babu. "Ba sace ki nayi ba, Cin Abinci kika rako mijinki, dan haka You Are safe, ki saki jikinki, bana sace mutane" Kallonsa take, kamar ba shi ne ya gama yi mata tsawa ba. Yayi musu order Abinci, amma taƙi ci. "Nifa Mutum ne ba dodo ba, stop looking at me, like this" "Dan Allah ka mai da ni, dan Allah kayi haƙuri" Wani irin kallo yake mata, wanda sai da ta ji tsigar jikinta na tashi. Sauke idanunsa yayi, ya cigaba da cin abincinsa. "Ki dena kallona kar in ƙware". "Ai ba kallonka nake ba" ta faɗa a raunane. "Ya maganarmu ne?". "Wace Maganar?" Ya ɗago ya kalleta yace "ina tambayar ki, ki na tambayata?" Ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Abra talk" yayi Maganar in a cool voice, kamar ba shi ba. Shiru tayi bata amsa ba. Adnan yasa hannu ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna. Ya ɗan kashe mata ido yace "Yaushe zan zo gidanku in ga Major? Kinga ni ba ƙaramin yaro bane, ki dena mini wasa da hankali, ina ta binki amma kina mini wasa da hankali?" Tace "bakomai" A hankali ya saki haɓarta yace "muje mota, in baki wayarki, sai muje in ga gidan naku". "Za'ai mini faɗa a gida" "Ba za'ai miki faɗa ba, tashi muje". Gaba ɗaya Abra tsoron sa take ji, duk da tayi mamakin yadda yake Magana yanzu kamar ba shi ba. Haka ya sata gaba, zuwa cikin mota, a motar ya bata wayarta. Har bakin layinsu ya kaita, ya kalleta yace "Ranar Saturday zan zo insha Allah, ki shirya karɓa ta" Ba tace Komai ba, ta fara ƙoƙarin buɗe motar ta fita. "Wai ke ba ki iya godiya bane? Ko nace na sallameki ne?" "Nagode" ta faɗa tana tsoron kar wani ya ganta, dan ma motar tint ce. Yace "Well, a sauka lafiya Angel" da sauri ta waiwayo tana kallonsa. "In baki gama kallon nawa ba, sai in juyo" ba shiri ta buɗe motar ta fice, tana waige-waige kar taje wani ya ganta. Ihsan ce tai wani ɗan ihu tace "Janna, Baby kunga Mutumin nan ya rikice, wai Zai zo ya sameni, ko nawane zai sai videon in goge shi". Baby tayi dariya tace "A siyar masa a farashi mai tsada, sannan ki goge amma muna nan da shi ai, zai gane kuskuren sa, duk da ya saki kuɗi, da ba'ai haka ba, yanzu mu dai zamu fita, ki janyo shi nan, ya zo ki tatse mana shi. Haka suka cigaba da shewa, suna shawarwarin nawa zasu tatse shi. Suka shirya tsaf suka tafi nasu guri, suka bar Ihsan kawai tana jiran zuwan Yallaɓai. Su Janna basu koma ba sai bayan la'asar daga nasu gantali, Sai dai abunda suka gani ne ya girgiza su, cikin tashin hankali Janna ta ƙwala ihu, gawar Ihsan ce kwance a cikin jini! Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/1, 3:01 PM] Abk: A gigice Baby ta cillar da jakar hannunta, cikin waro ido ta kurma wani uban ihu tare da ficewa daga ɗakin hotel ɗin a ruɗe. Ƙarasawa Janna ta yi ta shiga girgiza ƙafar Ihsan cikin kuka da tsananin tashin hankali. Ɗaya daga cikin ma'aikatan hotel ɗin ne ya hawo sama da sauri jin kururuwar Baby. "Hey, Lafiya kike mana wannan kwakwazon?" Kasa magana Baby ta yi, nuna masa ɗakin kawai take yi da hannu tare da toshe bakinta. Shiga ɗakin ya yi cikin sauri, cak ya tsaya tare da dafe ƙirjinsa cikin firgici. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un!" Abun da ya furta kenan a fili idanunsa akan gawar Ihsan dake kwance cikin jini malel-male. Da sauri ya juya ya fita ya je ya sanar da Manager na hotel ɗin abun da yake faruwa. After some minutes Su Janna ne zaune a police station mafi kusa da hotel ɗin, idanuwansu sun yi luhu-luhu alamun sun ci kuka sun gode Allah, sai zazzare idanuwa suke yi cikin firgici. D.p.o dake bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya ya dubi wani jami'i ya ba shi  umarnin ya shigar da Janna cikin cell, kuka ta fara tare da yi masa magiya tana ba shi haƙuri, tsawa ya daka mata wanda ta sa su duka suka razana, ba shiri ta yi shiru ta shiga jujjuya kai. Tasa ƙeyarta jami'in ya yi har cikin cell. "Ki nutsu, tambayoyi zan miki, kuma ki faɗa mini gaskiyar abin da kika sani, domin idan ma kin mini ƙarya zan gano daga baya, kuma hakan ba zai haifar miki da ɗa mai ido ba." Cewar D.p.o yana kallon Baby da jikinta ke tsuma. "In...insha Allahu zan faɗa maka gaskiya yallaɓai." "Good." Ya faɗa cikin gyaɗa kai. "Mene ne alaƙarki da wacce aka kashe?" "Ƙawata ce." Jinjina kai ya yi ya ce. "Tsawon wane lokaci kuka ɗauka tare? Kuma a ina kuka haɗu?" "4 Years back, a makaranta muka haɗu, A.b.u Zaria, course ɗinmu ɗaya da ita." "Okay, shi ne aka haɗa baki dake kenan aka kashe ta?" Cikin kuka Baby ta ce. "Wallahi ba haka ba ne Yallaɓai, ba ni da masaniya akan kisan Ihsan, ta yaya ma za a haɗa baki da ni a kashe ta? Ƙawata ce fa." D.p.o ya ce. "Ku ƴan wanne gari ne?" "Dukanmu ƴan Kaduna state ne." "Kaduna? Amma me ya kawo ku Abuja?" Shiru Baby ta yi ta fara sosa kanta tana rarraba idanuwa. "I'm toking to you my friend." Ya faɗa cikin tsawa. Zabura ta yi ta ce. "Mun zo ganin wani mutumi ne?" Ya ce. "Wane wanin? Daga Kadunan kuke yanzu?" "A'a, muna zaune a school hostel ne, daga can muka zo nan." Jinjina kai ya yi cikin nazartar ta ya ce. "Okay, cigaba da bayani, gurinwa kuka zo?" Cikin rawar murya ta ce. "Wani tsohon Soja ne, ita ƙawar tamu da aka kashe muka rako nan Abuja, don ta gana da shi akan wani abu." Tattara hankalinsa gabaɗaya D.P.O ya yi a kanta ya ce. "Wanne abu ne wannan da kuka taho tun daga Kaduna har Abuja saboda kawai su yi magana a kansa?" Baby tana hawaye ta ba shi labarin duk abun da ya faru tsakanin Ihsan da General Ibrahim, ganin ba ta da mafita, kuma tana son ta kuɓuta daga zargin su da ake yi. D.P.O ya ce. "Kin tabbata abun da kike faɗa mini gaskiya ne?" "Wallahi gaskiya ne ranka ya daɗe, kuma dalilin da ya sa ma ba mu fita tare da ita ba saboda zai zo su haɗu a lokacin." D.P.O ya ce. "Kuna da tabbas ɗin ya zo sun haɗun bayan kun fita? Kuma menene shaidar ku akan abun da kika faɗa." A raunane Baby ta ce. "Eh, lokacin da ya zo ta kira mu ta sanar mana zuwansa cikin murna, dan muna tunanin ya zo ya ba ta kuɗin da muka nema ne daga hannunsa, shaidar kuma akwai short video na tattaunawarsu ita da shi akan cikin jikinta a cikin wayoyinmu, wanda muka yi masa barazanar da shi." Numfashi D.P.O ya sauke tare da shafa kansa ya ce. "Ya sunan shi Sojan?" "General Ibrahim A.M" "What? General Ibrahim A.M? Are You sure?" Ya tambaya cikin shock. Gyaɗa masa kai ta yi cikin tabbatarwa. Girgiza kai ya yi ya ce "Oh My God!" Duban jami'in da ya kai Janna cell ya yi ya ce. "Officer." "Yes sir." Ya faɗa tare da ƙamewa. "Ka shigar da wannan ciki ka fito ɗayar." A ruɗe Baby ya ce. "Yallaɓai dan Allah ka sallame ni tunda na faɗa maka gaskiyar abin da ya faru, wallahi ba mu muka kashe ta ba, ba mu.." "Shut up, tashi mu je." Officer ya buga mata tsawa da faɗin haka. Kuka ta fashe da shi tare da miƙewa ta yi gaba. Exactly abun da Baby ta faɗa shi Janna ta faɗawa D.O.P, bayan ta gama yi masa jawabin ya bayar da umarni aka kawo masa wayoyinsu da aka karɓa, ya cewa Janna ta ɗauki tata ta cire key ta nuna masa videon tattaunawar Ihsan da General Ibrahim. Da wannan damar Janna ta yi amfani ta ɗora videon a social media in seconds, sannan ta miƙawa D.P.O wayar. Bayan ya gama kalla ya dubi wani police dake tsaye a gabansa ya ce. "Inspector, a cigaba da tsare yaran nan har zuwa lokacin da za mu gama bincike, sannan a je a taho da General Ibrahim A.M, yarinyar da aka kashe kuma a san yanda za a yi iyayenta su samu labari, and lastly aje a zo mini da Manager na hotel ɗin da abun da ya faru a ciki yanzu, a kuma bincika CC TV camera domin a tabbatar da General Ibrahim ya je hotel ɗin a yau ko akasin haka." "Done Sir." Inspector ya faɗa tare da sara masa. Bayan ya fita D.O.P ya dubi Janna dake ta kuka ta ce. "Wannan ya isa ya zama izna a gare ku da masu hali irin naku, yara ƙanana da ku iyayenku sun tura ku karatu amma kuna irin wannan rayuwar, yanzu wa gari ya waya? A misali idan General ɗin ne ya kashe ta hakan ya isa ku gane ba ku da wata daraja da ƙima a idanun irin waɗannan Mazan da kuke bi, ba su ɗauke ku a bakin komai ba, sun mayar da ku kamar ledar pure water saboda yawan da kuka yi a gari. Ya kashe ta ne saboda ya tsira da mutuncinsa kar abun da yake aikatawa ya fito fili, kuma a lokacin da ya kashe tan yana fita idan ya haɗu da wata ɗaukarta zai yi ya je ya sheƙa ayarsa da ita hankali kwance, ita kuma wannan ya gama da ita, da ita da Dabba duk matsayinsu ɗaya a gurinsa. Ina baki misali ne kawai ba wai ina faɗa dan ya aikata ba, dafatan kin fahimta?" Janna da kanta ke ƙasa tana hawaye ta gyaɗa masa kai. Girgiza kai ya yi cikin takaici ya ce. "Allah ya shirya." Sannan ya bayar da umarnin a mayar da ita ciki. General Ibrahim A.M ne zaune a gaban kujerar gaban table ɗin D.O.P, cikin shiga ta kamala, ba zaka taɓa cewa shi yake aikata baɗala da Ƴaƴan cikinsa a bayan fage ba. Bayan sun gaisa cikin ƙwarewar aiki D.P.O ya ce. "General, muna son za mu yi maka wasu ƴan tambayoyi ne a kan kisan wata yarinya da aka yi mai suna Ihsan Sadam Malali a Aminci Hotel."  Damm zuciyar General Ibrahim ta buga, amma da yake cikakken ɗan duniya ne kuma ya san ta kan harkar bincike sai ya ce. "D.P.O ni kuma? Wacce yarinya ce wannan? Me ya sa kuka gayyato ni akan kisan ta? Ba na jin ko a cikin familynmu akwai mai sunan da ka ambata balle na yi tunanin ko ina da wata dangantaka ta jini da ita, Ihsan ka ce ko wa?" Cikin nazartar shi D.P.O ya ce. "Bari ka ga hotonta, na san idan ka gani may be ka shaida ta." Bai jira cewar shi ba ya ɗauki wayarsa ya latsa sannan ya nuna wa General Ibrahim pics ɗin fuskar Ihsan da ya cika screen ɗin wayar. Ƙarɓa ya yi ya duba, cikin ɓoye razanin da zuciyarsa take ciki ya ce. "Gaskiya ban san wannan yarinyar ba D.P.O." "Ko?" D.P.O ya faɗa tare da karɓar wayarsa. "Ina jin mistake kuka yi ba ni za ku kira ba." "Kai kuwa za mu kira, saboda bincikenmu ya tabbatar mana da a guest house ɗinka yarinyar ta sauka ita ƙawayenta shekaran jiya." Cikin maziya General Ibrahim ya ce. "Eh hakan zai iya yiyuwa, saboda akwai abokaina da dama da suke saukar baƙinsu a gidan ba tare da na sani ba, because mun zama ɗaya na yarje musu hakan. Cikin gyaɗa kai D.P.O ya ce. "General please kar ka wahalar da mu ka wahalar da kanka, ka amsa kawai ka san yarinyar nan, in yi maka tambayoyin da zan yi maka, that is all." "A'a fa, ban san ta ba zan amsa na san ta ne? Da kuka kira ni in zo akan abun da ban sani ba na yi muku musu? Na taso na zo duk da ina gaba da ku a matsayi da miƙami, amma saboda ina girmama kaki da mahukunta ya sa na zo cikin salama ba tare da jayayya ba." General ya faɗa cikin harzuƙa. "Akan aikina nake General, kuma sanin kanka ne babu ruwan doka da wani muƙami ko matsayi, idan abu ya biyo ta kan mutum ko waye shi dole a tuhume shi, but ba wannan ne a gabanmu ba yanzu, let me show you something." D.P.O ya faɗi haka tare da ƙara ɗaukar wayarsa a karo na biyu. A ɗarare ta shiga gida zuciyarta cike da tsoron Na'ima, kasancewar Major ba ya gari. Allah ya taimake ta Na'ima ba ta main Parlor tana ɗakinta, ajiyar zuciya ta sauke ta shige ɗakinta. A bakin gado ta zauna tare da ƙurawa wayarta ido, sai dai a zahiri ba wayar take kallo ba, tunanin wanda ya ba ta wayar da kasancewar da suka yi tare na wasu mintuna take tunawa. Har yanzu zuciyarta ba ta daina bugawa ba, ta tsorata sosai da farko, dan wannan ne karo na farko da ta taɓa daɗewa tare da wani Namiji bayan relatives ɗinta. Sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tare da kai wayarta kan hancinta ta shaƙi ƙamshinsa, tun a jikin i.d card ɗinta ta ji tana son ƙamshin, sometimes idan za ta kwanta bacci sai ta ɗauko ta shinshina. Mr unknown ne ya faɗo mata a rai, da sauri ta latsa wayar ta cire password tare da cire ta daga Flight mode ɗin take, kamar jira ake messages suka dinga shigowa. Hannunta har rawa yake wajen dannawa ta buɗe ta karanta. Messages ɗinsa ya kai 15 ta gani, duk na yanda yake tsananin son ta ne da missing ɗinta da ya yi, a ƙarshe kuma sai ya roƙe ta akan ta taimaka ta yi masa reply koda da "Okay" ne, dan ya ji daɗi a cikin ransa. Murmushi ta yi ta tura masa da. "Hey, How are you." Message ɗin yana tafiya kira ya shigo cikin wayar da sabuwar Number, kallon special Numbern ta tsaya tana yi, sai da ta kusa katsewa sannan ta yi pick. "Assalamu alaikum." Wata murya mai cike kamala da daɗin sauti ta doki kunnenta. Sai da gabanta ya faɗi jin muryar wanda ba ta za ta ba, lumshe ido ta yi a hankali tare da gyara zama ta amsa masa cikin sassanyar muryarta. "Na kasa cigaba da driving a dalilin kyakkyawar fuskar matata dake ta mun gizo gami da tunaninta da ya addabi zuciyata, shi ya sa na kira ki don na samu nutsuwa, i hope kin shiga gida lafiya?" Ya yi maganar cikin wani irin salo da ya ratsa zuciya gami da ko'ina a jikinta. Shiru ta yi ta rasa me za ta ce, jin al'amarin take wani mai girma a kanta. "Ba na son ina magana ana ji na a yi shiru" Ya faɗi haka a ɗan kausashe kamar ba shi ya gama magana cikin kulawa yanzu ba. Turo baki ta yi kamar yana gabanta ta ce. "I'm sorry, ban san me zan ce ba ne." Murmushi ya yi mai sauti ya ce. "Just say I love you My husband." Waro ido ta yi ba ta ce komai ba. Ya ce. "I'm waiting for you Madam." Nan ma shiru ta yi sai sauke numfashi kawai take yi. Murmushi ya ƙara yi ya ce. "Okay bye, thank you, take care of yourself." Bai jira amsar ta ba ya kashe wayar. Ajiyar zuciya ta sauke tare da zare wayar daga kunnenta. sai ta tsinci zuciyarta da blaming kanta, kamar ba ta kyauta masa ba da ta yi shiru, to amma me za ta ce masa? Ita fa jinta take duk a takure, ga wani kwarjinin da yake yi mata, ga kunyar shi da take ji duk ita kaɗai. _Adnan_ ta ambaci sunansa a cikin zuciyarta, sunan ya yi mata daɗi ba kaɗan ba. Lumshe idanunta ta yi tana hango yanda yake magana cikin nutsuwa yana motsa ƙananun lips ɗinsa kamar ba ya son maganar ko wanda aka yiwa dole. Murmushi ne ya kufce mata ba tare da shirya yin sa ba, saboda tuno kyawawan fararen idanuwansa da yake tsare ta da su. "Angel!" Salman ya faɗa da ɗan ƙarfi lokacin da ya shigo ɗakin yana ƙare mata kallo. Da sauri ta buɗe idonta cikin ƙoƙarin daidaita nutsuwarta. "Me ya sa kika taho ba tare da kin sanar mini ba?" Kalar tausayi ta yi ta ce. "I'm sorry bloody, bayan na baro class ɗinku na ji ina son shiga toilet, kuma ka san i can't use toilet ɗin school, that is why na taho gida." Ajiyar zuciya ya sauke ya ce. "Shikenan, amma kin ɗaga mini hankali sosai, kin san irin neman da na yi miki kuwa?" "Sorry sweet Bro, ka je ka huta bari na tashi na haɗa maka delicious yanzun nan." Murmushi ya yi ya ce. "Baby girl, shi ne kika zo kika ba ni kunya a class." Cikin shagwaɓa ta ce. "Kunyar me kuma Faris?" "Ba ta komai, ni abun da ya fi ba ni haushi yanda ake ta tanka ki, bayan mun fito harda masu cewa in ba su contact ɗinki wai kin burge su." Ya ƙarashe zancen tare da jan tsaki. Murmushi kawai ta yi, ta rasa me ya sa Salman yake mata haka? Ba ya so ya ga maza suna kallon ta ko su yi mata magana, yanzu zai shiga ɓaɓɓata rai da jan tsaki. Lallaɓa shi ta yi ya sauko daga kumburin da yake, ta nuna masa an ba ta wayarta yau, taya ta murna ya yi sannan suka fita tare, ta shiga kitchen shi kuma ya yi ɗakinsa. Ba ƙaramin firgicewa General Ibrahim ya yi ba da ganin wannan videon, wani irin gumi ya shiga tsatstsafowa a jikinsa. D.P.O dake karantarsa ya ce. "Zaka ce ba kai ba ne wani ne ya yi amfani da fuskarka? Wannan ƙaryar da ka yi ta ƙara sanya mini zargi a kanka." General dai kasa magana ya yi, sai goge zufa yake yana zare ido. D.P.O ya janyo laptop ɗin dake gabansa ya yi yan danne-danne sannan ya juya ta yanda za ta fuskanci General Ibrahim, bai ce komai ba sai wani kallo da yake bin sa da shi. General Ibrahim ya ɗaga ido daƙyar ya dubi laptop ɗin, videon lokacin da ya shiga reception ɗin Aminci Hotel ne. "Wannan ma ko za ka musa ne? Ka saka facemask a lokacin dan ka yi badda kama, ma'aikacin hotel ɗin ya buƙaci ka buɗe fuskarka ya gan ka, sai ka ba shi cin hanci na 20k dan ya ƙyale ka wuce ka je ka kashe ƴar mutane. A matsayinka na babban jami'in tsaron ƙasa, wanda ƙasa take alfahari da kai." "Haba D.P.O ya zaka dinga alaƙanta ni da abun da ban sani ba? Ni fa ba ni ba ne wannan da kake magana akansa." General Ibrahim ya faɗi haka cikin borin kunya zuciyarsa na tsananta bugu. Miƙewa D.P.O ya yi ya ce. "Idan mun je gaba ka yi musu duk wannan bayanin." Bai jira cewarsa ba ya ƙwallawa Inspector kira, bayan ya shigo ya ce masa. "Ku tafi da shi headquarter tare da ƴan'matan nan, I.G yana jira, ya ce a mayar da case ɗin can, i will fallow you back. Kafin dare labarin kisan Ihsan da videon da ta ɗauka nasu ita da General Ibrahim ya gama zagaye ƙasa da kewaye, duk inda ka je zancen ake yi. Al'amarin ya girgiza manyan ƙasa da Sojoji waɗanda suka san General Ibrahim, saboda yadda yake nuna shi na Allah ne akan komai, da yawa ba su yi tunanin zai aikata hakan ba. Kwance yake akan gadonsa ya mimmiƙe baƙaƙen ƙafafuwansa, wata mata wadda da alama Matarsa ce tana yi masa tausa. Taba ce a hannunsa yana ƙarawa sama hazo daga kwancen da yake. Wayarsa dake gefensa ce ta shiga ruri, tsaki ya yi cikin maganar riƙaƙƙun ƴan daba ya ce. "Ba za a taɓa barin mutum ya huta ba." Ɗaukar wayar ya yi ya ɗaga ya kara a kunne, sai da ya zuga ya fesar sannan ya ce. "Ina jin ka ya aka yi ne? Kira da sakaliyar yammar nan?" "Ban gane in hau WhatsApp za ka tura mini abu ba, kawai ka faɗa mini, ka san ni yanar gizon nan ba wani gane mata nake ba." "To na ji, tunda ka dage zan hau." Ya ƙara jan tsaki sannan ya katse wayar. Yana ƴan mintocinsa ya siyi data ya kunna ya shiga WhatsApp. Wani uban ihu ya kurma tare da yar da wayar a ƙasa, cikin zafin zuciya ya cillar da tabar hannunsa tare da narka wani uban ashar ya ce. "Yata Ihsan ɗin aka kashe? Sannan kuma wancan tsohon matsiyacin gajeren Sojan ake zargi? Bayan ya gama lalata da ita? Taɓdi jan, Ibrahim ya deɓo ruwan dafa kansa, wallahi, wallahi, wallahi sai na ɗauki fansar jinin ƴata." Aruɗe mahaifiyar Ihsan ta miƙe cikin ƙaraji ta ce. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Mai gida me kake cewa ne? Ban fahimta ba, wacce Ihsai ɗin aka kashe? Ba dai yata ba?" "Ita fa Rabi, wai tun rana abun ya faru, ana ta kiran wayarmu daga ni har ke ba a same mu ba. An taɓo tsuliyar dodo Rabi, za a yi yaƙin da ba a taɓa yin kamar shi ba a duniya wallahi." Rabi da ba fahimtar abun da yake cewa take ba ta ɗauki wayar da ya cillar cikin rawar jiki ta latsa, videon gawar Ihsan da bayanin abun da ya faru ya bayyana, ƙara ta fasa tare da zubewa a ƙasa sumammiya. Na'ima na zaune a parlour ita kaɗai tana kallo wayarta ta fara ringing, murmurshi ta yi tare da ɗagawa. "Hello Hajiya Maryam ya ake ciki ne?" Daga ɗaya ɓangaren Hajiya Maryam ta ce. "Komai ya kammala ƙawata, ba dai level 1 take ba department of Mass communication?" Da sauri Mami ta ce. "Nan ne." "To ki kwantar da hankalinki tamkar tsumma a cikin randa, wanɗanda na bawa aikin nan ba ni da haufi a kansu, gwanaye ne, ba su taɓa aiki an samu matsala ba, ke dai kawai da zarar aiki ya cika ki cika musu aljihunsu da ƴaƴan banki." "Ba su da matsala da wannan, kin san kuɗi ba damuwata ba ne, ni dai kawai buƙatata ta biya, tsinanniyar yarinyar nan ta bar mini gida ko na huta, haba na gaji, na yi makircin na yi amma har yanzu ban ci nasara ba?" "To daga wannan karon kin gama cizan yatsa ƙawata." Murmushi Na'ima ta yi ta ce. "Da kuwa na zuba ruwa a ƙasa na sha." Maryam na dariya ta ce. "Ko acikin kwata ne ma ki zuba ki sha, duk a cikin celebration ne." Dariya suka yi a tare cikin tsananin farinciki. Washegari 8 Salman yake da lecture, Abra kuma sai 10 hakan ya sa ba su tafi tare ba. Ƙarfe 1 Salman ya fito daga lecture, bayan ya yi Sallah ya nufi department ɗin su Abra, ya jira har ƙarfe biyu suka fito daga lecture. Yana tsaye a bakin class dinsu yana zuba idon ganin ta, amma har kowa ya gama fitowa bai ga ko mai kama da Abra ba. Cikin mamaki ya shiga dudduba cikin department ɗin nasu amma bai gan ta ba, ya kira wayarta ya fi sau 20 ba a ɗauka ba. Hankali a tashe ya kira Na'ima ya tambaye ta ko Abra ta dawo gida? Sanar masa ta yi tana zaune a main parlour tun 12 amma ba ta ga shigowar Abra ba, direbansu ya kira ya tambaye shi ko Abra ta kira shi ya zo ya ɗauke ta? shi ma ya ce masa ba ta kira shi ba. Hankalin Salman idan ya yi dubu ya tashi, duk inda yake tunanin zai ga Abra ya duba amma bai gan ta ba, ya tattambayi classmates ɗinta amma duk amsar ɗaya ce ba su gan ta ba, majority ma ce masa suke yi ba su san ta ba, tunda kullum cikin facemaks take. University ba secondary school ba, balle ya yi report ya ce bai ga Abra ba, to wa ma zai yiwa report ɗin? Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/1, 3:01 PM] Abk: Wani irin Yarrr Abra ta ji a jikinta, saboda rashin sabo, nan da nan ta ji ta shiga wani yanayi, da ba ta taɓa tsintar kanta a ciki ba. Ya janyo hannunta zuwa kan ɗaya daga cikin kujerun gurin ya zaunar da ita. Abra kam ji take tamkar ta nutse a gurin nan, saboda yadda kusancin su yayi yawa, ga wannan turaren na sa mai matuƙar kashe mata jiki. Adnan ya fuskanci yadda Abra ta shiga fargaba na rashin sabo, dan tamkar kace kyat ta gudu, sai sauke numfashi take yi. Cikin dakakkiyar muryarsa mai cike da kwarjini yace "Abraaah" yadda ya ja sunan na ta ne ha sake jefata cikin wani yanayi, me wuyar fassara. "Look up" yai maganar yana sake tsareta da idanunsa. Yayi ajiyar zuciya yace "Shikenan, ba gaisuwa ma, ko ba ki yi murna da zuwana ba?" Ta girgiza masa kai. "Talk mana, ya kike mini rowar muryar ta ki". "Ina wuni". A shagwaɓe yace "gaskiya sai kin kalleni". Murmushi ne ya suɓuce mata, har sai da ta rufe bakinta tana dariyar. Yace "Na baki dariya ko? In dai ni ne za ki sha shagwaɓa, dan shagwaɓaɓɓe ne ni, the only son of his parents, dan haka sai kin yi haƙuri". "Ba ka da ƙanne?" Ta tsinci kanta da yi masa tambayar, ba tare da ta shirya ba. Ya yi murmushi ya ce "Ni ka ɗai ne, shiyasa Aka takura mini in yi Aure, ko iyayena saga jikokinsu, ban yi planing ɗin yin Aure ba yanzu Abra, na fi son mai da hankalina akan aikina sosai, saboda yanayin aikina na rashin zama guri ɗaya, amma ina ganinki komai nawa ya canza, ni ban ma zaci zan iya soyayyar ba, dan ban taɓa yi ba, shiyasa na ke jin tsoro, Allah ya sa kar wani ya yi mink kutse" shiru Abra tayi ba tace Komai ba. "Angel" ta ɗago ta kalleshi. Yace "Say something mana". "To me zance?" Yadda tayi maganar ne, cikin halin na ta na shagwaɓa ya sa ya sake ƙure ta da ido. "Abra kina son Adnan?". Jin Maganar ta yi a bazata. "Ki gayamini, ba na son doguwar magana, amma saboda ke sai surutu na ke, duk na gaji, kuma kin ƙi yin Magana". "Ba ka sha ruwan ba" Abra ta faɗa tana ƙoƙarin basar da Maganar da yake yi. "Ni ba ruwa zan sha ba, ki gaya mini idan kina so na?". Tura baki tayi, ta ƙi magana, sai ma ta nuna kamar ya takura mata. Hannayenta ya sake haɗewa a cikin nata, yana ƙurawa fuskarta ido, "Abra talk, do you Love me?" Ɗago fararen idanunta ta yi tace "ka sakar mini hannuna". "Sai kin bani amsa tukuna" wata irin kunya ce ta mamaye Abra, ga kwarjini da yayi mata. "Shikenan, bari in tashi in koma, in gayawa Abba na kince ba kya sona" yai maganar yana ƙoƙarin tashi tsaye. "A'a nifa ba haka nace ba" tai maganar kamar me koyon magana". "To me ki ka ce?". "To ni kunya na ke ji" Adnan ya zauna yace "Na rufe idona, gaya mini". "A'a ba Yanzu ba" "Sai Yaushe?". Tace "in ba ka nan" murmushi yayi, gaba ɗaya yarinyar ba ta da wayo. Ya ce "Shikenan, tun da kin mini wayo. Kin yi kyau sosai kamar in tafi da ke gidana daga nan". Lumshe idonta tai, ta na jin daɗin yabonta da yake yi. "My wife, ina Faris ne?" Murmushi tayi tace "ya tafi ball" "Da alama, dan da yana nan wataƙila tare zaku zo zancen" Ba ta san lokacin da dariya ta ƙwace mata ba, ƙasan zuciyar ta na fargabar kar ma Salman ya dawo ya tarar da Adnan, dan zai iya ɓata mata rai, kuma ga Adnan ba sa'an Faris ɗin ba ne. "My wife, zuba mini ko ruwan ne in sha". Ba musu ta fara ƙoƙarin zuba masa ruwa, ya zuba mata ido yana kallon yadda take komai a nutse. "Which tribe are you?" Ya tambayeta. Abra ta ɗan yi Jimm sannan tace"Hausa Fulani". "I doubt" ya faɗa a taƙaice. Tace "Why?". "You are very beautiful My Wife, kamar ba kya jin Hausa ma, gaskiya zan so in ga Abbi da wuri, kar wani ya rigani, a sa ranar Aurenmu nan kusa". Zaro ido tayi tace "Aure kuma?". "Yes my dear, ko ba kya sona ne?" Jiki a sanyaye tace "Abbi ba ze mini Aure yanzu ba, ni karatu na ke so". Murmushi yayi bece komai ba, ya kai ruwan bakinsa yana sha, idanunsa akan Abra. Hannunsa ya miƙa ya riƙo ɗan ƙaramin hannunta cikin nasa, yana ɗan murzawa a hankali, Abra tai tsuru-tsuru. Adnan yace "kinga yadda ki ka haskani, nifa cewa Hajiyata nai zan Auri balarabiya, zaki Auri baƙi?". Zame hannunta tayi daga nasa tace "bari in barka kaci Abinci". "A'a zauna inci ina kallon ki, Abbi yana nan ne?". Abra tace "A'a". "Ok na gaisa da Maman kan in wuce". Adnan ya ci Abinci yana ta santi yana yabawa Abra, yau gaba ɗaya Abra Adnan mamaki ya bata, farkon mu'amalarsu ta ɗauka ba shi da mutunci, amma yau ta ga saɓanin abunda take tunani. Ya ce ta kira masa Maminta su gaisa, Abra ta ji daɗin hakan, dan dama a takure take. A falo ta tarar da Hajiya Na'ima, ta kalleta tace "ya na ganki kamar korarriya?". "Mami wai gaishe ki ze yi". Hajiya Na'ima tayi murmushi tace "Masha Allah, babu laifi, amma dai ba zuwa ki kayi kina wannan zazzare idon ba, kamar wadda za'a kashe". "Mami cewa yai wai sai na gaya masa idan ina son sa". "To ke kuma sai ki ka ce masa me?". "To ai Mami kunya nake ji". "Kunya, waike yaushe zakiyi wayau, kamar ba mace ba, sam baki da wayo, in kika ce kina son sa gutsurar ki zai yi?" Shiru Abra tai ba tace komai ba. 'duk jarabarki da gidan nan dai, dole kiyi aure ki bar shi, gara tun wuri ma ki san abun yi. Ki je ki ɗakko mini mayafi na, ki shigo da shi".  Abra ta kaiwa Mami mayafinta, tana tunanin tayaya za ta gayawa Adnan wai tana son sa?. Haka taje ta taho da shi falon. Tun da yai Sallama Na'ima ta ƙare masa kallo, Abra ba ta fi iya ƙirjinsa ba, dogon namiji ne, duk da baƙi ne amma yana da haske, gashi Kyakywa Masha Allah. A ranta tace "taɓ, wannan ya za tai da shi, oho mata ma koma dai menene sai ta bar mini gida kawai'. Suka ƙarasa falon, Adnan ya kame a kan kujera ya ɗan sunkuya ya gaida Hajiya Na'ima. Cikin mutunci ta amsa ta ce "Kai ne sirikin namu?". Adnan yayi ɗan murmushi yace "Eh ni ne". Ta ce "Masha Allah, ya sunanka?" "Adnan Aliyu Matawalle". "Madalla, insha Allah idan har dagaske ka ke, in megidan ya dawo, za'a sanar masa". Adnan yace "Nagode sosai da sosai, kuma insha Allah ni da gaske nake, da zarar an bani dama zan turo magabatana ayi magana". Zaro ido Abra ta yi, Hajiya Na'ima tai wurga mata wata irin harara. Wadda ta sa Abra shan jinin jikinta. Nan dai ta gama yi masa tambayoyi, duk ya amsa mata, sannan suka yi sallama Abra ta tafi raka shi. Har gaban motarsa ta raka shi, sai dai kanta a ƙasa ba ta iya cewa uffan. A jikin motar ya tsaya yana cigaba da kallon yadda dressing ɗin jikinta ya karɓeta matuƙa "My wife, gashi zan tafi, amma ba ki gaya mini abunda ke ranki game da ni ba". Murmushin da ya zame mata ɗabi'a, shi ta cigaba da sakar masa. Adnan yayi ajiyar zuciya yace "Yaushe zan dawo?" "Gobe" ta bashi amsa. Murmushi yayi yace "Lallai kin kamu da son ɗan baƙin mijin nan na ki, tun da har kike son in dawo gobe". Ɗauke kai tayi, kamar ba ita tace ya dawo goben ba. "Wai Nikam da wa kike kama ne, a tsakanin Mami da kuma Abbinki?". Tace "Da Faris nake kama" "Shi Faris ɗin da wa yake kama?" "Da ni" ta bashi amsa. Dariya yayi yace "da alama zan sha fama, haryanzu kina fama da yarinta, zan koma My Angel, insha Allah zan dawo in ga Abbi, nan kusa nake son muyi Aure" Ɗan yamutsa fuska tayi, ta kau da kai gefe. "My wife, ya naga kin haɗe rai haka, ko ba kya sona ne?". Ta girgiza kai, yace "to meyasa kika haɗe rai?" "Makaranta fa" tai maganar idonta na tara hawaye. A ransa ya ce 'lallai wannan yarinyar an shagwaɓata da yawa, komai kuka' "To ai zaki cigaba da makarantar ki". "Ni ba na son in tafi in bar su Abbi da Faris". Yace "idan na Aureki sai in ginawa Faris ɗaki a gidan, tun da ba zaki iya rayuwa babu shi ba" yai maganar cikin gatse, dan ya fara ƙuluwa da yawan zancen Faris ɗin nan. Ya saka hannu a aljihunsa ya ɗakko bandir ɗin kuɗi ya miƙa mata ya ce "gashi nan, kwalliya tayi kyau, Abinci yayi daɗi sosai, ga wannan kya saka a jakarki". "A'a ka barshi nagode". "Ba'a yi mini musu ai, ki dena mini musu bana so, karɓi" Ta sake girgiza kai a karo na biyu. "Ki karɓa bana son musu" yai mata wata razananniyar tsawa, wadda sai da ta ruɗe gaba ɗaya, ta karɓi kuɗin ba shiri jikinta yana tsuma. Ya buɗe motarsa ya shiga ya zauna, ya kuma ɗagowa ya kalleta, kamar ba shi yayi mata tsawa yanzu ba ya ce "Ina sonki Angel, ki kula mini da kanki, I will call you when I reach home" ya kashe mata ido ɗaya, ya ja motarsa ya nufi barin gidan. Ta jujjuya uban kuɗin da yake hannunta, ta koma cikin gida. Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750 Part ɗin Hajiya Na'ima ta wuce, ta tarar da ita a bedroom. Tana ganin Abra tace "Lallai Yarinya kin iya zaɓen miji, bari Abbin ya dawo, a san abun yi". "Mami nifa bana son Aure Yanzu". Sheƙeƙe Hajiya Na'ima ta kalleta tace "Au zaman jiranki za ai har sai kin shirya Auren? Ko kuma jiƙaki za muyi a ruwa mu sha? Aure kuwa dolenki ba bu fashi". Jiki a sanyaye ta miƙawa Mami kuɗin da Adnan ya bata. Ta kalleta tace "wannan kuma fa?" "Bani yayi" tai maganar a sanyaye. "Roƙarsa ki kayi ko?" Da sauri Abra ta girgiza kai tace "A'a Mami, wallahi ban roƙe shi ba, cewa yayi dole sai na karɓa". Na'ima tace "Shikenan, ajiye mini su a kan side bed". Ta ajiye mata kuɗin ta juya ta bar ɗakin. A ɗakinta kuwa, wayarta ta ɗauka ta duba, ta tarar da saƙonnin unknown ɗinta. Murmushi tayi ta fara yi masa reply, daga bisani kuma saƙon dodonta ya shigo wayar, wato Adnan. "I miss your fume my cuty" tura baki tayi kamar tana gabansa tace "ba zan reply ba, bayan kayi mini tsawa ɗazu". General Ibrahim kuwa kamar jira akeyi, shedu suka dinga fitowa a kansa, a kan zagon ƙasar da ya dinga yiwa harkar tsaro lokacin yana bakin aiki. Major Khamal Khamis, zai iya cewa ya fi kowa farincikin wannan kame da akayi, dan ya daɗe da sanin da hannun General Ibrahim a ayyukan ta'addanci, sai dai babu wata ƙwaƙƙwarar hujja da ze iya bayyanawa, wadda za ta sanya a kama General Ibrahim ɗin da laifi kai tsaye. Aka same shi da badaƙalar kuɗin siyan makamai, a gwamnatin baya, tare da wasu manya -manyan ƙasa, da wasu ƙusoshin gwamnatin da ta gabata, abun takaici kuma sune da a cikin Gwamnatin da take mulki. Abun takaici, Manyan mutane ne, da al'umma suke yiwa kallon jagorori, kuma madubi, wanda suka saka ran samun sassauci daga gare su, ashe sune suka maida harkar tsaro, harkar kasuwancinsu. Suka yi sanadiyar tarwatsewar al'umma da dama da aka daɗe ana ginawa. Tofin Allah tsine da General Ibrahim da iyayen gidansa, da kuma yaransa suka dinga samu kuwa ba a Magana, tabbas ya ci amanar ƙasa, mussaman da a dalilinsa rayukan iya sojojin da suka salwanta ba adadi, ba'a ma kallon wancan laifin da ya aikata, ni lalalata da kuma kisan kai, tsabar Mamaki da takaicin taƙadirancinsa ya hana mutane magan, sai zuba ido domin suga, irin matakin da za'a ɗauka a kansu. Sai magariba Salman ya dawo daga gurin ƙwallo, dan sai da yayi sallar magariba sannan ya dawo gida. Sashen Mami ya wuce da kofin juice a hannunsa. "Sai yanzu ka dawo?" "Na tsaya nayi Salla ne Mami, baƙi mukayi a gidan ne? Naga guest room da kayan ciye-ciye, suwaye suka zo?". "Abra ce tai baƙo". Turus yayi yana kallon Mami yace "Wane irin baƙo kuma?". Hajiya Na'ima tace "Ah, saurayi tayi, shine ya zo gurinta, kuma very soon zai zo yayi Maganar Aure". "Impossible, akan me za'ai mata Aure? Idan har ina raye ba wanda zai auri Abra" yayi Maganar jijiyoyin kansa na miƙewa. Na'ima ta ce "ba ka da hankali ne? Uban me za'ai da ita idan ba tayi Aure ba? Ai gara tai Auren ta bar mana gida, ko mahaifinka ya maida hankali sosai a kanka". "Ba wanda zai Auri Abrah Mami? Abra tawa ce, Wallahi duk wanda ya kuma zuwa gidan nan da sunan yana sonta, sai na masa illa". A fusace ta miƙe ta ce "Salman, ka san me kake faɗa kuwa? Me kake nufi da Abra taka ce?". "Mami, let me voice out my secret to you, Wallahi Mami am in love with my sister, ina kishinta, Mami tun lokacin da kika gaya mini ba ke kika haifeta ba, na gane son da nake mata ba na 'yan uwanta bane kawai, Auren Abra nak.....  Marin da ta sauke masa ne, ya hana shi ƙarasa Maganar, ya dafe kuncinsa yana kallon Hajiya Na'ima. "Baka isa ba Salman, Wallahi kayi kaɗan, ni zaka tonawa asiri, yarinyar ta girmeka da shekaru uku, kace mini ita ka ke so, kwata kwata shekarunka nawa zaka yi wani zancen soyayya, ko dan kana ganin ka haka da girman jiki?, yarinyar da ta zame mana alaƙaƙai nake neman maraba da ita. Wato so kake ka tona mini Asiri, mahaifinka ya san na gaya maka ba ni na haifeta ba ko? Wai kai banda hauka irin na ka ka manta ubanku ɗaya da ita? Karuwar babanka ce ta haifeta ta yaya za kuyi Aure?". Girgiza kai Salman yayi yace "A'a Mami, Abbi ba ze taɓa aikata abunda kika faɗa ba, ina nan akan bakana Mami, Abra nake so, Ina sonta Sosai". "Shut up Salman! Wato ba zaka dena wannan banzar Maganar ba ko? Gara yayi ya dawo in sanar masa, ayi a aurara da ita in ga ta tsiya, idan kuma shirya tona mini Asiri ka yi a gurin mahaifinka ga fili ga mai doki. Amma duk jarabarka Wallahi ba zaka auri yarinyar nan ba, dole ta auri wani ta bar gidan nan". "Am sorry Mami, amma babban kuskuren da za'a aikata shine a aurawa Angel wani ba ni ba, zan iya aikata duk abunda zuciyata ta raya mini, dan cinma burina, she's mine" ya faɗa tare da nuna ƙirjinsa da yatsa, daga nan ya fice daga ɗakin. Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke ta ce "tirƙashi, lallai Salman ba ka da hankali, ba za ka janyo mini sakiyar da babu ruwa ba, dole in maganinku gaba ɗaya. Major Khamal kuwa, cike da farin ciki, gefe guda kuma baƙin ciki ya dawo Kaduna, dan ji yake ko ba duka, an samo lagon rashin tsaron da ya addabi ƙasar mu, daga gefe yana sake jinjina tare da baƙi cikin samun bara gurbi a cikin rundunar tsaro. Bayan Adnan ya sauka a Kaduna, har dare Abra ba ta neme shi ba, sai shi ya nemeta duk da kuwa yadda tai kewarsa. Ita Abra babban abun da ya dameta rashin ganin Faris, taje ɗakinsa ta tarar ya rufe ƙofa, dan haka ta haƙura ta koma ɗakinta. Tana zuwa ta tarar da kiran Adnan na shigowa wayar ta ta, ta sa hannu ta ɗau wayar, tare da kwanciya akan lafiyayyen gadonta. "Angel shine ko ki neme ni, balle ki ji yana je gida ko?". Tace "Na neme ka mana" "A ina?". "Addu'a na yi maka, Allah ya kaika lafiya". "Na ji, na kuma gode, amma ai Yakamata ki kirani ki ji ko naje lafiya". "Ba kai ne kai mini tsawa ba kafin ka tafi". Adnan yayi dariya yace "Fushi kike kenan? Ai idan nace bana son abu, bana buƙatar sake maimaitawa, amma ke se kiyi biris, shiyasa nai miki tsawa, amma na dena kinji My wife". Tayi ajiyar zuciya tace "to ya kaje gida?". "Ba na so, tun da sai da na roƙa". "To nima ban haƙura ba da kai mini tsawa". Abra ba dai shiririta ba, ya faɗa a ransa, ya dinga janta da hira, har kusan ƙarfe goma na dare, sannan sukayi sallama. Duk ɗokin da Abra take idan Abbi zai dawo, a wannan karon sai ta shiga fargaba da zullumi, dan bata san ya zai ɗauki Maganar Adnan ba idan Mami ta gaya masa. Da daddare Hajiya Na'ima ta sami Major a ɗakinsa, suna cikin hira ta ce "to kai fa 'yar ka magana ta ɗakko". "Wace Maganar kenan?". "Ta zo ta sameni da wani batu, ta ce mini in sanar maka ita Aure ta ke so". "What? Abran ce ta gaya miki haka?" "Ƙwarai kuwa, tace mini Aure take so, dan ta kawon wanda take so ɗin har gidan nan ya zo jiya". "Dan meyasa kika bari wani yazo mini gurin 'ya ta ba da izinina ba?". Hajiya Na'ima tace 'ban gane ba, ta zo ta sameni da Magana, kuma sa ince mata a'a". "Tambayar ki nake dan me wani zai zo mini gida gurin 'yata ba da izini na ba? Kuma ita Abran zan sameta, karatu za tayi ba Aure ba". "Wai me kake nufi ne da yarinyar nan? Idan ba ai mata Aure yanzu ba sai Yaushe, kai da ɗanka kun hana kowa ya zo gurinta da sunan yana son ta, wai ni ko kai ke son yarinyar nan ne?". Major yayi murmushi yace "Ina son 'ya ta mana, amma kin manta ni ne ubanta, ko har kin manta 'yar da karuwa ta haifa mini ce?" Hajiya Na'ima ta kwantar da murya, ganin yana nema ya maida Maganar wani na daban. "Major dan Allah ka duba lamarin nan, yarinyar nan tum da har ta riga ta furta tana son Auren nan, ni banga dalilin da zai sa ka ce saita gama karatu ba sannan za'ai mata Aure, yarinyar nan Allah yayi mata kyau me ɗaukar hankali, baka tunanin abunda ka iya faruwa a jami'ar da ka tuarata. Shi kuwa Aure garkuwa ne ga 'ya mace, idan akai mata Aure zata samu wata kariya daga sharrin mazan jami'a da lalacewa". "In kinga ɗa ya lalace a makaranta, to dama can lalataccen ne, amma ni 'ya ta ba lallatacciya bace, kuma ba gazawa nai da ɗaukar ɗawainiyarta ba, dan haka a ƙyalemini 'ya ta". "Yanzu kana ganin lamarin nan ba abun dubawa ba ne? Ita fa da bakinta ta ce mini Auren ta ke so". "Na'ima, ba zanwa Abra Aure yanzu ba, na gama Magana" yana faɗin haka, ya tashi ya bar mata ɗakin. Shiru ta yi tana tunanin, meye mafita al'amura na neman su kwaɓe mata, ga Salman na neman bijiro da wata Magana, ga mahaifinsa ya dage baze aurara da Abra yanzu ba, dole ta yi wani abu a kai, dan kar abunda ta ke gudu ya faru, wato Salman ya auri Abra. Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750 [10/3, 2:40 PM] Abk: Miƙewa Na'ima ta yi ta nufi ɗakin Abra. Tana kwance idanunta a lumshe cikin damuwa da fargabar yadda Abbinta zai karɓi maganar Adnan, saboda Adnan ya takura mata akan maganar Aure daga daren jiya zuwa safiyar yau, ya sanar mata har ya faɗa wa Abbansa ya ce Next week za su zo tambayar Auranta, ga rashin saka Salman a idonta, tun jiya kafin ya tafi Ball ba su ƙara haɗuwa ba, ta kikkira wayarsa kuma ba ya ɗauka, ga Mr unknown sai Text yake mata na magiyar yana son duk rintsi duk wuya kar ta rabu da shi, soon zai bayyana a gare ta. "Abra! Abra! Abra!" Ta tsinkayi muryar Mami a cikin kanta, a hankali ta buɗe idonta tare da tashi zaune cikin sanyin jiki. Zama Na'ima ta yi a gefenta ta ce. "Ke lafiya kike kuwa?" Numfashi ta sauke ta ce. "Lafiya ƙalau Mami." Taɓa baki Mami ta yi ta ce. "Idan ma akan maganar Aurenki ne ki kwantar da hankalinki tamkar an yi an gama, abun da nake so dake kawai idan Abbinku ya tambaye ki kina son Auren ki ce masa eh, shi ne kawai solution. Gyaɗa mata kai Abra ta yi cikin kunya, mamakin abun take, wai ita ce yau ake maganar za a yi Auranta, abun da ba ta taɓa tunanin yin shi nan kusa ba. "Yawwa ƴar Albarka, fatanmu kawai Allah ya kai mu lokacin mu sha biki." Na'ima ta faɗa cikin murmurshi tare da dafa kafaɗarta. Rufe fuskarta ta yi da hannunta tana murmurshin ita ma. Yau kam ta gasgata maganar Salman da yake ce mata Mami tana son ta, for the first time in her life ta goyi bayan abun da take so, kuma har ta zauna tana yi mata magana cikin kulawa da fara'a, hakan ba ƙaramin farinciki da jin daɗi ya haifar mata ba. Kwantar da kanta ta yi akan kafaɗar Mami, wata muguwar harara Na'ima ta gallawa kan Abra, a ranta tana jin tamkar ta shaƙe ta har lahira, amma a fili sai ta shiga shafa kanta. "Mami yau Salman ya fito kuwa?" "Wai mene damuwarki ne akan hakan? Tun da kika tashi sai tambaya ta Salman kike, yaro ne shi ko jariri da za a saka masa ido irin haka?" "Mami may be fa ba shi da lafiya ne." Ta yi maganar kamar za ta yi kuka. "Lafiyar kenan, don lafiya ita take sa a ji shiru, da wani abu yana damun shi ai da tuni mun sani." Na'ima ta faɗi haka tare da zame kan Abra daga jikinta ta miƙe ta fice. Bin ta da kallo Abra ta yi, zuciyarta cike da mamakin Mami, yanda Mami take nuna over caring akan Salman da damuwar shi amma yau ta ga kamar ko a jikinta da rashin fitowar tasa, don ɗazu ma a da za su yi breakfast ta ce za ta kira Salman ganin bai fito ba hana ta Mamin ta yi ta ce ta ƙyale shi, cikinsa ne ai ba na wani ba. Tashi ta yi da sauri ta gyara hular kanta ta fice zuwa ɗakin Salman. Yana zaune akan bedside drawer hannayensa duka a cikin sumar kansa yana yamutsawa Abra ta yi knocking Kofar ɗakinsa. Ko ba a faɗa masa ba ya san ita ce, kamar ya share ta kamar yadda ya yi mata ɗazu amma sai ya kasa, numfashi ya sauke tare miƙewa ya je ya buɗe ƙofar. "Bloody what happened to you?" Abra ta faɗa kamar za ta yi kuka. Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi tare da lumshe idonsa, kaso mafi yawa na damuwa da ɓacin ran da yake ciki ya fara gushewa, sakamakon tozali da kyakkyawar fuskar Angel ɗinsa gami da shaƙar sassanyan daddaɗan ƙamshinta. Juyawa ya yi ya koma ya zauna a bakin gado ba tare da ya ba ta amsa ba. Ƙara tashi hankalin Abra ya yi ganin yanayinsa kamar yana cikin damuwa, bin bayansa ta yi da sauri ta dafa kafaɗunsa idanunta cike da ƙwalla ta ce. "Faris please talk to me, me ya sa jiya ba ka fito ba? Ko dinner ba ka yi ba, yau ma ba ka yi breakfast ba." Ganin tana shirin fashewa da kuka ya kama hannunta ya zaunar da ita a gefensa, idanunsa cikin nata ya ce. "Ke ce Angel, kin hana zuciyata sukuni, jiya ko bacci ban iya yi ba." Ya yi maganar cikin tsantsar damuwa. "Innalillahi! Ni kuma Faris? Me na yi maka?" Shiru ya yi bai ce komai ba sai hannunta da yake murzawa a hankali tare da sauke ƙananun ajiyar zuciya, bai san ya yi missing ɗinta over ba sai da ya gan ta yanzu a kusa da shi, ba ƙaramin daure zuciyarsa ya yi ba na hana kansa ganin ta ba a jiya, ya kwana cikin ɓacin rai da takaicinta ita da Mami. "My Faris ka faɗa mini abun da na yi maka mana, tun kafin ka faɗa mun na yi maka alƙawarin ba zan kuma ba, I'm sorry please, ka san bana son ganin ka a irin wannan yanayin na damuna ko?" "Abra! ashe zaki iya yin Saurayi har ya zo gidan nan ba tare da na sani ba? Ashe akwai abun da zaki iya ɓoye mini a rayuwarki?" Ƙasa ta yi da kanta cikin rashin ganin kyautawarta, amma ita ta yi hakan ne saboda gudun ɓacin ransa, ashe ta yi gudun gara ne ta tadda zago, kuma ba ta yi tunanin zai sani ba, yanzun ma ta san Mami ce ta faɗa masa. "I'm sorry Bloody." Ta faɗa cikin raunin murya. "Hmm, kin san ba zan iya dogon fushi dake ba ne shi ya sa kike mini abun da kika so, babu komai." "Haba Salman, don Allah kar ka ce haka, kai ma ka san ba haka ba ne." "Ya ya ne?" "Bana son ɓacin ranka ne, kai ma ka sani." Kama haɓarta ya yi ya saka idanunsa a cikin nata dake cike da hawaye, cikin raunin murya ya fara magana. "Angel dama za ki iya tafiya ki bar ni? Dama akwai ranar da za ki bi wani alhalin gani? Please My Baby ki tausayawa ɗan ƙaninki, kar ki bar ni Pleaseee!" Ya ƙarashe maganar da jan harafin ƙarshe cikin wata irin siga. Lumshe idonta ta yi ba tare da ta shirya hakan ba, ko kaɗan ba ta ɗauki kalaman Salman da wata manufar ba, ta ɗauke su matsayin tsananin shaƙuwar dake tsakinsu ce ta saka ba ya son su rabu. Ba tare da ta buɗe idonta ba ta ce. "Ni ma bana son na yi nesa da kai My Faris, amma ka san ai aure dole ne, watarana dole na y......" "Na sani Angel, za ki yi aure, amma ba da wani ba." Ya katse ta da faɗin hakan cikin kaushin murya. Buɗe idonta ta yi tare da waro su waje ta ce. "To da wa zan yi?" "Da mijinki, wanda yake ƙaunarki fiye da kowa a duniyar nan, wanda ya yi shekaru yana dakon son ki a cikin zuciyarsa." Murmushi ta yi tare da cire hannunsa daga kan fuskarta ta ce. "To ai shi ne wanda...." "Ba shi ba ne." Ɓata fuska ta yi ta ce. "Ta yaya ka sani? Ni ma fa ina son shi." Runtse idonsa ya yi da sauri yana jin tamkar ta soka masa mashi a cikin zuciyarsa, cikin wata irin murya ya ce. "Please Angel kar ki ƙara faɗar haka a gabana." "Why?" "Kawai." "Shikenan, ni mu bar wannan zancen, ka taso mu je ka ci abinci, jiya da ƙyar na iya bacci saboda rashin sanin halin da kake ciki." "I'm Okay." Ya faɗa a tak'aice. "Kana son ka gan ni a cikin damuwa ne Faris? Ba ka san yanda nake ji ba idan na gan ka haka, Please ka taso mu je ka ci abinci." Ta yi maganar kamar za ta yi kuka. Ganin yanda ta nuna damuwarta a kansa sai ya ji wani sanyi a ransa, cikin shagwaɓa ya ce. "Sai dai in zaki ba ni a baki." Da sauri ta ce. "To zan baka, ni dai burina ka ci abincin." Bai ce komai ba sai hannunta da ya kama ya ɗora akan ƙirjinsa, saitin zuciyarsa, yana bin ta da wani irin kallo mai kashe jiki ya ce. "Ji yanda zuciyata take bugawa saboda ke Angel." Murmushi ta yi cikin wautar rashin sanin abun da yake nufi ta yi sama da hannunta ta shafi kuncinsa ta ce. "Ka daina damuwa bloody, ba abun da zai raba ni da kai." "Sure?" Gyaɗa masa kai ta yi tare da jan karan hancinsa da ɗan ƙarfi. Ɓata fuska ya yi ya ce. "Kin takura wa hancina Angel, ko dan kin ga ya fi naki kyau ne?" "No, daɗin ja ne da shi kawai." Ta yi maganar tare da ƙara jan hancin nasa. Murmushi suka yi a tare cikin tsananin shauƙin junansu da suke ji a cikin ransu, daidai lokacin Mami ta turo ƙofar ɗakin da ƙarfi. Cikin ɓacin rai take duban su ɗaya baya ɗaya, tsayar da idanunta ta yi akan Abra cikin haɗe rai ta ce. "Me kike anan? Wai ku ba za ku taɓa girma ba ne? Goɗai-goɗai dake kin wani taho ɗakin ƙaninki, wanne irin shashanci ne wannan?" Sunkuyar da kai Abra ta yi tare da faɗin. "Ki yi haƙuri Mami." "Dalla ni ta so ki wuce, tun ɗazu Abbi na neman ki, na je ɗakinki ba kya nan, na jira ko kina toilet amma shiru, dama na san babu inda za ki yi sai nan." Jiki a saɓule ta miƙe ta fice cikin mamakin yanda Mami ta koma mata sak ta da, kamar ba ita ce ta gama yi mata magana cikin kulawa da ƙauna ba ɗazu. "Wato ko gaishe ni ban isa ka yi ba ko Salman?" "Zan gaishe ki mana Mami, na ga kina magana ne shi ya sa, ina kwana?" "Ban sani ba, ka riƙe gaisuwarka bana so, mara kunya kawai, har ka yi girman da za ka dinga irin wannan abubuwan ko? Yaushe na haife ka? Yaushe na gama goya ka a bayana?" "I'm sorry." "Sorry for your self." Ta ƙarashe zancen tare da jan tsaki sannan ta juya ta fita. Bin bayanta da kallo Salman ya yi, cikin ransa yana faɗin, duk rintsi ba zai rabu da Abra ba, ba gudu ba ja da baya a soyayyar ta." A parlour Mami ta tarar da Abra a zaune. "Mami ina Abbin ban gan shi ba?" "Ya fita zai amso saƙo, tun ɗazu yana ta jiran ki har aka kira shi ya fita." Na'ima ta faɗa ba yabo ba fallasa. Gyaɗa kai kawai ta yi zuciyarta cike da fargaba, tsoron gamuwa da Abbi take tunda ta Na'ima ta ce ta faɗa masa maganar Adnan, addu'ar ta ɗaya Allah ya sa ya amince. Fahimtar hakan ya sa Na'ima ta fara kwantar mata da hankali, tare da jadda mata ta kafe akan ra'ayinta ko me Khamal zai ce mata. "Abra burin kowacce Uwa ta gari ta ga aurar da ƴarta, shi ya sa kina mini batun yaron nan na ji daɗi a raina, musamman da na fuskance shi da gaske yake, ba kamar sauran samarin yanzu mayaudara ba, dan haka kar ki bari ya kufce miki, ki riƙe shi hannu bibbiyu." "Insha Allah Mami na gode." Abra ta faɗa cikin gamsuwa, dan malaminsu na islamiyya ya taɓa faɗa musu cewa duk Uwa ta gari burinta da fatanta ta ga ta kai ƴarta ɗakin Mijinta. Wannan dalilin ya sa yau ta fara kawar da tunanin da Mami ba mahaifiyarta ba ce kamar yadda take tunani a baya. Ganin Salman bai fito ba ya sa ta miƙewa ta shiga ɗakinta don ta kira shi a waya ta lallaɓa shi ya fito ya ci abincin. Tana ɗaukar wayar ta tarar da 3 missed call na Adnan, bin bayan kiran ta yi cikin sauri. Tana shiga ya katse ya kira ta. "Amincin Allah ya tabbata ga kyakkywar Amaryata." Abun da ya faɗa kenan bayan ta ɗaga wayar. Murmushi ta yi tare da zama ta ce. "Tare da kai." "Ina kika shiga mijinki yana kiran ki ba ki ɗauka ba, na kasa komai saboda rashin jin daddaɗar muryarki mai mantar da ni inda nake." Dariya ta yi ba tare da tunanin komai ba ta ce. "Na je ɗakin Faris ne." Shiru ya yi na 2 seconds sannan ya ce. "Faris, Faris dai, magana ɗaya sai kin ce Faris." "Faris is my best friend, he is my everything at all." "Ko?" Ya tambaya cikin gatse. "Yeah." Ta ba shi amsa iya gaskiyarta. "Ina son na maye gurbin Faris a cikin zuciyarki ko ma na zamo fiye da shi. Now tell me, me Abbi ya ce game da maganata, na san yau Sunday yana gari." "Mami ta faɗa masa." "Ya amince?" "Idon't know, amma duk yanda ake ciki zan sanar maka." "Allah ya sa mu ji Alkhairi matata, ya nuna mana ranar da za ki kasance mallakina, ban san irin farincikin da zan yi ba a ranar Angel, because I love you will All my heart." Murmurshi ta yi cikin jin daɗin kalamansa, hira suka cigaba da yi, Adnan na faɗa mata yanda yake tsananin ƙaunar ta, tare da son koya mata ƙaunar shi. Har sai da Mami ta shigo ta kira ta tare da sanar mata Abbin ya dawo. Cikin faɗuwar gaba ta miƙe ta bi bayan Na'ima zuwa part ɗin Abbi, yana zaune akan kujera suka shiga, Na'ima ta zauna a gefensa Abra kuma a saman carpet ɗin dake shimfid'e a parlour'n. "Sannu da hutawa Abbi." Ta faɗa kanta a ƙasa. "Yawwa Daughter, Mamanku ta zo mini da wata magana jiya wadda ban amince da ita ba, ki faɗawa shi yaron da kika kawo shi gidana ba tare da iznina ba ya nemi wata, ke yanzu karatu zaki yi ba aure ba." Dam zuciyar Abra ta buga, satar kallon Na'ima ta yi, Signa ta yi mata alamun ta faɗi duk abubuwan da ta ce mata. "Dan Allah Abbi ka yi haƙuri ka amince wallahi ina son sh....." "Shut up! Ni zan dinga faɗar abun da za a yi kina cewa ba haka ba? Wato har kin yi girman da zaki fara jayayya da ni ko? To na faɗa na kuma faɗa, ba zan yi miki aure yanzu ba karatu zaki yi." Khamal ya katse ta da faɗin haka cikin tsawa. Kuka Abra ta saka ta fara bawa Abbi haƙuri, bai saurare ta ba ya ce ta tashi ta tafi. Kallon Khamal kawai Na'ima take yi cikin ƙunar zuci, cike da takaici ta ce. "Gaskiya Major abun da ka yi ba ka kyauta ba, wai mene dalilinka na ƙin son aurar da yarinyar nan ne? Ni fa ban gane ba, ko kwaɗata za mu yi mu cinye? Haba yarinya ta fi 20 years amma ka ce ba za ka aurar da ita ba wani karatu za ta yi, karatun me? Ai aure ba ya hana karatu, haka ma karatu ba ya hana Aure." Wani mugun kallo khamal ya wurga mata sannan ya miƙe ya bar parlour'n. Jijjiga kai ta yi tare da miƙewa ta fice ita ma. Ɗakin Abra ta je, tarar da ita ta yi ta kifa kanta akan gado tana kuka. A hankali ta ɗago da ita ta rungume ta. Cikin sigar rarrashi ta ce. "Ki yi shiru haka kar kanki ya yi ciwo, ki bar ni da Abbi na san ta inda zan ɓullo masa." Cikin kuka Abra ta ce. "Mami na haƙura tunda Abbi ba ya so, bana son in ga yana fushi da Ni." Da sauri Na'ima ta ce. "A'a Daughter, tunda kina son shi yaron zan yi duk yanda zan yi na ga kin Aure shi, kar ma ki ƙara tunanin za ku rabo, ko ba kya son shi ne?" "Ina son shi." "To kuma, abun da nake so dake kawai guda ɗaya ne, ki daina mayar da hankali akan karatunki." Cikin mamaki Abra ta ce. "Ban gane ba Mami." Zama ta yi a gefenta ta ce. "Yawwa, abun da nake nufi ki daina karatu, idan an ba ku assignment ki daina yi, ba dai saboda karatun ya ce ba zai aurar da ke ba?" Gyaɗa mata kai Abra ta yi. "To idan ya ga an kafe result duk kin faɗi dole ya aurar da ke ai." Shiru Abra ta yi tana nazarin abun da Mami ta ce, anya kuwa za ta iya? Idan ta yi hakan fa tamkar ta watsa wa Abbinta ƙasa a ido ne, wani b'arin na zuciyarta kuma hango mata yake rabuwar su da Adnan, gaskiya ba za ta so su rabu ba, kawai za ta bi shawarar Mami. Cikin rashin wayo ta ce. "Za mu yi text gobe, kar na yi karatun ta kenan Mami?" "Kar ki yi, idan kin je class an yi muku attendance kar ki kuma yi, ko assignment aka ba ku ki daina yi kin ji yarinyar kirki?" Shiru Abra ta yi tana tunani, ganin kamar ba ta gamsu ba ya sa Na'ima ta gyara zama ta shiga kalailame ta da nuna mata illar rabuwar ta Adnan, har ta samu ta amince da shawarar tata ta daina yin karatu, cikin murmushin mugunta ta rungume ta ajikinta tare da saka mata albarka. Abra har cikin ranta ta yarda da abubuwan da Mami ta faɗa mata, soyayyar Adnan da ta yiwa zuciyarta mugun kamu gami da tsoron rabuwa da shi su suka taimaka gurin ƙara assasa amincewa da hakan, ta manta Abbinta mutum ne mai magana ɗaya gami da kafiya akan abun da ya ce, ko da ba ta mayar da hankali akan karatun ba idan bai so ba, ba zai aurar da ita ba. Bayan Magriba Na'ima na zaune a parlour suna waya da Ammi tana sanar mata halin da ake ciki. Bayan ta gama Ammi ta ce. "Wacce irin magana ce wannan? Me Babana yake nufi da aikata wannan ɗanyen aikin da yake ƙoƙarin yi? Idan ba a aurar da yarinyar ba saka ta za mu yi a gaba mu dinga kallon ta? Ai aure shi ne mutuncin kowacce mace, kowa na addu'a Allah ya kawo wa yarsa miji na gari shi kuma ya samu zai ce a'a, to bai zai yiyu ba, zan zo har gidan in same shi in nusar da shi illar abun da yake ƙoƙarin aikatawa? Bokon me? da za a ce saboda ita za a jinkirta aure, komai fa lokaci ne da shi, ban da abun Babana ai wannan abin farinciki, addu'a kawai ya kamata ya yi tare da bincike akan yaron da ahalinsa dan tabbatar da nagartar shi." Cikin jin daɗi Na'ima ta ce. "Abun da na yi ta faɗa masa kenan Ammi, amma ya ƙi ji ya yi biris da ni, kuma wallahi Ammi ba ki ga yaron ba nutsatstse ga hankali, daga gani ɗan gidan manyan mutane ne wanda suka san darajar kansu. Gashi ita ma Abran tana son shi sosai, dan baki ga yanda take kuka ba da Khamal ya ƙi amincewa." Salman da ya fito dan zuwa kitchen ya samarwa kansa abun da zai ci jin yunwa na ƙoƙarin hallaka shi kalaman Mami suka doki dodon kunnansa. Cak ya tsaya cikin wani irin yanayi, a razane ya ce. "What? Mami! Ammi kika sanarwa da wannan maganar?" Hararar shi Na'ima ta yi ta cigaba da sauraren Ammi dake sanar mata gobe da safe za ta yi sammako ta zo ta sami Khamal kafin ya tafi gurin aiki, don ta ba shi umarnin amincewa da batun neman Auren Adnan da Abra. Dafe kai Salman ya yi cikin takaici, Mami ba ƙaramin gamawa da shi ta yi ba da ta sanar da Ammi maganar nan, saboda yanda Ammi ba ta zance kodayaushe sai na Allah ya kawo wa Abra miji ta yi aure. Amma duk da haka ba zai haƙura ba, matuƙar yana numfashi ba zai bari wani ya auri Abra ba shi ba, dan haka zai fasa ƙwai kowa ma ya san abun da yake faruwa, zai sanar da Abbi cewa yana son Abra zai aure ta a yau ba gobe ba, in ya so duk abun da zai faru sai dai ya faru![10/4, 3:15 PM] Abk: A fusace Salman ya juya kai tsaye kuma Part ɗin Abbi ya nufa, zuciyarsa babu daɗi ji ya ke tamkar zata faso ta tsakiyar ƙirjinsa ta fito, saboda tsananin bugawa da ta ke da ƙarfin gaske. Gane nufin Salman ya sanya Mami saurin miƙewa tare da shan gabansa, fuskarta sam babu walwala a kaushashe ta ce. "Well-done, wato kana nuna mini ban isa da kai ba? kada ka manta ni na ɗauki cikin ka, nai dakonsa na tsayin watanni tara, na haife ka. Haihuwar da babu shiri, kana na raine ka, na shayar da kai nonona na tsayin shekaru biyu. Amma yau ni nake faɗa maka magana kana yi mini musu? Yarinyar da ba ni na haife ta ba, ta fika yin biyayya a gareni ko Salman" "Mami ya ya ki ke so na yi da raina? tun da na buɗe idanu da Yaya na fara arba cikin rayuwata, ita ce komai nawa, jin daɗina, farin cikina, kwanciyar hankalina, gaba ɗaya Abra ce silar komai Mami, ko kuka nake zata sanyani dariya, bata bari na cikin damuwa, she love's me, and I love  her too, we love each other Mami" Zuciya ce ta kwashi Mami bata tsaya jiran komai ba, ta ɗauke Salman da wani irin wawan mari wanda ya sanya ya yi saurin runste idanunsa tare da safe kuncinsa, idanunsa ya yi jajur sai ajjiyar zuciya ya ke saukewa. Da hannu ta nuna shi tana mai girgiza kai  ta ce. "You are lying, if I am alive you will never marry Abra, kai da ita sai dai hange da ga nesa, ba zaku taɓa zama abu guda ba,You want  reveal the secret and make your father divorce me" Kallon ta kawai Salman ya ke, yayin da ya ke jin ƙuncin zuciyarsa na ƙaruwa fiye dana baya. "Mami marina ba zai hana na janye da ga kan ƙudirina ba, me yasa ki ke son a dole ki gyara kuskuren da kin riga da kin aikata?, da ace kin ajjiye cewa Abra ba ƴarki bace a zuciyar ki, baki gaya mini na, da yanzu ban furta kalma SO ba, da ban yadda sonta yayi mini illa na, balle har aje ga batun aure, da har zuwa yanzu zan cigaba da ɗaukar som da nake mata na 'yan uwanta ka, buy it's too late to cry Mami wallahi wallahi I will never stop loving her, and I wan marry her, zan faɗawa Abbi everything dake faruwa zan faɗa masa yadda nake son Angel, wataƙila shi ya fahimce ni" "Ni kuma faɗa masa daidai yake da in tsine maka albarka!, wallahi ko da wasa ka faɗawa mahaifinka, cewa kana son Abra sai na tsine maka, kabi duniya in huta da Masifa, wannan wace irin jaraba ce? Tunda yarinyar nan ta shigo rayuwarmu komai ya lalace mini" Sai kuma ta saka kuka tana faɗin "Yanzu Salman a duniya ko ban haifeka ba, nace kada ka aikata abu ba zaka iya yimin alfarmar hakan ba albarkacin riƙon da nayi maka?. Balle kuma ni nasan zafin haihuwar ka, akan mace zaka nuna fifiko akan mahaifiyar ka?" Idanun Salman cike da hawaye ya ce. "shi kenan, amma duk abun da ya sameni a rayuwa Mami ke ce sila, rasa Angel daidai ya ke da rasa raina" Yana faɗin hakan ya juya da sauri tare da barin gidan baki ɗaya, domin da zarar yaci gaba da zama komai zai iya faruwa. Da daddare Abbi na zaune akan kujera sanye da kayan bacci, idanunsa maƙale akan system yana duba wani abu, gefe guda kuma black tea ne wanda aka matsa masa lemon akai. Mami ce ta shigo cikin bedroom ɗin tana zabga ƙamshi cikin shirinta na kwanciya bacci, a hankali ta zauna gefen sa tana faɗin. "Barka da dare Yallaɓai" "Yawwa" ya amsa ba yabo ba fallasa ganin yanayin sa ya sanya ta ce "You are still angry because I told you the truth?" "Sure" Ya bata amsa nan ma a gajarce har yanzu kuma bai ɗaga kai ya kalleta ba, sai ma tea ɗinsa da ya ɗauka yana sha a nutse. Cikin damuwa Mami ta ce. "Na kasa fahimta, kai na ya ɗaure" sai a lokacin ya buɗe baki cikin ko in kula ya ce "ba zaki gane ba daman, bana da tabbacin kuma zaki gane" "Idan baka bari Abra tayi aure ba, kai ne zaka aureta?"  Da shock Abbi ya ke kallon Hajiya Na'ima, jin anun da ta faɗa, sai kuma ya saki Murmushi cikin nutsuwa ya furta. "Ina tunanin babu haramun a hakan, dani dake kin san ba ƴar cikina bace, so anything can happen as you said" "Me kake nufi? I can't hear you correctly me kake son faɗa mini?" Juyawa ya yi gaba ɗaya zuwa inda take idanunsa cikin nata kafin ya numfasa ya ce. "Ina nufin ba zanwa Abra aure a wannan situation ɗin ba, sai ta gama schoo'l ta zama ƴar jarida. Idan da hali ta haɗa komai nata na karatu, ban damu da adadin shekarun da zata ɗauka ba, cikakken ilimi nake son bata wanda za tayi alfahari da shi, sannan innzaɓa mata nagartaccen miji, wannan shine gatan da zan yiwa Abra, wanda zai amfaneta ko bayan raina, don Allah kada ki sake zuwar mini da maganar wani aure i don't like it. Bana jin kuma akwai wanda zai sauya min tunani kada na sake jin labarin kuma wani ya zo ƙofar gidan nan da niyyar zance wajan Abra Khamal Khamis. Idan har kin ɗaukeni matsayin miji" Yana faɗin hakan ya miƙe tsaye tare da ɗauke system da tea ɗinsa ya nufi cikin library gidan domin samun peace of mind. Mami kasa motsawa ta yi me hakan ke nufi? Kada fa dace ta jawa kanta, garin neman gira a rasa idanu. Kamar mahaukaciya haka ta miƙe ta nufi part ɗinta. Washe gari bayan sallar Subhi Abra na zaune tana azkar kamar yadda ta saba, lokacin ƙarfe 6:10 wayarta ce ta ɗauki vibration alamar notification ya shigo. Hannunta har rawa yake wajan buɗewa musamman da idanunta ya sauka akan number _Unknown_ mutumin da a koda yaushe take jin tsananin faɗuwar gaba idan ta riski saƙonsa, rashin ganin saƙon kuma ya kan jefata tunanin a wane hali yake ciki. Fararen idanunta dake cike da bacci ta lumshe a hankali kuma ta buɗe su, tare da sauke ganinta saman screen ɗin wayar. Message ne rututu daga na _I love You_ sai na _I miss You_ tare da jaddada kalmar _LOVE_ Saƙon farko ta buɗe a hankali ta fara karantawa kamar haka. _Your love splashes on my mind, I cannot do without thinking of the moments that concern us both. You are my laughter, joy, and peace. Anytime I can find you beside me, it means I am deprive of these virtues. I know I am not that strong enough to come see you right now, but I have you in my heart beating in a speed of light._ Idanunta ne ya cicciko da hawaye, a fili ta furta "Who are you? Mene yasa kake ɓoyewa? Maybe Adnan Aliyu Matawalle ne? Anya mutumin da kai tsaye ya bayyana mini abun da ke ransa, mai zasa ya dinga yi mini wasa da hankali?"  saƙo na biyu ta duba mai ɗauke da faɗin. _Kiyi haƙuri da rayuwa a duk sanda ta zo maki, ina ji a Zuciyata ke ta musamman ce, ke abar alfahari ce, burina ki ai jirani soona or later zan bayyana a gareki Abra, ban san ya zan kwatanta maki yadda matsayinki yake a zuciyata ba, zan baki misali da wanda aka ce yau ya wayi gari zuciyar sa ta  daina aiki. You're a darling. Anna Uhibbukiiii_ Jikinta na rawa ta duba buɗe saƙo na ukun mai ɗauke da crying na Emoji da kuma heart, sai double kiss sama da ashirin tare da sticker ta hug. "Ba'a wasa da kalmar soyayya, don Allah ka bayyana a gareni kada ka sanya zuciyata ta buga" cikin sauri take typing ɗin tana gamawa ta danna _Send_ ya tafi sai kuma ta yi shiru tana tunani, mai yasa ta damu da wannan unkown ɗin bayan ga Adnan ɗinta?. Babu jimawa ya yi mata reply da _Just pray_ kasa reply tayi tunani duk ya addabi zuciyarta. Shiru tayi ta shiga kogin tunani, yau tana da test, gashi Mami ta hanata karatu. ' Mami ki kewa karatun? Kin san ambition ɗin da mahaifin ki yake da shi akan ki? Kin kyuta masa ke nan?' wata zuciyar ta gargaɗeta ita kanta ta san ba daidai bane, dole ta san abun da ta ke, ba zata taɓa yarda ta ɓatawa Abbi rai akan soyayyarta da Adnan ba. This is not fair. Sai Yamma suka dawo da ga makaranta, duk tsayin lokacin da sukai a school tsakaninta da Salman Idanu, sai ya zauna ya yi ta Kallonta ko kuma da sun haɗa idanu ya lumshe nasa idanun,ya zama wani so silent duk surutun nan nasa babu, ko littafi ya ɗauka zai karatu sai ya tafi tunani. Ammi ce zaune a Parlourn dake part ɗin Abbi, bata samu zuwa ba sai yamma, yayin da Abbi ke zaune ƙasan carpet kansa a ƙasa yana sauraren abun da take faɗa masa. A sanyaye ya ce. "Ammi ban hana Abra aure ba, ban kuma ce ba zata ba, abun da ka sani shi ne sai ta kammala makaranta zan aurar da ita, nasan yarinyata zatai mini biyayya ba zata taɓa watsa min ƙasa a idanu ba" "Ni kuma a matsayina, na uwa a gareka wacce ta kawo ka duniya nace dole a Aurar da Abra, kuma ka bayar da dama ga wanda ya ke son nata ya turo magabata ai magana, ka faɗa mini inda aka ce karatu ne gaba da aure? banda Aƙidar banza da wofi ma mene wani karatu, wallahi akan maganar nan sai na saɓa maka" Kamar Abbi zai kuka haka ya buɗe baki da ƙyar ya ce. "Shi kenan Ammi, zan yi bincike akan yaron sai na bashi dama, kiyi haƙuri na janye kalamai na" Murmushi ta yi ta ce "Ma sha Allah, Ubangiji ya yi maka albarka dakai da zuri'ar ka, Allah ya sanyawa auren albarka" "Amin" ya ce yana Miƙewa tsaye tare da barin parlourn zuciyarsa babu daɗi sam. Salman dake bakin ƙofa yana jin duk abinda ake faɗa, jikinsa na rawa ya buɗe ƙofar zai shiga Mami tayi saurin kama hannunsa tare da jansa zuwa part ɗinsa. Idanunta cikin nasa ta ce. "Da kyau, Ammin zaka je ka faɗawa kana son Abra kana son aurenta ko? To jeka ban hanaka ba, amma kasan abinda zuwan naka ke nufi" Tana faɗin hakan ta fice daga ɗakin tare da banko masa ƙofa, Salman ji yayi wani zazzaɓi na neman kama shi ga wani ciwon kai dake neman tarwatsa masa ƙwaƙwalwarsa. Sama da marwa kawai yake a cikin haɗaɗɗan bedroom ɗin nasa, tunanin mafita yake amma ya gagara samu gaba ɗaya. "What should I do? Ko na faɗawa Granny nasan she most do something" zubewa ya yi a kan gadon, ya na dafe kansa. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Hasbunallahu! Ubangiji ka kawo mafita" shiru ya yi yana tunani a fili ya sake ce wa "If na gayawa mayen na Abra gasky tare da faɗa masa ina son ta, nine kuma zan aureta fa?" Girgiza kai ya yi yana sauke numfashi ya ce. "Mami zata tsine min, she's my mother ban son hakan ya kasance"  ganin ya rasa mafita ya ɗauki wayarsa tare da ƙorawa photon Abra kallo, Murmushin da ke shimfiɗe akan fuskar ta shi kaɗai ya isa ya sanya ya samu nutsuwa. Kwanciya ya yi yana ƙanƙame wayarsa a ƙirjinsa kamar da wasa kuma zazzaɓi ya rufesa tare da ciwon kai mai zafi. Mami na fita ta kira Anty Suwaiba a waya cikin damuwa ta ce "Ni yaron nan ke son tonawa asiri Anuty Suwaiba?. Babbar matsalar da ya faɗi komai Uban sa sakina zai yi, bana son hakan ta kasance gaba ɗaya na rasa yadda, al'amarin na son fin ƙarfina" Anuty Suwaiba ta cikin wayar ta saki dariya sai da tayi mai isarta kafin ta ce "akwai shawara, ki bawa mahaifin nasa shawara a kan ya fitar da shi ƙasar waje karatu tun da Abra aure za tai, kuma kina da tabbacin ba zai mai da hankali ya yi karatun da ake buƙatar ya yi ba, idan ya so yana can sai ayi mata Auren idan ya dawo dai duk jarabarsa ta zama matar wani" Jinjina kai Mami ta yi cike da gamsuwa kafin ta ce "shawara mai kyau, ban yi tunanin hakan ba shi ya sa nake son kawo maki damuwata thank you Anty" tattaunawa suka sakeyi a kan lamarin. Washe gari da safe bayan Abbi ya yi breakfast, Hajiya Na'ima ta je masa da maganar ta inda ya shiga bata ban yake fita ba, kamar ya ari baki saboda masifa. "Ban san me kike nufi dani ba, ban san kuma abinda ya ke kan ki ba Na'ima, karatun Salman kuma yanzu ki ke son lalatawa, shirme da haukan na ki har akan ɗan da kika haifa na gaji na gaji" fuuuu! Ya yi waje rai ɓace. Cikin tashin hankali Mami ta kira Anty Suwaiba "wallahi ba zai yarda ba Anty yanzu yaya zan yi? Ya fara ɗaukar zafi, dama a ƙule yake dani na haɗa shi da mahaifiyarsa" Anty Suwaiba ta ce "kwantar da hankalin ki, ki shirya akwai mafita, gurin malami zamu kai shi, a rufe masa baki, dolensa ya amine Salman ya bar ƙasar nan" shirya komai suka yi, Na'ima ta amince akan zasu wajan wani malami, saboda samun mafita, kar ramin muguntar da take shiryawa ya rufta da ita. Kamar yadda Abbi ya yi alƙawari, haka ya cika ta hanyar yin bincike har Kaduna, akan Sp Adnan Aliyu Matawalle, ya samu good Information. Halin Adnan mai kyau ne, kuma mutum ne mai asali, mahaifinsa sanannane ne. A satin Abbi ya nemi ya zauna da Adnan, shi kansa Abbi ya yaba da hankali nutsuwa, da kuma kamala ta Adnan, dan haka ya bashi damar ya turo magabatansa, su nema masa Auren Abra. Ko da Adnan yaje da wannan batu gida, farinciki gurin iyayensa ba'a magana, mussaman Hajiya Mama, bata taɓa tunanin abubuwa za su zo da sauƙi haka ba, saboda gani take Adnan ba zai iya kwantar da kai yayi Soyayya ba, saboda tsananin zafin zuciyar sa. Sosai Mama da Abba suka yaba da Abra, da ya nuna musu hotonta, kuma suka yi duk binciken da za suyi a kanta, amma ba su samu wani mummunan abu ba akanta, mussaman da ya zamana Major Khamal Khamis, sunansa shahararre ne a ƙasa. Abban Adnan ya wakilta 'yan uwansa, zuwa nemawa Adnan ɗin Auren Abra, kuma, Abbi ya basu auren cikin aminci, farin ciki wajan Mami ba'a magana, gani take ta samu mafita da kaso mai rinjaye na matsalolinta. gefe guda a ranar Sp Adnan Aliyu Matawalle da Abra Khamal Khamis raya daren sukai da Soyayyar juna ta waya. Sp Adnan ya koyar da Abra Soyayya, ita kanta wasu lokutan har mamakin kanta take, saboda irin soyayyar da take nuna masa. Duk zafin zuciyarsa, ya ƙware a fannin iya rarrashi da tarairayar Abran, da biyewa dukkanin shagwaɓarta da shirmenta. Haka suka raba dare, Adnan yana tsara musu yadda zasu gina rayuwarsu, bayan sun yi Aure, har sai da ya kusa fara sakin layi, Abra tayi masa sallama ta kashe wayar. A hankali ta tura ƙofar ɗakin yana kwance ya juyawa ƙofar baya babu abun da yake bayyane a jikinsa sai fuskarsa, gaba ɗaya jikinsa rawar zazzaɓi yake. Da ɗan sauri Abra ta ƙaraso tare da zama a bakin gadon daidai kansa muryarta na rawa ta ce. "Subuhanallahi Faris baka da lafiya? Wayyo Allah na" gaba ɗaya idanunta ya cicciko da hawaye. Wata irin soyayya ce tsakanin Abra da Salman irin soyayyar da Ubangiji ne kawai ke haɗata, raba irin wannan soyayya kan iya jawo rasa rai ko rayuka. Juyawa ya yi tare da Kallonta da idanunsa wanda sukai jaa sosai tamkar gauta. Kallon ta ya ke kamar bai taɓa ganinta ba a hankali ya kama hannunta tare da riƙewa cikin nasa. Abra ta ƙara hawa kan gadon tare da shafa sumar kansa muryarta na rawa ta ce. "Meke damunka Faris ɗi na? bari na faɗa wa Mami, Abbi ya riga ya tafi, ya tambayi kana ina Mami ta ce ka fita" Girgiza mata kai ya yi, yana ƙara matse hannunta da ke cikin nasa. "Bari na kira Dr ya duba ka" Murmushi ya sakar mata cikin dauriya ya ce. "Mami, Abbi, Dr. Basu da maganin abin da yake damuna Angel leave them" "Jikin ka yayi zafi fa, ta yaya ka ke tunanin zan jure ganinka haka?" "Zaki jure mana Angel? tunda gashi aure zaki ki barni" yayi Maganar a raunane. Shiru tai ta kasa cewa komai domin ita ma tana hango ranar da za'a ce wai zata bar gidan kuma tabar Faris ɗinta?. "Yanzu me ka ke so?" "I  just need you by my side, stay with me Angel don Allah". Kansa ta ɗauka tare da ɗorawa akan cinyarta a hankali take shafa sumar kansa hawaye na saukar mata ta ce. "I'm here I'll Spend all my time with you Faris". Lamo ya yi akan cinyarta yana murza hannunta zuciyar sa sai bugawa take. "I love You. I love you Angel" Murmushi tayi tana jan hancinsa ta ce. "I know, and I love you too u don't have to  worry bloody..." Shiru duk sukai ga mamakin Salman, numfashin Abra yaji yana sauka a hankali, alamar bacci ya ɗauke ta, gently ya miƙe da ga kan cinyarta. "Angel ragowar yarinya, dana aureki kin daina wahala Insha Allah, da yardar Ubangiji ke matata ce mallakina ce" A hankali ya sumbaci goshinta ya ce "you're my life" Gently ya yi 6nata nose Kiss ya ce "My everything" a nuste ya yi mata cheeks kiss ya ce "rest of my life. Mother of my children" ji yake kamar ya maida ita cikinsa, kowama ya dena ganinga. Wayar Abra ce ta fara ringing kallon screen ɗin wayar ya yi yaga _Heartbeat_  kallon wayar ya yi har kiran ya katse. Sai da akai kira uku a fusace ya ɗauka. "Ruhin Sp Adnan Aliyu Matawalle. Na kusa mutuwa da rashin jin muryarki" Adnan dake tsaka da driving gefensa kuma Usman ne yana ta tsokanar sa. Jin shiru Adnan ya ce. "Hello Angel are you there?" "She's sleeping in my laps u can call later" Salman ya faɗi maganar hankali kwance. "Who are you? And  a ina take bacci?" Adnan ya furta rai ɓace. "Tana wajan wanda ya dace mana? Ka faɗi yaren da kake ji, idan baka gane wanda nayi ba, sai nayi maka bayani da shi" sai yanzu Adnan ya ɗauki murya murmushi ya yi yace "Oh! Faris ƙaninmu how are you? I'll call later bye" Yana faɗin hakan ya kashe wayar, Salman datse lip's ɗinsa ya yi yana jin duniyar na juya masa. Ranar da ya fara arba da Adnan a gidan ya zo gurin Abra, ji yayi tamkar ya haɗiyi zuciya ya mutu. Shi kansa Adnan ya lura da irin mugun kallon da yaron yake masa idan ya zo, amma bai ɗauki hakan a matsayin komai ba. Gyara mata kwanciya Salman ya yi yana zame mata rolling ɗin kanta. An saka ranar bikin Abra wata biyu kacal. A satin kuma Adnan ya sauka Kano, ko da suka haɗu da Salman kamar haɗuwar zaki da damusa haka ta kasance, saboda Salman ji ya dinga yi tamkar ya kashe Adnan ya huta. Haka ya shiga ɗakinsa, ya kulle kansa ya dinga kuka kamar ƙaramin yaro. "Abra is leaving me, why? Abbina kaima ba ka fuskanci halin da nake ciki ba? Na kamu da soyayyar yarinyar da ka tsinta ka riƙe tsawon shekaru, a matsayin yayata, Abbi I love her, meyasa zaka bawa wani?" Haka ya dinga surutai tamkar yana gaban Abbi. Salman ne zaune sanye da farar singlet ya rame sosai, abun duniya ya yi masa yawa, soyayyar Abra na addabar zuciyarsa, ga tsinewar da Mami ta ce za tai masa, ga lokacin bikin Abra na kusantowa, gaba ɗaya baya hayyacinsa, ko Makaranta ya je, baya gane komai ba ya iya cin abinci sam. Ga shi ita kanta Abra yanzu, tafi maida hankali akan wayarta, ta dena bashi attention ɗinta kamar da, kullum tana maƙale da waya tare da Adnan. Gashi Adnan ya auri hanyar Kano, kullum yana hanyar zuwa gurin ganin Abra, hakan ya sa sukayi wani irin sabo da shaƙuwa, wanda yasa Abra sakewa da Adnan Sosai. Sai dai duk da haka, tana damuwa da halin da Salman ke ciki, wanda ba ta san asalin abun da yake damunsa ba, ta barshi a alhinin rabuwa da za su yi, wanda ita kanta tana tsintar kanta a irin wannan yanayin, ba ta jin ko Abbi za tayi missing Kamar yadda za tai missing Faris. Ta kan yi kuka sosai da sosai, idan ta tuna lokaci ƙalilan ya rage, su rabu da Faris ɗinta. Salman ya lula a duniyar tunani, Kamar da ga sama yaga Abbi ya shigo bedroom ɗin nasa, hannunsa riƙe da tarin takardu. Miƙewa tsaye Salman ya yi yana faɗin "Wlcm back Abbi ya hanya? Ashe ka dawo?" ba yabo ba fallasa ya ce "Yawwa, tun ɗazu nake cigiyarka ai, naga ba ka da niyyar fitowa, ko ba ka ji dawowata ba ne oho" Salman ya ce "Abbi na ɗan yi bacci ne, shiyasa". miƙawa Salman takardun ya yi Salman ya bisu da idanu kafin ya ce "Na mene wannan Abbi?" Abbi ya kalli Salman sosai ya ce "Na gama dukkanin shirye shiryen da ya dace, na biya maka Makaranta a China, a can zaka cigaba da karatunka, saboda karatu a wannan ƙasar sai a hankali, babu wani inganci, dan haka next week zaku fara lectures, jibi in Allah ya kaimu zaka tafi, dan haka ka shirya!!! LITTAFIN RUƊI NE ₦300 NE Via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750 [10/5, 5:43 PM] Abk: Saroro Salman ya bi Abbi da kallo, kamar bai gane da yaren da Abbi yai Maganar ba. Abba yace "Look Salman, mahaifiyarka ce ta zo mini da batun gara a kaika karatu China, kuma ba mun yanke wannan hukuncin ne dan ɓata maka bane, ka san karatun Nigeria sai a hankali". Cikin rauni Salman ya ce "Abbi, exams ɗin first semester fa zamu fara, you are planing to make me far away from my sister, ko Auren na ta ba zaku bari in gani ba Abbi?" "My Son, ban amince da hakan dan nesan ta ka da Abra ba, ko ba daɗe ko a jima dole wataran zaku rabu, tafiyar ce ta zo daidai yanzu kayi haƙuri ka ji Salman, idan ka zo hutu sai kaje har gidanta, ai ba wanda ya isa ya raba hanta da jini" Salman ya jinjina kai, Abbi kuma ya juya bar ɗakin. Abbi na fita Salman ya saki takardun a ƙasa, ya faɗa kan gadonsa ya lumshe idanunsa, hawaye na zuba daga idonsa a hankali ya ke furta 'Mami why? Har abun ya kai kisa a rabani da ƙasar, Mami why" haka ya dinga maimaitawa a hankali. Na'ima kuwa ba ƙaramin farinciki ta yi ba, dan tun bayan da Anty Suwaiba ta rakata gurin malami, ta biya kuɗi dan a rufe bakin Abbi a kan tafiyar Salman ƙasar waje, kuma a cire Abra daga zuriyar Salman. Bayaj sun dawo gida ne, ta kuma samun Abbi a kan tafiyar Salman, da fari yayi mata buyagin na sa, amma ta kwantar da kai, tare da nuna masa illar barin Salman a ƙasar nan yaga bikin Abra, Abra za ta iya tuburewa ta ce ta fasa Auren, ko kuma ya ce zai dinga zarya a gidan Abra, wanda ba kowane miji ne zai yadda ba, da haka ta lallaɓa Abbi ya amince, ya nemawa Salman Makaranta a China. Sallama ya ke ta kwaɗawa a falon, kamar baza'a amsa ba, sai kuma can a kasa amsa cikin siririyar muryarta mai cike da iyayi. Cikin Palourn ya shiga, Meenal ta kalli mutumin ta ce "ya dai?" "Dama saƙo ne wani mutum ya kawo, ya ce a bawa doctor idan ya dawo". Maman Meenal da ke zaune ba tace uffan ba, sai yanzu da ta ji ance saƙo za'a bawa Doctor sannan ta kalli mai gadin ta ce "Bani nan" ya ƙarasa ya miƙa mata envelope ɗin ya fice. Meenal ta kalli Mummynta ta ce "Mummy, sai na dawo" "Shikenan, ki kula da hanya, ayi tuƙi a hankali". "Ok Mum" Meenal ta amsa tana ficewa daga falon. Mummy ta fara buɗe envelope, dan ganin mai aka kawo a ajiyewa doctor. A razane ta miƙe tsaye, a lokacin da ta yi tozali da abun da yake cikin envelope ɗin. Jikinta ne ya hau rawa, ta fara waige-waige don tabattar da babu wanda ya ganta. Da hanzari ta nufi ƙofar falon, ta fito harabar gidan tana ƙwalawa maigadi kira. Ya ƙaraso cikin rawar jiki yana faɗin gani Hajiya. "Waye ya baka wannan saƙon?". "Wasu ne Hajiya" "Ba ka san su ba?" "Eh gaskiya ban san su ba, dan ban taɓa ganinsu ba" Ta yi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan koma bakin aikinka". Cikin gida ta koma, kai tsaye ta wuce kitchen, ta rufe ƙofar kitchen ɗin da key, ta yayyaga saƙon nan, ta kunna masa ashana ta ƙone tsaf, ta tattare tokar ta bar kitchen ɗin. Salman kam nan da nan yayi wata uwar rama, ko falo ba ya fitowa kullum yana ɗaki, yana tunani tare da zullumin yadda zai tafi ya bar Abra ta auri wani. Yana kwance a kan gadonsa, Mami tayi sallama ta shigo ɗakin. "Kai Salman" a hankali ya buɗe jajayen idanunsa yana kallon Mami. "Babanka bai zo ya gaya maka cewar ya biya maka kuɗin Makaranta, zaka tafi China ba? Na zubamaka ido inga iya gudu ruwanka, ko zaka zo ka sameni da batun, a fara ƙoƙarin fara shirin tafiyarka, amma kullum kana ɗaki ka ƙi zancen ma gaba ɗaya" Lumshe idanunsa ya kuma yi, saiga hawaye na zubowa ta gefen idonsa. "Sakarcin meye haka kuma Salman, kuka kamar wani yaro ƙarami". Salman ya tashi zaune ya kalli Mamai ya ce "Mami, bayan kandagarkin da kika mini akan soyayyar Abra, shine kuma kika sa a rabani da ƙasar ma? Mami kin san wannan abubuwan zasu biyo baya, mai yasa kika bari na san Abra ba 'yar uwata ba ce, Mami ko kin rabani da ƙasar nan zuciyata na Nigeria tare da Abra, ina sonta Mami, amma ai ko Auren na ta kya bari in gani". Ajiyar zuciya Mami ta yi, ta zauna kusa da Salman ta ce "Salman, kai baka tunanin halin da zata shiga idan har ta san cewa bamu muka haifeta ba, kai kanka kawai ka sani, baka tunanin abunda kake shirin yi mai zai haifar, barinka ƙasar nan shine samun nutsuwarka kuma ka manta da ita, haba Faris ɗina da kaina zan samo maka tsaleliyar yarinha da ta fita komai in aura maka, ka fara shirin tafiyarka ka ji Salman" tayi maganar tana share masa hawaye, daga haka kuma ta fice daga ɗakin. Bin ta yayi da kallo, Maminsu a komai son kanta kawai take dubawa. Abra kuwa yanzu kusan kullum tana kan wayarta, tare da Adnan hakan yasa ba ta iya maida hankali akan komai, sai dai ta lura tunda aka kawo kuɗin Auren nan, Salman ba shi da walwala, kuma a 'yan kwanakin nan kamar wani abu yana faruwa a gidan, wanda ba ta gane ko menene ba. Lokaci lokaci, ta kan shiga cikin matsananciyar damuwa, idan ta tuna idan tayi Aure, zata rabu da Faris ɗinta, ba ta jin za tayi Missing ɗin wani kamar Salman ɗin ta. Yanzu ma ɗakinsa ta nufa, tana shiga ta tarar yayi rigingine ya ƙurawa roofing ɗin ɗakin ido. Sai dai yayi rama matuƙa, ga ɗan siririn saje da ya fara fito masa da gashin baki na girma. "Bloody what's wrong with you ne? Gaba ɗaya gidan nan yayi duhu saboda baka walwala, meyafaru da ne?" Tayi maganar tana ƙarasawa kan gadon. Juya mata baya yayi, yaƙi ko kallon in da take. Zagayawa tayi ta hau gadon tana kuma cewa "Faris wai menene?" Miƙewa yayi, ya sauka daga kan gadon, ya janyo Akwati ya fara ƙoƙarin zuba kayansa. Cikin fushi ta ce "Faris wai meye haka ne? Wannan kayan na menene ina maka Magana ka mini shiru". "Leave me alone Abra!" Ya faɗa cikin tsawa, wanda saida ta firgita. "Abra dama Akwai lokacin da zai zo ki manta dani? Kwana biyu ina cikin yanayi na damuwa, amma wands zai aureki ya ɗauke miki hankali ko nemana ba kya yi, ba ki san halin da nake ciki ba? Abra China zan tafi ina fatan Allah ya sa haka shine mafi Alkhairi". "Faris, ka yi mini uzuri mana, muna cikin weekends ne, kuma ga shirin exams muna yi, don't judge me wrongly please, but ban gane China ba ina ne China?". "Ohh baki ma san meke faruwa ba, Abbi ya biya mini Makaranta a China, jibi in Allah ya kaimu zan tafi, bana nan za'ayi Aurenki, ina fatan Allah ya baku zaman lafiya, ya dawwamar da farinciki a rayuwar Aurenki da wanda kike so". "Impossible" Abra ta faɗa tana wani haɗe rai. "Meye ma'anar tafiyarka China? Saboda me?" "Bani zaki yiwa wannan tambayar ba, kamar yadda kika ji maganar sama ta ka, nima haka na ji ta". Da gudu Abra ta juya, ba ta tsaya ko ina ba sai sashen Abbi. "Abbi, Abbi!  Abbi". Abbi ya ce "Na'am Sweetheart ya akayi?". Na'ima ta ce 'Wannan wane irin rashin hankali ne?" Abra ba ta kula Na'ima ba ta ce "Abbi, mai yasa za'a kai Faris China? Laifin me yayi? Mai yasa za'a rabani da shi tun Yanzu, har ace zai tafi jibi ban sani ba, amma dai Abbi Faris da wasa yake mini ko?" Abbi ya ce "To Abra ya zanyi muku? Nace a bari ki kammala karatu, kince ke A'a, Aure zakiyi, kuma kinga tafiyarsa shine Mafi Alkhairi, idan ki kayi Aure zai shiga damuwa sosai". "Abbi shine kuma za'a rabani da shi tun yanzu, duk duniya kun san bani da wani ɗan uwa bayan shi, ni na fasa Auren nan, dan Allah ku ƙyale mini Faris ɗina, na fasa Auren Abbi". Gaba ɗaya Abra ta birkice, Abbi ya tashi ya riƙota yana faɗin "Calm down Abra, ai zai dinga zuwa har gidanki, kuma...... "A'a Abbi, ni rayuwar ɗan uwana ta fiye mini dukkan wani farinciki, Abbi na fasa Auren, dan Allah kar Faris ya tafi China". Na'ima ta hayayyaƙo zata fara masifa, amma sai taga idanun Abra sun lumshe, jikinta ya saki ta tafi zata faɗi Abbi ya tare ta. Abbi ya ce "Subhanallah". Na'ima ta ce "wai ni wannan wace irin Yarinya ce? Ba damar ta shiga damuwa sai ta hau suma, yanzu da za tayi Aure, namijin ƙanin uwatta ne da ba zai ɓata mata rai ba?". "Na'ima, this is not time for discussing this issue, kira mini Salman ya ɗakko mota mu tafi Asibiti. Mami ta kira Salman a waya, nan da nan sai gashi ya zo. Yana ganin Abra a kwance a jikin Abbi, ya rikice, da sauri yayi waje ya ɗauko Mota, suka tafi Asibiti. Abbi yana mamakin irin wannan yanayi da Abra kan shiga, idan ta shiga firgici ko fushi, amma duk wani bincike da za ayi anyi, amma ba'a gano dalilin da yake sanyata haka ba. Abbi ya ga dacewar idan Adnan ya kuma zuwa ya zauna da shi, ya sanar masa da wannan rashin lafiyar ta ta. A hankali Abra ta motsa, tare da buɗe idanunta, da idanun Salman ta fara tozali, a hankali ta ce "Faris". Salman yayi ajiyar zuciya sannan ya ce "Na'am Angel". "Dan Allah kar ka tafi ka bar ni". "Angel dole in tafi in barki, kin zaɓi wani a kaina". "Faris, ina son Adnan, amma ba zan iya jure ganin ka nesanta da ni ba, dan Allah kar ka tafi ka ka barni". Shiru Salman yayi bai ce komai ba. Abra ta yunƙura ta tashi zaune, ta riƙo hannayensa a cikin nata, muryarta na rawa ta ce "Please Faris, dan Allah kar ka tafi ka barni, I can't survive without you, Faris kai kaɗai ne nake da shi a matsayin ɗan uwa, bana son kayi nisa da ni Please Faris". Shiru Salman yayi, ya ƙi Magana. Hannunta ta saƙalo a wuyansa tana kuka, "Talk mana Faris, please talk Brother" Kasa magana yayi, sai ɗora fuskarsa akan tata, suna iya jin numfashin juna, a hankali hawaye ya fara zuba daga idanunsa, Abra tana masa so na 'yan uwanta ka, shi kuma yana mata so irin na Aure". "Faris talk" ta kuma Maganar tana sake maƙalƙalo shi, wanda hakan ya jefa Faris ɗin cikin wani mawuyacin hali. Ba zato ba tsammani Farisa ya shammaceta, ya haɗe bakinsa da nata, jikin Abra ya hau rawa, saboda yadda taji abun ba tsammani, ga rashin sabo, sai dai tana jin yadda jikinta ke karɓar saƙonsa. Sosai idonsa ya rufe, yana shafa gashin kanta. Da sauri Abra ta farga, tare da tuna Faris ne fa ƙaninta, ture shi tayi da sauri tana mai da numfashi. A hankali Salman ya ce "Am sorry Please, zanje reception, kan Mami ta dawo". "In ka je gida, ka taho mini da wayata Please". "Ok" shine abun da ya faɗa ya bar ɗakin. Meenal ce zaune a wani katafaren Joint, ta kammala cin abinci, ta tashi tana niyyar tafiya. "Hi beauty" ba tare da sanin da wa ake ba, ta waigo domin taga waye. Wani kyakykyawan matashi ne a tsaye a bayanta, yana murmushi. Ya kuma cewa "Tun da kika shigo gurin nan, nake jiranki ki kammala kar in takura miki". "Ok what happens?" Ta tambayeshi cikin iyayi. "Wow, beb you are so beautiful fa" yayi Maganar yana ƙare mata kallo daga sama har ƙasa. Yadda duk wata surar jikinta a bayyane take, cikin doguwar rigar jikinta. "Anyway, if you have nothing to say, i have something to do". Ya ce "Well, ko zanyi dropping ɗinki, a in da zaki?". Car key ɗin hannunta ta ɗaga masa, alamar da motar ta tazo. Yayi murmushi tare da gyara tsayuwarsa ya ce "Can i have your number please?". Ba musu Meenal ta bashi lambar wayarta, saboda ita kanta ya burgeta, ya haɗu gayen. Suka yi musayar lambar waya, sannan ta wuce ta tafi. A yau ne aka fara sauraran ƙarar da gwamnatin tarayya ta shigar a kan General Ibrahim mai retire, tare da wasu tsofaffin manyan mutane da suka riƙe maƙamai a ƙasa, da wasu daga cikin jami'an tsaro, da manyan 'yan ta'adda a gaban kotu, da tuhume-tuhume daban-daban, akan haɗin baki, tare da yiwa ƙasa zagon ƙasa akan harkar tsaro, ga cin hanci da kisan kai da ake zargin General Ibrahim mai retire. An gabatar da shedu da hujjoji, da aka fara gudanar da shari'a. Ba yadda Manyan lawyoyi ba suyi ba masu kare su General Ibrahim, akan a bada belin su, amma lawyoyin gwamnati suka yi suka, Alƙali ya hana ba da su beli. Salman yana tafe a hanya wayar Abra sai vibrating take, saƙonni suna shigowa. 'Unknown' ya maimaita ko waye kuma unkown oho mata, sai kuma Adnan da ke ta kiran wayarta ba ƙaƙƙautawa. A fusace Salman ya ɗaga wayar ya ce "Dan Allah malam ka tsahirta haka da kiran wayar nan, tana Asibiti ba lafiya Malam". Adnan yayi murmushi ya ce "Matata babu Lafiya amma a kasa gaya mini Faris" "Ai ka bari a ɗaura Auren, kafin ka kirata matarka, kuma kar ka sake kiran wayar nan yanzu". Adnan yayi murmushi yana jujjuya maganar Salman, ya kasa gane meyasa yaron nan baya ƙaunarsa. Likita ya ce ba zai sallami Abra ba, saboda jininta yana hawa yana sauka. Salman ya je Asibiti ya tarar da Abra tana bacci, ya ƙura mata ido, hawayensa na ɗiga a kan fuskar Abra, ya durƙusa ya sumbaci goshinta, ya ajiye mata wayarta a gefen pillown ta, har ya kai ƙofa ya tsaya ya waiwayo ya kalli yadda take baccinta Hankali kwance. Ya juya ya fice. Abbi ya biya duk bills ɗin da Abar taci, Ba yadda Mami ba tayi ba, a kan a sallami Abra a daren amma abu ya gagara, kuma ga Abbi na nan ba damar tace ba zata kwana a gurin Abra ba. Sai cikin dare Abra ta sake farkawa daga baccin da takeyi, tayi alwala tayi sallar da ke kanta. Mami nata baccinta, Abra ta ɗau wayarta, ta shiga duba saƙonnin da ke wayar tata. Saƙonnin unknown ba adadi a wayar nan, yana bata tabbacin kowane lokaci zai iya bayyana mata kansa. Ajiyar zuciya tayi tai masa reply da "Is too late!!!". Ta buɗe what's app ɗin ta, Adnan yayi mata messages kala-kala na soyayya da sannu. Murmushi tayi ba tare da tayi masa reply ba. Lambar Salman ta nemo, ta kirashi ƙarfe biyu da rabi na dare. Ba tsammani ta ji ya ɗaga wayar "Hello Angel" "Na'am Bloody na, ba kayi bacci ba?" "Na kasa bacci Angel". "Faris why?" "Nothing, ya jikin naki?" "Naji sauƙi Alhamdilillah, ina ga da safe in Allah ya kaimu za'a sallameni, kaina ne kawai yake ta ciwo, kamar zai fashe". "Sorry, ki kwanta kiyi bacci kar kan ya cigaba da ciwo" "Faris, ya batun tafiyar nan, ai ka fasa ko? Abbi ya janye tafiyar ta ka ko?" Ajiyar zuciya yayi ya ce "Kiyi bacci Angel". "Faris ka gaya mini mana, hankalina ya kasa kwanciya, kuma ban sake ganin Abbin ba". "Zamuyi magana da safe insha Allah, sleep well Dear" ya katse wayar. Abra tayi shiru tana tunani kala-kala a zuciyarta. Wayewar gari ma Abra da matsanancin ciwon kai ta tashi, sai kuka take yi, hakan ya sake tilasta wa likitoci yi mata allurar bacci, saboda daren sam ba tayi bacci ba, ta kwana kukan ciwon kai. Da safe da Salman ya dawo duba Abra, bacci take yi, dan haka ya juya ya koma gida. A harabar Asibitin ya ci karo da Adnan, ƙarfe tara da rabi na safe, har Adnan ya dira a garin Kano. Wani irin mugun kallo Salman ya yiwa Adnan, ji yake tamkar ya shaƙe Adnan ya huta. Adnan kuwa murmushi yayi ya ce "Faris our lil Brother, ya Jikin matar tawa? Ina fatan tana samun sauƙi, na kasa samun nutsuwa gaba ɗaya, a wani ɗakin take ne? Naje can gida aka ce mini kuna nan Asibitin". "Idan ka shiga idanunka sa gane maka" Amsar da Faris ya iya bashi kenan ya nufi mota, Adnan bin Faris yayi da kallo yana murmushi. Adnan Ya shiga ya tambaya a reception, aka gaya masa lambar ɗakin da Abra take, yana zuwa ya tarar da Mami a zaune tana waya. Cikin girmamawa suka gaisa da Mami, yayi mata ya mai jiki, ta amsa masa da sauƙi, daga nan ta tashi ta basu guri. Gaban gadon Abra yaje ya tsaya, ya zubawa kyakywar fuskarta ido, da uban gashinta da yake baje a kan pillown da take kai. A hankali ya kai hannu ya shafa gashin na ta, dan tabattar da ko nata ne, ba ƙari bane gashin Abra ne, fal da shi akan pillow. A hankali ya kai hannunsa inda hearing aid ɗin ta yake a kunnenta. A hankali yake taɓa aid ɗin yana tunanin, wannan meye amfaninsa a kunnenta?. Ya koma ya kulle ƙofar ɗakin, ya dawo ya zauna a gefen gadon, ya ɗago Abra daga kwanciyar da take. "Mhmm Faris" ta faɗa cikin shagwaɓa. "Ba Faris bane Baby, Adnan ne" A hankali ta buɗe idonta akan Adnan. Zaro ido tayi, ta tashi daga jikinsa tana faɗin "Yaushe ka zo?". "Yanzun nan, na kasa samun nutsuwa jiya na kira wayarki, Faris ya ɗaga yace mink baki da lafiya, meyake damunki ne?" Kawai Abra ta fashe da kuka. "Angel menene kuma?". "Wai Abbi ne ya ce sai Faris ya tafi China karatu". "To shine me?". "Dan me za'a ɗauke mini shi? Wa zan dinga gani, na saba da Faris". "Ni ɗin kuma fa?" Adnan yayi Maganar in a serious tone. "Kai mijina ne, Faris kuma jinina ne, the only Brother i have, ni ji nake Kamar in fasa Auren nan". Ɗan shiru Adnan yayi ya ce "Baby kin dena sona kenan?". "A'a ina sonka, amma bana son in rasa Faris ɗina". "To shikenan, ki kwantar da hankalinki, kin ji Babyna ba in da Faris za shi ya barki, ai ni in cewa ki kai a gidana a ginawa Faris ɗaki, ku tare a tare ba matsala" yayi Maganar cikin sigar rarrashi. Adnan da shi aka wuni a Asibiti, Ana jinya, Su Ammi na ta yabawa kyawu da nutsuwar Adnan, a matsayin siriki. Abra sai tambaya take ina Faris, amma ba wanda ya bata wata gamshashiyar amsa, ta kira wayarsa amma shiru ba ta shiga. Bayan la'asar aka sallami Abra, Sai da Adnan ya rakasu har gida, wanda a nan ne Abbi ya sanar masa da larurar Abra, na rashin ji sosai sai da hearin aid, da kuma halin da take shiga idan ta shiga firgici da damuwa. Adnan ya nunawa Abbi babu matsala, A nan Adnan ya sanarwa da Abbi Kaduna zai kai Abra, a nan Abbi ya ce bai amince ba, ba ta da kowa a Kaduna, kuma ga batun karatunta, kasancewar su Shureim ma suna gidan, su suka yi tausar Abbi, sun nuna masa aure ba in da baya kai mace, kuma sai a mata transfer, ko ta sake fresh tun da karatun ba nisa tayi ba. Ƙarfe takwas na dare, Abra ta ɗaga hankalin kowa a gidan, a kan ina Faris ɗinta, ta je ɗakinsa baya nan. Abba ya zaunar da Abra ya ce "Abra, ni mahaifinku ne, ba zamu taɓa zaɓa muku abunda zai cutar da ku ba, Faris jirginsa ya tashi ƙarfe sha biyu na rana, yanzu haka ya kusa China!!! LITTAFIN RUƊI NE ₦300 NE Via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750 [10/6, 5:01 PM] Abk: Kallon Abbi kawai Abra take yi kamar ba ta fahimci me ya ce ba, idanunta duka a waje cikin kuka ta ce. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, why Abbi, me ya sa za ku nesanta ni da jinin jikina, Abbi dan Allah ka dawo da shi, ba zan iya rayuwa babu Salman a kusa da ni ba." Cikin rarrashi Abbi ya ce. "I'm sorry Daughter, na san dole ki ji babu daɗi, amma haƙuri zaki yi, ni ma ba son raina ba ne hakan." Kuka ta fashe da shi tare da faɗin. "Amma Abbi me ya sa ya tafi ba mu yi sallama ba? Me ya sa bai zo na gan shi ba?" "Ya zo da safe kina bacci." Abbi ya yi maganar tare da kamo hannunta, za ta kuma magana ya hana ta da faɗin. "Just pray for him Daughter, shi ne kawai soyayyar da zaki nuna masa, ki bar wannan koke-koken kin ga baki da lafiya, kar ki ƙarawa kanki wani ciwon." Numfashi ta sauke mai zafi tare da miƙewa ba tare da ta ce komai ba, ɗakinta ta shiga ta faɗa kan gado ta shiga raira kuka mai tsuma zuciya. 'Shikenan Salman ya tafi? Ya yi nesa da ganin ta? Anya za ta iya rayuwa mai tsayi ba tare da Salman ba? Faris ɗinta mai share mata hawaye akodayaushe, mai fifita farincikinta akan nasa. Wata irin kewar shi ta ji tana nuƙurƙusar zuciyarta. Kuka sosai Abra ta yi akan tafiyar Salman, tunda ta shiga ɗaki ba ta fito ba har bayan isha'i, Sallah ce kawai take ɗaga ta, ita ma da ƙyar take iya tashi ta yi saboda wani azababben ciwon kai da yake damun ta, ji take kamar kan nata zai tsage gida biyu. Tana jin wayarta na ta vibrate amma ba ta kula ba, duk da ta san Adnan ne yake kiran ta. Hajiya Na'ima ce zaune a gefen Khamal cikin farinciki, zuciyarta fess take jin ta yau, tamkar wadda aka yiwa bushara da wani babban albishir. Kallon ta Khamal ya yi na wasu sakanni cikin murmurshi ya ce. "Wai yau nishaɗin me kike yi ne Wifey? Na ga kamar ma ko kewar ɗan gaban goshin naki ba kya yi?" Yalwataccen murmushi ta saki ta ce. "Ai ko da bakina na faɗa maka ban yi kewar Salman ba na san ba za ka yarda ba My Man, kawai ina ɓoyewa ne saboda ban san na damu kaina akan abin da ya zama dole, nishaɗin da nake yi kuma na kasancewa tare da kai ne Mijina." Ta ƙarashe maganar tare da kashe masa ido. Murmushi Khamal ya yi ya ce. "Bayan wannan kamar akwai wani abun a ranki, ki faɗa mini mana sai na taya ki farincikin." "Babu komai, idan ma da akwai bai wuce na zumuɗin ganin ranar Auren Daughter ba." "Uhm, saboda kin kusa zama surika ko?" "Suruka kuma ta nawa? sai dai ka ce saboda na kusa zama granny." Murmurshi suka yi a tare, duban time Abbi ya yi ya ce. "Har 9 ta kusa amma Daughter ba ta fito ba? Allah ya sa ba jikin nata ba ne?" Taɓe baki Na'ima ta yi ta ce. "Ko dai sakarcin nata ne ya motsa ba, na san yanzu tana can tana ta aikin kuka saboda tafiyar Salman." "Kin ga lefinta dan ta damu? Ni kaina sai bayan ya tafin kuma jikina ya yi sanyi, na san tsananin shaƙuwar yaran nan, ba ƙaramar damuwa za su shiga da rashin juna ba." "Ai gara su saba, tunda ko ba su rabu ba yanzu za su rabu lokacin da za ta yi aure, bari na je na dubo ta." Na'ima ta faɗi haka tare da miƙewa. "Abra! Abra." A hankali ta buɗe idanunta da suka gaji da tsiyayar da hawaye tare da juya kanta da ƙyar ta dubi Nai'ma. Cikin raunin murya ta ce. "Mami Faris...." "Shiiiii! kar ki ishe ni da wani zancen Faris, ki tashi ki ci abinci ki sha magungunanki." "Bakina ɗaci Mami, ba zan iya cin komai ba, Faris kawai nake son gani, dan Allah Mami ki lallaɓa Abbi ya dawo mini da ɗan'uwana kusa da ni." Ta yi maganar wasu hawaye masu ɗumi na kwaranyo daga cikin idonta. Cikin takaici Mami ta ce. "Sai dai nai uban lallaɓa Abbi, yarinya sai masifar tsiya, ina murna hankalina ya fara kwanciya kina ƙoƙarin tayar mini da shi, saboda wannan damuwar da kika yi har ya fara cewa jikinsa ya yi sanyi da ma bai tura shi karatun ba, nan gaba kuma na san zai iya cewa zai dawo da shi, tunda ba ya son ganin ki cikin damuwa. Wallahi idan baki bar koke-koken banzan nan ba sai na saɓar miki, ki tashi ki je ki wanke fuskarki mu tafi parlour ki ci abinci, saura kuma idan kin je ki cigaba da nuna wannan damuwar, ni da ke ne." Cikin dauriya Abra ta tashi ta shiga toilet, Na'ima ta bi ta da harara. Sai da ta sake yin wani kukan sannan wanke fuskarta ta fito. Sosai Abbi ya dinga lallaɓa Abra tare da ba ta baki, dan duk da ta ɓoye damurta amma kallo ɗaya ya yi mata ya san tana cikin damuwa. Ya sanar mata Salman ya kira ya ce ya sauka lafiya, lokacin tana ɗaki. Da sauri ta ce. "Abbi ba ni numbern da ya kira in kira shi." "Ba numbernsa ba ce ara ya yi, sai gobe idan Allah ya kai mu zai siya nasa sim ɗin, na san kuma ke zai fara kira da shi." Abbi ya ba ta amsa cikin murmurshi. Murmushin yaƙe ta yi ba ta ce komai ba ta cigaba da cin abincin dake gabanta, wanda take jin shi tamkar maɗaciya a bakinta, da ƙyar take iya taunawa ta haɗiye. Kallon seat ɗin da Salman yake yawan zama ta yi idan za su ci abinci, ƙwalla ce ta tarar mata a ido, ƙoƙarin mayar da ita ta yi tare da lumshe idanunta, can ƙasan mak'oshi ta ce. "I'm missing you Bloody, yaushe zaka dawo gare ni?" Adnan ne zaune akan two seater a guest parlour'n gidan Fayyad, hankalinsa gabaɗaya yana kan wayarsa yana tura wa Abra text, na k'auna da irin missing ɗinta da ya yi daga yamma zuwa dare da bai ji muryarta ba, sai tarin addu'oi da fatan samun lafiya. Fayyad dake kallon shi ya yi murmurshi ya ce. "Thank God, yau Allah ya nuna mini wannan ranar, kamar a mafarki sai ga Adnan a cikin soyayya dumu-dumu." Murmurshi Adnan ya yi bai ce komai ba. Gyara zama Fayyad ya yi ya ce. "Ya kamata zuwa yanzu a ce mun fara shirye-shiryen abubuwan da za a yi a bikin nan fa, na ga kai ta soyayyar ka kawai kake, kuma ga lokaci yana ta motsowa." "Shirye-shirye like how?" "Su dinner da sauransu." "No need, ɗaurin Aure kawai za a yi a kawo mini matata." Hararar shi Fayyad ya yi ya ce. "Wallahi ba ka isa ba, dole mu warwasa." With serious Adnan ya ce. "Sai dai ku warwasa ku kaɗai, amma babu wani abu da zan yi, kawai matata ta yi kwalliya a gama kalle mini ita, a yi ta mata pictures ana ɗorawa a media kowane kare da biri ya gani, ba zai yiyu ba gaskiya." Murmurshi Fayyad ya yi ya ce. "Mayar da wuƙar Baban kishi, mu duk da aka kalle namu matan ai ba ma son su." Ɗage kafaɗa Adnan ya yi bai kuma magana ba. Sai after 10 na dare sannan Abra ta kira Adnan, time ɗin ya koma masaukinsa fitowar shi kenan daga wanka ya ji wayarsa na ƙara, with special sound ɗin da ya saka wa Numbern Abra. Cike da zaƙuwa da son jin muryarta ya ɗaga kiran. "Matata!" Ya faɗa cikin tsantsar k'auna. A hankali ta ce. "Na'am." Ajiyar zuciya ya sauke ya ce. "I missed you Baby, ya jikin naki?" "Alhamdulillah, na ji sauƙi." "Are You sure?" Gyaɗa masa kai kawai ta yi, saboda da ƙyar take iya magana. "Ya na ji muryarki haka kuma? Ko dai jikin ne Sweetheart?" Ya yi maganar cikin kulawa. Ya sosa mata inda yake mata ƙaiƙayi, hakan ya sa ta fashe masa da kuka. A rud'e ya ce. "Subhanallahi, Angel what happened? Are you okay?" Cikin kuka ta ce. "Faris ya tafi China." "Oh My God, sorry Angel, yaushe ya tafi?" "Ɗazu, kuma ko sallama ba mu yi ba." Cikin rarrashi ya ce. "Stop crying please My love, ai dan ya yafi China ba yana nufin kun rabu ba ne har abada, tunda ga waya duk time ɗin da kike so zaki yi magana da shi. Please ki bar damun kanki, ko so kike in kasa bacci?" "A'a." "To ki yi shiru, na yi miki alƙawari bayan mun yi aure da kaina zan kai ki ki ga Salman ɗinki." Cikin farinciki ta ce. "Dagaske?" "Eh mana, mene a ciki, duk abun da zai saka ki farinciki kome ne zan yi miki, kin wuce haka a gurina." Ajiyar zuciya ta sauke cikin jin daɗi, cikin murna ta ce. "Thank you." "Don't mind Dear, bari na saka kaya, fitowata kenan daga wanka kika kira ni, i will call you later." "Okay sai ka gama." Cikin shagwaɓa ya ce. "Ki zo ki shirya ni my love, I'm tried." Murmurshi ta yi mai sauti cikin kunya ba ta ce komai ba, shi ma murmushin ya yi ya ce. "Bye, Sarkin kunya, soon zan cire miki duk wannan kunyar taki, wuyarta a kawo ki gidana mu kwana tar...." Bai ƙarasa ba ta kashe wayar still tana murmurshi, wani irin son Adnan na ƙara mamaye zuciyarta, wayar da suka yi yanzu ta sa ta fara jin sauƙin damuwar tafiyar Faris da kewar shi. Cikin takunta na ɗaukar hankali mai cike da izza ta shiga parlour'n part ɗin Momy. A shagwab'e take kiran sunan, "Mommy, Mommy." "Na'am Daughter har kin dawo?" "Na dawo Mommy." "Welcome" Hajiya Saudat ta faɗa tare da rungume Meenal." "Thank you Mom, I want to take Bath, ki saka wata a cikin baƙaƙen yaran nan ta haɗa mini ruwa a toilet yanzu." Shafa kanta Mommy ta yi ta ce. "Yanzu kuwa." Around 11pm Meenal tana online tana chat mutumin da suka haɗu ɗazu ya yi mata magana, babu bata lokaci ta yi masa reply. Introducing kansa ya yi mata ya sanar mata sunansa Abdul. Daga nan suka fara hira, Abdul ya iya tsara mace, hakan ya sa a cikin daren ya sace zuciyar Meenal. Dama 2 days ta rasa gane kan Usman, ya canza mata gaba-d'aya. Har 2 na dare suka kai suna chat ɗin, wanda rabi duk stickers ne da emoji na love da hug da kisses Abdul ya cika ta da shi. Cikin lokacin ƙanƙani Meenal suka saba da Abdul sosai, kodayaushe cikin chat da waya suke, video call kam kusan raba dare suke suna yi. 1 week da haɗuwarsu ya zo gidansu, aka sauke shi a parlour'n saukar baƙin Bulama. Abdul Saɓanin Usman yake, sun banbanta a halayya, dan shi Meenal tana zuwa ya rungume ta tare da kissing ɗinta. Hakan ko a jikin Meenal, ta biye masa sukai ta shashanci. Shirye-shiryen biki ya kankama ta kowanne ɓangare, su Hajiya Na'ima ba zama, ana ta shirye-shiryen yanda abubuwa za su kasance. Yanda Na'ima take murna da rawar ƙafa akan bakin ba ƙaramin mamaki ya ba wa su Aunty Iman ba, sanadiyyar ƙin Abra da suka san Na'ima tana yi. A ɓangaren Amarya kuwa tana cikin tashin hankali da damuwa, sakamakon kewar Salman dake addabar ta. Kullum sai ta ɓuya a ɗaki ta ci kuka ta ƙoshi. Ko kuma ta zauna ta saka hoton shi a gaba tay ta kallo tana hawaye, ko ta faki ikon Mami ta shiga ɗakinsa ta kwanta tana shaƙar ƙamshinsa da har lokacin bai bar ɗakin ba. Babbar damuwarta rashin ji daga Salman tun da ya tafi, komai take yi wayarta na hannunta cikin tsammanin kiran shi ko ganin text ɗinsa amma shiru. Ta karɓi sabuwar Numbernsa ta ƙasar Chinan a gurin Abbi, amma idan ta kira ba ta shiga, ta duba kuma numbern ba a WhatsApp da ita. Abun da yake rage mata damuwa Adnan, saboda wata irin kulawa da ƙauna gami da tattali na musamman yake nuna mata. Damuwar rashin Salman a kusa da ita ya sa duk ta rame. Meenal ce tsaye a gaban mudubi tana shiryawa, sanye take cikin wasu matsatstsun kaya riga da wando, wanda suka bayyana surar jikinta. Wani yalolon mayafi net ɗan ƙarami ta saka akanta, rabin gashinta daga gaba duk a waje, mayafin kuma iya ƙasan wuyanta ya tsaya. Cikin takunta na ƙasaita da ji da kai ta fice ta sauka ƙasa. Hajiya Saudat na zaune ita da wata k'anwar BULAMA da ta kawo mata ziyara suna hira, takun saukowar Meenal daga kan step ya sa su ɗaga ido suna kallon ta. Tun kafin ta ƙaraso ƙamshinta ya gama cika parlour'n. Baki buɗe Aunty Murja take kallon ta cikin ɗaurewar kai. Hajiya Saudat kuwa murmurshi ta saki ta ce. "Wow, Daughter irin wannan kyau haka? You look so beautiful!" Murmurshi Meenal ta yi cikin jin daɗi tare da juya ido ta ce. "Thank you Mom." Sannan ta dubi Aunty Murja daga tsayen da take ta ce. "Ina Yini Aunty?" Numfashi Aunty Murja ta sauke ta ce. "Lafiya ƙalau Meenal." Duban Hajiya Saudat ta yi ta ce. "Bye Mommy sai na dawo, Abdul na jira na tun ɗazu." "To a dawo lafiya, Allah ya kiyaye ya tsare." Bayan Meenal ta fita cike da al'ajabi Aunty Murja ta ce. "Aunty Saudat! Yanzu da wannan shigar kamar ta ƴaƴan turai kika bar Meenal ta fita?" Ɓata fuska Hajiya Saudat ta yi ta ce. "Ban gane ba? Me ne laifin shigar jikin Meenal?" "Haba Aunty Murja, ƴar taki guda ɗaya tal a duniya kikewa irin wannan tarbiyyar? Gaskiya wannan al'amarin naki da sake, kamar ba ki ga yanayin shigar tata ba ne? Kuma idan na ji da kyau kamar wani ta ce yana jiran ta." "To sai me? Kawai sai in hana yarinya sakewa ta yi abun da take so? Mene a ciki dan sun fita da saurayi? Kuma ba wani gurin za ta je ba birthdayn ƙawarta zai raka ta." "Taɓdi can! To ko ma ina zai raka ta ai bai dace ba, yaran yanzu ka yi iya yinka ma ya aka ƙare balle ka yi musu irin wannan riƙon sakainar kashin." Haɗe rai Hajiya Saudat ta yi ta ce. "Me kike nufi Murja? Wacce irin magana ce wannan? Ni fa ba na son irin wannan sa idon, haba daga yarinya ta fita sai ki fara wani zancen mara tushe?" "Zancen nawa ne mara tushe Aunty Saudat? Shikenan Allah ya kyauta ya kare." Tunda ta fito ya ƙura mata ido ta cikin glass ɗin Motarsa, lips ɗinsa na ƙasa ya lasa cikin duniyanci. "Oh My God! Irin wannan kyau haka Baby na?" Abdul ya faɗa lokacin da Meenal ta buɗe Motar ta shiga. Murmurshi ta yi tare da yin fari da ido ba ta ce komai ba. Hugging ɗinta ya yi suka fara shashancinsu. Bayan wasu mintuna ya kunna Motar suka tafi. Wani ɗan ƙaramin gida mai kyau suka je, babu kowa a gidan, shi ya fita ma ya buɗe gate suka shiga. Bayan sun shiga ya fita ya buɗe wa Meenal Motor tare da faɗin. "I want to show you a special love today my Baby." Ya ƙarashe maganar tare da kashe mata ido. "Mee too." Ta ba shi amsa tare da kwanciya a jikinsa. Kissing forehead ɗinta ya yi sannan ya kama hannunta suka shiga cikin gidan. Direct wani bedroom suka shiga suka faɗa kan gado rungume da juna, shaiɗan na kaɗa musu ganga a tsakiyar kai. Har bayan Magriba Meenal tana gidan Abdul, wanda ya yi nasarar raba ta da budurcinta a yau. Da farko Meenal ta ɗan damu bayan komai ya kammala, amma Abdul ya kalailame ta da daɗin baki, ya nuna mata hakan ba wani abu ba ne tunda shi zai aure ta. Ba tare da fargabar komai ko damuwa ba ta kimtsa ya mayar da ita gida. Abdul sai soyayya da ƙauna da tarairaya yake nuna mata. Jiki babu ƙwari ta shiga gida saboda yanda take ji ko'ina na jikinta na yi mata ciwo saboda rashin sabo, yanayin tafiyarta kaɗai zai saka duk wani mai hankali da ya san me yake yi ya gane abun da ya faru. Amma Meenal tana cewa Hajiya Saudat ciwon mararta ne ya tashi ta yarda. Tun daga wannan rana Abdul da Meenal suka zamto tamkar mata da miji, kodayaushe cikin sheƙe ayarsu suke. Yau Lahadi, wanda ya kama saura sati Uku a fara shagalin biki, yau ne kuma za a kawo lefen Abra daga gidansu Adnan. Tun da safe driver ya kai ta gidan Aunty Iman, kasancewar Maza ne za su kawo kayan. Tana kwance a bedroom ɗin Aunty Iman, idanunta a lumshe hawaye na fita daga cikinsu yana bi ta gefen idonta ya sauka akan pillow'n da take kai. A haka Aunty Iman ta shigo ta same ta. Cikin mamaki ta ce. "Subhanallahi, kukan me kike yi Abra? Ko auren ne ba kya so?" Buɗe idonta ta yi tare da taune lips ɗinta na ƙasa, cikin muryar kuka ta ce. "Ina so Aunty, kuma ina son Adnan sosai, damuwata kawai Salman ne." "Me ya samu Salman ɗin?" "Ban san me na yi masa ba Aunty, tunda ya tafi ko kira na bai yi ba, kuma ya san ina cikin tsananin kewar shi." "Ki yi haƙuri, may be sha'anin karatu ne." Girgiza kai ta yi ta ce. "Ba karatu ba ne na sani, tunda yanzu bai isa fara karatun ba, sai ya fara koyon yaren ƙasar na 1 Year fa, idan ma karatun ne ai ko text ne ya turo mini." Lallaɓa Abra Aunty Iman ta yi ta samu ta bar kukan da take da ƙyar. Amma a cikin zuciyarta ba ta daina ba, saboda ita kaɗai ta san halin da take ciki, gabaɗaya babu wani karsashi ko ɗokin bikinta da take yi, saboda rashin Salman a kusa da ita. Da yamma Abban Adnan suna zaune a parlour shi da Yayansa suna tattaunawa akan lamarin bikin mutanen da suka kai lefe suka dawo. Uncle Kabir ƙanin Abba shi ya fara shigowa cikin wani irin yanayi, da kallo su Abba suka bi shi har ya zauna. Yayan Abba mai suna Alh. Mustapha ya dube shi ya ce. "Yaya Kabir? lafiya kuwa?" "Akwai matsala Yaya." "Subhanallahi? matsala kuma? ta mece ce?" Abba ya tambaya cikin ruɗu. "Yarinyar da Adnan zai aura, Major Khamal ba shi ne ainihin Mahaifinta ba, tsinto ta ya yi a daji." "Kai kuwa a ina ka jiyo wannan maganar mara daɗin ji?" Cewar Alhaji Mustapha cikin tsananin mamaki. "Daga majiya mai ƙarfi, dan haka da sake wai an bai wa mai kaza kai da ƙafafuwa, tunda Allah ya sa kafin a ɗaura Aure muka samu wannan labarin dole a fasa abun nan, dan ba za mu haɗa iri da Yarinyar da ba a san asalinta ba!" Littafin nan na kuɗi ne ₦300 NE Via 0116886423  Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne mtn na 500 idan transfer ta account ne ɗari uku kacal. Evidence of payment 07063065680 ko 09047871750. [10/7, 2:28 PM] Abk: "Sunan zuri'armu zai ɓaci muddin muka bari Adnan ya auri yarinyar nan wacce babu wanda ya san Asalinta balle iyayen da suka haife ta, We want a girl with originality and roots" Cewar Uncle Khabir ya faɗa yana mai girgiza kansa, alamar abinda ya ke faɗa tun da ga ƙasan zuciyarsa ya ke fitowa. "this is not a problem, and Adnan must marry this girl as he intended, ni baga wani aibun Auren ta ba gaskiya, kowa akwai yadda Ubangiji ke tsara masa rayuwa" Kallon Alhj Mustapha Uncle Khabir ya yi fuska babu walwala ya ce. "Yaya mara asalin kake so yaronmu ya aura? Kada ka manta yadda jama'a ke mutun ta familynmu, ta yaya zamu zuba idanu Adnan ya aure ta, bayan mun san abinda hakan ke nufi? Our dignity is seen, we have money, education. Mun fito daga cikin Ahhali mai kyau da nagarta, auren Adnan da wannan yarinyar na nufin zubewar Alhhalin Matawalle I don't want that to happen" Da Mamaki Alhj Mustapha ke kallon Uncle Khabir, he just thinking ina ilimin Khabir ya tafi haka? numfashi ya sauke cikin tarin nutsuwa da nuni d cewa shi ɗin he's educated ya ce. "Idan Abra Khamal Khamis ta kasance Shegiya ko mara tushe da asali kamar yadda kake ta ɗaga murya kana faɗa, ina tunanin cewa ba ita ta tsarawa kanta yadda za tazo duniya ba. Kuma bada yardar ta abinda ya kasance ya kasance ɗin ba, God determines everything that happens, and He determines how a person will come to earth. Ka ɗauka hakan zai iya kasancewa da wani namu, ɗa kuma na kowa ne so please ka bar wannan maganar" Jinjina kai Uncle Khabir ya yi cikin girmamawa kuma ya ce "Shi kenan yaya, Allah ya basu zama lafiya" "Amin, Amin" Alhj Mustapha ya faɗa yana sakin Murmushin jin daɗi na amincewar ɗan uwan nasa. "Do me a favor, please." Professor Aliyu Matawalle ya faɗa yana gyara zamansa kana kallon su kasan cewa, kuɗi ya gama yin kuka a jikinsu, ga tarin ilimi komai nasu a waye ya ke kuma cike da tsari. "Muna jinka idan har bai gagara ba" "Ba zai gagara ba Insha Allah" Abba ya faɗa idanunsa akan Uncle Khabir kafin ya ce. "Maganar nan ta tsaya iya mu, bana son Sp Adnan yaji wannan maganar, balle wata rana ya goranta mata, I know he loves her, but the heart can decide for him one day. Even Hajiya bana son ta san haka balle ya fita zuwa Matawalle Family please brother's" Murmushi Alhj Mustapha ya ƙara saki ya ce. "U don't have to be worried about, babu wanda zai ji haka Insha Allah. Adnan nada hankali da tausayi ba zai taɓa aikata hakan ba koda yaji haka, nasan kuma Barrister ba zata ce komai ba" "Bar sha'anin mata yaya, bana son Hajiya ta san zan can wallahi kasan abin surutu da yayatawa baya yi musu yawa, zata iya hana auren wanda kan janyo matsala ga Adnan. Bana son komai ya samu Adnan" Uncle Khabir ya ce. "Extly. Mace taji zance ka tabbatar kowa ya sani more Especially irin wannan, Allah dai ya ki yaye" Rufe zan can sukai tare da fara tattaunawa akan sabon Companyn da zasu buɗe ƙarƙashin Matawalle Family. Bayan Magrib Sp Adnan ne zaune shi da Usman cikin wani ƙaramin garden dake gidan, ba zaka taɓa cewa duhun dare ya fara kawo kai ba, sbd yadda wajan ya ƙayatu haske ko ina. A hankali Sp ke sipping tea ɗin da ke kusa da shi, yana lumshe fararen idanunsa gaba ɗaya gajiya ta saukar masa a karo na farko na rayuwarsa damuwa ta bayyana akan fuskarsa. "Gaskiya gidan ka ya haɗu Sp duk wanda ya yi maka zanan gidan ya iya, anya ba za'ai min irinsa ba" Harara Sp ya watsawa Usman ba tare da ya ce komai ba. Usman ya gyara zama ya ce "U looks so worried what's up?" Watsa hannun Sp ya yi a hankali ya ce. "Time ɗin bikina nake gani kamar baya zuwa" "Are you serious? Maganar 3weeks ake shi ne baya sauri this is wonderful yau Sp ke son kasancewa da mace" Idanunsa dake a rufe ya buɗe tare da kai hannunsa ya ja zip ɗin gaban rigarsa surar jikinsa ta bayyana. "Ina jinta a nan" Ya faɗa yana nuna saitin zuciyarsa da hannunsa "komai ƙwace min ya ke idan naji muryar ta, i can't control myself idan nai tozali da Fuskar ta, kamar nai ta kasancewa da ita har gaban Abada" "The day I've been waiting for has come. Allah ya nuna min Annabi kamar yadda naga wannan ranar, yau Adnan ke sambatu akan wata" "Ba wata bace, she's my wife mother of my children my life partner" Sai kuma ya gyara zamansa sosai jikinsa na fidda Ƙamshin Pur oud ya ce. "My wife is different from other women, firstly sanyin halinta ke ƙara sawa na sota, uwa uba haƙuri da biyayya, she never lie to me" baya ya yi kaɗan yana lilo jikin Kujera da ya ke zaune tare da rufe idanunsa a hankali ya saki lallausan murmushi wanda ya sanya fararen haƙoransa bayyana cikin husky voice ya ce. "A beautiful woman, with big white eyes and a small mouth with a sweet voice and a lot of religious knowledge. Wow Sp Adnan Aliyu Matawalle I'm lucky ni mai sa'a ne" Dariya Usman ya yi sosai yana ɗaukan bottle of water tare da ɓalle murfin gorar ya tsiyaya wa Adnan ya ce. "You have to drink this ko ka samu nutsuwa" tashi Adnan ya yi yana shafa kansa bai ƙara cewa komai ba ya nufi cikin gida saboda kiran sallar issha da ya ji. Miƙewa Usman ya yi ya ce. "Amma da ga ɗan iska sai kai, ka kirani akan tsara Invitation na ɗaurin aure, But you didn't tell me anything about it,We don't have time, we don't have anything planned for the ceremony" "Karka min ihu akan I.v ko da shi ko babu dole a ɗaura min aure kuma a kawo min Angle gidana" dry kawai Usman ya yi yana ƙara mamakin yadda idanun Sp ya rufe akan Abra, ga shi ko a photo ya hana ya ganta Maybe shi da ganinta sai kuma biki idan Allah ya kaimu da rai da lafiya. Bayan sallar issha Sp da Abba da Hajiya Mama duk suna zaune a dining area suna yin dinner, rabin cin abincin Abba ne da Hajiya, Sp tea kawai ya ke sha a hankali, sai fried indomie wacce akai masa ta sha hanta sai Ƙamshin ta ke, bayan sun kammala ne Hajiya ta kalli Sp ta ce. "Ya kamata a kawo min Daughter-in-law" ɗago kansa ya yi a hankali ya zubawa mahaifiyar tasa ba tare da ya ce komai ba. "Ka tsare ni da idanunka ko baka gane bane?" Ɗan marairaicewa ya yi ya ce "Haba Hajiyata idan ban gane ba to maganar wa zan gane?" Abba ya kalli Adnan ya ce. "Rigima ce kawai ta Barrister amma tun daga Kano ya ɗakko ƴar mutane har Kaduna, ai iyayen ta ba zasu amince ba" Jinjina Kai Sp ya yi kafin ya ɗauki wayarsa ya ce "Ina laifi a haɗaku V.c amma is too par from kano to Kaduna" "I knw, na matso naga Daughter-in-law ɗita nima kafin Allah ya kawo mana Grandchildren" Shafa kansa ya yi zuwa Fuskarsa yana sakin Murmushi "I'm so anger to see my wife kusa dani" "Me kace?" Hajiya Mama ta watso masa tambayar domin kusan a fili ya yi maganar bawai a zuciya ba kamar yadda yai niyya. Miƙewa ya yi idanunsa akan wayarsa ganin notification. "Abba, Hajiyata good night" da idanu suka bisa sai da ya ɓacewa idanunsa Hajiya Mama ta ce "A wanne part zai saka Amaryar ne naga baya magana hakan?" "A gidan sa zai sakata" nan da nan Mama ta ɓata fuska domin har zuciyata ta ke son zaman Abra kusa da ita, ko Adnan baya nan sai su zauna tare. Haƙuri Abba ya bata akan ta rabo da shi yanzu yana kan giyyar soyayya ba zai fahimta ba. Misalin 11:00 na dare bayan ya kammala shirin kwanciya bacci sbd gobe tafiya ce da shi mai muhimmanci, a hankali ya gama saka rigar pyjamas ɗin kana ya zauna gefen gado yana kwanciya tare da sakin ajjiyar zuciya. Wayarsa mai ƙirar iphone 13max pro ya ɗauka a nutse ya lalubi number ta tare da danna call ba tai wani rigging da yawa ba akai picking call ɗin. "Bebbbb" Ta faɗa cikin siririyar muryarta wacce bata fita sosai, saurare ɗaya kuma zakai mata kasan cewa mamallakiyyar muryar tana cikin damuwa. "What happened to your voice?" A shagwaɓe ta ce masa "Nothing, how are you?" "Good and you?" Cikin salon taɓara ta ƙara narkar da muryarta ta ce "not good" a hankali Sp Adnan Aliyu Matawalle ya mirgina kaɗan yana jan pillow zuwa jikinsa. "Lafiya? Jikin ne?" Kamar tana gaban sa ta girgiza masa kai low ɗin voice ɗinta tasa keyi "No lafiya nake, I'm just wanted to see you please" wani kalar murmushi ya saki ya ce. "Cewa zaki kina son ganin mijinki right?" Turo masa baki tayi ba tare da ta ce komai ba, kamar wanda ya ke Kallon ta ya ce. "Allah ya baki sa'a a turo bakin nan a gabana yarinya" "Me zakai to?" Ta tambaya tana gyara kwanciyarta "idan Kinyi zaki gani, now tell ya Faris ya kiraki?" Kamar mai jiran kaɗan ta saka masa kuka sai ka ɗauka shi ne yai mata ba daidai ba, shiru ya yi mata tayi kukan yadda ta keso kafin ya ce. "Cry... Cry... Cry as so much as you can" kukanta ta ƙarawa sauti sai da numfashinta ya fara fisga ya ce "Ya isa, kada na ƙara jin sautin kukan nan" ya faɗa babu wasa kuma alamar warning. Shiru ta yi masa shi ma bai sake cewa komai ba, sai sautin bugun zuciyoyinsu dake fita lokacin ɗaya, idan akwai abinda Sp Adnan Aliyu Matawalle ya tsana ya ji mace na kuka, balle yanzu da ya kewa Abra kallon komai na rayuwarsa ta yaya zai so yaji kukan ta? Sam zuciyarsa ba zata jure ba. Kashe wayar ya yi baki ɗaya tare da kwanciya zuciyarsa babu daɗi. Da ga can ɓangaren Abra lumshe idanunta ta yi hawayen da ke maƙale ya silalo zuwa saman fuskarta, tana ƙanƙame wayar a jikinta numfashinta na fita da ƙyar murya a daƙushe ta ce. "Why Faris? Ban cancanci hakan a gareka ba, mene ya sa zakai nisa da duniyata? Mene ya sa zaka barni a lokacin da nake tsananin buƙatar ka kusa dani, please come back to me wallahi na maka Al'ƙawarin na fasa auren ba zanyi ba, ina jin tsoro gabana faɗuwa kamar wani abu ne ya sameka" Wani raunataccen kuka ta saki sai da tayi mai isarta kafin ta miƙe zuwa toilet ta wanke fuskarta tare da ajjiye wayarta, fita ta yi da ga cikin ɗakin kai tsaye bedroom ɗin Salmanun-faris ta nufa ta ci sa'a a buɗe ya ke. Tana shiga ta kwanta a kan gadon sa, tare da jan pillow ta rungome kewarsa na fisgarta, a hankali ta saka hannunta ta shafi laɓɓanta sai a yanzu Abinda Ya yi mata ya shiga dawowa cikin kwakwalwarta, tana ganin abun tamkar a mafarki ƙara ƙanƙame pillown ta yi domin ji tayi kamar yanzu ne Faris ke sumbatar bakinta. "I miss You Faris, I love you ɗan ƙanina please ki sau ɗaya ne ka kirani just to say hi to me" Washe gari da sassafe Mami ta shirya ta nufi gidansu sbd kiran da Anuty Suwaiba tai mata, Abra bata san tafiyar ta ba, sai farkawa tayi ta ga mata nan, daman Abbi ya koma wajan aiki. Tana zaune a Parlour ita ɗaya kamar mayya tunanin Faris da Unknown ɗinta ya addabi zuciyarta, wayarta ce ta fara kawo haske ganin sunan da tayi Saved number Abbi ya sa ta ɗauka da sauri tana faɗin "Abbina" "Sweetheart" Abbi ya faɗa a taushashe yana gyara zamansa akan kujerar da ya ke zaune tare da sakin Murmushi. "Abbina gidan babu daɗi ni ɗaya ce Abbi please ka dawo min da Faris" "Ohh na ɗauka zaki ce na dawo? Ni ba'a damu dani ba sai Faris Faris, ga kuma kamar Jaririya?" Kamar ya ce tayi ta sakar masa kuka gaba ɗaya ta addabi zuciyarta da kanta baki ɗaya. Baya Abbi ya yi yana ta shi tsaye tare da goya hannunsa ɗaya a baya ya shiga takawa cikin nutsuwa. "Zaki tarwatsa min zuciya sweetheart? Kullum kuka Ohhh yaaaa shiru da bakin ki a nan wajan" Shiru ta yi masa sai ajjiyar zuciyar da ta ke saukewa wanda ya ke jinta sosai ta cikin wayar a kame ya ce. "Ki daina kuka sbd Allah da kuma ni Abbinki bani da nutsuwa" a sanyaye ta ce "na daina Abbi ya aiki? Ka yi waya da Salman?" "Kince ke ɗaya ce ko?" Ya tambaya tare da yin rejecting questions ɗin ta."E,Abbi" jinjina kansa ya yi kafin ya ce. "Ta shi kije Garden ki sha fresh air zaki ji sauƙin zuciyarki,amma idan kika sake kuka mun ɓata ba ruwana da ke" da sauri Abra ta ce "ban sakewa Abbi" "That's my girl Abra Khamal Khamis smile" Murmushi ta sakar masa "Thank you Abbi" bai ce komai ba ya kashe wayar baki ɗaya. Wayar ta bi da kallo sai kuma ta miƙe tare da ajjiye ta a Parlour ta nufi Garden. Uncle Faisal ne tsaye a gaban Mami sai Masifa ya ke. "Ni nace ina son Yarinyar nan kuma auren ta zan amma sbd an raina min hankali aka bawa wani ita, na cire kunyata har wajan fake father ɗin nata naje amma ya nuna bai amince ba" "Saurara Faisal ni kake son tunawa asiri? Matsayin ƙanin uwa kake wajan Abra sai kuma kace kana son ta? Kasan abinda hakan ke nufi? Yana nufin tona asirin shekaru kusan ashirin ke nan, wanda kuma daidai ya ke dana rasa igiyar aurena, bana son shirman banza kada ka sake yi min magana akan Abra,banda masifa me zakai da ita?" Mami ta ƙare zan can cikin ɓacin rai da kuma damuwa. A fusace shima Uncle Faisal ya ce. "Igiyar auren ki bata gabana, kuma aure ne anyi mugani sai dai idan bana raye wallahi, Abra mallakina ce tun tana ƙarama nake fama da son ta a zuciyata to ayi mu gani idan tusa zata hura wuta" Yana faɗin hakan ya fice da ga cikin gidan baki ɗaya, Anuty Suwaiba ta ce. "Kan uba me Faisal ke nufi? Me zai aikata Na'ima ba kiga ta zama ba, idan baki son ki dawo gida mu jere matsayin zawarawa sai ki san abinyi" Dafe kai Mami ta yi cikin rashin sanin Abinyi ta ce "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" A hankali motar Fayyad ta shigo cikin Railway quarters ɗin yana zaune ɓangaren mai zaman banza sai Fayyad da ke driving yana tsokanar Sp Adnan. "Da safe munyi waya baka ce min zaka zo ba, sai yanzu naji kira da ga sama wai kana airport" Idanunsa akan gate ɗin gidan su Abra ya ce. "To Ubana ne kai da zan faɗa maka? Ko shi bai san zan zo kano ba" Parking Fayyad ya yi yana faɗin. "Fitar min a mota to mara mutunci" kafaɗa ya ɗaga irin ko a jikinsa ɗin nan. Fita ya yi a motar Fayyad na faɗin "babu ko godiya?" Banza ya yi masa. Walking slowly ya nufi gate ɗin, yana zuwa gatekeeper ya buɗe masa ƙofar cikin girmamawa, gaba ɗaya sojojin da suke wajan suka gaishe sa dake duk sun san shi. Wayarta ya fara kira amma bata ɗauka ba, ga shi ba abin ya shiga gidan kai tsaye ba, kuma ba zai iya komawa bai ganta ba, tafiya ce da shi zuwa Egypt. A hankali ya kalli ɗaya da ga cikin sojojin kafin ya yi magana wani ya ce. "She's in the garden" Hanyar Garden ɗin aka nuna masa, a hankali cikin nutsuwa da kamala ya nufi ciki, tun daga nesa ya hango ta ƙasan wata bishiya ta ɗora kanta akan wani ƙaramin dining dake wajan sai bottle water da ke kusa da ita, ta ɓoye kanta a hannayenta. Kamar mai bacci a hakan, har ya Ƙarasa inda take ya ja Kujera ya zauna bata sani ba. Hannunsa ya sa baki ɗaya ya ɗagota, ganin bacci ta ke a hakan ya sa ya ɗan tsora mata shanyayyun idanunsa, yana ƙara yaba kyan da Ubangiji ya yi mata. Kumatun ta ya shiga bubbugawa daidai kunnen ta ya ce. "Open your eyes Wife ga mijinki ya amsa kira" Turo baki tayi ta ce "Faris i knw one day zaka dawo gareni please kada ka sake barina" ta faɗa tana ƙanƙame jikin Sp Adnan Aliyu Matawalle tare da ɓoye fuskarta a ƙirjin sa a tunaninta Faris ne, domin bacci ta ke amma mafarkin sa ta ke. Bakin ta Sp ya kama ya murza yana faɗin "Ohh Wannan Faris anya ba zan tayaki biko ba?" jin yadda ake murza bakinta ga Ƙamshin Pur oud da ke ratsa hancinta ya sanya tayi saurin buɗe idanunta da ke cike da bacci. Haɗa idanu sukai ta ganta male-male a jikin mutum, jikinta na rawa ta fara ƙoƙarin sauka amma ya riƙeta sosai. "Ba inda zaki, tunda a nan kike bacci gwamma kiyi a jikin mijinki" ya faɗa yana ƙara riƙe ta. turo baki tayi ta ce "ka cikani ba ruwana da kai" ganin abinda ya ke ƙoƙarin yi tayi saurin ɗauke fuskarta ta shiga dokan ƙirjinsa tana sakin kuka.. "Ba ruwana Allah ba kace ba zaka zo ba?kayi tafiyarka ni ban son auren na fasa" "Baki son auren ko baki sona" kuka kawai ta ke sakar masa hadda shassheƙa, shiru ya yi mata yana ƙara riƙeta a jikinsa. Washe gari bayan taiwa Sp rigima sosai a makaranta da ke a Kano ya kwana da ƙyar ya rarrashe ta, ta ce Faris ya tafi shima zai ta fi ya barta a haka suka rabo da al'ƙawarin zai dawo Soon. Har yamma tana shcl karatu ya fara ɗaukan zafi, da ƙyar ta ke yaƙi da zuciyarta wajan ganin tai karatu amma tunanin Faris da Unknown Kullum da su take kwana ta ke ta shi, wanne hali Faris ke ciki? Fushi ya ke da ita ko mene?. Waye Unknown mene ya sa kalamansa suke da tasiri a Zuciyarta yaushe zai bayyana gareta mene ya sa ya daina yi mata messages yanzu?. Meenal ce tsaye a gaban makeken Bulama hospital, cikin nutsuwa ta shigo reception ɗin tana bin mutunan wajan da kallo. Wata mata dake riƙe da yarinya mai Sikila ta kalla kafin ta ce. "Ya kike zaune da ita tana soma? Ko ba soma bane?" Kafin tai magana da ga bayanta akace "ku kaita Emergency room yanzu, ai mata duk abinda ya dace ban san mene ya sa kuke barin patient ba kulawa haka ba" "Daddy" Meenal ta faɗa daidai kunan Bulama, hannunta ya kama yana nufar office ɗinsa da ita ya ce. "My dear zuwan ba zata?" Fari tai da idanu ta ce. "Wallahi Daddy kawai naji ina son zuwa hospital naka, amma banji daɗin yadda naga marasa lafiya haka ba" "Shi yasa na so ki karanci Ɓangaren lafiya amma kika watsa min ƙasa a idanu, gaba ɗaya basu da serious akan aikin su, banda muna da tsananin kulawa ban san zai dinga faruwa ba, wasu da ga cikin Likitocin kuma idan ba kuɗi basa duba mara lafiya" "But this is not fair Daddy, yaya mutum zai idan bai da kuɗi gsky ana kulawa wanda ya taimaki wani sai Allah ya taimake sa" kallon Meenal Daddy ya yi kafin ya ce. "That's why na ware ɓangaren marasa ƙarfi ana musu komai as voluntary" Yana zaunar da itace a office ɗin ya fito da sauri yana haɗa kan Likitocin da nurse's ɗin ya ce. "Duk wanda suke reception a duba so kyauta don't make any mistake" kamar yasan Meenal zata zaga asibiti ganin komai lafiya wasu sai godiya suke ta ƙara gasgata girman tausayin Mahaifinta. A hankali lokacin ya fara juyawa, satittika suka fara zama kwanaki har Ubangiji ya kawo satin bikin Abra Khamal Khamis da Sp Adnan Aliyu Matawalle. Shiri ake da ga ko wanne ɓangare, abinka da masu kuɗi sai ka rasa wanne ɓangare ne ya fi ji da bikin. Gefen Abra abin ba sauƙi ta rame sosai Kullum cikin kuka ta ke, gaba ɗaya ta tashi hankalinta akan Salman, wanda ya sa Ammi ta ɗauke ta zuwa can gidanta a can ake mata gyara jiki. Sp Adnan ango Kullum yana tare da amaryarsa a waya yana yin iya bakin ƙoƙarinsa wajan ganin ya faranta mata, gefe guda kuma har lokacin Abbi bai dawo ba, Khairy sai shige da fice suke domin sun haɗa plain na dinner a ɓoye ita da Usman da su Fayyad. The day. Yau ya kama ranar juma'a wanda ya yi dadai da ranar da za'a fara biki wato Kamu. Tun safe aka fara zuba decorations a harabar gidan Abbi sai ka ɗauka babban hall aka kama sbd tsarin wajan. Har yamma babu amarya babu labarinta, Hankali ta she Mami ta kira Khairy ta ce. "Ummulkhairy ina Abra?" Khairy da ke gidan kwalliya ta ce. "Mami ina gidan kwalliya Abra ma tana gidan da za'ai mata kwalliya" "Ok call her immediately" Katse kiran ta yi, khairy ta kira number Abra a kashe hakan ya sa ta kira number mai make up ɗin tana ɗauka ta ce. "Hello don Allah Abra fa?" Mai make up ɗin ta ce "Tun 3 aka gama mata kwalliya na ce ta jira ta ce zata da ganta yanzu wajan 5 ake nema na yamma tayi kusan 2hours da tafiya" A fili Khairy ta ce. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un kanan dai ta gudu kamar yadda ta ce..... Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 08081012143 [10/10, 4:17 PM] Abk: Jiki na rawa, Khairy ta kira Mami tana salati tana salallami, Mami ta ɗaga wayar ta ce "Ya aka yi? Ta na ina ne, mutane sun fara taruwa fa?". Khairy murya na rawa ta ce "Mami na kira mai kwalliyar ta ce mini tun uku, aka gama kwalliyar, kuma ta tafi". Mami ta ce "Ta tafi taje ina?" "Mami Wallahi ban sani ba, ba guri ɗaya muka je kwalliyar da ita ba, ni gurin da naje daban". Mami ta ajiye waya tana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yarinyar nan gidan ubanwa ta tafi ne? Ace an gama kwalliya tun uku amma har haɗu da rabi ba ta iso gida ba, ga mutane sun fara taruwa". Anty suwaiba ta ce"Allah yasa ba guduwa ta yi ba". Mami ta zare ido ta ce "Ta gudu ta je gidan uban wa? Lallai ma yarinyar nan". Abu kamar wasa, ba Abra babu dalilinta, tun ana maganar ƙasa_ƙasa, har mutane suka fara jin halin da ake ciki. Abokan aikin Adnan ne, suke ta shiri cikin shigarsu ta police, domin dai za'a yi parrate na ban girma ga Adnan da amarayarsa. Usman ne ya kalli Adnan da ke ta haɗe rai ya ce "Wai haɗe ran me kake ne?". Adnan ya ce "Am jealous ne, duk wannan garadan sai kun je kun kalle mini mata". Aminu ya ce "Kai dalla ware, ai kaima gardin ne, sai kace a kanka aka fara Aure, ko da yake tsiyar mutum ya zama tuzuru kenan, duk sai ya fara behaving abnormal". "Meye banbancina da kai? Har gara ma ni yanzu zan shige daga ciki, kai kana waje". "Nima ina hanya ne" Usman yayi Maganar yana murmushi. Daga haka suka kammala shirinsu, suka fara haramar tafiya gidansu Abra. Granny ce ta shiga sashin Na'ima tana faɗin "Ke Na'ima, wai wace Maganar banza nake ji ne? Wai kamar Ana Abra ta ɓata, gidan ubanwa ki kai ta?" "Haba granny, Ina kuwa zan Kai ta, daga zuwa kwalliya ba ta dawo ba". "Ƙarya ki keyi, ana Magana kina wani ƙifta ido kamar ta Allah, ki fito da yarinyar nan duk in da ki ka kaita, kan in samo madoki in shemeki a gurin nan". Ammi ce ta ce "Granny ki yi haƙuri, ya za'ayi ta aikata haka ga 'yar ta, Yanzu dai muyi ta addu'a, kuma a kira shi angon a sanar masa dan a san abun yi". Granny ta ce "Wai ke Yaushe zaki gane kan makircin wannan yarinyar ne? Ai duk abun da akace tayi babu mamaki, yau duk abun da za'ayi sai an nemo mini jikata. Amm ke nace ina tabarau na ne? in ƙarewa wannan mara Kunyar kallo, in kalli idanunta sosai, dan ni idan na kalli idon mara gaskiya ina gane shi". Ammi ta ce "Glass ɗinki yana in da ki ka yi salla, amma dan Allah ki dena wannan maganganun, bari a san abunyi, ko a tura wasu gurin mai kwalliyar". Na'ima kuwa iya ƙuluwa ta ƙulu, ji take kamar ta rufe Granny da duka, shegiyar tsohuwa hayyataciya, sai tsawon rai kamar dabino, ta ƙi mutuwa kuma kullum cikin rikici take, tsawon shekarun da Na'ima tayi tare da Khamal Granny ba ta ƙaunarta sam. Gida ya rikice ana neman Abra, ita kuma Granny ta rikice tana neman tabarau, ta ɗora da masifar cewa bayan sace Abra da Na'ima tayi, ta kuma sace mata glashinta, saboda baƙin hali. Anty Suwaiba ta ce "Wai ke Na'ima ba wani mataki da zaki ɗauka a kan wannan sokuwar tsohuwar, shegen surutun tsiya kamar an jefeta a ka?". "To ni ya zan yi da ita? Wannan kaidinta ya fi yadda kike tunani, yanzun nan za ta ƙullawa mutum sharri. Ɗakin Salman Granny ta nufa, tana cigaba da zage Na'ima, Ammi ta ce "Granny me zaki yi a nan kuma?". "Tabarau na nake nema". "To mai ze kai glass ɗinki nan kuma? Na ga tunda muka zo baki je nan ba". "A'a, ance idan raƙuminka ya ɓata ka neme shi har kura tandu, yo na sani ko wannan algungumar ta yi garkuwa shi ta kai ta ɓoye" ta ƙarasa Maganar, tana nufar ɗakin Salman. Sai dai tana shiga ɗakin, ta ƙwala uban ihun da ya janyo hankalin 'yan biki. "Gata nan ku zo gata!" Ta yi maganar cikin ihu. Su Ammi na zuwa, suka tarar da Abra a zaune, fuskarta sharkaf hawaye. Ashe tun bai fi uku da rabi ta dawo gida ba, ta shiga ta ƙofar baya, tabi ta kitchen ta shige ɗakin Salman abunta, kuma ta kashe wayoyinta. Ammi ta ce "Abra, dama kina nan ki ka ɗagawa mutane hankali? Kuma kalli duk kin fara ɓata kwalliyar". Cikin kuka Abra ta ce "Ammi Faris ɗina, zan yi Aure baya nan, dan Allah Ammi kice musu na fasa Auren nan a dawo mini da Faris ɗina". N'a'ima a fusace ta ce "wannan wane irin sakarci ne haka Abra? Mun tara mutane kina neman ki bamu Kunya? Kawai kin ɗagawa mutane hankali". "Mami ni bana son Auren nan na fasa, dan girman Allah Ku dawo mini da ɗan uwana" tayi maganar tana ƙoƙarin cire ɗaurin kanta, ga numfashinta da ya fara sama. Ammi ta girgiza wa Na'ima kai, alamar ta dena yiwa Abra faɗa. Granny ta ce "Ji min 'ya da wauta, ke yanzu sai ki fasa Auren, aikuwa da kin yiwa kanki kutunguilar tsiya, hmm jiya ba yau ba tsohuwa ta tuna kwanan turaka, yarinya karki cuci kanki" Granny ta yi maganar tana watsa guntun goronta a baki, ta bar ɗakin, murmushi Ammi ta yi, Granny ba ruwanta haka take sakin 'yan maganganunta idan ta raya mata". Ammi ta maida hankalinta kan Abra, ta din ga yi mata Nasiha tana rarrashinta, ƙarshe sai da aka kira Abbi video call, shima yayi ta rarrashinta, Sannan ta haƙura. Aka samo wata mai kwalliyar ta gyara mata kwalliyar da ta fara ɓatawa da hawaye. Na'ima ma haɗawa tayi cikin wani rantsatsten leshi fari da golden, tun daga wuyanta zuwa yatsunta gwal ne. Hakan yayi daidai da ƙarasowar Adnan da da abokansa, haka zalika mota mota na 'yan uwan Adnan ɗin suka hallara a ƙatuwar harabar gidan Major Khamal Khamis, wadda akai matuƙar ƙawatawa. Mami ce da kanta ta kamo hannun Abra ta fito da ita daga cikin gida, duk da kanta a sunkuye yake, ta rufe jikinta da mayafi, amma hakan be hana Adnan tsinkayen farar fatarta da ta sha gyara ba. Nan masu police band suka sauke gangunan su, suka fara bugawa domin gabatar da parrate na ban girma ga Ango sha guɗa Sp Adnan Aliyu Matawalle, da matarsa gimbiya Abra Khamal Khamis, abun na masu ɗamara ne, dan haka parrate ɗin ya ƙayatar matuƙa, tare da crossing sword da aka gabatar duk dan murna ga amarya da ango. A ka zo ɓangaren kamu, a kama amarya ta buɗe fuskarta, ƙanwar Hajiyar Adnan, ta ce sun biya dubu ɗari biyar a buɗe musu fuskar Amarya. Nan wasu suka shiga tafi, yayin da Mami ta ce "ita dubu ɗari biyar yayi kaɗan". Ammi ce tsawatar dan kar ayi halin ƙaranta. Nan aka shiga gudanar da shagali, bayan Abra ta buɗe fuskarta, wanda ba su santa ba, suka dinga jinjina kyawunta, wasu kuma suna gulmar ya za tayi da Adnan, dan da kaɗan ta wuce cikinsa. "Sweetheart,yau ranar farinciki ce, amma ya naga kamar za kiyi kuka?" Adnan ya faɗa a saitin kunnenta. "Wani farinciki bai taɓa riskata, Faris baya kusa da ni ba, sai a wannan lokacin, wannan ne karo na farko, ban taɓa tunanin Faris ba zai kasance da ni ba, Ranar Aurena akan high table, ana mana hotuna da ni da shi da angona ba, sai dai....." Hawaye ne suka fara saukowa da ga idanunta. Da sauri Adnan ya ciro hanky yana share mata ya ce "dan Allah kar ki ɓata mana Wannan Farincikin, ba kowane buri namu ne yake zuwa ya cika a yadda muke so ba, kiyi haƙuri" haka ya rarrasheta, aka kammala event ɗin wannan ranar. Daren ranar, haka Adnan ya kasance da ita a waya, yana cigba da aikin rarrashi. Zuba mata idanunsa yayi yana kallonta, yadda take maye, cike da rashin Sabo, sai tamɓele take ya sakata a gaba kawai yana murmushi, yana zuƙar shisha yana fesar da hayaƙin a cikin iska. Ganin tana ƙoƙarin faɗuwa ne ya sanya shi tashi da sauri ya riƙota yana murmushi "Sweetheart, it seems like you are enjoying the moment" yayi Maganar tare da kissing ɗin goshinta. Kan makeken gadon dake tsakiyar ɗakin ya kaita, ya kwantar da ita, yana shafa dogon gashinta. Gaba ɗaya Meenal ba ta hayyacinta, ba ta tashi farkawa daga mayen da take yi ba, sai bayan magariba. A hankali ta buɗe idanunta ta kalli in da ya idar da salla, ta tashi da sauri ta kalli agogo, a gigice ta ce "Ya a kai na kai wannan lokacin? Me ka bani haka na sha?". "Calm down Baby, kayan caji ne fa kawai" "Kamar yaya kayan caji, lokacin komawata gida tuni ya ƙure, me zanje in ce a gida?" "Haba ke kuwa, kamar ba babbar yarinya ba, da alama fa kin ji daɗin cajin nan da kika yi" Wani gululun baƙin ciki ne ya cunkushe mata zuciya, a gurguje ta tattara kayanta da mukullin motarta, tai waje. Gudu take tamkar zata tashi sama, saboda tsananin tashin hankali, cike da fargaba da zullumi ta shiga cikin gidan, a Falo ta tarar da Mummy tana kaiwa tana komowa, tana ganin Meenal a rikice ta ce "Ke daga gidan ubanwa kike Yanzu?". "Amm...mm..... Mummy da..dama". "Dama me? Gidan ubanwa kika tafi? Ƙarfe nawa yanzu? Kin sanya ya tayar mini da hankali, yanzu haka ya tafi kai report gurin hukuma, akan cewar kin ɓata, ina ki ka je?". Kan Meenal ta bata amsa, sai ga Doctor Bulama ya shigo, yana ganin Meenal rai a ɓace ya ce "Ke! Daga ina kike?" "Ba ko ina". "Daga ina kike?!" Ya sake tambayar cikin tsawa. Rawar baki ta fara yi, amma ta kasa Magana, aikuwa yayi kanta ya shaƙota yana zazzare ido tare da maimaita tambayar daga ina take?" "Haba doctor,ka bita a hankali mana, idan ka illata ta fa, ko ka manta uta kaɗaice da mu?". "Dan ita kaɗaice da mu ba shi ya bata lasisin yin iskancin da ta ga dama ba, gidan wa kika je?". A shaƙe Meenal ta ce "Dan Allah Daddy ka yi haƙuri, ƙawata na bi gidansu, muka tafi gurin biki daga school". "Meyasa baki kira kin gaya mini ba, aka dinga kiran wayarki amma a kashe?". "Nayi kuskure, amma dan Allah kayi haƙuri kar ka kasheni" da Doctor ya ƙyale Meenal, bayan ta sha shaƙar da sai da ta kusa zuwa lahira. Hall ya haɗu iya haɗuwa, Abra ta haɗe cikin wani danƙareren Material, kai da gani ka san ba duk jiki ba, sai jikin 'yar gata. Adnan kuwa gaba ɗaya kishi ne ya mamaye masa zuciya, yadda kowa ke ɗaukar hoton matarsa a waya, shifa wannan taron bidi'ar dan anfi ƙarfinsa ne, amma da babu dalilin da zai sanya ayi wannan taron ana kallon matarsa. MC ne ya kira Amarya, tare da umartar ta da taje ta taho da mamanta. Cikin takun Abra na nutsuwa, taje gaban table ɗin da Hajiya Na'ima take, ta durƙusa ta kamo hannunta zuwa filin rawa. MC ya ce "Ki kalli Mamanki, ki ce nata kin gode, kuma kina sonta" Abra ta kama hannun Hajiya Na'ima, ta kalli idonta murya na rawa ta ce "Thank you very much Mamina, for all you did for me Bani da Abun da zance miki sai Allah ya baki Aljanna maɗaukaiya, and I love You Mamina" ta ƙarasa Maganar tana rungume Na'ima, tare da sakin wani irin kuka mai ban tausayi. Nan dj ya saki waƙar Wayyo Allah mamana, Na'ima ma rungume Abran ta yi tana ɗan dukan bayanta alamar rarrashi. Yayin da ta ɓalle bakin jaka, ta dinga zubawa Abra kuɗi kamar ba gobe, ji take dama Abra 'yar ta ce ta halak, da shagalin da za tayi a bikin nan yafi haka. Haka aka yi Dinner, 'yan uwa da abokan arziki, duk sun yi bajinta, ta hanyar liƙi da bada gudunmawa. Abbi tuni ya sauka garin Kano tare da tasa tawagar, kasancewar bayan ɗaurin Aure akwai reception na mussaman, da kuma parrate na sojoji, abunka da masu abu da abunsu. A can birnin Sin kuwa, Salman ne zaune a wani katafaren ɗaki, a gaban madubi ya sanya hoton Abra a gaba, ya ƙura masa idanu, idan lissafinsa daidai ne, yau ne ake ɗaurawa Abra Aure, Abran da ya ƙallafa a rai, ya taso ya rayu da soyayyarta, a yau ta zama mallakin wani ba shi ba, ina ma Mami ba ta sanar masa Abra ba 'yar uwassa ba ce ta jini, da duk wannan al'amuran basu faru ba, gaba ɗaya tun da ya zo China ba ya jin daɗin garin, komai nasu daban kamar ba Normal Mutane ba, gashi ko turancin ma ba kowane ya iya ba a cikinsu, dan haka abubuwa suna masa wahala, duk da wai kafin su fara lectures, sai sunyi wata shida ana koya musu Yaren Chinese. An ɗaura Auren Adnan da Abra, wanda dubban mutane suka sheda hakan, ɗaurin Auren da ya samu halartar manyan ƙasa daga ɓangarori daban-daban ciki har da Captain Faruk da aka tsinto Abra da shi. Daidai gwargwado an yiwa Abra Nasiha mai ratsa zuciya game da rayuwar Aure, yayin da Granny ta ta Nasihar mai ɓaro_ɓaro ce ba rufi ba kunyar komai. Da la'asar aka shirya Abra cikin wata dakakkiyar rantsatsiyar lafaya, Mami ta kaita gurin Abbi, yayi mata nasiha sosai tare da Adduoi da fatan shiga ɗakin miji a sa'a. Dangin Adnan sun zo da manyan motoci, domin ɗaukar Amarayar su. Sai dai Abra ta ƙanƙame Mami tana kuka, karo na farko a rayuwar Na'ima, tun da ta fara riƙon Abra, taji jikinta yayi sanyi, dan tun a gurin Dinner jiya Abran ta sa jikin Na'ima yin sanyi. Abra ta ƙanƙame Na'ima tana faɗin "Mamina, a zaman mu idan na yi miki laifi ki yafe mini, Mami bana son barinki". Anty Suwaiba ce cikin masifa ta ce "Wai ke bayinki ne mutanen da suka tsaya suna jiran ki, dalla ki fito ki wuce mu tafi" A hankali Na'ima ta shafa bayan Abra ta ce "Na yafe miki Abra, Allah ya baku zaman lafiya, muje in rakaki bakin Mota". "Mami to ke yaushe zaki zo?". "Very soon" daga haka ta ja hannun Abra zuwa bakin mota. Da ƙyar Abra ta yadda ta shiga, tana kuka tana ɗagawa Mami hannu. Anty Suwaiba ta ce "Ke Na'ima, wai me kike yi hakane kamar kin damu da tafiyar yarinyar nan? Allah ya raba ki da ƙwallon mangwaro kin huta da ƙuda, amma naga kamar kina cikin damuwa? Wai ni fa kamar ƙwalla nake gani a idanun ki". Jiki a sanyaye Na'ima ta ce "Gaskiyar Husawa da suka ce, 'Sabo turken wawa' a zamana da yarinyar nan ban taɓa jin abunda na ji ba jiya da ta kalli idanuna tana mini Addu'a tare da jaddada soyayyarta a gareni, idanunta ɗauke da zallar soyayyar uwa da ɗa, duk da kwashe shekarun da nayi ina azabtar da ita, amma tana mini biyayya fiye da yadda ɗan da na durƙusa na haifa yake mini, ko ba komai da ina ganin gilmawar ta da ta Salman, amma Yanzu shi ya tafi, ita ma kuma haka". "To shine me? Ke ba hutunki bane bama, ta je can ta ƙarata Allah ya tsare miki mijinki da ɗan ki". Na'ima ta ce "Hakane, dama babban fatana kenan, ta bar mini gida, shekarun da mukayi Allah ya amfana, kawai dai kin san zuciya". "Ke dalla can manta da ita". Awanni uku cif, da magariba su Abra suka isa garin Kaduna, aka fara kaita gidan su Adnan, aka yi mata nasiha, suka bata kyaututtuka, sannan suka wuce da ita gidanta. Tubarkallah Adnan ya ƙera mata gida na gani na faɗa, Abbi kuma da Hajiya Na'ima sun cika gidan da kaya na kerewa sa'a, Masha Allah gida yayi komai tsaf. Wanda suka rako Abra daga Kano, suka koma gidansu Adnan su kwana a can, daga nan su koma Kano, Abra ji tayi Kamar ta tashi ta bisu, haka suka watse suka bar Abra. Abra ta zauna jiran shigowar Ango, sai dai har ƙarfe goma sha ɗaya ba ango ba dalilinsa, tun Abra na jira har ta fara gajiya, tsoro ya fara kamata, ta takure a ƙuryar gado, gaba ɗaya tsoro ya baibayeta. Abu kamar wasa har ƙarfe biyu na dare, Adnan be shigo ba, ta ɗauko wayarta domin ta kirashi amma wayarta ta ɗauke babu caji. Rashin sanin abun yi ya sanya ta fara kuka. Haka Abra ta kwana a zaune, sai ɗan gyangyaɗi da ta dinga yi daga zaune a haka har Asuba tayi. A tsorace ta lallaɓa ta shiga banɗakin da ke cikin ɗakin tayi alwala, ta gabatar da sallar Asubahi, ta koma gefe ta takure. Mami 'yan biki sun watse, sai wanda ba'a rasa ba. Tayi wanka tana ƙoƙarin shiryawa, ta ga wata takarda ta faɗo daga cikin wardrobe ɗin ta. Ta sunkuya ta ɗau takardar ta buɗe, rubutun Salman ta gani a jiki, hakan ya sanya ta sake gyara tsayuwarta ta fara karantawa. *Assalamu alaikum warahmtullah. Ina fatan lokacin da saƙon nan zai riskeki kina cikin ƙoshin lafiya Mamina. Na san zakiyi mamakin ajiye miki wannan takarda da nayi, amma ba abun mamaki bane, duk da ba zan kira hukuncin da kika yanke a kaina kuskure ba, amma zan iya kiransa da shamaki da farinciki na, ta hanyar nisata ni da abu mai daraja da nake matuƙar ƙauna. Domin sake nesanta kaina da Abra kasancewar na san mallakin wani zata zama, ina mai sanar miki da cewa daga ranar da na bar Nigeria ba zan sake dawowa ba har Abad, dan muddin ina Nigeria, ruhina yana tare da Soyayar Abra, dan tabbatar da samun farincikinki da nutsuwar ki, ba zan sake dawowa Nigeria ba. Idan kuma kika yi ƙoƙarin tursasa sai na dawo, zan bar China in koma ba im da ba wanda ya sani. Ki huta lafiya Mamina, ki gaishe mini da Abra tare da yi mata fatan Alkhairi a rayuwar Aurenta. Salman Khamal Khamis*. Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 08081012143 [10/11, 7:20 PM] Abk: Take jikin Hajiya Na'ima ya ɗau rawa, hannunta ya fara karkarwa, ta nemi guri ta zauna a gefen gado, wani irin gumi yana tsatstsafowa a goshinta, a hankali ta furta "Na shiga uku, mai yaron nan yake nufi dani ne?" Cikin azama ta miƙe, ta ɓoue takardar ba tare da ta nunawa kowa ba. Sai ƙarfe takwas na safe sannan Adnan ya shigo gidan, shi ma bai shigo inda take ba, maganarsa ta jiyo a parlour suna gaisawa da waɗanda da suka kawo ta, hakan ya sa ta fita parlour'n da sauri, zuciyarta cike da ɗokin ganin shi. Gaishe shi ta yi, sarari ya ji ta amma ya ɗauke kai kamar bai ji ba, hakan ya faɗar mata da gaba. Amma dai ta daure suka yi sallama da waɗanda suka kawo ta, har da kukanta lokacin da suka fice daga parlour'n. A tunaninta bayan fitar su Aunty Suwaiba Adnan zai taho gare ta cikin zumuɗi ya rarrashe ta, amma sai ta ga saɓanin haka. Ƙafa ya ɗora ɗaya akan ɗaya yana latsa wayarsa, tamkar bai san da halittar ta a parlour'n ba. Cikin tsananin shock Abra ta ce. "Baby! Me yake faruwa ne? Jiya ba ka dawo ba ka bar ni na kwana ni kaɗai cikin jin tsoro, yanzu kuma ka dawo amma ka yi kamar ba ka ganni ba." Tamkar da dutse take magana, ko motsi bai yi ba da sunan ba ta amsa. Ƙura masa ido ta yi tana kallon shi cikin mamaki, Adnan ɗinta ne kuwa wannan ko an canza mata wani? Adnan ɗin da ya ci burin ganin wannan ranar da za ta kasance a gidansa, amma me ya yasa ya yi mata haka? Me yasa tana yi masa magana ya share ta? Ko dai something bad happened to him? Tunanin hakan ya sa ta matsawa kusa da shi da niyyar ta ji abun da yake damun shi. Wata uwar harara da ya ɗago kai ya banka mata yasa ta tsayawa cak a inda take cikin bugawar zuciya. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un." Abun da ta ambata a fili kenan. Rasa abun yi ta yi hakan ya sa ta koma ɗakinta cikin sauri, faɗawa kan gado ta yi tare da sauke wani wahalallen numfashi. So take ta tuno ko ta yi wa Adnan wani lefin amma ta kasa, hakan ya sa ta fashewa da kuka. Sai da ta yi mai isarta sannan ta tashi ta shiga toilet ta wanke fuskarta. Bayan ta fito ta tsaya a gaban mudubi tana kallon kanta, cikin ƙoƙarin son gano ko wani abun Adnan ya gani a jikinta da bai masa ba, amma ba ta ga komai ba. Duk da ita ba ma'abociyar son kwalliya ba ce amma haka ta zage ta tsantsara ta tare da kafa ɗaurin ɗankwali mai kyau, ita kanta ta san ta yi kyau, duk da yanda take jin wata irin fargaba a cikin zuciyarta amma sai ta murmusa, ta san dole kwalliyar tata ta burge Adnan. Daddaɗar humra mai daɗin ƙamshi ta shafe jikinta da ita, sannan ta fita zuwa ɗakin Adnan. Sai da ta fara shiga kitchen ta haɗa masa breakfast wanda aka ajiye dan shi sannan ta nufi ɗakin nasa. A zaune ta tarar da shi a kan gado yana operating system. Cikin sanyin jikinta ta yi masa sallama, ko d'agowa bai yi ba balle ya amsa mata. Hakan ya ƙara tsinkar mata da gaba, zuwa yanzu kam ta gane da akwai matsala. Kanta a ƙasa ta ce. "Ga abinci." Nan ma bai kula ta ba, kawai sai ta fashe da kuka cikin rashin sanin abun yi. Ta daɗe a duƙurshe tana kuka mai tsuma zuciya, yana jin ta amma ko tari bai yi ba, ƙarshe ma tashi ya yi ya ɗauki car key ya fice ya bar mata gidan. Hasbunallahu..... kawai Abra take maimaitawa, a ranta tana tambayar kanta me yake shirin faruwa da ita ne? Me Adnan yake nufi da ita? Jiki a saɓule ta miƙe ta koma ɗakinta ta kwanta akan gado ta cigaba da kukanta, kewar Faris da Abbi da Mami na nuƙurƙusar zuciyarta, wani azababben ciwon kai ne ya far mata lokaci ɗaya, cikin dauriya ta janyo bargo ta lulluɓe jikinta, saboda yanda take jin wani sanyi na ratsa gaɓoɓin jikinta, tamkar wadda za ta yi zazzaɓi, a haka wani wahalallen bacci ya ɗauke ta. Sai Azhar ta farka, shi ma ƙarar doorbell ya tashe ta, cikin sauri ta miƙe ta shiga toilet ta wanke fuskarta da ruwa sannan ta fito ta saka hijabi ta fita. Mata ne kusan su takwas ta gani, cikin fara'a ta tarɓe su tare da yi musu iso. Bayan sun zauna sun gaisa ta kawo musu drinks da kayan garar ta, anan suke gabatar mata da kansu. Dukkansu cousins ɗin Adnan, Ƴanmata shida sai matan aure biyu. Ta ji daɗin zuwansu ba kaɗan ba, dan ba ƙaramin ɗebe mata kewa suka yi ba. Sai dai duk bayan sakanni idan ta tuna Adnan da yanayin da ya nuna mata ɗazu sai gabanta ya faɗi. Da abinci suka zo, hakan ya sa ba ta yi girki ba shi suka ci, ita ɗan caccakalar abincin ta yi kaɗan ta ci ba don daɗi ba. Sai kusan Magriba suka tafi suna ta tsokanar ta wai kar Ango ya dawo ya same su ya yi musu korar kare, ita dai murmurshin yaƙe kawai take, sai ta ji dama kar su tafi. Ba ta zauna ba sai da ta tsaftace gidan ta saka turaren wuta a burner, hakan ya sa gidan gabaɗaya ya karaɗe da ƙamshi. Bayan ta yi Sallah ta yi wanka ta shirya cikin wani tsadadden yadi mai kyau maroon color, ya yi mata sosai ya haska farar fatarta. Parlour ta fita ta jera abinci akan dinning sannan ta koma ta yi Sallar Isha'i da aka fara kira. Tana idarwa ta janyo wayarta dan ta kira Abbi amma ta tarar wayar a kashe, ta manta tun jiya wayar babu chaji ta mutu. Chajin ta jona ta zauna jiran ya ɗan yi, Salman ne ya faɗo mata a rai. A fili ta ce. "Kana ina My Faris? Me kake yi yanzu? Me ya sa ba ka kira ni ba tunda ka tafi? Yaushe zaka dawo ka zo gidana in gan ka ɗan ƙanina? Na yi tsananin kewar ka." Daga haka ta fashe da kuka. Khamal na zaune a parlour'nsa shi da Na'ima wadda zuciyarta ke cike da tsananin farinciki, jin ta take kamar a mafarki yau Allah ya yi Abra ta bar mata gida, shikenan fargabarta ta ƙare. Sai dai tuno letter Salman da ta gani ya sa gabanta fad'uwa da ƙarfi, ta rasa me ya sa abun ya dame ta? Dan da farko shirme ta ɗauki abun, saboda sanin komai daren daɗewa dole Salman ya neme su, ba kuma zai taɓa iya yin zuciya da su ba, letter da ya yi mata dan yana cikin ɓacin rai ne, abun yana cin shi a lokacin shi ya sa, amma ta san idan tafiya ta yi tafiya komai zai wuce. Khamal yana duban ta ya ce. "Komai lokaci ne, kamar ba yau ake zancen bikin Daughter ba, ga shi har an yi an gama, ta tafi ta bar mu da kewar ta. Cikin kissa Na'ima ta ce. "Ta bar mu da kewa kam, don gidan babu daɗi yanzu ko kaɗan, ga ba Salman." Khamal ya nisa ya ce. "Har kin tuna mini kuwa, na kai sati ina trying his number ba ta shiga, amma na kira mutumin da ya kira ni da numbern shi lokacin da ya sauka a garin, ya ce mini neighbours suke, idan sun haɗu zai kira ni ya haɗa mu." Murmushi Na'ima ta yi ta ce. "Allah Sarki yaron kirki, Allah ya tsare mana shi." Khamal ya amsa da Amin tare da zaro wayarsa daga aljihu ya kira layin Abra amma sai aka ce masa a kashe, tun rana yake kira ta ba ta shiga. Numbern Adnan ya kira, dan ya san duk sabon ango i yanzu yana gida. Bayan ya ɗaga suka gaisa cikin mutuntawa, Khamal ya tambayi Abra, Adnan ya tabbatar masa tana nan ƙalau, wayarta kuma babu caji ne shi ya sa bai same ta. Khamal ya buƙaci Adnan ya ba wa Abra wayar, sai ya ce ya ɗan fita, idan ya koma gidan zai haɗa su, daga haka suka yi sallama. Tana zaune takure a bakin gado ta yi tsumu cikin alamun tsoro, ita kaɗai a gida har tara ta yi amma babu Adnan babu labarin shi. Ƙwaƙwalwarta har ta gaji da tunanin dalilin da ya sa Adnan yake yi mata haka, kanta kamar zai tsage saboda ciwo. Unexpected ta ji an buɗo ƙofar ɗakin an shigo, lumshe ido ta yi cikin jin daɗi dalilin shaƙar ƙamshinsa, a hankali ta buɗe idonta ta kalle shi, yanda ta ga ya murtuke fuska ne ya sa gabanta mummunar faɗuwa, amma duk da haka ta daure cikin raunin murya ta ce. "Sannu da zuwa." Ta ƙarashe maganar hawayen da take ƙoƙarin ɓoyewa suna zubo wa. Bai kula ta ba, wayarta dake chaji kawai ya ɗauka ya fice. Da ido ta bi shi cikin kokawa da numfashinta dake barazanar ɗaukewa. Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un ta shiga maimaitawa hannunta dafe da kanta, wani irin raɗaɗi da zafi take ji a cikin zuciyarta. Tambayar kanta ta shiga yi, dama haka Auren yake? Ko kuma ita kaɗai ta fara da matsala? Ina tarin ƙauna da soyayyar da Adnan yake yi mata? Ina tanadin kulawa da tattalin da ya ce ya mata? Ko dai mafarki take yi? Ta rasa da wanne za ta ji, da rashin Faris a kusa da ita ko kuma da kewar su Abbi ko da abun da Adnan yake mata? Sunan Allah ta dinga ambata har ta ji sauƙin radad'in da zuciyarta ke mata. So take ta tashi ta je gurin Adnan ta ji me ta yi me masa? Amma a yanda take jin jikinta kamar ba nata ba ta san ba za ta iya tashi ba. Kwanciya ta yi saboda juyawar da kanta yake yi mata. Wannan shi ne dare mai tsayi da muni da Abra ta gani a rayuwarta, dan bacci duk iya satarsa bai sace ta ba. Nasihar Ammi da ta ce ta dinga tashi cikin dare tana yin Sallah ko raka'a biyu ce ta dawo cikin kwanyarta, hakan ya sa ta lallaɓa ta tashi ta shiga toilet ta ɗaure alwala ta raya daren, ta kai wa Ubangiji kukanta tare da roƙon ya kawo mata ɗauki. Bayan an yi Sallar Asuba ta ɗauko alƙur'ani mai girma ta karanta, bayan ta gama ta yi azkar ɗinta. Hakan ya sa ta ji sauƙin damuwar dake cunkushe a cikin ranta. Sai kusan takwas ta fita parlour bayan ta yi wanka. Gyaran gidan ta fara yi cikin matuƙar sanyin jiki, tana cikin yi Driver'n gidan Hajiya Mama ya kawo breakfast, ta karɓa ta yi masa godiya ta kai dinning ta ajiye. Tana zaune har 10 tana jiran fitowar Adnan amma shiru ko motsinsa ba ta ji ba. Wasa-wasa yau har Magriba ba ta ɗora Adnan a idonta ba, sauƙinta yau ma ta yi baƙi har sau biyu sun ɗebe mata kewa. Sai bayan Magriba ya shigo gidan, lokacin tana zaune a parlour ta kunna kallo, a ƙoƙarinta na son ya ɗebe mata kewa, sai dai damuwar dake cikin ranta ta hana ta gane me firlm ɗin ma ya ƙunsa. Duk yanda yunwa da ƙishirwar son ganin shi suka cika mata zuciya amma sai ta kasa ɗaga ido ta kalle shi, ƙasa ta yi kanta tana sauraren yanda zuciyarta ke bugawa. Karon farko tun bayan da aka kawo ta, ta ji muryarsa ya yi mata sallama, sai dai ba a yanda ta so jin maganar tasa ta ji ba, ba cikin soyayya da kulawa ba. Fuskarsa a murtuke tamkar aka yiwa saƙon mutuwa, cikin isa da gadara kamar an masa dole ya ce. "Je ki ɗauko hijabinki." A hankali ta ɗago ta dube shi idanunta cike da ƙwalla, kafin ta kai ga yin magana ya juya ya shige ɗakinsa. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka ta miƙe ta je ta ɗauko hijabin ta saka, tana cikin kashe kayan kallon ya fito daga ɗakinsa ya yi hanyar waje ba tare da ya kalli inda take ba. Bin bayansa ta yi cikin sanyin jiki tana sharar hawaye. Ganin ya shiga Motor ta buɗe front seat ta shiga, wai mugun kallo ya watsa mata tare da faɗin. "Kar ki bari na ƙara ganin wani abu mai kama da hawaye a fuskarki." Ba ta ce komai ba ta share hawayen tare da lumshe idonta. Gidan Hajiya Mama suka je. Abba da Hajiya Mama sun karɓe ta cikin fara'a da soyayya, sai nan-nan suke da ita. Ita kam kanta na ƙasa kunya duk ta ishe ta, idan an yi magana sai dai kawai ta murmusa. Adnan kuwa sai shagwaɓa yake musu wai yanzu sun daina son shi Abra suke so. Abun da ya ba wa Abra mamaki yanda ya dinga yi mata magana cikin kulawa da sakin fuska a gabansu Abba, hakan ya jefa ta cikin tunanin me Adnan yake nufi da ita? A nan suka yi dinner tare da su Abba, tun tana jin kunyar su har ta ɗan ware, saboda su babu ruwansu, musamman Abba he is so friendly, yanata jan ta da hira. Sai ta ji dama Adnan ɗinta ne haka. Hajiya Mama ta lura da yanayin Abra kamar wani abu yana damun ta, idanuwanta ma sun nuna alamun ta yi kuka. Ba ta yi tunanin komai game da hakan ba, sai ta alaƙanta hakan da kewar gida take yi da kuma rashin sabo na mu'amalar Aure. Kafin su tafi Adnan ya sanar da su zai yi tafiya zuwa Abuja akan wani muhimmin aiki da ya taso masa, za su tafi tare da Abra. Addu'a fatan isa lafiya sukai musu. Sai wajen 10 suka dawo gida. Bai ko kalle ta ba bayan ya yi parking ya buɗe Motar ya fice. Bin bayansa ta yi kallo cikin wani irin yanayi na ƙuncin zuciya. Ajiyar zuciya ta sauke tare da buɗe Motar ta fita. Tun daga lokacin ba ta ƙara saka shi a idonta ba sai washegari bayan Sallar Asuba ya shigo ɗakinta. Time ɗin tana karatun Alkur'ani, bayan ta kai ajiye ta rufe tare da gaishe shi cikin girmamawa. Bai amsa mata ba sai bin ta da wani wulaƙantaccen kallo da ya yi. Cikin ƙaunshin murya ya ce. "Zan yi tafiya yanzu, ba na zo kuma dan in sanar miki ba ne saboda ba ki kai wannan matsayin ba a gurina, na zo in ja miki warning ne akan ko da wasa kar wani ya ji labarin ba da ke na yi tafiyar ba, idan kunne ya ji jiki ya tsira." Ya ƙarashe maganar tare da jan tsaki. Cikin kukan da ya taho mata ta ce. "Dan Allah kar ka tafi ka bar ni, ni kaɗai, wallahi tsoro nake ji." "Abun da kike jin tsoron ya kashe shi." Ya faɗi haka tare da juyawa da niyyar ficewa." "Please where is my phone, ka dawo mini da ita Dan Allah." Ta faɗa cikin matsanancin kuka. Ko juyowa bai yi ba ya yi ficewarsa abunsa. Kifa kanta ta yi akan cinyoyinta ta shiga rera kuka mai ban tausayi. Why Adnan? Me nake yi maka da ka zaɓi mu yi irin wannan rayuwar mai cike da ƙunci da damuwa? Ya Allah ka kawo mini ɗauki akan sabon babin ƙaddarata da ya buɗe, Allah ka sassauta mini. Abun da take faɗa a ranta kenan cikin tsantsar damuwa. Yau kwana biyar da kai Abra gidanta, wadda waɗannan kwanakin suka kasance kwanaki mafi muni da tsaho a cikin rayuwarta. Gabaɗaya ta rame ta fita daga hayyacinta, ga babu waya balle ta kira su Abbi ko ta ji sauƙi a cikin ranta, ga kewar Salman da kullum ƙara yawaita take a cikin zuciyarta. Alkur'ani shi ya zamto abokin hirar ta akodayaushe, sai kuka da kullum sai ta yi shi ba adadi. Misalin ƙarfe goma sha biyu na rana tana kwance a parlour akan carpet, idanunta a lumshe hawaye na zirara ta ƙasansu. Tana jin yanda cikinta yake ta ƙugin yunwa amma ta kasa tashi ta samar wa kanta abin da za ta ci, ga wani azababben ciwon kai da ya aure ta, kullum da shi take kwana take tashi. Kamar a mafarki ta ji an buɗe ƙofar parlour'n an shigo, ko ba a faɗa mata ta san Adnan ne ya dawo, saboda da zai tafi ya kulle ƙofar parlour'n ta waje, ta gane hakan ne a lokuta da dama da ta yi yunk'urin fita harabar gidan ko za ta ga abun da zai ɗebe mata kewa damuwar zuciyarta ta ragu. Ko matsawa ba ta yi ba da niyyar tarɓar shi, sanin da ta yi ko ta masa magana ba amsawa zai yi ba. Sai dai jin kamar ba shi kaɗai ya shigo ba ya sa ta buɗe idonta da sauri tare da goge hawayen fuskarta ta tashi zaune. Abun da ta yi tozali da shi ne ya sa numfashinta ɗaukewa na wucen gadi. Adnan ne tare da wata mace wadda kallo ɗaya za kai mata ka gane ƴar duniya ce ta ƙarshe, duba da yanayin shigar jikinta da uban bleaching ɗin da ta ci, ga kitson attachment a kanta gami da gashin ido maƙale a saman idanunta. Wannan duk ba shi ne abun da ya fi ɗagawa Abra hankali ba, jakar matar da Adnan ya riƙo a hannunsa da kallon da yake jifan ta da shi mai nuni da tsantsar soyayya, a ƙarshe kuma ya tsugunna yana cire mata hill shoe ɗin dake ƙafarta. Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 09047871750 or 08081012143. [10/12, 7:18 PM] Abk: Mugun ganin da Abra ta yi, ya sanya ƙirjinta fara ɗa gawa zuciyarta tai mata nauyi. Rutse idanunta ta sakeyi tana ganin abin kamar almara, amma ta hana Zuciyarta gasgata abin da ta ke raya mata. A hankali ta yi ƙasa da kanta ta shiga wasa da yatsun hannunta, jikinta duk rawa ya ke, ji ta ke kamar zuciyarta tai bindiga sbd fargaba. Juyawa Adnan ya yi tare da kallon budurwar ta ke tsaye a gefensa, cikin nutsuwa ya sakar mata wani kwantaccen Murmushi mai nakar da zuciyar ko wacce ƴar mace. Fari ta yi masa da idanu tana girgiza ƙirji ganin hakan ya sanya Adnan, janye nasa idon ya lumshe kafin a hankali ya ce "My Surry" kashe murya wacce aka kira da Surry ta yi ta na shafa fuskar Adnan ta ce. "Darling bee" Hannunsa ya watsa yana ƙare mata kallo tare da ɗan matsawa kusa da ita he's trying to kiss her cheeks sai kuma ya ɗaga mata gira ya ce. "Finally Bibina this is my house" "It's beautiful I like it but" hannunta ya kama ya ce "but what? Say it" rungomesa ta yi sosai ta ce "isn't ur house is our house okay" holding nata back yai ya ce "Oh! I almost frgt sbd ke ma na gina gidan". "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" sune kalaman da suka fita da ga cikin bakin Abra a wahale. Ta kasa fahimta, ta kuma kasa gane inda kalaman mijin nata ya dosa "My Surry? Bibina? Our house? What does that means?" Idanunta da suka sauya kala da ga farin da suke da shi zuwa launin jaa ta buɗe da ƙyar tare da zuba musu idanu. Frm Head to toe ta ke kallon wacce aka kira da Surry, a ƙalla zasu iya age mate da Adnan idan ma zai girmeta sai da shekara ɗaya ko watanni, daurewa ta yi cikin sassauta muryarta tare da ɗauke damuwar da ke zuciyarta, but under her heart sunan Allah kawai ta ke kira, wasu har ƙwace mata suke. Kusa da Adnan ta ja ta tsaya idanunta akan Fuskar sa, shi kuma yana kallon Surry. "Sannu da hanya" shirun da ta ji ne ya sanya ta ƙara cewa "Wlcm Bebbb" dry Surry ta yi kafin ta kalli Abra sai kuma ta kalli Adnan ta ce "Bebbb ana kira" haɗe fuska ya yi sosai ba tare da ya ce komai ba. "Is she your wife?" "Waa?" Da hannu ta nuna masa Abra ta ce "I think tana buƙatar ka" "Kin taɓa ganin wuta da ruwa sun haɗu?" Surry ta ce "A'a never" juyawa ya yi gaba ɗaya wajan Abra a hankali ya ja idanunsa ya lumshe kafin ya buɗe a nuste ya kai kallonsa ga fararen yatsun hannun ta wanda suka sha henna sai ɗaukan idanu suke, dugun wuyan ta maƙale da wata siririyar necklace mai ɗauke da red ɗin stone. Jajayen laɓɓan ta wanda suke rawa da karkarwa sbd tsananin tsoro da kuma abin da zai iya zuwa ya dawo. "Idan har wuta da ruwa ba zasu haɗu ba, ta ya ya ki ke tunanin zan iya kiran maid ina nufin ƴar aikin gidan da matsayin mata? Maid ɗina ce" "Dam!" Zuciyar Abra ta buga a hargitse kuma ta ke duban Adnan muryarta na rawa ta ce "Ni... Ni... ni ce ƴar aikin naka? ina matsayin matar ka mene maka wacece ita?" Ta ƙare maganar tana riƙe ƙirjinta sbd yadda ya ke ɗa ga mata tamkar zuciyarta zata tsaga ƙirjinta ta fito haka ta ke ji, bai ce mata komai ba sai kallon Surry da ya yi ya ce. "Lemme take a shower" tana rangwaɗa tare da juya ƙugu wanda duk shan magani ya fara lalata su ta Ƙarasa wajan Adnan ta na kama hannunsa tare da kwantar da kanta a jikinsa ta ce. "Can I help you?" "Sure Bibi" kama hannunta ya yi suka nufi part ɗin sa, sai da suka nisa Surry ta juya ta kalli Abra ta ce. "Ki haɗa min Indomie with egg ta ji Attahiru" Zubewa Abra ta yi tare da zaman ƴan buri a wajan kamar mahaukaciya haka ta fara kuka tare da kunce ɗaurin kanta tana hargitsa kanta, ko idanunta bata iya buɗewa sbd nauyin da Zuciyarta ta yi mata, a wahale ta riƙe ƙirjinta da hannu bibbiyu ta na ƙoƙarin hanasa ɗagawa, sbd ji ta ke tamkar ranta zai fita idan numfashinta ya shiga tare da ɗagawar ƙirjinta. Tun tana addu'a har ta kasa faɗin komai sai idanunta dake lumshewa bakinta na rawa a hankali ta sulale ƙasan carpet kamar sumammiyya. Saukar ruwan mai tsananin sanyi a jikinta shi ne suka taimaka wajan farfaɗo da numfashinta wanda ya bar jikinta, kafin dawowa cikin hayyacinta taji saukar wani ruwan a jikinta wanda yafi na baya sanyi tamkar wanda ya ke ɗauke da ice sbd sanyi. Jikinta na kyarma da ɓari ta buɗe idanunta a tsaye ta gansa da ga shi sai farar Armless da 3Qauter sai ƙamshin Pur oud, Kallon sa ta ke kafin ta ce. "Ka dubi girman Allah ka faɗa min abin da nai maka, bana da kowa a nan kai kawai na sani mene yasa zaka juya min baya a lokacin da nake tsanin buƙatar ka? Ka ɗauke min dukkan wani farin ciki da jin daɗina ta hanyar nuna rashin kulawa a gareni, kada ka manta a ni amana ce a gareka,ka faɗa min abin da nai maka nayi maka Al'ƙawarin zan gyara kuma na baka hqr" ta faɗa tana sakin kuka tare da kallon sa ta na haɗe hannaye waje guda alamar roƙo. Kallon tsaf ya yi mata kamar ba zai magana ba, sai kuma ya ce "Ina girkin da sweetheart ta ce ki mata? Ko kin mata aikin ki ne?" Miƙewa ta yi tsaye zuciyarta na yi mata zafi, wani irin kishi ya rufeta har bata san lokacin da ta wurgawa Surry uwar harara ba. Da sauri kuma ta juya zata shige part ɗin ta. "Idan har kika bar parlourn nan wallahi na lahira zai fiki jin daɗi Abra Khamal Khamis" Cak Abra ta tsaya ba tare da ta kallesa ba, a wannan lokacin ba komai ta ke ganewa ba, ji ta ke inama ba zai auren ba, an faɗa mata daɗin aure an kuma faɗa mata duk soyayyar dake tsakani wata rana ana samun saɓani domin ko harshe da haƙori ana sabawa, balle mutum mai ɗauke da Zuciya wacce jiki ke gudana a cikinta. Sai dai tunaninta ya samu tawaya ta wannan ɓangaren, babu abu mai muhimmancin kamar daren farko na rayuwar ma'aurata amma ita nata daren ya zo mata a yadda ba tai tunani ba, ta kasan fahimtar Dare da duhun da ke cikin al'amarin. Wanne al'amarin ya ke shirin faruwa acikin rayuwarta dama duniyar ta baki ɗaya?. DESTINY. Wata zuciyar ta ce. "Ƙaddara ta ki har nawa ne? U have to think Abra, think think think.... Ta tashi cikin rashin kulawar uwa, ta girma da ƙaunar ƙarninta farin cikin ta, lokaci ɗaya ƙaddara tai mata kutse cikin rayuwarsu aka rabata da jinin jikinta Faris, ta ɗauki ƙaddara ganin yadda Adnan ke nuna mata kulawa tare da yi mata Al'ƙawari kala-kala, hakan duk a cikin tsarin ƙaddarorinta suke? Ko kuma wani abun ke son faruwa ne?... Wani abu mai kama da JUYAYI. "Heyyy You jakanesss" Muryar Sp Adnan Aliyu Matawalle ya sauka a kunnanta a gigice ta dawo hayyacinta duk ba sosai ta jisa ba, hannunta na rawa ta taɓa kunnanta sai a lokacin ta ji hearing aid ɗin ne ya goce. "20mints ya yi maki yawa wajan kawo sweetheart ɗina abinci" zaman hearing aid ta gyara idanunta cike da hawaye ta kallesa ba tare da ta ce komai ba. "I'm i your mate da ina magana kika zuba idanu ko matar amarci ke damunki ki ke son cinye ni eye?" Murmushi kawai ta yi irin Murmushi da gwanda mutum ya yi kuka akan ya yi irinsa. "Idan kai zanwa zan yi, it's my responsibility nauyin ka yana kai na, amma ba zan taɓa yiwa karuwar can abinci ta ci ba....," "Kauuu!! Kauuuu!!!" Ya sauke mata wasu tagwayen maruka kamar kumurciu zaki haka ya ke huci idanunsa akanta ya ce. "How dare you da zaki faɗa min haka Ehh? Kada ki dama idan kin amsa Sunan Abra Khamal Khamis kiga, and wannan da kike maganar karuwa ko....?" Ƙwafa ya yi tare da juyawa ya kama hannun Surry suka shige ɗakinsa sai maƙale jikinsa ta ke tana sakin kuka ance mata karuwa. Dafe kanta da ke juyawa mata tayi, da ƙyar ta ja ƙafafuwanta zuwa kicthen domin ko ta kansa bata sani ba, ganin da akwai komai ta ɗauki Onion da red pepper ta ɗauki Egg da Indomie, tana aiki tana tana sakin ajjiyar zuciya, ga jiri dake ɗaukanta. "Yaya.. Angel Zanci Indomie Yaya please yunwa na keji" "Yaya gidan wani zaki,kina gwarara jikin ki" "Angel waya saki aiki, ba Abbi ya ce ki daina aiki ba" Ajjiyar zuciya ta sauke sbd wuƙar data ya ke. "My Angel kalli hannunki kin yanke, matsa zan yi aiki jeki zauna" "I love You Angel wannan girki kamar a restaurant" "Idan ban kula dake ba, waye zai kula dake ni ki daina ɗauka na matsayin ƙani kawai Yaya Angel" Wani Uban Ihu Abra ta fasa lokacin da maganar Salman ɗaya-ɗaya ta shiga dawowa cikin kwakwalwarta tamkar yanzu ne muryarsa ke mata kuuwa a cikin kunnanta. sai da tayi kuka mai cin rai tana kiran sunan Salmanun-faris come to back to me zan bika duk inda zaka. Plate ɗin Indomie ta ɗauka, a Parlour ta samesu suna kallo da sauri ta ajjiye plate ɗin jikinta na rawa tabar parlourn sai numfashi ta ke fitarwa, har dare bata sake fitowa bata da tabbacin a gidan suka kwana ko a waje?. China. A hankali ya ke tafiya kansa a ƙasa, hannunsa duk biyun zube cikin Aljihu, da ga shi sai wata ƙaramar black t.shirt wacce ta kama jikinsa, sai ƙaramin wando mai kama da trousers. Ƙafarsa sanye cikin wani baƙin takalmi me kyau. Gefen wani kogi ya ja ya tsaya inda ake shan iska ga few mutane a wajan kowa yana abin da ya ke gabansa. Iskar data kaɗa ya sa shi rufe idanu tare da zame hannunsa guda ɗaya ya ɗora daidai saitin ƙahon zuciyarsa "fat! fat!! fat!!" Haka sautin bugawar ta ke badawa, idanunsa ya ware akan ruwan tare da ƙurawa wasu tattabaro idanu farare tas dasu mace dana miji, irin tattabaron nan ne masu kama da ɗawisu sun ɗaga jela sama tai wani scale kamar zanan love Wayarsa ya ɗauka tare da ɗaukan su a taushashe ya ce. "With my heart desires my dream" idanunsa ya ɗan sauya kala kamar zai kuka hawaye kwance a idanunsa ya ƙara sakin Murmushi a karo na biyu "happy married life Angel stay blessings with your husband not ur choice" Salman Khamal Khamis kenan, yaro mai mafarki wanda lokaci guda zanan ƙaddara ya rusa masa mafarkin. Yasa ko wacce kala rayuwa zai a yanzu zai yi ne kara zube ba tare da farin ciki ba, she tooks his happiness ta ɗauke komai nasa ta tafi da shi, baya jin tana da laifi zurfin ciki ya sanya komai faruwa. Komai jimawa soona or later sai ta zama mallakinsa halaliyyarsa. Kujera ya nema ya zauna yana miƙar da ƙafafuwansa, jikinsa ya yi fresh ya murje but ya rame sai idanunsa da Matashin gemunsa haɗi da saje da suka fara cika fuska sbd sauyin weather ta ƙasa. Washegari. Kasa jurewar yunwar da ke damunta ta yi, a hankali ya dubi agogo 12:44 shi ne abin da Idanunta ya gani, da sauri ta sakko ko sallar wahalar da ta ke bata samu yi ba. Zaman rigar jikinta ta gyara har ta fita sai kuma ta dawo ta ɗauki perfume ya fesa ta gyara fuskarta, a hankali ta zame rolling ɗin kanta, sumar kanta ta sauka har baya, a tunaninta ko hakan zai burgesa duk da bata da tabbacin ko yana ma gidan. "Allahumma ajirni fil musibatii, Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" ta faɗa ta sauri ƙirjinta na bugawa da ƙarfi kafin ta sake motsawa jiri ya kwashi ya kaita ƙasa, kanta ya daki jikin canter na parlourn. Ba ita ba shi kansa sai da ya ji kunyar yadda ta samesa tare da Surry, amma sai ya zame ko a jikinsa. Ta jima durƙoshe ko idanu ta kasa buɗewa sai duhu da ta ke gani kamar mai hawan jini. Sunayen Allah ta ke faɗa babu saurarawa, a hankali ta ɗauko tare da ƙara duban Surry wacce ke kwance jikin Adnan tana shafa gashin ƙirjinsa wanda da alama bai daɗe da yin wanka ba, ko ita bata samu damar yin haka ba, amma wata banza ce kwance jikin mijinta. Abin ka dame haƙuri wanda idan ya ta shi abu bai iya yinsa ba. Duk da jirin da ke ɗau kanta haka tai kan Surry kamar mahaukaciya, yadda ta nufi Surry zaka ɗauka aljanu gareta. Tana zuwa ta damƙi wuyanta tana shaƙeta zafin shaƙar ya sa Surry sakin ƙara. Hankali tashe Adnan ya yi kan Abra zai daka kafin ya ƙarasa Abra ta damƙe ƙirjin Surry wanda ya kewa Adnan iyayi dasu, wani ihu Surry ta kwarara tana faɗin. "Wayyo Allah! Zata tsinka zata tsinka na shiga uku" ganin yadda Adnan yayu kanta gadan-gadan ya sanya ta ƙara fisgar ƙirjin Surry. "Wayyo uwata wayyo wallahi ta tsinka" da gudu Abra ta saki Surry ta koma part ɗin ta. Tun kafin ta ƙarasa jikin gado jikinta ya fara rawa numfashinta ya fara fisga kamar mai Asthma idanunta rufe ya ɗauki Alkur'ani ta fara karatu da dukkan muryarta wacce ta kusa cika part ɗinta dana Adnan Aliyu Matawalle ɗin. A karatu ta ke da iya ƙarfinta tun tana yi da ƙarfi har numfashinta ya kasa jurewa, a hankali tai gaba tare da kifawa muryarta a sanyaye ta ce. "Ka gani ko Faris?" Cak kuma Numfashinsa ya tsaya. A haka rayuwar Adnan da Abra ta kasance tsayin sati biyu tun daga ranar kuma bata sake saka shi cikin idanunta ba. Mami damuwa tai mata Abbi ya tsallake ya barta, babu Salman ɗan da ake tutiyya da shi kullum gida shiru kamar mayya lokaci zuwa lokaci kewar Abra na damunta ko za ta ce za kici Ubanki Abra yau ta ji zamanta na ɗauke mata kewa. Faris baya nemanta wani time ɗin ta kira number Abra sai ace a kashe. Cikin sati na uku mafarin faruwar komai tare da toshe da kuma asalin abin da zuciya ke ɗauke da shi, mafarin rusa farin cikin wasu. Iddar da sallarta kenan ta nufi bathroom tare da yin wanka, a hankali ta fito da ga cikin toilet ɗin ɗaure da ƙaramin towel wanda ya tsaya iya cinya ruwa na zuba a jikinta, ga gyaran jikin nan nata yana nan fata sai glowing ta ke. Tana cikin tsane jikinta ta ji an murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin kafin ta motsa ya shigo cikin bedroom ɗin, a hankali ya ke binta da kallo kamar wanda baya cikin hayyacinsa, hannunsa dafe da cikinsa wanda ya ke masa matsanancin ciwo har idanunsa sai da suka nuna alamar hakan. Fararen ƙafarta yabi da kallo zuwa hips ɗinta kana ya maida kallonsa zuwa sama. Kamar wanda ake fisga da mayan ƙarfe haka ya nufi inda ta ke, tsoran yanayinsa ya sanya Abra fara yin baya tare da ɗaga ƙafa zata gudu, domin tunaninta dukanta zai. Gaba ɗaya ta jita male-male a saman ƙirjinsa ya rungome ta tare da bata ƙyakkyawan ma sauki a ƙirjinsa. Bai zo da niyyar hakan ba amma gaba ɗaya a kallon farko tunaninsa ya tsaya, cikin ƙaramin lokacin abubuwa da suka faru suka zama abu mai matuƙar baƙin ciki a rayuwar Abra Khamal Khamis, domin babu imani cikin lamarin Adnan bata taɓa tunanin haka al'amarin ya ke ba, bai saurara mata bai nuna mata soyayya kulawa tare da tattali ba, bai barta ba sai daya tabbatar da ita matsayin cikakken mace wacce tabi layin saurin mata. Wani zazzafan zazzaɓi ya rufe Abra jikinta sai rawa ya ke, haƙoranta na haɗewa a haka ya tsallake ya barta ya nufi nasa Part ɗin yana jin ciwon cikin ya lafa sai kansa da zazzaɓi shima daya saukar masa. Duk inda kake tunanin azaba a wannan daren Abra ta shata, sai Subhi ta samu tai wanka tai sallah jiki na rawa ta koma ta kwanta tana jan numfashi, a hankali hawaye ya sakko mata tunanin kiss ɗin Faris ne ya faɗo mata, soyayya da ƙauna haɗi da kulawa sune ta ke gani cikin idanun Salmanun-faris a lokacin da ya ke sumbatar bakinta. Misalin 1:20 ya turo ƙofar ya shigo kamar ma ƙasar zai bari sai dube-dube ya ke alamar abu ya ke nema ko inda ta ke bai kalla ba. A hankali ta sauka da ga gadon ba zato ya ji ta riƙe masa ƙafafuwa tare da ɗora kanta a jikin ƙafar tasa, wani raunataccen kuka ya ƙwace mata cikin kuka ta ce. "Kaji tsoran Allah ka daina azabtar dani da abin da bai san da shi ba,ka faɗa min laifina wallahi zuciyata zata buga,ina Soyayyar da kake min? Ina kulawar da ka ke faɗa min kayi min adaninta ko haka auren ya ke? Don darajar Allah da Manzonsa ka faɗa min abin da nai maka" Kallon ta ya yi sai kawai ya juya zai fita da sauri ta ce. "Matar ka ce ni, har lahira da ke zanyi alfahari bani da kamarka a yanzu kai ne duniya ta, kai ne dangina kai ne komai nawa, ba danni ba ba dan na isa ba ka faɗa min abin da nai maka na san kana so na" Murmushi ya yi tare da sunkuyawa ya ɗagota zuwa tsaye cije baki tayi sbd zafin da ta keji ko tsaiwa bata iyawa. Shoulder ɗinta ya riƙe tare da matsawa ya ce. "You deceived yourself Abra Khamal Khamis, Adnan Aliyu Matawalle bai taɓa sonki ba, kuma bai taɓa sonki ba, infact mujiya ki ke a cikin idanuna" girgiza kai tayi bakinta na rawa ta ce "what... what do you mean by that? baka so na kake cewa" hannunsa ya sanya ya tallafo fuskarta ya ce. "Idan baƙin maciji ya sareki ina da tabbacin ki kaga baƙar leda cewa zaki shine, wallahi da naga fuskarki gwara na kalli mujiya, a duk lokacin da naji muryar ki ji nake kamar ana zuba min ruwan dalma a zuciya, idan kina kusa dani kowa ji nake kamar na saka hannu na shaƙeƙi na huta, babu abin da na tsana a duniya kamarki bana Sonki bana Sonki bana Sonki na tsaneki kamar yadda bana ƙaunar mutuwa ta a yanzu" baya Abra ta yi kamar zata faɗi tana riƙe ƙirjinta ɗakin ne ya shiga juyawa mata wani duhu na mamaye cikin idanunta gyara zaman hearing aid ɗin ta yi ko tunaninta ita ce bata ji daidai ba. "Baka so na mene yasa ka aureni?" "To take a revenge" "Revenge? Me na yi maka ni? mene aikata maka da har zaka ɗauki Revenge akai na?" Murmushi ya yi kafin ya ce "Baki min komai ba, laifin da Ubanki ya yi min shi ne ya sanya zan ɗauki Revenge akanki, zan raba shi da farin cikin sa kamar yadda ya zama silar lalacewar nawa, ba zan taɓa yafe masa ba sai na tabbatar yaji Abin da naji this is my promise" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wacce rana ce wannan me ya ke son faruwa da ita? Rarrafawa ta yi zuwa inda ya ke tana riƙe ƙafarsa ta ce "Me Abbina ya yi maka? Wallahi Abbina ba zai taɓa cutar da wani ba, idan ma ya yi sai dai kuskure kada ka cutar dani don girma Allah ban san komai ba" gyara tsaiwa Adnan ya yi ya ce "Ba muriƙinki nake magana ba, ba Abbinki ba Uba maifi wanda ya yi silar zuwanki duniya" "Abbine mahaifina bana da wani Uba sai shi shi ne mahaifina" dry Adnan ya sake yi kafin ya ce "Abra Khamal Khamis? To ba haka sunan naki ya ke ba, ke TSINTACCIYA ce, tsintar ki Abbi ya yi acikin jeji ya ɗauki tare da baki kulawa kamar ƴar cikinki, kuma ke ɗin bawai Shegiya bace mugun Ubanki shi ne yaja baki yadda ya rabani da farin ciki shima sai na raba shi da shi, zan ɗauki fansar abin da ya yi min akanki *REVENGE MARRIED* Sunan aurenmu" "bana da wani Uba wanda ya shige Abbi kai ma ka sani" hannunsa ya tsawa ya ce "bance ki yarda ba, amma ni da Abbin naki musan cewa ke ba ƴarsa bace kiyi tunani kaf dangin ku dawa ki ke kama? Just think bance ki yarda ba, amma zaki rayu a gidan nan tamkar baiwa!" [10/13, 11:29 AM] Abk: Jiki na rawa, Khairy ta kira Mami tana salati tana salallami, Mami ta ɗaga wayar ta ce "Ya aka yi? Ta na ina ne, mutane sun fara taruwa fa?". Khairy murya na rawa ta ce "Mami na kira mai kwalliyar ta ce mini tun uku, aka gama kwalliyar, kuma ta tafi". Mami ta ce "Ta tafi taje ina?" "Mami Wallahi ban sani ba, ba guri ɗaya muka je kwalliyar da ita ba, ni gurin da naje daban". Mami ta ajiye waya tana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yarinyar nan gidan ubanwa ta tafi ne? Ace an gama kwalliya tun uku amma har haɗu da rabi ba ta iso gida ba, ga mutane sun fara taruwa". Anty suwaiba ta ce"Allah yasa ba guduwa ta yi ba". Mami ta zare ido ta ce "Ta gudu ta je gidan uban wa? Lallai ma yarinyar nan". Abu kamar wasa, ba Abra babu dalilinta, tun ana maganar ƙasa_ƙasa, har mutane suka fara jin halin da ake ciki. Abokan aikin Adnan ne, suke ta shiri cikin shigarsu ta police, domin dai za'a yi parrate na ban girma ga Adnan da amarayarsa. Usman ne ya kalli Adnan da ke ta haɗe rai ya ce "Wai haɗe ran me kake ne?". Adnan ya ce "Am jealous ne, duk wannan garadan sai kun je kun kalle mini mata". Aminu ya ce "Kai dalla ware, ai kaima gardin ne, sai kace a kanka aka fara Aure, ko da yake tsiyar mutum ya zama tuzuru kenan, duk sai ya fara behaving abnormal". "Meye banbancina da kai? Har gara ma ni yanzu zan shige daga ciki, kai kana waje". "Nima ina hanya ne" Usman yayi Maganar yana murmushi. Daga haka suka kammala shirinsu, suka fara haramar tafiya gidansu Abra. Granny ce ta shiga sashin Na'ima tana faɗin "Ke Na'ima, wai wace Maganar banza nake ji ne? Wai kamar Ana Abra ta ɓata, gidan ubanwa ki kai ta?" "Haba granny, Ina kuwa zan Kai ta, daga zuwa kwalliya ba ta dawo ba". "Ƙarya ki keyi, ana Magana kina wani ƙifta ido kamar ta Allah, ki fito da yarinyar nan duk in da ki ka kaita, kan in samo madoki in shemeki a gurin nan". Ammi ce ta ce "Granny ki yi haƙuri, ya za'ayi ta aikata haka ga 'yar ta, Yanzu dai muyi ta addu'a, kuma a kira shi angon a sanar masa dan a san abun yi". Granny ta ce "Wai ke Yaushe zaki gane kan makircin wannan yarinyar ne? Ai duk abun da akace tayi babu mamaki, yau duk abun da za'ayi sai an nemo mini jikata. Amm ke nace ina tabarau na ne? in ƙarewa wannan mara Kunyar kallo, in kalli idanunta sosai, dan ni idan na kalli idon mara gaskiya ina gane shi". Ammi ta ce "Glass ɗinki yana in da ki ka yi salla, amma dan Allah ki dena wannan maganganun, bari a san abunyi, ko a tura wasu gurin mai kwalliyar". Na'ima kuwa iya ƙuluwa ta ƙulu, ji take kamar ta rufe Granny da duka, shegiyar tsohuwa hayyataciya, sai tsawon rai kamar dabino, ta ƙi mutuwa kuma kullum cikin rikici take, tsawon shekarun da Na'ima tayi tare da Khamal Granny ba ta ƙaunarta sam. Gida ya rikice ana neman Abra, ita kuma Granny ta rikice tana neman tabarau, ta ɗora da masifar cewa bayan sace Abra da Na'ima tayi, ta kuma sace mata glashinta, saboda baƙin hali. Anty Suwaiba ta ce "Wai ke Na'ima ba wani mataki da zaki ɗauka a kan wannan sokuwar tsohuwar, shegen surutun tsiya kamar an jefeta a ka?". "To ni ya zan yi da ita? Wannan kaidinta ya fi yadda kike tunani, yanzun nan za ta ƙullawa mutum sharri. Ɗakin Salman Granny ta nufa, tana cigaba da zage Na'ima, Ammi ta ce "Granny me zaki yi a nan kuma?". "Tabarau na nake nema". "To mai ze kai glass ɗinki nan kuma? Na ga tunda muka zo baki je nan ba". "A'a, ance idan raƙuminka ya ɓata ka neme shi har kura tandu, yo na sani ko wannan algungumar ta yi garkuwa shi ta kai ta ɓoye" ta ƙarasa Maganar, tana nufar ɗakin Salman. Sai dai tana shiga ɗakin, ta ƙwala uban ihun da ya janyo hankalin 'yan biki. "Gata nan ku zo gata!" Ta yi maganar cikin ihu. Su Ammi na zuwa, suka tarar da Abra a zaune, fuskarta sharkaf hawaye. Ashe tun bai fi uku da rabi ta dawo gida ba, ta shiga ta ƙofar baya, tabi ta kitchen ta shige ɗakin Salman abunta, kuma ta kashe wayoyinta. Ammi ta ce "Abra, dama kina nan ki ka ɗagawa mutane hankali? Kuma kalli duk kin fara ɓata kwalliyar". Cikin kuka Abra ta ce "Ammi Faris ɗina, zan yi Aure baya nan, dan Allah Ammi kice musu na fasa Auren nan a dawo mini da Faris ɗina". N'a'ima a fusace ta ce "wannan wane irin sakarci ne haka Abra? Mun tara mutane kina neman ki bamu Kunya? Kawai kin ɗagawa mutane hankali". "Mami ni bana son Auren nan na fasa, dan girman Allah Ku dawo mini da ɗan uwana" tayi maganar tana ƙoƙarin cire ɗaurin kanta, ga numfashinta da ya fara sama. Ammi ta girgiza wa Na'ima kai, alamar ta dena yiwa Abra faɗa. Granny ta ce "Ji min 'ya da wauta, ke yanzu sai ki fasa Auren, aikuwa da kin yiwa kanki kutunguilar tsiya, hmm jiya ba yau ba tsohuwa ta tuna kwanan turaka, yarinya karki cuci kanki" Granny ta yi maganar tana watsa guntun goronta a baki, ta bar ɗakin, murmushi Ammi ta yi, Granny ba ruwanta haka take sakin 'yan maganganunta idan ta raya mata". Ammi ta maida hankalinta kan Abra, ta din ga yi mata Nasiha tana rarrashinta, ƙarshe sai da aka kira Abbi video call, shima yayi ta rarrashinta, Sannan ta haƙura. Aka samo wata mai kwalliyar ta gyara mata kwalliyar da ta fara ɓatawa da hawaye. Na'ima ma haɗawa tayi cikin wani rantsatsten leshi fari da golden, tun daga wuyanta zuwa yatsunta gwal ne. Hakan yayi daidai da ƙarasowar Adnan da da abokansa, haka zalika mota mota na 'yan uwan Adnan ɗin suka hallara a ƙatuwar harabar gidan Major Khamal Khamis, wadda akai matuƙar ƙawatawa. Mami ce da kanta ta kamo hannun Abra ta fito da ita daga cikin gida, duk da kanta a sunkuye yake, ta rufe jikinta da mayafi, amma hakan be hana Adnan tsinkayen farar fatarta da ta sha gyara ba. Nan masu police band suka sauke gangunan su, suka fara bugawa domin gabatar da parrate na ban girma ga Ango sha guɗa Sp Adnan Aliyu Matawalle, da matarsa gimbiya Abra Khamal Khamis, abun na masu ɗamara ne, dan haka parrate ɗin ya ƙayatar matuƙa, tare da crossing sword da aka gabatar duk dan murna ga amarya da ango. A ka zo ɓangaren kamu, a kama amarya ta buɗe fuskarta, ƙanwar Hajiyar Adnan, ta ce sun biya dubu ɗari biyar a buɗe musu fuskar Amarya. Nan wasu suka shiga tafi, yayin da Mami ta ce "ita dubu ɗari biyar yayi kaɗan". Ammi ce tsawatar dan kar ayi halin ƙaranta. Nan aka shiga gudanar da shagali, bayan Abra ta buɗe fuskarta, wanda ba su santa ba, suka dinga jinjina kyawunta, wasu kuma suna gulmar ya za tayi da Adnan, dan da kaɗan ta wuce cikinsa. "Sweetheart,yau ranar farinciki ce, amma ya naga kamar za kiyi kuka?" Adnan ya faɗa a saitin kunnenta. "Wani farinciki bai taɓa riskata, Faris baya kusa da ni ba, sai a wannan lokacin, wannan ne karo na farko, ban taɓa tunanin Faris ba zai kasance da ni ba, Ranar Aurena akan high table, ana mana hotuna da ni da shi da angona ba, sai dai....." Hawaye ne suka fara saukowa da ga idanunta. Da sauri Adnan ya ciro hanky yana share mata ya ce "dan Allah kar ki ɓata mana Wannan Farincikin, ba kowane buri namu ne yake zuwa ya cika a yadda muke so ba, kiyi haƙuri" haka ya rarrasheta, aka kammala event ɗin wannan ranar. Daren ranar, haka Adnan ya kasance da ita a waya, yana cigba da aikin rarrashi. Zuba mata idanunsa yayi yana kallonta, yadda take maye, cike da rashin Sabo, sai tamɓele take ya sakata a gaba kawai yana murmushi, yana zuƙar shisha yana fesar da hayaƙin a cikin iska. Ganin tana ƙoƙarin faɗuwa ne ya sanya shi tashi da sauri ya riƙota yana murmushi "Sweetheart, it seems like you are enjoying the moment" yayi Maganar tare da kissing ɗin goshinta. Kan makeken gadon dake tsakiyar ɗakin ya kaita, ya kwantar da ita, yana shafa dogon gashinta. Gaba ɗaya Meenal ba ta hayyacinta, ba ta tashi farkawa daga mayen da take yi ba, sai bayan magariba. A hankali ta buɗe idanunta ta kalli in da ya idar da salla, ta tashi da sauri ta kalli agogo, a gigice ta ce "Ya a kai na kai wannan lokacin? Me ka bani haka na sha?". "Calm down Baby, kayan caji ne fa kawai" "Kamar yaya kayan caji, lokacin komawata gida tuni ya ƙure, me zanje in ce a gida?" "Haba ke kuwa, kamar ba babbar yarinya ba, da alama fa kin ji daɗin cajin nan da kika yi" Wani gululun baƙin ciki ne ya cunkushe mata zuciya, a gurguje ta tattara kayanta da mukullin motarta, tai waje. Gudu take tamkar zata tashi sama, saboda tsananin tashin hankali, cike da fargaba da zullumi ta shiga cikin gidan, a Falo ta tarar da Mummy tana kaiwa tana komowa, tana ganin Meenal a rikice ta ce "Ke daga gidan ubanwa kike Yanzu?". "Amm...mm..... Mummy da..dama". "Dama me? Gidan ubanwa kika tafi? Ƙarfe nawa yanzu? Kin sanya ya tayar mini da hankali, yanzu haka ya tafi kai report gurin hukuma, akan cewar kin ɓata, ina ki ka je?". Kan Meenal ta bata amsa, sai ga Doctor Bulama ya shigo, yana ganin Meenal rai a ɓace ya ce "Ke! Daga ina kike?" "Ba ko ina". "Daga ina kike?!" Ya sake tambayar cikin tsawa. Rawar baki ta fara yi, amma ta kasa Magana, aikuwa yayi kanta ya shaƙota yana zazzare ido tare da maimaita tambayar daga ina take?" "Haba doctor,ka bita a hankali mana, idan ka illata ta fa, ko ka manta uta kaɗaice da mu?". "Dan ita kaɗaice da mu ba shi ya bata lasisin yin iskancin da ta ga dama ba, gidan wa kika je?". A shaƙe Meenal ta ce "Dan Allah Daddy ka yi haƙuri, ƙawata na bi gidansu, muka tafi gurin biki daga school". "Meyasa baki kira kin gaya mini ba, aka dinga kiran wayarki amma a kashe?". "Nayi kuskure, amma dan Allah kayi haƙuri kar ka kasheni" da Doctor ya ƙyale Meenal, bayan ta sha shaƙar da sai da ta kusa zuwa lahira. Hall ya haɗu iya haɗuwa, Abra ta haɗe cikin wani danƙareren Material, kai da gani ka san ba duk jiki ba, sai jikin 'yar gata. Adnan kuwa gaba ɗaya kishi ne ya mamaye masa zuciya, yadda kowa ke ɗaukar hoton matarsa a waya, shifa wannan taron bidi'ar dan anfi ƙarfinsa ne, amma da babu dalilin da zai sanya ayi wannan taron ana kallon matarsa. MC ne ya kira Amarya, tare da umartar ta da taje ta taho da mamanta. Cikin takun Abra na nutsuwa, taje gaban table ɗin da Hajiya Na'ima take, ta durƙusa ta kamo hannunta zuwa filin rawa. MC ya ce "Ki kalli Mamanki, ki ce nata kin gode, kuma kina sonta" Abra ta kama hannun Hajiya Na'ima, ta kalli idonta murya na rawa ta ce "Thank you very much Mamina, for all you did for me Bani da Abun da zance miki sai Allah ya baki Aljanna maɗaukaiya, and I love You Mamina" ta ƙarasa Maganar tana rungume Na'ima, tare da sakin wani irin kuka mai ban tausayi. Nan dj ya saki waƙar Wayyo Allah mamana, Na'ima ma rungume Abran ta yi tana ɗan dukan bayanta alamar rarrashi. Yayin da ta ɓalle bakin jaka, ta dinga zubawa Abra kuɗi kamar ba gobe, ji take dama Abra 'yar ta ce ta halak, da shagalin da za tayi a bikin nan yafi haka. Haka aka yi Dinner, 'yan uwa da abokan arziki, duk sun yi bajinta, ta hanyar liƙi da bada gudunmawa. Abbi tuni ya sauka garin Kano tare da tasa tawagar, kasancewar bayan ɗaurin Aure akwai reception na mussaman, da kuma parrate na sojoji, abunka da masu abu da abunsu. A can birnin Sin kuwa, Salman ne zaune a wani katafaren ɗaki, a gaban madubi ya sanya hoton Abra a gaba, ya ƙura masa idanu, idan lissafinsa daidai ne, yau ne ake ɗaurawa Abra Aure, Abran da ya ƙallafa a rai, ya taso ya rayu da soyayyarta, a yau ta zama mallakin wani ba shi ba, ina ma Mami ba ta sanar masa Abra ba 'yar uwassa ba ce ta jini, da duk wannan al'amuran basu faru ba, gaba ɗaya tun da ya zo China ba ya jin daɗin garin, komai nasu daban kamar ba Normal Mutane ba, gashi ko turancin ma ba kowane ya iya ba a cikinsu, dan haka abubuwa suna masa wahala, duk da wai kafin su fara lectures, sai sunyi wata shida ana koya musu Yaren Chinese. An ɗaura Auren Adnan da Abra, wanda dubban mutane suka sheda hakan, ɗaurin Auren da ya samu halartar manyan ƙasa daga ɓangarori daban-daban ciki har da Captain Faruk da aka tsinto Abra da shi. Daidai gwargwado an yiwa Abra Nasiha mai ratsa zuciya game da rayuwar Aure, yayin da Granny ta ta Nasihar mai ɓaro_ɓaro ce ba rufi ba kunyar komai. Da la'asar aka shirya Abra cikin wata dakakkiyar rantsatsiyar lafaya, Mami ta kaita gurin Abbi, yayi mata nasiha sosai tare da Adduoi da fatan shiga ɗakin miji a sa'a. Dangin Adnan sun zo da manyan motoci, domin ɗaukar Amarayar su. Sai dai Abra ta ƙanƙame Mami tana kuka, karo na farko a rayuwar Na'ima, tun da ta fara riƙon Abra, taji jikinta yayi sanyi, dan tun a gurin Dinner jiya Abran ta sa jikin Na'ima yin sanyi. Abra ta ƙanƙame Na'ima tana faɗin "Mamina, a zaman mu idan na yi miki laifi ki yafe mini, Mami bana son barinki". Anty Suwaiba ce cikin masifa ta ce "Wai ke bayinki ne mutanen da suka tsaya suna jiran ki, dalla ki fito ki wuce mu tafi" A hankali Na'ima ta shafa bayan Abra ta ce "Na yafe miki Abra, Allah ya baku zaman lafiya, muje in rakaki bakin Mota". "Mami to ke yaushe zaki zo?". "Very soon" daga haka ta ja hannun Abra zuwa bakin mota. Da ƙyar Abra ta yadda ta shiga, tana kuka tana ɗagawa Mami hannu. Anty Suwaiba ta ce "Ke Na'ima, wai me kike yi hakane kamar kin damu da tafiyar yarinyar nan? Allah ya raba ki da ƙwallon mangwaro kin huta da ƙuda, amma naga kamar kina cikin damuwa? Wai ni fa kamar ƙwalla nake gani a idanun ki". Jiki a sanyaye Na'ima ta ce "Gaskiyar Husawa da suka ce, 'Sabo turken wawa' a zamana da yarinyar nan ban taɓa jin abunda na ji ba jiya da ta kalli idanuna tana mini Addu'a tare da jaddada soyayyarta a gareni, idanunta ɗauke da zallar soyayyar uwa da ɗa, duk da kwashe shekarun da nayi ina azabtar da ita, amma tana mini biyayya fiye da yadda ɗan da na durƙusa na haifa yake mini, ko ba komai da ina ganin gilmawar ta da ta Salman, amma Yanzu shi ya tafi, ita ma kuma haka". "To shine me? Ke ba hutunki bane bama, ta je can ta ƙarata Allah ya tsare miki mijinki da ɗan ki". Na'ima ta ce "Hakane, dama babban fatana kenan, ta bar mini gida, shekarun da mukayi Allah ya amfana, kawai dai kin san zuciya". "Ke dalla can manta da ita". Awanni uku cif, da magariba su Abra suka isa garin Kaduna, aka fara kaita gidan su Adnan, aka yi mata nasiha, suka bata kyaututtuka, sannan suka wuce da ita gidanta. Tubarkallah Adnan ya ƙera mata gida na gani na faɗa, Abbi kuma da Hajiya Na'ima sun cika gidan da kaya na kerewa sa'a, Masha Allah gida yayi komai tsaf. Wanda suka rako Abra daga Kano, suka koma gidansu Adnan su kwana a can, daga nan su koma Kano, Abra ji tayi Kamar ta tashi ta bisu, haka suka watse suka bar Abra. Abra ta zauna jiran shigowar Ango, sai dai har ƙarfe goma sha ɗaya ba ango ba dalilinsa, tun Abra na jira har ta fara gajiya, tsoro ya fara kamata, ta takure a ƙuryar gado, gaba ɗaya tsoro ya baibayeta. Abu kamar wasa har ƙarfe biyu na dare, Adnan be shigo ba, ta ɗauko wayarta domin ta kirashi amma wayarta ta ɗauke babu caji. Rashin sanin abun yi ya sanya ta fara kuka. Haka Abra ta kwana a zaune, sai ɗan gyangyaɗi da ta dinga yi daga zaune a haka har Asuba tayi. A tsorace ta lallaɓa ta shiga banɗakin da ke cikin ɗakin tayi alwala, ta gabatar da sallar Asubahi, ta koma gefe ta takure. Mami 'yan biki sun watse, sai wanda ba'a rasa ba. Tayi wanka tana ƙoƙarin shiryawa, ta ga wata takarda ta faɗo daga cikin wardrobe ɗin ta. Ta sunkuya ta ɗau takardar ta buɗe, rubutun Salman ta gani a jiki, hakan ya sanya ta sake gyara tsayuwarta ta fara karantawa. *Assalamu alaikum warahmtullah. Ina fatan lokacin da saƙon nan zai riskeki kina cikin ƙoshin lafiya Mamina. Na san zakiyi mamakin ajiye miki wannan takarda da nayi, amma ba abun mamaki bane, duk da ba zan kira hukuncin da kika yanke a kaina kuskure ba, amma zan iya kiransa da shamaki da farinciki na, ta hanyar nisata ni da abu mai daraja da nake matuƙar ƙauna. Domin sake nesanta kaina da Abra kasancewar na san mallakin wani zata zama, ina mai sanar miki da cewa daga ranar da na bar Nigeria ba zan sake dawowa ba har Abad, dan muddin ina Nigeria, ruhina yana tare da Soyayar Abra, dan tabbatar da samun farincikinki da nutsuwar ki, ba zan sake dawowa Nigeria ba. Idan kuma kika yi ƙoƙarin tursasa sai na dawo, zan bar China in koma ba im da ba wanda ya sani. Ki huta lafiya Mamina, ki gaishe mini da Abra tare da yi mata fatan Alkhairi a rayuwar Aurenta. Salman Khamal Khamis*. Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 08081012143 [10/13, 11:29 AM] Abk: Mugun ganin da Abra ta yi, ya sanya ƙirjinta fara ɗa gawa zuciyarta tai mata nauyi. Rutse idanunta ta sakeyi tana ganin abin kamar almara, amma ta hana Zuciyarta gasgata abin da ta ke raya mata. A hankali ta yi ƙasa da kanta ta shiga wasa da yatsun hannunta, jikinta duk rawa ya ke, ji ta ke kamar zuciyarta tai bindiga sbd fargaba. Juyawa Adnan ya yi tare da kallon budurwar ta ke tsaye a gefensa, cikin nutsuwa ya sakar mata wani kwantaccen Murmushi mai nakar da zuciyar ko wacce ƴar mace. Fari ta yi masa da idanu tana girgiza ƙirji ganin hakan ya sanya Adnan, janye nasa idon ya lumshe kafin a hankali ya ce "My Surry" kashe murya wacce aka kira da Surry ta yi ta na shafa fuskar Adnan ta ce. "Darling bee" Hannunsa ya watsa yana ƙare mata kallo tare da ɗan matsawa kusa da ita he's trying to kiss her cheeks sai kuma ya ɗaga mata gira ya ce. "Finally Bibina this is my house" "It's beautiful I like it but" hannunta ya kama ya ce "but what? Say it" rungomesa ta yi sosai ta ce "isn't ur house is our house okay" holding nata back yai ya ce "Oh! I almost frgt sbd ke ma na gina gidan". "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" sune kalaman da suka fita da ga cikin bakin Abra a wahale. Ta kasa fahimta, ta kuma kasa gane inda kalaman mijin nata ya dosa "My Surry? Bibina? Our house? What does that means?" Idanunta da suka sauya kala da ga farin da suke da shi zuwa launin jaa ta buɗe da ƙyar tare da zuba musu idanu. Frm Head to toe ta ke kallon wacce aka kira da Surry, a ƙalla zasu iya age mate da Adnan idan ma zai girmeta sai da shekara ɗaya ko watanni, daurewa ta yi cikin sassauta muryarta tare da ɗauke damuwar da ke zuciyarta, but under her heart sunan Allah kawai ta ke kira, wasu har ƙwace mata suke. Kusa da Adnan ta ja ta tsaya idanunta akan Fuskar sa, shi kuma yana kallon Surry. "Sannu da hanya" shirun da ta ji ne ya sanya ta ƙara cewa "Wlcm Bebbb" dry Surry ta yi kafin ta kalli Abra sai kuma ta kalli Adnan ta ce "Bebbb ana kira" haɗe fuska ya yi sosai ba tare da ya ce komai ba. "Is she your wife?" "Waa?" Da hannu ta nuna masa Abra ta ce "I think tana buƙatar ka" "Kin taɓa ganin wuta da ruwa sun haɗu?" Surry ta ce "A'a never" juyawa ya yi gaba ɗaya wajan Abra a hankali ya ja idanunsa ya lumshe kafin ya buɗe a nuste ya kai kallonsa ga fararen yatsun hannun ta wanda suka sha henna sai ɗaukan idanu suke, dugun wuyan ta maƙale da wata siririyar necklace mai ɗauke da red ɗin stone. Jajayen laɓɓan ta wanda suke rawa da karkarwa sbd tsananin tsoro da kuma abin da zai iya zuwa ya dawo. "Idan har wuta da ruwa ba zasu haɗu ba, ta ya ya ki ke tunanin zan iya kiran maid ina nufin ƴar aikin gidan da matsayin mata? Maid ɗina ce" "Dam!" Zuciyar Abra ta buga a hargitse kuma ta ke duban Adnan muryarta na rawa ta ce "Ni... Ni... ni ce ƴar aikin naka? ina matsayin matar ka mene maka wacece ita?" Ta ƙare maganar tana riƙe ƙirjinta sbd yadda ya ke ɗa ga mata tamkar zuciyarta zata tsaga ƙirjinta ta fito haka ta ke ji, bai ce mata komai ba sai kallon Surry da ya yi ya ce. "Lemme take a shower" tana rangwaɗa tare da juya ƙugu wanda duk shan magani ya fara lalata su ta Ƙarasa wajan Adnan ta na kama hannunsa tare da kwantar da kanta a jikinsa ta ce. "Can I help you?" "Sure Bibi" kama hannunta ya yi suka nufi part ɗin sa, sai da suka nisa Surry ta juya ta kalli Abra ta ce. "Ki haɗa min Indomie with egg ta ji Attahiru" Zubewa Abra ta yi tare da zaman ƴan buri a wajan kamar mahaukaciya haka ta fara kuka tare da kunce ɗaurin kanta tana hargitsa kanta, ko idanunta bata iya buɗewa sbd nauyin da Zuciyarta ta yi mata, a wahale ta riƙe ƙirjinta da hannu bibbiyu ta na ƙoƙarin hanasa ɗagawa, sbd ji ta ke tamkar ranta zai fita idan numfashinta ya shiga tare da ɗagawar ƙirjinta. Tun tana addu'a har ta kasa faɗin komai sai idanunta dake lumshewa bakinta na rawa a hankali ta sulale ƙasan carpet kamar sumammiyya. Saukar ruwan mai tsananin sanyi a jikinta shi ne suka taimaka wajan farfaɗo da numfashinta wanda ya bar jikinta, kafin dawowa cikin hayyacinta taji saukar wani ruwan a jikinta wanda yafi na baya sanyi tamkar wanda ya ke ɗauke da ice sbd sanyi. Jikinta na kyarma da ɓari ta buɗe idanunta a tsaye ta gansa da ga shi sai farar Armless da 3Qauter sai ƙamshin Pur oud, Kallon sa ta ke kafin ta ce. "Ka dubi girman Allah ka faɗa min abin da nai maka, bana da kowa a nan kai kawai na sani mene yasa zaka juya min baya a lokacin da nake tsanin buƙatar ka? Ka ɗauke min dukkan wani farin ciki da jin daɗina ta hanyar nuna rashin kulawa a gareni, kada ka manta a ni amana ce a gareka,ka faɗa min abin da nai maka nayi maka Al'ƙawarin zan gyara kuma na baka hqr" ta faɗa tana sakin kuka tare da kallon sa ta na haɗe hannaye waje guda alamar roƙo. Kallon tsaf ya yi mata kamar ba zai magana ba, sai kuma ya ce "Ina girkin da sweetheart ta ce ki mata? Ko kin mata aikin ki ne?" Miƙewa ta yi tsaye zuciyarta na yi mata zafi, wani irin kishi ya rufeta har bata san lokacin da ta wurgawa Surry uwar harara ba. Da sauri kuma ta juya zata shige part ɗin ta. "Idan har kika bar parlourn nan wallahi na lahira zai fiki jin daɗi Abra Khamal Khamis" Cak Abra ta tsaya ba tare da ta kallesa ba, a wannan lokacin ba komai ta ke ganewa ba, ji ta ke inama ba zai auren ba, an faɗa mata daɗin aure an kuma faɗa mata duk soyayyar dake tsakani wata rana ana samun saɓani domin ko harshe da haƙori ana sabawa, balle mutum mai ɗauke da Zuciya wacce jiki ke gudana a cikinta. Sai dai tunaninta ya samu tawaya ta wannan ɓangaren, babu abu mai muhimmancin kamar daren farko na rayuwar ma'aurata amma ita nata daren ya zo mata a yadda ba tai tunani ba, ta kasan fahimtar Dare da duhun da ke cikin al'amarin. Wanne al'amarin ya ke shirin faruwa acikin rayuwarta dama duniyar ta baki ɗaya?. DESTINY. Wata zuciyar ta ce. "Ƙaddara ta ki har nawa ne? U have to think Abra, think think think.... Ta tashi cikin rashin kulawar uwa, ta girma da ƙaunar ƙarninta farin cikin ta, lokaci ɗaya ƙaddara tai mata kutse cikin rayuwarsu aka rabata da jinin jikinta Faris, ta ɗauki ƙaddara ganin yadda Adnan ke nuna mata kulawa tare da yi mata Al'ƙawari kala-kala, hakan duk a cikin tsarin ƙaddarorinta suke? Ko kuma wani abun ke son faruwa ne?... Wani abu mai kama da JUYAYI. "Heyyy You jakanesss" Muryar Sp Adnan Aliyu Matawalle ya sauka a kunnanta a gigice ta dawo hayyacinta duk ba sosai ta jisa ba, hannunta na rawa ta taɓa kunnanta sai a lokacin ta ji hearing aid ɗin ne ya goce. "20mints ya yi maki yawa wajan kawo sweetheart ɗina abinci" zaman hearing aid ta gyara idanunta cike da hawaye ta kallesa ba tare da ta ce komai ba. "I'm i your mate da ina magana kika zuba idanu ko matar amarci ke damunki ki ke son cinye ni eye?" Murmushi kawai ta yi irin Murmushi da gwanda mutum ya yi kuka akan ya yi irinsa. "Idan kai zanwa zan yi, it's my responsibility nauyin ka yana kai na, amma ba zan taɓa yiwa karuwar can abinci ta ci ba....," "Kauuu!! Kauuuu!!!" Ya sauke mata wasu tagwayen maruka kamar kumurciu zaki haka ya ke huci idanunsa akanta ya ce. "How dare you da zaki faɗa min haka Ehh? Kada ki dama idan kin amsa Sunan Abra Khamal Khamis kiga, and wannan da kike maganar karuwa ko....?" Ƙwafa ya yi tare da juyawa ya kama hannun Surry suka shige ɗakinsa sai maƙale jikinsa ta ke tana sakin kuka ance mata karuwa. Dafe kanta da ke juyawa mata tayi, da ƙyar ta ja ƙafafuwanta zuwa kicthen domin ko ta kansa bata sani ba, ganin da akwai komai ta ɗauki Onion da red pepper ta ɗauki Egg da Indomie, tana aiki tana tana sakin ajjiyar zuciya, ga jiri dake ɗaukanta. "Yaya.. Angel Zanci Indomie Yaya please yunwa na keji" "Yaya gidan wani zaki,kina gwarara jikin ki" "Angel waya saki aiki, ba Abbi ya ce ki daina aiki ba" Ajjiyar zuciya ta sauke sbd wuƙar data ya ke. "My Angel kalli hannunki kin yanke, matsa zan yi aiki jeki zauna" "I love You Angel wannan girki kamar a restaurant" "Idan ban kula dake ba, waye zai kula dake ni ki daina ɗauka na matsayin ƙani kawai Yaya Angel" Wani Uban Ihu Abra ta fasa lokacin da maganar Salman ɗaya-ɗaya ta shiga dawowa cikin kwakwalwarta tamkar yanzu ne muryarsa ke mata kuuwa a cikin kunnanta. sai da tayi kuka mai cin rai tana kiran sunan Salmanun-faris come to back to me zan bika duk inda zaka. Plate ɗin Indomie ta ɗauka, a Parlour ta samesu suna kallo da sauri ta ajjiye plate ɗin jikinta na rawa tabar parlourn sai numfashi ta ke fitarwa, har dare bata sake fitowa bata da tabbacin a gidan suka kwana ko a waje?. China. A hankali ya ke tafiya kansa a ƙasa, hannunsa duk biyun zube cikin Aljihu, da ga shi sai wata ƙaramar black t.shirt wacce ta kama jikinsa, sai ƙaramin wando mai kama da trousers. Ƙafarsa sanye cikin wani baƙin takalmi me kyau. Gefen wani kogi ya ja ya tsaya inda ake shan iska ga few mutane a wajan kowa yana abin da ya ke gabansa. Iskar data kaɗa ya sa shi rufe idanu tare da zame hannunsa guda ɗaya ya ɗora daidai saitin ƙahon zuciyarsa "fat! fat!! fat!!" Haka sautin bugawar ta ke badawa, idanunsa ya ware akan ruwan tare da ƙurawa wasu tattabaro idanu farare tas dasu mace dana miji, irin tattabaron nan ne masu kama da ɗawisu sun ɗaga jela sama tai wani scale kamar zanan love Wayarsa ya ɗauka tare da ɗaukan su a taushashe ya ce. "With my heart desires my dream" idanunsa ya ɗan sauya kala kamar zai kuka hawaye kwance a idanunsa ya ƙara sakin Murmushi a karo na biyu "happy married life Angel stay blessings with your husband not ur choice" Salman Khamal Khamis kenan, yaro mai mafarki wanda lokaci guda zanan ƙaddara ya rusa masa mafarkin. Yasa ko wacce kala rayuwa zai a yanzu zai yi ne kara zube ba tare da farin ciki ba, she tooks his happiness ta ɗauke komai nasa ta tafi da shi, baya jin tana da laifi zurfin ciki ya sanya komai faruwa. Komai jimawa soona or later sai ta zama mallakinsa halaliyyarsa. Kujera ya nema ya zauna yana miƙar da ƙafafuwansa, jikinsa ya yi fresh ya murje but ya rame sai idanunsa da Matashin gemunsa haɗi da saje da suka fara cika fuska sbd sauyin weather ta ƙasa. Washegari. Kasa jurewar yunwar da ke damunta ta yi, a hankali ya dubi agogo 12:44 shi ne abin da Idanunta ya gani, da sauri ta sakko ko sallar wahalar da ta ke bata samu yi ba. Zaman rigar jikinta ta gyara har ta fita sai kuma ta dawo ta ɗauki perfume ya fesa ta gyara fuskarta, a hankali ta zame rolling ɗin kanta, sumar kanta ta sauka har baya, a tunaninta ko hakan zai burgesa duk da bata da tabbacin ko yana ma gidan. "Allahumma ajirni fil musibatii, Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" ta faɗa ta sauri ƙirjinta na bugawa da ƙarfi kafin ta sake motsawa jiri ya kwashi ya kaita ƙasa, kanta ya daki jikin canter na parlourn. Ba ita ba shi kansa sai da ya ji kunyar yadda ta samesa tare da Surry, amma sai ya zame ko a jikinsa. Ta jima durƙoshe ko idanu ta kasa buɗewa sai duhu da ta ke gani kamar mai hawan jini. Sunayen Allah ta ke faɗa babu saurarawa, a hankali ta ɗauko tare da ƙara duban Surry wacce ke kwance jikin Adnan tana shafa gashin ƙirjinsa wanda da alama bai daɗe da yin wanka ba, ko ita bata samu damar yin haka ba, amma wata banza ce kwance jikin mijinta. Abin ka dame haƙuri wanda idan ya ta shi abu bai iya yinsa ba. Duk da jirin da ke ɗau kanta haka tai kan Surry kamar mahaukaciya, yadda ta nufi Surry zaka ɗauka aljanu gareta. Tana zuwa ta damƙi wuyanta tana shaƙeta zafin shaƙar ya sa Surry sakin ƙara. Hankali tashe Adnan ya yi kan Abra zai daka kafin ya ƙarasa Abra ta damƙe ƙirjin Surry wanda ya kewa Adnan iyayi dasu, wani ihu Surry ta kwarara tana faɗin. "Wayyo Allah! Zata tsinka zata tsinka na shiga uku" ganin yadda Adnan yayu kanta gadan-gadan ya sanya ta ƙara fisgar ƙirjin Surry. "Wayyo uwata wayyo wallahi ta tsinka" da gudu Abra ta saki Surry ta koma part ɗin ta. Tun kafin ta ƙarasa jikin gado jikinta ya fara rawa numfashinta ya fara fisga kamar mai Asthma idanunta rufe ya ɗauki Alkur'ani ta fara karatu da dukkan muryarta wacce ta kusa cika part ɗinta dana Adnan Aliyu Matawalle ɗin. A karatu ta ke da iya ƙarfinta tun tana yi da ƙarfi har numfashinta ya kasa jurewa, a hankali tai gaba tare da kifawa muryarta a sanyaye ta ce. "Ka gani ko Faris?" Cak kuma Numfashinsa ya tsaya. A haka rayuwar Adnan da Abra ta kasance tsayin sati biyu tun daga ranar kuma bata sake saka shi cikin idanunta ba. Mami damuwa tai mata Abbi ya tsallake ya barta, babu Salman ɗan da ake tutiyya da shi kullum gida shiru kamar mayya lokaci zuwa lokaci kewar Abra na damunta ko za ta ce za kici Ubanki Abra yau ta ji zamanta na ɗauke mata kewa. Faris baya nemanta wani time ɗin ta kira number Abra sai ace a kashe. Cikin sati na uku mafarin faruwar komai tare da toshe da kuma asalin abin da zuciya ke ɗauke da shi, mafarin rusa farin cikin wasu. Iddar da sallarta kenan ta nufi bathroom tare da yin wanka, a hankali ta fito da ga cikin toilet ɗin ɗaure da ƙaramin towel wanda ya tsaya iya cinya ruwa na zuba a jikinta, ga gyaran jikin nan nata yana nan fata sai glowing ta ke. Tana cikin tsane jikinta ta ji an murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin kafin ta motsa ya shigo cikin bedroom ɗin, a hankali ya ke binta da kallo kamar wanda baya cikin hayyacinsa, hannunsa dafe da cikinsa wanda ya ke masa matsanancin ciwo har idanunsa sai da suka nuna alamar hakan. Fararen ƙafarta yabi da kallo zuwa hips ɗinta kana ya maida kallonsa zuwa sama. Kamar wanda ake fisga da mayan ƙarfe haka ya nufi inda ta ke, tsoran yanayinsa ya sanya Abra fara yin baya tare da ɗaga ƙafa zata gudu, domin tunaninta dukanta zai. Gaba ɗaya ta jita male-male a saman ƙirjinsa ya rungome ta tare da bata ƙyakkyawan ma sauki a ƙirjinsa. Bai zo da niyyar hakan ba amma gaba ɗaya a kallon farko tunaninsa ya tsaya, cikin ƙaramin lokacin abubuwa da suka faru suka zama abu mai matuƙar baƙin ciki a rayuwar Abra Khamal Khamis, domin babu imani cikin lamarin Adnan bata taɓa tunanin haka al'amarin ya ke ba, bai saurara mata bai nuna mata soyayya kulawa tare da tattali ba, bai barta ba sai daya tabbatar da ita matsayin cikakken mace wacce tabi layin saurin mata. Wani zazzafan zazzaɓi ya rufe Abra jikinta sai rawa ya ke, haƙoranta na haɗewa a haka ya tsallake ya barta ya nufi nasa Part ɗin yana jin ciwon cikin ya lafa sai kansa da zazzaɓi shima daya saukar masa. Duk inda kake tunanin azaba a wannan daren Abra ta shata, sai Subhi ta samu tai wanka tai sallah jiki na rawa ta koma ta kwanta tana jan numfashi, a hankali hawaye ya sakko mata tunanin kiss ɗin Faris ne ya faɗo mata, soyayya da ƙauna haɗi da kulawa sune ta ke gani cikin idanun Salmanun-faris a lokacin da ya ke sumbatar bakinta. Misalin 1:20 ya turo ƙofar ya shigo kamar ma ƙasar zai bari sai dube-dube ya ke alamar abu ya ke nema ko inda ta ke bai kalla ba. A hankali ta sauka da ga gadon ba zato ya ji ta riƙe masa ƙafafuwa tare da ɗora kanta a jikin ƙafar tasa, wani raunataccen kuka ya ƙwace mata cikin kuka ta ce. "Kaji tsoran Allah ka daina azabtar dani da abin da bai san da shi ba,ka faɗa min laifina wallahi zuciyata zata buga,ina Soyayyar da kake min? Ina kulawar da ka ke faɗa min kayi min adaninta ko haka auren ya ke? Don darajar Allah da Manzonsa ka faɗa min abin da nai maka" Kallon ta ya yi sai kawai ya juya zai fita da sauri ta ce. "Matar ka ce ni, har lahira da ke zanyi alfahari bani da kamarka a yanzu kai ne duniya ta, kai ne dangina kai ne komai nawa, ba danni ba ba dan na isa ba ka faɗa min abin da nai maka na san kana so na" Murmushi ya yi tare da sunkuyawa ya ɗagota zuwa tsaye cije baki tayi sbd zafin da ta keji ko tsaiwa bata iyawa. Shoulder ɗinta ya riƙe tare da matsawa ya ce. "You deceived yourself Abra Khamal Khamis, Adnan Aliyu Matawalle bai taɓa sonki ba, kuma bai taɓa sonki ba, infact mujiya ki ke a cikin idanuna" girgiza kai tayi bakinta na rawa ta ce "what... what do you mean by that? baka so na kake cewa" hannunsa ya sanya ya tallafo fuskarta ya ce. "Idan baƙin maciji ya sareki ina da tabbacin ki kaga baƙar leda cewa zaki shine, wallahi da naga fuskarki gwara na kalli mujiya, a duk lokacin da naji muryar ki ji nake kamar ana zuba min ruwan dalma a zuciya, idan kina kusa dani kowa ji nake kamar na saka hannu na shaƙeƙi na huta, babu abin da na tsana a duniya kamarki bana Sonki bana Sonki bana Sonki na tsaneki kamar yadda bana ƙaunar mutuwa ta a yanzu" baya Abra ta yi kamar zata faɗi tana riƙe ƙirjinta ɗakin ne ya shiga juyawa mata wani duhu na mamaye cikin idanunta gyara zaman hearing aid ɗin ta yi ko tunaninta ita ce bata ji daidai ba. "Baka so na mene yasa ka aureni?" "To take a revenge" "Revenge? Me na yi maka ni? mene aikata maka da har zaka ɗauki Revenge akai na?" Murmushi ya yi kafin ya ce "Baki min komai ba, laifin da Ubanki ya yi min shi ne ya sanya zan ɗauki Revenge akanki, zan raba shi da farin cikin sa kamar yadda ya zama silar lalacewar nawa, ba zan taɓa yafe masa ba sai na tabbatar yaji Abin da naji this is my promise" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wacce rana ce wannan me ya ke son faruwa da ita? Rarrafawa ta yi zuwa inda ya ke tana riƙe ƙafarsa ta ce "Me Abbina ya yi maka? Wallahi Abbina ba zai taɓa cutar da wani ba, idan ma ya yi sai dai kuskure kada ka cutar dani don girma Allah ban san komai ba" gyara tsaiwa Adnan ya yi ya ce "Ba muriƙinki nake magana ba, ba Abbinki ba Uba maifi wanda ya yi silar zuwanki duniya" "Abbine mahaifina bana da wani Uba sai shi shi ne mahaifina" dry Adnan ya sake yi kafin ya ce "Abra Khamal Khamis? To ba haka sunan naki ya ke ba, ke TSINTACCIYA ce, tsintar ki Abbi ya yi acikin jeji ya ɗauki tare da baki kulawa kamar ƴar cikinki, kuma ke ɗin bawai Shegiya bace mugun Ubanki shi ne yaja baki yadda ya rabani da farin ciki shima sai na raba shi da shi, zan ɗauki fansar abin da ya yi min akanki *REVENGE MARRIED* Sunan aurenmu" "bana da wani Uba wanda ya shige Abbi kai ma ka sani" hannunsa ya tsawa ya ce "bance ki yarda ba, amma ni da Abbin naki musan cewa ke ba ƴarsa bace kiyi tunani kaf dangin ku dawa ki ke kama? Just think bance ki yarda ba, amma zaki rayu a gidan nan tamkar baiwa!" [10/13, 11:29 AM] Abk: Take jikin Hajiya Na'ima ya ɗau rawa, hannunta ya fara karkarwa, ta nemi guri ta zauna a gefen gado, wani irin gumi yana tsatstsafowa a goshinta, a hankali ta furta "Na shiga uku, mai yaron nan yake nufi dani ne?" Cikin azama ta miƙe, ta ɓoue takardar ba tare da ta nunawa kowa ba. Sai ƙarfe takwas na safe sannan Adnan ya shigo gidan, shi ma bai shigo inda take ba, maganarsa ta jiyo a parlour suna gaisawa da waɗanda da suka kawo ta, hakan ya sa ta fita parlour'n da sauri, zuciyarta cike da ɗokin ganin shi. Gaishe shi ta yi, sarari ya ji ta amma ya ɗauke kai kamar bai ji ba, hakan ya faɗar mata da gaba. Amma dai ta daure suka yi sallama da waɗanda suka kawo ta, har da kukanta lokacin da suka fice daga parlour'n. A tunaninta bayan fitar su Aunty Suwaiba Adnan zai taho gare ta cikin zumuɗi ya rarrashe ta, amma sai ta ga saɓanin haka. Ƙafa ya ɗora ɗaya akan ɗaya yana latsa wayarsa, tamkar bai san da halittar ta a parlour'n ba. Cikin tsananin shock Abra ta ce. "Baby! Me yake faruwa ne? Jiya ba ka dawo ba ka bar ni na kwana ni kaɗai cikin jin tsoro, yanzu kuma ka dawo amma ka yi kamar ba ka ganni ba." Tamkar da dutse take magana, ko motsi bai yi ba da sunan ba ta amsa. Ƙura masa ido ta yi tana kallon shi cikin mamaki, Adnan ɗinta ne kuwa wannan ko an canza mata wani? Adnan ɗin da ya ci burin ganin wannan ranar da za ta kasance a gidansa, amma me ya yasa ya yi mata haka? Me yasa tana yi masa magana ya share ta? Ko dai something bad happened to him? Tunanin hakan ya sa ta matsawa kusa da shi da niyyar ta ji abun da yake damun shi. Wata uwar harara da ya ɗago kai ya banka mata yasa ta tsayawa cak a inda take cikin bugawar zuciya. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un." Abun da ta ambata a fili kenan. Rasa abun yi ta yi hakan ya sa ta koma ɗakinta cikin sauri, faɗawa kan gado ta yi tare da sauke wani wahalallen numfashi. So take ta tuno ko ta yi wa Adnan wani lefin amma ta kasa, hakan ya sa ta fashewa da kuka. Sai da ta yi mai isarta sannan ta tashi ta shiga toilet ta wanke fuskarta. Bayan ta fito ta tsaya a gaban mudubi tana kallon kanta, cikin ƙoƙarin son gano ko wani abun Adnan ya gani a jikinta da bai masa ba, amma ba ta ga komai ba. Duk da ita ba ma'abociyar son kwalliya ba ce amma haka ta zage ta tsantsara ta tare da kafa ɗaurin ɗankwali mai kyau, ita kanta ta san ta yi kyau, duk da yanda take jin wata irin fargaba a cikin zuciyarta amma sai ta murmusa, ta san dole kwalliyar tata ta burge Adnan. Daddaɗar humra mai daɗin ƙamshi ta shafe jikinta da ita, sannan ta fita zuwa ɗakin Adnan. Sai da ta fara shiga kitchen ta haɗa masa breakfast wanda aka ajiye dan shi sannan ta nufi ɗakin nasa. A zaune ta tarar da shi a kan gado yana operating system. Cikin sanyin jikinta ta yi masa sallama, ko d'agowa bai yi ba balle ya amsa mata. Hakan ya ƙara tsinkar mata da gaba, zuwa yanzu kam ta gane da akwai matsala. Kanta a ƙasa ta ce. "Ga abinci." Nan ma bai kula ta ba, kawai sai ta fashe da kuka cikin rashin sanin abun yi. Ta daɗe a duƙurshe tana kuka mai tsuma zuciya, yana jin ta amma ko tari bai yi ba, ƙarshe ma tashi ya yi ya ɗauki car key ya fice ya bar mata gidan. Hasbunallahu..... kawai Abra take maimaitawa, a ranta tana tambayar kanta me yake shirin faruwa da ita ne? Me Adnan yake nufi da ita? Jiki a saɓule ta miƙe ta koma ɗakinta ta kwanta akan gado ta cigaba da kukanta, kewar Faris da Abbi da Mami na nuƙurƙusar zuciyarta, wani azababben ciwon kai ne ya far mata lokaci ɗaya, cikin dauriya ta janyo bargo ta lulluɓe jikinta, saboda yanda take jin wani sanyi na ratsa gaɓoɓin jikinta, tamkar wadda za ta yi zazzaɓi, a haka wani wahalallen bacci ya ɗauke ta. Sai Azhar ta farka, shi ma ƙarar doorbell ya tashe ta, cikin sauri ta miƙe ta shiga toilet ta wanke fuskarta da ruwa sannan ta fito ta saka hijabi ta fita. Mata ne kusan su takwas ta gani, cikin fara'a ta tarɓe su tare da yi musu iso. Bayan sun zauna sun gaisa ta kawo musu drinks da kayan garar ta, anan suke gabatar mata da kansu. Dukkansu cousins ɗin Adnan, Ƴanmata shida sai matan aure biyu. Ta ji daɗin zuwansu ba kaɗan ba, dan ba ƙaramin ɗebe mata kewa suka yi ba. Sai dai duk bayan sakanni idan ta tuna Adnan da yanayin da ya nuna mata ɗazu sai gabanta ya faɗi. Da abinci suka zo, hakan ya sa ba ta yi girki ba shi suka ci, ita ɗan caccakalar abincin ta yi kaɗan ta ci ba don daɗi ba. Sai kusan Magriba suka tafi suna ta tsokanar ta wai kar Ango ya dawo ya same su ya yi musu korar kare, ita dai murmurshin yaƙe kawai take, sai ta ji dama kar su tafi. Ba ta zauna ba sai da ta tsaftace gidan ta saka turaren wuta a burner, hakan ya sa gidan gabaɗaya ya karaɗe da ƙamshi. Bayan ta yi Sallah ta yi wanka ta shirya cikin wani tsadadden yadi mai kyau maroon color, ya yi mata sosai ya haska farar fatarta. Parlour ta fita ta jera abinci akan dinning sannan ta koma ta yi Sallar Isha'i da aka fara kira. Tana idarwa ta janyo wayarta dan ta kira Abbi amma ta tarar wayar a kashe, ta manta tun jiya wayar babu chaji ta mutu. Chajin ta jona ta zauna jiran ya ɗan yi, Salman ne ya faɗo mata a rai. A fili ta ce. "Kana ina My Faris? Me kake yi yanzu? Me ya sa ba ka kira ni ba tunda ka tafi? Yaushe zaka dawo ka zo gidana in gan ka ɗan ƙanina? Na yi tsananin kewar ka." Daga haka ta fashe da kuka. Khamal na zaune a parlour'nsa shi da Na'ima wadda zuciyarta ke cike da tsananin farinciki, jin ta take kamar a mafarki yau Allah ya yi Abra ta bar mata gida, shikenan fargabarta ta ƙare. Sai dai tuno letter Salman da ta gani ya sa gabanta fad'uwa da ƙarfi, ta rasa me ya sa abun ya dame ta? Dan da farko shirme ta ɗauki abun, saboda sanin komai daren daɗewa dole Salman ya neme su, ba kuma zai taɓa iya yin zuciya da su ba, letter da ya yi mata dan yana cikin ɓacin rai ne, abun yana cin shi a lokacin shi ya sa, amma ta san idan tafiya ta yi tafiya komai zai wuce. Khamal yana duban ta ya ce. "Komai lokaci ne, kamar ba yau ake zancen bikin Daughter ba, ga shi har an yi an gama, ta tafi ta bar mu da kewar ta. Cikin kissa Na'ima ta ce. "Ta bar mu da kewa kam, don gidan babu daɗi yanzu ko kaɗan, ga ba Salman." Khamal ya nisa ya ce. "Har kin tuna mini kuwa, na kai sati ina trying his number ba ta shiga, amma na kira mutumin da ya kira ni da numbern shi lokacin da ya sauka a garin, ya ce mini neighbours suke, idan sun haɗu zai kira ni ya haɗa mu." Murmushi Na'ima ta yi ta ce. "Allah Sarki yaron kirki, Allah ya tsare mana shi." Khamal ya amsa da Amin tare da zaro wayarsa daga aljihu ya kira layin Abra amma sai aka ce masa a kashe, tun rana yake kira ta ba ta shiga. Numbern Adnan ya kira, dan ya san duk sabon ango i yanzu yana gida. Bayan ya ɗaga suka gaisa cikin mutuntawa, Khamal ya tambayi Abra, Adnan ya tabbatar masa tana nan ƙalau, wayarta kuma babu caji ne shi ya sa bai same ta. Khamal ya buƙaci Adnan ya ba wa Abra wayar, sai ya ce ya ɗan fita, idan ya koma gidan zai haɗa su, daga haka suka yi sallama. Tana zaune takure a bakin gado ta yi tsumu cikin alamun tsoro, ita kaɗai a gida har tara ta yi amma babu Adnan babu labarin shi. Ƙwaƙwalwarta har ta gaji da tunanin dalilin da ya sa Adnan yake yi mata haka, kanta kamar zai tsage saboda ciwo. Unexpected ta ji an buɗo ƙofar ɗakin an shigo, lumshe ido ta yi cikin jin daɗi dalilin shaƙar ƙamshinsa, a hankali ta buɗe idonta ta kalle shi, yanda ta ga ya murtuke fuska ne ya sa gabanta mummunar faɗuwa, amma duk da haka ta daure cikin raunin murya ta ce. "Sannu da zuwa." Ta ƙarashe maganar hawayen da take ƙoƙarin ɓoyewa suna zubo wa. Bai kula ta ba, wayarta dake chaji kawai ya ɗauka ya fice. Da ido ta bi shi cikin kokawa da numfashinta dake barazanar ɗaukewa. Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un ta shiga maimaitawa hannunta dafe da kanta, wani irin raɗaɗi da zafi take ji a cikin zuciyarta. Tambayar kanta ta shiga yi, dama haka Auren yake? Ko kuma ita kaɗai ta fara da matsala? Ina tarin ƙauna da soyayyar da Adnan yake yi mata? Ina tanadin kulawa da tattalin da ya ce ya mata? Ko dai mafarki take yi? Ta rasa da wanne za ta ji, da rashin Faris a kusa da ita ko kuma da kewar su Abbi ko da abun da Adnan yake mata? Sunan Allah ta dinga ambata har ta ji sauƙin radad'in da zuciyarta ke mata. So take ta tashi ta je gurin Adnan ta ji me ta yi me masa? Amma a yanda take jin jikinta kamar ba nata ba ta san ba za ta iya tashi ba. Kwanciya ta yi saboda juyawar da kanta yake yi mata. Wannan shi ne dare mai tsayi da muni da Abra ta gani a rayuwarta, dan bacci duk iya satarsa bai sace ta ba. Nasihar Ammi da ta ce ta dinga tashi cikin dare tana yin Sallah ko raka'a biyu ce ta dawo cikin kwanyarta, hakan ya sa ta lallaɓa ta tashi ta shiga toilet ta ɗaure alwala ta raya daren, ta kai wa Ubangiji kukanta tare da roƙon ya kawo mata ɗauki. Bayan an yi Sallar Asuba ta ɗauko alƙur'ani mai girma ta karanta, bayan ta gama ta yi azkar ɗinta. Hakan ya sa ta ji sauƙin damuwar dake cunkushe a cikin ranta. Sai kusan takwas ta fita parlour bayan ta yi wanka. Gyaran gidan ta fara yi cikin matuƙar sanyin jiki, tana cikin yi Driver'n gidan Hajiya Mama ya kawo breakfast, ta karɓa ta yi masa godiya ta kai dinning ta ajiye. Tana zaune har 10 tana jiran fitowar Adnan amma shiru ko motsinsa ba ta ji ba. Wasa-wasa yau har Magriba ba ta ɗora Adnan a idonta ba, sauƙinta yau ma ta yi baƙi har sau biyu sun ɗebe mata kewa. Sai bayan Magriba ya shigo gidan, lokacin tana zaune a parlour ta kunna kallo, a ƙoƙarinta na son ya ɗebe mata kewa, sai dai damuwar dake cikin ranta ta hana ta gane me firlm ɗin ma ya ƙunsa. Duk yanda yunwa da ƙishirwar son ganin shi suka cika mata zuciya amma sai ta kasa ɗaga ido ta kalle shi, ƙasa ta yi kanta tana sauraren yanda zuciyarta ke bugawa. Karon farko tun bayan da aka kawo ta, ta ji muryarsa ya yi mata sallama, sai dai ba a yanda ta so jin maganar tasa ta ji ba, ba cikin soyayya da kulawa ba. Fuskarsa a murtuke tamkar aka yiwa saƙon mutuwa, cikin isa da gadara kamar an masa dole ya ce. "Je ki ɗauko hijabinki." A hankali ta ɗago ta dube shi idanunta cike da ƙwalla, kafin ta kai ga yin magana ya juya ya shige ɗakinsa. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka ta miƙe ta je ta ɗauko hijabin ta saka, tana cikin kashe kayan kallon ya fito daga ɗakinsa ya yi hanyar waje ba tare da ya kalli inda take ba. Bin bayansa ta yi cikin sanyin jiki tana sharar hawaye. Ganin ya shiga Motor ta buɗe front seat ta shiga, wai mugun kallo ya watsa mata tare da faɗin. "Kar ki bari na ƙara ganin wani abu mai kama da hawaye a fuskarki." Ba ta ce komai ba ta share hawayen tare da lumshe idonta. Gidan Hajiya Mama suka je. Abba da Hajiya Mama sun karɓe ta cikin fara'a da soyayya, sai nan-nan suke da ita. Ita kam kanta na ƙasa kunya duk ta ishe ta, idan an yi magana sai dai kawai ta murmusa. Adnan kuwa sai shagwaɓa yake musu wai yanzu sun daina son shi Abra suke so. Abun da ya ba wa Abra mamaki yanda ya dinga yi mata magana cikin kulawa da sakin fuska a gabansu Abba, hakan ya jefa ta cikin tunanin me Adnan yake nufi da ita? A nan suka yi dinner tare da su Abba, tun tana jin kunyar su har ta ɗan ware, saboda su babu ruwansu, musamman Abba he is so friendly, yanata jan ta da hira. Sai ta ji dama Adnan ɗinta ne haka. Hajiya Mama ta lura da yanayin Abra kamar wani abu yana damun ta, idanuwanta ma sun nuna alamun ta yi kuka. Ba ta yi tunanin komai game da hakan ba, sai ta alaƙanta hakan da kewar gida take yi da kuma rashin sabo na mu'amalar Aure. Kafin su tafi Adnan ya sanar da su zai yi tafiya zuwa Abuja akan wani muhimmin aiki da ya taso masa, za su tafi tare da Abra. Addu'a fatan isa lafiya sukai musu. Sai wajen 10 suka dawo gida. Bai ko kalle ta ba bayan ya yi parking ya buɗe Motar ya fice. Bin bayansa ta yi kallo cikin wani irin yanayi na ƙuncin zuciya. Ajiyar zuciya ta sauke tare da buɗe Motar ta fita. Tun daga lokacin ba ta ƙara saka shi a idonta ba sai washegari bayan Sallar Asuba ya shigo ɗakinta. Time ɗin tana karatun Alkur'ani, bayan ta kai ajiye ta rufe tare da gaishe shi cikin girmamawa. Bai amsa mata ba sai bin ta da wani wulaƙantaccen kallo da ya yi. Cikin ƙaunshin murya ya ce. "Zan yi tafiya yanzu, ba na zo kuma dan in sanar miki ba ne saboda ba ki kai wannan matsayin ba a gurina, na zo in ja miki warning ne akan ko da wasa kar wani ya ji labarin ba da ke na yi tafiyar ba, idan kunne ya ji jiki ya tsira." Ya ƙarashe maganar tare da jan tsaki. Cikin kukan da ya taho mata ta ce. "Dan Allah kar ka tafi ka bar ni, ni kaɗai, wallahi tsoro nake ji." "Abun da kike jin tsoron ya kashe shi." Ya faɗi haka tare da juyawa da niyyar ficewa." "Please where is my phone, ka dawo mini da ita Dan Allah." Ta faɗa cikin matsanancin kuka. Ko juyowa bai yi ba ya yi ficewarsa abunsa. Kifa kanta ta yi akan cinyoyinta ta shiga rera kuka mai ban tausayi. Why Adnan? Me nake yi maka da ka zaɓi mu yi irin wannan rayuwar mai cike da ƙunci da damuwa? Ya Allah ka kawo mini ɗauki akan sabon babin ƙaddarata da ya buɗe, Allah ka sassauta mini. Abun da take faɗa a ranta kenan cikin tsantsar damuwa. Yau kwana biyar da kai Abra gidanta, wadda waɗannan kwanakin suka kasance kwanaki mafi muni da tsaho a cikin rayuwarta. Gabaɗaya ta rame ta fita daga hayyacinta, ga babu waya balle ta kira su Abbi ko ta ji sauƙi a cikin ranta, ga kewar Salman da kullum ƙara yawaita take a cikin zuciyarta. Alkur'ani shi ya zamto abokin hirar ta akodayaushe, sai kuka da kullum sai ta yi shi ba adadi. Misalin ƙarfe goma sha biyu na rana tana kwance a parlour akan carpet, idanunta a lumshe hawaye na zirara ta ƙasansu. Tana jin yanda cikinta yake ta ƙugin yunwa amma ta kasa tashi ta samar wa kanta abin da za ta ci, ga wani azababben ciwon kai da ya aure ta, kullum da shi take kwana take tashi. Kamar a mafarki ta ji an buɗe ƙofar parlour'n an shigo, ko ba a faɗa mata ta san Adnan ne ya dawo, saboda da zai tafi ya kulle ƙofar parlour'n ta waje, ta gane hakan ne a lokuta da dama da ta yi yunk'urin fita harabar gidan ko za ta ga abun da zai ɗebe mata kewa damuwar zuciyarta ta ragu. Ko matsawa ba ta yi ba da niyyar tarɓar shi, sanin da ta yi ko ta masa magana ba amsawa zai yi ba. Sai dai jin kamar ba shi kaɗai ya shigo ba ya sa ta buɗe idonta da sauri tare da goge hawayen fuskarta ta tashi zaune. Abun da ta yi tozali da shi ne ya sa numfashinta ɗaukewa na wucen gadi. Adnan ne tare da wata mace wadda kallo ɗaya za kai mata ka gane ƴar duniya ce ta ƙarshe, duba da yanayin shigar jikinta da uban bleaching ɗin da ta ci, ga kitson attachment a kanta gami da gashin ido maƙale a saman idanunta. Wannan duk ba shi ne abun da ya fi ɗagawa Abra hankali ba, jakar matar da Adnan ya riƙo a hannunsa da kallon da yake jifan ta da shi mai nuni da tsantsar soyayya, a ƙarshe kuma ya tsugunna yana cire mata hill shoe ɗin dake ƙafarta. Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 09047871750 or 08081012143.[10/13, 2:20 PM] Abk: Cikin rawar murya Abra ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, you are lying Sp, ba zai taɓa yiwuwa ba". Adnan ya ce "Ban gaya miki dan ki yarda ba, na gaya miki ne dan ki san irin zaman da zaki yi a gidana, Abra akan ki zan ɗau fansar abun da mahaifinki yayi mini, mummunan tabo mai raɗaɗi da ke cunkushe a zuciyata, ina son ya ɗanɗani abun da na ɗanɗana ya ji idan da daɗi" Ƙirjinta ne ya dinga wani irin bugu, kamar zai tsage, da gaske Adnan yake abun da ya faɗa? Kai wannan ƙarya ce, ta yaya ma haka zata kasance ta yaya za'ace ba Abbi ne ya haifeta ba?. Adnan na ƙoƙarin barin ɗakin, yaji timmm. Yana waiwaya wa, ya ga Abra ta kai ƙasa, ta faɗi a sume, tunowa yayi yadda Abbi ya taɓa yi masa bayanin irin wannan ciwon da take fama da shi, taɓe baki yayi yai ficewarsa ya bar ta, ba tare da wani tausayi ko jin ƙai ba. Karatun su Faris yayi nisa, sai dai ba shi da wata walawala, ya kasa sakewa da kowa, balle ya saba da halin da ya tsinci kansa a ciki, kullum tunanin Abra na cikin zuciyarsa, yadda take bashi kulawa da tarairayarsa, ba ta san damuwarsa ko kaɗan. Tabbas da Mami ta bashi goyon baya,ya san Abra ba zata ƙi Aurensa ba, amma Mami tayi duk mai yiwuwa ta toshe duk wata kafa, da zata sada shi da cinmma muradinsa, a hankali kuma sai ya koma tunanin ko Abra zata haɗu da iyayenta kan ta koma ga Allah? Ya zataji a lokacin da ta san cewar ba su Abbi ne suka haifeta ba? Tun da ya san gaskiyar wannan maganar, ya san komai daɗewa ita ma Abram zata sani. Adnan bai dawo gida ba sai azahar, a gurin aiki Usman yana ta damunsa a kan cewar zai zo gidansa cin girkin amarya, amma Adnan yace bai isa ba, ba ze kuma kowa ya kallar masa mata ba. Ko da ya koma gida, a gurin da ya bar Abra, a nan ya tarar da ita, ko motsi ba ta yi daga gurin ba, ya kalli agogon da ke ɗakin, tun takwas da rabi ya fita, yanzu ƙarfe uku da kwata amma tana kwance a gurin a ƙasa. Durƙusawa yayi, ya ɗauke ta, ya shimfiɗeta a kan gadonta, ya kalli yadda gashin kanta ya baje a gurin, gashi idan tana bacci wani irin kyau take ƙara yi, ya ɗan taɓe baki, tare da furta "kyan ɗan maciji, mahaifinki shine kyau, kuma ya haifi kyau amma sai baƙar zuciya da muguwar aniya". Ya ɗauko ruwa mai sanyi a fridge, ya ɗagota ya dinga zuba mata ruwan nan a fuska, ko tsoron ya shige mata hanci ba yayi. Ganin ko motsi ba yi ba, ya sanya ya cire mata rigar jikinta, ya buɗe robar ruwa yana zuba mata, a gigice ta motsa tare da wata irin ajiyar zuciya, cikin muryar fita hayyaci ta ce "Faris!" "Dalla buɗe idonki malama, ba Mayen naki bane nine nan" Sauke numfashi take, tana kallon Adnan tare da jin ina ma mafarki take yi ba gaske ba. Sai yanzu ta lura da babu riga a jikinta, da sauri ta janyo rigarta tana rufe jikinta, tsaki yayi ya ce "Malama ki tashi ki je ki dafa mini abun da zan ci, ina jin yunawa ba zan iya cin abinci a waje ba" "Baby kaina ciwo yake, jiri nake ji" ta faɗa a raunane. "I don't care, ki tashi kawai" ya ƙarasa maganar cikin tsawa. Abra ta sauko a hankali daga kan gadon, tana dafa bango ta bar ɗakin. A hankali take gudanar da komai a kitchen ɗin saboda ji take tamkar zata faɗi ƙasa. Allah sarki, da a gida ne duk da faɗan Mami, idan ta shiga wannan yanayin Mamin ma na ɗaga mata ƙafa, ko ba zata je kanta ba, amma tana ƙyaleta ta huta, her Faris kuwa yana kusa da ita yana sannu, da ta motsa zai fara "me kike so?" Take maganganun da Adnan ya gaya mata da safe suka faɗo ranta, ta tuna ko salloli ba tayi ba, tuno maganganun nasa tayi, kamar saukar wuta a kanta, cikin rashin sani, da firgici ta ture tukunyar da ke kan gas, aikuwa ruwan zafin ya zubo mata a ƙafa. Wani uban ihu ta saki, wanda ya sanya Adnan tasowa da sauri, ya shigo kitchen ɗin, ya kalli yadda tunkuyar ta faɗi ƙasa, ruwan zafi ya zube mata a jiki da ƙafarta, sauran ya malale a kitchen ɗin. "Wai ke wace irin Yarinya ce mara hankali da nutsuwa? Mai yasa baki da tunani ne? Ko da yake babanki ma haka yake, ba shi da lissafi balle tunani, Wallahi kika kuma yi mini ihu haka a cikin gida sai na tattakaki" yayi maganar yana huci ya juya ya bar kitchen ɗin. Toshe bakinta Abra tayi, ta dinga wani irin kuka, mai tsuma zuciya, a hankali tana ɗingisa ƙafarta da ke mata wani irin azabar zugi, ta fito falo, sai dai ta kasa cigaba da tafiya saboda yadda ƙafar tayi jawur, take mata wani irin zafi. Adnan ne yake waya a falon "Wallahi Abbi duk lafiyar mu ƙalau Alhamdilillah". "Adnan lafiya kuwa har yanzu wayar Abra ba ta shiga, hankalin mahaifiyarta ya tashi da nasu Ammi, ta ce tun da aka kawota ba su kuma waya ba, nima sai dai muyi waya da kai amma ba'a samunta?". Adnan ya ce "Abbi wayar nake so na canza mata, ban zauna bane abubuwa sun yi mini yawa sosai, amma a satin nan nake sa ran za'a kawo mata". Abbi ya ce "Ok, shikenan haɗani da ita dan Allah". Adnan ya kalli in da Abra ke zaune, ta zubo masa idanu tana jiran ya bata waya, amma sai ya ce "Abbi bacci take yi". "Bacci kuma da la'asar haka?". "Eh ba ta jin daɗi ne, an mata allurai". Abbi ya ce "subhanallah, amma shine baka gaya mini ba? Mai ya sameta?". Adnan ya ce "Abbi ɗan menstrual pain ne, kuma an mata allura ta samu releif". "To shikenan, a kula da ita please, in an jima zan kuma kira inji jikin nata". Adnan na gama wayar, ya kashe wayar gaba ɗaya ya ajiyeye a gefensa ya cigaba da kallo. Wani sabon kukan ta sake fashewa da shi, mai tsuma zuciya da nuna tsantsar damuwa, amma Adnan ko a jikinsa, ƙarshe ma sai tashi yayi ya bar mata falon gaba ɗaya. Da ƙyar ta ja jikinta ta koma ɗakinta, tayi sallolin da suke kanta, ta nemi guri ta zauna ta takure, tana sake jujjuya maganganun Adnan, da ƙoƙarin gano gaskiyar lamari, sai dai babu yadda za'a yi ta san gaskiyar lamari, in dai bata bakin wani taji a gidan su ba, wani irin abu mai ɗaci ya zo ya tokare mata tun daga ƙirjinta zuwa wuyanta da kan harshenta, ƙirjin yayi mata wani irin nauyi, da ƙyar take iya numfarfashi saboda tsananin damuwa. Daf da magariba ta kuma jin fitar Adnan, wata irin yunwa ce ta ke sassaƙarta, haka ta kuma fitowa ta tafi kitchen, ta fara ƙoƙarin ɗora abincin dare. Abbi yayi mamakin yadda yake cigaba da kiran wayar Adnan, amma shiru ba ta shiga, haka Salman ma kusan wata guda kenan, ba'aji daga gareshi ba. Gefe Na'ima ta uzzurawa Abbi da kira, da cewar ba fa ta samun yaran nan a waya gaba ɗaya, mussaman Salman, da ta tsorata da lamarin Salman sosai da sosai, dan alamu sun fara nuna cewar abun da ya bar mata wasiƙa na shirin faruwa, gashi babu damar ta sanar da Major abun da ya bar mata a wasiƙa. Da daddare Adnan ya dawo, ya tarar Abra tayi girki, ba kunya ya zauna yana cin Abincin sa, har Abra ta fara shirin kwanciya, amma ta fasa ta fito falo, tana ɗingisa ƙafarta. Kusa da Adnan taje ta zauna, bai ko kalli in da take ba, ya cigaba da abun da yake yi. "Baby" ta faɗa a hankali. Ya amsa mata da Angel, ji tayi sunan ya tsirga mata kamar yau ya fara gaya mata, duk da suna ne da Salman yake kiranta da shi, amma idan Adnan ya faɗa jin sunan take na musamman a bakin sa. "Baby, dan Allah dan Annabi, tun da kace ba Abbi ne mahaifina ba, ka gaya mini waye mahaifina ka nuna mini shi". Wata makirar dariya Adnan yayi ya ce "Ashe ma ba fansar zan ɗauka ba, idan har zan haɗa ki da shi, ai Abra ke da mahaifinki ya sanya ki a idanunsa sai a lahira, dan nayi ƙoƙarin toshe duk wata kafa da zata sada ki da shi har Abada" "Dan Allah kar ka yi mini haka, ka yafe masa koma me yayi maka, dan girman Allah ka haɗani da shi ko sau ɗaya ne, ba dan halina ba". "Tashi ki bani guri, kafin in tashi in ƙwallo dake a gurin nan, zancen mahaifinki kawai in ana yi ji nake tsanarsa da duk wani abu da ya raɓe shi yana sake ninkuwa a zuciyata, ki tashi ki bani guri kafin in miki illa, 'yar zuriyar masu baƙin hali" Abra ta miƙe, maganganun Adnan na mata amsa kuwwa a kunnuwanta 'yar zuriyar masu baƙin hali! Gani take tamkar an canza mata Adnan ɗin ta, da ta san haka Aure yake, da har gaban abada ba zata yi shi ba. Ta koma ɗakinta, ta takure a kan gado, tana ambaton sunan Allah, ko ta samu sassauci a zuciyarta. Tana nan zaune a kan gado, fitilar ɗakinta a kashe, Adnan ya shigo ɗakin, yana shigowa gabanta ya faɗi, dan ba ta san da wacce ya zo ba a wannan tsohon daren. Ba kunya ta ga ya hawo kan gadonta, ba tsoron Allah, ya janyota jikinsa da ƙarfi, ba wani tunani ko tausayawa ya nemi haƙƙinsa na Aure, ya sauke mata duk wata gajiyarsa ta wunin ranar kamar wata Akuya ba ɗan Adam ba, kuma ya tashi ya shiga toilet ɗinta, ya tsarkake jikinsa ya fice ya bar ta ko kallonta bai yi ba. Al'amarin Adnan ya dai na bawa Abra mamaki, sai dai tsoro babu alamar rahama ko tausayawa a tare da shi, zuciyarsa a dake take, ta bushe da rashin imani. Adnan kam, baccinsa yayi mai daɗi ya bar Abra da matsanancin ciwon jiki, duk lokacin da zai kasance da ita, yana tsintar kansa cikin tsantsar nishaɗi da jinsa free from any sadness, halin da zata shiga kuwa sam baya damunsa. GY BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY. Nurse Jamila ce tsaye a gefen Bulama, yana duba wani scaning da ta kawo masa na wata mata, rufe file ɗin gabansa yayi ya kalli Nurse Jamila ya ce "Yi min magana da mijin matar nan, aiki za mu yi mata" Ɗan waro idanu ta yi ta ce "Doctor, na ga kamar scanic ɗin ya nuna bakomai, kamar peptic ulcer ne kawai, kuma kace aiki zaka yi mata" "To doctor Jamila, mai Yakamata ayi?" Shiru tayi, bayan tuna cewar ya hanata yi masa shishshigi a cikin lamarin aikinsa, ba ta kuma cewa komai ba ta fita ta kirawo mijin matar . Nan Bulama ya din ga yi masa wani surkullen bayani irin na su na likitoci, yadda mutumin ba zai wani gane ba, ya ce mutumin ya je ya biya kuɗin aikin a shiga da ita da gaggawa. Lamarin Adnan da muguntarsa ƙara gaba yake yi, dan yanzu duk lokacin da ya buƙaci Abra ko da dare ko rana, haka yake zuwar mata kansa tsaye. Hakan ya ƙara jefa Abra cikin tsoro da firgici, ko muryar Adnan taji sai gabanta ya faɗi hankalinta ya tashi, ga tsananin damuwar rashin jin Muryar kowa daga gida dan ba ta da waya. Tana cikin wannan zullumin Dodon nata wato Adnan ya shigo, tana ganinsa jikinta ya hau rawa. A kausashe ya ce "In Allah ya kaimu anjima, su Hajiya Mama za su zo, idan kin ga dama ki yi wani misbehaving ki ga yadda zan yi dake". Ba tace masa ci kanka ba, ya gama maganganunsa ya fice. Kitchen ta shiga ta shirya girke girke, domin tarbar su Hajiya Mama, dan iyayen Adnan ba dai karamci ba. Sai azahar sannan suka zo, Abra taji daɗin zuwansu, sai dai a kallon Farko da Maman ta yiwa Abra, ta ga yadda yarinyar ta ƙara ramewa, tai duhu. Mama ba tace Komai ba, suka dinga hira da Abra, sai da zasu tafi sannan ta bi Abra ɗakinta ta kalleta tace "Abra, meke faruwa ne?" "Mama me kika gani?". "Abra alamu sun nuna akwai wata damuwa a ƙasa, menene ke faruwa?". "Ai kamar Mama ta taɓo mata abun da yake mata ƙaiƙayi, ta fashe da kuka, sai da tayi mai isarta sannan Mama ta ce "gaya mini ina jinki" Abra ta ce "Mama ni gida nake so, gida zan koma". "Haba Abra, saboda me?" "Bakomai, kawai gida nake son komawa" Mama ta ce "kiyi haƙuri, haka Aure yake a hankali kowa yake sabawa, ke dai ki kwantar da hankalinki ki dinga ci kina ƙoshi". Ita Abra ma sam ba ta gane me Mama ke nufi ba. Bayan sun fito daga ɗakin Abra sai ga Adnan ya dawo. "Mama wai tafiya zaki yi ba tare da kin ganni ba, wato tunda kinga Angel shikenan" "Eh shikenan Mana, kai ɗin da kusan kullum sai ka zo gida ka isheni, ai gara in zo in ga 'ya ta' Adnan ya kwaɓe fuska ya ce "My Angel kin ƙwace mini Mama, gaskiya kishi nake, haka ake yi". Kallon Adnan take da mamaki, a gaban mutane yayi ta nuna mata kulawa, amma daga ita sai shi, yayi ta cuzguna mata. Ya dage a kan Mama ba zata tafi yanzu ba, ƙanwar Mama da suka zo tare, wato Hajiya Bilki ta ce ita kam tafiya za ta yi, ta bar yara a gida. Abra ta bawa Mama da Adnan guri dan su yi hira. Mama ta kalli Adnan ta ce "My son, magana nake son mu yi" Ya ɗan yi jimm, yayi zaton ko Abra ta gayawa Mama wani abu, ya maze ya ce "To Hajiya". "Duk da bai kamata in maka katsalandan a lamarin Aurenka ba, amma ni uwa ce, kuma 'ya mace ce, yarinyar nan Abra, ta rame da yawa, na yi imani da Allah idan iyayenta suka ganta haka ba zasu ji daɗi ba, dan ba a haka suka baka 'yar su ba. Kai kuma kalli yadda ka yi wata uwar ƙiba, kai tsaf da kai, na yi magana da ita, amma ba ta ce mini komai ba, sai kuka tana cewa ita gida. A ɗan abin da na fuskanta, kana takura yarinyar nan Adnan". "Mama takurawa kuma? Me nake mata? Ki tambayeta ni abin da nake mata". Mama ta ce "Ƙaniyarka, ni zaka mayar ƙaramar yarinya, ai ka gane sarai me nake nufi" sai kuma ya kama sosa ƙeya yana ɗan basarwa. "Ba ina nufin yi muku shishshigi bane, amma dan Allah a dinga ɗaga mata ƙafa, ramar ta yi yawa". "To Hajiya" ya amsa cikin jin nauyi. "Yawwa kirawo mini ita muyi sallama" Adnan ya kira Abra dan suyi sallama da Mama, amma Abra ta fara kuka ta ce "Mama dan Allah zan biki". "Abra kiyi haƙuri, na yi masa faɗa, ba yadda za'a yi da aurenki ki bar gidanki ki biyo ni". "Haba Angel, ya kike haka kamar wata ƙaramar yarinya, me kike so in sai miki? Ku mu fita yawo yau" yayi Maganar yana rungumeta a jikinsa cike da kulawa. Abar kuwa sororo tayi tana kallon Adnan, suka yiwa Mama sallama, har mota ta tafi. Yana dawowa ya tarar da ita a falo, ta na ta gyarawa, ya zuba mata ido, tana ɗagowa suka haɗa ido, sai da ta sha jinin jikinta. "Shi ne ki ka kawa mahaifiyata ƙarata ko?". Ta shiga girgiza kai ta ce "Wallahi ban kai mata ƙararaka ba". "Idan ma ƙarar ta wa ki ka kai mata, ko sani, ba yadda za a yi in sanya kuɗi na in Auroki in kasa karɓar hakkina na Aure, ba dan iya fansa kawai na Aureki ba, na Aureki ne dan ina da buƙatar yin hakan ne. Kuma duk in da baiwa take a ubangidanta yana da iko a kanta, dan haka ba zan fasa ba sai dai ki mutu. Kuma Wallahi ki ka bari wani ya san irin zaman da nake da ke, sai kin gane shayi ruwa ne" Abra tayi shiru, tana sake jinjina azabar rashin imani irin na Adnan. Ba ta karaya ba, ta bishi ɗakinsa, ta tarar yana ƙoƙarin shiga wanka, ya kalleta ya ce "Uban me kika biyo ni ki mini". "Baby alfarma nake nema". "Ina jin ki". Ta ƙaraso gabansa ta durƙusa a kan gwiwowinta ta haɗa hannayenta ta ce "Idan kana son ganin Annabin tsira, ka bani wayata, ko ka haɗani da Abbi na a waya, dan girman Allah". "Annabin tsira insha Allah zan ganshi, wayarki kuma ta tafi kenan, dan ba zan baki waya ki dinga Magana da Wannan mayen naki ba, Suleiman yake ko wa?" "Dan Allah, ka taimaka magana nake son yi da Abbi na dan Allah" wayar Adnan ce ta fara ringing, ya ɗauka ya duba, yayi murmushin mugunta ya ce "Gaskiya wannan baban naki na riƙo yana ji da ke, dama shine babanki mahaifi, da kin ji daɗi". Ya gyara tsayuwarsa ya ɗaga wayar, suka gaisa da Adnan. Abbi ya ce "Adnan anya kuwa lafiya, yarinyar nan mahaifiyarta da kkanninta duk sun isheni ba'a samunta a waya, ni jikina yana bani kamar ba ta cikin farinciki, a weekend zan zo in ganta, kai kan ka wayarka ba ta shiga". "Abbi Abra tana lafiya ƙalau fa, ga ta ma a kusa dani". "Bani ita maza". Ya miƙawa Abra wayar jiki na rawa ta karɓa "Hello Abbi na". "Na'am Babyna, yaya akayi bana samun ki, kina lafiya kuwa?". "Abbi, Abbina" tayi Maganar tana kuka. "Ina jinki Abrana, mai yasa kike kuka? Meyafaru ni jikina gaba ɗaya ya gama bani babu lafiya" Abbi yayi Maganar a rikice. "Abbi wai da gaske ba kai ne babana ba?" Ras!!! Gaban Abbi ya faɗi, dan yaji maganar ta ta a bazata. "Waye ya gaya miki wannan banzar Maganar?". "Abbi dan Allah ka gaya mini, ba kai ka haifeni ba ko? Wai tsinto ni ka yi ka riƙeni". "Abra waye ya gaya miki wannan maganar? Naima ce ko?" Abbi yayi Maganar cikin wata irin razananniyar tsawa. Abra kasa magana ta yi, sai kuka. Adnan ya fizge wayarsa ya ce "Abbi kaji dalilin da ya sanya na ƙwace wayarta, na kuma hanata wayata ku yi magana, ta isheni da koke koke, ban san a ina ta ji wannan maganar ba. Ai Abbi bai ba shi amsa ba, ya katse kiran. Adnan yayi murmushi ya ce "Ina fatan ko wannan rikicewar da Abbin naki yayi, ya isa ya tabbatar miki da ba shine ya haifeki ba, saboda kin gano sirrin da ya ɓoye duk ya rikice, tabbas yana miki so irin na 'ya da uba". Abra ta ɗora hannunta a ka ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na shiga uku, waye babana? Dan girman Allah ka gaya mini wanene ya haifeni, suwaye iyayena" ta riƙe hannun Adnan tana Magana cikin kuka. Shi ba halin da take ciki ne ya dame shi ba, sai yadda ƙamshin turarenta da yadda kwalliyarta suka yi turning ɗinsa on ne suka dame shi, kamar kullum yayi abun da Allah ya nufe shi da yi, duk da halin da Abra take ciki na damuwa da tashin hankali. "Kaji tsoron Allah, ko tausayin halin da nake ciki baka ji? Buƙatarka ce kawai a gabanka" tai maganar tana kuka. "Halin da kike ciki ke ya dama ba ni ba, dan haka damuwarki ba zata hana ni jin daɗin rayuwata ba. Mami ta rasa sukuni balle mafita, gaba ɗaya gidan yayi mata faɗi, tana zaune tana ta jujjuya takardar da Salman ya bari, ta kira Anty Suwaiba ko zata samu mafita, bayan ta gama korawa Anty Suwaiba bayani, Anty Suwaiba ta jinjina kai ta ce "Taɓɗijan, shi Salman wannan wane irin hali ne? Daga wannan sai wannan, ki sanar da mahaifinsa kawai". "Anty Suwaiba ta yaya zan sanar da mahaifinsa, bayan bai san na gayawa Salman ɗin cewar bani na haifi Abra ba?". Anty Suwaiba ta ce "kin ga wannan maganar ba ta waya bace, kinga bana gida amma insha Allah wajen jibi zan shigo gidan naki". 'To shikenan, Allah ya kaimu" Mami na gama wayar, taji jiniyar motocin sojoji, alamun Major ya sauka a gari. Mamaki ne ya kamata, ta fito falo, kamar an wurgo shi haka ya shigo a birkice. Mami ta ce "Yallaɓai lafiya kuwa? Yana ganka a gida yau ba ko sanarwa?". Wani mugun kallo ya yiwa Mami ya wuce part ɗin sa. Binsa ta yi cikin mamaki "Yallaɓai dan Allah ka gaya mini meke faruwa?" Ko kallon in da take bai yi ba, ya cigaba da abin da yake gabansa. Da yaga zata dame shi, ya buga masa wata razananniyar tsawa, wadda ba shiri ta bar masa ɗakin, tana mamakin meke faruwa. Kusan awanni biyu da dawowar Major, ya sami Na'ima a ɗakinta yana binta da wani mugun kallo ya ce "Na'ima, ubanwa ye ya sanya ki gayawa Abra cewar ba mune muka haifeta ba?" Dafe ƙirji tayi tana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ita Abran ce ta ce maka ni na gaya mata?". "Shut up! Sai ta gayamini cewar ke ce? Ta kirani tana kuka cewar wai ba mu muka haifeta ba, shiyasa mijinta ya ƙwace wayoyinta saboda kar ta kira ta ɗaga mini hankali? Waye ya sa ki gayawa Abra am talking to you". "Wallahi ni ban gaya mata ba, bani bace ba" "Ashe har kin manta sharaɗin dana sa miki akan, daga ranar da wani ya san bamu muka haifeta ba, ta dalilinki a bakin Aurenki ba? Ashe zaman haramci muke yi, ki tattara ki bar mini gida na sake ki, saki ɗaya". "Na shiga uku, baka sakeni tun da ƙuriciyata ba sai yanzu, da girmana har na kai 'ya ɗaki". "Ƙarya ki ke yi, munafuka" "Ni kake kira munafuka, a kan laifin da ba...... "Shut up! Kar ki bari in dawo ɗakin nan in tarar ba ki tafi ba. Har ya juya zai fita ya hangi takarda a ƙasan madubi, da irin signing ɗin Salman. Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via  0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 08081012143 [10/14, 1:45 PM] Abk: Ɗauke idonsa ya yi daga kan takardar ya juya da niyyar fita amma sai ya ji zuciyarsa na son sanin me takardar ta ƙunsa, ko don yana cikin kewar ɗan nasa ne? A hankali ya juyo ba tare da ya kalli inda Na'ima take ba, wadda ke gunjin kuka kamar za ta shiɗe. Sunkuyawa ya yi tare da kai hannu zai ɗauka, kamar an cillo kibiya daga cikin baka haka ya ga Na'ima ta yi tsalle ta dira a gabansa, da mamaki yake kallon ta bai ce komai ba. Cikin bugawar zuciya Na'ima ta matsar da takardar gefe cikin pretending irin ba ta san ta yi hakan ba. Wani mugun kallo ya watsa mata ya miƙe ya ɗauki takardar ya fara karantawa a zuci. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, na shiga uku!" Naima ta faɗi haka a fili cikin tsananin ruɗewa da rawar jiki. Kallo mai kama da na tsana Abbi yake jifan ta da shi, cikin matuƙar takaici da ɓacin rai ya ce. "Me takardar nan take nufi Na'ima?" Kasa magana ta yi sai rawar baki take tana haɗa hannayenta alamar roƙo. "I'm asking you Na'ima me kika aikata? Wacce irin soyayya Salman yake nufin yana yi wa Abra?" Ya yi maganar cikin ƙaraji da tsawa, wanda hakan ya ƙara firgita ta." Cikin rawar murya ta ce. "Don Allah My Man ka saurare ni, wallahi ban aikata abin da kake zargi na da shi ba." "Wannan takardar kuma ita ta ƙirƙiri kanta kenan?" Ya yi maganar cikin hucin ɓacin rai. Rasa abin cewa ta yi sai matsanancin kuka da ta fashe da shi cikin nadamar faɗawa Salman ba su suka haifi Abra ba, da ta san haka al'amarin zai juye mata da ba za ta soma faɗa masa ba. "Wannan takardar ta ƙara tabbatar mini da ke kika faɗa wa Abra ba mu muka haife ta ba kamar yadda kika faɗa wa Salman, tabbas biri ya yi kama da mutum, yanayin Salman kafin ya tafi china irin na wanda yake cikin tsantsar damuwa ne, na so na fahimci hakan, amma saboda kin san me kika shirya da na faɗa miki sai kika ce ba haka ba ne, miskilanci kawai ya koya. Kin cuce ni Nai'ma da kika bari yaran nan suka san su ba ƴan'uwan juna ba ne, kin kuma cuci kanki, domin ba zan ƙara zaman aure da ke ba har abada, I hate You!" "Khamal ni ce fa, ni ce Na'imanka don Allah kar ka mini haka, na san na yi kuskure amma ka yafe mini, ka tsaya ka fahimce ni." Na'ima ta faɗi haka tare da riƙe ƙafafuwansa. Hamɓare ta ya yi a zuciya ya ce. "Last maganata da ke, na ba ki 30 minutes ki tattara kayanki ki bar mini gidana." Bai jira cewarta ba ya fice daga ɗakin, part ɗinsa ya nufa ya shiga bedroom ɗinsa ya kulle ƙofa. Innalillahi.... kawai yake maimaitawa a cikin ransa cikin tsantsar damuwa, sai taune lips ɗinsa yake tamkar zai tsinka shi, kyawawan fararen idanuwansa sun yi jajur saboda tsananin ɓacin rai. Ji yake kamar ya rufe Na'ima da duka saboda baƙin ciki, damuwarsa halin da Abra take ciki a yanzu, ya san ba ƙaramar damuwa za ta ɗora wa kanta ba. Tsaki ya ja cikin jin haushin kansa na amince wa Na'ima da ya yi akan Abra, gaskiya ne da aka ce bakin da ya furta ƙi ba zai taɓa furta so ba. Amma me ya sa ya kasa gane pretending kawai Na'ima take? Duk da kasancewar shi mai saurin fuskantar abu. _ƙaddara_ zuciyarsa ta ba shi amsa. Hand bag kawai Na'ima ta ɗauka ta saka hijabi tare da zira takalmi ta fice cikin tsananin tashin hankali. Domin ba ta ji a ranta ta bar gidan Khamal kenan, zuciyarta ba za ta iya ɗaukar hakan ba, tana son Mijinta ba ta son rabuwa da shi. Aunty Suwaiba ce ke kaikawo a parlour bayan Na'ima ta gama zayyane musu abun da yake faruwa. Cikin damuwa ta ce. "Wautarki ta yi yawa Na'ima, abun da nake jiye miki kenan tun farko, shi ya sa nake tausar ki akodayaushe akan ki dinga danne ƙiyayyar yarinyar nan da kishinki a kanta, amma ki ka ƙi ji, gashi nan ya sake ki." Cikin kuka Na'ima ta ce. "Wallahi Aunty ba ni da masaniyar abun da yake zargi na da shi, ni ban faɗa wa yarinyar cewa ba mu muka haife ta ba har yau." "To waye ya faɗa mata? Ni dai a sani na ko Kaduna ba ku taɓa zuwa ba, balle a ce wani ya san ku a can ya faɗa mata. Kuma abubuwan da kike yi wa yarinyar ne ya saka ko da ba ke kika faɗa mata zai ce ke ce." "Dan Allah Aunty ki bar ni da maganganun nan, in ji da abun da yake damu na mana, haba." "Na bar ki Na'ima, amma ko kin ƙi ko kin so shegen kishin da ɗora wa kanki ne ya jawo miki." A ƙufule Mama ta ce. "Wai wannan maganganun na mene ne? Abin da ya faru ya riga ya faru sai dai mu nemo hanyar da za a gyara shi, tunda kin ce saki ɗaya ne ko?" Ta ƙarashe maganar idanunta a kan Na'ima. Gyaɗa mata kai ta yi tana sharar hawaye. Duk wannan fafutukar da boloƙon da ta yi saboda Abra ta bar musu gida amma ƙarshe abin a kanta ya ƙare, tana murna shirinta ya tafi daidai ashe zai warware ne tas. Tana ji Adnan ya shiga toilet ya yi wanka ya fito amma ita ta kasa ko da ɗaga ɗan'yatsanta ne, wani irin nauyi take jin kanta ya yi mata, ga duk jikinta dake mata ciwo saboda gajiyar da Adnan ya tara mata. Ita kaɗai ta san me take ji a cikin ranta na tsantsar damuwa, addu'a take yi Ubangiji ya sa mafarki take ba gaske ba ne ABBI BA SHI NE YA HAIFE TA BA. Zuciyarta ta kasa yarda da hakan duk kuwa da yanda Adnan yake ta nanata mata, tabbas a yau ta yarda Adnan ba ya ƙaunarta kamar yadda yake furtawa, tunda har iya faɗa mata abin da zai tarwatsa mata zuciya. Idanunta a kansa yana shiryawa cikin kwanciyar hankali da nishaɗi, alamun rayuwar tana yi masa daɗi. Wasu hawaye masu ɗumi ne suka shiga kwaranya daga cikin idanunta. Cikin dauriya ta tashi zaune da ƙyar ta ja rigarta ta saka, hannunta dafe da ƙirjinta saboda nauyin da ta ji ya yi mata, cikin haki ta ce. "Adnan! Don girman Allah dan darajar iyayenka ka taimake ni ka sauwaƙe mini aurenka, ba don ni ba." Sai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya da karyar da zuciyar duk wani mai imani. Wani mugun kallo ya wurga mata cikin tsawa ya ce. "In kin ga kin bar gidan nan to gawarki a ka fitar." Kallon shi ta yi tana son ta yi magana amma ta kasa. A tsawace ya ce. "Malama ki tasar mini daga kan gado da najasa a jikinki, ki kuma gyara mini shi kafin warin abin da kika fitar ya hautsina mini ciki." Duk da yanayin da take ciki amma sai da ta yi wani murmushi da ya fi kuka ciwo sannan ta yunƙura ta sauka daga kan gadon. Kamar yadda ya umurce ta, ta kama zanin gadon da nufin cire shi amma sai ya bar hannun nata saboda rawar da jikinta yake yi kamar ana kaɗa mata gangi. Dafe kanta ta yi da sauri saboda juyawar da ta ji yana mata, ƙofa ta nufa don ta fice zuwa ɗakinta, kafin ta kai ga yin hakan ta faɗi a ƙasa sumammiya. Adnan dake kallon ta ya ja tsaki cikin takaici ya ce. "Yarinya sai ka ce mai farfaɗiya, abu kaɗan sai ki zube salon ki janyo wa mutane masifa." Kamar wata Dabba haka ya ja ta ya fitar da ita parlour ya juya ya koma ɗakinsa ba tare da ya ƙara bi ta kanta ba. Sai wajen ƙarfe ɗaya na dare Adnan ya fita dan da ya haɗa coffee, a inda ya bar ta ya tarar da ita kwance tamkar gawa, tsaki ya ja ya ƙarasa ya buɗe fridge ya ɗauko ruwa mai sanyi ya shiga sheƙa mata daga tsaye, kusan 3 minutes sannan ya ji ta ja dogon numfashi tare da motsawa. Taɓe baki ya yi ya tafi ya bar ta. A hankali ta buɗe idonta da suka yi mata nauyi ta bi bayansa da kallo, ta daɗe a haka sannan ta miƙe da ƙyar ko gani ba ta yi sosai ta shiga ɗakinta ta faɗa kan gado. Rabi da rabi baccin Abbi ya kasance a yau saboda tunanin halin da Abra take ciki. Washegari da sassafe ya shirya direbansa ya kai shi airport ya bi Flight ɗin ƙarfe takwas zuwa Kaduna. Wata dattijuwar mata ce zaune a gaban gadon marasa lafiya da wani tsoho yake kwance, ta yi tagumi tana kallon yanda numfashisa yake fita da wani irin sauti gami da ɗagawar da ƙirjinsa yake yi, lokaci zuwa lokaci tana share hawayen dake fita daga cikin idonta. A hankali ta ɗaga kanta tare da amsa sallamar da wani matashi yake yi a kusa da ita. Cikin damuwa ta ce. "Ba su zo ba ko Musa?" Numfashi ya sauke cikin damuwa ya ce. "Ba su zo ba Inna, sai waɗannan masu fararen kayan ne kawai." "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, kalli yanda numfashin Malam yake fita fa musa, wallahi gabana sai faɗuwa yake, ina tsoron kar mu rasa shi." Inna ta faɗi haka cikin kuka. "Ki yi haƙuri Inna, insha Allahu Malam zai samu lafiya, cuta ai ba mutuwa ba ce. "Ba za ka gane ba Musa, ka kira masu fararen kayan don Allah su zo ko za su iya yi masa wani taimakon." Wata mata dake zaune a kusa da gadonsu tana jinyar nata mai gidan ta ce, "Sai haƙuri Baba, haka muke fama da likitocin nan, ba sa son zuwa da wuri, Nurses ɗin nan kuma ba wani abu za su iya ba, sai dai kawai su ta ƙara wa mutum ruwa da ɗan abun da ba za a rasa ba." "To me ya sa su likitocin ba sa zuwa da wuri? tun cikin dare Malam yake wannan abun, waɗanda suka yi aikin kwana sun yi masa gwaje-gwaje sun ce mu jira sakamakon idan likitan da zai karɓi aikin safe ya zo zai ba mu, muna ta jira har ƙarfe tara amma babu wanda ya zo." "Hmm, asibitin gwamnati kenan, sai haƙuri, ku yi ta addu'a kawai. Dan shi wannan likitan ma da zai duba shi sau ɗaya yake zuwa a sati" Girgiza kai Inna ta yi ta ce. "Allah Sarki takaka, shikenan bari mu jira." Sai Asuba sannan Abra ta iya tashi ta shiga toilet ta yi wanka tare da ɗauro alwala ta fito ta yi sallolin dake kanta a zaune. Sosai ciwon da kanta yake mata ya tsananta, tamkar zai tarwatse haka take ji. Ga wani irin zafi da raɗaɗi da zuciyarta ke mata. Tana idar da Sallar ta koma kan gado ta ƙudundu ne a cikin bargo saboda sanyin da ta ji yana ratsa ta, wani irin zazzaɓi mai zafin gaske ne ya rufe ta wanda ya haifar mata da rawar ɗari. A haka Adnan ya shigo ɗakin ya tarar da ita tana numfarfashi. Cikin nuna ko in kula da halin da ya gan ta a ciki ya watsa mata singlets and boxes ɗinsa a jikinta tare da ba ta umarnin tashi ta wanke masa a lokacin. Ɗaga kai ta yi da ƙyar ta dube shi amma ta kasa magana, hawaye ne kawai yake zuba daga cikin idonta. Ƙoƙarin jan bargon da ya yaye mata ta yi amma ya riƙe bargon tare da buga mata tsawa da faɗin. "Tashin ne ba za ki yi ba ko me da kike ƙoƙarin jan bargo? Wato ga mahaukaci yana magana ba za ki tashi ki yi abin da na saka k....." Ƙarar doorbell ta hana shi ƙarasa faɗar zancensa. Ƙwafa ya yi tare da nuna ta da hannu ya ce. "Na dawo na tarar ba ki tashi ba, wallahi na lahira sai ya fi ki jin daɗi." Ya ƙarashe maganar tare da yarɓar mata da bargon a fuska. Lumshe idonta kawai ta yi tana jin yanda zuciyarta ke bugawa da sauri da sauri. Adnan da matsalarsa ba su ne damuwarta ba a yanzu, damuwarta kawai sanin gaskiyar abin da Adnan ya faɗa mata na cewa ita TSINTACCIYA ce, Abbinta mafi soyuwa a gare ta ba shi ya haife ta ba, ba ta fatan hakan ya kasance, domin ta san zuciyarta ba za ta iya ɗauka ba bugawa za ta yi. Addu'a take Allah ya sa Abbinta ya musan mata ya ce ba haka ba ne, domin ta ƙudurce a ranta duk wanda zai faɗa mata ba za ta taɓa yarda ba, ko da Mami ne da Salman kuwa, Abbi kawai zai tabbatar mata da gaskiya ne ba shi ya haife ta ba ta yarda. Adnan yana buɗe ƙofa kamar a mafarki ya ga Abbi tsaye cikin wani irin yanayi, sai da gabansa ya faɗi amma bai nuna hakan ba, murmushi ya yi tare da yi masa iso zuwa cikin parlour'n cike da girmamawa. Sai ƙarfe tara da rabi wani likita ya zo ya ƙara dudduba jikin malam, bayan ya gama ya ce su Inna su same shi a office. Bayanin ciwon dake damun Malam ɗin ya yi musu wato ciwon zuciya wanda already sun san da shi. Ya ƙara da faɗin, "Ciwon nasa ya yi tsanani sosai, don haka ana buƙatar yi masa aiki cikin gaggawa. Amma gaskiya wannan Asibitin ba mu da kayan aikin, sannan likitan da yake aikin bai ƙaraso ba" A ruɗe Inna ta ce. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! To likita ku yi masa aikin mana, don Allah ka taimake mu ka ceto mana rayuwarsa, idan muka rasa shi za mu shiga cikin wani hali, shi ne bangon rayuwarmu." Cikin son kwantar mata da hankali likitan ya ce. "Kar ki damu Hajiya, zai samu lafiya insha Allahu, sannan kuma a nan asibitin ba mu da kayan aiki masu kyan da za mu yi masa aiki, amma zan tura ku wani babban Private Hospital wanda da yardar Allah za a yi aikin successfully." "Likita ina ne firaben honfital kuma?" Inna ta tambaye cikin damuwa. "Asibitin kuɗi kenan, sunansa G.Y BULAMA, suna da ƙwararrun likitoci gami da kayan aiki masu inganci." "Asibitin kuɗi fa ka ce ɗana, ai ba mu da kuɗin da za mu biya, na gwamnatin ma da ƙyar muke iyawa." "To Hajiya, in dai kuna son samun lafiyar shi gaskiya ku je can ɗin." Inna za ta kuma magana Musa ya hana ta da faɗin. "Shikenan likita, mun gode sosai." Sannan ya dubi Inna ya ce. "Mu je Inna." Bayan sun fita Inna ta saka kuka ta ce. "Allah ka fitar da mu daga cikin wannan tashin hankalin, yanzu Musa ya za mu yi?" Cikin damuwa Musa ya ce. "Inna mu je can inda ya ce manan kawai, don gaskiya likitan nan ya faɗa mana a asibitin nan ba yi masa aikin za su yi ba, kin manta yanda aka yi ne wancan karon, kullum cikin saka mana ranar aikin suke amma ba su yi ba har Allah ya ba shi lafiya muka koma gida." Gyaɗa kai Inna ta yi ta ce. "Haka ne, to amma Musa kuɗin nake ji, ba mu san nawa za su ce mana ba." "Allah ba zai hana mu yanda za mu yi ba, mu je ya yi mana kwatancen asibitin." Jiki a sanyaye Inna ta ce. "Toh, addu'ata kullum kar Allah ya karɓi ran malam ba tare da ya sanar da mu aihinin gaskiyar al'amarin nan ba, domin mu san ta inda za mu fara bincikawa, tunda komai daren daɗewa sai gaskiya ta yi halinta." "Insha Allahu Malam zai samu lafiya har ya warware komai da kansa kamar yadda yake da buri, ki kwantar da hankalinki Inna, mu dai mu yi ta addu'a Allah ya ba shi lafiya kawai." "To amin amin .Amma naji ance shi likitan da zamu je gurin nasa yana zuwa nan duba marasa lafiya, ba za mu jira shi ba?" Musa ya ce "Inna ance yau babu lallai ya shigo, kawai gara mu bishi can ɗin, bari in je sun ce zasu bamu wata takarda mu tafi da ita". Inna ta ce "Shikenan, je ka dawo mu tafi". Musa ya juya ya fice, yayin da mara lafiyan ke ta cigaba da kakari. Kamar yadda aka yi musu kwatance haka suka isa GY BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY. A gaggauce Musa ya shiga cikin Asibitin, ya fito da Wheel chair, suka ɗora Malam a kai, ya tura shi zuwa cikin Asibitin. Gaba ɗaya Musa a rikice yake, bai tsaya saurarar kowa ba ya fara bulayin in da zai kai Malam ya kwantar. Wata Nurse ce tayi masa tsawa ta ce "Malam lafiya, ya zaka zo da mara lafiya kawai ka wuce mu?" Musa ya ce "Yi haƙuri, wallahi duk a gigice nake ne, shiyasa daga Asibitin cikin gari aka turo mu nan, aka ce mu zo muga likita nan". "To ai ba Chemist bane nan, ba haka kai tsaye aka ganin likitan ba, zaku fara buɗe file dubu goma". Musa yayi turus, ya ce "bakomai a buɗe masa". Inna cikin damuwa ta ce "Musa idan ka biya dubu goma, abun da zai yi saura a hannunmu ba shi da yawa". "Bakomai Inna, Allah zai bada yadda za'a yi". Ya cire kuɗi ya miƙa, ya biya aka buɗe File ɗin. Nurse Jamila ce ta taho, hannunta riƙe da wasu files, ta kalli Musa ta ce "Bawan Allah, tura dattijon nan daga gefe mana, ka bar shi yana ta haki haka, tallafo kansa ka maida shi gefe". Musa yaji daɗin yadda Nurse Jamila ta kula su da nuna wa mahaifinsu kulawa. Ya ce "Wallahi hajiya a rikice muke ne, mun kai shi babban Asibitin birni, aka ce mana likitan da yake zuwa duba masu irin rashin lafiyarsa sau ɗaya yake zuwa a sati, kuma yau ba zai zo ba, shine suka turo mu nan da wannan takardar". Nurse Jamila ta karɓi referral later, sannan ta kalli su Musa, wani irin tausayinsu ya kamata, ta ce "Kaga, ga Emergency room can, ku shiga da shi ku kwantar, bari na je na kai wa likitan". Musa kamar zai durƙusa wa Jamila abinka da mutumin ƙauye "Mun gode hajiya, Allah ya saka da alkhairi". "Ba komai ku je, ina zuwa". GY BULAMA ne ya gifta ta can gefensu, yana cikin rigarsa fara ƙal ta aiki, sai zuba ƙamshi yake yi, yana takunsa cike da ƙasaita, kyawunsa ya ɓoye tsufansa ma'aikatan suna masa sannu da zuwa, yana ɗaga musu hannu tare da yi musu sannu da aiki". Musa bai lura da abin da Malam ya ƙurawa idanu ba, sai ji ya yi Inna tana cewa Alhamdilillah, Malam ya buɗe ido. Suna masa sannu haka suka kai shi Emergency suka kwantar. A Office Jamila ta samu MD, ta yi masa bayanin Komai. Ya karɓi takardar ya duba, ya ajiye takardar ya ce "Kije ki gaya musu, yana buƙatar ayi masa aiki da gaggawa, kuma kin san da likitoci turawa muke aikin nan, dan haka zasu biya 2.5millon, wani rami ne a zuciyar tasa. Nurse Jamila jiki a sanyaye ta ce "Doctor, Ba su da wannan ƙarfin, dan da alama daga karkara suka zo". "Well sai ku sallame su". "Amma da mun je ka gan shi, ko wani taimakon gaggawa ne sai ka rubuta a yi masa, ba ma sallame su haka ba, yana cikin mawuyacin hali". "Mai kike so in yi musu? Kin san muddin ba aikin nan aka yi ba mutuwa zai yi, dan haka ku sallame su, kar ya mace mana a nan a zo ana yadda za ai a fita da gawar". "Please doctor, ko yaya idan suka ga an basu kulawa ko mutuwa ya yi, ba za su ce an wulaƙanta su ba, ko oxygen a sa masa a bashi wani abin da zai samu releif". "Idan za su biya sai a sanya masa, in kuma ba haka ba maza ku sallame su". "Please doctor...." "Jamila out of my office, Asibiti na ba na taimako ba ne, na neman kuɗi ne". "Amma.... "Ohhh my God, Jamila kina daf da kai ni bango a Asibitin nan, get out". Jamila ta fita jiki a sanyaye, Musa na ganin ta ya ce "'yar uwa zo kiga abin da yake yi, dan Allah ki kira mana likitan ya duba shi" Musa ya yi Maganar kamar zai fashe da kuka. Jiki a sanyaye Jamila ta ƙarasa, ta tarar da dattijuwar matar ta riƙe hannun dattijon da yake ta kokawa da numfashi. Wani irin tausayinsu ya sake kama ta. Duk da wannan hali da dattijon ke ciki, nuna musu wani guri yake yana faɗin "'yar Baba" "Me 'yar Baban tayi Malam, ka kwantar da hankalinka, in Allah ya yarda lafiya za mu koma gida, ka ga 'yar Baba". Jamila ta ce "Ku yi haƙuri, yana duba wani mara lafiyan ne, idan ya gama zai zo". "Ba wani likitan da zai zo kansa ne?" Dattijiwar tayi maganar tana share hawaye. "Shikaɗai ne likitan zuciya, bari in koma in gani ko ya gama". Jamila ba ta karaya ba, ta koma gurin Bulama, amma ya balbaleta da masifa, ya ce "Ba zan je kansa ba, ko naje ba zan hana shi mutuwa ba, dan haka ki je ki yi abin da na ce ki sallame su, su je su kai shi wani wurin". "Doctor ba zan iya faɗa musu haka ba, dan Allah ko ganin ka ne ka je su yi a kan mara lafiyan su, sai ka gaya musu da bakinka". "Fitar mini daga office, wace irin masifa ce haka, shi kansa doctor Shamsu zan ja masa kunne, Asibitina ba na taimako bane, ya daina turo mini Mutanen da ya san they can not afford our services". Jamila ta kuma komawa, Musa ya tare ta yana faɗin "Dan Allah ni ki nuna mini likitan in roƙe shi, kar mu rasa shi, yana da wata 'ya da idan muka rasa shi bamu san halin da zata shiga ba". "Ɗan uwa kayi haƙuri, likita ba zai iya cire masa ciwon ba, sai dai ya taimaka masa, mu je in ga idan da Allurar da zan iya yi masa ko bacci ya samu". "Suna shiga ta tarar Wannan dattijo ya kai gargara, sai numfarfashi yake yana kiran " 'Yar Baba, ki zo....ki zo. ...kusa da ni, abi....abin da.....zan faɗa mu.......muku.... 'yar Baba". Jamila ta ce "wace wannan 'yar baban da yake ta faɗa?" Musa ya ce " 'yar sa ce, ku taimaka mana, Wallahi zamu iya yin rashi biyu, mu rasashi mu rasata, a duniya soyayyar da yake mata ba kowa yakewa ba". Cikin hanzari Nurse Jamila ta fara ƙoƙarin neman allurar da za ta yi wa dattijon, idan yaso ko me doctor zai yi ya yi. Sai dai kash tana dawowa ta tarar Dattijon ya yi kalmar shahada ya cika!!!. A ɗaki Adnan ya samu Abra ya ce "Sai ki tashi, ga babanki na riƙo can ya zo" duk tsananin jiri da zafin zazzaɓin da ke jikin Abra, ba shiri ta miƙe ta sakko zata fita. "Ke mahaukaciya, ba fa babanki ne mahaifi ba, babanki ne na riƙo haka zaki fita da wannan rigar? Wuce ki wanke fuskar ki, ki sanya kaya". A gaggauce ta iya dafa bango ta zura doguwar riga tayi falo da sauri, tana zuwa ta zube a jikin Abbi tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka. Cikin jarumta Abbi ya ce "Haba Sweetheart, kinga yadda kika rame kuwa? Kin yi duhu haka meke damunki?". Adnan da ya kamile a gefe ya ce "Ai Abbi tun da aka yi Auren nan a haka muke, ko Abincin kirki ba ta iya ci, ba bacci kullum cikin kuka, na rasa a ina ta ji wannan mummunar Maganar". Abra har mamakin makircin Adnan take, kamar wani mace, amma dayake ba ta tashi take ba, cikin kuka ta ce "Abbi, tun da aka kawo ni, ba ka zo ka ganni ba, Mami ba ta zo ba, su Ammi ma haka, Faris ɗina ma.... Sai ta sake rushewa da kuka". Abbi ya shiga goge mata hawaye yana faɗin "Am sorry daughter, kin san an naɗani a shugabancin kwamitin binciken General Ibrahim, ko weekends bana iya zuwa, kina raina, Ammi ce kuma ta hana kowa zuwa, ta ce bai kamata daga kawoki a dinga yi muku sintiri ba, amma kiyi haƙuri" ya ƙarasa Maganar yana sake gyara mata zaman hearing aid ɗinta. "Abbi waye babana? Dagaske tsinto ni ka yi?" Abbi yayi shiru sannan ya ce "Waye ya gaya miki wannan maganar ne?". "Abbi ka daina binciken waye ya gaya mini, dan Allah Abbi ka gaya mini gaskiya" wata irin karaya da tausayin Abra ya kama Abbi. Abra ta fara ƙoƙarin sanya idanunta a cikin na Abbi, amma ya ɗauke kasa ya ƙi kallon ta yana girgiza kai. "Abbi kar kace mini zancen nan gaskiya ne? Abbi idan ba kaine babana ba waye?". "Abra bani da amsar tambayar ki" "Abbi ta tabbata tsinto ni kayi kenan?". "A'a ba haka ba ne Abra" "To Abbina yaya ne? Abbi baka yi mini ƙarya tun tasowata, hasali da kai nake koyi gurin gaskiya da riƙon amana, Abbi daga bakinka ne kawai zan iya jin abin da zai fidda zuciyata daga shakku komai ɗacinsa ka gaya mini zan dake". Adnan ya ce "Kinga Abra, ki ƙyale Abbi, daga zuwansa ba gaisuwa baki bashi Abinci ba, amma kin cika shi da tambayoyi marasa ma'ana". "Dalla ka rufe mini baki, kai mini shiru ba da kai nake ba, Abbi kayi Magana dan Allah". Ta yiwa Adnan Magana cikin tsawa. Abbi ya ce "Ya na ji jikinki da zafi haka? bari temperature jikinki ta saki sai mu yi Magana". "Abbi ta tabatta haka ne kenan? Zargina gaskiya ne? Abbi kar ƙwaƙwalwa ta ta juye in haukace, ka gaya mini dan Allah". Gaba ɗaya Abra ta fara fita hayyacinta, ga hawaye ga gumi ga majina, ga jikinta na rawar sanyi saboda zazzaɓi. "Haka ne Abra haka ne, amma...." Toshe wa Abbi baki tayi, ta fara maimaita "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" tare da miƙewa tsaye ta tsaya cak, can ta yi wata irin shaƙuwa tamkar fitar rai, ta faɗi a gurin! Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via  0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 08081012143 or 09047871750 [10/20, 12:46 PM] Abk: A kusan tare cikin gigita da firgici Abbi da Adnan suka fasa ƙara tare da faɗin "Abra!" Kafin Abbi ya Ƙarasa gareta Adnan ya rigasa gaba ɗaya ya sanya hannunsa tare da ɗagota zuwa jikinsa yana bubbuga ta tare da kiran sunanta. "Angel.. Angel... Angel" Ya faɗa yana girgiza ta da iya ƙarfinsa ganin ko motsi ba tayi sai ya kalli Abbi da Yake tsugune dab da su hannunsa riƙe dana Abra yana murzawa. Cikin tashin hankali Adnan ya dubi Abra hannunsa na rawa ya kama nata hannun, jin babu alamar jijiyar hannun na harbawa ya sanya shi kara kunnensa a ƙirjinta nan ma bai ji bugawar zuciyar ta ba, hannunsa ya mayar kan hancin ta sai a lokacin ya ji kamar huci na fita. Muryarsa na rawa sosai ya dubi Abbi ya ce. "Help me Abbi I don't want to lose my wife. Angel, open your eyes" Adnan ya faɗa a gigice,tare da nuna kulawarsa ga Abra wacce ke kwance kan cinyarsa. Seeing Abbi in front of him made him pretend to be worried about Abra's illness but in his mind it was all a plan. "Adnan tunda ta zo gidan ka tayi Irin haka?" Girgiza kai Adnan yayi still holding onto her yana shafa kanta ya ce. "No, she didn't, Abbi. we are happy. Tunda ta samu wannan maganar komai ya lalace,she is not happy, she has stopped everything, eating, talking, she is always crying in her room. Ta rame tai baƙi ta damu kanta. Mahaifiyata har ganin laifina tayi" Shiru Abbi yayi shi kansa, baya cikin hayyacinsa komai nasa ya tsaya dauriya kawai yake na ganin ya nuna babu komai, amma rashin iyaye a wannan rayuwa babbar illa ne ga mutum. Musamman ga Abra wacce ta ɗauki soyayya mai tarin yawa ta ɗora akan su, ba lallai ta jure zafin wannan ƙaddara ba, ya san tana da haƙuri da karɓar dukkan abin da ya zo mata da hannu bibbiyu. Amma wannan abu ne wanda kai tsaye ba zaka iya gane al'amarin sa ba, bayan tsintar ta da ya yi ita ɗin halattacciyar ƴa ce kamar ko wanne yaro? Ko kuma an sameta ne ta gurɓatacciyar hanya? Wannan abin shi ke kaiwa da dawowa cikin tunanin Major Khamal Khamis. "take her to the car" Abbi ya faɗa yana mai ɗauke kansa cike da kamewa ganin yadda Adnan ko kunya babu yake ta rungome ta a jikinsa. Kamar wanda yake jira haka ya sunkuceta zuwa mota. Abbi yabi bayan su, Adnan na baya da Abra, Abbi na gaba sai driver a haka suka nufi asibiti har lokacin babu inda yake motsi a jikinta tamkar gawa haka ta kasance kwance jikin Adnan. Shi kuma ya tsura mata shanyayyun idanunsa yana ƙare fuskarta kallo ganin yadda tai duhu sai dugun hanci, da wuyanta da ya ƙara tsayi. Abin mamaki kuma ƙirjinta Ma sha Allah a cike yake kamar ana ƙara masa girma kullum!. Har suka isa Asibiti Adnan yana riƙe da Abra a jikinsa,He shows his compassion and care for her. Da sauri Nurses suka amshi Abra daga hannun Adnan wanda da ƙyar ya amince ya bada ita, sai da Abbi ya bashi haƙuri tare da rarrashin sa, sannan ya bawa Nurse's ɗin ita. Kai tsaye Emergency suka shiga da ita, Oxcgyen aka sanya mata bayan sun kammala bincikar abin da ya ke damunta, kafin suka sanya mata drip tare da injection. Abbi na tsaye ya goya hannunsa a bayansa, tare da ƙorawa ƙofar Room da aka kwantar da Abra ido. Tunanin yadda zata iya fuskanta rayuwar ta a nan gaba yake, ba zata taɓa jurewa ba, zuciyar ta, ta raunata ainun. Yana tsaye wani Doctor ya fito yana goge zufa, da sauri Adnan ya miƙe yana kallon likitan baki na rawa ya ce. "Ya matata likita? she recovered from her coma,Don't say anything happened to my wife" Kafaɗar Adnan Likitan ya ɗan buga idanunsa akan Abbi ganin yadda shi kaɗai yake girgiza kai kafin ya maida ganinsa zuwa ga Adnan wanda yake da tabbacin shi ne mijin yarinyar da aka kawo, ganin kamar yafi Abbi ruɗewa da shiga tashin hankali kallo ɗaya zakai masa ka fahimci hakan a kwance saman baƙar fuskarsa. "pray for her, she will get relief from the pain that is bothering her". Ya ƙare maganar yana ƙara bubbuga kafaɗar Adnan can kuma ya ce. "Who is the husband of Abra Khamal Khamis?" Abbi dake tsaye ganin Adnan ya kasa magana sai ya kalli Likitan tare da nuna Adnan ya ce. "Gashi nan" Kallon Adnan Dr ya yi kafin ya ɗan yi tako ɗaya zuwa biyu yana faɗin "Oh! I see." "Follow me to my office" ya ƙara cewa yana yin gaba. Sai a lokacin Adnan ya buɗe baki da ƙyar ya ce "Ni? Ko Abbi?" Likitan ya tsaya yana duban Abbi kafin ya ce "Who is he to her?" "Her father" Cewar Adnan yana kallon ƙofar Room da Abran ke ciki, a zuciyarsa yana tunanin wani abu nada ban. "Oops. Both of you follow me" yana faɗin hakan ya shige Office nasa, Adnan ne ya fara yin gaba dai Abbi yabi bayan sa jiki a sanyaye, tare da tsoran abin da likitan zai faɗa masa wanda yake damun Abra a wannan karon duk da ya san larurar Abran amma yanzu tunaninsa ya saɓa zatonsa. A zaune ya samu Adnan a gaban Likitan shi ma ya ja Kujera ya zauna. Shiru sukai tare da zaman jiran jin ta bakin Likitan. Gyara zama Dr ya yi yana duban su, kafin ya zame farin Photochromic glasses ɗin idanunsa. Cikin nutsuwa ya du bi Adnan ya ce. "Before even bringing her to the hospital, what happened to her at home?" Ganin yadda Adnan ya rikice kamar ma baya cikin hankalinsa ya sa Abbi faɗawa Dr cewa faɗuwa tayi. "Haka kawai ta faɗi, or something was said to her that upset her. or something bad she heard or saw?" "It's almost like that Doctor" Abbi ya faɗa a taƙaice, domin baya son maganar tai tsayi har ya kai ga an maimaita zancan da kunnuwansa a yanzu basa buƙatar sake jinsa. Yana son Abra ta kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali. Dr bai damu da sanin abin da ya sanya Abra cikin halin suma ba, ya gyara zama in a serious tone ya ce. "She is having breathing problems, wanda duk sanda ta samu rikicewa ko wani abu ya sameta wanda zuciyarta ta kasa ɗauka zata iya suma a ko wanne hali take ciki. This is the reason why her lungs started having problems. Munyi ƙoƙarin Seeing that she regained consciousness, Allhamdulillah yanzu bacci take amma sai an dinga ki ya ye wa, domin wannan Matsalar babba ce banda Ubangiji ya taƙaita". "Thank you Doctor" "It's my responsibility. Allah ya bata lafiya" cewar Dr yana kallon Abbi da ya yi maganar. "Doctor I can see her now" "why not?" Adnan ya jinjina kai yana Miƙewa tsaye tare da faɗin. "Thank you" Kai tsaye Room da aka kwantar da ita ya nufa, a hankali ya murɗa handle ɗin without making any sounds wanda zai iya damunta, duk tunaninsa Abbi na biye da shi. Tsaye yayi yana ƙare mata kallo tare da bin Oxcgyen ɗin dake maƙale da ita wacce take taimaka mata wajan yin numfashi. Taɓe bakinsa ya yi, irin ko a ƙafarsa ɗin nan, kafin ya Ƙarasa gefenta ya zauna yana kallon yadda take sauke numfashi gaba ɗaya ta faɗa ta zama wata kala tamkar ba Abra Khamal Khamis. Sai ka ɗauka ta shekara tana jinya, lallai anyi gaskiya da akace damuwa itace hanya ta farko wajan latata mutum. There is no compassion or compassion in Adnan's heart. Wutar ɗaukan fansa ce kawai ke ƙara ruruwa a cikin zuciyarsa, tare da tunanin duk wata hanya da zaibi ya datse ƙaddarar da zata sada Abra da Real father ɗinta. Baya so baya kuma ƙaunar ganin haka, Imma mahaifin Abra zai ganta sai dai cikin makara yayin jana'izar ta. Ko kuma ita ta gan shi yayin tasa jana'izar. Zuciyarsa ta kasa jure abin da aka aikata a garesa, da ace zai yafe da tuni ya yafe amma wannan ba ƙaddara bace zallar son zuciya ne bama za'a haɗasa da kuskure ba. Ajjiyar zuciya ya sauke yana jan idanunsa tare da rufewa zuciyarsa nayi masa nauyi tamkar yanzu ne abin da akai masa yake faruwa. Baya jin koda Abra zata mutu ta dawo ƙarƙashin inuwar auren shi zai yafe wannan laifin dole sai ya ɗauki fansa. Domin da wutar ɗaukan fansa ya RAYU. China. Mirginawa ya yi daga kwancan da ya ke. Idanunsa dake a lumshe ya buɗe yana ƙara kallon A.c. dake ɗakin, gently kuma ya juyar da kansa idanunsa ya sauka akan makeken photon sanyin idaniyarsa, wanda ya kai aka buɗa masa shi ya zama babba. Tashi ya yi daga kwanciyar da yake ya nufi inda ya ajjiye photon daidai wajan ya tsuguna tare da miƙa hannunsa ya ɗauki photon, idan ba gizo idanunsa suke masa ba sai yaga photon kamar ya sauya idanunta sai sheƙi suke tamkar zasu zub da ƙwalla. A nutse ya shafi fuskarta idanunsa akan ƙaramin bakinta cikin muryarsa mai nutsuwa da kamala wacce girma da samartaka suka ƙara kamata ya ce. "Yaya" Ya faɗa yana kallon Fuskarta sai kuma ya ce "Akwai matsala yaya, na kasa samun nutsuwa me ya sa kike zuwa cikin baccina kina kiran sunana tare da yi min kuka? Why Angel ko akwai abin da ya ke damunki? Bai kamata ki damu ba, kina tare da wanda kike so kika zaɓa matsayin abokin Rayuwar ki. Uba ga yaranki kin samu abin da ki ke so. Nima kuma zan maki tawa rantsuwar yanzu" Miƙewa tsaye ya yi hannunsa zube cikin Aljihu gashin ƙirjinsa ya kwantar lub sai sheƙi yake a saman farar fatarsa abin ka da farin bafulatani. Da ɗan sauri-sauri yake duba cikin wata box har ya samu sabuwar reza jikinsa na rawa ya ɗauki reza ɗin tare da tsayawa akan photon Abra ya ce. "I, Salman Khamal Khamis, promise you if I don't find you as my wife... Ni ba ɗan halak bane Abra" yana faɗin hakan ya tsaga tafin hannunsa da rezar nan ta ke jini ya fara zuba, Murmushi ya yi yana zubawa photonta ido ganin jinin da ke zuba a jikinsa yana sauka a photon ya ce. "Ban damu da shekara nawa za kuyi tare ba, ban damu da yaran da zaku haifa tare ba, ban damu da girma ko tsofan da zaki kafin na dawo gareki ba, ke nake buƙata a cikin rayuwata. IDAN BA KE babu ni Abra, I love You, I love, I love Abra Khamal Khamis" Yana faɗin haka ya sake tsaga hannunsa da rezar ga wani gumin azaba dake tsastsafo masa a tsakiyar goshinsa. Kamar yana magana da photon nata ya ce "Yaya, I promise to love you unconditionally. Darling, you are the love of my life, I promise never to break your heart as it will also break mine. I love you so much. I promise to be with you forever. Honey, I know life has many challenges, but I promise to be dedicated to you. For better or worse I will always stand by your side until death separates us" A hankali wasu hawaye Masu zafi suka shiga fitowa daga cikin idanunsa, amma a hakan bai sare ba ya ƙara sakin Murmushi wanda ya fidda zallar kyansa cikin wata kalar Murya wacce babu tsoro ko rauni a cikinta ya ce. "Every day when I wake up, the first thing that comes to my mind is you. You know, how only a few things in this world make you happy with the fact that they are there and make your life great. You are one of those very few things. Thank you for being my destiny. You are my destiny. You are my dream come true. I can’t imagine myself with anyone else. I love you and just want to thank you for every single thing you do. You are the reason why I live, the air that I breathe and the love of my life!Wherever you go, whatever you do, I want you to know that you are my destiny" Ƙirjinsa ya buɗe jikinsa na rawa na tsananin azaba amma a haka ya rubuta alphabet letter na A. Nan take jini ya fara zuba kamar daga sama wani abokinsa mai suna Sunday ya shigo ganin Salman cikin wannan hali ya sa Sunday faɗin. "What happened to you Friend?" Shiru Salmanun-faris ya yi yana kifa kansa a jikin photon Abra. While jini na zuba daga ƙirjinsa zuwa hannunsa. Sunday ya matsa kusa da Salman ya ce. "你怎么了?你的情况呢? Nǐ zěnmeliǎo? Nǐ de qíngkuàng ne?" Ma'ana "Mene ya sameka? Kalli halin da kake ciki fa?". Salman was speechless, hannunsa ɗaya dafe da ƙirjinsa ɗayan kuma ya rungome photon Abra a jikinsa idanuna rufe. Ganin Salman yaƙi magana ya sanya Sunday matsawa tare da ƙoƙarin taɓa Salman a hargitse cikin zafin zuciya ya ce. "Don't torch me, i Said get out of my room". Abbi da Adnan na zaune a gefen gadon da aka kwantar da Abra, har lokacin bata ta shi ba. Abbi da hankalinsa ke kanta a hankali yaga tana motsa bakinta kamar mai yin magana, sai hannunta da yake ɗan fisga, ganin yadda bakin ke motsawa sosai ya sanya Abbi matsawa kusa da ita, tare da ranƙwafawa daidai saitin bakinta. Ga mmakinsa babu abin da take cewa Maybe zafin ciwo yasa take haka. "Innalillahi Faris, Faris mene wannan, mu gani" da sauri wannan kalaman suke fita daga cikin bakinta a kuma bayyane, Adnan dake zaune ya gyara zama yana binta da masifaffun idanunsa, wanda kuma zallar kallo ne na taƙaici musamman ganin yadda Abbi yake da riƙeta shi ba muharraminta ba, ga wannan ban zan Salman da take kira ba dare ba rana ba kullum bakinta cikin ambaton sunansa yake. Kama hannunta Abbi ya yi cikin kulawa ya ce "Sweetheart kin farka?" A hankali ta buɗe idanunta bakinta har lokacin yana motsawa. Kallon Abbi ta shiga yi wani Irin kallo mai kama dana tuhuma, Murmushi yayi yace "Sannu Sweetheart sannu Kinji" kafin tai magana Adnan ya tashi da sauri ya zo inda take gaba ɗaya kan gadon ya hau ya ce. "Naji tsoro Angel, i can't life without you ki daina suma irin haka please Angel zuciyata ba zata ɗauka ba" ya ƙare maganar yana ɗora kanta a kan cinyarsa, ya shiga shafa kanta. Da ace tana da ƙwarin barin jikinsa tabbas da tayi haka domin babu abin da zai sanya ga Abbinta wannan mugun azzalumin ya riƙe tare da nuna mata soyayyar ƙarya. Maganganun Abbi ta tuna wanda ya sanya ta fara zubar da hawaye ba tare data shirya ba. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wacce kalar rana yau ta zame mini? wacce rayuwa zan fuskanta a nan gaba, mene aikata a gare su da suka zaɓi haihuwata ta wannan sigar tare da yardani? Laifina ne, ni nace su aikata abin da suka aikata su waye iyayena mene yasa za suyi mini haka wayyo Allah" Wani irin raunataccen kuka Abra ta saki hadda shassheƙa kamar numfashinta zai bar jikinta,da Yadda take ji a cikin zuciyarta gwara ace bata zo duniya baki ɗaya ko kuma aci gaba da ɓoye mata Asalinta. "Ka kula da ita bari na kira Likita" Abbi na faɗin haka ya fita daga cikin Room ɗin. Baya son Abbi ya fahimci wani abu wannan dalilin yasa ya jawota jikinsa tare da Rungometa yana faɗin "Kee, Shiitt dalla Malama kin daman" ƙoƙarin sauka take daga jikinsa ya hanata ta hanyar ƙara matseta a jikinsa yana jan tsaki kamar an masa dole. Suna zaune Abbi ya shigo likita na bin bayansa. Dubata ya sakeyi ya tabbatar musu komai lafiya ya ƙara jaddada gudun Abin da zai ƙara sata cikin wannan halin. Gaba ɗaya suka nufi gida tun a mota Abra take maƙale da Abbi tana faɗin zata bisa, amma ya yi mata shiru har suka isa gida babu wanda ya samu zarafin yin magana. Abbi ya kalli Abra ya ce. "Abra baki da ikon bina, a baya nike kula da Al'amarin ki, amma yanzu ragamar rayuwar ki ta tattara ne a hannun mijinki, ki sani babu kyau abin da bakin ki ke furtawa. Shi aure ɗan haƙuri kiyi ta addu'a nima zan tayaki kuma In sha Allah daga wannan rana zan fara bincikar asalinki har mu gano iyayenki na gaskiya, naso riƙe ƙi roƙa na har abada, amma Abin da ka tsara bashi Ubangiji ya tsara ba. Ni nayi kuskure domin nasan komai jimawa dole wannan ranar zata riskemu, Kiyi haƙuri ki yafewa Abbinki na rashin faɗa maki gaskiya da ya yi, amma dake da Salman abu guda a zuciyata soyayya ɗaya nake muku. Bake kika tsara yadda zaki zo duniya ba, kuma mu duka bamu da tabbacin cewa kina da Iyaye ko kuma ke ba halattacciya bace, lokaci da bincike shi ne zai tabbatar da ainihin wace ke" Shiru ya yi yana sauke numfashi ƙara riƙe hannun Abra ya yi wacce take ta kuka kamar ranta zai fita kafin ya numfasa ya ce. "Kimin wannan alfarma don darajar Allah ki daina saka damuwa a ranki, ina kasa sukuni bana samun nutsuwa. Kin samu miji mai tsananin son ki da ƙaunar ki na imani da Allah zai tallafi maraicinki ya riƙeƙi da amana" "Abbi don Allah ka tafi dani, idan har farin ciki kake so nayi idan ina nan wata rana zaka iya samun ganganar jikina a matsayin gawa" kafin Abbi ya yi magana Adnan ya ce. "Ina son duk abin da Angel ɗina ke so, Abbi idan tafiyar zai sanya tai farin ciki na amince ka tafi da ita, ni zan dinga zuwa" da sauri Abra ta ce "A'a ba sai ka zo ba" Murmushi kawai Abbi ya yi ganin tsakani da Allah Abra ke duka maganganun ta. "Adnan ta ya ya ɗan kwali zai ja hula? Abra akwai tarin ƙuruciya da kuma rashin sabo a tattare da ita, shi ya sa take cewa haka. Ka kula da ita a yanzu kai take buƙata zuwa next week zan zo tare da Farouk haɗi da duk bayanan binciken da mu kayi zan sanya Private investigator In sha Allah komai zai zo cikin sauƙi" Jinjina kai Adnan ya yi kafin ya ce "Mun gode sosai Allah ya saka da alkairi, zan kula da Angel kulawa da ko a wajanka bata samu ba, nima a matsayina na Police zanyi ƙoƙarina wajan bincika asalin Real parent's ɗinta" Ganin da gske Abbi tafiya zai ya barta yasa Abra ƙankame jikin Abbi tana rusa kuka wanda duk wanda yaji kukan da take dole ya tausaya mata. He couldn't feel yadda hawayenta suka jiƙa masa jiki. Shi kansa idanunsa sunyi jajir Na'ima ta gama cutarsa itace silar komai da duk wani abu ɗaya faru ta ya ya zai yafe mata? Har Abada. Da ƙyar Adnan ya janye Abra daga jikin Abbi ya mayar da ita nasa jikin, tare da rungometa sosai yana faɗin. "Me ya sa ki ke gudana Angel? I'm your husband ni ki ke buƙata a yanzu, the you know how much I love you?" Girgiza kai kawai Abbi ya yi tare da juyawa ya fita zuciyarsa cike da so da tausayin Abra. Cilli Adnan ya yi da Abra yana nunata da hannu ya ce "Idan kinso ki mutu babu ruwan Sp Adnan Aliyu Matawalle, ko kin faɗawa Uban riƙon naki ba zai taɓa sawa na sakeki ba, domin na fishi iko da ke useless.." goge hawayenta tayi tsaf tare da kallon Adnan cikin dauriya tace. "Ba zan taɓa mutuwa sbd kai ba Sp Adnan Aliyu Matawalle, abubuwan da kke min idan ka haifu kada ka fasa" tana faɗin haka ta juya da sauri ta nufi Bedroom ɗin ta. Mamakin martanin da tayi masa yasa Adnan kasa motsawa balle yayi tunanin ɗaukan mataki akanta me hakan ke nufi? ta daina shakkar sa ko yaya ne?.Ya daɗe tsaye a wajan kafin ya nufi bedroom ɗinsa zuciya cike da tunanin abin da zai mata. Abra taci kuka ta ƙoshi harta dan gana haka ta raya daren tana kaiwa Allah kukanta akan ya shiga lamarinta ya kawo mata mafita cikin abin da ke damunta ya kuma bayyana mata iyayenta, daga ƙarshe ta roƙi Allah akan ya haɗata da Salmanun-faris cikin gaggawa. Washegari tana kwance tayi wanka wata simple duguwar riga ce a jikinta iya qwiwa sai fararen ƙafarta da suke a waje. Tai lamo jikin bed rungome da pillow gaba ɗaya tunaninta ya tsaya komai nata ya tsaya tana nan kamar wata statue. A hankali ta ji an murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin nata, Ƙamshin Pur oud da taji ya sa ta tabbatar da shi ne ya shigo ƙara haɗe fuska tayi ba tare data amsa Sallamar sa ba. Tsaye ya yi a kan yana harɗe hannayensa a ƙirji Looking at her daga shi sai trousers babu ko singlet dai murɗaɗɗen jikinsa da yake a buɗe. "Where's my breakfast?" Shiru not respond domin yi tayi kamar bata ji Abin da yake faɗa ba. "Ni sa'an mugun Ubanki ne da zan dinga magana kina jina? Ko kuma mugun halin uban naki kika fara wanda ban san da shi ba?" Sai a lokacin ta buɗe idanunta ta kallesa tare da mirginawa wanda ya sanya duguwar rigarta tattarewa zuwa can sama, har farin pant ɗinta ya bayyana cikin ƙasa da murya ta ce. "Daman ance ai kyan ɗan ƙwarai ya gaji iyayensa,babu laifi dan na ɗauki halin mahaifina" a fusace yayi kanta zai daka tayi saurin zillewa wanda ya sa gaba ɗaya rigar jikinta barin jikin tai naked! Cak Adnan ya tsaya domin it's the first time daya ganta naked haka nan cikin haske, notin kansa ya nemi kuncewa domin idan akwai abin da ke saurin raunata zuciyarsa bai shige buƙatarsa zuwa ga matarsa ba, Abin da yake kwaɗayi a kullum wanda yake sanyaya zuciyarsa. Takawa ya shiga yi zuwa inda take sai da sukai dab da juna ya ce "Ubanki mugu ne Abra, Azzalumi,Macuci, Ma yaudari, mai baƙar zuciya kona bar shi Ubangiji ba zai bar shi ba. Domin Ubanki kura da fatar Akuya ne!" "Ka sani Uba, Uba ne ba'a taɓa sauyawa tuwo suna, duk lalacewar shi, shi ne ya yi sanadiyar zuwana duniya. Ka saurara da aibata min shi duk da ban san abin da ya aikata a gare ka ba, zuciya nake gudu kada haƙurina ya gaza" Zuciyar Adnan na tafasa ya ce "Well-done Abra Khamal Khamis. Well-done barewa ba tayi gudu ɗanta ya kasa rarrafawa ba, yanzu ne wasan namu zai fara bada citta tunda har kin zamu zarafin mai da min da martani haka nake so muje zuwa shege ka fasa" banza tai masa da sauri ta juya zata shige bathroom. Bata san mene ya faru ba, sai jinta tayi kane kane a jikin Sp Adnan Aliyu Matawalle yayi mata wata iriyar ƙyakkyawar runguma wacce da iya zuciya ɗaya yayi mata ita, domin gangar jiki bata iya ɓoye ainahin abin da zuciya ke buƙata. He started kissing her from her mouth to her neck. It was a kiss that he had never given her before, babu wutar ɗaukan fansa ko ta ƙiyayya. It is something that shows what the heart wants and needs. Now Abra needs it in his body. Nan take ya nuna mata buƙatar miji zuwa ga matarsa. Abra ta rasa yaya zatai, a kullum faɗo mata yake kamar jaka ba tare da so ko tattali ba, yana sauke buƙatarsa shi ke nan. Daga baya kuma ya ci mata mutuncin da ko maƙiyinta ba lallai yayi mata ba. Tana karatun novel dan haka zai wani tunani ya faɗo jikin ranta. Taya shi abin da yake tayi sai da yazo gangara ta tsakanin buƙata ta hankaɗa shi gefe da gudu tai bathroom tana haki. Adnan ji yayi kamar zai mutu ko hannunsa ya kasa motsawa sbd ciwon da mararsa ke masa, zai zufa dake yanko masa idanunsa yayi jajur ya ƙorawa ƙofar bathroom ɗin idanun, zubar da aji ne yayi begin nata akan wani abu na jikinta. Ta daɗe cikin bathroom ɗin kafin ta fito, ga mmakinta sai taga ɗakin nata yayi duhu sosai kafin ta motsa taji an cillata kan gado, duk yadda taso ƙwace kanta kasawa tayi sai da ya tara masa gajiya tare da jifatanta da maganganun masu ɗaci kafin ya fita yana faɗin. "Ba kyauta aka bani ke ba, kuɗi nasa na aureki kuma dole nazo maki aduk sanda nai niyya Ubanki ma yake abin da yaga dama balle ni da nake miji a gareki, mara galihu baiwata!" Ashe kuka ma cikin rahama yake domin kasa yinsa tayi a yanzu Zuciyarta tai mata nauyi sosai. Misalin ƙarfe huɗu na yamma tana zaune a Parlour sanye take da duguwar riga mara nauyi sosai, gashin kanta duk a cukurkuɗe tai zururu a hankali taji an murɗa handle ɗin ƙofar parlourn an shigo, bata motsa ba domin ta san shi ne ba kuma ta mara ba dawowar shi. Idanu taji a jikinta alamar ana Kallonta haka kawai taji gabanta ya faɗi da sauri ta ɗaga kanta, Innalillahi wanda ta gani tsaye ya shammaceta bata taɓa zato ko tunanin ganinsa a wannan lokacin ba. Jikinta na rawa ta miƙe tsaye tana binsa da kallo cikin wata murya ta ce "Faris.." sai kuma ta kwasa da gudu tai kansa...... LITTAFIN DARE DA DUHU, na kuɗi ne biya 300 ta wannan acct ɗin 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne zaka biya 500 kai Mgn ta wannan number. 09047871750/08081012143 [10/20, 7:45 PM] Abk: Da sauri Salman ya shiga girgiza mata kai, alamar kada ta ƙaraso wajansa domin ya san abin da zai faru idan ta zo. Ita ta haramta a garesa kamar yadda ya haramta a gareta. Da sauri ya yi baya ganin yadda ta yo kansa gadan-gadan, hawaye na bin fuskarta ga wani irin kuka da take tamkar wacce akai wa mutuwa. Juyawa ya yi da sauri ba tare daya shirya ba da nufin barin parlourn yama fita daga cikin gidan baki ɗaya. Ƙyakkyawar rungomar da Abra tayi masa ta baya ita tayi sanadiyar ɗaukewar wutar kan Salman, cak ya tsaya zuciyarsa na bugawa da ƙarfin gaske, shi kansa ya san ya azabtu da rashin Yayar tasa, amma ba shi da iko da ita a yanzu mummunar ƙaddara tai musu shamaki da juna. Gaba ɗaya ya kasa motsawa sbd yadda Abra ta ƙankamesa ta baya hannunta ɗaya a ƙirjinsa ɗaya kuma ta riƙe ƙugunsa dashi, wani irin kuka take wanda yake ratsa zuciyar Salman, saurare ɗaya yayiwa kukan yasan cewa bawai Iya na farin cikin ganinsa bane, akwai abin da yake faruwa a ƙasa. Idanunsa da sukai jaa ya buɗe a hankali cikin nutsuwa ya saka hannunsa tare da zame hannayenta dake rungome da jikinsa da ƙyar. Juyawa yai ya fuskance ta ƙanta a ƙasa yana kallon yadda take kuka kamar zata haɗiyi zuciya. Tun daga sama har ƙasa yabi jikinta da kallo babu abin da ya bashi tsoro sai ramar da yaga tayi ba haka ya tafi yabar Angel ɗinsa ba. Inda take ya matsa tare da sanya hannunsa duk biyun ya tallafo haɓarta fuskarta ta samu gurbi a cikin hannunsa, kasa magana ya yi sai binta da idanu kawai da yake, Eyeballs to Eyeballs suke kallo juna, Abra na shassheƙa ta ce. "Faris" Kasa amsata ya yi yana son tantance muryar data kirasa da ita, hannunsa ya zame kaɗan yana mai dashi cikin Aljihu a nutse ya ɗaga kansa sama ya fara bin parlourn da kallo kamar daga sama taji ya ce. "Kin rame, kamar ba Angel tawa mai son girman nan ba" kwaɓe fuska tayi tare da matsawa kusa dashi ta shiga dukan ƙirjinsa tana sakin kuka tare da faɗin. "Why did you go and leave me? Kai ne wanda nake gani naji daɗi, kai ne walwalata, farin cikina, me ne yasa zaka barni a lokacin da nake buƙatar ka? Why Why Why Faris" ta faɗa tana sakin raunataccen kuka while tana ƙara dukan ƙirjinsa da dukkan ƙarfin ta. Jajayen idanunsa ya lumshe yana jin yadda take dukansa kamar wanda yayi mata babban laifin nan, baya ita ce wacce ta bashi lasisi da damar tafiya ya barta,ita ta zaɓi waninsa ta kasa fahimtar feelings ɗinsa a gareta, ta gagara gane cewa so da ƙaunar da yake mata ba iya na ƴan uwa bane, so ne irin na masoya wanda zai kai matakin Mata da Miji. Jin kukanta yake har ƙasan zuciyarsa, zafin da zuciyarsa ke masa a yanzu ya tabbatar yafi wanda zuciyar take mata, ji yake kamar ana ɗiga masa ruwan dalma a zuciyarsa. Ganin yadda take kukan har numfashinta ya fara sama alamar zata sume masa, cikin rashin abin yi da mafita yabi umarni da kuma ragamar zuciyarsa ya jawota jikinsa tare da yi mata masauƙi a jikinsa ya rufe ta ruf da hannayensa. Kamar tana jira tai holding nasa back sai kuka take tana ƙankamesa tare da faɗin. "Stay with me, don't leave me again. I am happy when you are near me. Idan zaka tafi ka tafi dani kaji" Shiru Salman ya yi mata, har lokacin yana riƙe da ita a jikinsa zuciyarsa kamar zata fito waje haka nan ya keji. "Faris.." ta faɗa tana ɗaga kanta tare da kallon fuskarsa wacce tayi jaa sosai. "Kayi magana mana ɗan ƙanina" ta ƙare maganar tana Murmushi while hawaye na zubu mata ta rasa yadda zatai she can't believe wai Faris ne tsaye a gabanta. Hannunta ta miƙa taja dogun hancinsa tana faɗin "Say sometimes yaushe ka zo? Waya faɗa maka gidana" zameta yayi daga jikinsa ya tsaya kamar an dasa shi ya ce. "Banji daɗin ganinki haka ba, Abra." Kanta ta sunkuyar ƙasa a karo na farko taji kamar ta faɗawa wani halin da take ciki musamman yanzu da take ganin Salman a gabanta. Amma idan ta tuna gargaɗin Adnan a gareta, sai ta ji tsoro da fargaba ya kamata, kuma tayi tuni ga Sirrin Aure tsakanin ma'aurata, sai taji duk jikinta yayi sanyi. Shiru ta yiwa Salman ba tare da ta ce komai ba. "Is something bad happened to you? Look Angel kasa jurewa da ganinki a cikin mafarkina da nayi ne ya sanya na biyo jirgi na tawo ba tare da sanin makarantar da nake ba,kina so zuciyar Faris ɗinki ta buga ne?" Girgiza masa kai tayi muryarta na rawa tace "Ka zauna na kawo maka ruwa, me zaka ci?" "Banzo dan naci abincin gidan mijinki ba, I'm here sbd sanin halin da kike ciki, da kuma dalilin da yasa kike addabata a cikin barcina" shiru tayi masa hawaye wani yana bin wani wata tsawa ya buga ya ce "Talk Abra, Talk" dugun numfashi taja tana ɗaga kai da sauri ya ƙaraso inda take tsaye ya kama hannunta zuwa kan kujera ya zaunar da ita. Juyawa yayi da sauri kuma ya nufi wajan deep freezer yaje ya buɗe, ruwa mai sanyi ya ɗauka ya dawo inda take zaune, a lokacin har idanunta ya fara lumshe a gefenta ya zauna ya kama Fuskarta tare da bata ruwan, tana sha yana ɗan bubbuga bayanta tare da shafa kanta. Ajjiyar zuciya mai ƙarfi ta saki kanta ta ɗora saman cinyarsa ta ce. "Zuciyata babu daɗi Faris, komai ya lalace duniya ta juya min baya nasan da kana kusa dani da hakan bai faru ba, bana da mafita bana da mataimaki, bana da ikon faɗin abin da yake raina, Ubangiji ne zai min maganin komai ka tayani da addu'a...," Kukan da yaci ƙarfinta ne yasa ta kasa ƙarasa abin da tai niyya. Shiru yayi mata har lokacin yana shafa kanta ganin ta fara dawowa hayyacinta ya sa ya ce. "Kinci Abinci?" Kai ta girgiza masa ya ce "to ɗagani, kin wani haye min cinya" murmushi tayi tana faɗin. "Wallahi bacci ma nake shirin yi, naji cinyar ta ƙara laushi" "Ko?" Ta miƙe tsaye tana faɗin "Sure" sai a lokacin ta shiga kallonsa maroon ɗin voyel ne jikinsa mai manyan zane amma shara shara haka Voyel ɗin yake, hatta farar singlet ɗinsa ana gani ya ƙara fari tas dashi, ga ƙirjinsa daya buɗe fuskarsa ta fara cika da gemu da saje, sai jajayen laɓɓansa da suke haske. Zaka iya tunanin yayi shekaru ashirin da biyar ko da bakwai haka. Marairaice mata fuska ya yi ya ce "Yaya" dry tai tana watsa hannunta ta ce "You have changed totally wallahi mai kake ci acan China?" "Tunanin ki ke ƙara min lafiya" idanunta a kansa ta kasa magana yana ɗago kai suka haɗa idanu ya zaro mata idanunsa ya ce "Ki je ki kawo Abinci Angel stop looking at me haka nan, kada ki fara ganin munina tun ina kyau a idanunki" "Zoka ta yani" Waro idanu ya yi waje ya ce "Wa? Ni Salman Khamal Khamis? Jeki kawai Yaya ina jiran ki" "haba mana Faris yaushe rabon da muyi girki tare" girgiza kai kawai yayi ya ce. "Yaya gsky ba zan iya ba" Turo baki tayi ta juya zuwa kitchen ɗin ajjiyar zuciya ya sauke sai a lokacin hawayen da suke maƙale a idanunsa suka silalo a hankali, da sauri ya sa hannunsa ya goge tare da Miƙewa yabi bayanta. Duk abin da take da Idanu kawai yake binta, yana nan tsaye da ƙyar ta samu ya yanka mata albasa da carrot. Babu jimawa ta kammala haɗa fried rice with chicken kabab. A plate ɗaya ta zuba ta saka 2 spoons, ya rigata tafiya a zaune ta samesa kan kujera ta ce. "Baka gaya min ya Mamina take ba da Abbi, Ammi, Granny i so much missing them wallahi" shi dai bai ce komai ba ta ce. "Ga abinci" "kefa?" Girgiza kai tayi ta ce "bana ci" ƙuri yayi mata da ido kafin ya ɗauki spoon yana sakkowa ƙasa, A nutse yake bata abincin tana ci harta ƙoshi . Zamewa tayi ta ɗora kanta a cinyarsa idanunta a sama shi dai bai motsa sai girgiza ƙafarsa da yake, hakan yai wa Abra daɗi domin sai ya zamana kamar rarrashinta yake bai aune ba yaji saukar numfashinta bacci ya ɗauke ta. Tunani Salman ya fara, game da sauyin Abra amma ya kasa gane gaskiyar al'amarin, sai ya alaƙanta hakan da sabuwar rayuwar data samu kanta ciki, da kuma tafiyar da ya yi barta wannan dalilin sune suka sauyata, ya san tana son mijinta tana kuma farin ciki da aurensa. Babu wanda ya san da batun zuwansa Nigeria, domin shi kansa bai yi tunanin cewa zai iya zuwa cikin gaggawa haka ba, Khairy ce ta bashi Information na gidan Abra, kuma yaci sa'a yana da aboki a Kaduna, yana zuwa kuma bai sha Wahala wajan maigadin gidan ba, har lokacin da ya nufi ƙofar parlourn bai yi tunanin zai sanya Abra acikin ƙwayar idanunsa ba, sai gashi yana buɗe ƙofar ta sadashi yayar tasa. Numfashi ya sauke yana kallon yadda take bacci ta ƙanƙame hannunsa a ƙirjinta, zuciyarta na ɗan bugawa a hankali. "Zaki dawo gareni, zaki zama mallakina Insha Allah yaya" kwanciya ya fara tunanin gyara mata. Yana ƙoƙarin ɗaukanta zuwa saman kejera yaji ance "Well-done Salman Khamal Khamis Well-done masoyi na ƙwarai" ko ba a faɗawa Salman ba ya san Sp Adnan Aliyu Matawalle ne. Murmushi ya yi a hankali ya ɗauki Abra ya kwantar saman Kujera yana duba yadda baccin nata ya yi nisa, hannunsa ya zuba cikin Aljihu idanunsa akan Adnan ba tare da ya ce komai ba. Adnan daman ba barin gidan ya yi ba, domin tun safe yana nan, kuma a lokacin daya fita yabar ƙofar a buɗe ne, sbd bai tunanin zai jima, sai gashi yana zuwa cikin Garden ɗin gidan nasa har bacci ya ɗaukesa a can, wannan dalilin ne ya bawa Salman damar ganin Abra cikin sauƙin. Adnan ya ce "Daka fahimci ka zama loser a Soyayyar Abra sai ka tattara kayanka zuwa China, saboda kada ayi aurenta akan idanunka right?" Salman ya juya ya kalli Abra ba tare daya kalli Adnan ba ya ce. "I love her, duk wani bugun numfashina da Soyayyarta yake fita, ban san adadin son da nake mata, idan da ace nine mijin Angel a yanzu ina da tabbaci da tafi haka, fari, ƙiba, kwanciyar hankali" janye idanunsa ya yi daga kanta ya kalli Adnan ya ce. "Loser? Haka kace ko baka da labarin sbd ina gab da rabaku aka tura ni China karatu? Baka da labarin Soyayyar da Angel ke min kwatankwacin ta bata yi maka? Ban san ina tunanin Sp Adnan Aliyu Matawalle ya tafi ba, daya kasa gane cewa ba soyayyya ƴan uwa Abra ke min soyayya ce irin ta Miji da mata" Tafa hannu Adnan ya shiga yi kafin ya ce "Kace duk a sbd farin cikin Abra aka haɗa baki dakai wajan muna furtarta, kuka kasa faɗa mata cewa Major Khamal Khamis ba shi ne ya haifeta ba?" Dry Faris ya yi irinta Abbi sak kafin ya riƙe ƙirjinsa sosai ya ce. "Masoyi na Gaskiya shi ne zai gujewa ɓacin ran wacce yake so, Abra matsalar ta shafa amma naji inama nine wanda aka tsinta ba ita ba, a kuma ranar dana san ba a ciki ɗaya muka fito ba, na gane cewa ina tsanin so da ƙaunar Abra, ina mata son da ko rabinsa baka yi mata, ban taɓa zama loser akan abu ba, haka ba zan fara akan soyayyar Abra ba, ka sanya a ranka tamkar ajjiya haka take a wajanka Tabbas zan dawo na amsheta a hannunka a lokacin da babu abin da ka isa ka aikata". "The you love me Faris?" Suka ji saukar Muryar Abra a kunnuwansu. Runste idanunsa ya yi ya kasa juyawa ya kalleta. "Mene ya sa Faris? Ashe kasan gaskiya wacece ni ka kasa faɗa min? Kana tunanin rashin faɗa min zai sanya nai farin ciki? Ina yarda da junan da mukai? Ina kariyar da kace zaka bani tana ina?" Shiru kawai ya yi mata da sauri ta ƙarasa gabansa ta ce. "Magana nake Faris" idanunsa da sukai jajur ya buɗe tare da zuba mata su. Ya ce "kibar wannan maganar yaya" "Me ya sa zan bari Faris? Ka faɗa min gsky Say something Salman Khamal Khamis say it" ta faɗa tana jijjiga shi idanunsa a kanta ya riƙe hannayenta ya ce. "Sbd ina Sonki, Ina Sonki Angel, na buɗe idanu dake, na rayuwa dake, mun tashi tare da Soyayyar juna, ina jinki a Zuciyata ina kishin ki tun ban san wacece ke ba, na ɓoye miki gskyar Al'amarin sbd farin cikinki ki, ina son ki dauwama cikin farin ciki. A duk sanda kika gane cewa Abbi ba shine wanda ya haifeki ba kina iya zama wata Abrar ba wacce na sani ba, a lokacin kuma na fahimci tsanar da Mami ke maki haka ne sanadi, daga nan kuma soyayyar da nake maki ta fara juyewa zuwa so na aure. Na kasa fahimtar dake how much I loves you, how much I care for you... Kullum cikin tunanin ni ƙaninki kike, kallon yaro kike min Angel so I have no choice wanda ya sa dole naja bakina nai shiru ina kishin mutumin da kika aura". "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" shi ne abin da Abra ta faɗa, is that the reason da ya sa Faris yayi kissing nata a lokacin da zai bar ƙasar? Ta kasa fahimta. Kuka ne ya kwace mata ta ce "Me yasa ka tafi ka barni?" "Bani da laifi, Mami ta shirya komai sbd na faɗa mata sonki nake ƙaunarki nake, gaba ɗaya plan ɗinta ne, babu wanda ya san da zuwana ƙasar nan a family Khairy ce ta bani Information inda kike zaune da komai. Bani da farin ciki Yaya ban ga alamar kina farin ciki da wanda kike aure ba?" Abra ta kasa cewa komai domin bata san da wacce kalma zatai amfani da ita wajan faɗawa Salman cewa bata jin daɗin auren ba, kuma bata da ikon faɗa masa komai, ajjiyar zuciya ta sauke "tayaya zan farin ciki Faris? Baka tare dani rashin ka shine sanadin shigata cikin wannan halin" Adnan dake tsaye ya dakawa Salman tsayawa ya ce "out of my house loser!" Girgiza kai Abra tai ta ce "No Salman kada ka tafi akwai abin da nake son faɗa maka" Kauuuu!! Adnan ya ɗauke ta da mari, haushi, baƙin ciki, kishi suka taso masa lokaci guda kafin ya ce "Kina matsayin matata kike magana da wani banza ɗan iska under age? You're mad Abra!" A zafafa Abra ta ce "Salman ɗin shi ne ɗan Iska?" "In a capital letter YES ɗan iska akwai abin da zaki ne?" Abin ka da mai haƙuri gaba ɗaya tai kansa tana ɗaga murya ta ce "Sai dai idan kai ne...." "Nooo!!! Abra don't try he's your husband karki ƙarasa" Salman ya faɗi haka cikin tsawa kuka ta sanya ta ce "ba kaji ya ce maka ɗan iska ba? Bayan shi...," "Shut up, nace kiyi shiru and so what dan ya ce min ɗan iska? No matter what Kada ki kuskura ki aibata mijinki" Numfashinta ne ya fara sama tana ƙoƙarin kiran sunan Salman Amma ta kasa luuu tayi zata kifa Salman ya yi kanta kafin ya ƙarasa Adnan ya kai masa duka a ciki, tare da ɗauke sa da wasu maruka ya ce. "Useless, Wanda ba shi da rabo. Wallahi wallahi zan illataka anan wajan kai da Abra kuma har Abada, ba zaka sake ganinta ba kuma ba zata sake ganin ka ba, This is my promise ka saka ranka sai dai ku haɗu a darun Salam.." "Zan nuna maka cewa, a rayuwa Salman baya taɓa zama loser baya neman abu ya rasa, Salman a kullum cikin samun nasara yake, ko yara nawa zaku tara,duk tsofan da zaka sanya tayi duk lalacewa da tayi ka ɗauka ita ɗin ajjiya ce a gareka, zan dawo na ɗauke ta... Abra is my life just wait for me" yana faɗin haka yai waje kai tsaye kuma airport ɗin kaduna ya nufa yaci Sa'a akwai jirgi babu jimawa jirgin ya keta hazo a karo na biyu zuciyoyi biyun suka sake rabuwa. Paid book.... Contact to subscribe if you need 08119237616 [10/21, 1:06 PM] Abk: "Faris! Faris! Faris!" Shi ne kawai abin da take maimaitawa cikin fitar hayyaci. Adnan dake tsaye yana huci cikin Masifa ya ce. "Ki daina kira mini sunan wani gardi a cikin gidan aurena." Duk da halin da take ciki na tashin hankali bai hana ta duban shi a fusace ba tare da faɗin. "Ba zan daina ba ɗin, na faɗa na maimaita Salmanul Farisi, Namijin duniya, yaro mai halin manya, and lastly I love him with all my hear....." Ba ta ƙarasa ba saboda wata damƙa da Adnan ya yi mata, cikin zaro ido ya ce. "Ko me za ki faɗa ki faɗa, amma ki sani ke da shi har abada, na riga na gina katangar ƙarfe a tsakaninku, wadda ba za ta taɓa rushewa ba." Ya ƙarashe maganar tare da wancakalar da ita. Kafe shi ta yi da idanunta da suka ƙirmushe babu alamar hawaye a cikinsu ba ta ce komai ba, sai haki kawai take da rawar jiki. Tsaki ya ja tare da yin ƙwafa ya juya ya bar parlour'n. Sai a lokacin wasu hawaye masu ɗumi suka samu damar zubowa daga cikin idanunta, slowly ta lumshe idonta tana shaƙar ƙamshin Salman da har lokacin bai bar parlour'n ba, zuciyarta cike da tsananin shauƙinsa. "Me ya sa ka sake tafiya ka bar ni a karo na biyu? A lokacin da nake tsananin buƙatar ka a kusa da ni, why my Faris? Yaushe za ka ƙara dawowa gare ni?" Ta faɗi haka a fili cikin tsananin damuwa da ƙunar zuci. Hajiya Ni'ima ce kwance a kan dogowar kujera a parlour'n gidansu, idanunta a lumshe tana tunanin abin da ya dame ta. Siririn tsaki ta ja saboda yadda hayaniyar da Aunty Suwaiba da Uncle Faisal ke yi ta cika mata kunne, ga yunwa dake damun ta, sakamakon kasa cin abinci da ta yi. Cikin takaici ta buɗe idonta tare da miƙewa ta tashi ta shiga ɗakin Mahaifiyarsu. "Wai don Allah Mama har yanzu su Aunty ba su girma da wannan faɗace-faɗacen ba? Ni fa shi ya sa ban fiya son in zo gidan nan in zauna ba." Taɓe baki Mama ta yi ta ce. "Ina za su girma, ai ita Suwaiban ce ba ta jan girmanta, shi ya sa shi kuma ya raina ta." Cike da takaici Na'ima ta ce. "Allah ya sawwaƙe, ni yunwa ma nake ji, kuma gaskiya ba zan iya cin wannan tuwon da Aunty ta jaɓa ba." "Sai ki fitar da kuɗinki ki sayi abin da za ki iya ci." "Dole na ma." Na'ima ta faɗi haka tare da ficewa daga ɗakin. Tunda Major ya dawo gida ya rasa me yake masa daɗi, idan ya tuno halin damuwar da ya baro Abra a ciki sai ya ji damuwarsa ta ninku, babban problem ɗin kuma bai san ta inda zai fara neman asalinta ba, don tun farko da ya kalle ta ba ta yi masa kala da ƴan ƙasar nan ba, ta fi kala da half case. Haka ya shirya yau da safe ya koma gurin aiki, cike da ƙudirin fara bincike a kan Abra, don gano asalinta kamar yadda ya yi mata alƙawari. Zaune yake shi kaɗai a cikin ƙawataccen office ɗinsa, yanayinsa kaɗai za ka kalla ka san yana cikin damuwa, duba da yadda yake yawan yamutsa kwantacciyar sumar kansa, gami da sauke numfashi akai-akai. Runtse idonsa ya yi a lokacin da kalaman tsohuwar da ko fuskarta bai gani ba suke yi masa amsa kuwwa a cikin kunnensa, a karo na babu adaɗi. _"Malam ya mutu, ya tafi ya bar mu a lokacin da muke tsananin buƙatar shi a cikin rayuwarmu, Ubangiji ba ya barin wani don wani ya ji daɗi, kuma duk wanda ya mutu kwanansa ne ya ƙare. Amma mutuwar Malam tana da sanadi, har abada ba za mu taɓa mantawa da asibitin nan da mara mutuncin likitan da ya ƙi zuwa ya duba Malam ba, saboda Ubangiji ya ba shi dama sai ya yi amfani da ita ya dinga wulaƙanta talakawa marasa ƙarfi, maimakon ya yi amfani da ita ta hanyar da za ta kai shi ga shiga aljanna. To insha Allahu a dalilin wannan wulaƙancin nasa sai ya yi da na sani da nadama watarana, insha Allahu sai ya yi kuka da idanunsa."_ A jiya bayan mutuwar tsohon da Jamila ta dinga yi masa nacin ya je ya duba shi ya sauka ƙasa da niyyar fita ya ji tsohuwar tana wannan maganganun cikin kuka ta window'n baya na emergency room, a lokacin murmushi kawai ya yi ya wuce, cikin ransa yana mamakin ƙarfin hali irin na talaka, shi bai biya kuɗin da za a duba mara lafiyarsa ba kuma ya dinga masifa don ba a duba shi ba. Sai dai me? A lokacin da ya zo bacci sai maganganun nata suka dinga yi masa amsa kuwwa, tamkar a lokacin take faɗar su. Yau ma yana tashi ya ji maganar tsohuwar tana dawo masa, abin ya ba shi mamaki ba kaɗan ba, don ba wannan ne karon farko da aka taɓa jifan shi da miyagun kalamai ba, waɗanda suka fi wannan muni ma, amma ko kaɗan ba sa damun shi, tunda ya san a kan aikinsa yake. Tsaki ya ja tare da jan numfashi ya ɗan buga table ɗin gabansa, cikin takaici da haushin zuciyarsa da ta damu da maganganun tsohuwar har take ƙoƙarin jefa shi cikin damuwa. Buɗe ƙofar office ɗin da aka yi tare da sallama ya saka shi buɗe kyawawan idanunsa. Amsawa ya yi yana bin ta da kallo, Nurse Jamila ce. Cikin girmamawa ta ce. "Barka da yamma Doctor." Gyaɗa mata kai kawai ya yi. "Doctor ɗan gidan Senator shattima aka kawo, asthma ɗinsa ce ta tashi." Kafin ta gama rufe baki ya miƙe cikin sauri tare da faɗin. "Subhanallahi! Maza-maza akai shi V.l.p room, ki sanar da Doctor Jibril da Lukman su je su ba shi taimakon gaggawa, ga ni nan zuwa yanzun nan." "Ok Doctor." Ta faɗa tare da juyawa ta fice, zuciyarta cike da tsananin mamakin halin Bulama, yadda yake rawar jiki saboda an ce an kawo ɗan masu hannu da shuni, sai ta tuno jiya bala'in da ya dinga yi mata kamar zai cinye ta ɗanya akan yunƙurin allurar da taso yi wa tsohon da ya rasu, a lokacin ma kuka take yi na tausayin bayin Allan, amma bai damu ba ya dinga zazzaga mata masifa tare da gargaɗin kar ta ƙara yi masa irin haka, ita ba ta ma san wa ya faɗa masa ba. Tafiyarta, maganarta da yadda ƙwayar idonta ta juye zai saka a kallo ɗaya idan an yi mata a gane cikakkiyar ƴar shaye-shaye ce. Tafiya take cikin rangaji kamar za ta faɗi, Abdul dake cikin Motar yana kallon ta zuciyarsa cike da mamakin yadda cikin lokaci ƙanƙani ta saba da shaye-shaye over, ko wanda yake harkar shekara da shekaru ba zai nuna mata yawan shan abubuwan maye a kullum ba. Domin ta mayar da su tamkar ruwan shanta da abincinta. Yanzu kullum da sassafe take ficewa, ba ta dawowa kuma sai dare. Weekend ne kawai idan Bulama yana nan take takatsantsan. A haka ta shiga part ɗin Hajiya Saudat. Tana hakimce akan kujera ta miƙe ƙafa ɗaya daga cikin masu aikin gidan tana mammatsa mata, wata kuma na yi mata firfita da mafici na alfarma tamkar wata sarauniya, duk kuwa da air conditioner ɗin dake parlour'n. Sai wata dake yayyanka mata fruits tana ɗauka tana ci kamar ba ta so, idanunta a kan plasma TV tana kallon wani Indian film. Yadda Meenal ta buɗe ƙofar parlour'n da ƙarfi ya sa su kallon wurin cikin sauri, tana ɗan tangaɗi ta ƙaraso ta zauna a kusa da mahaifiyarta. Wata irin faɗuwar gaba ce ta riski Hajiya Saudat, cikin tsananin kaɗuwa take bin ƴar tata da kallo. A fusace Meenal ta ce wa masu aikin. "Uban me kuke kallo haka a jikina? Kun wani zuzzura mini ido kamar baƙaƙen Mayu? Ku tashi ku bar parlour'n nan!" Ta yi maganar cikin ƙaraji da tsawa. Ko gama rufe baki ba ta yi ba suka miƙe sum-sum suka fice. "Mene haka Meenal? Warin me nake ji yana tashi a jikinki?" Hajiya Saudat ta tambaya a firgice. Cikin maye ta ce "Don't worry Mom ba wani abu ba ne, I just......." Ba ta ƙarasa ba Hajiya Saudat ta ɗaga hannu da nufin wanka mata mari, ko me ta tuna sai kuma ta fasa ta yarfar hannun gefe ta shiga girgiza kai tana faɗin. "Na shiga uku! Shaye-shaye kika fara Meenal? Me zan ce wa mahaifinki idan ya gano hakan? Wa ya jefa ki a cikin wannan mummunar rayuwar, ko ma waye ya cuce mu, ki faɗa mini waye? Wallahi sai na yi shari'a da shi tunda ya gurɓata mini rayuwarki." Meenal da ba ta fahimtar abin da take cewa ta miƙe tare da faɗin. "Oh Mom, ya kike faɗa haka kamar haushin kare? Ko Dad ne ya ɓata miki rai? In shi ne kawai ki ɗan mazmazge shi...." Cikin takaici Hajiya Saudat ta lailayo ashar ta ƙunduma tare da fashewa da kuka, tana yiwa wanda ya ɓata mata rayuwar ya Allah ya isa, maimakon ta yi wa ƴar tata addu'ar neman shiriya. Upstairs Meenal ta nufa, ta zo daidai ƙofar kitchen ta shaƙi ƙamshin farfesun kifin da Hajiya Saudat ta saka a yi mata, da sauri ta toshe hancinta saboda yadda ta ji ƙamshin ya hautsina mata ciki, ta ji ba ta ƙaunar sake shaƙar shi. Lokaci ɗaya ta ji amai ya taho mata, hakan ya sa ta durƙusawa ta fara kelaya shi a nan tsakiyar parlour'n. Da sauri Mommy ta yi kanta ta riƙe ta tare da faɗin. "Ba ki da lafiya ne Daughter? Sorr...." Kasa ƙarasa abin da ta yi niyyar faɗa ta yi, sakamakon lura da wani irin fari da ɗashewa da Meenal ta yi, ƙirjinta ya cika tam kamar zai faso ɗamammiyar rigar jikinta ya fito. Waro ido ta yi tare da faɗin. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Na shiga uku ni Saudat! Me yake shirin faruwa da ni ne?" Zaune take a kan darduma ta ɗaga hannayenta sama idanunta na zubar da hawaye, a fili take faɗin. "Ya Allah kai ne Sarkin kowa da komai, kai ka yi rayuwata a haka, Allah ka sassauta mini ka ba ni ikon cinye dukkan jarabawar dake cikin rayuwata." Ta ƙarashe addu'ar tare da fashewa da kuka, cikin ranta tana hoping a ce duk wannan abubuwan da suke faruwa mafarki take yi, za ta farka ta gan ta a gidan Abbinta sun cigaba da rayuwa da Faris ɗinta cikin farinciki da jin daɗi. Wani irin tuƙuƙi take ji a cikin ranta, a yanda take jin zuciyarta tamkar za ta buga saboda tsananin damuwa da tashin hankali. Ba ta taɓa tunanin za ta riski irin wannan damuwar a cikin rayuwarta ba, ko da wasa aka ce Adnan zai aikata mata haka za ta ƙaryata, duba da tarin soyayya, kulawa da tattalin da ya nuna mata kafin Aurensu. A hankali take jin tsanar shi na maye gurbin tarin ƙaunar da take masa a cikin zuciyarta. Sai a yanzu ta gane tana tsananin so da ƙaunar Faris, so irin na aure ba na ƴan'uwantaka ba. Abin da ya sa ba ta gane hakan ba tun farko saboda rashin sanin Salman ba ɗan'uwanta ba ne na jini. "Ya Allah!" Ta furta a fili cikin bugawar zuciya, ta rasa ma tunanin me za ta yi a matsayin abin da yake damun ta. Tabbatar mata da Abbi ya yi ita ba ƴar cikinsa ba ce ba ta da asali kamar yadda Adnan yake yi mata gori kullum ko kuma tunanin rashin masoyi na haƙika da ta yi? "Why Faris? Me ya sa ba ka bayyana mini soyayyar ka ba? Why Bloody? Kai nake so! Kai nake son kasancewa da kai har ƙarshen rayuwata, don Allah ka dawo gare ni Pleaseeeee!" Ta ƙarashe maganar tare da ɗora kanta a kan abin gado ta shiga bubbugawa. A hankali ta dinga furta "Astagfirullah." Saboda tunawa da ta yi da aurenta bai kama ta dinga tunanin wani namijin ba, duk da ta san hakan ƙaddararta ne, kuma har ta koma ga mahaliccinta tunanin Salman ba zai taɓa barin zuciyarta ba. Rarrafawa ta yi a hankali ta ɗauko alƙur'ani ta buɗe da niyyar karantawa don samun sauƙin damuwar dake cikin zuciyarta. Sai dai babu abin da idanunta suke iya gane mata daga cikin rubutun alƙur'anin, duk yadda taso cizewa ta karanta amma abu ya gagara, wani irin ciwo take ji ƙirjinta yana mata gami da juyawar kai. A dole ta ajiye alƙur'anin ta ɗauki drugs ɗinta ta sha ta kwanta. Ko 30 minutes ba ta yi da kwanciya ba aka buɗo ƙofar ɗakin aka shigo, ko a faɗa mata ta san waye, ƙamshinsa da a yanzu take jin shi tamkar ɗoyin kashin shanu ya ƙara tabbatar mata da haka. Gyara kwanciyarta ta yi tare da ƙara runtse idonta. Cikin taƙama ya ƙaraso gadon ya yaye duvet ɗin da ta lulluɓa, fuska a murtuke ya ce. "Where is my food?" Kamar ta share shi sai kuma ta taɓe-taɓe baki a ranta tana faɗin. 'Acici' Buɗe idonta ta yi da ƙyar ta dube shi, cikin raunin muryar dake nuni da tsantsar damuwar da zuciyarta take ciki ta ce. "Yana kitchen." "To da kaina zan zuba ko azzalumin ubanki zan kira ya zuba mini?" "Na faɗa maka ka daina zagin mahaifina a gabana, don ni ko a yaya yake ina son shi a haka, sannan kuma ba zan iya tashi ba saboda bana jin daɗi." Ta yi maganar cikin ƙarfin hali. A fusace Adnan ya riƙo gashin kanta cikin mugunta tare da faɗin. "Weldone TSINTACCIYA, mara asali da 'yanci, ke har kin isa ina magana kina musa mini, wato kin waye wuyanki ya isa yanka? Who are you? Kin yi kaɗan wallahi!" Fizge kanta ta yi saboda wata irin azaba da ta ji tun daga kanta har tafin ƙafarta, cikin kuka ta ce. "Wanne irin azzalumi ne kai mara imani da tausayi?" Dariyar rainin hankali ya yi ya ce. "Is your father, duk waɗannan abubuwan da kika lissafa halinsa ne ɗabi'arsa ce. Abra Khamal Khamis! Ko kashe ki na yi ban yi kwatankwatan zaluncin da mahaifinki yake aikatawa ba." Za ta kuma magana ya katse ta cikin tsawa da faɗin. "Za ki tashi ki yi abin da na saka ki ko ya?" Cikin kuka ta miƙe jiri na ɗibanta ta fice, har faɗuwa ta yi, amma ko a jikinsa. Bayan ta zuba masa abincin ta ajiye masa ya ce sai ta dafa masa coffee, ba ta yi musu ba ta dafa ta kawo masa cikin matuƙar dauriya da ƙarfin hali. Bayan ta koma ɗaki ta kwanta ta samu bacci ya ɗauke ta da ƙyar, amma Adnan ya zo ya katse mata baccin da buƙatar gangar jikinsa, cikin rashin imani da tausayi kamar yadda ya saba zuwar mata kodayaushe. Na'ima ce kwance a kan katifa idanunta a lumshe amma ba barci take ba, tunanin yadda za ta shawo kan Khamal ya haƙura ya mayar da ita ɗakinta kawai take. Idan ta tuno yanayinsa a lokacin da suka rabu sai ta ji gabanta ya yanke ya faɗi, saboda sanin da ta yi indai yay irin wannan fushin saukowar shi sai an ci ƙwaƙwa. Ba ta taɓa da na sanin tura Salman China da dagewa akan Auren Abra ba sai yanzu, don da suna nan ta san da yanzu tana gidanta, ko da Khamal ya sake ta ba zai kore ta daga gidansa ba, saboda gudun kar su Abra su shiga cikin damuwa, don idan akwai abin da Khamal ba ya so a duniyar nan bayan fushin iyayensa sai ganin ƴaƴansa a cikin damuwa. Cikin haka Nepa suka yi tsiyar su suka ɗauke wuta, hakan ya sa sauro ya fara shawagi. Tsaki Na'ima ta ja tare da yin juyi tana kore sauron dake yi mata kuka a cikin kunne. Ba ta kai ga sauke hannu ba wani ya millira mata cizo a gefen kunne, hakan ya sa ta tashi zaune ba shiri ta janyo wayarta ta kunna torchlight. Cikin mamakin take kallon Aunty Suwaiba dake baccinta hankali kwance, jinjina kai ta yi don ta san ita kam baccinta a haka ba zai yiyu ba in dai ba Nepa aka dawo da ita ba, ga wani irin zafi da ya rufe ta lokaci ɗaya. Gabaɗaya ta rasa sukuni, ta rasa inda za ta saka ranta. Baƙin ciki kamar ya kashe ta, ga sauraye sai watanda suke yi a jikinta. Ita kuma ba ta son maganin sauro balle ta kunna, mura yake saka ta. Wannan daren dai cikin wahala ta yi shi, sai washegari bayan Sallar Asuba ta samu bacci ya ɗauke ta. After 2 days Hajiya Na'ima ce tsugunne a gaban mahaifiyarta tana kuka tare da faɗin. "Kullum sai na kira shi sau ba adadi Mama amma ba ya shiga, na san kuma blocking ɗina ya yi, ko na yi masa text ma ba zai gani ba." Cikin damuwa ta ce. "Lallai ma yaron nan, wato shi ba ya uzuri a rayuwa ko? Bai san kuskure ba, ai ko Ubangijin da ya halicce mu muna saɓa masa kuma ya yafe mana. Amma ba komai, ba ni numbern Mahaifiyarsa mu tafi plan ɗinmu na biyu, in ya san wata ai bai san wata ba. Cikin rawar jiki Na'ima ta lalubo numbern Ammi ta yi dialling ta miƙa wa Mama wayar bayan ta shiga. Don ba ƙaramin gajiya ta yi da zaman gidan nasu ba, kullum cikin faɗa suke da Aunty Suwaiba, ga Faisal dake yi mata rashin kunya son ransa, saboda yana cike da haushin hana shi auren Abra da aka yi. Ga tattalin arziƙinta na neman ƙarewa a ɗan zaman da ta yi na kwana huɗu, ita ce sayan abincin gidan da kuɗin cefene, don Faisal daina bayarwa ya yi, ya ce tunda ta dawo gidan sai ta cigaba ita ma. Har ƙaton Gen. ta siya saboda ba za ta iya rayuwa cikin sauro da zafi ba, ga shi Mama kullum cikin cewa ta yi mata kaza ta saya mata kaza take. Gabaɗaya ta rame ta yi baƙi saboda damuwa da rashin kwanciyar hankali. Ammi tana ɗakin Baffa tana yi masa tausa a lokacin, kiran Na'ima ya shigo wayarta. Miƙewa ta yi ta ɗauko wayar, ganin Na'ima ce ya sa ta faɗin. "Alhaji ka ga ƴar halak, yanzun nan na gama zancen su ita ƴarta, na ce kwana biyu shiru ba mu gaisa ba, duk da ita Abran Babanta ya ce wayarta ce ta samu matsala." Ta ƙarashe maganar tare da daga wayar ta kara a kunnenta tare da yin sallama. Daga can Mama ta amsa mata, cikin mamaki Ammi ta ce. "Au Hajiya ke ce? Ina Na'iman?" "Tana nan ƙalau, daga yanda na ji maganarki da alama ba ku san abin yake faruwa ba." "Me ya faru kuma? Allah ya sa dai lafiya?" Ammi ta tambaya a ruɗe. Sanar da Ammi sakin Na'iman ta yi. Cikin jimantawa Ammi ta ce. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Subhanallahi! Baban nawa ne ya aikata haka? Da k'uruciya ma bai yi haka ba sai yanzu da girma ya fara kama su har an kai 'ya ɗakin miji? Wallahi ba mu sani ba bai sanar mana ba." "To dai yau kwananta huɗu a gida, abin dai ba daɗin ji." "Ku yi haƙuri Hajiya, insha Allahu za a daidaita tunda saki ɗaya ne, bari in kira shi yanzu." "Tom shikenan Hajiya mun gode, sai na ji ki." Bayan sun gama wayar Ammi ta kira layin Abbi, ta yi masa har 2 missed call amma bai ɗaga ba. Baffa dake sauraren duk abin da suka tattauna ya ce. "May be yana wani uzurin ne, idan ya gama na san zai kira, sai mu ji gaskiyar abin da yake faruwa." Ammi ta ce. "Haka ne, amma wannan abu bai daɗi ba ko kaɗan." "Allah ya kyauta kawai." Cewar Baffa cikin jimantawa. Kwance take a kan gado ta lulluɓe jikinta da bargo, fuskarta ce kawai a waje ta ƙura wa wuri ɗaya ido, ga dukkan alamu sana'ar tata take yi wato tunani. A haka Adnan ya shigo ɗakin ya same ta ba tare da ya yi sallama ba, uniform ɗinsa na police guda biyu ya watsa mata a jikinta, cikin ba da umarni ya ce. "Gashi nan ki wanke mini su yanzu-yanzu." Kallon kayan ta yi ta kalle shi ba ta ce komai ba, don ko magana ba ta son yi, saboda tarin damuwar dake cikin ranta, ga shi yau ta tashi ba ta jin daɗin jikinta, gaɓoɓin jikinta duka ciwo suke mata, ga ciwon kai da idan ana sabo da shi ta saba da shi, ga wata irin kasala da take ji. "I'm talking to you Madam!" Adnan ya faɗa cikin tsawa tare yin kanta. Cikin ɗaga murya gami da kuka ta ce. "Ba zan yi ba, idan ka tashi ka kashe ni, haba! Na gaji da wannan azabtarwar taka Adnan, ka yi mini duk abin da ka ga dama!" Ta ƙarashe maganar tare da tashi zaune ta ɗauki uniform ɗin nasa da niyyar ta cillar da shi, hakan ya sa ƙamshinsa dake manne a kayan bugar hancinta, da sauri ta saki kayan tare da toshe hancinta, don wani irin hautsinawa ta ji jikinta ya yi mata lokaci ɗaya. Dama tunda ya shigo ta shaƙi ƙamshin ta ji kamar za ta yi amai. Cikin masifa ya buɗe baki da nufin zazzage mata kwandon bala'i, miƙewar da ta yi cikin sauri kamar wadda aka tsikara ya hana shi abin da ya yi niyya, sakamakon ganin ta nufi toilet a guje ta fara kelaya amai kamar za ta amayar da kayan cikinta. It's not for free, contact us for more information. 09047871750 [10/24, 12:28 PM] Abk: Ta daɗe tana aman, sannan ta fito gaba ɗaya gaɓoɓinta sun saki, saboda yunƙurin amai. Ko da yake ba sabon abu bane a gurinta, dan haka kan faru da ita lokacin period ɗin ta. Ba ta ko kalli Adnan ba, ta wuce ta fara ƙoƙarin hayewa kan gado.   "Wai me kika mayar da ni ne? Na umarce ki ki mini abu, amma kin koma gado me kike nufi?". "Abin da idanunka suka gane maka, shi nake nufi" a sukwane ya yo kan gadon yana cigaba da bala'i "Ke kin isa babanki ya wulaƙantani, kema kice zaki mini rashin mutunci? Wato kin gado halin dabbanci irin na babanki". "Adnan! Kar ka sake zagin ubana,uba fa bai fi uba ba". "Kina nufin nima zagina za kiyi kenan?" Yayi Maganar yana nuna kansa da yatsa. "Allah ya tsare ni in zageka, ni mahaifinka uba na ɗauke shi, uba na gari makuwa, abin tausayi Allah ya bashi azzalumin ɗa mai fuska biyu". Taku ɗaya yayi, ya fizgota daga kan gadon, zai wanka mata mari, amma yaji jikinta zafi rauu, kamar an kunna wuta, hankaɗata yayi ta faɗa ƙasa ya nuna ta da yatsansa ya ce "Ko ki ɗau ubana uba, koma me kike ɗauke shi, abin da na sani shi ne, ubana yafi ubanki imani da mutunci, kuma na dawo na tarar da kayan nan baki wanke ba, sai na tattaka ki". Binsa ta yi da ido har ya fice. Girgiza kai kawai tayi, dan Yanzu zuciyarta ta fara bushewa da lamarin Adnan, dan haka a nan kan tiles ta gyara kwanciyarta, ta yi shiru abubuwa daban-daban na kai komo a kwanyarta. Hannu ya sa cikin sumarsa ya yamutsa ta, ya rintse idanunsa, a tunaninsa zuwan da yayi ya ga Abra, zai rage masa raɗaɗin da yake cikin zuciyarsa, da samun sassauci akan halin da yake ciki, duk da ya san hakan bai kyautu ba, kasancewar ita matar wani ce a yanzu, kuma ga alƙawarin da yayi, na ba zai sake zuwa Nigeria ba, amma ya kasa daurewa sai da yaje, amma zuwan nasa bai amfana masa Komai ba sai sake jefa shi cikin tarin damuwa da tambayoyi. Abra tana auren wanda take so amma ta furta masa kalmar so, yayi shiru tare da tuna yadda Adnan ya mari Abra saboda kishi, da yadda ya kira shi da loser "No! Am not a loser" ya faɗa yana dukan kan mirror. "Abra zata dawo gareni, amma ta yaya how? Wa zai bani goyon baya?" Can kuma sai wata zuciyar ta gargaɗe shi 'Ina imaninka da iliminka na Addini, duk wani abu da zakai yinƙurin aikatawa, don mallakarta alhalin tana matar wani ya saɓawa Shari'a' Rintse idanunsa yayi, tare da taune lips ɗinsa na ƙasa, da ya tuna yanzu Yaya ta san wacece ita, ta san matsayinta. Ko wani hali ta shiga lokacin da ta sani? Amma ya a kai ma ta sani, sam wannan bahagon mijin nata, ya hana shi ya samu ya sake da ita su yi hira. A hankali ya taka zuwa baki gado ya zauna, ya sunkuyar da kansa yana tunani. Abbi ya rasa ta ina ya kamata ya fara binciken iyayen Abra, sai yanzu ya gane cewar yayi kuskure, tsananin son Abra da tausayin ta lokacin da ya tsince ta, ya rufe masa idanu, ya kasa tsayawa yayi bincike a kan su waye iyayen Abra, ba tare da tunanin akwai rana kamar irin ta yau da zata zo ba, wanda dole Abra zata buƙaci sanin haƙiƙanin suwaye iyayenta. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, ya fara laluben wayarsa, sai dai yana dubawa ya ga missed calls ciki har da na su Ammi. Cikin hanzari ya shiga ƙoƙarin bin kiran Ammin. Ammi na ɗagawa cikin girmamawa suka gaisa. "Babana ina ka shiga ne haka? Ake ta kiranka baka ɗagawa?" Major ya ce "Afuwan Ammi, wayarce a silent". Ammi ta ce "Shikenan, kana gari ne?" "A'a Ammi, ina wurin aiki". "To duk abin da kake da ka shigo gari ka zo?". "Lafiya kuwa Ammi?" "Idan ka zo ka ji" "Shikenan dama shari'ar nan ce ta sanya na taho wurin aiki, amma tunda an kammala insha Allah zan biyo jirgin dare in taho". "To shikenan, Allah ya kawo ka lafiya" Ya amsa da "Ameen" Kamar yadda Abbi ya faɗa, a daren ya dawo gida, washegari da wuri ya shirya ya nufi gida, Mintuna kaɗan suka kai Abbi gidansu. Tun da ya ga Baffa a gidan a daidai wannan lokacin kuma da alama duk shi suke jira, ya sha jinin jikinsa. Ya gaishesu cikin girmamawa, sannan ya ɗora da Ammi "Gani, Allah yasa lafiya naji kin ce kuna nemana?" Baffa ya ce "Au tambaya ka ke ko lafiya? Kai ba abin kunya ne ba abin da ka aikata Kamal, da ƙuruciyarka ba ka saki matarka ba sai yanzu, kuma ace ba wanda ka kira ka gayawa wannan maganar? Sai su daga can gidan nasu ne aka kiramu aka sanar mana, me ka aikata kenana Khama? Wane laifi zata aikata maka a yanzu, wanda ba kayi haƙuri a baya ba, da har za ta kai ku ga saki, bayan har 'ya kun kai ɗaki". "Baffa dan Allah kuyi haƙuri, amma abin da Na'ima tayi mini bani da zaɓin da ya wuce aikata hakan". "Ka kyauta ai, sai ka tashi mu tafi can gidan nasu, mu zauna mu tattauna, a gano bakin zaren". Major ya ce "Baffa, zamu iya tattauna komai a nan, in gaya muku duk abin da ya faru". "Ba shawarar ka muke nema ba, tashi koma menene muje can a tattauna" ba yadda Major ya iya, haka ya tashi suka tafi gidansu Na'ima. Bacci ne mai nauyin gaske ya ɗauke Abra, sanyin tiles ɗin nan da ke ratsa ta ya sanya zazzaɓi ya ƙara rufeta sosai da sosai. Sai can azahar sannan ta farka daga nannauyan baccin da ya ɗauketa, har wani duhu take gani, saboda wata irin yunwa da take ji, ga jikinta babu daɗi. Ta kalli gurin da kayan Adnan suke a zube, kallon kayan kawai da tayi ta ji cikinta ya sake yamutsawa, zuciyarta ta fara tashi. Tsaki tayi ta ɗau kayan, tana toshe hanci, ga jiri na ɗibar ta ta tafi ɗakinsa, tana zuwa ta shiga toilet ɗinsa, ta zuba kayan a bucket ta fice. Ta nufi kitchen ta shiga buɗe buɗen kwanuka, ba abinda ta girka balle ta ci. Bredi ta tarar a kan dining, wanda Adnan ya karya ya fita, ta zauna ta dinga ci kamar mayunwaciya, sai da ta ci ta ƙoshi sosai, ta koma fridge ta ɗauko lemo mai sanyi ta sha sai da ta ji babu gurin zubawa komai sannan ta haƙura. A haka ta ɗora ruwa dan tayi wanka ta ɗora girkin rana, ta ɗan fara gyara gidan, duk da gidan ba wani datti yayi ba, tana yi tana kwanciya saboda gaba ɗaya jikinta babu daɗi. Cikinta ne ya fara juyawa kamar ɗazu da safe, nan ta dinga kwara amai, sai da ta amayar da duk abin da ta ci, ta dawo falo ta kwanta gaba ɗaya ta galabaita. Tun tana jin aman ta tashi ta tafi banɗaki, har ta koma toilet ta zauna gaba ɗaya, kan kace kwabo, Abra ta fita hayyacinta. Da ƙyar ta iya lallaɓawa ta yi wanka, shima ba sabulu iya ruwa ta watsa, ta dawo tai salla a zaune, ta kwanta. Amma amai bai tsaya ba dan ba ta fasa yinsa ba. "Kai muke saurara, kayi wa mutane bayani ya aka yi ka aikata wannan ɗanyen aikin, bamu sani ba laifin me tayi maka?". Major yayi ajiyar zuciya ya ce "Tun da na auri Na'ima, muka yi auren soyayya muke zane lafiya da ni da ita, har zuwa lokacin da na tsinci Abra, wanda tun daga wannan lokacin ta dinga bijiro mini da wasu irin halaye akan yarinyar, tana iƙrarin ni na haifi yarinyar da karuwa a waje, kuma ba zata riƙe ta ba. Idan ban manta ba a wancan lokacin na yi mata wani furuci na cewa, idan har ta bari wani yasan ba ni na haifi Abra ba daga gareta a bakin Aurenta. Sai ta dinga nuna mini bakomai, a gabana ta kula da Abra a bayan idona ta cutar da ita, wanda na daɗe da fukantar hakan amma nayi shiru na ƙyle. Ashe matar nan ta riga ta sanar da ɗanta cewar bamu muka haifi Abra ba, ina wurin aiki, na samu wayar mijin Abra ya haɗani da ita, yarinyar tana kuka ta sanar mini da cewa wai ashe bamu muka haifeta ba? Wanda na san ba mai gayamata sai Na'ima, kuma na dawo gida na tarar da wasiƙar da Salman ya bari a kan cewar ba zai sake dawowa Nigeria ba, ashe ya san Abra ba 'yar uwassa bace, ya fara sonta kuma ta sani duk ta munafunce ni, Wallahi Ammi bakiga a mawuyacin halin da na baro Abra ba, dan haka taje tayi rayuwarta nima in yi tawa, zan tabattar da samun farincikin yarana". Na'ima ta fashe da kuka tana faɗin "Wallahi ni ban gaya mata ba" Ammi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu kana nufin Abra ta san ba kai ka haifeta ba?". "Ta sani Ammi, ba kiga a yadda na baro ta ba, cikin matsanancin tashin hankali da damuwa, yanzu irin tsananin soyayya da shaƙuwar da ke tsakaninta da Salman da wani abu da ba a so ya shiga tsakaninsu fa a dalilin sanin su ba 'yan uwa bane? Duk bata kalli wannan ba amma ta sanar musu, ba yadda ban da Abra ba a kan ta gaya mini wanda ya gaya mata amma taƙi, wanda nasan dama ba zata gaya mini ba, saboda ba ta san ace ga laifin Na'ima dan ita uwa ta ɗauketa". "Wallahi ni bani na gaya mata". Ta sake Maganar cikin raunin murya. Baffa ya ce "Kuskure ne dai an riga an yi shi, amma kayi haƙuri ka maida yarinyar nan ɗakinta, ba shawara ba ce umarni ne". Abbi yayi jimm, yayin da ƙanin mahaifin Na'ima shima haƙurin yake bayarwa. Khamal ya ce "Shikenan, batun ɗan ta da ta sa na tura China kuma, sai taje ta nemo shi da kanta, dan dama ita tace a kai shi can, tun da yace ba zai dawo ba shikenan, dama mugunta ai fitsarin faƙo ce". Ammi ta ce "A'a ai duk ba za'ai haka ba, haƙurin dai shi zaka yi" aka haɗu akai ta bawa Abbi haƙuri, ya amince Mami ta koma ɗakinta. SP Adnan a gajiye ya dawo gida, saboda wani ƙauye suka je aiki, ya sha zirga-zirga, salla kawai yayi, ya duba fridge ya samu sauran juice da Abra take haɗawa ya sha. Bai nemi wurin da Abra take ba, ya shige ɗakinsa ya faɗa toilet dan yayi wanka, amma ya ga kayansa a cikin bokiti a banɗaki. Jinjina kai yayi da jinjina yadda Abra ta koyi taurin kai, wankansa yayi da niyyar ya kammala ya ci Abinci, ya ci ƙaniyar Abra. Sai dai bai ƙara tsinkewa da lamarin Abra ba, sai da ya duba ya ga ba tayi girki ba, ya duba kitchen ma bakomai.   A fusace ya nufi ɗakinta, yana zuwa ya tarar da ita a duƙunƙune cikin hijjabi tana ta bacci. Ƙafarsa ya sa yana takata ta tashi, amma ko motsi ba ta yi ba, baccinta kawai take. Yasa hannu ya ɗagota yayi wurgi da ita, zafin buguwar da ta yi ne ya sanya ta farka cikin wani irin razani. Adnan ta gani a gabanta yana wani irin zazzare idanu. "Dame kike taƙama har kike mini wannan iskancin a gida? Baki girki da safe ba, na bar miki wanki ba kiyi ba, dan kin mai da ni ɗan isaka, shine kika kai kayan banɗakina kika watsar, kuma still ba ki girki ba, me kike nufi?" Ikon Allah kawai take kallo, yadda yake ta zazzaga bala'i, babu alamar ma zai bata damar kare kanta. Sai da yayi ya gama ba tace uffan ba, ta miƙe a hankali ta fara ƙoƙarin gyara zaman towel ɗin jikinta. "Am i not talking to you Abra?" Ya sake tambayarta cikin tsawa. Hannayenta biyu ta sanya ta toshe kunnuwanta, dan ji take kamar a cikin kanta yake wannan ihun. Ganin ta toshe kunne ya sanya ya kuma harzuƙa, ya sauketa mata wani wawan mari a kan hannunta da toshe kunnen, wani irin zafi ya ratsata ta shiga zubar da hawaye, amma taƙi ce masa uffan, hannunsa ya sanya ya shaƙeta yadda ba zai mata illa ba ya ce "idan har kika cigaba da ƙoƙarin bijirewa umarnina a cikin gidan nan, Wallahi wahala zaki sha a gidan nan, sai kin gwammace kiɗa da karatu". Ai yana tsaka da maganar ta kyalayo masa amai a jikinsa, kallon Abra yayi cikin tsananin baƙin ciki ya hankaɗeta ta faɗi ƙasa, ta cigaba kakarin amai, sai dai babu komai a cikinta. Ya kalli hannunsa da jikinsa da ta ɓata amai, cikin takaici ya ce "Ƙazamar banza mara hankali" Ko ɗaga kaia ba tayi ba balle ta tanka masa, ya ƙare mata zagi ya fice. Gefe ta koma ta kwanta tana haki, saboda yadda ilahirin jikinta ke ciwo, tunani ta shiga yi a ranta, anya ba zata gudu ba, ko ta sanarwa Abbi irin halin da take ciki ba, sai kuma tayi tunanin dole Abbi zai shiga damuwa ya ga daga aurar da ita, har an fara samun matsala dan ta san tabbas sai ya kashe Auren nan. Tayi tunanin ko ta gayawa Abbi Adnan ya san waye mahaifinta, sai kuma taga idan har ta gayawa Abbi, to lallai fa zai gane irin zaman da take da Adnan, wanda hakan ne bata so, ba zata so ace daga yin Auren ace har Auren nata ya mutu ba, a fara lissafa mata Aure. "Ohhh Allah, Allah ka bani mafita. Faris come back to me, i need your help, kar wannan macucin ya kashe ni, bana son ɗagawa Abbi hankali, da saina kashe Auren nan" ta ƙarasa Maganar tana jin zafi a ƙirjinta. Na'ima Allah ya taimaketa ta koma gidanta, sai dai sam Major Khamal yaƙi bata fuska, ƙarewa idan ya fice tun sassafe ba zai dawo ba, sai can dare, ta shirya ta tafi sashinsa da nufin bashi haƙuri kamar yadda ta saba idan sun samu saɓani, amma ya koreta ya ce ta fita ta bashi guri. Gaba ɗaya zaman gidan sai yayi mata babu daɗi, ta san da yaran nan suna nan ko dan Albarkacin su kar su gane Akwai abin da yake faruwa zai haƙura, amma Yanzu da yake ba kowa sai ita kaɗai yaƙi saurarar ta, dan da alamu yayi fushi sosai da ita a wannan karon. Babban abin da ya sake jefata cikin damuwa shi ne yadda ya ce sai dai taje China ta nemo Salman, dan ba abin da yayi masa zafi da cewar da Salman yayi ba zai sake dawowa Nigeria ba. Gashi yanzu ta hankalta ta dawo daga rakiyar shawarwarin Anty Suwaiba dan ba in da shawarwarin na ta ke kai ta sai tashar Nadama!. Abra baiwar Allah, kwana biyun nan haka tayi su cikin tsananin ciwo, zazzafan zazzaɓi da amai ba ƙaƙƙautawa, ga bata iya cin komai, dan komai ta ci sai tayi amansa, Adnan kuwa ya daina ko zuwa in da take, idan ma ya zo sai dai ya tsaya daga bakin ƙofa ya zazzage mata masifa ya barta. Da safe ya shiga ɗakinta, ya tarar ta fito daga wanka, tana zaune a bakin gado, duk ta zabge ta rame sai idanuwa, so take ta shafa mai a jikinta amma ta kasa, hawaye ne kawai ke fita daga idanunta, kanta kamar zai tsage, dan bayan zazzaɓi har da damuwa ke damunta, saboda haryanzu zuciyarta na ƙuna akan rashin sanin haƙiƙanin suwaye iyayenta, ga Adnan ya sani amma azabar muguntarsa ya sanya ya ce na zai bari ta haɗu da su ba, kuma ko ta sanar da Abbi cewar Adnan yasan in da iyayenta suke, Adnan zai iya ƙaryatawa, dan ba ƙaramin makiri bane. "Ke! Nifa na gaji da wannan halin naki, ba zai yiwu na ajiye ki a gida, amma kullum sai na nemi abin da zanci ba, saboda baki da lafiya dole ki mini Abincin breakfast yau na gaji". Ɗauke kanta tayi, ta juya masa ƙeya, mai ɗauke da uban gashinta baƙi siɗik da ya sauka a kan gadon bayanta. "Ina miki magana kike juyowa mini wannan banzan gashin naki?". "Me kuma gashi na yayi maka, ko da yake ba abin mamaki bane, maybe burgeka yayi". "Meye abin birgewa a jikin duk wani abu da ya danganci zuriyarku, masu kyan ɗan maciji, miyagu azzalumai, ai duk wani abinda ya shafi mahaifinki muninsa ya ƙazanta". Cikin ƙarfin hali ta ce "Ai da yake gwano ba ya jin warin jikinsa, kai meye marabarka da miyagun maganganun da kake suffanta mahaifina da su? Wataƙila ma gara shi, baya neman matan banza, kai kuwa fa har karuwa ka kawo cikin gidanka dan abin kunya da..... Damƙe gashin kanta yayi, wanda azaba ya sanya tayi shiru, saboda tsananin zafi da ciwon da kan yake mata. Cikin tsantsar mugunta da rashin imani, ya cire towel ɗin jikin Abra, ya fara ƙoƙarin kwanciya da ita, duk da yadda yake jin wani irin hucin zafi da jikinta yake mata saboda ciwo. Kuka take sosai tana ƙoƙarin ƙwatar kansa, tare da kai masa duka, amma jikinta babu ƙwari, yayi abin da ransa yake so, cikin zallar mugunta tana kuka tana wani irin kakari na wahala, amma ko a jikinsa, sai da ya gama ya kalleta yana wani shu'umin murmushi ya ce "Idan nace zan gwada miki irin mugunta da zaluncin da mahaifinki yake yi, to mutuwa zaki yi, dan ba zaki rayu ba, zaluncinsa ya wuce duk wani tunani naki, ki sa a ranki ni ban iya komai ba a kan mahaifinki" Ido shine kaɗai abin da Abra ta iya raka Adnan da shi, ba ta san da ya zata misalta irin uƙubar da yake mata ba. 'Haka zaki zauna abubuwa na cigaba da kwaɓewa?' wata zuciyar ta tambayeta. Tana jinsa ya tada motarsa ya bar gidan, ta kai awa biyu a kwance, ko ƙwaƙwaran motsi ta kasa, daga bisani ta tashi da ƙyar ta shiga banɗaki ta gyara jikinta ta sanya kaya, ta duba tana da kuɗin da aka babbata lokacin da za'a kawota, ta zuba a jakarta ta nufi gate ta fice, wanda tun da aka kawota bata taɓa fita ita kaɗai ba. LITTAFIN KUƊI NE, KU SIYA KAFIN KU KARANTA. 0808102134 09047871750 [10/25, 4:54 PM] Abk: Tana tafe a hanya kamar za ta kifa, unguwar kamar quaters take, ita ko maƙotanta ba ta sani ba, dan Adnan bai bata damar ko sallama tayi musu ba da aka kawo ta, da ƙyar ta kai titi, dan ta huta babu adadi. Duk wasu shedu da yakamata, an tattara su a kan General Ibrahim mai retire,ya tabatta shine ya kashe karuwarsa a Hotel, kuma shike maƙarƙashi na bayyanar da sirrin tsaron ƙasa, dan haka yau Litinin ta kama ranar yanke hukunci, tun ranar Asabar Abbi ya tafi babban birnin tarayya Abuja, dan ganin shari'ar, Gwaska kuwa ya cika wandonsa da iska, ya bar Nigeria gaba ɗaya sai wasu daga yaransa aka kama. Abin kunya har da tsofaffin manyan 'yan siyasa, da suka riƙe manyan muƙamai a ƙasa a wannan almundahana da aka aikata. Bayan dogon turanci irin na kotu da alƙali ya gabatar, da faɗan manyan dokoki da ga cikin littafin da suke dogaro da shi gurin shari'a, aka yankewa General Ibrahim mai retire kisa ta hanyar rataya, abin da ya ƙara bawa mutane mamaki shine, hatta Manyan ƙusoshin gwamnatin nan, da aka samu da laifi hukuncin kisa aka yanke musu, abinda ba'a taɓa yi ba a ƙasa, amma aka basu damar ɗaukaka ƙara. General Ibrahim duk ya rame, tsufansa ya fito, ga shi zamansa a gidan yari, cututtuka suka baibaye shi, yana ta fama da ciwon zuciya da kuma ciwon sugar. Nan da nan jaridu da gidajen rediyo suka samu abin faɗa, ga lawyoyi duk sun karɓe masa 'yan kuɗaɗensa akan cewar zasu taimake shi yayi free. Adnan tun da ya tafi gurin aiki, sai tunanin yanayin da ya bar Abra ya dame shi, saboda jikinta da zafi sosai kamar wuta, kuma babu alamar tana iya cin wani abu. Tsaki yayi tare da ƙoƙarin cire tunaninta daga ransa, amma ya kasa ko yayi yinƙurin cigaba da aiki, da ya tuno ta sai yaji ya damu, ana haka Usman ya zo ya same shi a Office. Yayi sallama amma maimakon Adnan ya amsa sai yayi tsaki, Usman ya kalleshi ya ce 'Lafiya kuwa ina sallama amma kana tsaki?". Adnan ya kalleshi ya ce "Sorry, hankalina ne a wani gurin shiyasa". "Ok, ya garin ya Madam kuma?". "Wai kai ina ruwanka da Madam ɗin nan da kullum sai ka tambaye ta?". "To tambayar ma laifi ce kenan?" Adnan ya ce "Eh kusan haka, dan da bata lafiya ba zaka ganni a kan kujerar nan ba". Usman yayi murmushi ya ce "Yayi mijin balarabiya". "A daina tanka mini mata dan Allah, duk bakinku ya sa ta fara duhu" "Eh tunda gamu mayu ba". "Ni dai bance ba" Adnan yayi Maganar yana murmushi. Adnan ya ce "Wai ni ya batun Meenal ne, na jika shiru, ka rigani haɗuwa da ita fa kan in haɗu da Abra, amma haryanzu shiru, kar kayi wasa da hankalin 'yar mutane fa". Usman ya ce "Hmm" "Ban gane hmmm ba?" "Sp zancen babu daɗi ne sam, ni na fasa Auren Meenal" "Amma mai yasa?" "Abubuwan babu daɗi ne sam, amma zan maka bayani". "Allah ya sa ba daga gurinka aka samu matsalar ba Usman?" "Ba daga gurina bane, amma nasan ko kaine, abin da nayi shi zaka yi". "To shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi" suka gama hirar aikinsu. Suna magana amma hankalin Adnan yana kan Abra, haka ya lallaɓa ya kai azahar, yayi sallah ya tafi gida. Yana zuwa gida ya nufi ɗakin Abra, amma ya tarar ba ta ciki, kayanta da ta cire a ƙasa a tsakar ɗakin. Ya buɗe ƙofar banɗaki, amma bata ciki. Ya shiga ƙwala mata kira "Abra! Abra!" Ya duba kitchen amma ba ta nan, ya tafi ɗakinsa amma nan ma ba ta nan. Nan hankalin Adnan ya fara tashi, da ya tabbatar da Abra ba ta gidan gaba ɗaya. "Ina yarinyar nan ta shiga haka?" Ya tambayi kansa, gashi babu waya a hannunta balle ya kirata. Waje ya fita yana lelleƙawa, amma layin nasu tsit yake, ba kowa balle ya tambayi wani. Bai sare ba ya shiga bi gidajen dake kusa da nasu, yana ƙwanƙwasawa yana tambayar masu gadi, idan Abra taje amma ko ina sai suce su basu ganta ba, ba taje ba. Abra kuwa bayan ta isa titi, mai napep ta samu ta gaya masa sunan unguwar su Adnan, da suka isa unguwar, tace mai napep ɗin ya tambayi gidan Aliyu Matawalle. Ya ce mata ai yasan gidan, ya kaita har ƙofar gidan. Ta biya shi kuɗin motarsa, ta sauka ta shiga gidan tana bin bango, saboda tsananin ciwon da kanta yake mata, da kuma zazzaɓin da ya addabeta. Mai aikin hajiya Mama ce ta buɗewa Abra ƙofar falon, tana ganin Abra ta fara murmushi tana mata sannu da zuwa, Abra ta jinjina mata kai kawai, ta wuce cikin falon ta zube a kan kujera tana maida numfashi. Mai aikin ce taje ta kirawo Mama, tana fitowa ta tarar da Abra a kwance a kan kujera, tana sauke numfashi da ƙyar. Da sauri Mama ta ƙarasa in da Abra take tana faɗin "Abra lafiya kuwa?" Tayi maganar tana dafa kan Abra, jikin Abra zafi rau. Mama ta kalli mai aikinta ta ce "Ɗauko mini wayata in kira likita". Ta kuma kallon Abra ta ce "Ina Adnan ɗin yake?" Cikin rawar murya Abra ta ce "Ya tafi gurin aiki, ni kuma naji zan mutu shine na taho nan" "Amma wane irin rashin hankali ne Adnan yayi haka? Yaya za ayi matarka ba lafiya ka tafi aiki ka barta?" Mama ta kira likita a waya, sannan ta sa aka haɗawa Abra Abinci, ba ta ci da yawa ba, ta dinga amai. Likita ya ƙaraso gidan Hajiya Mama, ya yiwa Abra tambayoyi, ya yi mata allurai ya samata ruwa sannan yace da Mama "Idan jikin nata yayi sauƙi zuwa yamma shikenan, idan Allah ya kaimu gobe zan dawo in kuma duba jikin nata, sai ku taho da ita Asibiti for further investigation". Mama tace "to shikenan" Abra taji daɗin jikinta sosai, har sakwara Mama ta sa aka yi mata, ta samu ta ɗan ci. Abra ta ce "Mama dan Allah ki bani aron waya in kira su Mami". "A'a Abra, ba zaki kirasu ki ɗaga musu hankali ba" Abra ta marairaice ta ce "Mama tunda nayi Aure fa ya ƙwace mini waya, bana waya da kowa a gida, ba ɗaga musu hankali zan yi ba". 'mai yasa ya ƙwace miki wayar?" Abra ta ce "Nima ban sani ba" Mama ta girgiza kai ta bata wayarta. Wayar Abbi ta fara sanyawa ta kirashi, bugu biyu ya ɗaga "Hello Abbina". "Daughter na, ya kike ya jikin naki?" "Da sauƙi Abbi, ina Mami?" "Mami tana bacci". "Abbi ka tasheta ka bata muyi magana, tunda na bar gidan fa banyi waya da ita ba". Duk da Abbi baya shiga sabgar Mami, amma saboda farincikin Abra ya tafi ɗakin Na'ima, ya miƙa mata waya. Ta kalleshi da mamaki ta ce "waye?". "Ki karɓa kiji". Ta karɓa ta kara wayar a kunnenta. 'Hello Mami" "Na'am Abra" "Mami ba kya nemana ko? Kin ƙi zuwa gidana" Na'ima ta ce "Na nemi wayarki na ta shiga, kuma mijinki idan aka kira shi kullum baya nan". "Mami to ba zaki zo ba?" "Zan zo mana, amma jira muke a gama haɗa kayan garar ki, sai mu taho gaba ɗaya". "Haba Mami, ni dai kawai ki zo dan Allah, in ba haka ba ni zan dawo gida". "A ina kika taɓa ganin an yi haka? Ki kwantar da hankalinki zan zo insha Allah". "To Mami yaushe?". "Ba zan sa miki rana ba, amma zan zo insha Allah" Bayan waya da Mami, Abra har su Ammi ta dinga kira a waya, tana musu koke koke, sukai mata alƙawarin za so zo. Adnan fa hankalinsa yayi ƙololuwar tashi, ya rasa abin da yake masa daɗi, dan ya fara tunanin sanar da hukuma. Kafin yayi hakan, ya ɗau motarsa ya nufi gidansu, cike da zullumi da tunani. A falo ya tarar da Hajiya Mama, tana ganinsa ta ce "Yawwa dama kai nake nema". "Lafiya kuwa Mama?". "Dole ka tambayeni lafiya mana, ka fita ka bar Yarinya a gida babu lafiya, Allah yasa tayi kyan kai ta fito ta taho nan, a galabaice ta ƙaraso gidan nan". Adnan ya ce "Alhamdilillah, dama nan ta taho?". "Ban sani ba" Mama ta bashi amsa, Adnan ya sunkuyar da kai yana sosa ƙeya. "Tana ɗakina, likita ya bata magunguna ya sa mata ruwa, yace gobe in Allah ya kaimu kuje Asibiti ai mata teses". Adnan ya jinjina kai ya miƙe, ya nufi ɗakin Mama ya tarar da, Abra a kwance a kan katifa da ruwa a jikinta, hannunta ɗaya riƙe da wayar Mama. "Da iznin wa kika fita ki ka bar gida? Kika bar mini gida a buɗe ba kowa?" A hankali ta ɗaga idanunta ta kalleshi, ta ɗauke kanta ta mayar kan waya. "Ba Magana nake miki ba". "Dan Allah ni ka ƙyaleni in ji da kaina, idan ba haka ba Wallahi saina faɗi irin zaman da muke kowama yaji gayyar ta watse in huta da bala'inka da zaluncinka". "Ni kike gayawa haka?". "Na faɗa, idan kana da wuta ko Aljanna ka sani a ciki". Ƙwafa yayi, ya fisge wayar hannun Abra ta Mama, ya fito falo. Ya miƙawa Mama wayarta, Mama ta ce "Yauwa, maiyasa ka ƙwace mata waya ne? Ko waya bata yi da mutan gidan su". "Wallahi Mama takura musu da koke koke take tana ɗaga musu hankali, a kan bata da lafiya". Mama ta ce "ba hujja ba ce, ka bata wayarta, umarni nake baka, wannan ai mugunta ce, ka hanata waya da mutan gidansu akan me?". "Shikenan zan bata, bari ruwan ya ƙare in ɗauketa mu tafi". "A'a ka bari sai Allah ya kaimu dare" Cikin ikon Allah zuwa daren, Abra ta ɗan watstsake sai rashin ƙwarin jiki. Ji take kamar tace ba zata bin Adnan ba, amma ta dake ta tashi suka tafi. Suna tafe ba wanda yake tankawa wani har suka isa gida, kusan ƙarfe sha ɗaya na dare. Ba ta saurari Adnan ba ta wuce ɗakinta, ta gyara ta kwanta. Da safe kafin ya fita aiki ya shigo ɗakin, ya tarar da ita a zaune a kan gado, dan fitowarta kenan daga wannan aman da take. Ya cillo mata wayarta ya ce "gata nan, kin haɗani da mahaifiyata ta sa na baki wayarki, amma Wallahi muddin kika kuskura naga kina waya da wancan sakaran yaron ko makamancin haka Wallahi sai na ƙwace". "Wallahi ba sakarai bane, Faris ba sakarai bane dan ya fiye mini kai". Da wani irin mugun kallo ya bi Abra "Ni kike gayawa wancan shashashan ya fini?". "Eh, ya fiye mini kai, dan tsawon tasowata ya bani kariya da kulawa, kai kuma a zamana da kai ba abin da na tsinta banda ɓacin rai da tashin hankali a kan abinda ban san tushensa ba, wanda yayi maka laifin ma ban sanshi ba balle in san laifin da aka yi maka, dan haka na faɗa Faris ya fiye mini kai" Janyota yayi daga kan gadon, ya tsaida ita a kan ƙafafuwata, "Wallahi Abra idan kika kuma Magana a kan wannan banzan Salman ɗin saina casa ki". "Wallahi Salman ba banza bane, kar ka sake ce masa banza" Sauke mata wani lafiyayyen mari yayi ya ce "Nine banzan kenan?". "Wallahi Adnan kaci amanata, ba zan yafe maka ba, kai da Allah" hankaɗeta yayi a gurin ta zube, ya dinga wani irin huci, dan ya tsani yaji tana ambatar sunan Salman, sai dai ya ga Abra bata motsi, ga jini ya fara bin ƙafarta. Sai kuma ya nutsu, ya sunkuya ya ɗagota, amma bata motsi sai jini da yake bin ƙafarta. Sai kuma ya gigice, ya ɗagota jikinsa amma yaga jikinta ya saki, ba shiri ya miƙe ya gyara mata jikinta, ya sata a mota sai Asibiti. 6hrs later Abra ta buɗe idanunta, dishi-dishi take gani, a hankali ta gama buɗe idonta, ta kalli ruwan da ke shiga jikinta, da ƙyar ta tashi zaune, Adnan ya taso daga in da yake, kan ya ƙaraso Abra ta fizge ruwan nan daga jikinta. "Ke meye haka?" Ai bai rufe baki ba ta fara ƙoƙarin dirowa daga kan gadon. Aikuwa jini ya ɓalle ta jikin cannula hannunta, Adnan ya ƙaraso ya riƙeta yana faɗin "Abra kin yi hauka ne?" Duka ta dinga kaiwa Adnan a ƙirjinsa, tana ƙoƙarin fizgewa daga jikinsa. "Abra ki nutsu meye haka? Akwai ƙaramin ciki a jikinki, da yake barazanar zubewa ki nutsu". "Insha Allah sai cikin nan ya zube, Allah sai ya saka mini Adnan, insha Allah sai cikin nan ya zube ba zan haihu da kai ba". Jinin da take zubarwa a hannunta duk ya ɓata masa jiki, Nurses ne suka shigo dan bawa Abra magani, amma suka tarar da halin da take ciki, da ƙyar aka dannenta aka yi mata allurar bacci, duk ta galabaitar da kanta. Gargaɗi sosai likitan da ta duba Abra ta yi wa Adnan a kan a guji abin da zai dinga jefa ta a cikin damuwa, gudun kar a rasa ta ita da abin da ke cikinta, sannan ta ba ta bedrest na sati biyu. Ya kira Mama ya sanar mata halin da ake ciki, ta aiko mai aikinta ta kawo musu kayan buƙata, saboda ita ta je unguwa kuma wurin da nisa. Sai bayan Magriba Abra ta ƙara farkawa, har lokacin Adnan yana zaune a gaban gadon da take yana latsa waya. Duk da wata irin kasala da take ji amma haka ta daure ta tashi zaune. Cikin kulawa ya ce. "Kin tashi? Ya jikin naki?" Wata uwar harara ta wurga masa ba tare da ta ce komai ba, sai dafe kanta da ta yi. Miƙewa ya yi ya ce. "Ba dai kan ne ke ciwo ba? Sannu, How are you feeling now?" Tsaki ta ja cikin takaici ta ce. "Shut up Malam! Haba, tun ɗazu sai ihu kake mini a ka, Please ka bar gurin nan in daina ganin ka don bana ƙaunar ganin ka ko kaɗan wallahi." Murmushi ya yi ganin yadda ta yi maganar cikin tsiwa, wadda ba ta dace da ita ba sam. Bai ce komai ba ya juya don kiran Likita, ganin drip ɗin da aka saka mata ya ƙare. Lumshe idonta ta yi bayan ya fita, kalamansa na ɗazu ne suka dawo mata cikin kunnenta da yake cewa tana da ƙaramin ciki. Wasu hawaye masu ɗumi ne suka fara zuba daga cikin idonta. A fili ta furta. "Allah na gode maka da duk Yadda ka tsara rayuwata ta kasance, Allah ka ba ni ikon cinye jarrabawar cikinta." Slowly ta kai hannunta kan cikin ta shafa cikin wani irin yanayi, wanda ta kasa tantance na farin ciki ne ko akasin haka. The thing is so amazing to her, wai yau ita ce ɗauke da juna biyu? Za ta haifi girl or boy nan da wasu watanni? Za ta zama uwa ita ma? Dawowar Adnan tare da wata Nurse ya katse mata tunanin da take. Saurin share hawayen fuskarta ta yi ba tare da ta bari sun haɗa ido da ɗayansu ba. "Patient, ya jikin naki?" Nurse din ta faɗa cikin murmurshi. "Alhamdulillah." Ta amsa mata cikin sanyin murya. Bayan ta cire mata drip ɗin Abra ta dube ta in serious talk ta ce. "Don Allah Nurse ki taimake ni ki cire mini cikin dake jikina, ko ki faɗa mini abin da zan sha ya ɓare." Cikin matuƙar mamaki Nurse ɗin take duban ta, kallon Adnan ta yi ta ce. "A'a ba mijinki ba ne wannan? Ke kuwa me zai saka ki so rabuwa da Ni'imar da Ubangiji ya yi miki? Abin da wasu suke ta fafutukar nema ba su samu ba." "Ni dai in za ki taimaka mini ki taimaka mini kawai don Allah." Nurse din za ta yi magana Adnan da ya kafe Abra da ido ya ɗaga mata hannu tare da faɗin. "Don't worry, you can go idan kin gama yi mata abin da za ki mata, i will solve the problem." "Okay, Allah ya ƙara lafiya." "Amin, thank you." Kuka Abra ta saka bayan Nurse din ta fice, cikin ɗaga murya ta ce. "Kome za ka yi ba zan bar cikin nan ya zauna ba, domin ba zan so na hahu tare da azzalumi mugu mara imani ba." Wani murmushi ya yi ya ce. "Tunda Mother ta haƙura ta haife ki da azzalumin mutum ke ma sai ki haƙura ki haifa, kin ga an yi 1/1 kenan." Ya ƙarashe maganar cikin ɗage gira. Saboda baƙin ciki kasa magana ta yi, sai kuka da ta kuma fashewa da shi. Still yana murmushi ya tashi ya koma gefen gadon tare da zama daf da ita, ƙoƙarin ja baya ta yi saboda ƙamshinsa da ba ta ƙaunar shaƙa ko kaɗan, amma ya hana ta aiwatar da hakan sakamakon hannunsa da ya sa ya zagaye bayanta da shi tare da ƙara matsawa jikinta. Yana bin ta da wani irin kallo ya ce. "Abra Mrs Adnan, yau babu faɗa da rigima a tsakaninmu, saboda farin cikin da nake ciki na samun new Unborn." Ya ƙarashe maganar tare da ɗora hannunsa a kan cikinta ya fara shafawa a hankali. Cikin tsananin baƙin ciki Abra ta fizge jikinta, ji take kamar ta kikkifawa fuskarsa mari. Saurin riƙo ta ya kuma yi tare da faɗin. "Ki yi a hankali, kar ki illata mini gudan jinina." Tsaki ta ja ta juya masa baya ta kwanta, zuciyarta na mata tuƙiƙin baƙin ciki, ita kaɗai ta san abin da take ji a cikin ranta, Allah ya sani ba ta so haɗa zuri'a da Adnan ba, amma babu yadda za ta yi da ƙaddara. "Me za ki ci?" Ta tsinkayi muryarsa yana tambayar ta, banza ta bawa ajiyar shi. Shi kam ko a jikinsa, da gaske yake har cikin ransa yana ƙaunar abin da ke cikin Abra sosai, shi kansa ya yi mamakin faruwar hakan. Lumshe idonsa ya yi yana imagining ranar da Abra za ta haifa masa Baby, bai san irin farincikin da zai yi ba a lokacin. Bai haƙura ba ya cigaba da tambayar Abra abin da take son ci cikin lallaɓawa, ita kuma ta ƙi kula shi ta bar shi yana ɓaɓatu shi kaɗai. A haka Hajiya Mama ta zo ta same su, ba ƙaramin farinciki ta yi ba da jin Abra na da juna biyu. Ta dinga nan-nan da ita tare da ba ta kulawa. Ita ta kwana tare da Abra, ta ce Adnan ya koma gida. Washegari aka sallami Abra, Gidansu Adnan Hajiya Mama ta wuce da ita sai dare sannan Adnan ya zo ya ɗauke ta suka koma gidansu, tare suka tafi da mai aikin Hajiya Mama za ta zauna a gidan har zuwa lokacin da Abra za ta samu lafiya. Cikin ƴan kwanakin nan ta samu sauƙin tijara da takurar Adnan, don sosai yake nuna k'aunar cikin jikinta, amma in abin ya motso masa yana taɓawa. Ba ta kula shi saboda ba ta shi take ba, ta jinyar kanta take. Ga mai aikin Hajiya Mama tana ɗebe kewa sosai, don matar babu ruwanta tana da kirki. Yau kwana biyar da sallamo ta daga asibiti, da daddare tana kwance a ɗakinta suna chatting da Abbi yake mata zancen karatunta. "Daughter tunda an gama cin amarcin ya kamata a koma school kuma." Murmushi ta yi cikin jin kunya ta tura masa emojin rufe fuska. A hankali ta kai hannu ta shafa cikinta, tana jin yadda wata zazzafar soyayyar shi take zagaye ko wani gurbi na zuciyarta. Abbi bai san tana da ciki ba, shi ya sa yake mata zancen karatu, ta sanar masa dai ta yi ciwo, amma ba za ta iya faɗa masa tana da ciki ba. Sai dai ita ma tana son ta cigaba da karatun, damuwar da take ciki ne ya sa ta manta da babun shi, tunin Abbinta kuma a yanzu ya dawo mata da son karatun, ko ba komai idan tana zuwa school ɗin zai rage mata damuwa tare da ɗebe mata kewar kaɗaici. Sallama suka yi da Abbi ta miƙe ta nufi ɗakin Adnan. Tana shiga ta tarar da shi yana shiryawa, alamun bai jima da fitowa daga wanka ba. Kallo ɗaya ta yi masa ta ɗauke kanta, saɓanin shi da ya ƙura mata ido. Cikin haɗe rai ta ce. "Magana na zo mu yi Adnan." "Ba ni da lokaci." Ya faɗa tare da ɗauke idonsa daga kanta. "Kamar ya ba ka da lokaci? Maganar karatuna ce to ba wani abu ba, Abbi ya mini magana ya ce ya kamata zuwa yanzu na koma school, kar a mini nisa da yawa. Kallon sama da ƙasa ya yi mata ya ce, "Lallai wuyanki ya isa yanka, wato kwana biyu na sake miki shi ya sa har kika samu damar faɗa mini magana son ranki, saboda ba ki jibgu ba ko? To darajar cikin jikinki kike ci, domin duk ranar da ya bar jikinki sai na fanshe duk bashin da kika ɗauka." "Is not my concern, ka yi ko ma mene ne, ni yanzu maganar karatuna nake maka, ya ake ciki?" "To ba za ki cigaba ba, ke da karatu har abada in dai a gidan Adnan Aliyu Matawalle ne, saboda karatu na masu asali, gata da ƴanci ne, ba na TSINTATTU irin ki ba." Littafin kuɗi ne, ki/ka biya kafin ku karanta. Don neman ƙarin bayani 09047871750 [10/27, 11:38 AM] Abk: Kallonsa take cike da takaicin yadda gaba ɗaya yake son ɗauke mata dukkan wani farin ciki na rayuwarta. "I am your husband and I have control over you, karatu ne ke dashi har abada sai a lahira idan anayi, Everything I know will make you happy so I prevent it from happening.. Ki daina wahalar da kanki kina wahalar min da unborn okey" "Zaka iya hanani farin ciki, amma baka isa ka ɗauke mini raina ba, duk wahala duk tsananin nasan Ubangiji yana tare dani kuma shi ne zai saka mini akan cutar da kake aikatawa a gareni, I'm your wife amma na zama jaka a wajanka mara ƴan ci, ka sani ko Ubangiji baya kama bawa da laifin da bai san ya aikata ba, balle Mutum akwai haƙƙina a rataye a wuyanka" Tana faɗin hakan ya juya, har yaje baƙin ƙofa ta tsaya ba tare data kallesa ba tai Murmushi wanda yafi kuka ciwo ta ce. "Ciki? Ur unborn. Uhm you are doing wrong Sp Adnan Aliyu Matawalle, kayi gaggawar cire son abin da ke cikina daga zuciyarka, domin babu tabbacin zai haifeshi, Ba zan taɓa haihu da kai ba, inma na haihu zan shaidawa abin da na haifa cewa ubansa ba Mutumin ƙwarai bane. Azzalumi ne, Macuci ne, mayaudariya, mara imani ne, bashi da tausayin ƴa mace a ransa balle matarsa wacce tayi sanadin zuwan yaron duniya. Na tsaneka wallahi bana ko ƙaunar ganinka" Ta ƙare maganar wani raunataccen kuka na ƙwace mata, domin duk yadda ta kai ga hqr da kuma ɗauke kai na abin da yake mata, zuciyarta ta kasa ɗauka. Bata taɓa tunanin masoyinka zai juye zuwa maƙiyinka ba, ita a yanzu ta daina yi wa Adnan kallon maƙiyi, kallon makashinta take masa wanda yake ƙoƙarin kassara rayuwarta dayin sanadiyar Zuwanta zuwa koshewa. "Whatever Abra, i like your style ƙarfin halinka yana ban sha'awa. Ciki kuma idan kin fasa cirewa baki haifu cikin wannan mugun azzalumin uban naki ba, wanda ya maida son zuciya, halinsa, ɗabi'arsa da kuma bangon da yake jingina ni dake shege ka fasa, wawiyya. Get out of my room mumu" Kukanta ne ya tsaya sai kallonsa kawai da take tana sauke ajjiyar zuciya a wahale, domin gaba ɗaya hanyar shaƙar numfashinta toshewa tayi for some minutes. Juya tayi zata fita ya yi saurin cewa. "And if anything happens to my unborn ki kuka da kanki" "Idan fitsari banza ne kaza tayi mana? zaka iya ɗaukan cikin ka mayar zuwa naka" murmushi Adnan ya yi ganin abin na su ya zama kamar drama cikin shafa ƙirjinsa yana watsa hannunsa zuwa sama ya ce... "Tunda nai cikin, ai hakan mai sauƙi ne yarinya. Kuma da kike mgnar kaza mene? Ai ni ne wanda zan faɗi haka tunda gudunmawata yafi yawa wajan samar da cikin" Banza tai masa tare da ficewa daga cikin ɗakin zuciyarta babu daɗi gaba ɗaya. Idan tai tunanin saɓawa Adnan sai kuma ta tuna makomarta. Ita sam ba haka ta san ana rayuwar aure ba, ta karanta a Omdatul ahkam, Zadil zaujen, da sauransu. Koda yake daman ya ce bai aureta saboda yana son ta ba, ya aureta ne sbd hutar ɗaukan fansa da kuma rayuwa da abin da ya yi a zuciyarsa. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un. Wayyo ni Abra What should I do?" Ta tambayi kanta lokacin data ke zama a kan kujerar parlourn. Idanunta ya yi jaa sosai daman yawan azkar da karatun Alqur'anin da take yana ɗauke mata damuwar da Adnan ke cusa mata a zuciya. Sulalewa tayi a saman carpet tare da kwanciya sbd yadda take jin ƙasusuwan jikinta na mata zafi da ciwo kamar zasu karye. Ga matsanancin ciwon kai duk da yunwar da take ji amma hakan bai sa ta miƙe ba, gaba ɗaya gaɓoɓin jikinta sun saki a nan wajan barci ta ɗauketa. Cikin dare wani zazzafan zazzaɓi ya rufeta ruf, banda huci babu abin da jikinta keyi, sai rawar ɗari take hatta idanunta ta kasa samun zarafin buɗewa balle ta samu ƙarfin qwiwar barin parlourn. Sunayen Allah ta shiga shiga furtawa cikin zuciyarta da kuma neman ɗauki daga garesa. Kiran sallar Subhi da ake yi ne ya sanya Adnan motsawa bakinsa ɗauke da addu'ar tashi daga barci, gently ya buɗe idanunsa wanda sukai masa nauyi duk da kwana biyu baya iya barci abubuwa da yawa ne suke damun cikin tunaninsa. Miƙewa yai tare da ɗaukan wayar, ƙuri ya yiwa screen ɗin wayar tamkar mai neman wani abu, amma ya kasa fahimtar mene yake nema ɗin?. Kai tsaye Bathroom ya nufa ya sakarwa kansa shower tare da ɗaura alwala. Da sauri ya zuwa Arabian jallabiya ya fito zuwa parlourn da nufi shigewa masjid. Sai dai fitar numfashinta da sauri ya ankarar da shi, manyan idanunsa ya zaro waje ganin yadda ta zazzago daga saman kujerar zuwa ƙasa jiki na rawa ya Ƙarasa yana faɗin. "Abra! Ke Abra mene haka" Adnan ya faɗa yana ɗan bubbuga kafaɗarta, ganin ko motsi ba tayi. A hankali ya zameta tare da ɗagota baki ɗaya a karo na farko ya nufi part ɗinsa da ita, A zuciyarsa yana mmkin abin da ya jefata cikin wannan halin ko ciwon nata ne ya motsa? Juyawa ya yi bayan ya kwantar da ita a saman makeken gadonsa ya nufi masjid. Abra na jin duk abin da yake faɗa kawai bata da kuzarin motsawa ne balle ta buɗe idanunta, tana nan kwance ya dawo kai tsaye kuma wayarsa ya ɗauka ya kira number likitar data dubata, cikin ikon Allah aka ɗaga kiran. "Hello, I Adnan Aliyu Matawalle speaking, Abra's husband" "Oh Yeah. How is she is everything ok?" Dr ɗin ta tambaya domin tana kan bakin aiki sbd kwana tayi hospital shida nayi kuma zata bar wajan zuwa gidanta. "Allhmd, sai matsalar zazzaɓi yanzu haka dashi ta kwana ga wayan ɗaukewar numfashi" ya faɗa a sanyaye sbd ganin har yanzu cikin duhun asubahi ne. "Don't worry, zazzaɓin zai daina sai cikin ya yi ƙwari Maybe kalar nata laulayin kenan. A kula dai sbd cikin fari ne" Shafa kansa yai kamar zai shiru sai kuma ya ce. "Insha Allah. Zazzaɓin fa?" "Be with her, sanyin jikinka zai taimaka wajan sauke zafin jikin nata" jinjina kai ya yi kana yai mata gdy tare da kashe wayar yana bin Abra da kallo musamman lafaffan cikinta. Mami ce ta fito daga cikin bedroom ɗinta ta ɗauki wanka sai baza ƙamshi take, cike da muradin shawo kan Abbi ta nufi nasa sashin. Yana zaune a Parlourn dake part ɗinsa hannunsu riƙe da coffee yana sha a hankali, gabansa kuma system ce ya doƙufa wajan yin searching na abu. Sarai yaji shigowar ta, sanin amsa Sallama ɗaya cikin abin da Musulunci ya zo dashi, ya sa ya amsa can cikin maƙoshi, bare daya kalli ko inda take ba. Rashin sakin fuskar Abbi yasa duk jikinta yayi sanyi, muryarta na rawa ta ce. "Good Mrng Man" nan ma ya yi mata banza kamar zatai kuka ta ce. "Haba don Allah, na baka hqr nayi magiyar amma duk a banza, wallahi ban aikata lafin da kake tunanin nayi ba sai dai idan wani ke nufina da sharri, Ka dubi abin nan ka yafe min ina jin babu daɗi ganin yadda muke rayuwa,babu rana kusa dani babu farin cikinka na shiga uku" Hannunsa ya ɗaga mata ya ce "Point of corrections babu yaronki kusa dake, ba yaranki ba ok" "mekake nufi? Yanzu da ace Abra nan ai da naji sauƙin wani abun" "Yanzu kika san muhimmancin Abra? ba fata kike daman ki rabu da ita ba. Ina tunanin You don't have to be worry about abin da kike so ke ya samu, just be happy and celebrate Na'ima" Shiru tayi domin bata da gsky kuma daman dole wannan gorin yazo wata rana. Kallonsa tayi ta ce "Ina son magana da kai" Shiru ya yi mata ta ƙara cewa. "Ina magana" "Naji ai, bani da lokacin ki ne Na'ima" "Amma mene ya sa please nifa matarka ce, abin da zan faɗa yana da muhimmanci" miƙewa ya yi tare da ɗaukan system ɗin sa ya nufi cikin bedroom. "Magana zan maka akan Salman" sai a lokacin ya juya ya kalleta sosai kafin ya saki murmushi ya ce. "Ke ya shafa kuma kada ki sake zuwar mini da batu akan haka, abu ɗaya na sani duk abin da ya samu yarona sai nayi Shari'a dake" kafin tai magana wayar Abbi dake kan kujera wacce ya manta ta, ta fara ringing kafin ya Ƙarasa Mami ta ɗauki wayar. "Salima ta faɗa a fili" ganin yadda sunan Salima ke yawo akan screen ɗin wayar karɓar wayar ya yi yana answering tare da faɗin. "How are you Salima" Zuciyar Mami ta buga wata zufa na yanko mata jiki na rawa ta ce "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Salima? Wannan Shegiyar yarinyar again na shiga uku ni Na'ima" Miƙewa tayi zata bi bayansa kafin ta Ƙarasa ya yi saurin rufe ƙofarsa tare da murza mata key. Abin duniya ya isheni Mami ta rasa ta ina zata fara, tana buƙatar sanin halin da Salman ke ciki, gefe guda kuma tunanin Abra na addabar Zuciyarta a kwana biyun nan, gaba ɗaya ta rasa mafita ga kuma masifar dake shirin samunta na Salima, mene haɗin ta da mijinta? Me ya sa ta dawo garesa? Ko dai har yanzu tana bibiyarsa itace bata sani ba. "Na kashe kai na" bata da sauran wanda zata faɗawa damuwarta a yanzu, domin ko ta sha giyar wake ba zata ƙara neman shawara wajan Anuty Suwaiba ba. Ta riga ta gane hatsin ba tsaba. Yau ya kama Weekend ne cikin jerin watannin da Abra tayi a gidan Adnan a satin ƙarshen watan da zai sanya ta cika wata biyar cif a gidan aurenta. Amma duk tsayin kwanaki da kuma satittika zuwa watannin data riska babu wata rana data zame mata ranar farin ciki, tun ranar da aka kawota gidansa matsayin Amarya har zuwa Yanzu da take cika wata biyar dayin aure. A hankali ta ɗora hannunta a saman cikinta wanda ya fara girma sosai kasancewar ta mara jiki yasa cikin fitowa ya zauna das ƙasan mararta ya ƙara mata kyau na jiki. Amma tana nan yadda take a rame tai duhu sosai kamar ba ita ba. Fararen idanunta da suke a buɗe ta lumshe a karo na farko taji soyayyar abin da yake cikinta ya ratsa Zuciyarta. Musamman yanzu da take jin gilmawar abin da ke cikin nata, tabbacin yana cikin lafiya. "Banso aka samar dakai ta wannan hanyar ba, nasan ba zaka jure ganin wacce ta haifeka cikin uƙubar mahaifinka ba, amma zan tabbatar da cewa ba kayi masa kallon uba ba, zan shaida maka irin wahala da azabtarwar da mahaifinka ya yi mini, tun bayan rabuwata da Salman nake jin kamar na rabu da dukkan wani farin cikina. Amma yanzu sabuwarka cikin mahaifa ya sa naji na samu wani abokin rayuwar wanda zai maye gurbin Salman a zuciyata" hawayen da take ta ɓoyewa ne suka sakko mata cikin sauri ta goge ta ce. "why should i cry? Cry for no reason nayi Al'ƙawarin ba zan sake zubar da hawaye akan azabtarwar da Adnan ke min ba, zanyi hawaye na dalilin rashin sanin asalina da tushena" kukan da yaci ƙarfinta ne yasa ta kasa faɗin sauran maganar wanda kamar suke fitar da kansu bata shirya faɗar su ba. Mai aikin Hajiya Mama ce ta fito daga kitchen tare da kallon Abra ta ce "Hajiya ƙarama an gama lunch ɗin, na kawo maki nan?" Girgiza kai Abra tayi cikin sakin fuska bayan ta share hawayen idanunta ta ce. "Bana jin zanci abincin nan Laure, kawai ki zuba yadda zai maki kici sannu da ƙoƙari" "Ko babu yawa ya dace ace kinci sbd abin da yake cikinki ya samu kyakkyawar kulawa" Abra ta kalli mai aikin cikin tunani sai kuma ta ce "Shin abin da yake cikina zai samu illane game da rashin cin abincin nawa?" Da sauri mai aikin ta ce "Sosai, domin sai Kinci shima sai samu wanda zaici, rashin cin babbar illa ne zaki iya haifar babyn babu girma ko kuzari". Murmushi kawai Abra tayi ta ce "Ok thank you" "na kawo maki ko kaɗan ne?" Abra ta girgiza kai ta ce "ba zan iya ci ba Laure, ni bana jin wata yunwa" daga baƙin ƙofa suka ji ance "Idan kin gama aikinki jeki kawai" Laure ta juya ta kalli Adnan jiki na rawa ta gaida shi bai kula ba, da sauri ta nufi sashin da aka bata. Rufe idanu Abra tayi kamar mai bacci, a hankali Adnan yake binta da idanu yana mmkin lalacewar da take a kullum, ba ƙima, hasken ya dishe sai ƙirji kamar zai fasa riga ga kuma yadda cikin ya sake fitowa fili. Taɓe bakinsa ya yi irin ko a jikinsa ɗin nan kafin ya nufi kitchen babu jimawa ya dawo ɗauke da plate na abinci dambu ne, wanda ya sha kayan lambu da kuma zallar hatta yaji gyaɗa da zogala sai ƙamshi yake. Zama ya yi very close to her yana kame iyayen tare da faɗin "zaki iya zama da yunwa until unborn ɗina ya samu abincin, dan haka get ready zanyi feedings babyna" Ɗauke fuska tayi tare da ƙoƙarin Miƙewa zata bar wajan, amma gaba ɗaya jikinta ya saki sosai take jin ciwon jiki da wani zazzaɓi na cikin ƙashi. Hannunta ya kama yana mayar da ita zaune kafin ya ce. "Kina tacin albarkacin abin da yake cikinki, shine dalilin da yasa nake raga maki,amma ke baki ganin hakan ko? Nidai duk abin da ya sameki matsalarki ce kawai ki tabbatar jinina lafiya yake" Bata kulasa ba, ko fuskarsa bata ƙaunar gani nesa take da dukkan abin da zai sanya tai masa mgn ko yai mata. "Dole kici abincin nan Abra" a ɗan fusace ta ce "to ana dole ne? Don girman Allah dan darajar iyayenka ka rabu dani, stay away from me don Allah" ta faɗa tana runtse idanunta sbd kissing bakinta da taji ya yi a hankali. Plate ɗin abincin ya ajjiye a gefe tare da jawota jikinsa hannunsa ya ɗora akan cikinta yana lumshe idanunsa. "Kina cewa kin tsaneni, bayan so na da kike yasa idanunki ya rufe kika kasa fahimtar son da Salman yake maki, hakan na nufin duk wata ƙiyayya da zaki nuna min iya baki ne bai kai zuciya ba Angel" harara ta watsa masa ta ce. "Na soka a lokacin da nake tunanin zaka zame farin ciki, abokin rayuwa, zaka zama mai tausayi a gareni, da bani garkuwa, na soka a lokacin da nake ganin kyawawan halaye a tattare dakai. Amma wallahi wallahi Allah babu sonka a zuciyata, ban taɓa tsanar wani ba, ban taɓa jin akwai wani rai da zanji bana son ganin ko fuskarsa ba irin kai. Sp Adnan Aliyu Matawalle! Abra Khamal Khamis hate you. I hate you na tsaneka wallahi bana ƙaunar ganinka, zakai ladama, zakai dana sani ka rubuta ka Ajjiye zakai kuka da idanunka" Tana faɗin hakan ta miƙe tsaye jiki babu ƙauri ta nufi hanyar part ɗin ta. Cikin zafin nama Adnan ya sha gabanta ya ce "Ke har kin isa ki furta kalmar tsana a gareni? Wallahi ƙarya kike kina sona, kuka? Ko mugun azzalumi Ubanki mai zuciyar fir'auna bai sanya na zubar da hawaye ba, balle abin da ya haifa. Ki rubuta kema ki ajjiye a duk sanda nai kuka sbd ke a ranar wallahi zan daina duk wata mugunta da nayi miki, a lokacin zan fita daga sabgarki a lokacin zan zubar da makaman ɗaukan fansa na" Murmushi kawai tayi tana mmkin muguwar zuciya irinta Adnan a hankali tana jan numfashi ta ce. "Ta ina zan san kayi kukan? Abin zai zo maka ta hanyar da bakai tsammani ba, ka tsammaci abin da baka tsammani shi ne kawai" tana faɗin hakan tai ɗakin ta. Ya daɗe tsaye yana tunani ya kasa fahimtar komai. Har dare Abra bata fito ba, Adnan bai je inda take ba, balle yasan halin da take ciki, taci ko bata ci no one's know. A gefe guda kuma soyayyar abin da ke cikin Abra take da masa mugun kamu. Misalin 12 na dare tana kwance nannaɗe cikin duvet hannunta kuma ɗaya riƙe da azkar amma ko iya karantawa ba tai ba, ta dai riƙe kawai a wajanta ne. Tsaye ya yi a kanta cikin ko in kula ya ce "Madam nazo amsar haƙƙina ne" Shiru tai masa ganin tai shiru yasa shi faɗin "Ko ba zaki ban bane?" Idanunta ta buɗe tare da kallonsa cikin sanyin murya ta ce "Kaji nai mgn Bisimillah, ba zan taɓa hanaka ba" tana faɗin hakan ta ja bakinta tai shiru. Zama ya yi akan gadon yana kallonta sai bai lura da yadda jikinta ke rawar sanyi ba, a haka yaje gareta tare da sauke buƙatarsa da maitarsa. Nan kwance ya barta tana sauke numfashi, baƙin cikin yadda take sake masa jiki sai dai yai komai da kansa shi ke cika masa zuciya a kullum. Yana fita Abra ta ƙanƙame jikinta da shiga addu'ar neman sauƙi wajan Ubangiji. A fili kuma ta fara addu'ar yaye damuwa da ƙunci. *”لا إلهَ إلَّا أنتَ سبحانَك إنِّي كنتُ من الظالمينَ”* Daga wannan addu'ar ta koma wannan. *{اللهُمَّ رحمتَكَ أرجُو ، فلَا تكلْنِي إلى نفسِي طرْفَةَ عيْنٍ ، و أصلِحْ لِي شأنِي كلَّهُ ، لا إلهَ إلَّا أنتَ}* Haka ta dinga yi da ƙarfin da rage mata har barci ya ɗauke ta bakinta na motsawa. A hankali Meenal ke fitowa daga cikin part ɗinta zuwa Main Parlour, ganin babu kuwa yasa da sauri ta bar parlourn tai waje, jikinta na rawa ta shiga motarta gatekeeper ya buɗe mata gate tabar gidan cikin 160, na giyyar motarta. Sai da tayi nisa taja tsaki ta ce. "Haba aita takura mutum ana saka masa Idanu, duniyar nan kowa abinda yaga dama yake, amma an tirkeni kamar wata saniyyar ɗaure, daga nan sai club wallahi" number Abdul ta kira ta ce "Hy sweetheart, jiya na kwana da mafarkin madararka" shiru tai tana dry ta ce "Haba never nai maka sambatu sai dai kai, now tell me kana ina?" Jim tai ta ce "Oops hotel ɗin ranar nan? Kai kam kamar mara gsky, shikenan bani 10mnts I'll be there" kashe wayar tayi babu jimawa ta Ƙarasa kai tsaye room ɗin daya kama ta shiga. Knocking ƙofar ta fara, da sauri Abdul ya miƙe yana kallon Zee baby dake kwance a kan gadon ya ce "Hehhhh beb Meenal ta ƙaraso tashi ki ɓoye" taɓe baki tayi ta ce "Wai kai ina ruwana da wata Meenal" "No Beb, kin san bana son abin da zai dameki ke nake so kuma ke zan aura waccar ƴar wahala ce" miƙewa kawai tayi ta nufi toilet. Sai a lokacin ya buɗewa Meenal tana zuwa ta rungomesa ta ce "Me kake yi ne?" Kissing bakinta yai ya ce "Ina shirin yadda zan tarbeki mana, u knw you're special" suna tsaka da yin abin da suka saba. Zee baby ta fito tare da yi musu vedio tana sakin Murmushi duk irin ihu da sumbatun da suke yana cikin Vedion. Bayan faruwar komai ta ce "Abdul ina da ciki yaya zan?" Murmushi yai ya ce "Abin da aka saba mana" shiru tai ta ce "Na gaji da zub da ciki fa, ya kamata a nemi mafita" "ok kima Usman mgn ya fito ai auren, kin san daman matan aure sunfi daɗin harka tunda kince ba zaki auren ba" daga nan hospital suka nufa aka cire cikin. Abra na zaune a Parlour kamar daga sama taji ana faɗin "Huhuhu azaba ita daman kadunan haka take bani da labari? Wallahi kamar dai tafi Saudia nisa, wannan azababbiyar tafiya kamar za'a sai da mutum" Granny ta faɗa tana turo ƙofar. Murmushi kawai Adnan ya yi, Ammi ta ce "haka fa" a haka suka ƙarasa shiga Parlour, wayyooo Allah daɗi duk irin ciwon da Abra take ji haka ta miƙe jiki na rawa kai tsaye wajan Mami ta nufa tana zuwa ta faɗa jikinta tana sakin wani irin kuka kamar ranta zai fita. "Oh! Wannan kukan har yanzu yana nan ni Na'ima yaushe zaki girma" kuka kawai Abra take har da shassheƙa. "Ji Algunguma bafa kukan take ba sai yanzu data ganmu to kukan na menene ma ai babu kyau" Adnan dake tsaye ya ce "haka take Granny, kullum wai akaita wajanku shi ne nace bari ta haihu to" zare ido Granny tai ta ce "Ciki ne da ita? Oh na shiga uku abin babu wahala to wata nawa kuma?" Shafa kai Adnan ya yi ba tare da yace komai ba. Farin cikin da Abra tai ba zai misaltu ba, ta rasa inda zata saka kanta, Adnan komai Angel har kunya yake bawa su Ammi, Abra ko inda yake bata kallo. Sai da ya kirata tare da Kaɗa mata warning na zamantakewarsu. Da zasu tafi kuka tayi kamar ranta zai fita, a haka suka rakasu zuwa airport dake jirgi zasu shiga. Washegari ya kama Monday tana zaune a ɗaki Adnan ya shigo kallo ɗaya ya yi mata ya ce "12 jirginmu zai tashi zuwa Dubai sai ki shirya" da sauri ta kallesa ta ce "Dubai? Akan mene ko sbd ka samu damar wulaƙantani?" Kafaɗa ya ɗaga ya ce "Duk yadda kika ce, amma bana mgn biyu ki tabbatar kin shirya" yana faɗin hakan yai waje. Babu yadda ta iya bisa dole ta shirya kamar yadda ya ce 12:3 jirginsu ya tashi zuwa Dubai. *DUBAI* Dubai, da Larabci دبي‎, birni ne dake a masarautar Dubai, A ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa. Shi ne babban birnin masarautar Dubai, kuma da babban birnin tattalin arziƙin Hadaddiyar Daular Larabawa. Bisa ga ƙidayar jama'a a shekarar 2018, akwai jimillar mutane 3,137,463.An gina birnin Dubai a ƙarni na sha takwas bayan haihuwar annabi Isah. Kai tsaye wata unguwa mai suna Madinat Jumeirah. Motarsu ta nufa, cikin wani haɗaɗɗan gida mai kyau da tsari wanda ya kasance mallakin Aliyu Matawalle. Gaba ɗaya a gajiye suke musamman Abra wacce bata saba tafiya haka ba, ɗaki ya nuna mata ta kwanta shima ya nufi wani ɗakin. Bayan sallar issha tana tsaye a gaban mirror ta gama shiryawa cikin wata abaya mai kyau, Adnan da tun ɗazo yake tsaye yana kallon ta ya ce "Bani da time Malama" bayansa tabi har zuwa mota, shine da kansa yake driving dare ne amma sai ka rantse rana ce haske kamar zai illata ido sbd yawan da yayi. Wani mall suka shiga yace ta ɗauki abin da take so, yana faɗin hakan ya shige ciki. Juyawa Abra tayi a hankali ta rasa me zata ɗauka sai kawai ta nufi wani waje ta da nufin zama, kamar daga sama taga mutum a tsaye a gabanta, da sauri tai baya tana girgiza kanta mutumin data gani yasa hankalinta ta shi. Abdullah ya gyara tsaiwa tare da faɗin "You? Nasan dole zan sake ganinki" jiki na rawa ta juya zata bar wajan ya yi saurin kama hannunta yana faɗin "No please, may i have your number?" Shiru tai masa ya sunkuyar da kansa yana zaro Wayarsa tare da faɗin "Jikina yana bani daman zan sake ganinki please samin number ki" wayam babu Abra babu mai kama da ita, neman duniya babu ita a haka ya koma gida rai ɓace. Yanayin Yadda ya shiga ya sanya ƙyakkyawar matar dake zaune saman Kujera hannunta riƙe da littafi tana dubawa ɗago kanta cikin kulawa ta ce "Lafiya dai Abdullah?" Girgiza kai yai ya ce "Ummi kai na ke ciwo" da ido ta kallesa haka nan taji bata yarda ba, a nutse ta ce "Ciwon kai?" "E, Ummi maybe gajiya ne" numfashi ta sauke ta ce "Allah ya sawwaƙe, kasha magani ina son muyi magana akan Sabon Companyn da aka buɗe last year,bana gane kan komai na Companyn Abdullah na zuba biliyoyin kuɗi amma yanzu duk babu su, hankalina ya fara tashi" Abdullah ya ce "Waye manager na Companyn ma Ummi?" Girgiza kai tayi tana ɗaukan Jarida ta ce "Jeka huta, we'll talk later" "Ok Ummi" part ɗinsa ya shige Ummi ta bisa da kallo. Cike da tsoro Abra ta kwanta amma tana Mmkin gani na biyu da idanunta suka sake yiwa Abdullah waye shi? Mene yasa yake bibiyarta har haka? Da wannan tunani bacci ya ɗauke ta, cikin dare ta farka da matsanancin zazzaɓi hannunta ta miƙe da nufin riƙe kanta amma sai taji gashin kanta yana marmasuwa, da sauri ta saka hannunta duk biyu ai kam nan gaba ɗaya gashin ya shiga cirewa gefe guda na kanta tamkar wacce akai wa aski..... Littafin kuɗi ne, mai buƙata ya yi magana ta wannan number 09047871750 [10/27, 3:04 PM] Abk: Gabanta ne yayi mummunar faɗuwa, wane irin abu ne haka gashin kanta zai dinga zuba? Shiru ta yi tana tunani, a iya saninta bata taɓa abu makamancin haka ba. 'may be sauyin weather ne' wata zuciyar ta bata amsa, haka ta yi shiru tana Adduointa, har bacci ɓarawo ya saceta. Bayan sallar Asubahi ma, gado ta koma ta cigaba da bacci, tana cikin baccin taji an ɗagota daga kwanciyar da take gaba ɗaya. Buɗe ido ta yi tana tura baki, ta kalli fuskar Adnan ta ce "Meye haka? Bacci fa nake yi". "Ai na san baccin ki ke yi, ke baki san Yakamata ba ko? Kina da juna biyu amma har wannan lokacin kina bacci, ba zaki tashi ki nemi abin da zaki ci ba, baki san sai kin ci shima abin da ke cikin ki zai ci ba?". "Au haba? Ya daɗe bai ci ba, ba zan ci Abincin ba, sai dai wahala ta kashe shi na huta nima". "Aikuwa sai dai ku mutu tare, da in rasa abun cikinki gara ke in rasa ki, dama can ba ta taki nake ba, ki yi ƙoƙari mu rabu lafiya, ki haife mini yarona salin alin". "Mu rabu ka ce?" Tayi maganar tana kallon fuskarsa. "Eh mu rabu, ko da yake fa ashe ba zaki iya rayuwa babu ni ba ko?". Abra tayi wani murmushi mai ciwo ta ce "Ai ko kashin awaki muka zo duniya da kai, na tsaneka ko sunan ka bana ƙaunar ji, idan har zamu rabu ka yiwa Allah da ma'aikinsa mu rabu yanzu kan mu koma Nigeria, daga nan in wuce gidan ubana". "Gidan riƙo dai, a zatonki zan rabu da ke ne ki tafi da cikina gidan riƙo ya zama ɗan riƙo kamar yadda kika zama, no iya wuya banga wanda ya isa rabani da ke da cikin nan a jikinki ba". Abra ta ce"Wanda yayi ni yaui cikin fa?" Kallonta yayi amma bai ce komai ba, ya basar ya ce "Malama ki tashi kije ki karya". "Idan ka damu ɗanka ya ci Abinci, zaka iya zuwa ka haɗo Abincin ka kawo mini nan in ci, idan kuma ba ka matsu ba, kana iya ƙyaleni in cigaba da abin da yake gabana" Tana rufe baki ya wani irin fizgota daga kan gadon, Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Abra ji tayi tamkar an haɗa ilahirin ƙasusuwan jikinta ana ƙoƙarin kakkaryawa saboda azabar ciwon da ya ratsata tun daga kwanyarta zuwa yatsun ƙafarta. "Na shiga uku Adnan, kasheni zaka yi ne? Ka san yadda nake jin jikina kuwa?". "Ban damu da duk abin da kike ji ba, wannan ke ta shafa ba ni ba, burina ɗana ya rayu, ki lafiya ko kar kiyi matsalar ki ce, akan ina Magana kina mini gaddama, mussaman a kan abin da ya shafi cikin nan, sai na ɓata miki rai" yana gama maganar ya shiga janta, wanda jan nan da yake mata ji take tamkar yana ƙoƙarin rabata da ƙasusuwan hannunta. "Adnan Allah yana kallonka fa" ta faɗa cikin tsananin rauni. "Kar ki sake gatsa mini sunana haka kamar ke kika raɗa mini, mara tarbiyya shi ma uban riƙon naki baki samu tarbiyya a hannunsa ba kenan, da har kike iya kallon tsabar idona ki kirani da sunana". Ja tayi ta tsaya tare da riƙe ƙofa ta ce "Zan iya haƙuri idan ka zagi mahaifina, saboda ban san shi ba ban san mai ya haɗaku ba, amma ba zan juri ka zagi Abbina ba duk wani rashin mutunci da zaka yi mini ya ƙare a kaina ban da Abbi, kuma da ka auroni ai ina ɓoye sunan naka, amma na ga lamarinka babu mutunci dan haka na faɗa ADNAN ALIYU MATAWALLE, aka faɗi sunan Annabi ma balle sunan Azzalimin mutum irinka" rigarta ya sa ya shaƙo wuyanta yana huci, idanun Abra suka yo waje tana wani irin kakari, ya ƙarasa janyota cikin falon, ya jefata kan kujera. Ya ɗauko Abinci ya dinga ɗura mata tana kuka tana kakarin amai, amma babu tausayi ko imani a zuciyar Adnan. Zaune take a kan wasu irin katafaren kujeru, tana zaune hannunta riƙe da waya, tana jujjuya wayar fuskarta ɗauke da damuwa, a hankali ta fara daddanna wayar, sannan ta kara a kunnenta, sai da wayar ta kusa katsewa sannan aka ɗauka, sallama tayi tare da yin ajiyar zuciya. Daga can ɓangaren cikin wayar aka amsa mata. "Kana ina ne Yanzu?". "Ina nan lafiya, akwai damuwa ne?". "Ina son in ji Yaushe zaka zo ne, saboda akwai damuwa, ina son mu tattauna wata magana da kai" "Wace irin damuwa ce haka wadda har kike son in zo?". Ta sake sauke ajiyar zuciya, fuskarta na bayyanar da tsantsar damuwa ta ce "Nifa gaba ɗaya na kasa gane kan kasuwancin nan, shekara da shekaru abu yaƙi gaba yaƙi baya, akwai buƙatar mu dakatar da deal ɗin nan, zan tsayar da duk wasu harkokina na nan ƙasar, in sako jami'an tsaro da manyan accontants a gudanar da bincike, a gano a ina matsalar take" Daga cikin wayar mutumin ya ce "Haba Khair, kamar ba musulma ba, baki yadda da ƙaddara ba? Ki bi komai a hankali mana, idan kika dakatar da harkar kasuwanci shikenan a daina juya kuɗaɗen su lalace a haka? Bai kamata a dakatar da kasuwanci ba, a cigaba da harkokin idan ya so sai ayi binciken zuwa ƙarshen shekara idan Allah ya kaimu". "Na gaji ne, na gaji da irin yadda abubuwa suke gidana a harkokina, akwai wani abu wanda ban sani ba, da nake buƙatar gano shi a nan kusa". "Kiyi haƙuri ki bi komai a hankali, ki kwantar da hankalinki komai zai tafi daidai insha Allah" "Shikenan, amma yakamata ko mai kake yi ka zo, ka san ka daɗe dai baka zo ba" "Haka ne, zan zo insha Allah" "Ok sai an jima" ta ajiye wayar jiki a sanyaye tana tunani. Sallamar Abdallah ce ta katseta daga dogon tunanin da take yi. Ta amsa masa ya ƙaraso ya zauna, a ɗaya daga cikin kujerun falon. Ya dubeta ya ce "Lafiya kuwa Ummi?" Ummi ta ɗan girgiza kai ta ce "Abdullah, Ina cikin damuwa a kan harkar kasuwanci na, gaba ɗaya na kasa gane kan harkar nan, nayi waya da shi, ya ce mini yana nan zuwa, amma abin yana damuna". Abdallah ya ce "Kiyi haƙuri tin da yace zai zo da kansa, ki ɗan ƙara haƙuri". "Shikenan, bari ya zo ɗin in ji shawaa da zai yanke, amma zan gaya masa dole a bincika yadda al'amuran nan suke gudana". Abdallah ya ce "Hakane, Allah ya yi mana jagora". Ta amsa da "Ameen" Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, kusan satin su Abra biyu a Dubai, al'amarin Adnan babu sassauci, dan ko zata ci Abinci tana amai sai ta ci, ko tana so ko ba ta so. Kuma bai fasa zuwar mata da buƙatarsa ta Aure ba, duk da yadda yanayin jikinta yake. Abra ita kaɗai ta san irin wahalar da take sha a kan cikin nan, yana tsufa tana cigaba da shan baƙar wahala, wani irin zazzaɓi take wanda ba ta taɓa tunanin akwai irinsa ba, taji kamar ana sassara ƙasusuwanta, ga wani irin azabar raɗaɗi da take ji a ƙasan fatarta abin ba ya misaltuwa. Ta ƙara wata uwar rama ga duhu tayi sosai, ga gashi yana ta zubewa ta rasa abin da yake mata daɗi, gaba ɗaya ta sake zama wata so silent.   Satinsu biyu, suka baro Dubai sai dai babban abin da ya yiwa Abra daɗi da bata taɓa zato ba shi ne yadda suka sauka a Kano, wanda rabonta da Kano tun da aka ɗaura mata Aure aka kaita gidan Adnan.    Taji daɗin ganin Mami, sai dai Mamin ta tsorata da ganin yadda Abra ta koma, amma sai tayi zaton kawai laulayi ne ya mayar da ita haka, ga cikin ya fito Sosai kai kace da ta durƙusa za ta haife shi. Bayan Adnan ya kaita gida, a Hotel shi yaje ya sauka, ita kuma ya barta a nan gidan. Ganin gidan ta din ga yi duk ya sauya mata, ta dinga tuna irin rayuwar da tayi a gidan, duk da irin cuzguna mata da Hajiya Na'ima ta din ga yi, amma rayuwar gidan ta fi mata daɗi a kan wadda take yi a yanzu. Sai dai tana tuna cewa ba gidan mahaifinta bane, ita ɗin Tsintacciya ce, sai jikinta ya ƙara yin sanyi, amma duk da haka rayuwarta da Faris ta faɗo mata, rayuwa mai cike da ƙauna da soyayya. Jiki a sanyaye ta ce "Mami, wai kuna waya da Faris kuwa? Nifa bani da lambarsa duk ina cikin damuwa". "Wallahi Abra duk lambobinsa ba sa shiga, ina ta lallaɓa Abbinku ya je ya dubo mini shi". "Garin yaya lambobinsa ba sa shiga? Ni tun da yaje gidana ban samu na karɓi lambarsa ba". Cikin mamaki Mami ta ce "What? Me kike nufi yaje gidanki fa ki ka ce?". "Eh mana Mami, bai gaya miki ya zo ba?". Shiri mami tayi sannan tace "Yaushe ya je gidan naki?". "Almost 5 Months ago, wai be zo nan ba?" Mami ta ce "No ya zo, ban san yaje gidanki ba ne" da haka ta kawar da wannan hirar. Abra kuwa satar jiki tayi, ta tafi ɗakin Salman, komai yana nan yadda yake, gani take tamkar zata ganshi kamar yadda ta saba, ta kalli katafaren hotonsa da yake ɗakin da wanda suka yi su biyu, a saɓule ta zauna a kan gadonsa, ta fashe da kuka "Please Faris come back to me, i need you my caring brother, am missing you, kalli halin da Yaya ta shiga, mai yasa kayi nisa da Angel ɗin ka, ma one and only caring brother" ta ƙarasa Maganar cikin kuka mai tsuma zuciya. A hankali ta tashi zaune, ta shiga Gmail ɗin ta, ta fara rubutawa Salman saƙo mai cike da tsantsar nuna kewa, mai matuƙar ratsa rai da girgiza zukata, tana rubutawa tana zubar da hawaye, ta kammala ta ajiye wayar tare da lumshe idanunta. Meenal ce zaune a kan makeken gadonta, tana kiran layin Usman, tun safe take kiran wayarsa amm yaƙi ɗagawa, ba ta haƙura ba ta cigaba da nacin kira, sai da babu zato ba tsammani taji ya ɗaga bai ko yi mata Sallama ba ya fara faɗa "Wai me kike nema a gurina ne, tun safe kin hanani sukuni kin addabeni da kira meye haka?". "Haba Usy, ai ka ɗaga kaji dalilin kiran ko?". "Ba zan ɗaga ba idan na ɗaga me zan miki?". Cikin shagwaɓa ta ce "Please calm down baby, dan Allah ka fuskance ni". 'malama ki faɗi abin da zaki faɗa ina da ayuukan yi". "Amma ai naga yanzu ba lokacin aiki bane". "Zaki faɗa ko sai na kashe wayata?" Meenal ta marairaice ta ce "Yaushe zaka zo, sai mu yi magana". "Haba Meenal, ai ni da gidanku har abada, ko har kin manta wulaƙancin da ki ka yi mini?" "Dan Allah baby ka daina tunawa, sharrin shaiɗan ne, Please come to me haba My usy". Usman ya ce "Ke dakata, ba wata yaudara ko kalaman ƙarya da zaki yaudareni da su in amince da ke". Kawai ta fashe da kuka "Allah ba kalaman yaudara bane, dan Allah baby ka zo, Wallahi kai nake so". Usman ya ce "Eh saboda wancan ya gudu ko?" "Wallahi be gudu ba, kawai dai zuciyata kai take so". "Kin manta da rashin ɗaga wayata, da wulaƙanci da ki ka dinga yi mini a kan saurayinki ko?". "Dan Allah ka daina tunawa, kuskure ne ba zan sake ba". "Shikenan zan yi shawara". "A'a dan Allah ba sai kayi ba, Please Baby me, wlh Ina sonka Sosai na yi missing ɗin ka". 'hmm Allah yasa da gaske ki ke". "Wallahi da gaske nake". "Shikenan zan duba". "Yawwa Baby ina nan ina jiranka" bayan sun yi sallama tayi ajiyar zuciya ta kalli wayar ta ce "Gara tun wuri in yiwa kai na ƙiyamul laili, in lalaɓo shi ya dawo". Jin Abra ta zo,  ya sanya su Ammi suka zo, suka cika gidan wanda hakan ba ƙaramin daɗi ya yiwa Abra ba, Mutanen da ba ta da wata alaƙa da su ta jini, amma suna nuna mata soyayya haka, har hawaye ta dinga yi wanda basu san dalili ba, suka din ga yi mata nasiha a zatonsu duk kewarsu ce ta sanya ta haka. Sai da duk sun lura da irin ramar da tayi, ba wanda yayi Magana sai granny, da ta dinga bin ƙwaƙƙwafi a kan lallai sai ta ji mai ya samu Abra haka dan da alama ba iya laulayi ke damunta ba, amma Abran ta ƙi faɗa. Kwanan Abra biyu Adnan ya zo ya ce tafiya za suyi, Abra tamkar ta ɗora hannu a ka tayi ihu, gashi tun da ta zo Abbi baya gari basu haɗu ba, ta shiga cikin fargabar komawa cikin uƙubar Adnan, amma ta koma duba abinda ka iya faruwa idan da ta sanar da halin da take ciki, haka nan ba yadda ta iya, ta bishi suka koma Kaduna. Faris na zaune a aji ana mus lectures, sai dai ya ji bugun zuciyarsa na matuƙar ƙaruwa, ya rasa abin da yake masa daɗi, kuma ya rasa dalilin faruwar hakan, yayi ta maimaita "Hasbunallah wa ni'imal wakil" hakan ya sanya ya ɗan samu sassauci. Malamin da ke musu lectures na Anatomy yace su yi connecting Wifi a system ɗin su, zai tura musu wani abu. Salman yana Connecting, yaga messages na shigowa ta Gmail ɗinsa, dan rabonsa da amfani da daya har ya manta. Ana tsaka da lectures, amma hankalinsa na kan saƙonnin, ya fita ya tafi Gmail ɗin sa, ya ci karo da saƙon Abra. Cikin hanzari ya buɗe ya fara karantawa. Subhanallah duk da yadda sanyin A.c ke Ratsa ko ina a ajin, amma wani irin gumi ne ya shiga karyo masa, ya kasa gane kan in da saƙon nata ya dosa gaba ɗaya, take jikinsa ya ɗau rawa ya kasa mayar da hankali a kan karatun. Har aka kammala bai fuskanci komai ba, haka ya koma masaukinsa, ya karanta saƙon nan ya fi sau talatin yana sake jujjuya saƙon a zuciyarsa. Tuni zuciyarsa ta fara raya masa ya bar abin da yake, ya shirya ya tafi Nigeria ya ga Abra. "No she's married now" ya faɗa da ƙarfi yana rintse idanunsa. So yake ya cire Abra daga ransa, ya manta da shafin soyayyarta, dan haka dole ya nesanta kansa da duk wani abu da ya shafe ta. Kai tsaye ya fara ƙoƙarin goge message ɗin da ta turo masa, amma hannunsa ya hau rawa, ga wasu zafafan hawaye da suka fara sauka a fuskar sa. Copying ɗin message ɗin yayi, daga nan ya goge shi gaba ɗaya ya dangwarar da system ɗin ya zauna yana kuka. Tafiyar Abra da kwanaki uku Abbi ya dawo gari, sai dai haryanzu tsawon wannan lokaci ya ƙi sakin jiki da Mami su koma kamar da. Ta same shi a part ɗinsa, ta kai masa Abinci, bai ce mata uffan ba ya ci Abincinsa ya cigaba da sabgar gabansa. Ta ɗan gyara zama ta ce "Amm, Man Abra ta zo ita da Adnan kwananta biyu sannan suka tafi". "Good, Allah bai yi zamu haɗu ba, na je gidan nata da kaina in dubata". "Hmm, wai ashe Salman ya je gidanta bamu sani ba?". Ɗan juyowa Abbi yayi ya kalli Mami ya tsuke fuska ya ce "A kan me zai je mata gida, ko bai san matar Aure ba ce yanzu, salon yaje ya janyo mata matsala a gidan Aurenta?" "Ai shiyasa na ke son a yiwa tufkar hanci, har ya iya zuwa Nigeria yaje gidanta amma mu bamu ganshi ba, Akwai matsala, akwai buƙatar kaje can ƙasar da kanka". "Ban gaya miki kar ki sake yi mini zancen inje nemo miki ɗanki ba? Ba in da zani". "Dan Allah kayi haƙuri ba dan halina ba, kar in rasa ɗana kuskure ne na riga na yi shi, dan girman Allah Major ka yi haƙuri". Miƙewa yayi ya ce "Sai kuma ki yi". Da sauri ta zube a kan ƙafafuwanta ta riƙe ƙafarsa tana kuka "Don Allah Maajor kar ka yi mini haka, dan Allah ka yi mini afuwa". Kuka take sosai kamar ƙaramar yarinya wanda hakan ya sanya tausayinta ya kama shi. Hannunsa ya sanya ya ɗagota tsaye ya ce "ki daina mini kuka, zan ga abin da zan yi a kai" Rungume shi ta yi tana kuka ta ce "Thank you very much dear". Abin duniya ya sanya Abra a gaba, dan yanzu idan jikinta yayi ƙaiƙayi ta sosa sai wani irin dabbare dabbare ya fito a kan fatarta ga wasu irin ƙananan ƙuraje da ke fito mata har cikin kanta, ta yanke shawarar idan lokacin komawarta awo yayi, za tayi musu bayani su bata magani. Haka nan tana kwance ta ji ba abinda take buƙata sai kasancewa a jikin Adnan. Miƙewa tayi ta fito falo, ta tarar da Adnan yana zaune yana aiki a kan system ɗin sa, takawa tayi a hankali ta ƙarasa in da yake ta zauna, ba tace masa komai ba, shima bece mata ba, a hankali ta zame ta kwanta a jikinsa tana sauke numfashi, tana cigaba da jin tamkar ana kakkarya ƙasusuwan jikinta. Ture system ɗin yayi ya janyota jikinsa, sai da a wannan karon yayi mamakin samun haɗin kanta, sainda ya bari tayi reaching highest peak, Sannan ya tureta da ga jikinsa, tare da faɗin "Jarababbiya kawai" bin sa ta yi da ido galala tana kallon ikon Allah. Ya miƙe ya bar mata falon baki ɗaya. Haushin kanta ne ya kamata, da ba ta zo in da yake ba da duk haka bata faru ba, amma ya za tayi ita kaɗai ta san mai take ji a jikinta, kasancewarta a jikinsa skin to skin yana sanyawa ta ji sauƙin zafin da take ji a cikin jikinta. Haka ta lallaɓa ta koma ɗakinta, sai dai ba kunya Adnan ya dawo cikin dare yayi abin da Allah ya nufe shi da yi. Lokacin da yake ƙoƙarin tashi, ta rirriƙe shi tana kuka ta ce "Dan Allah Sp ka tsaya tare da ni, ko bacci in samu in yi, ɗumin jikinka kawai nake buƙata, dan Allah". "Kin daɗe ba ki ji ɗumin jikin nawa ba? Dalla cikani in je in kwanta, gobe in Allah ya kaimu ƙarfe huɗu zan  in tafi Enugu". "Sp a haka zaka tafi ka bar ni? Dan Allah kar ka tafi ka barni a wannan halin". "Hmm kalleki da Allah, ƙil da da ɗigon imani a zuciyar mahaifinki, da kin bani tausayi, amma da na tuno mahaifinki sam sai in kasa jin taisayinki, cikani dalla in kin ha dama ki tashi ki gyara jikinki, ko ki ta zama da najasa ƙazama" haka Abra ta bi shi da ido, tana zubar da hawaye. Washegari da safe da ƙyar ta iya tashi, ji take tamkar iska zata ɗagata ta watsar, salla kawai ta iya yi ta koma ta kwanta ko Abinci ba ta ci ba. Tana nan kwance salla kawai ke tashinta, Adnan ya shigo ɗakinta, ya tarar da ita a cikin bargo. Haushi ne ya kama shi, gani yake har da langwai Abra ta ke yi. "Wai ke malama meye haka? Sai kace a kan ki aka fara ciki? Dalla tashi". Shiru ta yi masa, ita da da wannan masifar da yake mata, dama rungumeta zai yi taji ɗumin jikinsa. Yaye bargon yayi, ya janyota "Ke kullum cikin kwanciya kamar ruwa, ki dinga ƙwarara jikinki malama". "Ba zan iya ba ne, ni kaɗai na san me nake ji, dan Allah ka yi mini Alfarma, ko mintuna uku ne in yi a jikinka". Gefen fuskar Abra ya kalla, ya ga wasu ƙananan ƙuraje sun mata dabbare-dabbare a gefen fuskarta ba kyan gani, ya kalli hannunta in da ya riƙe, ya ga har hannunta duk sun feso. Da hanzari ya cikata ya ja da baya, saboda yadda tsigar jikinsa ta tashi. "Meye wannan a jikinki haka?" Ta kalli jikinta ta ce 'Nima ban sani ba". "A haka kike cewa in rungume ki? Allah ya sa ba da wannan abun a jikinki na haɗa shimfiɗa da ke ba jiya, wannan ai ƙurajen ƙazanta ne, wannan ai ƙarzuwa ce. Kinga ni ga jakata can a Falo na shirya, sai jibi zan dawo an turani aiki" "Dan Allah kar ka tafi ka bar ni a haka, dan Allah Adnan". "Saboda me na zan tafi ba, in zauna in cigaba da kallon wannan ƙazantar". "Adnan ka yaudareni da daɗaɗan kalamanka na amince na aureka, Ruhin Adnan Alyu Matawalle, Zan rayu da ke in kula da ke, zan kasance mai tausayi a gareki, da duk irin wannan alƙawarurrukan, amma ka kasa cika ko guda. Shikenan ka je Allah ya yafe maka, Ya kai ka in da zaka lafiya" ta juya tana ƙoƙarin kwanciya ya ga yadda tsakiyar kanta duk babu, ya zube. Ga wannan ƙurajen duk sun yi tambari a gadon bayanta. Ya sa kai ya fice ya bar gidan, yana cigaba da jin yadda tsigar jikinsa ke tashi. Kwana biyu ya zaman banɗaki ma da ƙyar take iya zuwa, dama Abinci ba'a magana ba iya ci take ba, ta yanke shawarar zuwa Asibiti, dan ba zata iya jure cigaba da zama a haka har ranar awonta ta zagayo ba, dan da wani irin ciwon baya da ƙafafuwa ta tashi. Da ƙyar tana haki ta fito harabar gidan, da yake tun lokacin da ta gudu gidan su Adnan, ya kawo maigadi ya ajiye a gate. Mai gadin na ganin Abra na bin bango, ya taso da gudu yana faɗin "hajiya lafiya?" Kan tayi Magana, taga gari yayi mata duhu, yana jujjuya mata, ta yanke jiki ta faɗi a ƙasa. Mai gadin ya fita da gudu, ya ƙwanƙwasawa maƙwabtansu ƙofa, da gudu suka dawo tare da maigidan, suka tarar da Abra a kwance a ƙasa, maƙwabcin ya kira matarsa suka sanya Abra a mota zuwa Asibiti. GY BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY Ba free bane na kuɗi ne ₦300 kacal ku tuntuɓe mu a kan lambar wayoyin mu 08081012143 09047871750 [10/28, 5:00 PM] Abk: Cikin gaggawa suka shiga da Abra Asibitin. Bulama baya nan, doctor Aminu ne a bakin aiki, cikin gaggawa suka biya kuɗin ganin likitan, kasancewar maƙocin su Abran yana da file a Asibitin. Doctor Aminu ne yaje kan Abra, ya tambayi ina document ɗin ta na awo? Maƙwabcin ya ce "Wallahi ban sani ba, matar maƙwabcina ce". Doctor Aminu ya ce "Babu halin in taɓa ta ban san history ɗin ta ba, dan haka a nemo mijinta". Aka kira lambar Adnan ta ƙi shiga, gashi ba wanda ya ke da lambar wani na Abra. Maƙwabcin ya ce "A taimaka a duba ta, a bata taimakon gaggawa mana". Doctor ya ce "Bani da ikon taɓa ta banga documents ɗinta na awo ba, kuma kaga tases na ANC a Asibitin nan dubu hamsin ne, abu ɗaya zan iya yi muku, kuju ku yi scaning yanzu a kawo, kan in tashi idan na tashi sai dai ku jira likitan yamma. Haka suka kwashi Abra suka tafi sacaning, sai dan kan su dawo liktan ya tafi, sai dai su jira Bulma, wanda sai biyar zai shigo. Gaba daya kuma an rasa lambobin Adnan, maƙwabciyar ta koma gidan Shi ta duba ko zata ga wayar Abra, amma ba ta gani ba. A haka Abra ta farfaɗo, tana kiran sunan Allah sai juyi take Saboda azabar ciwon da take ji. Ba yadda ba suyi da Abra tayi magana ba, amm ta kasa salati kawai take yi, tana ambaton Allah. Sai biyar da kwata sannan Bulama ya shigo, ko da ya shigo Nurse ɗin da take duty taje ta yi masa bayani, bai je kan Abra ba sai cewa ya yi sai sun biya wannan dubu hamsin ɗin ta awo, sannan zai dubata kuma wannan scaning ya nuna akwai matsala dole ayi aiki, a cire cikin da gaggawa kar a rasa jaririyar, saboda ruwan da take ciki yayi kaɗan, dan haka sai an biya wannan dubu hamsin na awo da ba ta yi a Asibitin ba, sanan a biya dubu ɗari biyu da hamsin wanda za a yi mata aiki. Maƙwbcin ya ce Gaskiya ba zai iya biyan wannan kuɗin haka bai sai dai aita jarraba lambar mijinta har a samu. Matar maƙocin ta je ta samu Nurses ta ce "dan Allah ko wata allurar ce ku yi mata kan mijinta ya zo, Wallahi ko nawa ne zai biya" Ɗayar ta ce "Wallahi bamu da ikon yin hakan, tun da baku biya kuɗi ba, amma bari inje in tambayi likitan. Nurse ɗin ta koma gurin Bulama a fusace ya ce "Ke kar ki isheni, ba a biya kuɗ ba ya zan yi? Kuje ku yi mata wata analgesic ɗin ta samu releif. Nurse ɗin ta fito tana tunain wace allura ce analgesic, tun da ita food hygiene ta karanta ba Nurse ba ce. Gashi ita ganinta abun kunya ne ta tambayi abokan aikinta, da haka ta jeta ɗauko wata allura  da take kyautata zaton ita ce Analgesic. Ta huda Abra ya kai sau bakwai sannan ta samu jijiyarta, ashe ba a allurar a jijiya, bayan ta gama yin allurar ta tafi mintuna talatin jini ya ɓallewa Abra. Innalillahi wa Innalillahi raji'un, a guje matar da suka kawo Abra ta je ta samu Nurses ɗin ta gaya musu, suka zo suka duba suka tafi suka gayawa Bulama, amma ya ce 'ba Abin da zai iya a kai sai an biya kuɗin aiki. Adnan kuwan sai bayan magariba ya dawo daga tafiyar da ya yi, ya tarar gida ba kowa har maigadi, ransa ya ɓaci, ya duba ɗakin Abra amma bata nan, dama yana yi yan tsantsame jikinsa dan baya son ya ganta da wannan abun na jikinta. Ya duba kaf gidan bai ganta ba, a fusace ya fito harabar gidan, zai ɗau mota ya fita sai ga mai gadi ya dawo. "Daga ina kake? Dama na ɗauke ka ne dan ka dinga tafiya yawonka kana bar mini gida a buɗe?" "Yi haƙuri Yallaɓai, matar gidan ce ba lafiya an nemeka a waya ba a samu ba, an kaita Asibiti" "Asibiti, kamar yaya waye ya kai ta?". "Ni da maƙota ne, ana ta neman layinka ance aiki za ayi mata, sun ƙi taɓata saboda ba a biya kuɗn aikin ba". A gigice Adnan ya ce "Wane Asibitin aka kai ta?" Dan jim mai gadin ya yi alamun son tuno sunan asibitin. "I'm asking you Malam, Ina kuka kai mini matata? Ka tsaya kana kallo na kamar yau ka fara gani na?" Adnan ya faɗa cikin tsawa. Cikin girmamawa mai gadin ya ce. "Yallaɓai sunan asibitin nake tunowa, na manta amma kamar ko BULAMA mene ne?" "What! Me ka ce?" Adnan ya tambaya cikin ƙaraji tamkar zai fasa gidan da muryarsa. "Asibitin Bulama." Mai gadin ya ba shi amsa. Wani ɗan ƙaramin ihu Adnan ya saki ya nufi Motarsa cikin sauri-sauri gudu-gudu kamar sabon kamu, mara masa baya mai gadin ya yi zuciyarsa cike da mamakinsa gami da tausayinsa. Duk da uban gudun da yake tsalawa a kan titi tamkar don shi kaɗai aka yi amma gani yake kamar ba ya tafiya baya ma yake komawa. Mai gadi kuwa addu'a kawai yake yi a cikin zuciyarsa Allah ya kai su lafiya. Suna shiga asibitin ya yi parking a tsakiyar hanya ya fito ko kashe Motar bai yi ba. Cikin sauri mai gadi ya bi bayansa. Alhaji Nura maƙocin su Abra yana ganin Adnan ya gane shi, kamar yadda shi ma Adnan din ya gane shi, duk da ba sa wata mu'amala amma suna haɗuwa time to time su gaisa. Cikin jin daɗi da farinciki ya miƙe yana faɗin. "Ranka ya daɗe sannu da zuwa, tun ɗazu....." "Uban wa ya kawo mini mata wannan tsinannen asibitin?" Ya faɗa cikin cika da batsewa. "Subhanallahi! Me ya yi zafi ranka ya daɗe? Ni na ce mu kawo ta nan saboda muna da file, gudun kar mu je wani asibitin mu sha wuya, ganin mawuyacin halin da mai ɗakin naka take ciki?" Cewar Alhaji Nura cikin tausasa harshe. Cikin tsantsar tashin hankali da damuwa ya ce. "Where is she? Ina Matata? Me ya same ta?" Ɗakin da take matar Alhaji Nura ta nuna masa, bai ce komai ya nufi ɗakin. "Ikon Allah, baban Rahama lafiyar mutumin nan kuwa ƙalau? Daga taimako zai zo yana mana masifa? Mene aibun asibitin nan? Kuma ko tsayawa mu yi masa bayani bai yi ba ya yi gaba." "Ki yi masa uzuri, kin san mu maza muna da rauni a kan ku matanmu, idan kika lura ba ya hayyacinsa, a birkice yake." Tsaki Maman Rahama ta yi ta ce. "Ya san da hakan ya tafi ya bar ta ita kaɗai a cikin gida, kuma ya san ba lafiya ce da ita ba, ni wallahi duk haushinsa ma ya cika mini zuciya." Murmushi kawai Baban Rahama ya yi bai ce komai ba. Nurse ɗin da ta yi wa Abra allura tana bakin ɗakin da take tsaye cikin tashin hankali, don ta rasa ya za ta yi ta tsayar da jinin da take zubarwa, kuma tana tsoron ta faɗa wa wani gudun kar ta fuskanci hukunci. A haka Adnan ya ƙaraso kamar wani mayunwacin zaki yana huci, bai bi ta kanta ba ya yaye labulen ɗakin zai shiga. Saurin shan gabansa Nurse ɗin ta yi tare da faɗin. "Malam ya haka? Daga ina? Who are you?" Mugun kallon da ya watsa mata ya sa ta yin baya ba shiri ta ba shi hanya ya wuce, zuciyarta cike da matsanancin tsoro, don ba ƙaramin firgita ta yi ba da jajayen idon Adnan. "Abra! Abra! Abra!" Shi ne abin da Adnan ya faɗa cikin matsanancin tashin hankali, lokacin da ya yi tozali da ita kwance cikin jini babu alamar numfashi a tattare da ita. A ɗimauce ya cicciɓe ta ya yi waje da ita, har ya yi gaba ya juyo ya dubi Nurse ɗin da jikinta ke ɓari ya ce. "Wallahi wallahi idan har na rasa matata sai na yi da Shari'a da ko ma wanne shege ne ya yi sanadin mutuwar ta." Da kallo kawai Nurse ɗin ta bi shi, cikin zuciyarta tana sakin ajiyar zuciya. Ganin yanda Adnan ya dauko Abra jini na zuba a jikinta ya sa su Maman Rahama bin bayansa hankali a tashe, suna ƙoƙarin fita daga reception Doctor Bulama ya sakko daga sama. Wani irin kallo ya bi bayansu da shi, kafin ya taɓe baki ya dubi wata Nurse cikin yamutsa fuska ya ce. "Murja ku saka a gyara gurin nan yanzu-yanzu, ko wanne mara hankalin ne ya ɗauki patient jini na zuba daga jikinta ya ɓata mana wuri oho? Sometimes wasu mutanen they behave like animals." Ya ƙarashe maganar tare da jan tsaki. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Waye yake zubar da wannan jinin haka?" Nurse Jamila da ta fito daga wani ɗaki ta faɗi haka cikin bin wajen da kallo." "To uwar kwakwazo, sai ki bi su ki tambaya." Bulama ya faɗi haka tare da yin gaba. Cikin damuwa Jamila ta ce. "Hasbunallu'wa'ni'imal'wakil, ba dai fita aka yi da wanda ya zubar da jinin a haka ba, ba tare da an yi masa wani taimako ba? Idan jinin nasa ya ƙare kuma fa kafin su je wani asibitin? Wannan wacce irin rayuwa ce? Ba na raba ɗayan biyu kuma don ba su biya kuɗi ba ne." "To za a yi musu abu kyauta ne, ke fa wani lokacin kina da matsala." "Haba sister Murja, amma ko taimakon tsayar da jinin aka ba su ai an yi wani abu, don ba ɗan'uwanki ba ne ko ke ce shi ya sa." Taɓe baki Murja ta yi ta ce. "Sai ki faɗa wa mai asibitin ai." Daga haka ta yi gaba ta bar ta a gurin. Girgiza kai Jamila ta yi tare da barin gurin ita ma, zuciyarta babu daɗi. Wani Babban Private Hospital Adnan ya kai Abra, wanda anan take awo. Suna zuwa aka karɓe ta cikin sauri aka yi emergency ward da ita. Bin bayansu Adnan ya yi, amma wani babban likita ya hana shi shiga ɗakin da aka kai ta. Ba don ya so ba ya tsaya a bakin ƙofar ɗakin, amma yanda yake jin zuciyarsa tamkar ya kutsa kai ya shiga. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, Allah ka tashi ƙafaɗun matata, Allah ka ba ta lafiya, Allah na roƙe ka kar ka ɗauki ranta a yanzu, Allah ka ba ta lafiya ta koma gidana da ƙafafunta in nuna mata tsantsar soyayyar da nake mata, in nemi yafiyarta a kan muzgunawar da na yi mata, Allah na tuba Allah." A fili yake maganar cikin tsantsar damuwa da nadama, wasu hawaye masu ɗumi na zuba daga idonsa. Shi kaɗai ya san abin da yake ji a cikin ransa na halin ganin halin da Abra take ciki. "Sai haƙuri Sp, mu za mu koma gida Allah ya tashi ƙafaɗunta ya ba ta lafiya." Ko kallon Alhaji Nura Adnan bai yi ba, saboda gani yake duk abin da ya faru shi ya ja, sanadiyyar kai Abra matsiyacin asibitin Bulama. Jiki a sanyaye Alhaji Nura ya juya suka tafi. Duk yadda mutum yake tunanin tashin hankali Adnan yana cikin wanda ya fi shi, bai taɓa tunanin abun zai kasance masa haka ba, kuka sosai yake yi tare da surutai tamkar wani zautacce, duk wanda ya zo wucewa sai ya kalle shi, don ba shi da maraba da mahaukaci, ga jini duk ya ɓata masa kaya amma ko ajikinsa. Likitoci kusan biyar ne suka rufu a kan Abra, sun yi nasarar tsayar da jinin da take zubarwa tare da saka mata oxegen don taimaka mata gurin yin numfashi, bayan sun yi mata allurar bacci suka fito suna share zufa. A haukace Adnan ya yi kansu yana faɗin. "Doctor ya jikin nata? Ta farfaɗo? Tana numfashi? Ba ta mutu ba?" Numfashi likitan da ya kasance babba a cikinsu ya ja ya ce. "Mu je office na maka bayani." "Office ɗin me? Ka faɗa mini halin da matata take ciki a nan, ba zan iya ɗaga ƙafata ba, ba tare da na san a halin da take ciki ba." Ya yi maganar cikin tsawa. "Ranka ya daɗe ka yi haƙuri dai mu je, and ka kwantar da hankalinka mun yi nasarar tsayar da jinin da take zubarwa." Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi tare da faɗin. "Is she alive?" "Yes." "Alhamdulillah." Adnan ya faɗa tare da tsugunnawa cikin sauri ya yi sujjada ga Ubangiji. Girgiza kai likitan ya yi cikin tausayawa sannan ya yi gaba, maimakon Adnan ya bi bayansa sai ya shige ɗakin da Abra take. Sai da doctor ya shiga office ɗinsa sannan ya farga Adnan bai biyo shi ba, ko tantanma ba ya yi gurin Abra ya tafi. Yana da numbern Abban Adnan saboda asibitin suke zuwa kuma already ya san shi, hakan ya sa ya ɗakko wayarsa ya kira shi ya sanar masa halin da ake ciki, domin su zo ya yi musu bayanin abin da yake damun Abra, don yanayin halin firgicin da Adnan yake cikin bai zama lallai ma ya fuskanci abin da yake nufi ba, sai dai ya ƙara hargitsewa. Cikin rawar jiki da bugawar zuciya Adnan ya ƙarasa gaban gadon da Abra take kwance ya tsugunna tare da kamo hannunta mara drip ya riƙe gam tare da fashewa da kuka. Cikin tsantsar nadama da ƙaunar ta ya ce. "Na yi kuskuren ɗaukar fansar abin da mahaifinki ya yi mini a kanki, don't leave me please, kar ki mutu ki bar ni Abra, wallahi ke ce rayuwata, duk abubuwan da na miki na yi ne cikin fushi gami da radad'in abin da mahaifinki ya mini, but I love You since the first day I saw you. Ina son ki Abra, don Allah kar ki tafi ki bar ni, Please my love, my life, my everything, na yi nadamar duk abubuwan da na yi miki dan Allah Abra ki tashi ki kalleni, i regret what ever I deed to you, ba zan iya jure ganinki a wannan yanayin ba, dan Allah ki tashi." Ya ƙarashe maganar tare da manna hannunta a ƙirjinsa ya ɗora kansa a kai yana zubar da hawaye. Tare Abba suka zo da Hajiya Mama, direct office ɗin likitan da ya kira su suka je. Bayan sun gaisa ya dube su tare da gyara glass ɗin fuskarsa ya ce. "Adnan ya kawo mana matarsa cikin wani irin mawuyacin hali, ba don Ubangiji ya yi da sauran kwananta a gaba ba da tuni ta riga mu gidan gaskiya." A rud'e Hajiya Mama ta ce. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, me ya same ta har haka Doctor?" "Mun yi mata scanning mun gano wani ruwa ne ya kwanta a cikinta, wanda ake buƙatar a yi mata aiki cikin gaggawa a fito da abin da ke cikinta gudun kar a rasa ta ita da shi, sannan kuma bincikenmu ya nuna mana sun kai ta wani asibitin kafin su zo nan, an yi mata wata allura ba bisa ƙa'ida ba, wadda ta haifar mata da bleeding. Mun ɗibi jikinta don yi mata teses, a nan muka gano tana ɗauke da Blood Cancer stage two." "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, doctor cancer fa ka ce?" Abba ya tambaya a rud'e. Hajiya Mama kuwa tsabar firgici kasa magana ta yi. "Eh Alhaji, yanzu dai muna buƙatar jinin da za a ƙara mata cikin gaggawa, don ta zubar da jini sosai. Kuma jinita ya hau fiye da kima, akwai yiwuwar tayi jijjiga, kuma still akwai hatsari mu shiga da ita aiki, shi ya sa zamu bari zuwa safiya" Cikin hawaye Hajiya Mama ta ce. "Allah ka ba wa wannan yarinyar lafiya, Allah ka taƙaita mata, yanzu tana ina Doctor? Ina shi Adnan ɗin yake ya zo a gwada jininsa ko zai ya yi daidai da nata a ɗiba a ƙara mata." "Tana emergency ward room 3, v.i.p part." Godiya Abba ya yi wa likitan sannan suka miƙe suka fita, zuciyoyinsu cike da damuwa gami da zullumi. Turus Hajiya Mama ta tsaya tana kallon ikon Allah, Tsabar mamaki kasa magana ta yi. Duban Abba ta yi suka haɗa ido wanda shi ma ke cike da mamakin ganin hawayen Adnan, abin da suka manta rabon da su gani. "Haba Adnan, ya za ka tasa ta a gaba ka dinga kuka kamar wani ƙaramin yaro, ai addu'a ita ce mafita ba kuka ba." Hajiya Mama ta faɗa cikin tausasa harshe. A zabure ya juyo tare da sakin hannun Abra, lokaci ɗaya ya miƙe yana jan hanci ya ce. "Mama don Allah ki ce kar ta tafi ta bar ni, wallahi na yi nadama, ba zan ƙara cutar ta ita ba, da na sani ban yi tafiya na bar ta ita kaɗai a gida ba, na san ƙila da haka ba ta faru ba, da ba a kaita Asibitin waɗancan marasa imanin ba." Cikin mamaki Hajiya Mama ta ce. "Ban gane me kake faɗa ba Adnan, ƙara tafiya ka yi ka bar yarinya ita kaɗai a gida? Kai ba ka da hankali ne? Ba ka ganin yanayin da take ciki? Ai idan mace ta kai wannan lokacin ba a tafiya a bar ta ita ɗaya a gida. Kuma don iskanci maimakon ka kawo ta gida idan ba za ka iya tafiya da ta ba ko ka ce a zo a zauna da ita sai ka tafi ka ba bar ta?" "I'm sorry Mama, wallahi ƙaddara ce, don Allah ku taimake ni kar na rasa matata, wallahi ina son ta, ita ce rayuwata, na yi nadamar duk muzgunawar da dinga mata, akan lefin da ba ta ji ba, ba ta gani ba." Abba dai bai ce komai ba sai bin Adnan kawai yake da ido cikin nazartar shi, zuciyarsa take da takaicin shi. Juyawa Adnan ya yi ya riƙe Abra tare da jijjiga ta yana faɗin ta yafe masa cikin kuka da faɗar duk abubuwan da yake aikata mata na mugunta. Da ƙyar Hajiya Mama wadda ita ma ke kukan tausayin Abra ta janye shi. Gabaɗaya Adnan ya fita daga cikin hayyacinsa, surutu kawai yake yi cikin gigita kamar zararre. Abbi ne zaune a saman carpet yana operating system, lokaci ɗaya ya ture system ɗin tare da dafe kansa. Nai'ma dake gefensa ta kalle shi cikin kulawa ta ce. "Wai me yake damun ka ne man? Yanayinka kamar wanda yake cikin damuwa, ka sa na hado maka coffee kuma na kawo maka ba ka sha ba, abinci ma yau ka ƙi cin na kirki " Numfashi ya sauke ya ce. "Ba na jin daɗin jikina ne, gabana kuma sai faɗuwa yake yi, kamar wani mugun abun zai same ni." Cikin marairaicewa ta ce "Hasbunallahu, insha Allahu babu komai sai Alkhairi, ka daure ka sha coffee din, bari na hado maka wani." Kai kawai ya gyaɗa mata. Bayan ta dawo ya ce ta dauko masa wayarsa, Abra ya kira amma wayar ta ƙi tafiya. Cike da damuwa ya ce. "A cikin week din nan dole na je na gano daughter, kwana biyu ita take ta faɗo mini a rai." Na'ima ta ce "Allah ya kai mu, ni ma ina yawan tuna ta, kodan ta kusa haihuwa ne, Allah ya dai ya sauke ta lafiya." "Amin." Maman Rahama ce tsaye a kan dinning tana zuzzuba abinci, bayan ta gama ta zauna tare da rafka tagumi. Duban tsanaki Baban Rahama ya yi mata ya ce. "Ki ci abincin mana, tun ɗazu kin tasa shi a gaba, ko da akwai wata matsalar ne?" Tagumin ta sauke tare da faɗin. "Babu komai Abbansu, tunanin yarinyar nan da halin da take ciki ne kawai ya cika mini zuciya, ga shi mu ba numbern mijin nata ba bare mu kira mu ji ya jikin nata." Cikin damuwa Baban Rahama ya ce. "Ni ma yadda na ga jikin yarinyar nan ya tsaya mini a rai, abin tausayi wallahi." "Hmm, ai daga ganin mijin nan nata ba shi da kirki, ban da haka ya za ai ka yi tafiya ka bar yarinya mai tsohon ciki ita kaɗai a gida? Kuma ga dukkan alamu ta daɗe tana cutar, ba wai yau ta same ta ba. Ya zo ya ga kuma za ta mutu duk ya burcike, ni duk abubuwan da ya dinga yi ko kaɗan bai ba ni tausayi ba sai ma haushi, da ka ce mu bi shi lokacin da ya ɗauke ta kamar na ce ba za ni ba sai kuma na yi shiru muka bi shin, don dai kawai ina son sanin halin da yarinyar za ta kasance a ciki ne." "Sai haƙuri, kin san kowa da irinsa." "Amma dai wannan mutumin ba shi da kirki gaskiya, kana gani fa ko godiya bai yi mana ba sai masifa, a lokacin da ya zo so nake na yi masa bayanin halin da ake ciki, amma ganin yanayinsa na san ma ba saurara ta zai yi ba." "Allah ya dai ya ba ta lafiya kawai." "Amin ya Allah." An yi sa'a jinin Adnan ya zo daidai da na Abra, don haka aka ɗiba aka ƙara mata. An yi an yi da Adnan ya kwanta ya huta saboda ɗiban jinin da aka masa amma ya ƙi, duk da kuwa yana jiri na ɗiban shi. Da ƙyar Hajiya Mama ta lallaɓa shi direbansu ya kai shi gida ya sauya kayan jikinsa ya yi sallolin dake kansa. Abba kuwa ya ƙi kula shi, don zuciyarsa cike take da haushin shi akan abubuwan da ya ce ya yi wa Abra, ko kaɗan bai yi tunanin Adnan zai aikata irin wannan rashin imanin ba. Ba a yi wa Abra c.s ba a wannan daren, likitocin sun ce sai gobe ƙarfe bakwai na safe. A daren Abba ya saka Hajiya Mama ta kira su Abbi ta sanar musu halin da ake ciki, hankali a tashe Abbi ya ce za su yi asubanci su zo gobe. A asibitin Adnan ya kwana, duk yadda Hajiya Mama ta so ya koma gida amma ya ƙi, sai haƙura ta yi suka kwana tare. Yadda Adnan ya ga rana haka ya ga dare, a bakin gadon Abra ya zauna ya ƙura mata ido har garin Allah ya waye. An yi wa Abra c.s lafiya an fito da baby girl mai kyau, kamarta ɗaya sak da mahaifinta, sai dai ta ɗebo farin mamanta. Kasancewar watanninta 7 da satittika sai aka saka ta a kwalba. Ko kallon yarinyar Adnan bai yi ba, saboda ta uwarta yake ba ta ita ba, wadda har ƙarfe takwas na safe ba ta farfaɗo ba daga allurar baccin da aka mata. A lokacin ne kuma Abbi da Mami suka ƙaraso asibitin. It's paid book, contact us for more information. 09047871750[11/1, 1:10 PM] Abk: "Ya akai Abra ta samu blood cancer?" Abbi ya tambaya cike da damuwa da kuma tashin hankalin daya kasa ɓoyewa daga saman fuskarsa. Girgiza kai Abba yai Shima cike da damuwa makamanciyyar wacce Abbi yake ji. A hankali ya ce "It is what we do not know yet,she is in a difficult situation" dafe kai Abbi ya yi yana faɗin "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Ubangiji ka dubemu ka bawa daughter lafiya, kada ka ɗauki ranta ba tare data san wacece ita ba" ya faɗa cikin raunin murya mai nuna zallar damuwar da yake ciki. Ubangiji ya sani yadda yake jin Abra a ransa ko Salman baya ji haka, ita ɗin amanace a garesa,kusan marainiyya take,since he still could not find her real parents. "Insha Allah zata samu lafiya, mu ci-gaba dayi mata addu'a. Kayi haƙuri komai zai shige ta zama kamar kowa" Abba ya ƙare maganar yana kallon cikin ƙwayar idanun Abbi. Abbi kasa cewa komai yai domin bai fahimci mgnar da Abban Adnan yake ba, tunaninsa ya tafi can wani waje.. A hankali suka ƙarasa Vip part ɗin da aka kwantar da Abra, a nan bakin ƙofa suka samu Hajiya Mama da Uncle ɗin Adnan. Da sauri Mami ta ce. "Hajiya ya jikin nata? ta tashi wanne hali ƴata take ciki ne don Allah?" "Ki kwantar da hankalinki Hajiya Na'ima, Addu'a kawai za mu yiwa Abra,tare da babynta" Ajjiyar zuciya Mami ta sauke a wahale, Allah yana gani har ranta ta damu da halin da Abra take ciki, tsoro da ladamar abin da ta dinga aikata mata ya wanzu a zuciyar Mami. Idanunta ta ɗaga ta kalli Hajiya Mama kafin ta ce. "The baby is seven months pregnant?" Mami tayi tambayar cike da son jin cikakken bayanin da likita ya yi wa su Hajiya Mama. Jinjina kai Hajiya Mama tayi itama kafin ta ce. "as the doctor said, an sakata cikin kwalba babyn ba lafiya gareta ba itama, rashin lafiyar uwar ya taɓa ta tun a ciki" "Ya Salam, Ubangiji ya basu lafiya duk" Ammi wacce ta kasa mgn tun ɗazo ta kalli Hajiya Mama cikin jajintawa ta ce "Ya mai jikin? Allah yasa kaffara ne ya tashi kafaɗunta" "Amin Ya Rabbi Ammi" a karo na biyu Ammi ta ce "ba'a iya ganinta ne? Naga tunda muka zo kuma kuke waje a zaune, banga wani likita ba?" Hajiya Mama ta ce "Sure, she still hasn't recovered from the surgery. But Dr yace at Anything zata iya tashi" jinjina kai Ammi tayi tana da faɗin. "Allah sarki Abra Baiwar Allah,ta haɗu da mugun ciwo Allah ka yaye mata" duk suka amsa da Amin. Duk yadda za'a bayyana maka tashin hankali to na Abbi yafi ƙarfin a faɗesa, tunda suka zo ya kasa zama, banda sunan Allah babu abin da yake ambato a cikin bakinsa, sai ajjiyar zuciya da yake saukewa haka kurum fargaba ta riski zuciyarsa, tsoro da tunanin faruwar wani abu ya wanzu cikin tunaninsa, yana gani a wannan karan ba zai kuskuren da ya yi a baya ba, dole ne samu mafita, wacce zata yaye masa ciwon dake cin zuciyarsa na tsayin shekaru masu yawa. At this time dole ne idan Abra ta samu lafiya ya aiwatar da burin zuciyarsa duk da yana tunanin hakan abune mai wahalar gaske. Zuwan Dr wajan shi ne ya katse masa tunanin da yake, a hankali ya juya idanunsa da ya yi jajur ya kafe likitan dashi kamar yadda shima yake kallonsa. Likitan yaja numfashi bayan ya gama ƙare musu kallo, amma bai ga wanda yake nema ba cikin ƙasa da murya ya ce. "Where is Adnan Aliyu Matawalle?" Ya faɗa idanunsa akan Abban Adnan. Abba ya juya baya kaɗan ya ce " There he is behind you" Abba ya faɗa yana mai ɗaga murya "Adnan, Adnan" ya kira sunansa da ƙarfi kiran da babu wanda Adnan yaji ya tafi can duniyar tunani gaba ɗaya baya cikin hayyacinsa. Sai a kira na huɗu sannan ya miƙe a firgice yana dafe kansa dake barazanar tarwatsewa a haka ya ƙaraso wajan. Girgiza kai kawai Likitan yai kafin ya kalli Adnan sosai cikin tausayawa ya ce "Your wife wants to see you" Gaba ɗaya wajan suka miƙe tsaye kusan a tare suka ce "She woke up from the surgery?" "Sure. But yanzu mijinta take son gani, daga shi sai Abbi, who is he? Yana ina? ba a son mutane da yawa 1 by 1 ok" Adnan bai tsaya jin bayanin likitan ba, jiki na rawa ya nufi room ɗin da Abra ke ciki. A nutse Abbi ya ce. "See me here Dr. Ni ne Abbi" Dr ya jinjina kai ya ce "that's good after Adnan ya fito zaka iya shiga" jinjina kai kawai Abbi yai ba tare da yace komai ba, domin shi kaɗai yasan abin da yake masa yawo a cikin zuciyarsa dauriya kawai yake, ba iya Abra ce damuwarsa ba a yanzu haka kurum yaji tunanin Salman ya faɗo masa. Hannunsa na rawa ya murɗa handle ɗin room ɗin tare da turawa a hankali without making any sounds wanda zai iya damunta ba. Idanunsa akanta ya maida ƙofar ya rufe, ban san meke masa daɗi ba, amma wata mummunar faɗuwar gaba ce ta dirar masa, a lokacin daya daidai ƙwayar idanunsa akan fuskar Abra. Gani yai tai haske sosai kamar bata da jini sai kuma cikuwar da tayi wanda hakan baya rasa nasaba da ƙarin ruwan da ake mata akai akai. Ji yai kamar an zare masa lakar dake sarrafa ganganar jikinsa da ƙyar ya iya jan ƙafarsa zuwa bakin gadon daidai kanta ya nemi waje ya zauna. Ajjiyar zuciya ta sauke a hankali lokacin da Adnan ya zauna kusa da ita, idanunta rufe amma ta ɗan motsa kaɗan tana gyara kwanciyarta, ganin yadda take ƙoƙarin Zamewa ya sanya Adnan ɗagota baki ɗaya tare da kwantar da ita a jikinsa. "Oh sorry, sorry" ya faɗa in a very low voice ganin yadda ta cije bakinta. "Ya jikin Angel? kinji sauƙi ko, meke maki ciwo yanzu?" Adnan yai tambayar ajere cike da tashin hankali musamman da yaji jikinta zafi zau. Slowly ta shiga buɗe idanunta wanda suka fara juyewa kamar mai shirin sumewa, Adnan ta kalla ba tare da tace komai ba sai binsa da take da idanun kamar wanda bata sani ba, yau ta zama ranar farko da tayi arba da fuskarsa. "Why are: you silent Angel? Talk say something" tana jan numfashi da ƙyar ta ce "It's too late to cry Adnan" a ruɗe ya ce "kamarya? bana son irin haka, ki tashi mu tafi gida i knw kin samu lafiya Madam" ya faɗa yana tallafota gaba ɗaya zuwa jikinsa yama mance da batun ƙurajen da yake tsantsami ya rufeta ruf a jikinsa. A hankali ta kwantar da kanta a ƙirjinsa domin bata da wani kuzari ga C.s ga kuma ciwon da yaci ƙarfinta, a karo na farko tun bayan aurensu ta sakar masa wani irin sanyayyan murmushi wanda ya sanya kyunta bayyana muryarta na rawa tace "Me kake tsoro? Ina tunanin za kafi kowa farin ciki Adnan? Why are so worried? zakai rayuwa free yanzu burinka ya cika, na tabbatar da cewa kuma baka sona" da sauri ya rufe mata baki da tafin hannunsa yana riƙeta sosai a jikinsa ya ce "Na tuba, na tuba, na tuba ki yafe mini Abra,nabi Allah na biki kada ki tarwatsa mini zuciya da wannan maganganun naki, bana da kalmomin yi maki bayanin da zaki fahimta amma kece rayuwata ki sanya haka a ranki" jan numfashi tayi tana riƙe hannunsa sosai fuskarta cike da Murmushi kafin ta ce "Kada ka damu, nasan an maka ba daidai ba, kamar yadda ka ke faɗa. Sai dai kayi kuskuren ɗaukan fansar abun a kaina, bana da laifi bana laifi ban san me aka akaita maka har haka ba, ka cutar dani cuta mai yawa, ka yaudareni yaudarar da banyi tunaninta daga gareka ba, ka sanya na amince da kai,na guji Salman akan ka ka nuna mini SO da ƘAUNA, a wannan lokacin bana da wanda nake so nake da muradin kasancewa da shi kamar kai Adnan Aliyu Matawalle, but why why?" Ta faɗa murya shaƙe numfashinta na sama tuni hawaye suka cika idanun Adnan bai taɓa jin akwai abin da yake ladamar aikwata kamar yadda ya cutar da Abra ba, bai taɓa zaton abin da ya aikata ba daidai bane ba sai yanzu. Kafin yai mgn Abra ta zabura tare da ƙanƙamesa jikinta na rawa ta ce "mene laifna? yanzu burinka zai cika zan barka tare da mahaifin nawa wanda ban san shi ba, daman ka faɗa ka shaida masa cewa ina tsananin son sa da ƙaunarsa ina mafarkin haɗuwa dashi amma Ubangiji bai nufa ba" girgiza mata kai yai ya yi ya ce "No Abra, stop saying that yanzu a kuma yau za kiga mahaifinki na janye ƙudirana na zubar da dukkan makamaina na ɗaukan fansa, nima soyayya da kuma haushin abin da aka aikata a gareni ya sanya nai miki haka, an rabani da farin cikina, jin daɗina, kwanciyar hankalina, garkuwata, an rabani da abu mai muhimmanci a lokacin da nake tsananin so da ƙaunar kasancewa da abun" girgiza kai kawai tayi ba tare da tace komai ba, a hankali ta zame daga jikinsa ta koma saman pillow idanunta na zubar da hawaye. Sun jima a haka kafin ta ce "Me aka ciro a cikina?" Da sauri Adnan ya ce "It's a baby girl mai kama dake sak" ya faɗa yana kama hannunta tare da riƙesa cikin nasa hannun. Murmushi tai while hawaye na zuba daga idanunta ta ce "Kama dani? Uhm ka faɗa mata cewa ina sonta fiye da komai na duniya, idan babu damuwa kayi mini alfarma" jikinsa na rawa ya ce "faɗi komai kike so Abra, ko rayuwata kikeso zan baki wallahi Allah" "ka samawa yarinyar suna Aishatul-humaira" Hawayen idanunsa ya goge "Insha Allah, daga yanzu ma na raɗa mata suna da haka, Ubangiji ya raya mana Little Aishatul-humaira zamu reneta tare mu nuna mata zallar so da ƙauna irin na iyaye wanda duk daga ni harke bamu samu ba" Shiru tai masa idanunta rufe "Angel, Angel.. Abra! Abra".... "I'm still alive me kake tsoro" juyawa tai gaba ɗaya ta kallesa a hankali ta ce "Adnan" "na'am Angel" hannunta ya kama yana shafa raguwar sumar da tai saura a kanta ta ce "Ka yafe mini, banyi maka biyayya ba, na mayar maka da martani wanda mai dace da macen ƙwarai ba, kuma.....," Katse ta yai da faɗin "Baki mini komai ba, har wajan Ubangiji baki da laifi, idan ma Kinyi mini na yafe maki duniya da lahira don Allah ki yafe mini, na maki Al'ƙawari a lokaci na biyu zaki koma cikin gidana cike da jin daɗi da kwanciyar hankali, zan nuna maki soyayya wacce babu wanda ya taɓa samun irinta Abra, kiyi hqr ki zama mai yafiya" ita da bata zaton akwai wanda zai nuna mata soyayyar da Salman yai mata, har abada ba za'a samu ba. Murmushi tai masa a hankali fuskarta mai fidda annuri ta ce "Na yafe maka, amma zan barka ina mai jin tsanarka a zuciyata bana sonka Adnan, bana ƙaunar ganinka ina jin zafi da raɗaɗi a duk sanda na tuna abin da kai mini" a kiɗime Adnan zufa na yanko masa ya ce "No Abra kina so na, U love's me kada ki sanya zuciyarki cikin shakku akan soyayyata" hannunta ta miƙ tare da kama fuskarsa sosai ta ce "I hate you, wallahi bana ƙaunarka Adnan, kawai na san cewa na yafe maka, ina fatan ba zaka cutar da Aishatul-humaira kamar yadda ka cutar dani ba kaje abin ka, ka matsa daka kusa dani Mahaifina nake son gani" ta faɗa da ƙarfi ƙirjinta na ɗagawa sosai. Durƙushewa Adnan yai tare da fashewa da kuka sosai ya ce "Ina Son ki Abra, wallahi Allah ina son ki matata. Since the time I've met you, I cry a little less, laugh a little harder, and smile all the more, just because I have you, my life is a better place, naji dama ban aureki ba aduk sanda na azabtar dake, a kullum cikin kunci nake kwana, Every day with you is a wonderful addition to my life's journey, ki yafe mini ina tsananin buƙatar ki...." "Get out Adnan,I only want to see my father ka fita ka bani waje bana son ganinka wlh...," Fisgar da numfashinta yai ya sanya ta kasa magana sai rawa da jikinta ya fara. Da sauri Adnan ya miƙe yana faɗin "Bani 10 minutes Angel yanzu zan zo da Real father ɗinki I promise to you" yana faɗin hakan ya miƙe da sauri tare da nufar waje. "Adnan..." Ta kira sunansa a hankali juyawa yai suka haɗa idanu gani yai ta miƙa masa hannayenta a hankali ta ce "Come closer" kasa ƙara sawa yai murmushi ta saki tana jinjina masa kanta alamar yanzo ɗin, da ƙyar yaja ƙafarsa ya Ƙarasa wajanta yana zuwa ya zauna gefen gadon hannunta tasa ta jawosa jikinta holding nata back yai a tare suka saki ajjiyar zuciya tare da rungome juna. "I think I'm going now" hawaye na zuba daga cikin idanunta, shima kukan yake. Adnan dai bai fahimta riƙon da Abra tai masa ya shige na tunani kamar zata ɓallasa gida biyu "Am sorry Abra,.am sorry" ya faɗa yana sumbatar goshinta idanunta rufe bata ce komai ba, zare jikinsa yai da ƙyar ya jima yana kallonta kafin ya juya da sauri ya bar room ɗin. A haukace Adnan ya fito hankalinsa baya jikinsa Abbi da Abba a tare suka ce "Lafiya mene ya samu Abra meke faruwa" bai tsaya saurararsu ba ya fita da gudu zuwa reception kai tsaye ya nufi harabar asibiti mota ya shiga kamar zai tashi daga sama haka yabar cikin asibiti. Bayan Adnan Abba yabi, Abbi kuma da gudu ya shige room ɗin yana zuwa ya nufi kan Abra tare da kiran sunanta "Daughter" idanunta ta buɗe ta ce "Abbina?" "Na'am Daughter ya jikin?" "Naji sauƙi babu inda yake mini ciwo, Abbina ka kira min Salman ka kirasa shi kawai nake son gani Abbi ka taimaka mini don Allah" a rikice Abbi ya ce "zan kirasa ki kwantar da hankalinki zai zo insha Allah" jinjina kai tai tana ɗora kanta saman cinyar Abbi. "Abbi" ta kira sunansa kasa amsata yai sai Kallonta da yai ta ce "Allah ya saka maka da Alkairi Abbi, Ubangiji ya biya maka buƙa tunka na duniya da lahira, Allah yai maka kwatankwacin alherin da kai mini Abbi" "ya isa bana son magana irin haka, you'll be fine daughter" murmushi kawai tai domin a jikinta take jin cewa ta samu lafiya. "Abbi kada a bawa Adnan Aishatul-humaira, don Allah Abbi kada a bashi ƴata zai cutar da ita kamar yadda ya cutar dani kayi mini wannan alfarmar don Allah Abbina ka bawa Mami Aishatul-humaira na bar mata ita" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un kawai Abbi yake faɗa kafin da ƙarfi ya ce "Dr...!!!!!!". A hankali jirgin ya sauka a airport ɗin kaduna, wajan 10 minutes da saukarsa passenger's suka fara sauka daga cikin jirgin fuskarsu ɗauke da farin ciki. Kamar wanda ƙwai ya fashewa a ciki haka ya sakkowa daga cikin jirgin fuskarsa babu walwala hannunsa zube cikin Aljihu, farar fatarsa sai sheƙi take ya ƙara haske sosai da ƙiba ya zama saurayi sosai sai rashin kwanciyar hankali. Farar shadda ce a jikinsa wacce ta ƙara fito da kyansa na fulani sumar kansa tai kwance gwanin sha'awa. Salmanun-faris kenan yaro mai kyau da tsarin halitta. Yana sakkowa daga cikin jirgin kai tsaye wajan texsi ya nufa ya faɗa masa sunan unguwar da zai kaisa a nan Kaduna, har suka isa ƙofar gidan kansa a kife yake hannunsa dafe da saitin zuciyarsa dake harbawa da ƙarfi, fargaba ganinta a karo na biyu bayan tafiyarsa ta riski zuciyar Salman. "Saurayi waka ke nema?" Idanunsa ya ɗaga da ƙyar ya kalli Gatekeeper ɗin kafin a nutse kamar dole ya ce "Matar gidan" "wayyooo, Allah sarki baiwar Allah ko yaya jikin nata?" Da sauri Salman ya ce "what? Waye babu lafiya mene ya samu Angel?" Gatekeeper ɗin ya ce "Ayya yaro matar gidan babu lafiya suna asibiti kwana guda kenan da yini" dafe bango Salman yai sbd jirin dake neman yarda shi kafin ya ce "Wanne asibitin?" "Tana na wani private hospital amma yarinyar na jin jiki da....," "Shut up" Salman ya faɗa a hargitse yama manta tsoho ne mutumin. Jikinsa na rawa ya shiga mota Allah yasa mai texsi ɗin bai tafi ba. A haka suka bar wajan bayan an faɗa musu sunan asibitin mai texsi ɗin kuma yace ya san wajan. Gudu kawai Adnan yake shararawa a mota ikon Allah ya kai sa cikin wajan, ko kashe motar bai ba ya nufi ciki da gudu mutanan da suke cikin reception ne sukayo kan Adnan "Malam lafiya ka faɗo mana kamar wani sabon kamo kana neman taka mana patients?" Wani irin banzan kallo ya watsawa mai mgn ɗin kafin ya nufi ciki kai tsaye kuma wani office ya nufa. Yana zaune saman chair yana duba wani files kamar daga sama yaji an shaƙo wuyansa tare miƙar dashi tsaye. Kallon Adnan mutumin yai sosai kafin ya ce "who are you? How dare you come to my office without my permission eh? Mene matsalarka ba zan taɓa ko wanne mara lafiya ba sai an bada kuɗi cash, shi talaka wani lokacin bashi da lissafi gaba ɗaya" a hargitse cike da zafin zuciya Adnan ya ƙara shaƙe mutumin cikin zafin da ƙonar zuciya ya ce "Waye ni kake tambaya?" Mutumin ya ce "E, waye kai kuma da izinin wa ka shigo mini office" idanun Adnan cike da hawaye ya ce "Think.." "I don't have much time to think just explain Malam ko na kira securities" ƙara shaƙe masa wuya Adnan yai har sai da idanunsa ya fito waje kafin cikin ƙaraji kamar zaki Adnan ya ce "I Adnan Aliyu Matawalle, Yanzu ka tuna ko?" A wahale Mutumin ya ce "No, i can't ka sakeni Malam" girgiza kai Adnan yai kafin ya zaro Wayarsa daga cikin Aljihu ya shiga photos folder da aka saka _Life partner_ photon Abra ya fito dashi ya nunawa mutumin ya ce "Itama son zuciyarka ya sanya zaka kashe ta? Ya sanya zaka rabani da ita kamar yadda ka rabani da Mahaifiyata shekaru kusan 30 da suka shige? Ramin mugunta daman ance ka gina shi daidai kanka, ƙaiƙayi mai komawa kan masheƙiyya" mutumin ya kalli photon Abra sosai gabansa na faɗuwa ya ce "Wacece ita? Me nayi mata? Yaushe na aikata mata wani laifi?" Wani wawan kallo Adnan yai masa cikin ɗaga murya ya ce. "Ƴarka ce, wacce ka haifa da cikinka Abra Yusuf Garba Bulama.. duk abin da ya sameta dalilin G.Y Bulama hospital ne, wallahi idan na rasa matata kamar yadda na rasa mahaifiyata a sanadin wannan matsiyacin asibitin sai nayi Shari'a dakai, a wannan karan ba a matsayin talaka nazo ba, ba kuma a matsayin wanda ya kawo mara lafiya nazo ba, nazo tafiya dakai ne dalilin matata kuma ƴarka wacce ta buƙaci ganinka, kaje kaga halin da take ciki dalilin wulaƙanta ta da kayi asibitin ka, ka sanya anyi mata Allurar da sam bai dace da ciwonta ba" yana faɗin hakan yai cilli da Dr G.y wanda tunda Sp Adnan Aliyu Matawalle yake Masifa babu inda yake kallo sai fuskar wayar Adnan ɗin, zallar kamarsa yake kalla a fuskar Abra, wace ƴarsa? Yaushe ya samu yarinya kamar Abra? Duk duniya Yarinyarsa ɗaya Meenal, sai kuma wanda suka mutu bada haka ina ya samu wata yarinya? Zallar kamannin da suke da Abra ya ƙara sanya Dr G.y cikin ruɗu da kuma tashin hankali, ya kasa fahimtar komai shi kansa Adnan bai gama fahimtar wanne laifi ya aikatawa yaron ba, balle kuma ya samu zarafin tunani akan Abra?. Wayar Adnan ce ta fara ƙara ganin sunan Abba ya sanya ya ɗaga kiran da sauri yana faɗin "Abba ya jikin Angel?" Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya Abba ya sauke kamar ba zai mgn ba sai kuma ya ce "Duk inda kake kazo asibiti yanzu Adnan" jikin Adnan na rawa ya ce "Mene ya samu Abra Abba? Don Allah kada ka faɗa mini abin da zai iya tarwatsa mini zuciya" Abba ya ce "No lafiya lou take, infact ita ke nemanka" ajjiyar zuciya ya sauke ya ce "ok I'll be there yanzu Abba". Hajiya Mama ce ta riƙe Mami sosai wacce take rusa kuka tana neman kwacewa, Ammi na zaune ta kifa fuskarta a cinyarta tana salati da ƙarfi, Abbi kam yana jingine da jikin bango idanunsa sunyi jajir waya riƙe a hannunsa sai trying number Salman yake amma babu. Abba sai safa da marwa yake. Kamar daga Sama haka Abbi yaji saukar Muryar Salman cikin kunnansa yana faɗin "Abbi" da sauri Abbi ya juya domin ya ɗauka kunnansa ne kawai yaji haka, ganin Salman ya sanya Abbi sakin numfashi da sauri yaje ya rungomesa yana faɗin "Allhamdulillah" "Abbi Abra?" Kafin Abbi ya bawa Salman amsa wani Dr ya fito da sauri yana faɗin "waye Salman?" Da sauri Salman ya ƙarasa yana faɗin "I am" "Abra..." Kafin ya Ƙarasa Salman ya kwasa da gudu zuwa theatre room ɗin da Abra ke ciki, ƙwace ya sameta jikinta sai rawa yake ga wani jini dake zuba ta ƙasanta, harshenta ya zazzago idanunta ya fito waje kana ganinta kasan jijjiga take "Yaya, Yaya Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" gaba ɗaya Salman ya riƙice ya kama Abra ya Rungome yana sakin kuka tare da faɗin "Don Allah Yaya ki tashi, kada kiyi mini haka wallahi ba zan ƙara tafiya na barki ba" ciki wahala da fitar hayyaci Abra ta riƙe Salman tana faɗin "Ina son ka Salmanun-faris, ina son ka, i love You kai ne daidai da rayuwata Salman, ka biyoni muje idan kana so na da gaskiya" "Ina son ki yaya, burina na kasance dake matsayin matata Yaya ki tashi na maki al'ƙawarin ba zan nan asibitin ba, sai kin zama matata i promise you Abra" hancinsa taja tana riƙesa gam gam "Salman na baka Aishatul-humaira ka riƙeta wajanka, kayi aure ka bawa matarka ita, soyayyar da kake mini ta koma kan Aishatul-humaira Salman, Ubangiji bai ƙaddara zamu zama abu ɗaya ba, ka yafe mini Salman......," Ɗit! Ɗit!! Ɗit!!! Na'urar jikinta ta fara ƙara alamar numfashinta na sama yane ƙarewa, da sauri Abbi ya shigo ganinsu a haka yasa a kiɗime ya fara faɗin "La'ilaha illallahu Muhammadur Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallama" ya shiga faɗa da ƙarfi caraf Abra ta amsa ta shiga nanatawa a bakinta, gaba ɗaya Salman ya zare sai jijjigata yake ganin haka yasa Abba kama Salman amma yaƙi ya ƙara rungome Abra yana faɗin "No!!!! Don't do this to me Angel kada ki barni Yaya, yaya kece rayuwata ina son ki kada ki barni wallahi ƙarya kike babu inda zaki tafi dole mu rayu tare babu inda zaki yaya" daidai lokacin Likitoci suka shigo da gudu idanun Abra sukai sama har lokacin tana riƙe da hannun Salman. Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Abba kawai yake faɗa, Dr ya duba Abra muryar Abba na rawa ya ce "Dr ya dai?" Girgiza kai Dr yai domin bai taɓa ganin mutuwa mai tsayawa a rai kamar ta Abra ba "Sai haƙuri, Abra died!" Ya faɗa tare da jan farin yadin dake bed ɗin ya rufe mata fuska. Miƙewa tsaye Salman yai ya ce "Daman na sani, barci take tana farkawa zata ce ta fasa tafiya ta barni, Abbi kalli yaya ita ce komai tawa kalli yadda Abra ke barci" kasa mgn Abbi yai sai jawo Salman da yai jikinsa ya rungume amma gaba ɗaya jikin faris rawa da tsoma yake ga wani zafi da jikinsa ya ɗauka. Abba ya ce "Allahu Akbar Allah ya jiƙanƙi Abra Ubangiji ya sanya can tafi nan Allah yasa Aishatul-humaira ta zama garkuwarki rana gobe ƙiyama.." daidai lokacin Adnan ya faɗo cikin room ɗin idanunsa akan Abra wacce take ƙwance samɓal an rufeta da farin yadi. Juyawa yai ya kalli Abbi wanda yake rungome da Salman dake ta sumbatu kafin ya juya ya kalli Abba cikin rawar murya ya ce "Ina matata Abba?" Kasa mgn Abba yai da sauri Adnan ya Ƙarasa wajan gadon hannunsa na rawa ya yaye rufar da akai mata, Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un fuskar Abra yaci karo da ita idanunta rufe ruf sai haske da fuskarta tai sosai juyawa yai ya kalli Abba yana ƙoƙarin mgn jiri ya kwashe sa ya faɗi a wajan a sume babu numfashi, salati Abba ya fara likitoci suka ɗauki Adnan a wani gadon marasa lafiya, Mami da Hajiya Mama suka shigo banda kuka babu abin da suke, Ammi kasa shigowa tayi. Ganin wasu likitoci sun fara janye gadon da gawar Abra ke kwance akai yasa, Salman fasa ihu tare da faɗin "Yaya..." ya faɗa yana rike gadon tare da fara jijjiga gawar yana kiran sunanta kukansa ya tsaya domin gani yake she's still alive a koda wanne lokacin zata iya tashi tace "Faris ƙanina" Abbi mutuwar tsaye yai Sai ajjiyar zuciya yake saukewa da gske ne abin da likita ya faɗa Abra ta mutu? Jiri ne ya fara ɗaukansa ya zube a wajan saman qwiwoyinsa zufa na yanko masa,ƙam Salman ya riƙe gawar Abra yana surutai Mami ma haka, da ƙyar Abba ya zame Salman "Ka cikani yayata bata mutu ba, ba zata mutu ta barni ba wlh wasa take mini zata rama abin da nayi mata ne, barci take na faɗa muku" Sai kuma ya sulale a jikin Abba babu numfashi. Littafin kuɗi ne, mai so ya tuntuɓe mu ta wannan numbern. 09047871750 [11/2, 2:22 PM] Abk: Sannu a hankali ya dinga binsa a baya, a motarsa, duk da gudu yake tamkar zai tashi sama, baya kula da abin da yake gabansa balle yanayin tuƙin da yake yi. You tune yayi, ya cigaba kwarara gudu kamar mahaukaci. Harabar wani Asibiti ya shiga da motarsa, a ƙoƙarin da yake na ya cimmasa, motarsa ta yi faci, cikin sauri ya kashe motar ya tsallaka titi, ya shiga cikin Asibitin shima, sai dai Asibitin ƙato ne sosai bai san ina zai nufa ba balle ya ganshi, haka ya gama bulayinsa da leƙe leƙensa bai gano shi ba, haka ya juya ya bar Asibitin. A hankali ya motsa ƙafafuwansa, tare da ƙoƙarin buɗe idanunsa da suka yi masa nauyi, jin kansa yake tamkar an ɗora masa dutse, sannu a hankali ya buɗe idanunsa tangararau, ya shiga ƙare wa ɗakin kallo. Cikin ƙasa da mintuna biyu, ƙwaƙwalwarsa ta shiga tariyo masa abinda ya faru, sa'oin da suka shuɗe. A razane ya miƙe zaune tare da wani irin shouting "No! Ina mata ta take, Abra, Abra! Abra ki amsa mana, kin ganni nan zo mu tafi gida". "Adnan me kake yi hakane, shikenan ayi mutum babu tawakalli kamar ba musulmi ba". Cikin hanzari yai waiwayo ya riƙe hannun Mama ya ce "Hajiya Mama, an fito da Abra daga tiyatar ko? Eh haka ne, an ciro mana babynmu, Abra is under special care of doctors, bari in je in duba jikinta". Usman da ke gefe ya ƙaraso kusa da Adnan ya dafa shi ya ce "Sp, ka dawo hayyacinka mana, Abra is no more mun rasata, kayi mata Addu'a, dan ita tafi buƙata". Hankaɗe Usman Adnan yayi, ya fara ƙoƙarin sauka daga kan gadon, amma Usman yayi ta maza ya danne Adnan, Mama ta kira likitoci, suka zo suka maida Adnan bacci ta hanyar alluran da ake masa. Na'ima ce zaune a kan gadon marasa lafiya kusa da Salman, ta rungumeshi a jikinta tana kuka, Salman sai surutai yake yi "Mami, dan Allah kar ki ce mini da gaske na rasa Abra har abada, dan Allah ki tasheni daga baccin da nake yi, she's my life, ina sonta Mami". "Salman we miss her, Allah ya fi mu ƙaunarta, shi ya bamu ita kuma ya karɓeta, Salman na rasa 'yata, tun da nake a rayuwata ko mutuwar mahaifina ban ji ta kamar yadda naji mutuwar Abra ba, na rasa 'ya ta, 'ya mai biyayya da tsananin ƙaunata, Allah yayi miki rahama Abrana" Na'ima ta ƙarasa maganar, tana rushewa da kuka, mai cike da tsantsar damuwa da nadama. Salman da idanunsa suka yi jawurr, ya kalli Mami ya ce "Mami ina Abbi, mu tafi da gawar Abra Kaduna ayi mata sutura a can". Mami ta ce "Salman, kwanan Abra biyu a kabari, nan bana hayyacina, kaima ka suma suka tafi da gawar, aka yi mata jana'iza a gidan su mijinta, kuma babanku ya ce ba zaman makoki, kuma saboda rasuwar granny ma na can a gadon asibiti, Abbi ya tafi can wurinta". "What?! Mami a yiwa Angel sutura a binneta ban sani ba? Wayyo Allah na rayuwa shikenan ni da ita har Abada, ko sallama ba muyi ba, halinki na gari ya biki. Mami dan me za'a kaita gidansu Adnan kamar bata da galihu, mu meye amfanin mu?". "Faris, gidan mijinta ne fa, a nan yafi cancanta a mata sutura". Rungume Mami yayi ya sake fashewa da kuka ya ce "Mami, ki daina kirana da wannan sunan, kina karya mini zuciya, Angel ita ta raɗa mini sunan nan, yanzu ta tafi ta barni, dama ni na Aureta na rayu da ita zuwa yanzu". Jin Surtan Salman na neman wuce ƙa'ida, ya sanya Mami ta rungumeshi tana ta karanta masa Adduoi daban daban. 3days back Tun da ya koma Asibitinsa ya kasa zaune ya kasa tsaye, yayi shiru yana tunanin wasu abubuwa da suka shuɗe a rayuwar sa. Kamar mahaukaci haka ya fita reception, ya tattara ma'aikatansa gaba ɗaya, sai da ya fara ƙare musu kallo, sannan ya ce "Wacece a duty 3days back?" Aka nuna masa Nurse ɗin da take on duty. Ya kalleta ya ce "Ranar wace allura kika yiwa matar nan, bayan kin bar office ɗina?". "Wadda kace na yi mata ce" ta faɗa ba ƙwarin gwiwa. "Wacce nace ki mata?". "Amm, na manta sunanta bari in ɗakko kwalin" Kafin ta dawo, ya sa aka binciko file ɗin da aka duba Abra a ciki. Ya duba hoton mai File ɗin, amma ya ga ba fuskar Adnan ba ce a jiki, ya ɗau sheet ɗin da aka yi documenting ɗin case ɗin Abra a jiki, ya duba yana tsaka da dubawar Nurse ɗin ta dawo da kwalin allurar a hannunta. Ya karɓa ya fara dubawa, jifa yai da kwalin allurar ya shaƙo hijjabinta jikinsa yana rawa ya ce "Are You mad? Kin taɓa ganin an bawa mai ciki wannan allurar? Kin yi kisan kai ana nema a ɗora zargin a kaina a rufe mini Asbiti, kin yi hauka ne?" Nan take idanunta suka yo waje ta fara nishi da ƙyar, sai da ma'aikatan wurin suka haɗu da kyar suka ƙwaceta. Yana wani irin huci, ya kwafe lambar wayar jikin mai file ɗin nan ya fice, jikinsa na wani irin rawa, gaba ɗaya ya rikice kalaman matashin nan da yayi masa, da hoton yarinyar da ya gani ya jefa shi. Ya shiga tsananin tunani, dan son gano dalilin da ya sanya wannan yarinya ta ke kama da shi, shi dai a rayuwarsa ya san 'yar sa guda ɗaya ce tal, amma mai ya haɗashi kamanni da wannan kyakywar balarabiyar yarinyar?. "A wane hali take sanadin allurar da aka yi mata, an fita da ita daga Asibitin nan tana zubar da jini bana wasa ba, ko ta rayu? Ko kuma ta haɗu da wani ciwon sanadin allurar? Wane laifi na yiwa wannan matashin yaro?" Dafe kansa yayi da yake jin tamkar barazanar tsagewa, wani irin ɗaci na tasowa daga ƙirjinsa zuwa maƙogwaronsa, ga wani irin jiri da yake ɗibarsa, tun da yake bai taɓa dana sanin wasa da lafiyar wani ba, irin yadda aka yi wasa da lafiyar yarinyar nan da bai da tabaccin yanzu tana raye ko ta mutu oho, sannan yana son gano alaƙar da ke tsakanin sa da yarinyar, da har wannan matashi yake danganta ta da zama 'yar sa, alhalin 'ya ɗaya gare shi. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Mama wai ina Abba ne? Dan idan ke ba zaki gaya mini gaskia ba na san shi zai gaya mini, a nuna mini ɗakin da mata ta ke dan Allah, na tashi daga baccin da nake haka dan Allah ku haɗani da mata ta" Adnan ya cihaba da surutai tamkar mahaukaci. Tsawa Mama tayi masa "Adnan meye haka kake ne kamar ba musulmi ba? Ƙarshe wanda muka fi ƙauna a duniya shi ne Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, amma Allah ya karɓe shi baya duniya mun haƙura mun dangana, sai kace a kanka a fara yin rashi, duk kabi ka gallabi kan ka, ba zaka iya miƙa lamarinka ga Allah ba?". Cikin kuka Adnan ya ce "Yanzu Mama ta tabbata Abrana ba ta raye, ta tafi ta barni kenan?". "Zan maka ƙarya ne?". "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un! Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ka yafe mini. Allah Ina son matata, Allah.. Allah". "Kai kar ka mana saɓo, Addu'a zaka yi mata kawai". Miƙewa yayi ya sakko daga kan gadon, ya nufi hanyar fita, Mama ta ce "Ina zaka kuma?". "Zanje in ga gawarta ne, in mata addu'a in mata kallon ƙarshe". "To yau kwana uku da rasuwar Abra, kwananta uku a gidanta na gaskiya". Zaro jajayen idanunsa yayi ya ce "Mama kwana uku fa kika ce? Akan me za'a rufeta ban gama ganinta ba? Mama meyasa?". "To wa zai tsaya jiranka, ka fita hayyacinka kana ta sambatu, allurai aka yi ta yi maka, kwana uku kenan an binneta" ɗora hannu yayi a ka, ya zube ƙasa a gurin yana sake fashewa da kuka, just rembering the bad memories he makes with her, how bad he treated her, da sauran abubuwa marasa daɗi. Yayi kuka yayi kuka, sai da hawayensa suka bushe ya kalli Mama ya ce "Mama ina Abba ne?". "Kakar mahaifin Abra, wadda suke cewa Granny ce ta rasu jiya, saboda rasuwar Abra, tun da ta faɗi shikenan, ita ma jiya ta rasu, suna wajen zaman makoki, amma Salman da sirikarka suna Asibitin nan muna tare da su, amma basu sani ba, dan kar a sake ɗaga musu hankali, yanzu ka tashi kayi wanka da alwala, ka zo ka ci Abinci ka rama salloli duk na ji ance ruwan da aka dinga saka maka ba zai bari kaji yunwa ba". Kallon Mama yake, ita a tunninta har wani Abinci zai iya ci?. Har yaje yayi alwala ya tada salla, ya sanyawa ransa cewar mafarki yake yi, kuma zai farka. Lokaci ɗaya Salman yayi wata irin muguwar rama, yayi duhu fararen idanunsa sun yi jawur. Mami na ta rarrashinsa ya ci Abinci, amma yaƙi sai zubar hawaye kawai yake yi. Hajiya Mama ce tayi sallama a ɗakin na su, Mami ta amsa, Mama ta zauna suka gaisa tare da sake yiwa juna gaisuwa da kuma tambayar masu jiki. Mama ta ce "Salman ya dangana, Adnan kuwa sai fama nake da shi, haryanzu sai shirme yake yi, wai shi mafarki yake yi". Mami ta girgiza kai ta ce "Dole ya shiga cikin ɗimuwa Allah ya basu lafiya gaba ɗaya, ya jiƙan Abra". Mama ta amsa da Ameen, sannan ta ce "Amm na e Yakamata muje a duba jaririyar can ta cikin kwalba". Mami ta ce "Ni Wallahi tun da na rasa 'ya ta na manta da ita, shikenan bari muje, ni Major tunda yace mini zasu je Kano su dawo haryanzu shiru, na kirashi a waya sai yace mini zasu dawo, ina son in koma gida saboda masu gaisuwa". Mama ta ce "Eh ina ga ya bari ne ku ƙara samun sauƙi". Mami tace "Sauƙi kuma ai sai a hankali, amma har mu koma ga Allah ba zamu warke daga wannan rashin ba" tayi maganar tana share hawaye. Mama ta ce "Kiyi haƙuri, duk zaman jiranta muke yi". Haka suka tafi Nursery, wurin da aka sanya Aishatul Humaira a kwalba, ake cigaba da rainonta kasancewar ta bakwaini. Mami ta ƙurawa yarinyar ido, gata 'yar mistula sai uwar suma cunkus a kanta, ga dogon hanci kamar na babanta, sai farar fatar Abra da ta ɗakko, take ta hasko Abra lokacin da aka kawo mata ita tana yarinya, da yadda ta fara azabtar da ita, kawai ta fashe da wani irin kuka ta ce "Ni dama wannan 'yar ce ta mutu, aka bar mini tawa 'yar, wayyo Allah na Abrata, har Abada ba zan manta zaman da muka yi ba, kuma ba zan daina kewarki ba 'ya ta, ki yafe mini". Hajiya Mama tace "Kiyi haƙuri, shi Allah ba a tsara masa yadda zai yi, shi ya san hikimar karɓe uwar ya bar 'yar" Haka tayi ta rarrashin Na'ima, suka biya ta duba Adnan, shima duk ya ƙara rama, sai uban dogon hanci irin na 'yar sa. An kuma yi masa allurar bacci, amma yana yi yana surutai. Kwanakin Abra shida da rasuwa, sannan Abbi ya aiko da mota, Ya ce a tafi da su Salman, Hajiya Mama ta ce zata yi musu rakiya, suje ta ƙara musu gaisuwa. Adnan kuwa ko gaisuwa an hana ayi masa, saboda likitoci sun kafa doka sosai a kansa, idan ba abi an kiyaye ba ƙwaƙwalwarsa zata iya samun matsala. Kafin su Mami su tafi, ta tambayi yadda za ayi da Aisha, ko zasu tafi da ita, amma likitoci suka ce haryanzu ba ta yi ƙwari ba, sai an sake barinta. Gaba ɗaya hankalin Mami yayi gida, dan haka tace su bar Aisha, a dawo daga baya a ɗauketa, dan ta ita bata ƙi Aishan ta mutu ba, a dawo mata da Abra, ta nuna mata soyayyar 'ya da uwar da Abran tai ta roƙa a baya ba ta samu ba. Ga Mamakin Naima, maimakon ta ga an yi hanyar gida, amma sai taga an yi hanyar gidansu Ammi, ba ta yi mamaki ba a zatonta a can ake zaman makokin Abra, tun da gidansu ba kowa ba ta nan, sai dai bayan zuwansu suka riski labarin cewar makoki biyu ake yi, dana Abra da na Granny Innalillahi wa Innalillahi raji'un, tashin hankali ba a sa masa rana, da mutane da 'yan uwa sun dangana, amma zuwan Naima da Salman ya sanya mutuwar ta dawo sabuwa aka dinga koke_koke. Kwanan hajiya Mama ɗaya a Kaduna, tare da su Mami, sannan ta koma Kaduna, saboda hankalinta yana kan Adnan da ta baro shi a Asibiti. Zaune yake a falonsa, ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya, yayi shiru ya ƙurawa saman roofing, kusan kwanaki bakwan nan, baya iya bacci, hoton yarinyar nan fes ya ƙi barin idanunsa, zuciyarsa na cike da zullumi da son sanin tana raye ko kuwa? Sannan zuciyarsa ta kwaɗaitu da son sanin sahihiyar alaƙar da ke tsakanin ta da shi. Ya koma Asibitin da matashin yaron nan ya shiga babu adadi, amma bai ga ko alamar zai ga mai kama da Adnan ba. "Doctor wai meke faruwa ne, gaba ɗaya ka canza mai ya faru?" Ta faɗa tana zama a kusa da shi. "Bakomai" ya bata amsa a taƙaice. "Kamar yaya bakomai? Ba ka ko cin Abinci, ka daina zuwa wurin aiki, kuma kace mini bakoma". "Nace miki bakomai, ki ƙyaleni Please". "To naji zan ƙyaleka, magana ce dama nake son mu yi, Yaron nan da yake zuwa wurin Meenal ne yake son ya turo iyayensa, da tun wancan satin ma ya so ya turo, amma an musu rasuwa wai matar abokinsa ce ta rasu, kuma abokin nasa na Asibiti babu lafiya, amma yaushe za su sameka ko zuwa sati na gaba ne sai su zo ku yi magana". "Ke ki ƙyaleni na ce, ba wannan ne a gabana ba yanzu!" Yayi Maganar cikin tsawa. "To ko ma meye a gaban naka Allah yayi maka magani, amma dole ayi maganar auren 'yarka, koma menen tun da ba zaka faɗa ba kai ya dama, amma dole a san abin yi a kan Auren 'ya ta". Miƙewa yayi ya fice ya bar mata falon gaba ɗaya. Ƙwafa hajiya Saudat tayi, ta tashi ta koma sashinta. Meenal ce ta tarar da Mummy a ɗakinta. "Mummy kin gaya masa ya kuka yi da shi?". "Ni na rasa me yake damunsa, gaba ɗaya a takure yake, baya cin abinci ya daina zuwa wurin aiki, ko bacci ba ya iya yi" "To meya same shi?" "Ina na san masa, na tambaye shi yaƙi gaya mini". "To ni dai da kika gaya masa zancen Usman me yace miki? Ya ce su zo ɗin?". "Ina ya saurareni ma, balle muyi maganar" "Innalillahi, Mummy to jira za suyi har sai ya daina damuwar tukuna? Jira suke fa ya basu lokaci su zi". "Zan cigaba da yi masa magana, gara a san abun yi". "Yawwa Mummy, dan Allah ki cigaba da lallaɓa shi". "Ina jinjina abin da yake damunsa haka, na ga baya wasa da duk abin da ya shafe ki, amma naga yana cikin damuwa sosai". "To Allah ya yaye masa damuwar ta sa". Meenal ta amsa da "Ameen". Salman yana zaune a kan gadon Abra, yana tuna Abubuwa da suka shuɗe, na rayuwar da suka gudanar, tun daga ƙuruciya zuwa girmansu, halayyarta na shagwaɓa, a hankali ya lumshe idanunsa, yana tuna yadda ya dinga wasa da hankalinta a matsayin unkown ɗinta suna hira, lokaci ɗaya rabon Aishatul Humaira ya sanya Adnan ya kutso rayuwarsu, ya rabasu cikin gaggawa ashe rabon ajali ne ya sanya, da shigowar Adnan rayuwarta da Aurensu ba a ɗau lokaci mai tsawo ba. Hawaye yake sosai, yana ƙanƙame filonta a ƙirjinsa, yana juyi a kan gadonta, kansa har wani irin sarawa yake yi, saboda kuka. Sai da Abra ta kwana goma da rasuwa sannan aka sallami Adnan daga Asibiti, shima bisa sharuɗa da dokokin da likitoci suka shimfiɗa, saboda har yanzu baya hayyacinsa, da allurai sun sake shi, yake fara zabure-zabure da kuka shi wurin Abra zai je, a bashi matarsa su tafi. Idan ya ɗan watstsake, sai ya dinga tuna cewar rabon da ya ga Abbansa a kansa, tun lokacin da aka kawo Abra Asibiti. Hajiya Mama ce ke ta cigaba da rarrashinsa da bashi haƙuri, amma ya kasa yarda da cewar Abra ta mutu, lokuta da dama sai ya birkice yace mafarki yake yi. Kafin su tafi gida, Mama ta ce Adnan suje ya ga 'yar sa, dan bai ganta ba tun da aka haifeta. Tafiya yake tamkar wanda ya zare, jan ƙafarsa kawai yake yi, Mama na riƙe da hannunsa, wani Cousin ɗin Adnan Aminu na gefensa, jefa ƙafarsa kawai yake, yana kallon Asibitin. Haka suka je suka nemi izinin shiga wurin da jaririyar take, Adnan ya zubawa jaririyar idanu, Abra ba ta ga abin da ta haifa ba, gashi a hankali kamanninta juyewa suke zuwa na Abra, likitoci suka tabbatar da an kusa cireta da ga kwalba, a ɗorata a kan madara, ko kuma idan an samu mai shayar da ita a kafa masa dokokin kula da ita. "Mama ɗaukar mini ita a hoto" Adnan ya faɗa idanunsa na zub da hawaye. Mama ta ɗau hoton jaririyar, suka fito daga cikin wurin, zuwa cikin mota. Tun da Aminu yake bai taɓa ganin abin da ya sanya Adnan kuka ba irin mutuwar Abra, dan mutum ne mai dakakkiyar zuciya, ba komai ne ma yake ba shi tausayi ba, balle a sa ran zai yi kuka. Wayar Mama ya karɓa, yayi zooming ɗin fuskar Aishatul Humaira, wadda yake yiwa laƙabi da little Abra. Babban abin takaici shi ne da ka kalli jaririyar ka san jinin Bulama ce, dan a hankali kammaninta suke juyewa irin na Abra, ya tuna lokacin da ya ɗauko Abra daga Asibitin Bulama, tana zubar da jini, saboda halin ko in kula da wasa da rayuwarta da aka yi a Asibitin. Sakin wayar Adnan yayi ya ƙanƙame Mama yana kiran sunan Abra. Lamarin Adnan ya fara bawa Mama tsoro, amma tai shiru ta cigaba da yi masa Addu'a, har suka je gida yana kuka. "Mama ku fara kai ni kabarin Abra dan Allah" Mama ta ce "Adnan ni da ba dani aka kaita ba, ina na san kanarinta, muje gida Abbanka ya kai ka". "Mama Abba ya san Abra ta mutu ta barni kuwa?". Mama ta ɗan yi jimm, dan ba ta san ta ina zata fara yi masa bayani ba, amma ta basar ta ce "Eh ya sani mana, da shi aka kai ta gidanta na gaskiya ma" "Mama shi ne bai zo ya ganni ko sau ɗaya ba, shine bai bari na ganta ba yaje ya binne ta? Dan ba matarsa ba ce, shi lokacin da matarsa ta mutu haka aka yi masa? Ai shikenan idan na tashi daga baccin na san zan ganta a kusa da ni, ai tare muka kwanta jiya da daddare, har Abincin dare ta yi mana. Idan kuma muna Dubai ne sai inje gidan Abincin Hilal in sayo mana gasashen nama". Aminu ya ce "Anya Hajiya Adnan ba za a kai shi wurin likitocin ƙwaƙwalwa ba, kar fa abin ya zarce". Mama ta ce "Bari muje gidan tukuna, idan bai ware ba sai a san abun yi". Har suka je gida, Adnan surutai yake yi, yayi zancen hankali idan aka jima kuma, ya fara shirme da surutai. Haka suka isa gida, suna shiga cikin babban falon gidan suka tarar da Abba a zaune, yana duba system ɗin sa, Adnan na ganin Abba ya nufi wurin Abba, ya zube a kan gwiwowinsa ya riƙe ƙafar Abba yana faɗin "Abba, wai da gaske i loose my Abra, Abba ka sa aka binneta ban ganta ba, Abba ka nuna mini kabarinta in ganta kafin in tashi daga baccin" hankaɗe Adnan Abba yayi, ya zame ƙafarsa, ya kalli Adnan cikin tsananin takaici ya ce "Am disappointed on you Adnan, ban san a inda ka kwaso baƙin hali ba, ashe zamanka da yarinyar nan zalintar ta ka dinga yi? Na gode Allah da ba wani ne ya gaya mini ba, da bakinka Allah ya sa ka dinga faɗa, ba wani ne ya gaya mini ba balle in ce ƙarya ne, to kanka ka yiwa, kuma komai aka yi maka a rayuwar nan idan ka barwa Allah, ya gani zai saka maka, amma ina ruwan baiwar Allah da bata san laifin da aka yi maka ba, kai laifi nawa kake wa Ubangiji ya yafe maka? Ka samu yarinya 'yar mutunci mai haƙuri amma ka zalunceta, to ka sani har abada ba zaka taɓa samun yarinya mai haƙuri da kirki kamar Abra ba, Allah yayi mata rahama amma na yi dana sanin shigewa gaba wurin nemawa mutumin banza irinka Aure". Jiki a sanyeye Mama ta ce "Dan Allah Yallaɓai kayi haƙuri, ka tausaywa halin da yake ciki, likita ya kafa masa dokoki kar ya rasa hankalinsa". "I don't care, komai ya same shi shiya janyowa kansa, bai shafeni ba, na jinjinawa haƙurin yarinyar duk wannan zaman naku bata tona maka asiri ba, kaji kunya Adnan, kuma ka tattara ka bar mini gida ka koma gidanka kar ka sa in gaya maka wata muguwar Maganar" ƙurawa Abba Idanu Adnan yayi, ko ƙyaftawa ba yayi, kamar mai shirin aiwatar da wani abu. Bulama kuwa lambar maƙwabcin su Abra, ta jikin File ɗin Asibitinsu ya kira, yai sa'a mutumin ya ɗaga, suka yi arranging zasu haɗu da Bulama. Bayan haɗuwar ta su ne, Bulama ya sanar masa cewa yana son ya gaya masa alaƙarsa da matar da suka kai Asibiti ranar. "Matar maƙwabcina ce". "Yanzu ina maƙwabcin naka yake?". "Ai matar tasa ta rasu, shi kuma yana Asibiti babu lafiya". Wata irin mummunar faɗuwar gaba ce ta ziyarci Bulama, wani irin gumi ya shiga tsatstsafowa a goshinsa, wata irin nadama da tashin hankali suka mamaye shi. A saɓule ya ce "Ko zaka kwatanta mini Asibitin da yake?". Nan ya kwatanta masa Asibitin nan dai da yabi Adnan amma ya ɓace masa. Ya gaya masa har room ɗin, Bulama yayi masa godiya ya tafi. Adnan fa sai abin da ya ƙaru, gaba ɗaya ya ƙara birkicewa, dan an haɗasu da likitan ƙwaƙwalwa, saboda kar a rasa hankalinsa, Mama kuma nata rarrashin Abba a kan, ya sassauta fushin da yake da Adnan, kar abun yayi masa yawa. Ba ya cin komai sai ruwa sai kuka, wasu lokutan idan ya birkice sai dai ayi ta masa allurar bacci. Abbi da Mami tare da Salman, suka zo garin Kaduna domin karɓar jaririyar Abra, dan lokacin cirota daga kwalba yayi, Mami ta dage a kan cewar ita za'a bawa Little Abra ta riƙe. Abban Adnan ya koma wurin aikinsa, Adnan kuwa ba shi da lafiya da cikakken hankalin da za'a tambayi ra'ayinsa a kan riƙon Aisha. Tare da Hajiya Mama suka tafi Asibitin, suna nan tsaye suna ƙoƙarin shiga, Bulama ya fito daga cikin Asibitin, neman Adnan amma ya tarar an sallame shi. Salman ne yabi Bulama da ido, ko ƙyaftawa ba yayi amma ya kasa Magana. Na kuɗi ne a biya mu kan a karanta dan Allah 07063065680 [11/3, 6:09 PM] Abk: Har Bulama ya fice daga asibitin Salman bai daina kallon shi ba. Ajiyar zuciya ya sauke ya bi bayan su Abbi da suka wuce cikin kasala, kamar mutumin da Angel ɗinsa ta ɓaci, banbanci su kawai shi Namiji ne ita mace. Bai ɗauki hakan a matsayin wani abu ba, saboda yadda Abra take masa gizo akan duk abin da zai ɗora idonsa a kai sai ya ga fuskar Abra tana yi masa murmushi. Wasu hawaye masu ɗumi ne suka zubo akan kuncinsa. Cikin raunin murya ya furta. "Allah ya ji ƙan ki Yayata ya gafarta miki." Karɓar A'isha Humairah sai ya zamto fami a kan mikin dake kwance a zuciyar su Mami, tunda aka miƙo mata yarinyar take kuka, Hajiya Mama na taya ta da hawaye. Abbi kuwa ya yi shiru kawai sai numfashi yake saukewa. A haka Salman ya shiga inda suke ya same su, bai ce komai ba bayan sallamar da ya yi ya karɓi A'isha ya riƙe tare da zuba mata ido. Bacci take cikin kwanciyar hankali, ta ƙara girma da kyau da fari, a hankali ya kai hannu cikin ƙaunar ta ya shafa gashin girgarta zuwa kuncinta, idanunsa taf da hawaye ya ce. "Allah ya ji ƙan mahaifiyarki, ya raya mana ke, ya ba ki haƙuri da sanyin hali irin nata." "Amin ya Allah." Abbi ya amsa idanunsa a kansu. Kuka Nai'ma ta ƙara fashewa da shi tare da faɗin. "Da gaske dai ba zan farka daga wannan mummunan mafarkin da nake ba, ta tabbata Abra ta rasu, innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, na kasa sabawa da rashin ki ƴata, kodayaushe kewar ki ƙaruwa take a cikin zuciyata." "Sai haƙuri Hajiya, dukkan mai rai mamaci ne, mu ma duk zaman jiran ta muke, fatanmu kawai Allah ya sa mu cika da kyau da imani." Cewar Likitan da suka karɓi A'isha Humairah a hannunsa. Haka suka baro asibitin zuciyoyinsu babu daɗi, Salman dai na riƙe gam da Baby ya ƙi bawa kowa ita. A ranar suka juya Kano ba su kwana ba, duk kuwa da yadda Hajiya Mama ta so hakan, har suka taho ba su haɗu da Adnan ba, yana baccin allurar da aka yi masa. Daf da Magriba ya farka daga baccin a firgice yana kiran sunan Abra. Aminu dake ɗakin ya yi hanzarin yin kansa ya riƙe shi. "Abra! Tana Ina? Yanzu fa muke tare ta kawo mini ruwa mai sanyi ina sha tana ta mini murmushi, ashe ba ta mutu ba duk mafarki nake yi." Ya faɗa cikin son kwace jikinsa daga riƙon da Aminu yay masa tare da waige-waigen inda zai ga Abra." Cikin son kwantar masa da hankali Aminu ya ce. "Ta fita ne, amma yanzu za ta dawo." Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi tare da yin murmurshi ya ce. "Ina ta je? Raka ni gurin ta, bana son tana yin nesa da ni, kar na je mummunan mafarkin da na yi ya tabbata." "To zan raka ka, amma ka fara yin wanka ka ci abinci ka yi sallolin dake kanka?" "Me ya sa?" "Saboda ta ce idan ba ka yi ba kar na raka ka gurin ta." Zabura ya yi cikin ƙoƙarin saukowa daga kan gadon yana faɗin. "Zan yi yanzu." Taimaka masa Aminu ya yi ya raka shi toilet zuciyarsa cike da tausayin shi, idan ba dabara ake masa irin haka ba, ba za a samu kansa cikin sauƙi ba. Bayan ya fito ya yi Sallah ya fita parlour. Hajiya Mama da Abba ya tarar a parlour'n, cikin sauri ya ce. "Ina Abra? Where is my wife?" Dafe kai Hajiya Mama ta yi ta ce. "Oh My God! Adnan wai sai yaushe za ka yarda Abra ta rasu ne?" "Ba zan taɓa yarda ba, saboda in dai hakan ya tabbata ni ma bin ta zan yi." Ya yi maganar cikin hawaye. Kallon sama da ƙasa Abba ya yi masa, duk da yadda ya lalace ya yi baƙi amma bai ji tausayin shi ba ko kaɗan, taɓe baki ya yi tare da ɗauke kansa daga kallon shi. Kuka sosai Adnan ya saka tare da faɗin. "Abra me ya sa za ki tafi a lokacin da nake cikin tsananin ɓukatar ki a cikin rayuwata, ina son ki wallahi, na yi nadamar duk abubuwan da na aikata miki, don Allah ki dawo gare ni." "Haba Adnan, yaushe za ka daina wannan kukan da surutun ne? Sai ka ce ba musulmi ba, Ubangijin da ya ba mu Abra ya fi mu son ta shi ya sa ya ɗauke ta, addu'a kawai za ka yi mata, shi ne soyayyar da za ka nuna mata." "Shikenan Mama, na yarda na haƙura, na rasa masoyiyata." Ya yi maganar cikin wani irin yanayi tare da kwanciya a ƙasa. Girgiza kai Aminu da ya biyo bayan shi ya yi zuciyarsa cike da ɗimbin mamakin dama akwai abin da zai mayar da Adnan haka? Mutum mai tsananin zuciya da zafin rai gami da dakiya, lallai ya tabbatar ba ƙaramar k'auna yake yi wa matar nan tasa ba. Hajiya Saudat ce zaune a bakin gado ta yi tagumi tana kallon Bulama dake kai kawo a ɗakinsa kamar wani sabon soja. "Wai don girman Allah Doctor me yake damun ka ne kwana biyu? Ka daina walwala, ka daina cin abinci, office ma an ce ka daina zuwa, ka faɗa mini me yake damun ka." "Ba zan faɗa ba Saudat, na ce ki ƙyale ni ki daina biyo ni kina mini waɗannan tambayoyin amma ƙin ki ko? Wallahi zan saɓar miki!" Ya yi maganar cikin ɗaga murya. Cikin tsantsar mamaki ta ce. "Ni ce fa Saudat matarka Doctor kake mini magana cikin tsawa? Ko ka manta ne?" "Get out from My room, kafin na wurga ki ta window!" Jijjiga kai ta yi ba ta ce komai ba ta tashi ta fice. Da wani mugun kallo ya raka ta, bayan ta fice ya rufe ƙofarsa tare da faɗin. "Idiot, abu yana damun mutum za ta ishe shi da wasu mahaukatan tambayoyinta." "Me ya faru Mom na gan ki a haka?" Meenal ta tambayi Hajiya Saudat. "Akwai matsala Daughter, mahaifinki ya burkice gabaɗaya, har da yi mini tsawa yau." "Ni dai ba wannan ne damuwata ba, kin ƙara masa maganar Usman?" "Ki shiga ki yi masa da kanki." Hajiya Saudat ta faɗa cikin harararar Meenal. Baki ta tura gaba ta fara ƙunƙuni tare da magana ƙasa-ƙasa, ƙwafa Hajiya Saudat ta yi ta shige ɗakinta. "Maman Rahama har yanzu kin kasa cire damuwar mutuwar yarinyar nan daga ranki, ta riga ta tafi fa, ba za ta dawo ba." Tagumin da ta yi ta sauke ta ce. "Dole na damu Baban Rahama, ranar da muka kai ta asibiti kawai nake tunawa, ashe mutuwa za ta yi ma, Allah Sarki baiwar Allah." "Addu'armu kawai take buƙata a halin yanzu." "To Allah ya ji ƙan ta, ya gafar ta mata, amma mutuwar ta ta duke ni ba kaɗan ba." "Haka rayuwar take, ni sai damu na da kira Doctor Bulama yake, wai dole sai na haɗa shi da mijinta." Tsaki Maman Rahama ta yi ta ce. "Rabu da shi, bayan wulaƙancin da suka yi mana a asibitinsa, ana ta fadar rashin mutuncin mutumin nan, amma ban zata ya kai haka ba." "Shi ya sa na ce masa ban san inda zai same shi ba, don ni ma ranar ya ɓata mini rai." "Allah ya kyauta." Hajiya Nai'ma na zaune a main parlour tana jijjiga A'isha Humairah dake kuka. Abbi dake parlour'n yana karatun Alqur'ani ya ce. "Kukan little Abra ya yi yawa yau, ko wani abun ke damun ta?" Cikin damuwa Nai'ma ta ce. "Ban sani ba ni ma, amma ina jin ko cikinta ne ya ɗan kumbura, don kafin ka ji kukanta ana daɗewa, na ba ta abincinta ma ta ƙi shan na kirki." "To, ko sai mun ga likita ne?" Kafin Nai'ma ta yi magana Salman ya shigo parlour'n, bin shi suka yi da kallo ganin yanayin shi, kullum Salman ƙara lalacewa yake saboda damuwar rashin Abra. Jiki a sanyaye ya zauna a kan carpet bayan ya karɓi A'isha tare da gaishe da iyayensa. Jijjiga ta ya shiga yi a hankali, babu jimawa ta yi shiru bacci ya ɗauke ta. "Lalle ma yarinyar nan, saboda kina hannun Ubanki sai kika yi shiru ko?" Murmushi ya yi a saman leɓɓensa bai ce komai ba, karɓar ta Mami ta yi ta kwantar a kan kujera tare da faɗin. "Ga abinci can a dinning ka je ka ci." "Na ƙoshi Mami." Gyara zama Abbi ya yi ya ce. "Rayuwa ba za ta yiyu babu cin abinci ba Salman, ina lura da kai tunda Abra ta rasu ba ka wani cin abincin kirki. Haƙuri za ka yi ka daure, mu ma duk ƙarfin hali kawai muke." Cikin hawaye Salman ya ce. "Na kasa Abbi, na kasa daurewa, lokaci ɗaya a ce babu Yaya babu Granny." "Haƙuri za mu yi Salman, haka Ubangiji ya ƙadarto mana, Please my son ka rage wannan damuwar, We are all Muslim, yarda da ƙaddara mai kyau da mara kyau ya zama dole a gare mu, Abra ta tafi, amma ta bar mana wata, wadda muke fatan ta samu zuri'a daga gurin ta." Share hawaye Nai'ma ta yi ta ɗauki A'isha ta bar parlour'n, cikin ƙoƙarin mayar da kukan da ya taho mata. "Insha Allahu Abbi zan rage, sannan dama na zo ne in maka maganar komawa ta China a cikin week ɗin nan insha Allahu." "A yadda kake za ka fahimci wani karatu kuwa Salman?" "Zan fahimta Abbi, kar ka damu." "Tom shikenan, Allah ya kai mu ya ba da sa'a." Nasiha Abbi ya cigaba da yi wa Salman, wanda ya zaɓi komawa China ne ba don karatu ba kamar yadda ya ce wa Abbi, don shi a karan kansa ya san babu abin da zai fahimta, ya yi hakan ne kawai don ya nesanta kansa da duk wani abu da zai dinga tuna masa da Abra, saboda a kodayaushe gani yake kamar za ta dawo su cigaba da rayuwa, zuciyarsa ta kasa ɗaukar dangana da rashin Abra, ta kasa haƙurin rashin ta. Shi ya sa yanke wannan shawarar ko zai samu salama. Ganin yadda ake ta zuwa yi wa Adnan gaisuwa ya sa Hajiya Mama ta saka aka yi masa rubutun dangana take ba shi yake sha, saboda babu daɗi a dinga ganin shi a birkicen da yake, don ba shi da maraba da mahaukaci. Alhamdulillah kwalliya ta biya kuɗin sabulu, cikin kwana biyu ya fara dawowa cikin hayyacinsa, ya rage surutan da yake yi. Sai dai ba um ba um'um, sai ya wuni baiwa kowa magana ba, abinci kuwa da ƙyar yake yin 3 spoon a yini, sai ruwan bunu da Hajiya Mama take matsa masa yake sha. Gabaɗaya ya lalace ya zama abun tausayi, duk wannan abubuwan har yanzu Abba ba ya shiga harkarsa, ko Kallon inda yake ba ya yi, abun har ya fara damun Hajiya Mama. A hankali yake tafiya kamar zai fadi saboda rashin ƙwarin jikinsa, hannunsa ɗaya dafe da kansa dake yi masa wani irin ciwo, ɗayan kuma ya ɗora a kan ƙirjinsa da ya ji ya yi masa nauyi. Da kyar ya iya ƙarasawa compound din gidansu, cikin haki ya dubi direban Hajiya Mama wanda ya zuba ido masa cike da tausayawa, muryarsa ko fita ba ta yi sosai ya ce. "Kai ni gidana." Direban kamar ya yi magana sai kuma ya fasa ya miƙe ya nufi parking space, a galabaice Adnan ya mara masa baya. Da kallon tsantsar mamaki mai gadi yake bin Adnan da shi lokacin da ya fito daga mota, don da farko ma bai gane shi ba, sai da ya nutsu sosai ya gane mai gidan ne. Yana gaishe shi amma ko tsayawa saurar shi bai yi ba. "Ikon Allah, gaskiya mu ji tsoron duniya, yanzu yallaɓai ne ya koma haka? Ya rame ya ƙara duhu sai idanu ƙwala-ƙwala da suka ƙara fitowa, ga saje da sumar kansa duk sun yi wani iri, kamar ba shi ne ɗan gayun nan mai tafiyar jaruman Maza ba, Taɓdi! Allah dai ya sa mu dace." Mai gadi ya faɗa yana bin bayan Adnan da kallo. Ƙofar parlour'n a buɗe take, tun ranar da Abra ta fito ta faɗi take a haka, shi ma ranar da ya dawo bai tsaya rufewa ba jin tana asibiti. Hannunsa na rawa ya buɗe ƙofar ya shiga, cak ya tsaya idanunsa cike da hawaye yana kallon gurin da take yawan zama a parlour'n. "Angel don Allah ki fito, na san kina cikin gidan nan, za ki fito daga ɗaki ki tarɓe ni yanzu kamar yadda kika saba ko? Na san ba ki mutu ba, nan kika zo kika ɓuya." Ya ƙarashe maganar tare da nufar ɗakinta yana kuka wiwi. Tura ƙofar ɗakin ya yi da ƙarfi yana kiran sunanta. Ƙamshinta da bai bar ɗakin ba har lokacin ya ziyarci hancinsa. Kan gadon ya ƙurawa ido, cikin fatan ya gan ta a kwance kamar yadda ya saba ganin ta lokuta da yawa a baya. "Adnan, don Allah ka sauwaƙe mini wannan ƙaddararren auren naka." "Me ya sa za ka ɗauki fansa a kaina? me na yi maka? Mene laifi na? Don Allah kar ka cutar da ni akan abin da ba ni na aikata maka ba." "Ina son ka Adnan, don Allah kar ka juya mini baya." Maganganunta da ta yi masa a mabanbantan lokuta cikin kuka suka yi masa kuwwa a cikin kunne, kamar a yanzu take durƙushe tana roƙon shi. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Wallahi ina son ki matata, ki yafe mini ki dawo gare ni, na yi nadama da dana sanin cutar da ke a rayuwata." Adnan ya faɗi haka cikin kuka tare da faɗawa kan gado saboda jirin da ya kwashe shi. Ranar da ya fara ganin innocent face ɗinta a school ya tuna, da ranar da suka haɗu a cafeteria har ya ɗauke mata wayarta, da ranar da ya ɗauke ta suka je restaurant daga nan ya kai ta gida. Wani irin kuka ya fashe da shi lokacin da ya tuna yadda ta so shi, ba tare da wani jan rai ba, ta so shi saboda Allah ba don komai ba, amma ya butulce mata, ya muzguna mata, ya ƙunƙuta wa rayuwarta, gashi nan ta tafi ta bar masa duniyar. Sosai yake kuka tare da bubbuga kansa a jikin gado, muguntar da ya dinga yi mata kala-kala na faɗowa a cikin ransa. Babu abin da ya fi damun shi irin yadda yake zuwar mata ta ƙarfi a mu'amalar Aure, amma ba ta taɓa hana shi ba ko ta nuna rashin jin daɗin ta akan hakan, saboda ta san haƙƙinsa ne. Sai abu na biyu da ya yi mata wanda ba zai yafe wa kansa ba, ranar da ya kawo karuwa gidan, ba ya bin mata, hasalima ya tsani karuwar mace, amma saboda ya ƙuntata mata ya samo karuwar ta dalilin wani abokinsa da yake harkar, ya dinga tattaɓata duk da ƙyanƙyamin ta da yake yi. Saboda kawai ya ɓata wa baiwar Allar da ba ta ji ba, ba ta gani ba. Dama ana dawo da rayuwa baya, da ya dawo da tasa ya goge duk abin da ya yi wa Abra, ya maye gurbinsa da sanyata farinciki da jin daɗi, sai dai kash! Ba shi da wannan damar. Miƙewa ya yi a haukace ya buɗe wardrobe ɗinta ya shiga ɗebo kayanta yana shinshinawa tare da yin surutai irin na fitar hayyaci. Gabaɗaya ya hargitse ɗakin da sunan neman inda ta ɓuya yake, cikin haka ya ga wayarta a ƙasan gado. Jiki na rawa ya ɗauko ya kunna, ya yi sa'a da guntun chaji a ciki, kuma wayar babu key. Direct Gallery ya shiga ya fara kallon pics ɗinta da short videos. "Why Abra? Me ya sa za ki tafi ki bar ni? Ya Allah ka ɗauki raina cikin gaggawa, domin rayuwata ba ta da amfani idan babu Angel." Ya ƙarashe maganar tare da cillar da wayar saboda wani irin tari da ya turniƙe shi. Daidai lokacin direban da ya kawo shi ya shigo parlour'n, saboda tun ɗazu Hajiya Mama take kiran shi akan ya dawo da Adnan gida, ta shiga ɗakin Adnan ba ta gan shi ba sai ta fito harabar gidan ta tambayi mai gadi ko ya kan shi? Ya sanar mata ya ga driver ya ɗauke shi sun fita. Bai gan shi a parlour'n, hakan ya sa ya nufi ɗakin da yake jiyo ɗan motsi ya yi sallama, jin ba a amsa masa ba ya sa shi kutsa kai ciki ya tarar da Adnan cikin mawuyacin hali. Ganin yadda Adnan yake tarin kamar wadda ake zarar ransa ya sa ya kama shi cikin sauri suka fita. Fuskarsa duk dagaje-dagaje da hawaye da majina, ga gefen kansa ya fashe saboda buga kansa da ya dinga yi, gaban jallabiyar jikinsa ya jiƙe sharkaf da hawaye da gumi. Suna dawowa gida Hajiya Mama ta ce su tafi asibiti kawai, don a lokacin har ya sume. Kwanansu uku a asibitin aka sallamo shi, duk da bai warke ba amma ya fara jin sauƙi, bayan sun dawo gida Hajiya Mama ta same shi a ɗaki yana sana'ar tasa ta tunani, zama ta yi a kusa da shi cikin sanyin murya ta fara magana. "Adnan, ka takura sai an sallame ka mun dawo gida, to mun dawo ɗin, amma don Allah ka cire damuwa da tunanin da ka saka a cikin zuciyarka, ka ji likita ya ce jininka ya hau sosai, sannan kuma ciwon zuciya na daf da kama ka, ko so kake ƴarku ta rayu marainiya ba uwa ba uwa?" Girgiza kai ya yi a hankali. "To ka daina, ka bar wa Allah komai sai ka ga ya ba ka wata wadda ta fita." "Babu macen da tafi Abra a duniya Mama, ba zan taɓa samun mai haƙuri da ladabinta ba, na riga na yi babbar asara a rayuwata." Ya faɗi haka cikin kuka. "Wai yaushe za ka bar kukan nan ne, kamar ba namiji ba? Namijin ma Jarumi irinka, ka zamo mai tawakkali mana da miƙawa Allah al'amuranka, sai ka ga ya kawo maka komai cikin sauƙi." "Na cutar ita! Na zalunce ta! Na ƙuntata mata, akan abun da ba ta da masaniya a kai, na yi nadama mara adadi." "Ashsha! Shi ya sa ba komai zuciya take faɗawa mutum ya bi ba, domin ita ba ta da ƙashi, ka tafka babban kuskure a rayuwarka Adnan, ka yi wauta." Bai ƙara magana sai kansa da ya kifa akan pillow yana sassauke numfashi, girgiza kai Hajiya Mama ta yi ta tashi ta fice. Parlour'n Abba ta je ta same shi yana waya, bayan ya gama ta dube shi ta ce. "Alhaji don Allah ka sassauta fushin da kake da yaron nan, ko ya samu sauƙi a rayuwarsa, kwanansa uku a asibiti amma ba ka je ka duba shi ba." "Ni na ce fushi nake da shi ne? Abin da yake so ya ga dama ya aikata, to me zan yi masa kuma? Da na sani da kaico ne yanzu ya fara gani a cikin rayuwarsa." "Subhanallahi! Kar ka yi masa baki mana Alhaji." "Ba baki na yi masa ba, amma ni da ke da shi duk mun san *ABIN DA KA SHUKA* shi za ka girba, don haka bai ma fara girɓar abin da ya shuka ɗin ba, tukunna dai." Hajiya Mama ba ta kuma magana, don ta san idan Abba ya yi irin wannan fushin ba mai iya sakko da shi, sai ya ga dama ya sakko da kansa. 4 weeks later Mami ce zaune a ɗakinta rungume da A'isha Humairah tana yi mata wasa, ita kuma ta yi mata ƙuri da ido. Wata irin ƙaunar yarinyar Nai'ma take yi, musamman yanzu da kammaninta suka juye sak na Mamanta. Sai da ta yi bacci sannan ta kwantar da ita a kan gado ta ɗauki wayarta ta kunna data ta shiga WhatsApp. Reply na messages ta dinga yi, bayan ta gama ta tafi status ta fara kalla. Wata irin zabura ta yi lokaci ɗaya ta miƙe tare da cillar da wayar tata, kamar wata mahaukaci ta ƙwalla ƙara tare da murza idonta. "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un! Allah ka sa idona ne yake mini gizo abin da na gani ba daidai ba ne, no ba zai yiyu ba ma, babu ta yadda za a yi kwana uku da yin arba'in ɗin Abra hakan ta kasance, na san ma ba gaskiya ba ne." Ta ƙarashe maganar tana girgiza kai cikin tsananin firgici, ban da bugawa da ƙarfi babu abin da ƙirjinta yake. It's paid book. 09047871750 [11/4, 7:56 PM] Abk: A ruɗe Mami ta sake duba wayarta domin gani take kamar idanunta bai nuna mata daidai ba. Babu yadda za'ai ace hakan ta kasance domin ba abune mai sauƙi ba, "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un na shiga uku ni Na'ima" ta furta a fili lokacin data ƙara tabbatar da abin gsky bawai gizau ba amma zuciyarta ta kasa gasgata hakan. Jikinta na rawa ta ƙara duba status ɗin Uncle Shureim a karo na babu adadi, ƙurawa Invitation ɗin idanu tai zuciyarta na bugawa da ƙarfi ganin sunan Major Khamal Khamis and Salima Ibrahim Haroon. Zaman ƴan bori tai ta jima ba taga abin daya ɗaga mata hankali irin wannan ba, kafin ta dawo daga tunani ta ƙara ganin matar Uncle Shureim tai status da Invitation na ɗaurin aure ta saka _Wish You all the best babban yaya, Ubangiji ya baku zama lafiya yasa matarka ce har Abada. I'm so happy mun samu abokiyar hira_ Da ƙyar Mami ta Ƙarasa karanta rubutun dake ƙasan Invitation ɗin sbd yadda jikinta ke rawa da ɓari tashin hankali ya bayyana saman fuskarta shin da gaske ne? ko ƙarya ne? ko dai wani ne mai irin sunan mijinta, But how can that be possible ta ya ya ne Major zai aure ba tare data sani ba? Ganin kanta na neman kullewa na rashin gane gskyar abun yasa Mami da sauri taiwa Matar Uncle Shureim reply da. "Amin. But waye zai aure?" Matar Uncle Shureim ta jima tana dariya ganin rainin hankalin Na'ima sai kuma tai mata reply da. "Abbin Salman da Marigayiya Abra kakan Aishatul-humaira" tai mata reply da hakan tana tun tsira dariya. Da sauri Mami ta kashe datar idanunta na cika da hawaye baƙin ciki da kuma yadda Major yaci amanarta tare da ci mata zarafi da can bai mata kishiya ba sai yanzu? Me kishiya zata zo yi a cikinsu? Kishiyar ma wannan tsinanniyyar karuwar Salima. Number Anuty Suwaiba ta kira tana ɗauka ta fashe da kuka sosai tama kasa magana baki ɗaya. Daga cikin wayar Anuty Suwaiba taja tsaki cikin faɗa ta ce "Mtwss Malam kin kira kuma zaki cika mini kunne da ihun banza wani abin ne ya faru? domin nasan wannan gidan naki baya rabo da issues kamar gidan haya ko yari" cikin kuka Mami ta ce. "Na shiga uku Anuty Suwaiba Major Aure zai, kishiya zai yi mini dame zanji da rashin Abra ko da kula da Aishatul-humaira ko da masifar kishiya ba zan iya ba" kuka take sosai kamar ranta zai fita batun auren Major ya Girgizata ya zo mata hanyar da sam ba tai tunani ba. "Aure? Shi ne yace miki aure zai ƙara?" "Ai ya shige wai, domin Shureim da matarsa sun ɗora Invitation na ɗaurin a status ɗinsu, kuma matar Shureim ta tabbatar mini da hakan, Yanzu Abbin Salman ya kyauta mini kenan? Dame na ragesa tun ina amarya bai yi mini kishiya ba sai yanzu samu jika?" Tsaki Anuty Suwaiba taja kafin ta ce "Matsalata dake rashin tunani wani lokacin Na'ima, wace jikar waye kuma ya haifa miki, ai da baki gangancin riƙe Abra tun farko ba da Khamal bai isa ya rainaki har haka ba, Kin riƙe uwa yanzu zaki riƙe abin data haifa kamar baki san ciwon kanki ba wlh....," da sauri Mami ta ce "Look Anuty Suwaiba shawara na kira ki bani akan wannan mugun abin dake shirin faruwa dani, a baya nayi Kuskuren riƙe Abra da zuciya ɗaya, yanzu kuma nayi ladama riƙon da naiwa Abra ba shi zanwa Aishatul-humaira ba, da zuciya ɗaya zan riƙe ta, Ki bani shawara kawai idan zaki bani idan kuma ba zaki iya ba shikenan but please ki daina sako mini zancan Abra kina fama mini mikin dake zuciyata ne" "Ok haka kika ce? To kada ki sake kirana akan issues ɗinki tunda kina gani ba zan iya miki komai ba ki zauna kici miji tare da yaran riƙo" tana faɗin hakan ta kashe wayar. Abin duniya yaiwa Mami yawa sai kawai ta fashe da me tai maka mene yasa zai mata kishiya bayan yanzu basa samun saɓani. Sai da tayi kukanta ya isheta kafin ta tashi sbd kukan Aishatul-humaira da yaji. Yana kwance saman Royal bed ya rufe idanunsa tare da rungome pillow. A yanzu ko sarari tunani bashi da shi, ya daina surutai da kiran Abra. Amma ya tattara komai ya ajiye a cikin zuciyarsa. Ba zai taɓa yafewa kansa ba akan cutar da Abra dai ya yi, abubuwa da yai mata sai dawowa cikin ƙwaƙwalwarsa suke. Runste idanunsa yai sosai sbd tuna mganarta da yai. "Ka barni a jikinka ɗomin jikinka nake buƙata" ƙankame pillown yai yana jin kamar ya kurma ihu amma ba hali Allah sarki a lokacin ita kaɗai ta san me take ji a jikinta. A hankali aka turo ƙofar bedroom ɗin nasa, Hajiya Mama ce ta shigo riƙe da mug wanda ta haɗa masa coffee a ciki zama tai gefen gadon cikin sanyin murya ta ce. "Haba jarumin maza tun safe yau baka fito ba, are you okay?" Juyowa yai tare da mirginawa ya ɗora kansa a saman cinyar Hajiya Mama. "Mama ba zama Mutumin ƙwarai ba bani da imani Mama" rufe masa baki tai tana faɗin "Subuhanallahi kul ka sake jin irin haka a bakinka Adnan, Babu musulmin da babu imani a zuciyarsa, kai ta astagafirullah tare da neman yafiyar Ubangiji, akan laifukan daka aika ga Abra, Ubangiji mai jini kuma mai gani ne zai dubi zuciyarka ya sassauta maka abin da kake ji, ina da tabbacin Abra ta yafe maka, ko baka nemi yafiya wajanta ba?" "Na nema, amma na cutar da ita da yawa" shafa kansa Hajiya Mama tai cikin damuwa ta ce. "Shi ya sa a kullum nake ce maka ka rage zafin zuciya Adnan, babu inda zata kai ka sai ladama yanzu dame hakan yai kama? Kada ka manta A'isha Yaya ta ce, she's my sister mene yasa ban ɗauki mataki ba ni? Mene yasa Professor bai ɗauki mataki ba a matsayinsa na mijinta sai kai?" "Am sorry Mama nai laifi ki yafe mini" "Ka nemi yafiyar Ubangiji Adnan, shi ne zai yafe maka laifukan ka, and wannan zaman naka ya fara damuna kada ka samu matsala da zuciyarka" Tashi yai zaune sosai idanunsa akan Mama yace "Ina son komawa wajan aiki, idan ina zaune ni kaɗai bana iya cire tunani Angel a raina" "That's good ni ma hakan ya yi mini, yanzu ka sha wannan coffee ɗin kai wanka ka shirya ka fita ko lasvegas ne kasha iska" Girgiza kai kawai Adnan yai domin ya ɗauki Al'ƙawari duk abin da zai sanya shi farin ciki ba zai taɓa aikata shi ba, zai ta zama a haka har zuwa ƙarshen tasa rayuwar. Coffee ɗin ya fara sha a hankali Hajiya Mama na kallonsa cike da so da ƙaunar ɗan yayar ta ta A'isha. Har mamakin yadda Abra ta sakawa ƴarta suna Aishatul-humaira tai. Yana gama sha ta fita da mug ɗin shi kuma ya shiga bathroom. After 20 minutes. Walking slowly ya fito daga part ɗinsa cikin wata dakakkiyar shadda amy colour wacce ta amshi dark skin ɗinsa yai kyau sosai amma ya rame sosai idanunsa sun faɗa sai dugun hanci. Murmushi Hajiya Mama tai ta ce "Allahamdulillah, Masha Allah First born and last born sai yanzu naji daɗi shalalena" ta faɗa tana rungomesa marairaice mata fuska yai kamar ba zai magana ba sai kuma ya ce. "Ina Abba?" Juyawa tai sai kuma ta ce "Oh i almost frgt tafiyawta kama shi urgent he's alright left" "Mama me naiwa Abba ne haka? Idan zai tafiya duk sauri baya yi sai ya faɗa mini he has changed totally" "No, kasan Abbanka bai iya fushi ba, yana cikin damuwa da abin da ka aikata wannan shi ne kawai" shiru yai ganin yadda ya sauya yasa ta tallafo haɓarsa ta ce "What again? Laifinka ne, amma kada ka damu kaci gaba da addu'a kana tura masa saƙon apologies ta E-mail nasa yana son ka dole zai sakko" kai ya jinjina ba tare da ya ce komai ba yana ƙoƙarin fita ta ce. "Car key? Ina zaka bari na saka ai driving naka" idanunsa ya rufe a hankali ya ce "No Mama I can drive with myself ki mini addu'a" "To Allah ya tsare ya kai ka lafiya" da Amin Ya amsa tare da barin gidan. A hankali yake driving sbd rashin ƙarfin jiki yana hanya Fayyad ya kira shi amma ya kasa picking call ɗin har ya Ƙarasa police station ɗin kai tsaye Ɓangaren I.G ya nufa. Mutane sai zubewa suke suna gaida shi tare da faɗin "Wlcm Back sir" Duk wanda yai masa ta'aziyya ko ta kansa baya bi, a haka ya ƙara wani office. Cike da mamaki I.g ya miƙe tsaye yana sakin Murmushi na jin daɗin Sp Adnan Aliyu Matawalle zama sukai a hankali ya ce "Allahamdulillah, thank you sir" I.g ya ce "Good amma daka ƙara hutawa till now baka dawo daidai ba fa". "No bad, am okay sir" shiru duk sukai can I.g ya ce "ina tun wani case na ɗan mafiya ɗin nan wanda ake zarginsa da sace yara yana cire wani sashi na jikinsu?" Adnan ya jinjina kai alamar ya gane domin da case ɗin a hannunsa "Ana zargin mutumin yana ƙauyen Samil babu da tabbaci sai mun bincika,kasan ƙauyen babu hawaye musamman yanzu lokacin siyasa kada a cutar dasu sosai". "Yanzu waye za shi can ɗin?" Sp ya tambaya yana katse kiran da Fayyad ke sake yi masa. "Ina ci-gaba da bincikawa, Private investigator muke buƙata wanda zai komai cikin sirri ba tare da mutumin ya fahimta ba" shiru Sp yai can ya ce "Ok a bani case ɗin zani" I.g ya zare idanu yana faɗin "Rufa mini asiri, a ba aikin bane kai kake da ikon zaɓar wanda za shi ma, rashinka ya sa na tsaya a akan abun ba girman ka bane sam". "Ina son barin ƙasar ne daman, sabida na samu peace of mind amma zan bar komai naje ƙauyen da kai ne a can na samu nutsuwar zuciyar ka amince kawai, ba ruwana da girman aikin da nayi" I.g ya daɗe yana jinjina al'amarin, ta ya ya Sp da kansa zai je bincike? Amma kuma zuwan Sp ɗin shi ne daidai domin ya san me yake. "shikenan All the best yaushe zaka tafin?" Sp na Miƙewa tsaye ya ce "Gobe" Sallama sukai Sp Adnan Aliyu Matawalle ya koma gida yana zuwa ya samu Usman da Fayyad a can gidan suna zaman jiransa. Abbi na zaune hannunsa riƙe da Aishatul-humaira yana mata wasa, ta kafesa da fararen idanunsa duk idan yai da fuskarsa tana biye da ita dai na wasan zata saka kuka tana harba ƙafa, yana ci-gaba kuma zata kafesa da idanu wani lokacin har dariya take masa. Kamar daga sama yaga Mami ta faɗo cikin ɗakin nasa tana huci kamar zakayya. Kallonta kawai yake ba tare da ya ce komai ba. "Ni zaka ci amana kayi mini kishiya ba tare dana sani ba Khamal? Ban cancanci haka daga gareka ba, me na aikata maka har haka da zafi?" Kwantar da Aishatul-humaira yai yana gyara zama ya ce "Ba kiyi mini komai ba Na'ima, kawai naji ina son ƙara auren ne saboda Ubangiji ya bani dama kuma ya hure mini arziƙin da zan haka daga ɗaya har zuwa huɗu" cikin raunin murya Mami ta ce "Me na yi maka to? Ka rasa wacce zaka aura sai wannan Shegiyar karuwar? Wallahi idan ina gidan nan babu Shegiyar data isa ta shigo gidan nan a matsayin kishiyata, zan nuna mata asalin haka wallahi akan son ka sai na illata yarinya" Murmushi Abbi yai yana faɗin "Ashe? Ita karuwa ba mutum bace? And don Allah ki daina kiran matar da zan aura da karuwa kuma aure babu fashi duk abin da ki kai niyya Bisimillah ki aikata ban hanaki ba Na'ima, amma ki sani a wannan karan idanuna akan ki suke ba kamar baya ba, kuma baki isa kin yaudareni ba" zubewa tai a wajan tana sakin kuka ta ce "Wallahi Khamal ina son ka, ba zan iya jure ganinka da wata ƴa mace ba, kada ka hutani ta hanyar kishiya don Allah" "look Na'ima, idan hukuntaki zan yi da tuni nayi, aure ra'ayina ne ba sbd ke zan ba, don haka bana son wata fitina please" miƙewa tai idanunta cike da hawaye ta ce "Ok fine idan ba danni zakai ba, ai ka faɗa mini zakai aure na shirya? Ko yanzu ma ba kai ka faɗa mini ba a wajan ƴan uwanka na gani, zan bar maka gidan ka kawo Shegiyar karuwar taci gaba da zama a gidan" tana faɗin hakan ta saka hannu tare da ɗaukan Aishatul-humaira zata fita ya ce "Dawo ki Ajjiye mini Aishatul-humaira, Salima za taci gaba da kulawa da ita" cikin ɗaga murya ta ce "Wallahi babu tsinanniyyar da zan bawa Aishatul-humaira balle ta cutar mini da ita, kuma ni da Aishatul-humaira butu karaba" fuuuu tai waje tana zuwa ta ɗauki mayafi ta goya Aishatul-humaira tare da yin waje. Abdullah dake zaune saman Kujera idanunsa akan Ummi ya ce "Bana son ganinki cikin damuwa Ummi" Murmushi Ummi tai ta ce "Gajiyar azumin da nake ne Abdullah, ba damuwa nai ba, burina daman an rufe Companyn kuma an rufe Alhaji ya ce mini yana hanya, munyi waya da Shuwa itama ta ce tana hanya" Murmushi mai kyau Abdullah yai cikin nutsuwa da kamalarsa ya ce "Shikenan Ummi, kici gaba da kulawa bana son komai ya sameki" hararar wasa tai masa ta ce "Uhm sannu Audu, bayan kai na lura kana cikin damuwa amma u can't sharing with me" shafa kai kawai yai cike da kunya ba tare da ya ce komai ba. Ummi ta miƙe tana ɗaukan plate ɗin Apple ta ce "Ina son a turawa gidan marayun nan kuɗin da suka buƙata na taimako kamar 2.3m ne ko?" Abdullahi ya ce "Sure Ummi za a tura kije ki kwanta ki huta yanzu don Allah" dungure masa kai tayi ta ce "Wallahi ka nemo matar aure kafin na fita na nemaka da kai na tuzurun kawai" kunnensa ya riƙe da hannu bibbiyu ya ce "Afuwa Ummi am still searching" dry tai tana faɗin "Keep searching har network ya samu, wallahi ka kiyayeni Abdullah" ta faɗi hakan tana shigewa part ɗin ta. Fararen idanunsa ya rufe yana sauke numfashi ina zai ganta? Mene ya sa bashi da Sa'a a duk sanda zai ganta ne? Babu inda bai duba iya inda yake tunanin zai ganta a Dubai amma babu ita. A fili ya ce "Me ya sa kika tsaya mini arai ne?"... " 'Yar Baba mai sunan larabawa, kwanciyar ta isa haka, ki tashi ki je gangare ki karɓo mini gyaɗar nan" Wadda aka kira da 'yar Baba ta tura baki, ta ce "Ni wallahi ba ni da lafiya ki aiki Yaya Musa" "Ai na san baki da lafiyar, dan ki ji daɗin jikinki ne, kwanciyar ta isa haka" tana yamutsa fuska haka ta tashi daga kwanciyar, ta fita tsakar gida ta ɗebi ruwa a bokiti ta shiga wanka. Maimakon da ta fito daga banɗakin ta saka kaya, kawai sai ta bemi wuri ta kwanta tana kuka. "Wai ke meye haka ne? Wane irin sakarci ne haka?". Ƙara sautin kukan ta yi tana faɗin "Wayyo Allah Babana, Allah ya jiƙanka Baba" Matar ta ƙarasa gaban matashiyar yarinyar, ta shiga share mata hawayen fuskarta tana faɗin "Kiyi haƙuri 'yar Baba, muma duk zaman jiranta muke yi, kuma ba a yiwa mamaci kuka, ki daina addu'a zaki yi masa" da ƙyar ta rarrasheta ta yi shiru, ta saka kayanta, ta ɗauki wani ƙaton farantin silba, ta fice daga gidan. Sannu a hankali yake tuƙin, yana ratsa 'yar siriyar hanyar da ke tsakanin gonaki, sam hanyar ba ta da kyau, duk uban kwazazzabai, ga ƙura, yana yi yana duba kwatancen wurin a wayarsa. Kamar yadda aka tsara idan yaje garin, zsi sauka a gidan maigari ne, amma hanya na neman ta ƙwace masa. Tana tafe tana zancen zuci, da tunani daban daban a ranta, lokaci lokaci tana share hawaye da gefen ɗan ƙaramin mayafin da ta yafa a kafaɗarta, tayi tafiya mai nisa sosai sannan ta isa gidan da aka aiketa. Wani matashi ne ya washe korayen haƙoransa da ya ganota " 'yar Baba kin fi zinare, sarauniyar kyawawan garin nan, farin wata sha kallo, ke ɗaya kin fi duk matan karkarar nan, daga ina haka?". "Daga gidan ubanka" ta bashi amsa kai tsaye, tana watsa masa wani irin mugun kallo da idanuwanta da suka ƙanƙance suka yi jawur, saboda kuka. Buɗe baki yayi ya ce "Ni kike zagi?" "An zage ka ɗin, idan ka kuma shiga sabgata, ba zagi ba marinka zan yi, mutumin banza kawai". "Zaki gane kuskuren ki, zaki san ni kika zaga, ai mai goya miki baya kina iskanci a garin nan, ya mutu ba zamu ƙara ɗaga miki ƙafa ba". "In kun sake ɗaga mini ƙafa, Allah ya tsine muku" ta ƙarasa Maganar ta wuce shi ta shiga gidan da aka aiketa. Da an saba idan aka aiketa gidan, ai ta hira ana wasa ana dariya, amma ganin yadda ta shigo ranta a haɗe, ba wanda ta gaisar daga sallama sai miƙa farantin gyaɗa, ya sa ba wanda ya kulata suka bata saƙon gyaɗarta ta fito. Tafe take tana tunani, a kan abinda yafi komai ci mata tuwo a ƙwarya tsawon rayuwarta, ga rashin Babanta maganin kukanta. Wani uban ihu ta saki, ta faɗi ƙasa farantin gyaɗar ya faɗi, gyaɗar ta zube a wurin, ta sa hannayenta biyu ta ɗora a kanta. Sam ba ta san ta hawo hanya haka ba, saboda tunanin da take yi. Cikin tashin hankali Adnan ya fito daga motar, ganin babu abin da ya sameta amma ta ɗora hannun a kanta ta rintse ido, duk ta firgice ya sanya shi harzuƙa, ya kalli bayanta da ta juya, fari tas ga gashinta ta tufke amma ya fito ta ƙasan ɗankwalin ya kwanta a bayanta. "Mahaukaciyar ina ce ke, zaki hawo kan hanya haka ina miki horn, amma ki ka yi banza? Wace irin mara hankali ce ke?". "Kar ka sake ce mini mara hankali, kai ne mara hankalin ai, Yanzu da na mutu..... Kasa ƙarasa Maganar ta yi, ganin mutumin da yake tsae a kanta, sankacecen ingarman namiji, fuskarsa a ɗaure babu walwala, ko da idanunsu suka sarƙe a na juna, take ta ga ya sake ware idanuna a kanta. "A..Ab....Abra..My Angel you are still alive, dama na gaya musu ba ki mutu ba, dama nan ki ka taho ki ka ɓuya?" Zazzare ido ta shiga yi tana kallonsa, ita dai bata taɓa ganin sa ba, ko mai kama da shi a ƙauyen nan babu, ga kayan jikinsa masu kyau balle ta ce ko mahaukaci ne. "Abrana ki yi magana mana, Angel ashe baki mutu ba" ya ƙarasa Maganar tare da miƙa hannunsa zai ɗagota!!! Ki biya mu haƙƙinmu kan ki karanta, na kuɗi ne ₦300 kacal. 08081012143 [11/7, 6:36 PM] Abk: Ganin da tayi ya miƙo hannayensa gaba ɗaya zai ɗagota tsaye, ya sanya ta daddage ta ƙwala ihu "Wayyo Allah na shiga uku mahaukaci" tsayawa yayi sororo yana kallonta, ta tashi cikin hanzari ta suri farantin gyaɗar ba ta tsaya ta bia ta kan gyaɗar da ta watse ba, ta fyalla da gudu kamar ba zabgegiyar budurwa ba, binta Adnan ya yi yana kiran "Abra, dan Allah ki tsaya ki ji" sai dai kan kace Kobo, ta ɓace ɓat a cikin gonaki. Dawowa yayi, wurin da gyaɗar ta ta watse a ƙasa, ta bar mayafinta a wurin, ya durƙusa ya ɗauka yana jujjuya mayafin, take hawaye ya cika idonsa "Angel, Allah ya sa ba gizo kike mini ba, ko dai haukacewa na yi ne ban sani ba? Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ya daɗe a wurin a tsaye, sanan ya shiga motarsa ya ja ya cigaba da tafiya, ji yake tamkar an zare masa lakar jikinsa, ya rasa duk wani kuzarin sa. Ya samu ƙasan wata bishiyar tsamiya, yayi parking ya kifa kansa a kan sitiyarin motar, ya shiga duniyar ta sa ta tunani, da hasaso lokutan da suka shuɗe wanda ya kasance tare da Abra. Haka ya ɓata lokaci a wurin, yana ƙara rirriƙe mayafin yarinyar nan mai gyaɗa, yana son tabattar a zahiri Abra ya gani, ko mai kama da ita ce kawai, ko kuma dai duk gizo ne? Ganin ba shi da mai ba shi wannan amsar ne, ya sanya ya fito daga motar ya tambayi wasu samari, gidan maigari, suka kwatanta masa yayi musu godiya ya koma motarsa.   Tunani ya dinga yi ya aka yi bai tsaya ko sunanta ya sani ba, to ta yaya ma zai san sunanta yarinyar da ko tsayawa ba ta yi ba ta kwasa da gudu. "No my Angel can't run like this, sje might be her ghost, or am just hallucinating" ya yi maganar a fili yana taune leɓensa na ƙasa. Gaba ɗaya Hajiya Na'ima ta rasa me yake mata daɗi, duk ta birkice ta fita hayyacinta jin batun kishiyar nan, gashi Abbi ya sa ana ta gyaran gida, zai ƙara Aure, kuma duk wannan haukan da take, ko kallo ba ta ishe shi ba, balle ya bi ta kanta, sabgar Aurensa ce kawai a gabansa sai jikarsa Aishatul Humaira.   Na'ima na zaune a ɗakinta, tana rungume da Little Abra, sai dai gaba ɗaya hankalinta ba ya jikinta, she can't imagine sharing her husband with a prostitute. Sallamar Abbi a ɗakin ce ta dawo da ita hayyacinta, ba ta amsa masa ba, kuma ba ta kalli in da yake ba. Ya ƙaraso yana yiwa little murmushi, ya yin da ita kuma take ɗan murmusawa har dimples ɗinta suna lotsawa, haryanzu ba ta da wayo sosai, dan baka ba ta wani gane wasa, amma duk in da ta ga Abbi, tana yawan bin sa da idanunta, ko ma ta ɗan dinga yi masa murmushi. Abin har mamaki yake bawa Na'ima, dan Aishatul Humaira ba ta yi wayon gane wasa ba, amma tana gane Major. Ya miƙa hannu zai ɗau Little, amma Naima ta ƙanƙameta a jikinta tana watsa masa wani mugun kallo. "Ya haka? Ki bani yarinyata in gani". "Ba zan bayar ba, ka fita sabgata da ni da yarinyar nan, ka je ka yi rayuwarka mu yi ta mu". "Hmm ikon Allah, madam kenan, har kin manta jikar karuwa ce Humaira?". "Kar ka ƙara danganta mini 'ya da karuwa". "Ohh sorry, ai ba ni na fara faɗa ba, ke ce ki ke faɗa, ko har kin manta Abra 'ya ta ce da karuwa ta haifa mini?" Wata irin nadama da dana sani ne suka ziyarci Na'ima, ta tafka kuskuren da lokacin gyara ya ƙure mata. "Kinga gara in kawo kakarta, ta kula mini da ita yadda yakamata, kar ƙiyayyar da ki ka nunawa uwatta ya shafeta ita ma". "Ka ce mini ba zaka yi aure ne dan ka hukunta ni ba, amma wannan ƙananun maganganun da kake na menene?" Bai amsa mata ba, sai murmushi da ya yi. Ya kuma miƙa hannu zai ɗau Little. "Khamal ka ƙyaleni ka rabu da ni na gaya maka, idan duniya zata haɗu babu wanda ya isa ya rabani da jaririyar nan, kuma Wallahi ko ma wace tsinannaiyar zaka auro, babu ita ba Little, ka ƙyaleni ka rabu da ni". Major ya ce "Allah ya baki haƙuri, zaki tsorata yarinyar ta ki, dama na zo ne in tambayeki, part ɗin ki kike so, ko wancan da ake gyarawa?" "Ban sani ba, ida ka ga dama ka jani ka kai ni titi ka yar ka haɗa mini da saki, ka yi Aure ka sa a gidan". "Hmm Na'ima mai rikicin gangan, ai duk wani abu da za ayi, muna tare forver, duk da ɓata mini rai da ki ke yi, kina da wata kima da daraja a idanuna, shiyasa na ke tambayar ki abin da ki ke so, amma tin da ba kya so, shikenan" ya ƙarasa maganar tare da miƙewa ya fice. Yanzu da Abra tana nan, da wataƙila ita zata gayawa damuwar ta, ko ba komai ta tayata jin babu daɗi, amma Salman shi ba damuwa zai yi ba ko ta gaya masa, ga yadda suka ƙare da Anty Suwaiba, ta ƙanƙame Aisha ta fashe da kuka. Da gudu ta shiga cikin gidan, tana ta uban haki kamar ta yi dambe da kura, Yaya Musa da yake jan ruwa a rijiya ya kalleta ya ce "ke meye haka? Gudun me ki ke yi ne?". Da hanzari Inna ta fito daga wurin da suke girki, ta kalleta ta ce "meke faruwa haka? Ina gyaɗar?". Jifa ta yi da farantin gyaɗar ta nemi wuri ta zauna tana ta haki. Yaya Musa ya ce "Wai ma a haka ki ka fita aiken? Ina mayafinki?". "Dan Allah ka bari in dawo hayyacina" ta yi maganar tana haki. Sai da ta samu nutsuwa sannan ta fara ƙoƙarin tashi tsaye, Inna ta ce "Ina kuma zaki, ba ki mana bayanin mai ya faru ba? Ina aiken da na yi miki?". "Wai Inna ke ta gyaɗar ki ma ki ke yi ba ta ratuwata ba ko? Wani mahaukaci ne fa ya buge ni da mota, kuma ya fara kirana da wani suna yana ƙoƙarin rungumeni". Dafe ƙirji Inna ta yi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ban gane rungumeki ba, ya rungumekin ne ko kuwa?". "A'a, kan ya rungumenin ne na ɗau farantuna na gudo gida". "Ki gaya min gaskiya dan ubanki, mai ya yi miki?". "Be fa yi mini komai ba, ban bari ya taɓa ni ba". Yaya Musa ya ce "Wannan yarinyar wataƙila ma ƙarya take, wata maganar ta je ta ɗauko". Murguɗawa Yaya Musa ba ki ta yi, ta nufi ɗakinsu. "To ina gyaɗar? Ko baki karɓo ba?". "Ni fa wannan gyaɗar ta watse a hanya, kuma ban tsaye tsintowa ba, dan ban san me zai mini ba idan na tsaya". "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, shikenan yau asara ta hauni, gyaɗar duk ki ka watsar mini, kin kyauta". "Au Inna, in tsaya tsinto gyaɗa ya rungumeni ko? Kuma in dawo ki hau cajeni" "A'a ni bance ba, Allah ya mayar mini da alkhairi, amma dai kin gama da ni". "Allah sarki Baba, da yana nan da shi zai biyaki kuɗin gyaɗar nan, ki daina yi mini mita, amma yanzu ba mai biya mini sai mita ki ke yi, Allah ya jiƙan ka Baba" Inna ta ce "Ameen, amma ai dole in yi mita, tun da asara ki ka janyo mini" Inna ta ƙarasa maganar tana ɗagowa, sai dai tuni hawaye ya wankewa 'yar Baba fuska. "Wai ba zaki daina wannan koke koken haka ba? Kina tunanin kukan nan yana da amfani a gareki da kuma Baban ne? Ko shikenan idan kin yi laifi ba za ayi miki faɗa ba?" Cewar Yaya Musa da jikinsa ya yi san yi. "Yaya Musa, ba ina kuka ne saboda fa₦an Inna ba, in dai wannan faɗan ne ai na saba da shi, ina kuka ne saboda rashin Baba, da kuma yadda aka yi Baba ya rasa ransa. Ka san wacece ni, kuma ka san waye Baba a wurina, na so ace ya yi tsawon rai a duniya, dan in nuna masa gata. Ina fatan Allah ya bani damar da zan yi ilimi mai zurfi, yadda wani talaka kamar Baba, ba zai ƙara rasa ransa ba, saboda shi talaka ne ba. Wallahi ba zan taɓa yafewa waɗanda suka yi sakaci a kan rayuwarsa ba, na san lokacinsa ne ya yi, amma ya mutu a wulaƙance ba kulawa, Allah ya tsinewa wa...... "A'a A'a, kar ki kuskura in ji irin wannan mummunan furicin a bakin ki, ai ko baki faɗa ba, Allah ishashe ne, kuma ya ga abin da ya faru, shi baban na ki tunda ki ke da shi, kin taɓa jin ya tsinewa wani? To kar in kuma ji, maza je ki yi alwala ki ɗau carbi, ki ta masa addu'a". Abin duniya ya bi ya addabi zuciyar Bulama, ko wurin aiki ba ya iya zauwa, sai dai ya wuni a gida, kusan kullum cikin zarya yake tsakanin Asibitin da aka ce Adnan ya kwanta da kuma gidansa. Maƙwabcin Adnan ne ya nunawa Bulama gidan Adnan, da ya gaji da zaryar da yake masa, gidan Adnan ɗin ma idan yaje, sai mai gadi ya ce masa baya nan. Babban abin da ya ƙara ɗagawa Bulama hankali, bai wuce yadda aka ce masa yarinyar nan ta mutu ba, saboda zuciyarsa ta azalzalu da son ya ganta, ya gano ya aka yi ta zama 'yar sa, sai dai har duniya ta gushe, ba zai fasa ɗorawa kansa da Asibitinsa laifin da sa hannunsu a kisan Abra ba. "Yanzu kenan na bada gudunmawa wurin kashe 'yar da na haifa, idan ta tabatta 'ya ta ce?" Ya yi wa kansa wannan tambayar. Wasu hawaye ne da bai shirya zubarsu ba, suka gangaro a kan kuncinsa, bai taɓa aikata abin da ya zo ya dame shi ba, ya hana shi sukuni ba irin wannan. Shiryawa ya yi ya kuma ɗaukar mota, ya tafi gidan Adnan. Ya na zuwa ya tarar da maigadi suka gaisa, mai gadin ya ce "Wallahi ranka ya daɗe, yau ma baya nan, yama yi balaguro fa". Bulama ya ce "Bulaguro zuwa ina kenan?". "Wani aiki aka tura shi ƙauye, ka san jami'in tsaro ne". "Amm, ko zaka iya gaya mini cikakken sunansa?". "Wallahi ban sani ba, kawai dai Adnan na sani, amma ban san cikakken sunansa ba, da yake ban daɗe da fara yi masa gadi ba. Tun da dai matar nan ta sa ta rasu, gaba ɗaya ya zama sai a hankali". Bulama ya yi ajiyar zuciya, ya ce "Wane ƙauye aka tura shi aiki?" "Yo ni ina zan sani?". "Dan Allah idan ba damuwa, ka bani lambar wayarsa". Mai gadi ya ce "Babu damuwa, bari in baka" ya bawa Bulama lambar Adnan, ya yi masa sallama ya tafi. Ko da Adnan ya ƙarasa gidan maigari, aka yi masa iso, ya shiga suka gaisa, ya ce musu "Ni baƙo ne daga cikin garin Kano, ga takarda da aka bani na taho da ita zan yi wasu 'yan kwanaki a nan, kan in wuce". Mai gari ya nuna farin cikinsa da jin batun Adnan, suka karɓe shi hannu bibbiyu aka ba shi masauki, a wani gida, wanda galibi a nan suke saukar baƙin su, sai dai hankalin Adnan, sam ba ya kan aikin da aka turo shi, yana kan a ina zai sake ganin yarinyar nan? Ko kuma dai kamar yadda yayi tsammani, tsabar sanya Abra a ransa ne ya sanya ya ke ganin fuskarta na yi masa gizo a fuskar mutane?. Yayi alwala ya yi sallolin da suke kansa, bai nemi Abinci ba ya zauna ya cigaba da aikin na sa na tunani. Wayarsa ce ta fara ringing, ya duba wayar amma ya ga baƙuwar lamba, kawai sai ya share, ya cigaba da tunaninsa. Jin an cigaba da kiran ba ƙaƙƙautawa ne ya sanya, ya ɗau wayar zai sanya a silent, amma ya fasa ya ɗaga ya kai kunnensa tare da yin sallama. "Wa'alaikum salam, barka da yamma". "Yauwa wake magana?" Adnan ya faɗa cike da ƙosawa. "Doctor G.Y Bulama ne" Wani uban tsaki Adnan ya ja, "Me zan yi maka? Me ka kirani ka gaya mini?". Bulama ya kwantar da muryarsa ya ce "Dan Allah ka yi ka haƙuri ka tsaya mu fahimci juna". "Babu wata fahimta tsakani na da kai, ka jiraye ni zuwa lokacin da zan kai ka kotu, a kan kisan mata ta". "Kana da right ɗin da zaka yi haka, amma dan Allah ina son ka mini bayani yadda zan fahimta, ya aka yi yarinyar nan ta zama 'ya ta?". "Au mamaki ma ka ke yi? Bayan har gidanka na kai maka envelope da hotunan ta a ciki da wasiƙa watannin baya? Meyasa tun a lokacin ba ka yi ƙoƙarin neman 'yar ta ka ba, sai yanzu da ka kasheta?". "Adnan ka daina faɗan haka, ban kasheta ba, amma dan Allah ina son mu haɗu". "Mu haɗu ka yi mini me? Da fari ka kashe mahaifiyata shekaru Ashirin da uku da suka gabata, cike da zalunci ka sayar da jinin da za a sa mata, ka yi mata gurɓatacciyar allura, wadda ta yi ajalinta, katsam Allah ya haɗani da 'yar ka wadda ita kanta ba ta sanka ba, da yake Allah ba Azzalimin sarki ba ne, sai gashi irin halin da ka ke wa mutane na wasa da rayuwarsu, ka yiwa 'yar ka har ta rasa ranta. Haƙƙin rayukan mutane ba zai barka ba, kuma daga kan matata ba zaka ƙara wasa da lafiyar wani ba" Bulama zai yi magana, Adnan ya katse wayar, ya cillar da ita gefe, ya dafe kansa yana wani irin huci tare da haɗa gumi. Bulama ma ajiye wayar ya yi, ya dafe kansa yana tunanin, wace envelope aka kai masa? Shi ba wanda ya kai masa wata envelope. Ta da motarsa ya yi, ya ja ta a guje, ya nufi gida, yana parking ya fito, ya nufi wurin maigadi a sukwane. Ganin da mai gadi yayi Bulama ya nufo shi, ya sanya ya taso da sauri ya taho, tare da risinawa a gaban Bulama. Bulama ya kalleshi ya ce "Kwanakin baya, ko ma in ce watannin baya, an kawo wata envelope an ce a ajiye mini?". Mai gadi ya yi shiru, can ya ce "Tabbas Yallaɓai an yi haka, an kawo saƙo an ce a ajiye maka watannin baya". "Ina takaddar?". "Yallaɓai ban duba ba, ban san ko takadda ce a ciki ba, na kaiwa Hajiya ta karɓa ta ce zata ajiye maka". Jinjina kai ya yi ya tafi da sauri, Hajiya Saudat na ɗakinta, tana kwalliya a gaban mudubi, Bulama ya faɗa ɗakin ba bu ko sallama. "Doctor lafiya kuwa?". "Watannin baya an kawo saƙo a envelope, an bawa maigadi, shi kuma ya ce mini ya baki ki ajiye mini, ina saƙon?". "Wane saƙo kuma? Ni ba wani saƙo da ya bani". "Kar ki mini wasa da hankali, envelope aka kawo mini, da takadda a ciki da hotuna suna ina?". Gabanta ya yi mummunar faɗuwa, amma ta dake ta ce "Ni babu wata envelope da aka kawo mini, ka dai tambaye shi wanda ya bawa". "Shut up Saudat, Mutumin nan ba zai miki ƙarya ba, ki bani saƙon nan". "An ya ba ciwon damuwa ne ya kama ka ba, ya ke neman ya taɓa maka ƙwaƙwalwa ba?". "Ni ki ke gayawa ƙwaƙwalwata ta taɓu? Kin kyauta amma na fara tunanin wani abu, akwai abin da nake tunani, idan har ya tabbata zaki ga abin da ba ki tsammani ba". Ya juya fuuuu, ya tarar da Meenal a ƙofa a tsaye, jin hayaniya ya sanya ta fito, bai ko kalleta ba ya wuce yana huci. Meenal ta ƙarasa shiga ɗakin ta kalli Mummy ta ce "Mummy me ke faruwa ne? Wace takadda da hotuna Daddy ya ke magana a kai?". "Ke kar ki dameni dan Allah, koma ɗakinki" Ƙurawa Mummy Ido ta yi, ta ga gaba ɗaya gumi ya rufeta, alamun tsoro da rashin gaskiya suka bayyana ƙarara a fuskarta. "Mummy dan Allah ki gaya mini". "Get out from my sight, ki koma ɗakin ki na ce" ba shiri Meenal ta bar wurin, tana tunanin meke faruwa haka? Sintiri Hajiya Sauda ta shiga yi a ɗakin, tana jinjina kai tamkar ƙadangaruwa. "Kafin ka binciko komai, zan sake bunneka doctor, ba bu abin da zaka iya ganowa!' ta faɗa tana sauke ajiyar zuciya. Hajiya Mama ta kira Adnan a waya, ta ji ko ya sauka lafiya, suka taɓa hira, har ta tura masa hotunan Aishatul Humaira ta waya, kamar yadda Mami kan tura mata. Adnan ya ƙura mata izanu, ji yayi zuciyarsa na son ganin Aishatul Humaira, rabon da ya ganta tun tana kwalba, tun da aka tafi da ita bai sake zuwa ya ganta ba, wata irin soyayyar yarinyar ta mamaye zuciyarsa, musamman yadda kammaninta suka juue zuwa na Abra sak, wanda kyakykyawan hanci Bulama irinsa ne ɗoɗar a fuskar Aishatul Humaira. Nan ya barwa zuciyarsa cewar zai je Kano ya ga Little Abra. Kwanansa biyu a garin, ya je ofishin 'yan sanda na yankin, ya ga DPO, domin fara gabatar da aikin da ya kawo shi, daga nan kuma ya tafi Kano. Ba ƙaramin mamaki Mami ta yi ba da ganin Adnan, sam bai sanar da zuwansa ba, ita abin har mamaki yake bata, yadda ko ta waya baya neman ya 'yar ta sa take ciki, sai dai ta yi masa uzuri, kasancewar tun da Abra ta rasu, yake kwance ba lafiya, dan a yanzu ma ya rame da yawa, ya ƙara duhu sai idanu. Mami ta yi masa kyakywar tarba, tare da yi masa ya jiki. "Jiki da sauƙi Mami, ya Mamana?". Mami ta ce "Ai na ɗauka ka bar mini ita gaba ɗaya ne, baka sonta?" Adnan ya sunkuyar da kai ya ce "Mami ya za ayi in ce bana sonta, ina gujewa abin da zai sa in dinga tuna Abra ne kawai, yanzu haka ina cikin wani ƙauye a katsina, na tafi aiki, Mama ce ta turo mini hoton ta,naji lallai ina son in zo in ganta". Mami ta ce "Allah sarki, ai sai haƙuri mu cigaba da yi mata addu'a,bari in ɗauko maka ita". Ta shiga ɗaki ta ɗauko masa Little Abra, wadda ta ke ta bacci, ya ƙura mata idanu kamar zai cinyeta, tayi girma yanzu kamar ba wadda aka ciro a kwalba ba. Ya ɗagata yana cigaba da kallonta, amma sai lanƙwashe wuyanta ta ke tana tura baki, alamar bacci bai isheta ba. "Like Mother like daughter" ya furta yana tuna Abra, tuni idanunsa suka cika da hawaye. Mami ta ce "Ayi haƙuri dai, Ai mata Addu'a". Adnan ya jinjina kai sannan ya ce "Abbi ba ya gari ne?". Mami ta ɗan kwaɓe baki ta ce "Eh". "To, ga siyayya can na mata, kuma ina ganin tun da ta ƙara girma, ai mata hakika". Mami ta ce "Tun yaushe aka yi mata hakika, ai kana wannan rashin lafiyar aka mata komai, taron suna ne da bai yiwu ba, tunda ga abin da Allah ya saukar" Adnan ya ce "Haka ne, Allah Ya rayata ya jiƙan mamanta". Mami ta amsa da Ameen. Adnan ya kwaso uban kayan da ya sayowa Aishatul Humaira. Mami ta ce "Da ka yi shawara da ni ba zaka sayo wannan kayan ba, ta na da kaya da duk wani abun buƙata, da ga can ɓangaren ku sun kawo, nan ma duk an mata komai, madara kawai tana da gwangwani kusan Ashirin, diapers da komai duk akwai". "Lallai wannan 'ya 'yar gata ce, bakoma Mami ai alhakina ne nima na yi mata". Sai bayan azahar sannan Adnan ya yi haramar tafiya, kamar kar ya tafi, ji yake kamar ya ce a bashi 'yar sa ya tafi da ita. Ba yadda ya iya haka ya yi sallama, ya tafi, sai dai ko da ya wuce ta ƙofar sitting room ɗin da yake zama su yi hira da Abra, sai da gabansa ya faɗi, ya tuna yadda ta dinga nuna masa soyayya a wannan lokacin. Jiki a sanyaye haka ya baro gidan su Abra. Bai isa katsina ba sai dare, tun a hanya ya sai 'yan kayan da zai buƙata, da abin da zai ci ya kwana a wani Hotel, dan ba zai iya shiga wannan ƙauyen da daddare ba. Sai washegari da safe, sannan ya fara shirin tafiya ƙauyen. Har ya gama shiri, ya ga dacewar yakira Abba, ko ba zai amsa ba ya gaishe shi. Sai dai yadda Abban ya amsa gaisuwar ne, za ka tabattar da haryanzu Abba yana fushi da Adnan. A sanyaye ya shiga motarsa, ya cigaba da tafiya. Yaran garin kamar ba su taɓa ganin mota ba, da zarar Adnan ya yi parking ɗin mota, suke zuwa su kewaye motar suna kallo, saboda haka mai gari ya sa aka samo wuri na musamman da yake ajiye motar, gudun kar yaran su mata illa. Da yake har yanzu gajiya na damun Adnan, dan haka a ɗaki ya wuni, salla ce kawai take fito da shi. Bayan la'asar ya ga dacewar ya zazzaga garin, ya jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, ya ga ta ina zai fara bincikensa, kuma ko Allah zai sa ya sake ganin Abra. Sannu a hankali ya nausa cikin ƙauyen yana zagawa, sai ya ga wurin ya burgeshi, dan haka ya cigaba da kutsawa yana zagaye, har ya bar in da mutane suke. Tafiya ya yi sosai mai nisa, wurin ba kowa sai bishiyu da kukan tsuntsaye, ga manyan bishiyun fruit kala kala a wurin. Can ya hango wani tafki, ruwan ciki garai da shi, dan haka ya nufi wurin yana son ganin girman ruwan, sai ya tuna zamansu a Dubai, yadda Abra ke son ruwa, kuma tana tsoronsa. Kamar Aljana, haka zalika kamar a yadda ya ganta wancan lokacin, ta juya bayanta, ta zuba su a cikin ruwan, tana ta kaɗa ƙafafuwan ta a ciki. Da wata irin gaggawa, ya nufi in da take zaune. Jikinta ya bata a na tsaye a bayanta, ga kuma ƙamshin turaren da ba zata ta;a mantawa da shi ba ya daki hancinta. Ba tare da ta waigo ba, ta tashi da sauri, aikuwa gabanta ya faɗi da ta ga Adnan a tsaye kamar gini. Juyawa ta yi zata taka da gudu, dan ba ta gama yadda mutum ba ne, wannan mutum haka mai siffar shago. Yana gano nufinta ya danƙota, ya ja ta gefe, jikinta ne ya hau rawa "Ka ga dan Allah ka cika ni". "Abra, wai har yanzu ba ki gane ni ba? Na san loosing memory ki ka yi". "Allah ya sawwaƙe, kana nufin na haukace fa kenan, to Wallahi ni ba mahaukaciya ba ce". "Abra dan Allah ki saurareni" "Kai karka sake kirana da wannan sunan, wani suna kamar babur, kamar burabusko, ni ba sunana kenana ba, dan Allah ka cikani kar Inna ta gane Namiji yataɓa ni" "To ai ni mijinki ne Abra" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ko dai aljani ne ya aure ni ban sani ba?" Ƙara matso da ita jikinsa ya yi, yana ƙare mata kallo, duk da yamma ta ti sosai, Abransa ta fi wannan fari da ja, amma wannan ma fara ce tas, dan ba ta samu hutu bane, Abransa muryarta a hankali take yin ta, wannan kuwa muryar ta a tsaye take, cike da tsiwa da rashin kunya. Abra ta fi shagwaɓa a kan duk al'amuranta, wannan a tsaye take da ƙwarinta. Mutsu mutsun ƙwacewa take yi, tana ta kurma ihu. Adnan ya ce "Zan cika ki, amma muje in ga gidanku, zan magana da ke" Ta ce "To, na yadda". Adnan na cikata, kamar ya saki tattabara, ta watsa da gudu, ta nemi hanyar barin wurin. Littafin kuɗi ne, don biya ku tuntuɓe mu ta wannan lambar. 09047871750 [11/9, 11:32 AM] Abk: Ƙoƙarin kamo ta ya yi, amma yadda take gudu kamar mai fukafukai ya sa cikin sakanni ta ɓace wa ganin shi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da shafa sumar kansa, lallai wannan aikin da ya zo yi ba ƙaramin Alkhairi ya zamo a gare shi ba, bai taɓa tunanin zai ƙara yin farinciki a rayuwarsa ba, amma ganin wannan halittar mai kama da Abra da acting ɗinta ya fara saka shi cikin nishaɗi. Ya yarda Abransa ta tafi ta bar shi wannan ba ita ba ce, amma tsananin kamar da suke yi idan ba wanda ya yi wa Abra mugun sani ba idan ya ga wannan zai ce ita ce. Saboda yadda komai nasu yake iri ɗaya, ido, dogon hanci da dogon baƙin gashi, cikakkiyar gira da ɗan ƙaramin bakinsu gami da jerarrun fararen haƙora, hatta hannu da ƙafarsu duk iri ɗaya ne. Banbancin su kawai Abra ta taso a birni gidan hutu, ita kuma wannan yar ƙauye ce. Murmushi ya kuma yi a karo na biyu ya juya ya tafi don aiwatar da abin da ya kawo shi, zuciyarsa cike da addu'ar Allah ya sa ya kuma ganin ta a yau. "Wai don Allah ƴar Baba yaushe za ki yi hankali ne ki san kin girma? Sau nawa nake ce miki ki daina faɗo mana gida da gudu kamar wani filin ƙwallo" Zama ta yi tana haki tare da turo baki gaba ta ce. "Wai Inna ba ki san me ya faru ba za ki fara yi mini faɗa, ba ke ba ce kullum kike cewa kar in bari Namiji ya taɓa ni ba?" Inna ta ce. "Eh ni ce." "To wannan mutumin da na ce miki ya biyo ni jiya yau ma shi na ƙara gani a bakin teku, ya riƙe ni yana kira na da wani suna kamar babur, wai don Allah in daina gudun shi." Ido a waje Inna ta ce. "Wane shi? Me yake nema a gurin ki? Ɗan gidan waye a garin nan? Don ba zai yiyu ba sai mun je an kira iyayensa an yi wa tufkar hanci, akan me zai dinga taɓa ki?" "Kai Inna ya na ga duk kin tsora ta?" "A'a, kar na tsorata? Na san mugun nufin shi a kan ki?" "To Inna daga ganin shi ba ɗan garin nan ba ne, irin yan gayun nan ne yan birni, sai ma kin ji ƙamshin da yake mai daɗi." Ta ƙarashe maganar tana murmushi. Tsaki Inna ta yi ta ce. "Ko ma ɗan ina ne ba ruwana, bari Musa ya fito daga wanka mu je gidan mai gari". Ganin da gaske Inna take sai Ƴar Baba ta ce. "To ƙarya ma nake yi duk abin da na ce miki." A ƙufule Inna ta ɗauki mafirficin kaba za ta kwaɗa mata tana faɗin. "Ja'irar kashi, wato kin mayar da ni kakarki ko?" Kafin maficin ya sauka a jikinta ta kwasa da gudu ta yi ɗaki tana dariya. Musa da ya fito daga bayan gida a lokacin shi ma dariyar yake. Yana ajiye bokitin hannunsa ya ce. "Wani lokacin Inna kamar ba ki san halin ƴar Baba ba, ta zo ta zauna ta tsara miki zance na ƙarya, ke kuma ki hau kai ki ta banbanmi, sai kin gama ta ce ƙarya take." Inna ta ce. "Na daina yarda da ita ai, ja'ira kawai, Allah ya shirya mini ke." Ita kuwa tana shiga ɗakinta ta yi tsalle ta faɗa kan katifarta, haka kawai ta ji mutumin da take haɗuwa da shi ya tsaya mata a rai, ta rasa me ya sa kuma da Inna ta ce za ta kai ƙarar shi gurin mai gari ta yi saurin cewa ƙarya take, ita da take jiran ƙiris mutum ya yi mata abu ta kai shi ƙara. Tsaki ta ja a fili ta ce. "Ƙila ma aljani ne, ɗan baƙi kawai, bai san ma ni na fi son farin mutum ba, ta ƙarashe maganar tare da murguɗa baki. Tunowa ta yi wata ƙawar su ta haihu jiya, hakan ya sa ta miƙe ta fice daga ɗakin don zuwa ganin ɗa. "Inna zan je na ga jaririn Atine." Ta yi maganar tana saka takalmi. "Ki bari a yi Sallah mana, ko kuma gobe da safe kya je." Diddira ƙafa ta fara yi tare da faɗin. "Don Allah ki bar ni na je, duk su Lantana fa suna can tun ɗazu." "Allah ya tsare." Inna ta faɗa a takaice, don ta san idan ta hana ta ma zama zata yi ta cika musu kunne da ihu, don ba ƙaramin aikinta ba ne. Bayan Magriba Abbi ya sauka a Kano, direct gidan Ammi ya wuce, saboda ta kira shi akan tana son ganin shi. Bayan sun gaisa Ammi ta gyara zama ta ce. "Babana, ɗazu matarka ta kira ni tana ta kuka akan wannan auren da za ka ƙara, don Allah ka tausaya mata ko ɗaga bikin nan ne a yi mana, ka ga har yanzu tana cikin alhinin rashin Abra, wallahi tausayi take ba ni, duk ta bi ta ɗaga hankalinta." Cikin ladabi Abbi ya ce. "Ko shekara za a ƙara akan Auren nan idan aka tashi yi sai Nai'ma ta ƙara ɗaga hankalinta Ammi, kuma kin ga babu daɗi biki saura kwana biyar sannan a ce za a ɗaga saboda wani dalili mara ƙarfi, an riga an gama buga IV an raba, yarinya sun fitar da anko sun yi komai, sai a ɗauke mu ƙananun mutane." A sanyaye Ammi ta ce. "Shikenan, Allah ya tabbatar da Alkhairi ya ba ku zaman lafiya, Allah ya ba ka ikon yin adalci a tsakanin su." "Amin Ammi, bari na ƙarasa gida don sauka ta kenan na ce driver ya fara kawo ni nan, idan na je na yi wanka na huta zan je gidan Iman, ta dame ni akan za su yi Mother's day da sauran su." "Da ka rabu da su Babana, muna cikin alhinin mutuwar Granny da Abra babu wasu bidi'ebidi'e da za mu yi." "Na mata maganar hakan ni ma, amma ta ce mini ai ba kiɗa za a yi ba, kamar walima abin zai tashi, za a ci a sha ne kawai." Ammi ta ce. "Toh shikenan, Allah ya kai mu." Ya amsa da Amin tare da miƙewa ya yi mata sallama ya tafi. Sai kusan isha'i ta baro gidan Atine, tana tafe ita kaɗai cikin sauri ta ji ta yi karo da mutum. Cikin masifarta ta buɗe ba ki za ta yi magana amma maganar ta kakare, sakamakon ganin wanda ba ta yi zato ba. Adnan ne shi ma ya dawo daga inda ya je, hannunsa riƙe da torchlight yana haska hanya. Duk da ba ta kalli fuskarsa ba amma ƙamshinsa ya sanar mata shi ne. "Innahu Sulaimanu wa'innahu bismillahirrahmanirrahim." Ta faɗa tare da ja baya cikin tsoro da faɗuwar gaba, don zuwa yanzu ta fara tantamar anya ba aljani ba ne? Duk inda ta yi sai sun haɗu. "Angel!" Ya faɗa cikin murmurshi tare da haske fuskarta. Turo baki ta yi ta ce. "Wai kai a ina ka san ni ne? Don Allah ka daina bibiya ta, ni fa ban san ka ba ban taɓa ganin ka ba." "To ai yanzu kin san ni ko?" Ya yi maganar yana ƙoƙarin kamo hannunta." "Na shiga uku! Wai da wa Allah ya haɗa ni ne?" Ta yi maganar tare da tattare siket ɗinta ta manna da gudu. Da kallo ya bi ta har ta ɓace wa ganin shi, zuciyarsa cike da mamakin yadda ta ƙware a iya gudu haka. "Who is she?" Ya tambayi kan shi cikin rashin sani, yana son sanin wacece ita da gidan da take da tarihin rayuwarta, don kamar su da Abra ta fi ƙarfin a ce kama ce kawai, sai dai in da wata alaƙar, domin hatta muryar su iri ɗaya ce, yadda suke magana ne kawai ya banbanta. Kamar kodayaushe cikin gudu ta ƙarasa gida, tana tafe tana murguɗa baki da zancen Adnan a cikin ranta. Labarin na cin ta a rai amma ba ta faɗa wa Inna ba, saboda ɗazu ta riga ta ce mata ƙarya take. Nai'ma na zaune a main parlour ta yi tagumi abun duniya duk ya bi ishe ta Abbi ya yi sallama fuska babu walwala. Ba ta amsa masa ba sai ma haɗe rai da ta yi. Kallon yadda ta rame ta lalace ya yi, sai ya ji tausayin ta ya tsirga masa, takaicin ta na kiran Ammi da ta yi ya fara gushewa daga cikin ransa. Jakar hannunsa ya ajiye tare da zama a kusa da ita, cikin taushin murya ya kira sunanta. "Na'ima" "Kar ka ƙara kiran sunana, don bai dace da bakin macuci azzalumi mayaudari irin ka ba, wallahi Khamal ka ci amanata." Ta yi maganar cikin kuka. Ɗage kafaɗa ya yi ya ce. "Idan kina ganin wannan borin da botsarewar da kike ne zai saka na fasa aure to ki cigaba, amma ki sani idan kika kai ni bango duk abin da ya faru ki kuka da kan ki." "Ko me zai faru sai dai faru, ƙarkari ka ce ka sake ni ko? To ka sake ni ɗin sai me?" "Okay, maganar kayan faɗar kishiya, kuɗi kike so ko kaya?" "Ban sani ba, ba na son komai naka Khamal, idan ka ga ina yawo tsirara don Allah kar ka siya mini ko ƙyalle, ka bar ni in cigaba da yawo a haka." Girgiza kai kawai ya yi bai ce komai ba ya wuce part ɗinsa. Kuka ta fashe da shi mai tsananin gaske tare da ɗaukar pillows ɗin kujera tana cilli da su, ita kaɗai ta san me take ji a cikin ranta, ita kaɗai ta san zugi da raɗaɗin da zuciyarta take mata. Kamar wata mahaukaciya ta miƙe ta shiga ɗakinta da gudu ta ɗauki wayarta ta kira numbern Mama, bayan ta ɗaga ta fara magana cikin kuka. "Mama da gaske auren nan zai yi, don Allah ki faɗa mini mene ne mafita, na rasa madafa." A fusace Mama ta ce. "Taurin kanki ne ya yi yawa Na'ima, na faɗa miki ki ajiye wannan yarinyar ki baro masa gidansa amma kin ƙi." Kallon A'isha Humairah dake bacci ta yi, a raunane ta ce "Ba zan iya tafiya in bar ta ba Mam......" "Sai ki ta zama ciwon zuciya ya kama ki akan Namiji." Mama ta katse ta da faɗin haka tare da kashe wayarta. Tsugunnawa ta yi ta kifa kanta a jikin gado tare da toshe bakinta da hannunta, gudun kar ta tashi A'isha daga bacci, ta shiga rera kuka mai ban tausayi. Washegari ta tashi da zazzaɓi da matsanancin ciwon kai, da ƙyar ta iya tashi ta yi sallar asuba ta ba wa A'isha Humairah abincinta ta ci. Tana kwance Khamal ya shigo ɗakin, ko Kallon shi ba ta yi sai ma juya masa baya da ta yi daga kwancen da take, wasu hawaye masu ɗumi na zuba akan kuncinta. Bai kula ta ba shi ma ya ɗauki A'isha ya yi mata wasa tare da shishshilla ta, ita kuwa sai dariyar ƙuda take masa. 500k ya ajiye a kan madubi, yana duban Na'ima ya ce. "Ga kuɗi nan duk da kin ce ba kya so na ajiye miki, sannan gobe masu jere za su zo, idan akwai wani abun da kike buƙata bayan wannan sai ki sanar mini." Idan kuɗin da ya ajiye sun yi magana to Nai'ma ta tanka masa, ɗan murmushi ya yi ya kwantar da A'isha a gabanta, ba zato ta ji ya yi kissing forehead ɗinta tare da faɗin. "Sai na dawo uwargidan major Khamal Khamis." A zuciye ta ce. "Kar ma ka dawo, ka zauna a inda zaka je." Ta ƙarashe maganar tare da goge inda ya yi kissing ɗin." Tattausan murmushi ya sakar mata ya juya ya fita. "Ƴar Baba! Ƴar Baba." "Wai don Allah Inna ba za ki bar ni na yi baccin nan ba." Ƴar Baba ta faɗa tana tashi zaune. "Ko kasa ce ke sai kin tashi kin yi wanke-wanken can, don gidanku idan kin je gidanki haka za ki na kwanciya kina bacci ki bar gida da ƙazanta." "Gaskiya Inna kin daina so na yanzu, dama can Babana ne kaɗai yake so na, da yana raye babu mai tashi na daga bacci." Ta yi maganar cikin hawaye. Inna ba ta kuma magana ba ta fice daga ɗakin, tashi ta yi ta bi bayan ta ta kama wanke-wanken. Bayan ta gama ta share tsakar gida tare da wanke banɗaki. Inna ta ce. "To ko ke fa ƴar albarka, sannu da aiki, Allah ya saka da Alkhairi, yanzu sai ki wanke baki ki yi wanka ki zo ki ci abinci." "Ni dai ba zan yi wanka yanzu ba sai rana ta fito, safiya ce fa." Inna ta ce. "Kar ki yi ɗin, ke da ba a miki gwaninta, gwara ki koya tun yanzu, don watarana na asuba ma za ki yi ko na tsakar dare." Zunɓura baki ta yi ta ce. "Alkur'an ba zan yi wanka da tsakar dare ba, sai ka ce wata sabuwar aljana." Inna ta ce. "Idan lokacin ya zo kar ki yi, ki zo ki karya ni ki je ki karɓo mini gyaɗa, yau ma ki ƙara zubar mini da ita, ki ga yadda zan yi dake a gidan nan." "Allah Sarki Babana, Allah ya ji ƙan ka, saboda ba ka nan kullum sai an mini faɗa." Inna ba ta kula ta ba ta cigaba da sabgogin gabanta. Kamar yadda Abbi ya faɗa washegari ƴan uwan amarya suka zo suka yi jere a part ɗin da aka gyara, duk da ƙofar shigar shi ta cikin main parlour take amma ba su haɗu da Nai'ma ba, don ƙin fitowa ta yi daga ɗaki. Abinci ma sai Aunty Iman Abbi ya yiwa waya ta aiko aka kawo musu. Zaman kaɗaici ya ishi Nai'ma, ga shi tana ta kiran Salman a waya ba ta samun shi, hakan ya sa ta kira wasu cousins ɗinta guda biyu suka zo don taya ta zama. Ganin yadda ta tayar da hankalinta duk ta fige sai abun ya ba su mamaki. Ɗaya daga cikinsu mai suna Wasila ta ce. "Me zan gani haka? Cuta kika yi ne Na'ima? Ko duk alhinin yi miki kishiyar ne?" Maimakon ta ba ta amsa sai ta fashe da kuka, da ƙyar suka rarrashe ta ta yi shiru. Ɗayar mai suna Hajara ta ce. "Haba Aunty Na'ima, yanzu akan kishiyar kike haka? Ai idan ta zo ta tarar kina haka sai ta raina ki." "Mene ma ba zan yi ba, kun fi kowa sanin irin so da ƙaunar da nake wa mijina, amma ya ci amanata yake ƙoƙarin yin aure, me na rage shi da shi da bana masa?" "Haƙuri ake yi Aunty Nai'ma, abun da ciwo amma sai kin danne zuciyarki, idan kika yi haƙuri komai zai wuce." "Ba ni da wannan haƙurin kuma ba zan iya yi ba, wallahi ba don A'isha ba da tuni na bar masa gidansa, don ko ganin shi bana ƙaunar yi, ji nake kamar na cinna wa gidan wuta duk mu ƙune." Da sauri Wasila ta ce. "Subhanallahi! Me ya yi zafi shi ba wuta ba Na'ima? An sani kishiya babu daɗi, amma ya za mu yi sai haƙuri. Ki rage damuwar nan da kike, tunda mijinki yana son ki ni ban ga abun damuwa ba, domin na tabbata duk macen da Khamal zai so a bayan ki take. Yanzu ki tashi ki yi wanka mu je a yi miki wankin kai da ƙunshi da gyaran jiki, duk da lokaci ya ƙure amma ba za ki zauna haka ba, yadda Amarya za ta zo fess ke ma haka za a gan ki." Na'ima ta so ƙi amma suka tursasa mata, dole ta haƙura ta miƙe suka tafi ita da Wasila. Hajara kuma ta ɗauki kuɗin da Khamal ya ajiye ta tafi kasuwa ta yo sayayyar kayan sawa da takalma da jaka da mayafai masu kyau da tsada, wanda Nai'ma za ta yi fitar biki da su, daga kasuwa direct gurin tela ta biya ta ba shi kayan tare da cika masa kuɗi saboda ɗinkin urgently suke buƙatar shi. A daren yau ba su yi bacci ba sai da suka canza sabbin labulaye da Carpets part ɗin Nai'ma, suka sauya tsarin parlour'n da na kitchen, sai parts ɗin ya yi kyau ya haska shi ma. Wasila da Hajara Ya da ƙanwa ne, the same Mother the same Father, mahaifiyarsu ce k'anwar babansu Na'ima, suna da hankali su da sanin ya kamata, don shawarwarin da za su amfane ta suka dinga ba ta. A ɓangaren ta ita ma sosai ta ji daɗin zuwan su, sai ta ji dama tun saura sati ɗaya bikin ta kira su. Yau kwata-kwata Adnan ba su haɗu da ƴar Baba ba, hakan ya jefa shi cikin damuwa, ya dinga zagayawa a garin ko Allah zai saka ya gan ta amma bai gan ta ba. Washegari ta kama ranar Alhamis, ranar aka yi kamun amaryar Abbi kamar yadda aka tsara. An sha shagali sosai abin ya ƙayatar duk da ba a yi ƙida ba, manyan malamai mata aka kira suka yi wa'azi mai ratsa zuciya. Amarya ta sha pictures, dangin Abbi sukai ta ɗorawa a status, amma Nai'ma ba ta gani ba. Don ƙwace wayarta Wasila ta yi ta ce ba za ta ga abin da zai ɗaga mata hankali ba, don ta san halinta. Daren yau Na'ima ba ta iya runtsawa ba, kwana ta yi tana kuka tare da tunanin daga gobe Khamal ya zama nasu su biyu, za ta fara sharing ɗinsa da wata. Rana ba ta ƙarya, yau juma'a ranar ɗaurin Auren Abbi da amaryarsa Salima. Ba ƙaramin Dauriya Nai'ma ta yi ba ta shirya cikin wani tsadadden farin less mai adon red, bi sa takurawar su Wasila. Har gida Hajara ta kira wata mai make up ta zo ta yi mata. Duk da idonta a jeme yake saboda kuka amma ta yi kyau, sai dai ramar ta ta fito sosai. A'isha Humairah ma an mata kwalliya cikin sabbin kaya masu kyau white and red, tana rungume a jikin Nai'ma tana bacci bayan ta ci ta ƙoshi. Ƙawayen Nai'ma da wasu daga cikin danginta sun zo tun safe, don ita ma ranar za ta yi nata taron. A tsarin ta ba za ta yi taron komai ba, amma su Wasila suka dage sai an yi, don ƙin yin taron zai saka mutane su gane halin da take ciki na damuwa a kan auren, hakan zai saka kuma a yi mata dariya ne. Misalin ƙarfe goma sha biyu na rana suna zazzaune a bedroom ɗinta ita da su Aunty Suwaiba, ana ta dannar ƙirjinta, masu zuga ta akan ta yi hauka na yi, masu ba ta shawarwari na gari wanda za su amfane ta na yi. Ita dai duk ba fahimtar su take ba, don hankalinta gabaɗaya ba ya jikinta, yanda take jin zuciyarta kamar ta tashi tay ta zunduma ihu, ganin abun take tamkar a mafarki, wai yau ita za a yiwa kishiya? Ita da ta gama cika baki a cikin ƙawaye da dangi akan Khamal ba zai taɓa ƙara aure ba, amma ya watsa mata ƙasa a ido. A haka Abbi ya shigo ya same su cikin shirin shi na tafiya gurin ɗaurin Aure, ya fito tsaf a angon shi, ba za ka taɓa cewa ya ajiye ɗa kamar Salman ba. Bayan sun gaisa da mutanen ɗakin sai suka tashi suka fice don ba su guri. A hankali ta ɗago kanta dake sunkuye ta zuba masa ido, tunda ya shigo ta ji sallamar shi gami da ƙamshinsa da ya cika ɗakin ta sunkuyar da kanta, ya yi matuƙar yi mata kyau ba kaɗan ba, farar shaddar jikinsa ba ƙaramin haska shi ta yi ba. Shi ma kallon ta yake yi cikin wani irin yanayi hakan ya sa idanunsu suka sarƙe cikin na juna, ranar da ya fara ganin ta a rayuwarsa ya tuno, ya sani Nai'ma tana son shi ba kaɗan ba, shi ma kuma yana son ta, matsalar ta kawai zafin kishi. Ganin yadda ta rame sai ya ji tausayin ta mai ɗimbin yawa ya cika masa zuciya, a hankali ya taka ya ƙarasa ya tsugunna a gabanta tare da ɗora hannunsa a kan nata dake kan cikakkiyar sumar kan A'isha Humairah. "Wifey." Ya kira sunanta cikin wata irin murya. Duk yadda ta so daurewa kasawa ta yi ta fashe da kuka, cikin kukan ta ce. "Da gaske Khamal kishiya za ka yo mini? Ni ce fa Na'iman ka uwar Ƴaƴanka, me na yi maka ka zaɓi hukunta ni da abin da zuciyata ba za ta dauka ba, ka san ba zan juri ganin ka tare da wata ba. "Babu abin da kika mini Na'ima." Ya yi maganar yana ɗauke A'isha daga kan cinyarta ya kwantar da ita a gefe. Cikin ƙauna da kulawa ya rungume ta tare da faɗin. "I'm sorry, Ina son ki sosai matata, kuma duk wata mace da zan so a bayan ki take." Rarrashin ta ya yi sosai da daddaɗan kalamai har ya samu ta yi shiru, bai bar ɗakin ba sai da ya tabbatar ya sanyaya mata rai, ya yi musu pictures a wayarsa tare da A'isha Humairah, yana fita ta ƙara fashewa da kuka, a haka su Hajira suka dawo suka same ta. "Mene haka? Kukan na mene kuma? Sai kin ɓata kwalliyar? Haba Nai'ma sai ka ce wata yarinya, jama'a sun fara taruwa ke kuma kina nan kina kuka? Haka za a kawo amaryar kina wannan sakarcin? To wallahi idan ba kya danne kishin ki za ta samu lagon ki tana ƙunsa miki baƙin ciki, ki je ki yi tunda ke ba kya jin magana." "To ni Aunty Wasila ya kuke so in yi? Ko don ba ku san me nake ji ba ne a cikin raina?" Ganin yadda take kuka kamar za ta shiɗe sai suka shiga lallaɓa ta, har ta haƙura ta yi shiru ta shiga hada-hada da jama'a. Biki ya ƙayatar sosai, Nai'ma ta saki ranta ana ta hidima da ita, duk da ba ƙaramin dauriya take ba, don ji take tamkar ana rura mata garwashin wuta a cikin zuciyarta. Bayan Magriba aka kawo amarya, kafin ƙarfe tara kowa ya tafi, gidan ya rage daga Na'ima da Humairah sai amarya a part ɗinta, sai mai gadi da sauran masu aiki dake waje. Na'ima tana zaune tana ta trying numbern Salman amma ta ƙi tafiya Abbi ya shigo gidan. Part ɗinta ya zarce direct ya ajiye mata yoghurt da kazar ta, sannan ya sanar mata yana son ganin su a main parlour. Ba ta yi musu ba ta ce masa ga ta nan zuwa. Sai da ta kwantar da A'isha Humairah a cikin net ɗinta sannan ta yafa mayafi ta fita. Shigar ta parlour'n ya yi daidai da ɗago kai da amarya ta yi tana gyara mayafin jikinta. Turus Nai'ma ta ja ta tsaya cikin tsananin ƙaduwa da mamaki, lokaci ɗaya gabanta ya yi mummunar faɗuwa, sakamakon tozali da fuskar amaryar. Littafin kuɗi ne, don neman ƙarin bayani ku tuntuɓe mu a wannan lambar. 09047871750 [11/9, 8:06 PM] Abk: Da mamaki Na'ima ta din ga bin amaryar Abbi da kallo,dan abin da take gani ya saɓa zatonta, a tunaninta zata ga Salima, tsinanniyyar karuwar data maƙalewa mijinta Khamal Khamis. Matar data tsani jin ko sunanta balle kuma ta yi tozali da mummunar fuskarta wacce take ƙara harzuƙa Mami. Amma sai taga akasin haka dan kuwa wannan Salimar baƙa ce sannan yarinya ce ɗaya shakaf. Danne mamakinta ta yi tare da ƙarasowa ta nemi kujera can gefe da su ta zauna ba tare da tace musu komai ba. Gyara zama Abbi ya yi, yana ƙarewa matan nasa kallo cike da Soyayyar ko wacce a zuciyarsa,sai dai son wata ya rinjayi na wata. Sauke numfashi ya yi kafin yai gyaran murya yana kallonsu duka, a hankali ya fara magana yana ɗan satan kallon Na'ima da yaga ta sunkuyar da kanta tana kallon ƙasa,kwata-kwata taƙi kallon inda yake zaune bare kuma amarya tasa Salima. Nasiha ya yi musu sosai akan yadda zasu zauna da juna lafiya, su mutunta juna sannan ya juya ga Salima yana faɗin. "Salima ga yayarki nan, bana so ki ɗauke ta a matsayin kishiyarki ina so ki ɗauke ta a matsayin ƴar uwarki,wanda zaki iya tunkarar ta idan abu ya shige miki duhu, sannan ina so in sake jaddada miki ban aureki dan bana son Na'ima ba, ina son matata, bata taɓa nuna gazawa akan kulani da kuma iyalina ba, kada ki sawa ranki cewa don bana son matata na aureki ba, na aureki me sbd Ubangiji ya bani damar hakan. Allah ya ƙaddara ni acikin mutanen da zasu ƙara aure sannan su zauna da mata sama da ɗaya, saboda haka ina so ki girmamata ki mutunta ki bata girmanta a matsayinta na wacce take gaba da ke" Ita dai Na'ima har lokacin kanta a sunkuye yake tana yaƙi da hawayen dake son zubowa kan fuskarta amma taƙi bashi daman hakan, cikin kulawa Abbi ya juyo ga Na'ima ya ce. "Uwargida sarautar mata, Mrs Khamal ga ƙanwarki nan na kawo miki ita, please Na'ima bana so ki ɗauke ta less than a sister, ki gyara mata inda tayi kuskure ku taru ku bani farinciki, sannan bawai nayi aurennan bane dan kin gaza a wani guri ba,nayi aure ne dan Allah ya bani dama kuma ya hore mini arziƙin da zan zauna daga mace ɗaya har zuwa huɗu, saboda haka ina so ki karɓeta hannu bibbiyu ku zauna lafiya hakan zai sanya ni cikin farin ciki" Ƙala Na'ima bata ce ba, sai ma amarya Salima ce tayi gyaran murya tare da soma magana cikin kissa "Insha Allah zaka same mu masu maka biyayya, kuma daga yau wallahi na ɗauke ta kamar ƴar uwa kuma ina fatan nima zata ɗauke ni haka, Insha Allah babu abin da zaka samu daga garemu sai tarin farin ciki mara yankewa mijinmu" Murmushi kawai Abbi yayi kafin yace "Na gode"Sake kallon Na'ima yayi "Baki da abin faɗa ne uwargidan Khamal?" "Eh" kawai ta faɗa tare da miƙewa tana gyara mayafinta. "zan iya tafiya?" "Eh kije sai da safe" Bata jira komai ba tayi wucewarta ɗakinta, a hankali ta mayar da ƙofan ta rufe tana sauƙe ajiyar zuciya tare da bin ledojin da ya ajiye mata a bedside da kallo, ƙarasawa tayi ta buɗe, kaza ce guda uku sai fresh milk da sauran tarkacen su fruit da sauransu, tsaki tayi tare da sunkutar ledan ta fito falo, ganin Abbi shi kaɗai yasa ta ƙarasa ba tare da tace masa komai ba ta ajiye ledan akan table ɗin gabansa kafin ta juya zata bar wajen. "Na'ima" ya kira sunanta a hankali Daka tawa tayi da tafiyar da take ba tare da ta juyo ba, tana ƙoƙarin mai da hawayen idanunta. "Please ki kawo min Aishatul-humaira , i want to say goodnight" Juyowa tayi a fusace kamar za ta yi magana sai kuma ta fasa kallonsa kawai take hawaye na bin fuskarta, cikin sauri Abbi yace "Sorry Allah ya baki haƙuri, kije ki kwanta sai da safe we will meet in the morning, ki shafa min kan Aishatul-humaira bye" Daga haka ya miƙe ya nufi ɗakin Salima ba tare da ya sake cewa komai ba, ɗan juyowa ya yi yaga har lokacin tana tsaye ta ƙura masa idanu tana kallonsa ɗan murmushi Abbi yayi cikin tsokana yace. "Ko zaki rakani ɗakin amarya?" Kukan da take dannewa ne ya ƙwace mata kawai ta fashe da kuka tare da rugawa da gudu ta shige ɗakinta ta rufo ƙofar tana ci-gaba da kukanta. Murmushi kawai yayi kafin ya kakkashe komai ya wuce ɗakin amarya Salima. Washegari ma dai Na'ima ƙin tashi tayi bare tayi musu breakfast kamar yadda yawanci uwargida ce ke yi, sai ma Salimar ce tayi girkin, da tazo kiranta ma ko kallo bata ishe ta ba, cikin jin haushi Salima ta juya ta bar ɗakin tana faɗin "Mtsww cikin ki ko cikina kar ma ki ci mana" ita kaɗai tayi breakfast ɗinta kasancewar da ma Abbi baya fitowa da wuri, tana cikin karyawar Abbi ya fito kujera ya ja ya zauna yana murmushi tare da faɗin " Amarya bakya laifi" sunnar da kai tayi tana murmushi itama kafin ta miƙe tana tambayarsa mai zaici tayi serving ɗinsa, ganin Na'ima bata wajen ya sashi faɗin "Ina antyn taki kuma kike cin abinci ke kaɗai?" Cikin kissa da kisisina ta shiga faɗin "Wallahi nayi nayi ta zo muci abincin amma ko kallo ban isheta ba,kuma dama da naga ba tayi girkin ba na shiga kitchen nayi da kaina, shi ne naje part ɗin nata atleast tazo muci amma ban san ko mane yake damunta ba ko zaka kirata?" Miƙewa kawai Abbi yayi ba tare da ya karɓi plate ɗin soyayyen dankalin da take miƙa masa ba ya wuce ɗakin Na'ima A kwance ya sameta ta bawa ƙofan baya, jingina yayi da ƙofan kafin yace "Morning wifey" Bata juyo ba bare ya sa ran zata kula shi, "Me yasa kika ƙi fitowa muci abinci?" "Bana ra'ayi a ƙoshe nake"Ta faɗa ba tare da ta juyo ba. "Okay to, shikenan" ya faɗa tare da ƙarasawa ya ɗauki Aishatul-humaira dake ta wasan ta abin ta, zama yayi a gefen gadon yana mata wasa yana ɗan satan kallon Na'ima har dai ya gaji ya miƙe ya fice a ɗakin nata. Shima kaɗan yaci abincin kafin ya miƙe ya fice a gidan ma gaba ɗaya. Gidansu Ammi ya wuce ya gaishe su tare da sanar dasu dama yanaso ya koma bakin aikinsa cikin satinnan, babu wanda yace masa komai sai fatan alkhairi da suka masa tare da tambayar lafiyar su Na'imar. A kishingiɗe yake akan kujerun da ke gaban beach ɗin yana kallon yanda ruwa ke gudu akan surface ɗin, yana sanye cikin kayan shan iska guntun wando ne da ya wuce gwuiwarsa da kaɗan sai riga short sleeve, idanunsa da sunglasses sai cup na soft drink dake hannunsa. Faris kenan, wanda zuwa yanzu ya ƙara wani irin kyau da girma na ban mamaki, duk da har zuwa yanzu tunanin Abra ya kasa barin zuciya da gangar jikinsa, ya riga ya san ya rasa yayarsa har abada amma bai san me yasa ya kasa daina tunaninta ba. A hankali ya ajiye cup ɗin a gefensa yana ɗaukar wayarsa ta ke ta ruri tun ɗazun, ganin Mami ce mai kiran ya sashi saurin ɗagawa tare da yin sallama. Na'ima da har ta sadaƙar Faris bazai ɗauki wayar ba jin ya ɗauka ya sata fashewa da kuka. "Faris ina son ganinka urgently please ka dawo gida, akwai matsala ka dawo ina buƙatarka a kusa dani" Da sauri ya miƙe zaune hankali a tashe yake faɗin "Mami, lafiya?me ya faru?me aka yi miki sanar dani" Bata sake cewa komai ba sai ji yayi ta kashe wayar. Cikin sauri ya lalubo number Abbi, bugu ɗaya ana biyun ya ɗauka yana faɗin "Faris ya akayi? " "Me ya sami Mami?" "Da akayi me ?" "Yanzu ta kirani tace in dawo tana buƙatata kuma naji tana kuka me ya faru Abbi" "Kana jina Faris, kar ka damu da Maminka ta kasa daina tunanin Abra ne, maybe ta tuna ta ne shiyasa take kuka, ka kwantar da hankalinka, ka dage da karatunka duk da nasan bazaka iya dainawa ga baki ɗaya ba but please ka rage tunani more especially akan Abra kaji?" "Na ji Abbi but please you should be there for Mami, kaga yanzu bata da kowa bana nan yaya bata nan" "I will, karka damu" Daga haka suka yi sallama, ajiye wayar Faris yayi yana sauƙe numfashi, ya zai yi ya kasa hana kansa tunanin Abra, be couldnt stop himself but zai yi ƙoƙari yaga bai shafi studies ɗinsa ba insha Allah. Ƴar Baba na kwance a daɗi tai shiru idanunta rufe amma ta lula duniyar tunani, waye wannan ɗan gayon da yake ta damunta ne? Wace kuma Babur take kowa. Ko dai Aljani ne?. Da sauri ta girgiza kanta kafin a fili ta ce "Allah ya sauwaƙe na zama matarsa, ɗan Iska ne" da sauri ta ja iska tana shaƙar Ƙamshi ta ce "Kuma turarensa mai daɗi ne, amma baƙiƙƙirin dashi". "Wai Meke damunki ne ƴar baba? Ki yi ta kwanciya a ɗaki kamar ruwa, maza tashi kafin na dokeki" turo baki tayi cikin taɓara wacce ta zama ɗibi'arta ta ce. "Ni kam Inna idan kin tsaneni ne kawai ki faɗa mini na sani, bani da lafiya fa? Ba kiga na rame nai zuru-zuru ba, sai ki tayin mita da faɗa" Inna ta shiga tafa hannu sosai tana faɗin "Na shiga uku, yau naga abin da yafi ƙarfina,wai wacce irin yarinya ce ke ƴar baba? Ace ba zaki hankali ba kisan Annabi ya faku kalli sa'aninki fa duk suna ɗakin mazajansu amma ke jiya iyau" "Inna kina nufin nafi ƙarfi kenan? Gudana nawa nake gaba ɗaya da zanfi ƙarfin fisabilillahi" sai ta fashe da kuka tana kifa kanta a cinya. Zama Inna tayi tare da yin ƙasa da murya ta ce "Haba ƴar baba shallen Inna, ƴar gatan yayanta Musa, daina kukan kinji share hawayen ki saurare ni" "Ba dole nayi kuka ba Inna, tunda Baba ya rasu mitar yau daban ta gobe daban, daman shike so na" Inna ta kamata ta ce "Ba haka bane, ai ni uwa ce ba zan so ki lalace ko kuma ki sangarce a aikin banza ba, shi ya sa nake tsawatar dake amma babu abin da nake so sama dake" Ƴar Baba na dry sosai ta ce "Inna kinfi so na fiye da Yaya Musa ko?" Inna ta ɗaga kai ta ce "Sosai ma, ina ruwana da wani Musa, yanzu dai tashi ki shirya ki amso mini gyaɗa tun safe ake sallama a nema" turo baki tayi tace "Ke Inna wai babu wata sana'a sai gyaɗa ni banga wata riba a ciki ba" Inna ta riƙe haɓa ta ce "Oh! To aini na gani maza tashi tunda mun shirya idan ba mitar kike so ba, saura kije ki yi ta tsokana kina ja mana bada hqr ana zama lafiya" "Ni dai Inna ba zan kulaki ba, ki barni kawai da tunanin da nake shi kaɗai ya isheni" Inna ta ce "Meke damunki ƴar baba?" Shiru Ƴar baba tai tana mirginawa tare da juyawa Inna baya. Inna ta taɓe baki tai waje tana faɗin "Allah ya kyauta,ya shirya mini ke". Inna na fita ƴar Baba ta miƙe ta cire kaya tare da nufar banɗaki wanka tai, ta shirya cikin wata atamfa mai kyau, duk da cewa a ƙauye take amma bata zama cikin mummunar kama, Baba kafin ya rasu yana iya ƙoƙarinsa ganin ya kyautata mata, komai ya gani ƴar Baba haka Yaya Musa. Hakan yasa take da komai na buƙatun rayuwa kaf ƙawayenta ta fisu suttura mai kyau. Ƴar Baba na gyara zaman mayafin jikinta, ba wata kwalliyya a fuskarta dai kwalli da man leɓe hakan yasa fuskar tai sharr gwanin sha'awa, ga ɗan jikin nan nata ba auki wanda yake ƙara ɓoye shekarunta. "Allah ya a tsare, ki kula banda shirme banda....," Kafin Inna ta Ƙarasa Ƴar Baba ta ce "Banda tsona da kula samari, haka zaki ce ko? Ni fa duk na hadda ce wannan sai dai wani abun" girgiza kai kawai Inna tai. Ƴar Baba ta fita zuwa karɓar gyaɗa. A hankali take tafiya duk wanda ta gani sai ta murguɗa masa baki "Ƴar Baba an fito ne?" Cewar wani saurayi riƙe ƙugunta ta yi tana murguɗa baki ta ce "Wai kai sani mene matsalar ka dani ne? Ko baƙin ciki naka baban baya son ka?" Sani ya ware ido ya ce "Wai ni na isa na haɗa kai na dake ne? Ai ke ce sarauniyar ƙauyen nan kawai ki bani dama na nuna bajinta ta" tsaki tai ta ce "Allah ya sauwaƙe me zan dake, jibi ƙaton baki da ido ƴan mitsi mitsi ka fita a harkata wallahi" tana faɗin haka tai gaba Sani ya bita da idanu. A haka ta Ƙarasa gidan amsar gyaɗar mai maimakon ta amsa kamar yadda Inna taso sai ta nemi waje ta zauna suka kafa hira. Adnan na jingine a jikin wata bishiya ya harɗe hannayensa a ƙirji, yana sanye da wasu manyan kaya masu kyau, wanda suka haskaka baƙar fatarsa, fitowar sa kenan daga gidan da yake zaune sbd ya gaji da zama, honestly ma ba zai iya zama ba tare daya ƙara tozali da Yarinyar nan ma wacce yake jinta tamkar matarsa Abra. Lokacin guda so da ƙaunar Ƴar Baba ya gama ratsa zuciyarsa har yana jin babu abin da zai hana ya mayeta da gurbin murgayiya Abra Khamal Khamis. Ita ce zata goge masa tabon dake maƙale a zuciyarsa. Numfashi ya sauke yana duba agogon hannunsa ganin rana na shirin faɗuwa. Yana ƙoƙarin juyawa idanunsa ya sauka akan ta tana tafe farantin gyaɗa na kanta sai fari dake da idanun. Wani sanyayyan murmushi ya yi yana dubanta frm head to toe. Buwayi gagara misali. Al-hakkamu mai tsara komai a lokacin da ya so. Yana ganin identical twins masu tsananin kama da juna, amma bai taɓa ganin mutane masu kama da juna irin ƴar Baba da Abra ba. "Something fishy" ya faɗa cikin ransa. Ƴar Baba har ta shige ta gabansa bata lura da shi ba, kamar daga sama taji ya ce "Mai gyaɗa a bani gyaɗa" da sauri ta juya tana faɗin "Auzubillahi wayyo Allah Inna na shiga uku" ta faɗa tana dafe ƙirjinta da hannu ɗaya. Adnan ya ware manyan idanunsa waje cike da mmki yake binta da kallo ya ce "Kamar kinga aljani?" Murguɗa baki ta yi "Malam ɗan baƙi ka fita daga sabgata, Wlh kuma aniyyarka ta bika, idan kaci gaba da bina sai na kai ƙarar ka wajan Mai Gari" "Yanzu ko dai anjima, ko gobe?" Adnan ya tambaya "Kai baka jin tsoran Mai gari ne?" Ya watsa hannu ya ce "For what reason zan ji tsoron sa? Bayan ke ɗin matata ce ina nufin zaki zama matata kiyi ta haifa mini fitsararrun yara irinki" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un bata taɓa jin rashin kuka da batsa irin wannan ba, ita yake cewa zata haihu iskanci fa kenan? "Wallahi ni ba ƴar iska bace, Allah ya sauwaƙe na zama matar ɗan baƙi wallahi bari kaji ba zan taɓa son ka ba, daka ganinka mugu ne" Murmushi kawai ya yi yana faɗin "Kinga kuma ni ɗan iska ɗin ne, kuma dole na aureki" banza tai masa zata juya ya yi saurin kama hannunta ya ce "Wait don tsaya sbd darajar iyayenki" jin ya ce iyaye ya sa ta tsaya ta ce "Sake ni, shi ya sa kwana biyu Inna ke ta caje ni kamar wata ɓarauniya zama faɗi me kake son cewa" a hankali ya ce "Ya sunanki?" "Ƴar baba" ta bashi amsa a taƙaice ya Girgiza kai ya ce "Ƴar Baba isn't a real name, sunan gsky" fari ta yi ta ce "Ohhu maka ɗan anace natacce" juyawa ta yi zata tafi yai saurin riƙeta yana ƙwace farantin kanta tare da ajjiyewa gefe guda. "Babu inda zaki sai ki faɗa mini Wacece ke, su waye iyayenki ina gidanku yake.." a tsora ce tace "Na shiga uku Shikenan Inna ta samu abin mita ka cikani....," Jawota da Adnan ya yi zuwa jikinsa tare da rungometa sosai a ƙirjinsa shi ne yai saurin katse mata zan can da take yi.... [11/10, 8:23 PM] Abk: Ƙura mata ido ya yi, wanda ya saukar da wata irin kasala, taga Adnan ya yi mata wani irin kwarjini, bakinta ya mutu ɗif. "Ni ne mummuna ko?" Ta yi saurin girgiza masa kai, tare da sunkunyar da kanta ƙasa. "Kalleni" ya faɗa yana ƙura mata idanu. A hankali ta ɗago kai ta kalli Adnan, sam Adnan ba shi da muni, dan duk ƙauyen nan ba zata iya nuna wanda ya kai shi kyawu ba balle ya fishi, amma dakakkiyar muryarsa da yanayin jikinsa sai ta ke ganin kamar zai yi mugunta. "'yar uwakki sam ba ta da tsiwa, saliha ce, mai biyayya mai yasa halayenku suka sha banban?" "'Yar uwata kuma?" Ta yi maganar tana kallonsa. "Eh, wadda ki ka ji ina gaya miki sunanta" "Tana ina?" Adnan ya yi ajiyar zuciya ya ce "Mu je can wurin mu zauna in nuna miki hotonta". Haka nan 'yar Baba ta ji tana son ganin wadda ya ce "yar uwatta ce, dan ya soso mata abin da yake mata ƙaiƙayi a rai. Suka nufi kan wani dakali suka zauna. "Kafin in nuna miki, sai kin gaya mini sunan ki, da gidanku". " 'Yar Baba" ta bashi amsa"'. " 'yar Baba ai ba suna ba ne" "Afra" "Afra ko Abra". "Malam ni Afra nace maka" ta faɗa cikin tsiwa. "Waye ya sa miki sunan 'yan gayu haka?" "Wani ɗan sanda ne" ta bashi amsa. "Ɗan sanda kuma? Ya aka yi ɗan sanda ya sa miki suna? Shi ne mahaifinki?" "A'a cewa aka yi wai Baba tsinto ni ya yi" ta faɗa cikin rauni, idanunta na tara hawaye. Ras gaban Adnan ya faɗi, idan kuwa haka ne ya tabatta Afra da Abra suna da alaƙa, duk yaran Bulama ne. Ya zira hannunsa a aljihunsa, ya ciro wayarsa, ya lalubo hotunan Abra ya miƙa mata. Da sauri ta sa hannu ta karɓa, jikinta na rawa ta ƙurawa wayar idanu, cikin rawar murya ta ce "Kai, wannan ai nice". "Matsa can, matata ta fiki kyau, ke ba 'yar gayu ba ce ai". "Dan Allah da gaske 'yar uwata ce? Tana ina? Dan girman Allah a ina take?". Adnan ya karɓe wayarsa ya ce "Sai munje kin nuna mini gidanku tukuna" Da sauri ta tashi, ta ɗau farantin gyaɗar ta, ta ce "Tashi muje to ka gani" Adnan ya miƙe ya bita, suna tafe tana share hawaye. "To kuma kukan me ki ke yi?" Kasa magana ta yi, sai sake fashewa da kuka, alamar akwai wani abu da yake damunta a zuciyarta. "Bana son kuka, idan ba ki daina kukan nan ba, ba zan kai ki wurinta ba" ta saka hannu ta goge hawayen fuskarta ta ce "Na daina, dan Allah ka yi haƙuri" "Kin san wani Sadi a garin nan?" Zaro idanuwa ta yi ta ce "Kai wannan ɗan daban, me zai haɗani da shi?, na san shi". "Ya akai kika san shine, sannan A ina yake?". "Shikaɗai ne Sadi, ana ce masa ɗan kunama, Gidansa a garin nan, yana da mata da 'ya'ya, amma fa sai ya shekara biyar baya garin nan, bama a sanin ya zo balle a san ya tafi, 'yan sanda sun sha zuwa su kama shi, amma ba a samunsa". A hankali Adnan ya furta "Sadi ɗan kunama" Ta kalli bakinsa ta ce "Me kace?" "Ba komai, watarana zaki nuna mini gidansa". "Na shiga uku ni kaza, Wallahi ba zani ba, gaba ɗaya layin gidan nan mafarauta ne, karnuka ne sun fi Ashirin a layin nan, wallahi ba zani ba" "Ashe ba ki shirya ganin 'yar uwar ta ki ba". "A'a dan Allah kar ka yi mini haka, Wallahi ina son ganinta, kuma har babanmu da Babarmu duk zaka nuna mini? Dan Allah ba yaudarata ka ke ba 'yar uwata ce? Ya aka yi ka san 'yar uwata ce? An sha yi mini gori a garin nan wai ba'a san iyayena ba, Baba ne ya tsinto ni, shi yake mini komai, rashin lafiya ta kama shi, aka tura shi wani Asibiti a Kaduna, wasu azzalumai suka bar shi ya mutu" tuni hawaye ya gama wanke mata fuska. Wani irin tausayin yarinyar ya kama shi, ya tuna lokacin da Abra ke masa magiya a kan ya haɗata da mahaifinta, Allah sarki a wannan karon ba zai iya sanar da Afra wane irin uba ne da su ba. Abin da yake birge shi da ita shi ne, ba ta da rufi, yanzun nan zaka ji abubuwa da dama a bakinta, a yanzu haka ya samu abokiyar gabatar da aikin da ya zo yi garin. "Matata ki daina kuka, bana son sake ganin hawayenki dan Allah, ina son in goge laifin da na aikata miki a baya". "Matarka? Wane laifi ka yi mata? Ba 'yar uwar tawa ka ke aure ba amma ka ke kirana da matarka?" Sai da ta yi Magana sannan Adnan ya dawo hayyacinsa ya ce "Ai Yanzu tun da muna tare a nan kece matar tawa". "Allah ya kiyaye, ji mayaudari". Adnan ya haɗe rai ya ce "Ni kike cewa mayaudari?" "A'a yi haƙuri dan Allah, ga gidan namu munzo, bari in shiga in gaya wa Inna ita ma ka nuna mata hoton, sai ma ka gaya mata ka san iyayena". Adnan ya yi murmushi ya ce "To shikenan, maza shiga ki gaya mata". Da hanzari kamar zata kifa, ta dafe farantin gyaɗarta, ta shiga cikin gidan tun daga soro tana kiran Inna. Adnan ya ƙarewa gidan da Afra take ido, gidan ƙasa ne, ginin ƙauye ya jinjina kai ya ce "Afra, Allah ne ya so ni da rahama domin in gyara laifukana, ya haɗani da 'yar uwar Abra". "Inna! Inna fito fito" A gigice Inna ta fito daga banɗaki, ta yi jifa da butar hannunta, tana nema ta dungura, saboda yadda ta ji 'yar Baba na kwaɗa mata kira. "Ke lafiya?". Ta ƙaraso ta riƙe hannun Inna ta ce "Inna Allah ya karɓi Addu'a ta". "Wace Addu'ar?". "Inna na haɗu da wanda ya san iyayena, har ya nuna mini hotunan 'yar uwata, Wallahi Inna komai namu iri ɗaya". A fusace Inna ta ce "Matsa ki bani wuri mahaukaciya, kawai kin zo kina ɗaga mini hankali". "Wallahi Inna da gaske nake, ki zo muje yana ƙofar gida ki ganshi". Ta dinga jan hannun Inna zuwa ƙofar gida, sai dai suna zuwa Adnan ya tafi. Ai kuwa Inna ta mangarewa 'yar Baba ƙeya. "Dan ubanki kawai kin ɗaga mini hankali, kin zo kina mini hauka, ni anya ma ba da gaske aljanu ne suka shafeki ba, yarinya sam ba kya Hankali, tsugunno zan yi amma ki ka saka na fito a guje, na ɗauka wani abu ne ya sameki, ja'ira mara hankali". Jiki a sanyaye Afra ta ƙarasa shiga cikin gida, ita ma ta fara tunanin anya ba da gaske aljanu ne suke mata wasa da hankali ba?. Yaya Musa ne ya shigo gidan, yana faɗin "Inna ke da wa ki ke ta wannan faɗan?". "Ni da wannan yarinyar mana, ta shigo tana ƙwala mini kira, wai wani in zo wai ga wani mutum ya san 'yar uwatta. Ranar lahadi mai zuwa, dan ubanta gidan na rimi zan kai ta ya yi mata ruƙiyya". 'yar Baba ta zare ido ta ce "Kai, dukan mutane fa yake yi, ni wallahi bani da aljanu". "Aikuwa sai na kai ki, idan ma iskanci ne abin naki, ya zane mini ke". Mami ce zaune tana waya da Hajiya Mama, suna hirar yadda Little ta yi wayo, Mama ta ce "Ai insha Allah cikin satin nan muke sa ran zuwa, mu zo mu ganta". "Allah sarki, ubangiji Allah ya kawo ku, Allah yasa kar ta yi muku ƙyuwa, dan ta fara gane mutane yanzu". "Ai ni idan ta mini ƙyuya, ba ta yiwa maigidan na ta ba" suka yi dariya gaba ɗaya. Mama ta ce "Ya Major, da ɗana Salman?" "Salman kwana biyu bai leƙo mu ba, yana can makaranta, Major kuma ya yi Aure". "Subhanallah Aure kuma Hajiya Na'ima?". "Aure fa, yau kwana takwas". Hajiya Mama ta ce "Eyya, wannan abu bai yi daɗi ba, amma dan Allah ki yi haƙuri ki kwantar da hankalinki, komai nufi ne na Allah. Allah ya baku zaman lafiya kiyi haƙuri" wata irin karaya ta kama Hajiya Na'ima, dan a kwanaki takwas ɗin ita kaɗai ta san da yadda ta yi su, gashi yau Major zai dawo wurinta, amma sam ko ɗokin hakan ba ta yi, saboda gaba ɗaya haushinsa ta ke ji. "Ya na ji kin yi shiru?" Cikin raunin murya Mami ta ce "Ba komai". "Na'ima, na san na fiki shekaru, kuma nima mace ce, ƙarewa am a Marriage counsellor, na san abin da ki ke ji, irin wannan babu daɗi, kinga sanadin 'ya'ya Allah ya riga ya haɗa mu, mun zama 'yan uwa, dan Allah idan zan baki shawara, kar ki yadda wani ko wata su ziga ki, a 'yar haɗuwar da muke yi, mijinki yana nuna miki soyayya, kiyi amfani da damarki kar ki ce zaki bar mata shi ki zuba musu ido, kiyi ƙoƙari ki riƙe fadarki a wurinsa, na san da ciwo amma ki yi haƙuri". Mami ta yi ajiyar zuciya ta ce "To shikenan, na gode sosai". "Yauwa, sauran maganar idan na zo ma tattauna". "To shikenan Allah ya kawo ku lafiya, gaida Abban". Hajiya Mama ta ce "Zaiji insha Allah". Mami ta mayar da kallonta kan Little, da ta ƙura mata ido, Mami ta yi murmushi, ta janyo little tana shafa mata hoda a goshinta, daga ita sai Pampers. Mami ta ce "Sweetheart, bari in miki video in turawa Daddynki Salman, na san yanzu suna lectures da mun yi video call ko?" Ta yi maganar kamar Little tana jin me take faɗa. Ta ɗauko Comb ta shiga tajewa Little uwar sumar da ta cika mata kai. Ta ƙurawa Little ido, yarinyar tubarkallah, Allah ya yi mata kyau, ko sallama aka yi, Mami ɓoyeta take yi, ko yawan da ita ba ta yi, saboda baki. Ganin Mami ta ƙura mata idanu ne ya sanya, ta fara dariya har dimples ɗinta suna lotsawa, sak kammaninta da Abra suka ƙara bayyana. "Allah sarki Abrana, Allah ya yi miki rahama, ya raya mini abin da ki ka bari, ke babu ke, Faris ba ya kusa da ni, ga abin da babanku yayi mini, da muna tare da na san zaki tayani jin babu daɗin halin da nake ciki. Ina ma ban raba alaƙar da ke tsakanin ki da Faris ba, dama na bari kun yi Aure, kai na yi kuskuren da babu damar gyarawa" ta ƙarasa maganar tana hawaye. Sai da tayi mai isarta, sannan ta tashi, ta ɗau ado cikin wani rantsatsen leshi, ta sha ado sai zuba ƙamshi take yi, ta shirya Little cikin wasu haɗaɗɗun kaya sannan ta ɗauko wayarta ta kira Salman video call. Murmushi ne ya bayyana a fuskar Salman, ganin kiran Mami, ya amsa kiran, murmushin fuskarsa ne ya ƙara faɗaɗa da ya yi tozali da fuskar Mami tare da little. "Wow my little Angel, always looking so cute dear" Dariya little ta buɗe baki ta na yi, tana miƙa hannunta kan screen ɗin wayar. Kissing ɗin screen ɗin system ɗinsa Salman ya shiga yi, yana ɗagawa Little hannu. "To mai 'ya, ko ta ni baka yi, sai 'yar ka ko?". "Am sorry Mami, gaskiya am missing daughter Mami, ba kiga kamannin angel sun sake bayyana a jikin yarinyar nan ba, Mami ba zan zo in tafi da 'yata ba kuwa?" "Say hi Daddy, My Angel look up, baki kamar na mamanta" yayi Maganar yana murmushi. Idonsa ne ya kai kan Mami, da idanunta suka cika da hawaye. "Mamina, lafiya na ga idanunki kamar za ki yi kuka?". "Salman na kiraka a waya, nace ina son ka zo da gaggawa amma ka yi burus ko Faris?". "Mami ba burus na yi ba, muna daf da fara exams ne, kuma Abbi ne ya ce kar in zo". "Ai tunda ya san abin da yayi mini, dole ya faɗi haka?". "Mami me ya yi miki kuma?". "Aure ya ƙaro, yau kwana takwas kenan, ya auro budurwa". "Aure kuma Mami? Abbin?". "Zan maka ƙarya ne Salman?" Salman ya girgiza kai ya ce "Mami, na san Abbi ba zai taɓa yin abin da zai cutar da ke ba, dan Allah kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki, kwanakin nan damuwa ta miki yawa, dan Allah kar ki bari wani ciwon ya kama mini ke Mami, dan Allah ki cire komai daga ranki" Mami ta yi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, Allah ya bada sa'ar exams". "Ameen Mamina, kiyi haƙuri dan Allah, kar ki ji haushin Abbi" Murmushi ta yi mai ciwo ta katse kiran. Ta miƙe tsaye, ta ɗauki Little ta saɓata a kafaɗarta, ta fito falo. Tana fita falon ya gauraye da ƙamshi, hakan ya yi daidai da fitowar Abbi, tare da Salima. Bin Mami da ido ta yi, ba ƙarya Mami akwai iya gayu. Major ya yi mata wani lallausan murmushi ya ce "Wurinki zan taho ai, na zaci baku tashi ba". "Ni na tashi tun ɗazu" tai maganar tana nufar hanyar kitchen. Salima ta ce "Honey dan Allah ko sau ɗaya a bani Little in ɗauka mana, tun da na zo gidan nan ban taɓa ɗaukarta ba". Major ya ce "My dear, a taimaka a bamu aron Little mu ɗauka mana". "Duk abin da ya shafeka ban mata iyaka da shi ba, amma abin da ya shafeni da iyalina ni ya shafa, dan haka babu ruwanta da iyalina". "Na'ima meye haka ne? Wannan wace irin magana ce kike yi?" "Sai kuma kayi ai" ta wuce kitchen abinta. Ƙarfe goma da rabi na safe, Adnan ya tafi hanyar wucewarta ya zauna, ya shafe a ƙalla awa ɗaya da rabi, sannan ya hangota, tana tahowa, yau buhu ne ta maƙalo hammatarta, tana tafe tana murmushe gyaɗa tana ci. Tana tunkaro wurin taji ƙirjinta ya tsananta bugawa, ga kuma ƙamshin turaren sa da ya cika mata hanci, ji tayi kamar ta juya ta gudu gida, karta kuma haɗuwa da mutumin nan da ba ta da tabbacin mutum ne ko aljani. "Budurwar ƙauye, ƙaraso mana kina tafe kina ciye ciye, ko kunya ba kya ji?" Tsayawa ta yi cak tana kallonsa. "Idan kika gudu ba zan kai ki wurin 'yar uwakki ba". Ta yatsine baki ta ce "Ai na fuskanci raina mini hankali kake, yaudarata kawai ka ke, jiyan in shiga gida in fito da Inna ka gudu, ka sa ta dinga yi mini faɗa, har da zata kaini wurin masu ruƙiya aljani ya shiga jikina". Dariya Adnan ya yi ya ce "kin manta yadda ki ka dinga wahalar da ni ne nima? Ai ramawa nake yi, yanzu ina zuwa?". "Gona zani" "Me zakiyi a gona kuma?" "Roro zani". "Kinga, yanzu muje ki fara rakani gidan Sadi". Waro masa manyan idanunta ta yi "Taɓ kawai aje a gaya wa Inna an gani a layin gidan, duk fa 'yan farauta ne a wurin masu shaye-shaye". "Na dai ga alamar ba kya son in nuna miki in da iyayenki suke". "Wai kai sai ka yi ta amfani da wannan damar kana tursasani, yanzu aiken Innan zan fasa muje naka?" "Hukunci ya rage naki ai". Ta ɗan tura baki sannan ta ce "Naji zan raka ka, amma da sharaɗi, nima zaka rakani gona ka tayani roro" Shiru Adnan ya yi, sannan ya ce "Na amince" "To muje, kuma daga baya zan tsaya in nuno maka gidan in dawo, dan karnuka ba zasu cinye ni a banza ba" Nan ta yiwa Adnan jagora, suka nufi hanyar gidan Sadi ɗan kunama, wato baban yaron riƙaƙƙen ɗan ta'addan da ya addabi ƙasa tsawon shekaru. Cin gyaɗarta ta cigaba da yi, Adnan ya fizge ledar gyaɗar ya jefar ya ce "Ke kamar ba mace ba, ko kunyar ciye ciye ba kya ji?". "Kaga nifa ba zaka takurawa rayuwata ba gaskiya, kai Wallahi da gani mutum ne mai son kai, wannan 'yar uwa tawa da gani tana haƙuri, ka fiye masifar tsiya Wallahi". Jikin Adnan ya yi sanyi da jin abin da Afra ta faɗa, sai ya kasa ce mata komai sai cigaba da bin ta da ya yi. Sai da suka zo daidai wata ƙatuwar bishiyar tsamiya, ta ja ta tsaya ta kalleshi ta ce "Kaga hanyar can, da wancan karen me baƙin baki yake kwance? To duk wanda ka tambaya zai nuna maka gidansa". "Muje ki nuna mini mana". "Ai Wallahi ko me zaka yi, taku ɗaya ba zan ƙara ba, duk fa Mutanen banza ne a wurin" "Alright, hakan ma na gode". "To dan Allah yaushe zaka je wurin Inna ka gaya mata, muje ka kaini in ganta, ni ko ba 'yar uwata ba ce, dan Allah ka kai ni in ganta, ka ga kan in mutu dai na ga wani nawa a duniya" "Ina wanda ya tsinto ki?". "Ba nace maka ya rasu ba" Adnan ya yi ajiyar zuciya ya ce "To ke a ina aka tsinto kin?". Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Nima ban sani ba ni dai kawai yadda na ji labari, Baba ne ya tsinto ni, ya kai ni gidansa, sai ya je wurin 'yan sanda ya gaya musu ya tsinci jaririya, sai suka ce yaje Allah ne ya bashi. Sai Baba ya ce musu, ba wani bincike da za ayi? Sai suka ce ba yau aka fara haihuwar shegu a yar ba, dan da gani wannan kyan nawa ta hanyar banza aka sameni, ba lallai a samu iyayena ba, dan sun samini suna Afra saboda kyauna, yaje in zai riƙe sun bashi, to daga nan ya riƙeni ya sani a makarantar boko ai ta cewa bani da iyaye, samari da yawa na sona, amma saboda tsinto ni aka yi, sai su fasa aurena, wani ɗan gidan ɗan majalissa ne ya ce zai aureni, babansa ya ce bai yadda ba, da ƙyar babansa ya amince, an kusa kawo kuɗin Auren kuma, yayi hatsari ya mutu, kallon fa shegiya ake mini a garin nan" ta ƙarasa maganar fuskarta ta jiƙe da hawaye. Hanky ɗinsa ya ciro a aljihunsa, ya shiga goge mata hawayen fuskarta. "Angel, ke ba shegiya ba ce, ina da yaƙinin ke 'ya ce ta sunna, ina ga ke ce zaki dace kiga iyayenku, shiyasa Allah ya ɗauke mini Angel ya kawoni garin nan na haɗu da ke". "Me kake nufi?". "Twin sister ɗinki da na aura, Allah ya yi mata rasuwa kwanakin baya, ta rasu ta bar mini 'yar jaririya mace" yayi Maganar hawaye na zubowa daga idonsa. Zubewa ta yi a wurin ta ɗora hannu a kanta ta ce "Na shiga uku!" ₦300 NE DAN ALLAH KU SIYA KAN KU KARANTA MANA 08081012143 [11/12, 3:38 PM] Abk: Ƙasa Adnan ya yi da kansa cikin ƙoƙarin tsayar da hawayen idonsa amma ya ƙi tsayawa, ganin yadda yake kuka sai jikin ƴar Baba ya yi sanyi. Idanunta cike da hawaye ta ce. "Ka daina kuka, ba a son yi wa wanda ya mutu kuka, haka Inna take ce mini idan ina kukan rashin Baba." Bai ce komai ba sai da ya share hawayen fuskarsa duka, cikin raunin murya ya ce. "Ai za ki maye mini gurbin ta ko?" Turo baki ta yi ta ce. "Huh'um, wallahi ni ba na son ka, kalle ka fa baƙi." Duk da halin da yake ciki na tuna Abra sai da ya murmusa saboda yanda ta yi maganar. "Shikenan, tunda kin fi so na auro wata ta riƙe mini ƴata, in ma muguwa ce ta cutar da ita idan bana nan." Shiru ta yi kamar mai nazari tana kallon shi na wasu sakanni, taɓe baki ta yi ta ce. "Ina son ƴar taka, tunda ka ce ƴar'uwata ce ta haife ta, yaushe za ka kawo mini ita ko kai ni na gan ta?" "Ranar da kika fara so na." Ya faɗa idanunsa a cikin nata. Janye idanunta ta yi da sauri, cikin raunin murya ta ce. "Amma ka san iyayenmu? Me ya sa suka yarda da mu?" "Ban sani ba, amma ina nan ina bincike akan hakan, ni da wanda ya riƙi Abra." "Abra." Ta maimaita sunan kamar mai tunanin wani abu a cikinsa. Kallon yadda rana ta fito Adnan ya yi ya ce. "Lokaci yana tafiya, mu je ki raka ni gidan Sadin." "Gaskiya ba zan iya zuwa ba, ni roro na zan tafi, na san yanzu ana can ana ta yi, an kusa rore gyaɗar ma duka ni ban je ba." "Mu je na taya ki." Kallon shi ta yi cikin mamaki ta ce. "Ai ba ka iya ba." "Sai ki koya mini." "Tom shikenan mu je." Suna tafe yana tsokanar ta har suka ƙarasa gonar, wani irin farinciki da nishaɗi yake ji na kasancewa da ƴar Baba, ji yake tamkar Abransa ce ta dawo. Yara da manya damƙam a gonar, sun zagaye tumin gyaɗar kowa na roro. Cikin takaici Ƴar Baba ta dubi Adnan ta ce. "Ka ga har an cika ban zo ba, ni da nake riga kowa zuwa, kuma alƙur'an sai ka taya ni." Bai ce komai ba sai idanunsa da yake ba wa abinci yana kallon yadda ake roron gyaɗar. Ƴar Baba na ƙarasawa gurin aka fara kiran sunanta, ta kula wanda ta ga dama ta share waɗanda take jin haushi. Su kuwa ƴan ƙauyen sai kallon Adnan suke, cikin mamakin ganin shi tare da ƴar Baba, suna son su tambaye ta wane ne shi, amma yadda ta yi kicin-kicin da fuska ya sa kowa ya haɗiye gulmarsa bai fito da ita ba. "Ka zo ka taya ni, ka tsaya kana kallo na." Ta yi maganar cikin sangartar ta. Ƙarasowa ya yi ya tsugunna a kusa da ita ya ɗauki ganye ɗaya ya fara cire gyaɗar yadda ya ga suna yi cikin yamutsa fuska, a ransa yana tambayar kansa ko mene ne amfanin wannan abun? Wasa-wasa sai ga SP Adnan ɗan gayu mai ji da kansa ya wuni a gona yana roron gyaɗa, don hana shi tafiya 'yar Baba ta yi da rigimar ta, Sallah ce kawai take tayar da shi, rashin sabo ya sa duk ya galabaita, kayansa suka yi futu-futu da ƙura da ƙasa. Ƴar Baba kuwa sai murna take gyaɗarta ta fi ta kowa yawa, saboda taya ta da Adnan ya yi. Sai da mai gonar ya zo ya rarraba ya ba wa kowa ladan roronsa sannan suka tafi, lokacin Magriba ta kawo kai. Suna cikin tafiya 'yar Baba ta dube shi ta tuntsure da dariya, saboda yadda ya yi wani kalar tausayi, ga shi ya taka ƙaya a gonar da ɗingishi yake tafiya, ɓata fuska ya yi bai yi ce komai ba. "Gaskiya kai rago ne, kana namiji amma ɗan wannan aikin ya wahalar da kai, ba ni kwanon abincina da robar ruwan idan ba za ka iya riƙewa ba." Hararar ta ya yi tare da faɗin. "Idan na ba ki da wanne hannun za ki riƙe?" "A kai nake ɗora buhun gyaɗata, sai na riƙe kwanon a hannu, haka nake yi kullum." Jinjina kai ya yi, a ransa yana jinjina yadda mutan ƙauye suke shan wahalar rayuwa. Har ƙofar gida ya raka ta, har ta wuce za ta shiga gida ta dawo ta ce. "Yawwa na tuna, jiya na tafi kiran Inna shi ne ka gudu ko?" Cikin gajiyar dake addabar jikinsa ya ce. "I'm sorry." "Ba zan haƙura ba gaskiya, sai dai in ka yarda in kira Innar ta gan ka yanzu." "Ki bari sai gobe, zan zo na gaishe ta my Angel, yanzu duk a gajiye nake, kin ji ma an fara kiran Sallah, ko da yake na ga ke duk wunin da muka yi a gona ba ki yi Sallar ba." Murguɗa baki ta yi ta ce. "Ina ruwanka, dama saka mini ido kake yi." Murmushi ya yi tare da kama hannunta ya riƙe, idanunsa a cikin nata yana jifan ta da wani irin kallo. "Na shiga uku! Don Allah ka cika ni, kar Inna ta leƙo ta gan ni ko Yaya Musa ya zo wucewa." Ta yi maganar cikin tsantsar tsoro da fargaba, idanunta duka a waje tana kallon zauren gidansu. "Have a nice night, good bye, I love you." Ajiyar zuciya ta sauke jin ya sakar mata hannu ta rarumi bugun gyaɗarta ta yi cikin gida da gudu a ranta tana gulmar Adnan. Inna dake alwala ta saki salati tare da faɗin. "Wai ƴar Baba kanki ɗaya kuwa? Da magaribar ma ba za kina tafiya cikin nutsuwa ba? Wunin yau bakina shiru amma yanzu daga dawowar ki zaki fara sa ni magana, me yake damun ki ne wai?" Ba ta ce komai ba sai da ta koma ta ɗauko kwanonta ta dawo, bayan ta zauna a kan kujera yar tsugunne ta ce. "Inna daga dawowa ta maimakon ki tarɓe ni da ruwan sanyi na randa da abinci amma sai ki fara da faɗa? Na je na gaji na wahala amma ko ki mini sannu." "Ba zan yi ba, tunda ke yin abin da aka ce ki yi kike yi, yarinya kina girma amma kullum jiya i yau, ai ta maimaita magana ba kya ɗauka, sai dai ta shiga ta dama ta fita ta hagu, to in ma wani motsin ne a kanki gobe zan kai ki a miki roƙiyya a fitar." "Taɓ, wallahi ba zan biki a zane mini jikina ba haka kawai." Ta yi maganar tare da miƙewa ta shige ɗaki. A matuƙar gajiye ya ƙarasa gidan Hakimi, bai zauna ba sai da ya rage kayan jikinsa ya yi wanka ya shirya cikin ɓaddakama ta shiga irin ta matasan garin da kayan wani ɗan Hakimi da ya aro, bayan ya yi Sallah ya naɗe ƙafarsa da hanky, ya ci cakes ɗin da ya zo da su da lemo ya ɗauki torchlight da kuɗi ya fita. Da ƙyar yake iya tafiya saboda yadda ƙafar tasa ta ɗaure, ba ƙaramin cakar shi ƙatuwar ƙayar ta yi ba don da ƙyar ya iya zare ta saboda zugi da raɗaɗin da gurin yake masa a lokacin. Ba don dole ba da kwanciya zai yi a yanzu ya huta, amma aikin da ya zo yi ƙauyen ba na wasa ba ne, ga IG kullum sai ya tambaye shi akan ina aka kwana? Haɗuwa da ƴar Baba duk shi ya ɗauke masa hankali. Da ƙyar ya iya gano layin su Sadi ɗan kunama, yana shiga karnuka suka fara yi masa welcome da haushi.. "Kai, waye a nan?" Muryar wani ɗan tauri cikin shaye-shaye ta doki kunnensa. Cikin ƙwarewa a aiki ya sauya muryarsa zuwa ta yan yawa ya ce. "Ni ne, abin zuƙa nake buƙata, an ce mini babu inda zan samu sai nan." Haske shi aka yi da fitila mai haske ba tare da ya san waye ba, sai da suka ƙare masa kallo sannan wanda ya yi magana da farko ya ce. "Kawo silalla a baka abun duniya Baba." Bai ce komai ba ya zaro kuɗi ba tare da ya ƙirga ba ya ba su. Wiwi suka ba shi da wani abu a kwalba wanda ya tabbatar giya ce, karɓa ya yi ya zauna ɗan nesa da su yana kallon gurin cikin nazari, wani ƙaton gida da ya banbanta da ginin gidajen garin ya ƙurawa ido, ko tantanma ba ya yi nan ne gidan Sadi ɗan kunama. Mami ce zaune a main parlour tana ba wa little abincinta, bayan ta ƙoshi ta kwantar da ita akan carpet ta shiga kitchen don ɗauraye bowl. Kafin ta fito amarya Salima ta shigo parlour'n cikin wasu matsatstsun kaya riga da wando, sai baza ƙamshi take. Ganin little a kwance ita kaɗai ya sa ta ɗauke ta cikin sauri ta fara yi mata wasa tana shilla ta tare da yi mata waƙa. "Mamana kin fi ta kowa, ƴar fara kyakkywa, mai kama da mamanta." "Malama ya za ki ɗaukar mini yarinya kina ciccilla ta sama a daren nan? Mene haka?" Na'ima ta faɗa lokacin da ta dawo parlour'n tare da ƙwace little a fusace. "Ki yi haƙuri kar ki karya mata haƙarƙari." "In na karya kina da asara ne? Haba, bana son maita, na ce bana son ana ɗaukar mini yarinya amma don naci da rashin zuciya sai an ɗauka." "A'a, hayaniyar me nake jiyowa tun daga baranda? Lafiya?" Abbi da ya shigo gidan ya tambaya idonsa akan Nai'ma. Hawaye Salima ta ƙaƙaro cikin kissa ta ce. "Ban san me ya sa ba ta son na ɗauki little ba, ko na yi mata wani lefin ne ban sani ba, ni kuma ina da son yara, shi ya sa bana zuciya na ƙi ɗaukar tata." Duban Na'ima dake huci ya yi ya ce. "Na'ima ke kika haifi yarinyar nan ne ko ke kaɗai aka haifawa ita? Abra is my daughter, ke da Salima kuma duk matana ne, don haka yadda kike da iko da abin da Abra ta haifa ita ma haka, don haka kar na ƙara jin wata rigima ta tashi don ta ɗauki little." "Wallahi ba zai yiyu ba, Abran ai ni na riƙe ta ba wata can ba, don haka nike da iko da abin da ta haifa." "Okay, abin da na faɗa ne ba za ki bi kenan? To cigaba kar ki fasa, kar ki ɗauka wai na sauya ne daga Khamal ɗin da kika san ni saboda kwana biyu ina ɗaga miki ƙafa, fitina ce kawai bana so." Ya yi maganar cikin fusata. Miƙewa Salima ta yi ta kama hannun Abbi tare da kwantar da kanta a jikinsa, cikin muryar rarrashi mai cike da salo da shagwaɓa ta ce. "Honey please ka bar maganar, in dai little ce ba zan ƙara ɗaukar ta ba." Bai ce komai ba sai gefen fuskarta da ya shafa cikin ƙauna. Tsaki Nai'ma ta ja ta yi wucewar ta part ɗinta, zuciyarta cike da tuƙuƙin baƙin ciki da kishi. Tana shiga ɗaki ta goye A'isha Humairah sannan ta ɗauki wayarta ta kira Aunty Wasila, bayan ta ɗaga ta fashe mata da kuka. "To uwar kuka, yau kuma me ya faru?" "Na gaji Aunty wasila, na gaji da zaman baƙin ciki da ganin takaici, wallahi zuciyata ba za ta iya ɗauka ba, idan aka cigaba da haka watarana sai dai ku zo ku tarar da gawata." "Yanzu dai faɗa mini mene ya faru." Cikin gunjin kuka Mami ta ce. "A gabana fa Khamal yake nuna wa yarinyar nan k'auna, ya rungume ta ko ya ba ta abinci a gabana ba komai ba ne a gurin shi, washegarin da aka kawo ta da yamma har da fitowa main parlour tana tafiya ƙafa a tale, a dole sai ta nuna mini an ɓurma ta, iskanci dai kala-kala." "Ke ma sai ki tsuro da naki salon, mijinki ne fa, kin fi kowa sanin shi, ai kowa ya iya allonsa ya wanke kawai, amma kya zauna kina wani koke-koke, har yanzu ba ki bar shashancin nan ba Na'ima? Sai ka ce a kanki aka fara kishiya? Duk kin fice daga hayyacinki." Shiru Mami ta yi ba ta ce komai ba, ita kaɗai ta san halin zafin kishin Mijinta da zuciyarta take ciki, idan ta ga Abbi tare da Salima sai ta ji tamkar ta shaƙe su saboda tsananin baƙin ciki, ga yarinyar da shegiyar kissa da iyayi da firirita. Washegari da safe Nai'ma ta fito don haɗa wa kanta breakfast ta tarar da Abbi da Salima zaune akan dinning suna cin abinci a cikin plate ɗaya, Salima sai nanaƙe shi take tamkar za ta koma cikinsa, shi kuma sai jifan ta yake da wani irin kallo ƙasa-ƙasa. Wani irin abu mai kaifi da zafi ne ya soki zuciyar Mami, mijinta abin son ta wanda suka shafe fiye da 20 Years tare amma yau shi ne yake soyayya da wata macen da ba ta fi Yar cikinsa ba a gabanta, ji ta yi tamkar ta juya ta koma part ɗinta, amma dai ta ɗaure saboda kar a gane halin da take ciki ta nufi kitchen, cikin yaƙi da hawayen dake ƙoƙarin fita daga cikin idonta. Kamar yadda ta yi tamkar ba ta gan su ba haka su ma suka yi, sai Salima ce ta bi ta da kallon gefen ido tare da sakin wani munafukin murmushi. Rasa abin da za ta girka ta yi, yunwar da take ji ma nemar ta ta yi ta rasa saboda mugun ganin da ta yi, tana hawaye ta dafa noodles guda ɗaya ta juye ta a plate ta fito bayan ta goge hawayen fuskarta. Kakarin aman da Salima ta fara ne ya sa ta tsayawa cak ganin ta tashi ta shiga toilet ɗin dake parlour'n da sauri, a ruɗe Abbi ya bi bayan ta yana faɗin "Lafiya Baby? Me ya faru?" Ba ta ba shi amsa ba sai da ta gama aman, kamo ta ya yi suka fito yana yi mata sannu, har lokacin Nai'ma tana parlour'n a tsaye ta kasa tafiya. "Baby ko na ɗauko key ɗin Mota mu tafi asibiti ne?" Ya yi maganar yana shafa bayanta. Ƙara lafewa ta yi a jikinsa tana kallon Mami cikin yamutsa fuska ta ce. "A'a Honey ba wani abu ba ne, kawai ƙamshin turaren da Maman Salman ta fesa ne bai mini ba, tunda ta fito cikina ya fara hautsinawa, da ta dawo kuma sai na ji abin ya tsananta." Duban Mami Abbi ya yi cikin ko in kula ya ce. "Please ki daina saka turaren da kika sa, kin ga ya sa Baby amai, ko kuma idan kin san ki daina fitowa parlour idan tana nan." Ya ƙarashe maganar tare da kama hannun Salima dake ta toshe hanci suka bar parlour'n. Tsananin baƙin ciki da takaicin da Mami ta ji ba zai misaltu ba, ba ta san lokacin da ta saki plate ɗin hannunta ba indomien ta baje a ƙasa ba, cikin kuka mai cin rai ta yi part ɗinta da gudu. "Doctor magana fa nake maka ka mini shiru, haba, I'm tired da wannan sabon halin da ka tsiro da shi, gaskiya." "Na miki dole ki zauna da ni a hakan da nake ko kuma na ɗaure miki ƙafarki ne na hana ki tafiya? Idan ba za ki iya ba you are free to go." Cikin tsantsar mamaki da shock Hajiya Saudat ta ce. "Yusuf! Yau ni kake fadawa ba ka ɗaure wa ƙafa ka hana ni tafiya daga gidanka ba?" "Uwata ce ke da ba zan faɗa miki haka ba?" Ya yi maganar yana jifan ta da wani mugun kallo, kasa magana ta yi saboda tsananin al'ajabi. Dogon tsaki ya ja ya ɗauki coat ɗinsa da briefcase ya bar mata ɗakin. A wahalce ta yi zaman ƴan bori a ƙasan ɗakin jin kanta na juya mata, wata irin mummunar faɗuwa gaba ce ta ziyarce ta, lokacin da wani tunani ya ɗarsu a ranta. Daga yanayin yadda ya shigo asibitin ma'aikatan suka san babu lafiya, dama kwana biyu zuciyoyinsu cike suke da mamakin rashin zuwan shi Asibitin, kasancewar wannan ne karon farko da hakan ta taɓa faruwa. Suna gaishe shi amma ba ya amsawa, fuskarsa a cukule ya ƙara office ɗinsa. After 30 minutes ya aiko a kira masa Nurses and doctors ɗin dake asibitin. Bayan sun hallara ya dinga kiran su ɗaya bayan yana ba su wani envelope. Fuskokinsu cike da mamaki suke baro office ɗin. "Na shiga uku! Takardar sallama fa na gani." Cewar Nurse Basira cikin tashin hankali. "Ni ma haka." Sauran Nurses ɗin gurin suka haɗa baki gurin faɗar haka. Kafin su ƙara magana wani likita ya fito daga office ɗinsa fuskarsa ɗauke da tashin hankali, yana share zufa ya ce. "Don Allah ko kun san laifin da na aikata da na cancanci kora a asibitin nan? A sani na ni dai ban yi komai ba." "Ai ba kai kaɗai aka kora ba, mu ma nan duk korarraru ne." "Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un, to me yake damun Doctor Bulama? Me aka yi masa da lokaci ɗaya zai kori fiye da rabin ma'aikatan shi? Anya lafiya kuwa?" "Ƴar Baba ki je ki ɗebo mana ruwan nan, ko na shiga banɗaki fa babu a gidan nan." Diddire ƙafa ta fara yi tare da faɗin. "Wai don Allah Inna da girmana zan fita ɗiban ruwa? Salan a raina ni." "Ni zan fita in ɗebo kenan? Don yau ɗaya mai ɗebowar ba ya jin daɗi shi ne ba za ki fanshe shi ba? Shi ba mutum ba ne kenan da kullum yake ɗebowa kike facakar ki da shi." Ba ta kuma magana ba ta figi mayafinta ta ɗauki botikan ɗiban ruwan da guga ta fice kamar za ta tashi sama. "Budurwar ƙauye." Ta tsinkayi muryar Adnan a kanta yana kiran ta. Tsayawa ta yi amma ta ƙi juyawa ta kalle shi, sai cuno baki take kamar zai taɓo sama. "Ni fa ba sunana budurwar ƙauye ba, ba haka Babana ya raɗa mini ba gaskiya." Murmushi ya yi ya ce. "Ina zuwa da wannan botukan?" Ya soso mata inda yake mata ƙaiƙayi, hakan ya sa ta shagwaɓe fuska ta ce. "Yaya Musa ne ba shi da lafiya, shi ne Inna ta ce wai yau ni zan ɗebo ruwa." "Ina ne gurin ɗibar ruwan?" "Bayan nan ne." Ta yi maganar tare da nuna masa hanyar. Bai ce komai ba ya karɓi botikan suka jera suna tafiya. Gurin ɗiban ruwan rijiyoyi ne da yawa, mutane mata da maza kowa ya zira gugansa yana ɗiba. Ƴar Baba na zira guga Adnan ya karɓa ya fara janyo ruwan yana zuba mata a cikin botikan, bayan sun cika ya ɗauka ya kai mata har ƙofa gida, ita kuma ta ɗauka ta shiga da shi ciki. Haka suka dinga yi har ƴar Baba ta cika komai na gidan. "To ko ke fa, ba ga shi har kin gama ba, sannu Allah ya saka da Alkhairi, amma yau kin yi sauri, hala babu layi ne a gurin?" Inna ta faɗi haka lokacin da Ƴar Baba ta dire bokitin ƙarshe. "Ke dai ba na deɓo miki ruwan ki ba?" "To ai na ga da in kika tafi ɗiban ruwan sai ki wuni akan bokiti ɗaya, kina ta neman magana a can." Tura baki ta yi ba ta ce komai ba ta fita gurin Adnan dake jiran ta a waje. ganin yadda duk ya jiƙa wandon jikinsa ya sa ta kwashewa da dariya har da ƙyaƙyatawa. Ɓata fuska ya yi ya ce. "What's funny?" Girgiza kai ta yi tana cigaba da dariyar. Ɗage kafaɗa ya yi ya ce. "Gurin Inna na zo mu yi magana a kan ki, sannan in sanar mata iyayena za su zo neman aurenk.." "Taɓ, wallahi ni bana son ka ba zan aure ka ba." Ta katse shi da faɗin haka cikin serious dake tabbatar da abin da ta faɗa har cikin zuciyarta haka ne. Littafin kuɗi ne, ku biya kafin ku karanta. 09047871750 [11/14, 9:13 PM] Abk: "Are you sure baki so na ba zaki aure ni ba?" Adnan ya faɗa cikin tsoro da fargaba maganar data nemi ta sar masa da mikin dake damun zuciyarsa na rashin Abra. "Ni fa ba zan taɓa aurenka ba, gaskiya kayi mini baƙi da yawa kuma bana son ka shi ne kawai....," "Stop it.." ya faɗa a tsawa ce yana riƙe saitin zuciyarsa dake masa zafi lokaci guda, kalaman bakin Afra na neman sauya masa lissafi. Kasa magana ya yi sai idanunsu daya rufe zuciyarsa na harbawa. "Na kawo maka ruwa kasha ne, naga kamar ka ƙware?" Ɗago jajayen idanunshi ya yi tare da zuba mata akan fuskarta wanda a kullum take masa gizo, ƙarfin hali yake kawai na Kasancewar su tare da yawan lokota sai ya ji kamar ya jawota ya rungometa ya faɗa mata how much he loving her! Ya sauke numfashi a galabaici yana kallon yadda tai shiru tana binsa da idanu. Ba tare da ya ce komai ba ya juya ya bar ƙofar gidan nasu. Ita ma bata kira shi ba, amma har zuciyarta ta ji babu daɗi a shirunsa da tafiyar ta shi, zuwa yanzu ta fara sabawa da shi. "Wannan karan kuma mene ya faru kika shigo jiki a saɓule kamar kazar da ƙwai ya fashewa?" Inna ta tambayi Afra wacce ta shigo tana bin bango ta luuula duniyar tunani da alama bata ma san abin da Innar ke faɗa ba. "Yau naga abin da ya ishe ni, anya yarinyar nan lafiyarki ɗaya kowa? Ina ta ɓaɓatu kin yi mini shiru?. Haka kurum kada naje ina tufka wani na warware mini ita na shiga uku" Nan ma dai Afra ba ta ce komai ba sai bin bango da tayi ta zauna tana wawware idanunta. "Kee! Kee!! Ƴar Baba?" "Na'am Inna" Afra ta faɗa a gigice bayan Inna ta girgiza kafaɗarta. "Lafiya ke dawa,ina kika je bayan kin kawo ruwan?" "Gasky Inna tambayarki ba zata mutum ya yi ilimi ba, tunani nake fa amma gaba ɗaya kinsa na manta abin da nake ina jinki fa" Inna ta riƙe haɓa tana faɗin.. "Tunanin uban me kuma? Salon ki kawa kanki ciwo" ganin hawaye a fuskar Afra ya sanya jiki babu ƙwari Inna ta tana tambayar lafiya Meke faruwa da ita haka?.. "Inna tun bayan mutuwar wanda zan aura har yanzu babu wanda ya ce yana so na zai aureni, haka zan ta zama kenan kalli ƙawayena ko wacce tana yaranta abin sha'awa wasu kuma ciki garesu" Cikin kulawa irin ta Uwa da Ƴa Inna ta kama hannun Afra tana cewa. "A'a Ƴar Baba shi aure lokaci ne, na sha faɗa miki da lokacin ki ya yi ko bakya so sai kinyi auren nan, zaki auri miji wanda babu irinsa a garin nan ƙyakƙyawa ƙin kowa sai wanda ka taɓa, Ba kiga kalarki ba wanke hannu ka taɓa kada ki saka wannan a ranki muna ta addu'a kema kici gaba da yi" "Kuma bakya tunanin sbd bani da iyaye ba a zuwa neman aure na Inna?" Yanayin yadda ta yi maganar a raunace ya sa Inna yin shiru ita ma abin yana susa mata zuciya ainun bata da yadda za ta yi ne. Ɗaki Afra ta shige zuciyarta babu daɗi abubuwa suka dawo mata sabbi a rai. Tana jin kamar bata kyautawa Adnan ba, bata ji daɗin yadda ya tafi ba babu farin ciki akan fuskarsa kamar kullum. Kuma ba lallai ya dawo ba. Kuka ta fashe da shi na rashin abin yi a haka bacci ya ɗauke ta. Tun da ya shigo ɗakin ya kasa zaune ya kasa tsaye "Bana son ka" kalmar ta tsaya masa a rai, ashe haka ake ji idan an cewa mutum ba a son shi? Yaya matan da suka dinga son shi a baya suka ji a zuciyarsu? Afra akwai wauta amma zantunkan bakinta daga zuciyarta suke, babu alamar ƙarya ko wasa a cikinsu tana nufin abin da ta ce ne. "What should I do? Adnan think, think" ya faɗa a hankali yana rufe idanunshi. Ba zai fushi da ita ba,amma dole ya ɗaga mata ƙafa domin fahimtar zuciyarta. Wayarsa ya ɗauka ya kira Hajiya Mama tana ɗauka ya kwaɓe fuska tare da langwaɓar da kansa gefe guda. "Son ya dai?" Cikin ƙasa da murya ya ce "Evening Hajiyata" ta amsa da "How are you? Ya zaman village? The you like it" "Sure Mama, kawai ki tayani da addu'a wani abu na neman tunkaro ni kamar zai bani wahala kuma" Hajiya Mama bata fahimta ta ɗauka al'amarin aiki ne hakan ya sa ta ce. "Addu'a kam kullum muna yinta Sp Adnan Aliyu Matawalle, Allah ya taimaka ya baka sa a Insha Allah zaka samesa cikin sauƙi" Idanunshi ya lumshe yana jin nutsuwa na saukar masa a hankali ya mirgina gefe yana jan numfashi ya ce. "That's why i always love you Mom..." Murmushi tayi cike da jin daɗi domin tana ƙaunar Adnan ji take kamar ita ta haife shi duk da cewa ita bata taɓa haihuwa ba, maybe bata ɗaya daga cikin matan da suke haihuwa a nan duniya. "Hajiya, Abba...." Ya faɗa cike da rauni domin ya fara gajiya Abba shi ne cikon jin daɗinsa dama samun nasarar baki ɗaya, sai da shi duniyarsa ke zama cikakkiya. "Me Abba ya yi kuma Adnan?" A kasalance ya ce. "He still angry with me na rasa yaya zan yi ne bana jin daɗin" "Adnan my Son kada ka damu da hakan, Abbanka surprise ɗinka zai yi very soon ka mai da hankali kawai wajan yin aikinka Please" Hira su kaci gaba dayi cikin nuna soyayya a haka Adnan ya manta da ɓacin ran da Afra da haddasawa zuciyarsa. Yau ranar kirkin Mami ne tana zaune gefen gadonta lokacin kusan ƙarfe goma na dare ne, ta shirya cikin wasu haɗaɗɗun kaya na barci, hannunta ɗauke Aishatul-humaira wacce taƙi yin barci yau sai dry ta kewa Mami tana ɗaga ƙafa duk ta cire sosan da aka yi wa kanta ado da shi. "Sweetheart yau hirar dare za mu yi kenan, kwana biyu daddynki bai neme mu" "Idan ba Dady ai akwai grandfa right?" Abbi ya faɗa yana shigowa cikin bedroom ɗin sanye yake da ƙyakkyawar shiga ta barci sai ƙamshi yake zabgawa. Mami bata kallesa ba hankalinta akan Aishatul-humaira iya kuzarin yarinyar abin sha'awa ne. Hannu ya sa ya ɗauki little yana mata wasa amma ta ɓata fuska alamar anyi mata ba daidai ba. "Wato Na'ima na saka ki a bedroom tana hure miki kunne akan Granny naki ko, shi ne zaki ɓata fuska?" Kamar Aishatul-humaira ta fahimci abin da ya ce ta fashe da kuka sosai tana cilla ƙafa, Abbi ya waro ido yana miƙa wa Na'ima ita ya ce. "Wannan soyayyar taku daga Allah take, maza ki bata haƙuri" jijjigata ta dinga yi a haka tai barci tana sauke ajjiyar zuciya. A nutse Mami ta kwantar da ita bayan tai mata addu'a ta miƙe zata bar ɗakin "Na'ima" Abbi ya kira sunanta yana bin jikinta da kallo ƙamshinta na fisgarsa zuwa gare ta. Wajanta ya ƙarasa ya tsaya daidai bayanta tare da saƙalo waist ɗinta da hannunsa biyu cikin ƙasa da murya ya ce "Ni kike azabtarwa haka Na'ima? Ba zaki amshi wannan auren matsayin ƙaddararmu baki ɗaya ba? The you know how much i miss You? Baki san adadin son da nake miki ba ko?" Juyo da ita ya yi gabansa yana kallon yadda hawaye duk ya ɓata mata fuska ta wani shagwaɓe fuska. "Am sorry first love uwar gidan Major Khamal Khamis, ki yafe masa mana?" Ɗaga ta yi suka haɗa idanu ta ɓalla masa harara dry ya yi mai sauti yana jawota baki ɗaya zuwa jikinsa ya matse ya ce "Ohhhu dai naji, muje na nuna miki wani abu?" Ya faɗa yana sumbatar wuyanta tare da janta zuwa other bedroom. Washegari abin har mamaki ya bawa Salima ganin har 12 Abbi bai fito ba, kamar yadda ya saɓa ɗakinta ya tashi da wuri ya duba Na'ima da little ɗin. Tana zaune a Parlour watching TV taji dry ƙasa ƙasa da sauri ta juya zuciyarta ce ta buga ganin Na'ima cikin wani dakakken lace mai masifar kyau, sai Little a hannunta wacce ta farka tuni ita ta tashe su ma, Abbi ya saƙalo jikin Na'ima shi kansa bai san adadin son da yake mata ba. Zama sukai a saman Kujera Salima tai murmushi ta ce "Barka da fitowa honey?" "Yawwa Barka baby" ta juya kan Na'ima wacce take latsa waya tana ƙoƙarin ɗaukansu a photo ta turawa Salman "Maman Salman an tashi Lafiya?" Mami na ɗora kai a shoulder ɗin Abbi kamar dole ta ce. "Ya kike?" Kalmar ta daki zuciyar Salima sai kawai ta share, Naima na ƙoƙarin turawa Salmanun-faris photos taji Sallamar sa da sauri ta miƙe tsaye tana mmki, yana tsaye bakin ƙofa cikin wata dakakken shadda kyan da Salman ya yi ya ɓaci, ya zama cikakken matashi wanda samun kamarsa za a daɗe ga haiba da kwarjini. Cikin sauri ya ƙarasu yana ɗaukan Little wacce ta kafesa da idanu irin ta ganesa ɗin nan "My sweetheart my happiness daddy is here... Tsayin kwanaki uku ciff Adnan ya ɗauka bai sake haɗa hanya da ƴar Baba ba, hankalinsa akan aikin daya kawosa baya son haɗa abu biyu domin ya fahimci yarinyar na neman bashi ciwon kai. Cikin ikon Allah ya samu nasara cikin daren wata rana aka zo aka tafi da Ɗan kunama da sauran muƙarrabansa. Adnan kuma ya ce akwai abin da ya ke jira. Amma duk wanda ya gansa ya san baya cikin nutsuwar ya faɗa tsoro da zullumin yadda zai ƙara tunkarar Afra a lokaci na barkatai suka ƙara wanzuwa a ransa, neman aurenta ya bambanta dana Abra domin cikin lokaci kaɗan ta amince masa. Ƴar Baba na kwance abin duniya ya isheta ko abinci kaɗan take ci, tunanin rashin ganin Adnan kwana biyu ya addabi zuciyarta. Inna dake zaune ta juya tare da kallon Afra ta ce "Yau idan baki faɗa mini abin da ke damunki ba, babu abin da zai hanani yi miki doka wallahi" "Haba haba don Allah Inna dame zanji ne wai? Kawai baki san meke damuna ba kici zaki dakeni, ko na faɗa miki cewa zaki aljanu suka shafan nidai kawai ki barni da abin da ke damuna" Miƙewa tsaye Inna tayi tan ɗakko abin doka ta ce "Bari dai ki gani, kina zaton ba zan iya bugunki ba ƴar butu uwa kawai ja'ira" da gudu Afra ta bar gidan bayan ta ɗauki mayafinta. "Kinibabbiyya ki tsaya mana kiga yadda zan yi dake yarinya ta mayar dani kamar kakarta" Inna ta faɗi haka tana ajjiye abin dokan data ɗakko. Adnan na tsaye a ƙofar gidan cikin wasu ƙananun kaya masu kyau ya saka sunglasses a idanunshi ya harɗe hannayensa a ƙirji. Kamar daga sama ya ga ta fito tana haki ganin tana ƙoƙarin yin gaba ya sanya hannunsa tare da kamo nata. Jin an riƙe hannunta tayi saurin waigowa idanunta ya sauka akan sa bata taɓa tunanin zata gansa ba, ganina ya sanya ta masa ƙuri da idanu wanda suka cika da hawaye. Baya ta juya masa tana sakin kuka tako a hankali cikin nutsuwa zuwa inda take suka fuskanci juna, tallafo fuskarta yai yana kallon yadda take kuka sosai kamar wacce ya daka me hakan ke nufi? Kewarsa tayi ko mene? Ita da ta ce bata son shi. "Mene? Why are you cry" ya tambaya a hankali turo baki tayi tana ƙara fashewa da kuka. Adnan ya dafe kai ya ce "Goodnight Zaki tarwatsa mini zuciya angel bake kika ce bakya so na ba?" Cikin shassheƙar kuka ta ce. "Kuma don na faɗi haka sai ka daina zuwa ko?" "To tunda baki so na me zan miki?" Ta tura baki ta ce "Ni ba ruwana da kai,mun ɓata" ta ɗan dire ƙafarta tana ƙara sautin kukanta. Juyawa ya yi ganin ba kowa a wajan ya ɗan lumshe idanunshi yana jawota gefensa trying to hug her ya ce "Ohhh am sorry my rigimammiya yanzu gani" ya share mata hawayen tas yana riƙe da ita sosai kuma ba tai ƙoƙarin guduwa ba. Ya riƙe haɓarta ya ce "Ina son ganin Inna Angel zaki kiramin ita?" Kai ta ɗaga masa yaja hancinta tare da kai baki kamar zai sumbaci wajan ta zilli da sauri tana masa dry. Girgiza kai kawai ya yi yana tsaye ta dawo ta ce Inna ta ce ya shiga, da fara'a Inna ta amshesa bayan sun gaisa ya zayyana mata abin da ke faruwa, da zuwansa garin da ganin Afra da ya yi ya ɗauka matarsa ya yi mata bayanin komai. Ta jinjina kai ta ce "Ikon Allah, ashe rabon ganin wani dangin ƴar Baba ne ya sa kuka haɗu, Ubangiji ka amsa mana wannan addu'ar" "Amin" Adnan ya amsa idanunshi akan Afra wacce tayi kwance a cinyar Inna sumarta gwanin sha'awa duk ta bayyana domin ita har tafi Abra tsayin suma. "Ai ba zama bari a ki rawo kawonta sai an yi magana ta fahimta ko?" "Hakan yafi ina son komawa,amma sai an tsayar da manufa" "Ƴar Baba maza jeki kira kawonki yanzu" miƙewa tayi ganin Adnan ɗin ne kuma yasa ba tai musu ba. Suna zaune ta dawo tare da kawon nata. Sun gaisa da Adnan cikin sakin fuska, da farin ciki bayan ya gama jin komai ya ce. "Allahamdulilla Allah abin godiya, yanzu dole mu fara ji idan ita ƴar baba na son shi kuma zata aure shi ko?" Inna ta ce "Haka ne" ya juya kan Afra ya ce "Ƴar Baba kina son Adnan ɗin?" Ta kalli Adnan wanda yake Kallonta yaji abin da zata ce duk a tsorace yake. Kamar daga sama yaji ta ce "Kawo gaskiya bana son shi, kawai iyaye na nake son a kawo mini ko akai ni wajansu amma ba zan aure shi ba" Innalillahi wata zufa ce ta shiga yankowa Adnan ya kasa cewa komai sai kansa da ya sunkuyar zuwa ƙasa. "Yarona Adnan kada kaji komai, ina son ka kira wasu naka muyi magana ta fahimta batun ƴar Baba ka barta akwai ƙuruciya kaji ko?" A sanyaye Adnan ya yi musu godiya kana yabar gidan. Ikon Allah ne kawai ya kai Adnan gida yana zuwa wani zazzaɓi ya rufe shi jikinsa sai rawa yake, barci ya gagari idanunshi rashin Afra tamkar rasa ransa ne. Da gari ya hawaye ya kira Abbi ya faɗa masa komai tunda ya san Abba ba zai ɗauki abin serious ba. Ya kira Uncle Khabir tare da Uncle Mustapha ya faɗa musu komai. Abu kamar wasa har Abbi ya yi dirar mikiya a ƙauyen shi da Salmanun-faris Adnan bai iya cin komai ba, ya fito cikin ƙyakkyawar shiga ta amy colour ɗin shadda wacce ta yi masa kyau. Lokacin suna ƙofar gidan Hakimi Salman na cikin mota yana vedio call da Mami little nayin dry. Ganin Adnan ya sa Abbi ya yi Sallama dasu Hakimi idanunshi akan Adnan ya ce "What happing to you son? You looks so Lean and weak" murmushi kawai Adnan ya yi ya ce "Am okay Abbi ya mutan gidan?" "Lafiyarsu lou har little,tare muke da Salman ya dawo garin" shiru Adnan ya yi rabonsa da Salman har ya manta tun a ɗakin da Abra ta rasu, daman haɗuwar ƙarshe da sukai ba mai daɗi sukai ba, yasan zuciyar Salman ɗin cike da jin zafin shi. "Muje mota mu ƙarasa ko?" "Abbi a ƙasa za a shiga" Abbi ya ce "Ohh to bari na kira Salman" Salam na cikin mota Abbi ya bubbuga yana kiran sunansa. "Yes Abbi" buɗe motar da zai yi idanunshi ya sauka akan Adnan wanda yake tsaye ya zura hannunsa a cikin Aljihu. Fitowa ya yi shaddar jikinsa na ƙara wacce take iri ɗaya data Abbi, shi bai san me ya kawo su ƙauyen ba, bai taɓa tunanin zai haɗu da wannan mugun mutumin ba da bai zo ba. Babu wanda yaiwa ɗan uwansa magana Abbi na lura dasu bai ce komai ba, duk da har yanzu babu wani babban dalilin daya sanya suke hakan a garesa zai ma iya ɗauka ko rashin sabo da juna ne. A haka Adnan da Abbi na gaba Salman na baya shima hannunsa a Aljihu yana ƙarewa ƙauyen kallo har suka isa ƙofar gidan su Afra daman kawon nata yana nan. Iso akai musu suka zauna saman tabarma Salman bai shigo ba ya tsaya ɗaukan wayar Ammi dake tsokanar shi. "Yaronku ya zo mana da zance wanda a garemu zance mai muhimmanci ne, duba da halin da yarinya ke ciki muna saka ran ta dalilinsa zamu samu iyayenta, shi ya sa na nemi ganin wani nasa mu tattauna akai da kuma ƙara jin ta bakin yarinyar a karo na biyu" Abbi ya jinjina kai gaba ɗaya hankalinsa ya yafi zuwa inda zai ga mai kama da Abransa ya fito a hankali ya ce "Masha daga namu ɓangaren muma haka abin yake, zamu samu yarinya ta maye gurbin ƴar uwarta Sannan mu samu bayanin da zai taimaka mana wajan gano asalin abin da yake faruwa, ina kuka tsinceta?" "To a yadda murgayi ya faɗa wata rana yaje wajan gari gefen jeji domin duba wasu magunguna na itace, acikin wannan lokacin ne kuma ya tsinci Yarinya a ƙasa ita kaɗai, sai a sannan ya fahimci kamar ƴan daba ne suka shigo cikin jejin domin sama sama yake yajin ƙarar bindigogi, ya ɗauki yarinya kawota wajan ƴan sanda suka ce sun bashi domin babu wasu iyayenta da za a samu, suka saka mata suna Afra wannan shi ne abin da muka sani" "Ikon Allah, Ubangiji mai yadda ya su" Nan Abbi ya faɗa musu yasa ya tsinci Abra da komai har kawo rasuwarta "Yanzu ina ita yarinyar take, ai Wannan abin bana wasa bane muna buƙatar ta cikin familynmu" Inna ta shiga kiran sunan ƴar Baba fitowa tayi a ɗaki cikin ƙyakƙyawan shiga mai kyau, Abbi ya tsora mata idanu dauriya kawai ya yi da bai je ya riƙeta ba, yana ƙara jinjina girman zatin Ubangiji da ƙuddirarsa. Zama tayi tana gai da Abbi suna haɗa idanu da Adnan ta tura masa baki, ya yi mata kallon ki tausaya mini. Kawo ya gyara zama ya ce "Ƴar Baba zan ƙara tambayarki a karo na biyu kina son Adnan zaki aure shi ya sadaki da iyayenka na gaskiya?" Afra na ƙoƙarin magana Sallamar Salman ta daki kunnenta juya sukai banda adnan da zuciyarsa take cike da fargaba. Mutuwar tsaye Salman ya yi lokacin da idanunshi ya sauka akan Afra bakinsa na rawa ya ce "Yaya...!!!"[11/16, 6:44 PM] Abk: A gigice Salman ya ƙarasa wurin da 'yar Baba ke zaune, ya rirriƙeta yana girgiza kai "Abbi ban gaya maka ba? Dama na san Angel ba ta mutu ba" ƙura masa idanu Afra ta yi, tana bin fararen idanuwansa da kallo, Masha Allah ga wani daddaɗan ƙamshi da yake fitarwa. "Talk to me Angel, dan Allah ki yi magana Yaya". A ɗan shagwaɓe Afra ta ce "Kai ka cikani" wani malolon takaici ne ya ƙule zuciyar Adnan, ya yunƙura yana ƙoƙarin ɓanɓare Salman daga jikin Afra. Hankaɗe shi Salman ya yi, yana sake rirriƙe Afra. Abbi ne ya ɓanɓaro Salman daga jikin Afra, yana faɗin "haba Faris, your sister is no more, wannan ba ita bace 'yar uwatta ce" Dafe kai Salman ya yi, ya rintse idanunsa yana sauke ajiyar zuciya, ya kwanta a jikin Abbi yana ta maida numfashi. Tsura masa idanu Afra ta yi, gaba ɗaya tausayin Salman ya kamata, lallai suna matuƙar so da ƙaunar wannan yayar ta ta. "Inna wannan ne baban nawa?" Tayi maganar tana kallon Abbi. Abbi ya yi murmushin ƙarfin hali yana ƙarewa Afra kallo, idan ba wanda ya yiwa Abra kyakykyawan sani ba, babu yadda za ayi kace ba Abra ba ce ba. "Ni ne na tsinci 'yar uwakki, na riƙeta na raineta, har zuwa lokacin da Allah ya karɓeta. Kamar ki ɗaya sak da ita, tabbas da a wani wurin na ganki zan iya cewa Abra ce" Idanun Afra ya cika da hawaye ta ce "To ina babana, suwaye iyayenmu? Me yasa suka yar da mu? Ko mu ba 'yan halak bane?" Abbi ya ce "Kul kika ƙara faɗar wannan maganar, ku 'yan halak ne nine nan uba a gare ku baki ɗaya". Sosai Afra ta sake fashewa da kuka tana girgiza kai. Abbi ya ce "Ka bita a hankali, haka Abra ma take da yawan kuka" A hankali Salman ya gyara zamansa ya jingina da jikin Abbi, yana cigaba da bin Afra da kallo. Ita kuwa yadda Salman ya kashingiɗa jikin Abbi ne abin ya burgeta, da alama shima shagwaɓaɓɓe ne. Kawun su Afra ya ce "To yanzu ya muke ciki da batun neman Auren yarinyar nan da kuka zo?". Nan da nan Afra ta sake tsuke fuska tana harar Adnan. Abbi ya ce "Wani hanzari ba gudu ba, me zai hana a jinkirta batun neman Auren nan, yarinyar nan ta samu nutsuwa a karo na biyu sai a sake tambayar ta. Sannan dan Allah ina roƙon wata alfarma, ina son ku bani Afra in tafi da ita gidana, tun da ina kan neman iyayensu, kuma ko ba komai Yarinyar da Abra ta rasu ta bari, zata samu shaƙuwa da kusanci da 'yar uwar mahaifiyarta". Aikuwa Inna ta ce "Ai wannan abu ba mai yiwuwa bane, a gaskiya ba zan iya bada Afra ba, shekara da shekaru ina rainon a bata rana tsaka a rabani da ita ba, gaskiya ba zan iya ba" ta ƙarasa maganar a hasale. Adnan dai ya rasa bakin Magana, sai bin su da ido kawai da yake yi, yayin da 'yar Baba ke ta zubar da hawaye, wanda ita kanta ba ta san dalilin hakan ba. Salman ba kunya ya tashi, ya ƙarasa gaban Afra ya zauna, ya tsura mata idanu wanda sai da hakan ya takurata, ta ji jikinta na tsuma, saboda kwarjinin da ya yi mata. "Yaya" ya furta a sannu. A hankali ta ɗago fararen idanunta ta kalleshi, duk da bata san dalilin kiranta da hakan ba. "A duk lokacin da nake tare da Abra, babban abin da yake jefani a cikin damuwa da tashin hankali, shi ne zubar hawayenta, kamar yadda ta rayu da son ganin Farinciki da murmushi a fuskata, dan Allah ki daina zub da hawaye, ina ganinki ne kamar Abranmu, ni haryanzu ban yadda ba ke ce Abra ba, dan Allah ki bimu gidanmu ki maye mana gurbin Abra, duk da mahaifiyata na kula da Little, amma little na kewar mahaifiyarta. Ko zaki so ta rayu ba tare da sanin kowa nata ba, kamar yadda kuka rayu a mabanbantan duniyoyi ke da 'yar uwakki, dan Allah ki Angel ki taimakawa rayuwarmu, we still needs you in our lives, Ni, Little, Mami Abbi da sauran su" Inna kuwa kuka ta fara yi, tana share hawaye, tana faɗin "Wallahi ba mai rabani da 'ya ta, ba in da zata je" Kawun Su Musa ya ce "Hajara, wannan kukan da kike kina ba za su tafi da ita ba ba shine masalaha ba, dan Yarinyar nan ba zata cigaba da zama ba tare da an san suwaye iyayenta ba, wataƙila tafiyar ta su da ita ya zamana silar sanin in da iyayenta suke ba" Nan aka shiga jayayya, ɓangaren su Abbi suna roƙon a basu Afra, Inna kuma ta dage ta ce ba zata bayar ba, Adnan ka sa jurewa ya yi, ya tashi ya bar gidan ya zauna a waje. Sai da Inna ta ga an fi ƙarfinta, sannan ta amince ta ce sai an je wurin mai gari ayi abu a hukumance, kar a gudar mata da 'ya. Haka kuwa aka yi, aka je gaban maigari, aka kuma sake yin bayani, maigari ya sake jadadda musu bayanin yadda aka tsinci 'yar Baba da irin riƙon da marigayi ya yi mata. Nan Abbi shima ya kuma yi masa bayanin yadda ya tsinci Abra a daji wurin yaƙi, tare da nuna musu hotunan Abra, tare da yi musu bayanin buƙatar sa na a bashi Afra.   Da haka sai da aka dangana da wurin 'yan sanda, na wannan ƙauye, in da file ɗin Afra tsintar Afra yake, aka sake kaɗe File, Abbi yayi amfani da ƙarfin kaki a wurin, aka yi rubutu tare da amincewa zai tafi da Afra. Sai bayan la'asar su Abbi suka koma gidan su Afra, nan Baffa suka tabattar mata da cewa, an bawa Abbi izinin tafiya da Afra. Ita kanta Afra gaba ɗaya ta kiɗime, da jin wannan batun, tana da burin ganin iyayenta a rayuwarta. Salman kuwa ji yake tamkar Abran sa ce ta dawo rayuwarsa, babban jin daɗin sa shi ne tafiya da za su yi da Afra gida. Inna ta rungume Afra tana ta kuka, saboda sabo, shi kansa Yaya Musa sai da ya yi kuka, saboda 'yar Baba akwai shiga rai, tsawon shekarun da ta yi a tare da su, ba su taɓa rabuwa tsawon lokaci ba, sai dai yanzu rana tsaka an musu fin ƙarfi an raba su da ita. Haka Inna ta haɗawa Afra kayanta, tana kuka Afra na kuka su Abbi suka taho da ita. Yau Little rikici take ji, saboda zazzaɓi da yake ɗan damunta, Mami sai fama take da ita amma sai koke koke take yi, da ƙyar ta samu ta yi bacci, ta kwantar da ita a falo, ta shiga kitchen a gurguje tana gabatar da ayyukanta, dan tun da Abra ta yi Aure, ba ta yadda a kawo mata mai aiki ba, saboda ba ta son ƙazanta. Tana girki tana Mamakin yadda aka yi Su Abbi suka daɗe haka ba su dawo ba, wayarta ta ɗauka ta kira Abbi, amma bai ɗaga ba, ta kira Salman, shima sai da ta yi masa kira biyu sannan ta samu ya ɗaga. "Hello Mami, Ina daughter na?" "Kai na kiraka in ji ya akai na ji ku shiru, amma kana mini zacen daughter". Faris ya ce "Mami muna nan tafe da wani abin mamaki mai girgiza zukata". Saroro Mami tayi ta ce "Faris bana son shirme, wane irin abu ne haka?" Jiki a sanyaye Faris ya ce "Mami ki kwantar da hankalinki, muna Lafiya mun kusa shigowa cikin Kano insha Allah". "To shikenan, Allah ya kawo ku lafiya" ta ajiye wayar tare da komawa wurin da ta ajiye Little amma ba ta nan. Da sauri ta ƙarasa tana ɗaga filon kujera, amma ba ts ga Little ba. "Ki daina wahalar da kan ki, ni na ɗauketa kin ajiye yarinya a kan kujera, idan ta tashi ta faɗo baki da asara, ko da yake ba abin mamaki bane, ita ma zaki mata irin riƙon da ki ka yiwa babarta ko?" Cewar Salima da ke wa Mami Magana cike da gadara. Wani marurun takaici ne ya tokarewa Mami wuya, amma cike da salo na goggaun matan da suka kwana biyu a duniya, ta yi murmushi ba ta tankawa Salima ba, dan ba ta fi sa'ar Abranta ba, ta nemi wuri ta zauna a kan kujera, ta fara cin Abincin ta. Salima ta so Mami ta tanka mata, ta yaga mata rashin mutunci son ranta, amma sai ta ga saɓanin abin da ta yi tunani. Mami ta cigaba da kallo, tana sipping tea, suka jiyo Little tana ta tsala kuka, daga sashin Salima, da sauri Salima ta tafi ta ɗauki Little, sai dai juyin duniya, amma little ta ƙi yin shiru, sai cilla ƙafafuwa take tana rintse idanuwa, ba shiri ta fito da ita a kafaɗarta, tana miƙawa Mami ita. Maimakon Mami ta karɓeta sai ta miƙe, ta bar falon. Salima ta rasa yadda za ta yi da Little, gashi ita ba ta saba da kukan yaro ba. Tun a hanya suka rabu,  Adnan ya nufi Kaduna, dan zuciyarsa ba zata iya jure cigaba da kallon Afra tana furta ba ta son sa ba, yana ji yana gani, Abbi Salman, da Afra suka nufi Kano, sai dai Adnan tun kan ya ƙarasa Kaduna, wani irin zazzafan zazzaɓi ya rufe shi, gaba ɗaya al'amura sun cakuɗe masa, bai san ya zai yi ba idan har ya rasa Auren Afra a wannan karon, bai san abin yi ba. 'Allah sarki Abra, a kallon Farko da na yi mata, na ga tsoro a fuskarta, bayan nasarar kauda tsoron fuskarta da na yi, na maye gurbinsa da tsananin soyayyata a zuciyarta, sai dai kash na yi wautar da na sanya ƙiyayyata a zuciyar Abra, har kan ta rasu take sanar mini da bata ƙaunata, Allah ya jiƙanki matata ya yafe mini, Allah ya sa 'yar uwakki ta yadda ta Aureni' yayi Maganar yana zubar da hawaye. Afra tsayawa ta yi tana ƙarewa harabar gidan kallo, da ganin yadda sojoji ke kaiwa suna komowa a harabar gidan, ta jinjina Arziƙi da Allah ya yiwa mariƙin Abra, sai dai jikinta duk a sanyaye yake, dan tun yanzu kewar ƙauyensu ta fara damunta, sai dai ba ta da burin da ya wuce ace ta sadu da iyayenta, komai talaucinsu komai muninsu. Kukan little ne ya karaɗe gidan, Abbi ya shigo falo da sallama, ya tarar da Salima tana tsaye tana ta jijjiga little da ke tsala uban ihu. Ya ƙarasa ya karɓeta a hannunta, yana faɗin "Garin yaya aka barta take kuka haka?". Salima ta ce "Oho, ajiyeta ta yi a falo tai tafiyarta ta barta" Abbi ya karɓeta, ya nufi sashin Mami a fusace "Na'ima wane irin sakarci ne haka, zaki tafi ki bar Yarinya tana kuka a falo, kin san ƙyuya take kin barta da Salima sai kuka take mata, yanzu da tsautsayi ya sanya mun taho da mahaifin yarinyar nan, haka zai zo ya tarar da ita tana kuka". "Kar ka sake yi mini tsawa Khamal, baka san maiya faru ba kawai ka zo ka sani a gaba da faɗa, kar ka kuma yi mini tsawa, bani yarinyata, kuma Wallahi matarka ta kuma ɗaukar mini ita saina wanka mata mari" ta ƙarasa maganar tare da fizge little daga hannunsa. Shiru Mami ta yi, ta tuna watarana da ta taɓ haɗa baki da ƙawarta suka yiwa Abra sharri, har Major ya mareta, ashe haka Abra take ji idan ta yi mata ƙazafi. Wasu hawaye masu fitowa da ɗacin zuciya suka faa sakowa saman kuncinta. Abbi ya yi ajiyar zuciya ya ce "Ki zo muje falo, ki ga wani abu". "Ba abin da zan gani, kaje ka ƙyaleni kawai" Major ya ce "Abin yana da mahimmanci, ki zo muje". "Kaje ka nunawa matarka bani ba, ita ya dace taga abu mai mahimmanci daga gareka bani ba". "Ko da kuwa abin da ya shafi Salman ne ko Abra?"yai Maganar yana kallonta. Sai kuma jikinta ya yi sanyi, Abbi ya sanya hannu ya janyo hannun Mami zuwa falo. Afra kuwa tun da ta shigo, tangamemen hoton Abra ne da Salman ya yi mata maraba, babu yadda za'ai ka kalli hoton kace ba ita bace a jiki. Jikinta ne ya hau rawa tana nuna wa Salman hoton. Salman ya taka ya ciro hoton ya miƙawa Afra ya ce "This is your sister, we are really missing her" yayi maganar ba tare da ya iya tsayar da hawayen da suka taho masa ba. Salima kuwa bin su ta dinga yi da ido, tana son tayi magana, amma ta kasa magana, saboda yadda Salman ke mata kwarjini, sam yaron baya sakar mata fuska a matsayinta na matar mahaifinsa. "Yanzu ta mutu? Yayata ce ko ƙanwata ce, ko mu biyu ne? Babu wanda ya sani sai Allah, me yasa ban haɗu da ke kan ki mutu ba? 'yar uwata me yasa kika tafi ban ganki ba, a rayuwata ace ko sau ɗaya naga jinina, yanzu idan ba a gano iyayenmu ba fa, shikenan kin mutu kin barni ni ka ɗai haba 'yar uwata" tamkar mahaukaciya, haka Afra take gunjin kuka, Salman ya karɓe hoton yana share mata hawaye, ganinta yake ba ta da banbanci da Afransa. Mami ce ta fito tana hura hanci, hannunta ɗaya riƙe da Little, ɗaya kuma yana cikin na Abbi. Wata irin mummunar faɗuwar gaba ce ta ziyarci Mami, jikinta ya hau rawa bakinta ma haka. Nema take ta saki Little, Abbi yai sarin karɓeta daga hannunta. "Major me nake gani? Abra ce fa? Abra ce ko baka ganinta ne?". "Calm down please, ba Abra bace ba kalleta da kyau". Cikin tsawa ta ce "Ta yaya zaka cemini ba Abra bace, kalleta fa a kusa da Faris, Abra ba ta mutu ba kenan, ko kuma fatalwa ce" Salman ya taso da sauri ya karɓi Little, Mami kuwa gaba ɗaya ta birkice, Abbi ya zaunar da ita, amma ta kasa nutsuwa, sai nuna masa Afra take tana cewa Abra take gani. Abbi ya yiwa Afra nuni da ta zo, Afra ta taso ta ƙaraso gaban Mami, aikuwa ta rirriƙeta ta ce "Abrana, Wallahi Major Abra ce kalleta fa". Abbi ya kalli Afra ya ce "Afra, ga maman 'yar uwakki, ita ce ta riƙe Abra, wannan jaririyar kuma, ita ce wadda ta rasu ta bari, ki gaya mata ke ba Abra ba ce". Afra ta riƙo hannun Mami cikin nata, tana hawaye ta ce "Mamanmu, ba 'yar ki ba ce wadda ki ka rasa, amma zan iya cewa 'yar ki ce ta dawo gareki, kamar 'yar uwata nima tsinta ta aka yi, aka riƙeni a wani ƙauye har na girma, mijin 'yar uwata ne yaje ƙauyenmu ya ganni, shima da fari cewa ya yi, ni matarsa ce amma daga baya ya gano, ba ita bace, ni sunana Afra ana ce mini 'yar Baba a garinmu, ni a ƙauye na tashi, Abranki kuma a birni, mijin Abra ya ce ta fini hankali da nutsuwa, da rashin hayaniya, ni kuma... Sai kuma tai shiru tana murmushi, a lokacin da hawaye ke zuba daga idonta. "Major yanzu kana nufin ba Abra na ba ce?". "Ba Abranki ba ce, 'yar uwatta ce" Nan Abbi ya yiwa Mami bayanin komai. Mami ta rungume Afra a jikinta tana wani irin kuka, tamkar zata shiɗe, Afra ma ta rungumeta tana kuka. Salima ta ce "Sweetheart, nifa ban gane meke faruwa ba, wannan ba ita ce 'yarka ta hoton nan da aka ce ta mutu ba?" Abbi ya ce "Ba ita bace, zan miki bayani". Adnan kam ko da ya isa garin Kaduna, a Asibiti ya samu masauki, saboda yadda zazzaɓi da ciwon kai suka rufe shi, sai da aka sa masa ruwa sannan ya wuce gida. Ko da Adnan ya jewa Hajiya Mama da Abba  abin da ya faru Abba ya ce "Lallai wannan lamari akwai ban mamaki a cikin sa, dan haka zuwa jibi insha Allah, zan shirya in je Kano da kai na". Adnan ya ce "Dan Allah Abba idan ka je kace su bani Auren Afra, zan iya rasa raina idan ba sameta ba". "In ka rasa ranka Allah ya jiƙanka, ai Nagode Allah da ya sanya yarinyar ta ce bata sonka, ni dai Adnan ba zan kuma yin jagoranci a nema maka Aure ba, da mahaifiyarka ma ta mutu dangana na yi, kaima in ka mutu Allah ya jiƙanka". "Abba dan Allah, kai mini rai, na tuba nabi Allah na bika, ba zan sake maimaita kuskuren da nayi a baya ba" "Sai kuma kayi Adnan, idan har ina raye babu mai aura maka 'yar uwar Abra, kaje can ka nemi wata 'yar ka aura, amma ba 'yar uwar Abra ba". Mama ta ce "Dan Allah Yallaɓai ka sassautawa yaron nan, kalli yadda ya koma" Abba ya ɗaga mata hannu ya ce "Wannan yaron ba abin tausayi bane, kuma na gama Magana, kuma idan har ka takura sai sun baka yarinyar nan, zan tona maka Asirin irin riƙon da ka yiwa 'yar su" haka Adnan ya dinga kuka wiwi, kamar wanda uwarsa ta mutu. "Ok Zuwa next week nake son Visa don Allah, abu ne na gaggawa ya taso mini, da yake buƙatar in je da kaina" Hajiya Saudat ta zubawa doctor ido, tana saurarensa, sai da ya gama wayar sannan ta kalleshi ta ce "Wai ni don Allah doctor, sai yaushe zaka bawa iyayen yaron nan damar zuwa su ganka ne?" "Sai na dawo daga tafiya" "Ni ban ma tambayeka ba, ina zaka je naji kana maganar visa?". Doctor ya gyara zamansa ya ce "Dubai zanje" hantar cikinta ce ta kaɗa, ta dube shi a firgice ta ce "Kaje Dubai kayi me?" "Wurin wanda na ajiye zani, ai kin fi kowa sanin ina da ajiya a can". "Me kake nufi? Me kake nema a can da babu a nan?". Bulama ya ce "Abu mafi mahimmanci da kika sa na wofantar, dole in gano alaƙata da yarinyar da nake bincike a kai, dan haka dole in tafi Dubai" Gaba daya ta rikice ta ce  "Amma ka san zuwanka Dubai na nufin tonuwar Asirinka wataƙila ma da karayar arzikinka?" "Ban damu ba, ida har abin da na rasa ne zai dawo gareni" Wayar Hajiya Saudat ce ta fara ringing, jiki na rawa ganin lambar Meenal ce ta ɗaga. "Muna magana da mahaifiyar Meenal ne?". "Eh nice" "Ku zo nan Asibitin Health well, yarinyarki babu lafiya, ana buƙatar sa hannunku ku zo ku biya kuɗ ayi mata aikin gaggawa" ₦300 kacal, a biya kan a karanta dan Allah 08081012143 [11/17, 2:50 PM] Abk: A kiɗime Hajiya Saudat ta ce. "Wacce Meenal ɗin? Ban gane ba bawan Allah, me ya samu ƴata?" "Idan kika zo za ki fahimta, amma fa ana buƙatar ku yi gaggawar zuwan, saboda gudun kar a rasa rayuwar ta." Suɓucewa wayar ta yi daga hannunta ta faɗi ƙasa, cikin gigita ta ce. "Doctor wai Daughter ce babu lafiya, tana health well ana buƙatar mu je mu saka hannu za a yi mata aiki." Babu yabo ba fallasa ya ce. "Allah ya ba ta lafiya." "Haba Doctor, ya na ga kamar ba ka damu ba, ƴarmu fa Meenal nake magana a kai." "Damuwar da nake ciki ta fi ƙarfin wannan, ki ɗauki ATM ɗina ki je a yi duk abin da ya dace." Bai jira amsar ta ba ya fice daga ɗakin, zuciyarsa cike da tunanin wanne abu ne yake damun Meenal da har ya kai sai an yi mata aiki ba tare da sun sani ba? Da kallo Hajiya Saudat ta bi shi cikin bugawar zuciya, mamaki da fargaba sun cika mata fal a cikin ranta, yau Bulama ne take masa maganar Meenal tana cikin mawuyacin hali na ciwo amma ya kaɗa ƙafarsa ya yi gaba? Shi da ko ciwon kai take kusan tare suke jinyar saboda yadda yake nuna damuwarsa tare da ba ta kulawa. Lallai dole ta miƙe ta nemi mafita gami da kawar da abin da ya ɗauke masa hankali daga gare su. Cikin matuƙar tashin hankali ta zari gyalenta da handbag da wayarta dake yashe a ƙasa ta yi waje zuwa asibitin da aka ce mata Meenal tana can. Ɗakin Abra Abbi ya sa Salima ta gyara wa Afrah, bayan ta gama ta dawo parlour inda duk suke ta ce. "Our new daughter na kammala miki gyaran dakin, sai ki shiga ki kwanta ki huta." Murmushi Afra dake riƙe da Little ta yi, ba tare da ta ɗago kanta ba ta ce. "Na gode sosai Aunty." Cikin son cusa kai Salima ta ce. "Haba mene abun godiya don Uwa ta yi wa ƴarta abu?" Murmushi kawai Afra ta yi ba ta ce komai ba, sai shafa fuskar little take cikin ƙaunar ta da ta mamaye zuciyarta lokaci ɗaya, farinciki mara iyaka take ji a cikin ranta, yau ta ga jininta a duniya, Allah Sarki Baba, dama yana nan ya ga wannan ranar mai cike da tarin farinciki a gare su. Mami kuwa taɓe baki ta yi jin abin da Salima ta faɗa, Abbi kuwa murmurshi ya yi cikin jin daɗi ya ce. "Daughter, tashi ki je Antinki ta nuna miki ɗakinki." Cikin girmamawa ta ce. "Toh." Salman dake ta kallon ta ya miƙe tare da ɗauke little daga cinyarta, cikin murmurshi ya ce mu je na raka ki yayata." Da sauri ta kalle shi cikin mamakin jin ƙato da shi ya ce mata Yaya, shi ma kallon ta yake, hakan ya sa idanuwansu suka sarƙe cikin na juna, da sauri ta janye nata saboda wani irin abu da ta ji ya daki zuciyarta, bayan ya kai ta ɗakin yana ƙoƙarin fita ta ce. "Ka bar mini ita a nan." Fahimtar da ya yi little take nufi ya sa ya ce. "Kina buƙatar ki yi wanka a yanzu, ita kuma rigima ne da ita, kina ajiye ta za ta iya farkawa tay ta kuka, idan kin yin wankan sai Mami ta kawo miki ita." Gyaɗa masa kai ta yi ba tare da ta bari sun haɗa ido ba har ya fice, haka kawai ta ji suna mata kwarjini shi da Abbi, shi ya sa ta nutsu kamar ba ita ce Ƴar Baba gagarau ba. Bin ɗakin ta shiga yi da kallo, ƙawatuwar shi da yadda ya tsaru ba ƙaramin burge ta ya yi ba, sai tambayar kanta take yi wai wannan haɗaɗɗen ɗakin duk nata ne? Yau ita ce za ta kwana a birni gidan ƴan gayu mai kyau irin wannan, ba don halin kewar su Inna da take ba da sai ta raba dare tana tsallen murna a kan wannan luntsumemen gadon. "Allah Sarki Innata, na san yanzu suna can suna kuka da alhinin tafiyata ita da Yaya Musana." Ta faɗi haka a fili ƙwalla na cika mata ido. A hankali ta zauna a bakin gado tana ƙara bin ɗakin da kallo, Adnan ne ya faɗo mata a rai, turo baki ta yi kamar yana gabanta, lokacin da ta tuno yadda yake yi mata magiya akan ta so shi. Salima ce ta shigo ɗakin bakinta ɗauke da sallama, bayan ta amsa mata ta ajiye wata leda mai ɗauke da kayan bacci a kusa da Afra tare da faɗin. "Ga kayan bacci nan idan kika yi wankan sai ki saka." A hankali Afra ta ce. "Toh na gode, amma na taho da kayana ma suna cikin Mota ba a shigo da su ba ne." "Okay, bara zan yiwa Honey magana sai a shigo miki da su yanzu, ki saki jikinki kin ji, nan ma gidanku ne, bari na kawo miki abinci.' Gyaɗa mata kai ta yi ta ce. "Ina zan ɗebo ruwan da zan yi wanka da alwala?" Murmushi Salima ta yi ta ce. "Duk akwai a cikin toilet, mu je na raka ki, ki gani." Miƙewa ta yi ba tare da ta ce komai ba, duk wannan kanbanbar da Salima take ba ta wani yi mata ba, sai ta ji ta fi son farar matar nan mai kama da Salman. A toilet ɗin ma lalacewa ta yi wajen kallon yadda aka ƙawata shi, kasa ɗaurewa ta yi ta ce. "Yanzu nan ne bayin gida kamar wani ɗaki? Taɓ, ai da ni kaɗai na shigo fita zan yi na ce ban ga bayan gidan ba, na saba da namu na ƙauye ko rufi babu balle siminti." Murmushi Salima ta yi ta nunnuna mata duk abin da ta san zai mata wahalar ganewa da yadda za ta yi amfani da shi. Bayan ta fita ta ce. "Wai aljannar duniya, har da wani fanfon ruwan zafi? To shi daga ina yake zuwa kuma? Ko ta cikin ƙasa ake dafa shi?" "Khamal wai me kake nufi da ni a gidan nan ne? Ina cikin damuwar rashin Abra amma mai kama da ita ta zo sai kaita tura waccan matar tana yi mata abubuwa? Alhalin gani a zaune." "Na sani ko ita ma za ki ce ƴata ce karuwa ta haifa mini? Ki azabtar da ita kamar yadda kika yi wa Abra." Cikin hawaye Mami ta ce. "Me ya sa kake son dawo da abin da ya wuce ne? Ai babu wanda ba ya yin kuskure a rayuwarsa." Wani kallo ya watsa mata ya fice ba tare da ya kuma magana ba. A zuciye Mami ta ce. "Kuma yarinya a gurina za ta zauna ba a gurin wata baƙar yarinya ba, sai dai a yi duk abin da za a yi. Ban da neman fitina yarinyar kusan sa'ar ta amma ita za ta riƙe ta, ita ma shegiyar da neman gindin zama har da wani ce mata ƴarta, ko a gidan uwar wa ta haifi kamar ta oho?" Ta ƙarashe maganar tare da jan tsaki. "Doctor me yake damun ƴata da har ya kai a yi mata surgery without knowing us?" Hajiya Saudat ta tambaya a gigice. "Mu ƙarasa office mana sai mu yi maganar." "Ba ni da nutsuwar ƙara taku ko nan da can? Please tell me what happened to my daughter?" Ta yi maganar cikin kuka. Cikin tausawa likitan ya ce. "Ki dai daure mu ƙarasa office ɗin, kin ga nan reception ne, bai dace mu yi magana ba." Ba ta kuma magana ba ta bi shi suka tafi. Bayan sun shiga sun zauna ya ce mata. "An yi mata abortion ne, sai kuma aka samu matsala ta samu raptured utherus, mahaifarta ta ragargaje gabaɗaya, yanzu za a yi mata aikin gaggawa a cire t....." "Innalillahiwa'inna'ilaihirrajj'un, na shiga uku! Meenal ɗin za a cirewa mahaifa? Mahaifa fa ka ce Doctor?" "Eh, ta sha maganin abortion ne wanda ya wuce ƙa'ida, hakan ne ya janyo mata wannan matsalar, ba don da wata Nurse da take aiki a nan asibitin suka zo ba ma da ba za mu karɓe ta ba." Gumi ne ya shiga yankowa Hajiya Saudat ta ko'ina a jikinta, cikin rawar murya ta ce. "Doctor, kuma babu wani abu da za a iya yi dole sai dai a cire mahaifar?" "Babu." Ya faɗa a taƙaice. A dole ba bisa son rai ba Hajiya Saudat ta saka hannu aka yi wa Meenal aiki, wadda ke cikin mawuyacin halin ciwo. Ba ƙaramin tashi hankalin Hajiya Saudat ya yi ba da ta ga Meenal, Saboda yadda ta ɗashe ta yi fari fat alamun babu jini a jikinta, ga wata rama da ta yi kamar wadda ta daɗe tana jinya, tsabar galabaita ko magana ba ta iya yi, sai hawaye kawai take. Washegari bayan Salima ta gama haɗa breakfast ta shiga ɗakin Afra don ta taso ta. Tarar da ita ta yi har lokacin tana kwance tana bacci, saboda jiya ba ta yi bacci da wuri ba, kewar Inna da baƙunta sun hana ta. A hankali ta tashe ta, bayan ta shiga toilet ta fice ta ɗauko mata sabuwar abaya da undies a cikin kayan lefenta, ta haɗo da su lotion da powder ta kawo mata. Cikin mintuna ƙalilan Afra ta shirya, kasancewar ta mai kazar-kazar ba kamar Abra ba. Sosai ta yi kyau cikin bak'ar abayar da ta haska farar fatarta. Kallon kanta ta tsaya yi a mirror cikin murmurshi, gani take ba kamar ba ita ba saboda kyawun da ta ga ta yi. Sai da Salima ta ƙara dawowa ta kira ta sannan suka fita tare. Abbi na zaune a dinning suka shiga parlour'n, ɗagowa ya yi yana kallon su tare da amsa sallamar, cikin girmamawa Afra ta tsugunna ta ce. "Ina kwana?" "Lafiya ƙalau, ya kwanan baƙunta?" Ya amsa cikin fara'a. "Alhamdulillah." Ta faɗa cikin sanyin muryar da ta ara daga jiya, don sosai ta ji jikinta ya yi mata wani irin sanyi ba tare da ta san dalili ba. "Ƙaraso mu karya." Cewar Salima tana nufar dinning area. "Bari na fara gaishe da Mami idan ta tashi." Cikin jin haushin abin da ta faɗa Salima ta ce. "Ai ko da ƙyar in ta tashi." "Ta tashi, mu je na raka ki." Abbi ya faɗa cikin jin daɗin yadda ta nuna girmamawa ga Mami. Da kallo Salima ta bi su zuciyarta cike da baƙin ciki, ta gama yi wa yarinya hidima sannan tana fitowa ta ce wani za ta gaishe da Mami? Lallai dole ta tashi tsaye don ganin ta ja Afra jikinta sosai, ta san hakan zai ƙara ninka ƙaunar da Abbi yake mata. Mami tana shirya little suka shigo ɗakin, da fara'a ta ɗago tana duban Afra, Abbi kuwa juyawa ya yi ya koma parlour. "Daughter har kin tashi?" Gyaɗa mata kai ta yi tare da gaishe ta, rungume ta Nai'ma ta yi hawaye na cika mata ido saboda tuno Abra da ta yi, don ganin Afra cikin abaya ba ƙaramin ƙara kamar su da Abra ya yi ba, kasancewar ta ma'abociyar saka ta. "Lafiya ƙalau daughter, dafatan kin tashi lafiya?" "Lafiya ƙalau." Ta amsa tare da ɗaukar little, kamar wadda aka faɗawa yarinyar sai ba ta yi mata ƙiwa ba, sai ma dariya da ta shiga bangala mata. Socks Mami ta ɗauko ta fara saka mata tare da faɗin. "Lallai yarinyar nan, wato ke ba kya yi wa iyayenki ƙiwa ko? Da wani ne ya ɗauke ta da tuni kin cika ɗakin nan da kuka da ciccilla ƙafafuwa." Murmushi Afra ta yi tare da shafa sumar kan little, tana jin duk duniya babu abin da take so sama da yarinyar. Tare da suka koma parlour da Mami, lokacin har Salima da Abbi sun fara karyawa. Cikin son gwaninta Salima ta miƙe ta yi serving ɗinsu, don a gaban Abbi biyayya da girmamawa take yi wa Nai'ma. Ciki-ciki Mami ta ce. "Thanks." Abbi bai ji daɗin hakan ba, amma ya danne saboda Afra dake gurin bai nuna ba, fahimtar hakan ya sa Salima sakin murmushi cikin jin daɗi, dama abin da take so kenan a kodayaushe, Abbi ya dinga ganin lefin Mami a zamantakewar su. Tsurawa kayan breakfast ɗin ido Afra ta yi, a kallon farko da ta yi masa ta ji yawunta ya tsinke, ga ƙamshinsa da ya cika mata hanci, tun kafin ta ci ta san ba ƙaramin daɗi zai yi ba. Inna da Yaya Musa ne suka faɗo mata a rai, ji ta yi dama a ce tare da su za su kwashi wannan daɗin, ga masoyin nata bread ƙatoto a gurin. A hankali ta ɗauki cup ɗin da Salima ta haɗa mata tea ta yi Bismillah ta fara sha, daidai lokacin Salman ya shigo parlour'n. Gabansa ne ya yanke ya faɗi ganin Afra, don gani ya yi tamkar Abra ce zaune a gurin, hakan ya tuno masa lokuta da dama da suke yin breakfast exactly like this da Abra. Addu'a ya yi mata sannan ya ƙarasa dinning area ɗin cikin sanyin jiki. Bayan ya gaishe da su Abbi ya ɗauki little dake bacci sannan ya zauna. Kamar yadda Salima ta yiwa kowa haka ta tashi ta yi serving ɗin shi. Ba yabo ba fallasa ya yi mata godiya. A hankali Afra ta ɗaga kyawawan idanunta ta kalle shi tare da sakar masa murmushi, mayar da mata murmushin ya yi tare da yin ƙasa da murya ya ce mata. "Morning Angel, da fatan kin tashi lafiya?" "Lafiya ƙalau" Mami dake lura da su ta yi gyaran murya, hakan ya sa Salman haɗiye abin da yake son faɗa, sanin da ya yi ƙa'idar Abbi ne idan ana cin abinci ba a magana idan ba dole ba, gyaran muryar da Mami ta yi kuma ya san tuna masa hakan take. Bayan kowa ya gama cin abincin Abbi ya dubi Afra ya ce. "Yata a ina kika tsaya da karatu ne?" "Na yi Candy." Gyaɗa ya yi ya ce. "Da kyau, islamiyya fa?" "Muna izifi Ashirin." "Masha Allah, yanzu kina da takardun WAEC da NECO?" "Eh, na taho da ita ma, Inna ta haɗo mini a cikin kayana, amma NECO kawai na yi." "Okay." Abbi ya faɗa tare da mayar da duban shi ga Salman ya ce. "Idan Allah ya kai mu gobe Monday ka je ka yi mata registration a school ɗin English Academy, saboda ta samu bakinta ya faɗa a Turanci kafin ta shiga University, idan an fara registration na JAMB sai a yi mata, Islamiyya ma ka kai ta wadda kuka yi ta cigaba da karatun a can." "Insha Allahu Abbi." Cikin matuƙar farinciki Afra ta ce. "Na gode sosai Abbi, Allah ya ƙara girma da arziƙi." "Amin Daughter, babu komai. Yanzu sai ka kai ta, ta gaishe da su Ammi, idan kun dawo sai ku je tare da Auntinku ku yi mata shopping na kayan sawa da sauran abubuwan amfani." Ya ƙarashe maganar idanunsa a kan Salman. Godiya sosai Afra ta yi masa har da hawayenta, ta so a ce Baba yana raye ya ga wannan ranar, don ba shi da buri da ya wuce na ganin ta yi karatu mai zurfi na addini da na boko, karamcin da Abbi ya nuna mata a yanzu ya ƙara tabbatar mata da an yi wa ƴar'uwarta riƙon mutunci a gidan, hakan ya ƙara kwantar mata da hankali akan zamanta a gidan. Daren jiya Adnan bai samu ishashshen bacci ba saboda damuwar dake cunkushe a cikin ransa gami da fargabar rasa Afra. Raba dare ya yi yana kallon hotunan Abra cikin zubar hawaye tare da surutai, ta tafi ta bar shi cikin tsananin kewa da ƙaunar ta, ya samu wacce yake ganin za ta ɗebe masa kewar ta amma ita ma yana ƙoƙarin rasa ta. Sai bayan Sallar Asuba wani wahalallen bacci ya ɗauke shi, bai farka ba sai da goma ta wuce, ko sakkowa bai yi daga kan gadon ba ya lalubi wayarsa ya kira Mami, bayan sun gaisa ya ɓukaci ta ba wa Afra saboda muryar ta kawai yake son ji ko zai samu nutsuwa a cikin zuciyarsa, lokacin su kuma sun tafi gidan Ammi, cikin rashin jin daɗi ya yiwa Mami sallama, a ransa yana ƙudirce dole gobe ya yi wa Kano dirar mikiya. Littafin kuɗi ne, don neman ƙarin bayani: 09047871750 [11/20, 7:09 AM] Abk: Washegari kamar yadda Adnan ya sanya a ransa haka ne ya kasance. Tun asuba ya shirya cikin wata shadda shampoo maroon colour ya murza hula duk da bata dame shi sosai ba, amma ganin weather ya sanya ya yi shiga mai kyau. Sai ƙamshin Pur oud yake lokacin daya fito gari ya yi duhu sbd hadarin dake kwance a garin Kadunan. Ba tare da sanin Hajiya Mama da Abba ba ya nufi Kano cikin duhun asuba sai gudu yake shararawa burinsa kafin 11 na safe ya yiwa Kano tsinke idanunsu ya sauka akan Afra ko ya samu sauƙin ciwon da zuciyarsa ke masa akoda yaushe. Cikin wannan tunanin ya ƙarawa motar giya. Afra na zaune cikin wata white-collared t-shirts tare da wani red cropped trousers ta ɗora wata red ɗin kinomo a saman kayan, tayi kyau sosai domin duk a cikin kayan da Abbi ya bada akai mata shopping ne. Hannunta riƙe da Aishatul-humaira wacce a kullum ƙara wayo take. Mami data fito ta ce. "My dear kinji daɗi Little bata miki halin nata, ko dai ta gane ke Mother ɗin ta ce?" "Wallahi Mami ina sonta sosai, bana son rabuwa da ita kamar muna kama ko?" Kafin Mami tayi magana Salman dake gyara zaman babbar rigarsa ya ce. "Dake da ita ban san wanda nafi so, ina tunanin burina ya kusa cika" "What are you saying Salman?" Ya shafa sajan fuskarsa yana basarwa ya ce "No Mami,ina breakfast ɗina?" Mami ta Harare shi ta ce. "Liar, It's like I heard you say something?" Ya girgiza yana zama kusa da Afra idanun shi akanta ya ce. "It seems that Mami's ear is starting to have problems. Amma breakfast na ce ta, yunwa zata hallaka miki ɗan yaro Mami" "Allah ya shiryaka Salman, yunwar ka kewa haka?" Ya marairaice fuska sosai wanda ya bawa Afra mamaki ya sanya ta buɗe baki tana kallon ƙato da shagwaɓa. Da ƙyar ya ce "Da gaske Mami yunwa na keji sosai, Yaya Please abinci" ya faɗa tare da juyawa ya kalli Afra wacce ke riƙe da Aishatul-humaira tana mata tsalle tsalle da ƙafa a cinya. Barin wajan Mami tayi cike da fatan samawa Salman nasara domin ta riga da taji abin da ya ce. "Why are shy yaya my angel?" Ya faɗa yana saka hannunsa zuwa haɓarta tare da juyo da fuskarta suka fuskanci juna. Fararen idanunsa masu kaifi wanda suke ƙara sawa Afra kwarjinin Salman a idanunta ya zuba mata ya ce. "Ba haka yaya Abra ke mini ba, na sama hira da yayata sosai wani lokacin daja hancina kamar like this" ya ƙare maganar yana jan hancinta cike da ƙaunar ta wacce lokaci guda ta mamaye dukkan zuciyar shi. Cikin siririyar muryar ta ta ce "Uhm to aini ban girmeka ba" ya lumshe idanunsa yana mai girgiza kansa kaɗan tare da tura hular kansa zuwa gaba ya ce. "Injiwa? Tsakanina da Abra good 3yrs ne, ke da Abra twins shekara ɗaya aka haife ku Kinga kin zama yayata" "Kuma na ganka ƙatoto ni kuma ƙarama" zuba mata gajiyayyun idanun shi ya yi yana karantar yanayin ta sosai kafin speaking calmly ya ce. "Sbd ni ne mijin ai" ta ware ido ta ce "me kace?" Ya girgiza yana miƙewa tsaye tare da ɗaukan Little ya ce "I'll explain later" kafin tai magana ya miƙar da ita tsaye ba zato taji ya jawota ɓarin jikinsa ya yi musu photo yana murmushi ya ce "My family my happiness, zuri'ar Salmanun-faris" ita dai bata fahimta ba, sai saurin zame jikinta da tayi zuciyarta na bugawa da ɗan ƙarfi. Dining room suka nufa a can suka samu Salima Abbi daman tun 7 yabar gida yin binciken asalin iyayen Afra da Abra. Jikin Salima na ɗan rawa ta ce "Salman my son bari na serving naka abinci" idanun shi akan Afra ya ce. "No thanks, Afra please serve me" ya faɗa fuska a kame. Salima bata so hakan ba domin gaba ɗaya Salman birgeta yake tana neman duk yadda da zata samu connection da shi amma ya toshe ba lallai idan yana mata kallon matar Mahaifin nasa ba. Afra tai serving nasa a nutse take har kar nan gudun kada ta kwafsa, ta nuna ƙauyancin nata shi ya sa ta kame kanta da kyau domin siyawa kanta martaba da ƙima a idanun jama'ar gidan. Ganin daga Afra har Salman abinci suke ci babu wanda yako kalli inda Salima take, ya sanya jiki a sanyaye ta miƙe kamar zata ɗauki Little wacce take barci a jikin Salman ta wani ƙanƙame shi da duk hannunta biyu sai kawai ta fasa da ɗan sauri tabar wajan. Suna cin Abinci Mami ta fito cikin kwalliya sai ƙamshi take, ganin Afra da Salman ya bata sha'awa. Ta ɗauki Little tare da bar musu wajan. Lokaci zuwa lokaci Salman ke satar kallon Afra yana jin kamar ya faɗa mata abin da ke zuciyarsa kada ya ƙara rasa damar shi a wannan karon. "I love You" Ya furta a hankali daidai yadda za taji da sauri ya ɗago kanta ta kalle shi ganin kamar ba shi ne ya yi maganar ba, yasa ta ɗauke taci gaba da cin abincin maybe kunnuwanta ne kawai suka ji haka. Murmushi mai laushi Salman ya yi kyansa na fita calmly ya kuma cewa. "Ina son ki Afra, and I ready to marry you....." "Kai da Afra har abada domin ta haramta a gare ka ni ne zan aureta" daga Afra har Salman suka ɗago kansu, ganin mutum dake tsaye ya sanya Salman yin murmushi wato tarihi zai maimaita kansa kenan. Jikin Afra na rawa ta miƙe tsaye domin bata tsammani ganinsa ba a daidai wannan lokacin. Ƙoƙarin guduwa take ya sanya hannu tare da cafkota idanun shi sun kaɗa tare da yin jaa sosai kamar gauta cikin rawar murya ya ce. "Ni nake son ki ƴar baba tun kina ƙauye, ni ne na yi sanadiyar zuwanki nan gida, kuma a shirye nake da aurenki idan kin amince Wallahi ina son ki Please don't say No!" "Wallahi bana son ka, ba zan taɓa son ka ba, koda zaka mutu, ni ka rabu dani ka takura mini" Innalillahi Adnan gani yake da wannan maganar gwara ta ɗauki wuƙa ta caka masa zai fi masa sauƙin fahimta. Cikin damuwa ya ƙara matsawa gareta tare da ɗora hannunta a saitin ƙirjinsa idanunsa na sauya kala yana cika da hawaye ya ce. "Ki taimaka, ki taimaki rayuwata Afra, ko baki so na ki aure ni haka, indai zaki zauna dani matsayin miji ban damu da rashin soyayyar ba. "Ni dai ka sakeni, ba zan iya auren wanda bana so ba, sbd ba zan masa biyayya ba ga mata nan da yawa a duniya haba" Tashin hankali ya bayyana akan fuskar Adnan yau shi ne mace ke wahalar da rayuwar shi har yake zubar mata da hawaye? Lallai soyayyar Abra tayi tasiri a zuciyar shi, Domin son da yake mata ya sanya ba zai iya rayuwa babu Afra ba a yanzu komai nasu iri amma me ya sa halinsu ya bambanta?. Yi ya yi kamar zai jawota jikinsa tayi saurin ja baya kusa da Salman hawaye na zuba a fuskar Adnan sosai ya ce. "Don darajar Allah ki duba halin da zuciyata take ciki, ki sassauta yanayin ki a kai na, ki bani dama na sauya tunani zaki so ni ina da tabbacin zan sauya miki ra'ayi da kanki zaki furta kina so na, zan fifitaki da sauran mata, zan baki farin ciki da duk abin da kikeso, zaki rayuwar ƴan ci a gidan Adnan Aliyu Matawalle..... I love You Afra, i love You to the rest of my life, I can't imagine life without you wlh ina son ki ba zaki taɓa samun wanda zai so ki kamar ni ba" Salman ya gyara tsaiwa tare da gyara zaman babbar rigarsa cikin nutsuwa ya kalli Adnan kana ya juya ya kalli Afra a hankali ya saka hannu ya kama nata cikin nutsuwa ya ce. "Look into my eyes yaya" kasa kallonsa tayi Ubangiji yana gani Salman mugun kwarjini yake mata, yana yiwa idanunta tasiri sosai ba kaɗan ba. "Please yaya" ya ƙara faɗa a taushashe har ƙamshin spraymintt mouth freshener ɗin bakinsa yana dokan hancinta wanda ya sanya tayi saurin lumshe idanunta. ganin da gaske ba zata kalle shi ba ya sanya gaba ɗaya ya tallafo haɓarta yana sauke mata numfashi a fuska kamar zai haɗe fuskokinsu ya ce. "I love You Afra, From the moment I first laid eyes on you, I knew you were a perfect match for me. I love everything about you. Ina son ki so mai yawa, ina kishin da zai ɗauke numfashin sarrafa rayuwata, kada ki yi mamakin ganin bamu daɗe ba, ina jinki tamkar yaya a raina, ki bani dama na bayyanawa kowa irin soyayyar da nake maki, bana son nayi zurfin cikin da nayi a kan Abra. I will be always by your side in good and bad times, in happy and sad moments… because I love you! Accept my request please yaya" Ya kama fuskarta da dukkan hannunsa wanda itama a lokacin ta buɗe idanunta tare zuba masa su. Tana son fahimtar da gaske wannan kyakkyawan farin ne yake son ta kuma yake son aurenta? "Please yaya" Ya marairaice fuska yana narke mata. Kasancewar rayuwar ƙauye tayi babu wanda kunya sosai a tare da ita bakinta kuma baya sarrafa wani abubuwan kafin ta faɗa. Muryar ta na rawa ta ce. "Ina son ka ni ma, kuma zan aureka in dai da gaske kake zaka aure ni" Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya Salman ya sauke yana ƙara riƙe fuskarta da kyau! Wani farin ciki na ratsa zuciyarsa. A fusace Adnan ya fisge Afra daga wajan Salman idanunsa na zubar da ruwa bakinsa da gaba ɗaya jikinsa suna rawa kamar ana kaɗa masa gangi ya ce. "Ƙarya yake Afra, ta ya ya zaki aure wanda ki ka girma yayanki ne shi bai dace ya zama mijinki ba, ni ne daidai da rayuwar ki" ya faɗa yana jawota jikinsa sbd zafin da zuciyarsa ke masa. "Don't try to hug the girl I'm going to marry again, na fika hauka zafin kishina yafi naka, kuma ka kusa daina ganin ko fuskarta, ita ɗin mallakina ce" "Idan kai namiji ne sai ka hanani abin da na yi niyya" Adnan ya faɗa cikin raunin murya tare da ƙoƙarin kama bakin Afra da niyyar kissing. Cikin zafin zuciya Salman ya tattare hannun rigarsa farar fuskarsa ta yi jajir sbd abin da Adnan ɗin yake ƙoƙarin yi ɗin. Saukar marin da Salman ya ji ne ya sanya ya tsaya da sauri baki buɗe yake kallon Afra wacce ta fisge kanta da ƙyar daga hannun Adnan ta kuma sauke masa marin da ita kanta bata san tayi ba. Idanuna ya cika da hawaye sbd nauyin marin da tayi ya kalli Adnan ta ce. "Wa kake da suna? Wallahi na tsaneka ba zan taɓa son ka maye kawai" "Koda zan faɗa miki su waye iyayenki na gaskiya?" Ta watsa masa harara ta ce "Ai ƙarya kake tun a garinmu kake yaudarata, babu wasu iyayena daka sani" Adnan ya fara tari sosai idanunsa na rufewa tari yaci ƙarfin sa. Abbi da Mami da suke tsaye tun ɗazo suka ji kuma suka kaga abin da ke faruwa suka shigo cikin parlourn da sauri. "Subuhanallah! Adnan lafiya me ya sameka? Na'ima kawo mini ruwa" Adnan yakai hannu bakinsa sai ka jini ya wanke masa tafin hannun da alama kamar aman jini yake. Bai damu da halin da yake ciki ba, tarin na sarƙafe masa numfashi cikin mayuyacin hali ya kalli Afra da jikinta ya gama sanyi baki ɗaya ya ce. "Ko da zance maki Dr G.Y Bulama shi ne mahaifinki na gaskiya..." Cak numfashin sa ya tsaya jikinsa ya saki a jikin Abbi, a kiɗime Abbi ya ce "Salman get the car" A hankali cikin nutsuwa da kamala Abdullah ke driving motar daga Airport zuwa gida. Yana mamakin abin da ya hana Uncle ɗin magana, girgiza kai ya yi yana mai da idanunsa kan titi yasan yau Ummi kwanan farin ciki za tayi speaking calmly ya ce. "Uncle lafiya dai?" Wanda aka kira da Uncle ya juya ya kalli Abdullah a hankali ya ce. "Alhmd Abdullah" ba wanda ya sake magana a haka suka ƙarasa gida, Abdullah yai horn a gaban makaken gidan iya haɗuwa ya yi gatekeeper ya buɗe, a parking lot sukai parking kafin Abdullah ya fita ya riga shi. Ummi na zaune ta yi ado cikin wani dakakken lace sai ɗaukan ido yake ga gwalalen dake zube a hannunta. Ƙamshin turaren shi yasa ta tabbatar da zuwan mijin nata bayan wasu watanni zuwa shekara. Tsaye ta gansa ya zuba mata idanu cike da tunani a ransa da kuma son Ummi ɗin saura kaɗan ya yi kuskure a rayuwarsa. Ummi ta miƙe tsaye tare da ƙara sawa gabansa ta ce. "Wlcm Man" murmushi ya ƙirƙira kafin ya ce "I missing Maaah" girgiza kai kawai tayi suka ƙarasa parlour idanunsa a kanta ya ce "Kiran gaggawa ina tsaka da buɗe sabon company hope lafiya dai?" Tai murmushi cikin sanyin maganar ta ce. "Ka fara yin wanka kaci abinci?" "I can't dole na fara jin damuwarki a gigice na tahu" ta gyara zama cikin damuwa ta ce "Abubuwa ne suke ta fara, gaba ɗaya dukiyata na neman lalacewa kullum cikin asara da rasa kuɗaɗe nake, na rasa inda abin ya samu tushe ina son magance matsalar, wannan dalilin ya sanya na saka Abdullah ya rufe company ta kalman dana buɗe" Ya runtse idanunsa domin abin ya zo masa a bazata bai ɗauka abin zai sauri har haka ba, shi bama wannan ce damuwar shi ba. Yana ƙoƙarin magana wayar shi tayi ringing ganin wata number ya share, Ummi ta kafe shi da idanu can dai ya ɗaga a fusace ya ce. "Wai mene?" Tsaki kawai yaja ya ce. "Allah ya sawwaƙe" Ummi ta ce "Waye ba lafiya?" Yaja tsaki ya ce "No wani ma'aikacina ne" tana ƙoƙarin wata maganar aka sake kiran shi da sauri ya miƙe ganin number wanda yake ta jira. Jikinsa na rawa yama mance a gaban waye yake. "Hello, Assalamu alaika" daga can wayar aka ce "Muna magana da Dr Bulama" ya juya ya kalli Ummi ya ce "E, shi ne" aka ce "Mahaifin Adnan Aliyu Matawalle ke magana, ina son ganinka domin samun tabbaci shin da gaske Abra da Afra yaranka ne kai ne real father nasu?" Gaba ɗaya jikin Uncle ko nace Dr Bulama rawa yake ya ce "Oh!ok yanzu haka Ina Dubai, amma zuwa gobe zan sauka Nigeria I'll call you" Abba da Abbi suka kalli juna a tare suka ce "Dubai????" Ya ce "Eh, amma gobe zan zo Insha Allah" kashe wayar ya yi gaba ɗaya jikinsa rawa yake ya ce. "Rumaisa daman yaranmu ba mutuwa sukai ba???" Ummi da Abdullah suka ce "What???.... [11/22, 4:52 PM] Abk: Cikin gigicewa, da gurɓatacciyar hausarta, ta fara haɗa larabci, turanci da kuma hausa, ta kalli Bulama ta ce "Wane irin zance ne kake mini haka? Kamar yaya yaranmu ba mutuwa suka yi ba? Bayan ina labor room, aka ce mini na haifi yara tagwaye amma babu rai?". Jiki a sanyaye Bulama ya ce "Nima abin da nake mamaki kenan, ta yaya za ce suna raye?". Ummi ta ce "Wai wani irin zance ne wannan? Baka tabattar ba kenan, ya kake son ka yi mini wasa da hankali Yusuf Bulama?". Abdullah ya tattaro nutsuwarsa ya kalli Bulama, shi ya iya hausa sosai ba kamr rumaisa ba, ya ce "Ka sakamuna ruɗu ya kai Yusuf, ka sani cewa wannan maganganun naka barazana ne ga tunaninmu, da kuma zukatanmu, amma kuma biri ya yi kama da mutum, zan iya gasgata ka akan abin da kake faɗa, amma bamu labari, kafin ni in sanar da ku wani abu mai mahimmanci da Yakamata in faɗa". Bulama yayi jimm, sannan ya basu labari tiryan-tiryan yadda abubuwa suka wakana, har zuwa lokacin da Abra ta rasu. Gigicewa Rumai ta yi, yarana suna raye, ɗaya ta mutu? Waye ya yi mini wannan zaluncin, na rayu shekaru Ashirin da huɗu cikin ɗacin rai da ƙunar zuciya, yarana na raye amma suk rayu nesa da ni, ya za ayi ace na haifi yara aka ce mini sun mutu? Meyasa aka mini haka Ya kai Yusuf, ya a kai ka tabbatar da yarana na raye? Ka kaini in gansu a ina suke, ko da yake kace mini ɗaya ta mutu, to ina ɗayar a ina take? Dan Allah kar ka gaya mini abin da ba zai yiwu ba, in saka rai kuma in zo ba yarana ba ne". Abdallah yayi ajiyar zuciya ya ce "A shekarun baya,  da naje Nigeria, a garin Kano, naje sayayya wani mall, na haɗu da wata yarinya da sai da hantar cikina ta kaɗa saboda mamaki. Tana tsananin kama da shi Yusuf, kuma akwai wasu kamanni da ta ɗauko na ki, hatta wannan ɗigon baƙin na gefen idonki ta na da shi, mamaki da rikicewa ya sanya na kai hannu fuskarta, wanda suke tare da shi ya mareni, ina tunanin mijinta ne a wannan lokacin, ita yarinyar ta tsorata, har ta suma, ya ɗauketa suka bar wurin. Still a watannin da suka shuɗe, na haɗu da ita a nan Dubai, amma ita da wani daban n kuma ganinta, amma ban yi mata Magana ba saboda wanda suke tare ya mini kwarjini da yawa, kuma ina tsoron abin da ya faru wacan lokacin ya kuma faruwa, idan kuwa haka ne ina kyautata zaton ko da duk mutum ɗaya na gani, ko kuma su biyun ne Amma sanin gaibu sai Allah". Fashewa da kuka Ummi tayi, tana fitar da tulin damuwar da ke mamaye a ranta, saboda tun bayan haihuwar yaran nan ba ta kuma samun wani rabon ba, kuma gashi Allah ya jarabce ta da son yara, yo ta ina ma zata samu rabo, miji ma wata ƙasar ita ma tana wata ƙasar daban, sai su shafe watanni huɗu wani bai sa wani a idonsa ba. Cikin kuka ta ce "Abdallah, a gaggauta neman mini visa Nigeria, muje ya nuna mini 'ya'yana, ni da da yadda za ayi, a yanzun nan zamu tafi, amma ni haryanzu na kasa gazgata hakan" Bulama ya rungumeta a jikinsa yana rarrashinta, tare da bata tabbacin cewa zasu tafi Nigeria tare, dan tabattar da abin da yake faɗa mata. Afra kuwa ta ɗan fara tausayin Adnan, saboda yadda aka ce yana aman jini, gaba ɗaya baya hayyacinsa, amma sam ita Adnan bai mata ba, kallon mugu take masa, saboda yanayinsa yadda yake wasu abubuwan da zafi, Salman ya fishi kirki da bin komai a hankali, dan haka ita ba ta ga ta yadda zata zaɓi Adnan ba, ga salihi mai lallaɓata. Adnan kuwa yana kwance a gadon asibiti, an ɗaura masa drip, sai dai yadda yake numfashi kawai ya isa ya tabbatar maka da cewar, yana jin jiki, daga nesa ana iya ganin yadda ƙirjinsa ke fat-fat da sauri da sauri. Abbi kam mamaki ya cigaba da yi, dama Adnan ya san mahaifin Abra, amma yayi shiru da bakinsa bai faɗa ba? To yaya ma aka yi ya tabattar da Bulama ne mahaifinsu, ko dai zafin ciwo me ya sanya shi faɗar hakan, suka biye masa suka kira bawan Allah. Hajiya Saudat ta rasa in da zata saka kanta, abin duniya ya isheta, ga Meenal a kwance ba lafiya tun da aka yi aikin nan, ta ƙi lafiya, an cire mahaifa ɗungurun gum, ba ta taɓa sanin Meenal na bin maza ba, ga uwa ba, abin da Bulama ke shirin yi, idan bar tone tone yayi yawa, tabbas akwai Matsala, dan daga ita har shi suna cikin tsaka mai wuya, nan ta koma tunanin yadda zata shawo kan lamarin. Wayarta ta ɗauko, ta kira layin Bulama, ba ta damu da kuɗin da za a ja ba a waya, saboda kiran lambar ƙasar waje. Har ta fidda ran zai ɗaga, ya ɗaga wayar. "Hello, kana ina ne?" Haushi ne ya kama Bulama ya ce "Meye hak sai kace wani ɗanki? Ya ma dace ki kirani a halin yanzu? Kin fi kowa sanin ina na tafi, ina tare da Rumaisa, kuma sai ki kirani a waya?" "Dan me ba zan kirak a waya ba, in ruwana da wata Rumaisa? Ka tafi ka bar ni da yarinya da larura, ko ka kira kaji ya jikin nata" "Saudat, abin da ya samu Meenal, ke ta shafa da ke da ita, ni ban yiwa Meenal tarbiyyar taje ta bi maza a waje ba, har ta zubar da ciki wanda ya kusa ajalinta ba, dan haka ki gaggauta rabata da gidana kan in dawo, i disowned her as my child, taje ta nemi wani uban". "Wallahi ƙarya kake yi, Meenal jininka ce, 'ya ɗaya tilo da Allah ya baka, dan haka dole muyi haƙuri da ain daya sameta mu riƙeta". "Dole kiyi haƙuri dai, amm banda ni ku san yadda zaku yi ke da ita" ya katse wayarsa. Jifa tayi da wayar tare da taune lips ɗinta na ƙasa 'Anya zancen nan bai tabatta ba na cewar yaran nan suna raye ba, tun da har ya iya nuna halin ko in kula ga 'yar da ya ƙallafa ransa a kanta kasancewar ita kaɗaice ba? To yaya aka yi yaran suka rayu, bayan tun a Asibiti aka ce ba su zo da rai ba? Wane al'amari ne haka mai ban mamaki? Anya ba ƙarya bace da rainin hankali kawai? To amma hotunan da aka aiko masa fa kika ƙona' wata zuciyar ta tambayeta. Tabbs yarinyar jikin wannan hoton duk in da ta fito tana da alaƙa da Bulama. To ko dai matan banza ya fara bi? Aka haifa masa ita? Haka ta dinga tunani barkatai, ba tare da ta samo amsoshin tambayoyin ta ba, sai dai ta san tasowar wannan lamari barazana ne a gareta da Bualaman kansa, mussaman a kan sirrin da suka yi shekaru suna binnewa. Abba ne da Abbi tsaye a kan Adnan, da aka samu ya ɗan farfaɗo daga fita hayyacin da yayi, lokaci ɗaya duk ya yi rama, yayi zuru-zuru, Mami da Hajiya Mama kuwa suna reception, suna wa Adnan Adduar samun lafiya, saboda ya sha wahala. Abbi ya numfasa ya ce "Yanzu muna jiaran dawowar wannan mutumin, sannan shi Adnan ya ƙarasa warkewa, mu ji yaya aka yi suka zama 'ya'yan mutumin?". Abba ya ce "Ba zamu jira sai ya warke ba, dole ai wadda za ayi idan mutumin ya dawo gari, ko mu muje, ko shi ya zo ya same mu". Abbi ya gyara tsayuwarsa, yana kallon Adnan, a lokacin da Adnan ya gyara kwanciyarsa, yana bin sun Abbi da ido. Abbi ya ce "sannu Adnan, Allah ya baka lafiya, in dai a ka Afra ne, ka kwantar da hankalinka, ni zan rarrasheta, za a aura maka ita insha Allah, dan ita ya dace ta maye maka gurbin 'yar uwatta". Abba ya ce "In ji wa? Ai ida har ina raye Adnan ba zai auri Yarinyar nan ba, Salman shi ya dace ya auri Afra". Abbi ya ce "Me yasa zaka ce haka?". "Wa zai bawa Mutumin banza 'ya, ai shi ya san mai nake nufi" Adnan ya haɗa hannayensa biyu, alamar ban haƙuri, yana girgiza kansa, hawaye na fita daga idonsa. Abbi ya ce " Bai kamata ka faɗi haka a gabansa ba, bayan ga halin da yake ciki". Abba ya ce "Wannan yaron ba abin tausayi bane, gara a bari ya ɗanɗana kuɗarsa, kuma sati mai zuwa zan karɓawa Salman Auren Afra a wurinka, idan har zaka mini kara, Salman ɗana ne" Cikin hanzari Abbi ya janyo hannun Abba, zuwa waje ya ce "Duk laifin da yayi bai cancanci wannan horon ba, magana fa ake ta rayuwarsa". Abba ya ce "Amma dai ka san Aurensa da Afra ba abu ne mai yiwuwa ba ko? Alhalin ga Salman". "Na sani, amma sai a tausayawa halin da ya tsinci kansa a ciki, koma wani irin laifi ya aikata maka, bai kamata ace ka ɗau wannan zafin ba, har ka nesanta shi da tausayawarka ba, haba Alhaji Aliyu, ka zafafa da yawa, akwai buƙatar ka sassauta masa haka" Abba ya girgiza kai ya ce "Ba zaka gane bane Major, halin da Adnan yake ciki, dai-dai da shi ne, shiya janyowa kansa". Abbi ya ce "Ba ina son jin laifin da ya aikata maka bane, ina nema masa alfarma ne, dan Allah dan Annabi, a sassauta masa a duba halin da yake ciki, ka rage wannan fushin da ka ke da shi". Abba ya ce "Na ji, amma ni yanzu babbar damuwata shi ne, ba zan bar garin ba, sai Mutumin nan ya dawo, mun cinma matsaya, na tabattar da abin da Adnan yake faɗa, gaske ne ko kuma ƙarya yake yi". "Haba Alhaji Matawalle, ga gidana mai zai sa kaje ka kama hotel ka zauna, idan ma ba zaka zauna a gida na ba, akwai guest house ɗina, sai kaje can ku zauna, mu jira zuwan mutumin, Allah dai ya sanya mu ji alkhairi". Afra sai koke koke take yi, gaba ta ma rasa kukan me take yi ne? Damuwa da halin da Adnan yake ciki? Ko kuma farincikin an san waye mahaifinta? Bana wannan ba, ai haryanzu lalube ake a cikin duhu, ba tare da an tabattar da sahihancin cewar wanda Adnan ɗin ya ambata shi ne mahaifinta ba, wataƙila ma ƙarya yake mata, kamar yadda ya yi mata ƙarya a ƙauye. Kwanakin Adnan uku a Asibiti, ya ɗan farfaɗo jikinsa da sauƙi, Afra taje duba shi sau ɗaya yana bacci, ya yin da Salman kuwa, sai da Mami ta haɗa masa da zagi, sannan ya yadda yaje duba Adnan, duk da a ƙule yake da Adnan, amma ya tausaywa yadda ya ga Adnan ɗin ya koma. Akwa abubuwa da yawa da Salman ba zai taɓa mantawa da su ba a rayuwarsa, daga shigowar Adnan rayuwarsu, ya rusa musu farinciki, zuwa ga mutuwar Abra, ba zai taɓa manta lokacin da a gaban idonsa, Adnan ya mari Abra ba dan kawai ta ce tana son sa, da ya tuna ire-iren wannan abubuwan da suka faru, sai tsanar Adnan ta ninku a zuciyarsa, ban da zuciyar musulunci, da kuma yadda Mami ta dage da babu abin da zai sanya ya zo duba Adnan. Kuma a wannan karon ya ƙudirce a zuciyarsa ko mai za ayi, ba zai barwa Adnan Afra ba, a wannan karon Afra tasa ce. Wasa-wasa, sai da Bulama ya kwana biyar a Dubai, sannan passport ɗin Rumaisa ya zama ready, gaba ɗaya a kwanakin nan, banda aikin rarrashinta babu abin da yake yi, kullum cikin kuka take, ga gefe guda Saudat ta uzzura masa da kira, ƙarshe sai kashe wayarsa ya yi gaba ɗaya. Ranar Asabar, Bulama da Rumaisa tare Abdallah suka sauka a Nijeriya, a garin Kaduna, sai dai a guest house ɗin sa na Kaduna suka sauka, saboda baya son wani dalili ya sanya wani ya san da cewar, sun sauka da Rumaisa a Nigeria.     Lambar Adnan Bulama ya duba, ya kira shi, sai dai sam Adnan ya ƙi bawa kiran mahimmanci balle ya ɗauka, kasancewar yana tare da su Abba a guest house ɗin Abbi, Yana kwance a falo, Hajiya Mama na gefensa tana jan carbi, ta ji wayar Adnan ta cika mata kunne, amma ba shi da niyyar ɗaukar wayar. "Adnan ba wayarka ce take ringing ba" Cikin numfarfashi na marasa lafiya, Adnan ya ce "Mama I can't pick it". Mama ta miƙa hannu ta ɗaga wayar, cikin nutsuwa Bulama ya yi sallama, Mama ta amsa suka gaisa, Bulama ya ce me wayar yake nema. Mama ta ce "Bashi da lafiya, yana kwance" Bulama ya ce "Subhanallah, Allah ya bashi lafiya, dama nine Yusif Garba Bulama, wanda aka ce yarana na wurinku". Mama ta ce "Ahh, Allah sarki, ka dawo garin ne?" "Eh mun dawo, naje na taho da mahaifiyarsu ne, dan mu samu a tabattar idan yaran namu ne" Mama ta ce "Alhamdilillah, muna nan Kano dama ku muke jira, da ka ce tun a washegari zaka zo". "Eh, an tsaya gyara passport ɗin mahaifiyarsu ne, insha Allah gobe in Allah ya kaimu, da wuri zamu taho, sai a bani Address ɗin in da zamu zo". Mama ta tashi, taje ta kaiwa Baba waya, suka sake yin magana da Bulama, ya yi masa bayanin Adress ɗin. Washegari, wajen ƙarfe goma sha ɗaya na rana, Abba ya shigo ɗakin da Adnan yake ya ce "Ka tashi ka shirya, muje mu tari Mutanen nan, sai ka tabbatar mana da dalilin da yasa kace shi ne mahaifinsu, kuma ka gaya musu da ka auri 'yar su me kayi mata, da kuma dalili da ya sanya ka san in da mahaifin na su yake, amma ka ƙi faɗa da wuri". Marairaice fuska Adnan ya yi zai yi magana, amma Abba ya dakatar da shi ya ce "Kar ka gaya mini komai, ka tashi mu tafi, mutumin banza kawai, ai kai ba abin tausayi bane" Jiki ba ƙwari haka Adnan ya kammala shiryawa, suka tafi gidan su Salman. Suna zazzaune a falo, suna jiran zuwan su Bulama, Little da tuni ta fara rarrafe, ta na jikin Adnan tana wasa, ta ja masa gemu, ta ja masa gemu, yana kallonta yana murmushi, lokaci lokaci yana share ƙwalla. Ko da Afra ta fito falo ta yi tozali da Adnan sai da gabanta ya faɗi, yayi rama tamkar ba shi ba duk yayi wani iri, gashi yadda numfashinsa ke fita ma zai ƙara tabattar maka yana cikin mawuyacin hali. Kallo ɗaya yayi mata ya kauda kansa, ya cigaba da yiwa Little wasa, yana share hawaye, gaba ɗaya sai jikin Afra yayi sanyi, ko ba komai mijin 'yar uwatta ne, abin da tayi na nuna masa ƙiyayya, bai kamata ba, amma ba yadda zata yi, dan ita tafi son Salman a kansa. Abbi ne ya shigo tare da Abba ya kalli Mami sannan ya kalli Afra ya ce "Afra tashi ki koma ɗaki, make sure baku bari ta fito ba, sai mun gama tattauanawa, gasu can sun ƙaraso" Afra tana ji tana gani, aka kaita ɗaki aka rufe. Abbi ne ya yiwa su Bulama jagora, zuwa cikin katafaren falon gidan Major. Rumaisa sai rarraba ido take yi, Mami ta tsurawa Rumaisa ido, a ranta ta ce "Tsarki ya tabbata ga Allah, su Abra dai 'ya'yan balarabiya ne". Abdullah ya kalli hoton falon, cikin harshen larabci ya ce wa Rumaisa "Ai wannan ita ce yarinyar da nake baku labari, na haɗu da ita karo biyu". A gigice Rumaisa ta nufi hoton, tana ta larabci, ba komai suke ganewa a maganar ta ta ba, saboda kukan da take yi, da ƙyar Bulama ya rarrashi Rumaisa, su Abbi suna ta rarrashinta cikin harshen turanci. Tabbas babu wanda zai kalli matar nan ya ce ba ita ta haifi su Abra ba. Har ta zauna ta miƙe a gigice ta nufi in da Adnan ke zaune yana binta da ido, dan hatta yanayin rikicewarta tana kuka tamkar Abransa. Little ta ɗauka ta ƙanƙame, tana cewa Bulama wannan ma 'yar ta ce. Cikin harshen turanci Bulama ya ce "Ta yaya wannan zata zama 'yar ki, bayan 'ya'yanki sun kai aƙalla shekaru ashirin da huɗu". "To ina yaran nawa suke?" Ta tambaya tana zubar da hawaye, tare da sumbatar Little, duk ƙyuyar yarinyar amma ba ta yiwa Ummi ba, saima kallonta da take tayi. "Bayani za ai miki ai, amma ki zauna" Da ƙyar Rumaisa ta zauna, aka gaggaisa aka kawo musu ruwa, aka samu Rumaisa ta ɗan nutsu, sannan Abba ya kalli Adnan ya ce "To ka san dai kai ne silar taruwarmu a nan, dan haka saika warware mana abin da ka ƙulle a ranka, kayi da turanci yadda zata fahimta". Adnan ya ɗan yi jimmm, sannan yai ajiyar zuciya, jiki a sanyaye idonsa fal ƙwalla ya fara bada labarin abin da ya faru. Ya fara da irin soyayya da shaƙuwar da ke tsakanin sa da mahaifiyarsa, har zuwa lokacin da ta rasa ranta a sanadin Sakaci da son abin duniya na Bulama. Ya cigaba da bada labari, yadda ya rayu, da kewar rashin mahaifiyarsa har zuwa ranar da ya raka Usman gidan Bulama wurin Meenal, da hoton Bulama da ya gani, da fari a kan Meenal ya so ya aura, kuma ga Usman, katsam da yaje Kano, ya haɗu da Abra. Nan ya basu labarin yadda ya je har Yola, garin su Bulama samun bayanai a kansa, a nan ya tabattar da Abra 'yar sa ce. Rumaisa ta ce "Ita ba ta fahimta ba, wacece Meenal da ake magana a kanta, kuma wane Asibitin ake magana ba ta gane zancen ba?! FARKON LABARI YUSUF GARBA BULAMA ɗan asalin garin Adamawa ne cikin Yola NA KUƊI NE, A BIYAMU HAKKINMU KAN A KARANTA 08081012143 [11/23, 12:57 PM] Abk: Su biyu kacal iyayensu suka haifa, daga shi sai ƙanwarsa Murja. Sun taso cikin kulawa da soyayyar iyayensu, duk da ba masu ƙarfi ba ne sosai amma suna da rufin asiri daidai gwargwado, kuma babu abin da suka nema suka rasa a rayuwa. Yusuf ya kasance mutum ɗan gayu, mai son rayuwar ƙarya da sabgar masu kuɗi. Tun yana karami Mahaifinsa Garba Yusuf Bulama ya fahimci wannan halin nasa, hakan ya sa kodayaushe cikin masa nasiha da nusar da shi ya tsaya a duk inda Ubangiji ya ajiye shi a rayuwa yake. Yusuf ya kan nuna kamar ya ɗauki maganar mahaifinsa, amma cikin ransa ƙara burika ma yake yi, addu'ar shi da burinsa a kullum Allah ya sa ya zama shahararren mai kuɗi, wanda za a dinga kwatance da shi saboda kuɗinsa. Mahaifinsu ya saka su a makarantar boko da islamiyya, amma sai ya fi mayar da hankali a kan karatun boko, a cewar shi saboda shi ne karatun samun kuɗi. Suna daf da kammala secondary school suna SS 3 Allah ya yiwa mahaifinsu rasuwa. Bayan Mahaifiyarsu ta fita daga takaba sai Bulama ya fito da buƙatar cewa yana son ya cigaba da karatu, Mahaifiyarsu ta ce A'a, ita dai ta fi son ya zauna ya cigaba da kiwo ya gaji mahaifinsa, a ganin Bulama hakan faɗuwa ce a ce kamar shi wayayye ɗan boko da kiwo, ba zai iya ba gaskiya. Lallaɓa mahaifiyarsu ya dinga yi tare da nuna mata alfanun karatun fiye da Noma, har ya samu ta amince, aka siyar da wasu daga cikin shagun da baffansu ya bari aka damƙa masa kuɗin akan ya je ya cigaba da karatun da su. Yadda ake ba shi labarin ABU Zariya da kuma wasu daga cikin abokansa da suke can ya sa shi ma ya je ya fara karantar medicine. Shigar shi makaranta ya ƙara masa ƙarfin burinsa a cikin ransa, saboda ganin yadda ƴaƴan masu kuɗi suke rayuwa, abun yana matuƙar burge shi. Ba ya abota da ƴaƴan talakawa yan'uwansa sai dai da masu kuɗi, kasancewar shi kyakkywa kuma ɗan gayu ya saka ake ɗauka shi ma ɗan masu kuɗin ne. Suna level 3 aka tafi wani strike mai zafi, a lokacin wani abokinsa Munnir yake sanar masa mahaifinsa ya tura shi ƙasar Dubai akan harkar kasuwancinsa, zai tafi idan aka koma school sai ya dawo. Ranar da ya faɗa masa kasa bacci ya yi, don ji yake dama a ce shi ne zai tafi Dubai ɗin nan, ya dinga ƙissime-ƙissimen me zai siyar a cikin gadon da mahaifinsu ya bar musu wanda zai ishe shi kuɗin jirgi zuwa Dubai ya bi Munnir su tafi tare, amma duk abin da ya ayyana zai sanar sai ya ga ba zai kai ba, don duk saboda karatunsa da ƙaryayyakin da yake kiran Inna ya yi mata akan kuɗi, ya sa duk ta sissiyar da abubuwa da dama na gadon ta tura masa kuɗin. Bayan kwana biyu abin yana cin shi a rai ya kasa dannewa, hakan ya sa ya yanke shawarar kawai ya kira Munnir ya sanar masa, ko Allah zai saka a dace su tafi tare. Kamar wasa Munnir yana kai maganar gaban mahaifinsa ya amince, bayan ya kai masa Bulama ya yi masa tambayoyi a game da rayuwarsa, jin Maraya ne kuma ba shi da aikin yi ya sa ya amince, amma bisa sharaɗin sai iyayensa sun amince. Cikin tsantsar murna Yusuf ya koma gida ya sanar da Inna, da farko ƙin amincewa ta yi, sai da ya kira mahaifin Munnir ya yi mata bayani sosai yadda za ta gane sannan ta amince da ƙyar. Sun ci kuka lokacin da zai tafi ita da Murja wadda ake shirin aurenta a lokacin, amma shi ko ɗigon hawaye saboda farinciki da murnar da yake ciki, a ganin shi wannan dama ce da za ta taimaka wajen cimma burinsa. Sun isa garin Dubai lafiya, babu ɓata lokaci kuma suka shiga abin da ya kawo su na business, Bulama jin zuciyarsa yake fess yau ga shi a Dubai, tamkar wanda aka tsunduma a Aljannah haka yake jin kansa don farinciki. Ranar wata Juma'a da ba zai taɓa mantawa da ita ba a rayuwarsa sun je wani shago siyayya suka haɗu da Rumaisa. Shagon sayar da Gold's ne, su Bulama sun zo siya wanda za su tura wa Baban Munnir Nigeria ya sayar. Suna cikin zaɓa Bulama ya kai hannu zai ɗauka ita ma ta kawo kyakkyawan farin hannunta. A tare suka janye hannayen nasu tare da duban juna da sauri. Kasancewar ta mace mai fara'a sai ta sakar masa murmushi tare da faɗin. "I'm sorry." Cikin siririyar muryarta. Murmushin ya mayar mata tare da ɗaga mata hannu alamun babu komai, sannan ya bar gurin. Da kallo ta bi shi har ya ɓacewa ganin ta, ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da duba sarƙoƙin. Tunda Rumaisa ta koma gida sai Bulama yay ta faɗo mata a rai, abin ya ba ta mamaki ba kaɗan ba, don duk da kallo ɗaya ta yi masa amma ta gane ba ƙabilarta ba ne, bai ma yi mata kala da fararen fata ba, ya fi mata kala da ƴan Africa, duk da fari ne tass shi ma. Bayan wasu kwanaki suka ƙara haɗuwa a hanya, a lokacin suna tare da ƙaninta Abdallah, amma duk da haka sai ta yi masa magana, abin mamaki shi ma ya gane ta, gaisawa suka yi cikin fara'a kamar waɗanda suka daɗe da sanin juna. Watarana su Munnir sun je gurin da suke sayayyar kaya suka tarar kayan gurin duk an kwashe sai kaɗan, mai gurin ya ce su bari sai zuwa washegari za a jera wasu sai su zo su saya. Cikin rashin jin daɗi Munnir ya ce masa. "Ai kayan nan yau ake buƙatar su, saboda mahaifinmu yana ta kiran mu akan nasa sun kusa ƙarewa, kuma mun riga mun yi bucking Flight ɗin da zai tafi da kayan." Mai gurin ya ce musu babu damuwa, zai haɗa su da wata abokiyar kasuwancinsu, wadda Insha Allahu komai suke so za a su samu a gurinta. Ba su yi musu suka amince masa, bayan sun je suka tarar da fiye da abin da suka yi tsammani, don duk wani nauyi na Dubai gold akwai shi a shagon, kuma kayan gurin da sauƙi har ya fi na inda suke saya. Alokacin ba su haɗu da mai shagon ba sai yaranta, don ba ta zama ita a sati sau ɗaya take zuwa ta ga yadda abubuwa suke tafiya. Da za su ƙara sayan kaya sai suka koma gurin, saboda mahaifin Munnir ya yaba kayan sosai, ya ce idan za su ƙara saya su je can idan za a samu. A wannan zuwan Bulama suka ƙara haɗuwa da Rumaisa, ashe ita ce mai gurin. Ta yi mamakin ganin su sosai, shi ma haka. Tun daga ranar idan suka zo siyayya sometimes suna haɗuwa, har suka saba suka yi musayar contacts ɗin juna. Munnir ya dinga tsokanar Bulama yana cewa. "Ɗan fillo ko dai da ƴar Balarabiyar nan za a yi ne?" Idan ya faɗi haka sai ya yi murmurshi ya ce, babu ɗaya haɗuwar jini ce kawai. Asalin Rumaisa Balarabiya ce Ƴar ƙasar Dubai, kyakkyawa ce don ko a cikin larabawan mai kyau ce, ita kaɗai iyayenta suka haifa, tun tana yar ƙarama mahaifinta ya rasu. Mahaifinta shahararren mai kuɗi ne, ya mutu ya bar dukiya mai ɗimbin yawa. Mahaifiyarta ta ƙara aure bayan rasuwar mahaifinta ta haifi Ɗa Namiji Abdallah. Shaƙuwa mai ƙarfi ce ta shiga tsakanin Rumaisa da Yusuf Bulama, daga baya kuma ta rikiɗe ta koma soyayya. Tsakani da Allah Rumaisa take ƙaunar Yusuf, shi kuma yana son ta ne saboda tarin dukiyarta, amma ko kaɗan ba ya nuna mata hakan, don in ta ba shi abu ma ba ya karɓa sai ta nuna masa ɓacin ranta. Ƙauna da kulawa yake nuna mata sosai, wanda hakan yake ƙara dilmiyar da ita a cikin ƙaunar shi. Cikin haka aka janye strike ɗin da aka tafi na watanni goma sha uku, lokaci shekara guda cif da haɗuwar Rumaisa da Bulama. Ranar da za su dawo Nigeria ba ƙaramin tashin hankali da damuwa Rumaisa ta shiga ba, Yusuf ya dinga pretending as ya fita shiga damuwa, da ƙyar ya lallaɓa ta ɗan kwantar da hankalinta, a haka suka rabu zuciyoyinsu babu daɗi. Bayan Rumaisa ta gama cika shi da kayan arziƙi. Sun cigaba da soyayya kamar babu gobe ta waya, Rumaisa ta ɗauki dukkan yarda da k'auna ta damƙa wa Yusuf. Rumaisa macece mai kirki da addini da sanin ya kamata, matsalar ta ɗaya tana da zazzafan kishi, wanda wannan kamar a jinin larabawa yake. Tana mugun kishin Yusuf sosai, a kodayaushe cikin nanata masa kar ya ci amanarta take ko ya kula wata mace bayan ita, zuciyarta ba za ta ɗauki hakan ba, sannan ta yi masa alƙawarin tana nan tana jiran shi, ko shekara nawa zai yi kafin ya kammala karatunsa za ta jira har ya gama su yi aure. A tarayyar su ba ƙaramin kuɗi ta ba wa Bulama ba, duk da a zahiri yana nuna mata ba ya son ɗawainiyar da take shi amma ba ta fasawa. Lokaci ɗaya Bulama ya fara samun kuɗi, ya saya Mota da abubuwan more rayuwa. Inna ta san da zaman Rumaisa, amma ba ta san soyayya suke da Yusuf ba, a yadda ya faɗa mata abokiyar kasuwancinsu ce kawai suka saba da ita. Bayan kammala karatunsu da N.Y. S.C Ta turo masa kuɗin jirgi ya tafi Dubai ya ɗora karatu, Rumaisa ce ta ɗauki nauyin karatun da gurin zamansa da abin da zai ci da komai na buƙatun rayuwa. A lokacin Rumaisa ta sanar da danginta Yusuf take so, wanda a karon farko suka ce ba su amince da wannan maganar ba, duk larabawa da ƴan'uwanta da suke son ta, ta rasa wa za ta ce za ta aura sai bak'ar fata ɗan Nigeria. Jin haka ya sa Rumaisa shiga cikin tashin hankali da damuwa, ta dinga koke-koke da roƙon su akan su amince, ita a haka take son Yusuf ko ma ɗan ina ne, amma suka ce ba ta isa ba, tun wuri ma ta rabu da Yusuf kafin su saka a ɗaure shi. Mahaifiyarta ce kawai ta goyi bayanta a lokacin, duk da ita ma ba ta so, amma tausayin 'yarta da ƙaunar ta ya sa take supporting ɗinta. An yi badaƙala da ja'inja ba kaɗan ba tsakanin dangin mahaifin Rumaisa da mahaifiyarta kafin su amince ta auri Bulama, amma sun ce babu ruwansu duk abin da ya biyo baya mara daɗi kar ta neme su. Ba a yi Auren ba sai da dangin mahaifiyarta suka zo Nigeria suka ga asalin Bulama, shi kuma ya yi cike-ciken takardu na yarjejeniya a Dubai ɗin. Al'amarin ya ba wa kowa mamaki a Adamawa, musamman Inna da Murja, Yusuf da auren Balarabiya, abun kamar almara. Buri ya cika bayan fitar da rai da hakan, farincikin da Bulama da Rumaisa suka yi a lokacin Aurensu ba zai misaltu ba. Musamman shi da ya jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, yana son Rumaisa sannan kuma ya san dukiyarta yanzu za ta koma tasa da ta ƴaƴan da za su haifa. Soyayyar da Bulama ya nuna mata a zaman Aurensu ya sa ta ƙara yarda da shi da ƙaunar shi. Bayan ya kammala karatunsa ya shirya don komawa Nigeria, a nan mahaifiyar Rumaisa ta ce ba zai tafi da ita ba, ba za ta yarda yarta ta yi nesa da ita ba. Shi ma ya ce ba zai fasa komawa Nigeria ba, saboda Mahaifiyarsa da ƙanwarsa shi kaɗai suke da shi, suna buƙatar shi a kusa da su. Ba don Rumaisa taso ba ta bar shi ya tafi. Dawowar shi ba jimawa ya fara aiki a wani babban asibiti a nan Adamawa. Bayan wasu watanni ya koma ya ga Rumaisa, a lokacin ta raba dukiyarta biyu ta ba shi rabi, ta ce ya je ya yi duk kasuwancin da yake so a Nigeria ya juya kuɗin. Kusan haukacewa Bulama ya yi saboda tsabar murna da farinciki, ranar ƙaunar da ya nunawa Rumaisa bai taɓa nuna mata kamar ta ba. Bai jima ba ya ƙara dawowa Nigeria, anan ya yi deciding ya buɗe Babban Asibiti nasa na kansa. Bai buɗe a Adamawa ba saboda wani dalili nasa ya buɗe a Kaduna, ya saka masa sunan mahaifinsa GARBA YUSUF BULAMA. A lokacin ya haɗu da Saudat suka fara soyayya. Saudat irin matan nan masu feleƙe da iyayi da son sabgar ƙarya. Farkon haɗuwar su da bulama ba ta zata yana da mata ba sai da ya faɗa mata. Ta ji takaici da baƙincikin fara mallakar wata da ya yi kafin ita, amma haka ta daure suka cigaba da soyayyar su. Sai dai cikin ranta ƙiyayyar Rumaisa ce fal duk da ba ta taɓa ganin ta ba sai dai a hoto. Abin da yake ƙara ƙona mata rai yadda Bulama ya ɓoye wa Rumaisa tarayyar su, ya nuna ba ya son ta sani. Kammala ginin G.Y HOSPITAL AND MATERNITY Ya yi daidai da lokacin bikin SAUDAT da BULAMA, don haka aka sha shagali ba na wasa ba. Auren ya kasance tamkar na cin amana, tunda ba da sanin Rumaisa aka yi ba kuma da dukiyarta. Bayan bikin da wata biyu Bulama ya koma Dubai, a wannan zuwan Rumaisa ta samu ciki, bai jima ba ya dawo Nigeria saboda yana son ya kula da Hospital ɗinsa, sai dai bai sanarwa da Rumaisa ya buɗe asibitin ba. Watan cikin Rumaisa takwas ta kira Bulama ta ce za ta zo Nigeria ta gaishe da Inna ta zazzaga danginsa su san ta, ta san su. Bulama bai so hakan ba saboda gudun tonuwar asirin Auren Saudat, amma bai nuna mata ba saboda kar ta yi tunanin wani abu, dama tana ta complain akan yana daɗewa yanzu kafin ya je ya gan ta. Bayan sun gama wayar ya fara haɗa kayansa, cikin mamaki Saudat da ta shigo ɗakin da yake ta ce masa. "Lafiya kake haɗa kaya da sakaliyar yammar nan Doctor?" "Adamawa zan je." Ya ba ta amsa a tak'aice "Adamawa kuma? Shi ne ba ka sanar mini na fara haɗa kaya ba ni ma?" Yana zuge zip ɗin trolley ɗinsa ya ce. "Ba da ke zan tafi ba, Rumaisa ce za ta sauka a ƙasar nan gobe, kin kuma san ba ta san da zamana a Kaduna ba balle aurenki da na yi, don haka dole ya zamana a Adamawa za ta same ni." Cikin takaici ta ce. "Sai yaushe kuma za ka dawo?" "Sai ranar da ta tafi." "Asibitinka kuma fa." "Akwai masu kula shi kamar ina nan ai." "To amma ni haka zan ta zama ni kaɗai, kana ƙasar ma amma ba za mu haɗu ba har sai ranar da ta tafi?" Cikin fusata ya ce. "Haba Saudat ya kike so in yi ne? Ke duk watanni da nake yi a gurinki ban je wajenta ba, ba kya gani? Sai yau ɗaya za ki ɗaga mini hankali. Rumaisa tana buƙatar kulawata a halin yanzu sosai fiye da ke, saboda tana ɗauke da juna biyu, don haka ko da ba za ta zo ba ni zan je. And lastly kar ki kuskura ki kira ni ko ki mini text, ni zan na kiran ki da kaina, sai na dawo, zan miki transfer ɗin kuɗi idan na ƙarasa." Ya ƙarashe maganar tare miƙewa ya fita. Da wani irin kallo ta bi shi cikin bugawar zuciya da tsananin tashin hankali har ya fice. Gwauron numfashi ta sauke tare da furta "Ciki?" Tana gyaɗa kai, lokaci ɗaya ta miƙe kamar wadda aka tsikara ta shiga kaiwa da komowa a cikin ɗakin. Littafin kuɗi ne, ku biya kafin ku karanta. 09047871750 [11/25, 10:36 AM] Abk: Maganar samun cikin Rumaisa ya ɗagawa Saudat hankali, zuciyarta ta fara saƙawa kwakwalwarta mugun tunani. Ta ɓangaren Rumaisa ta samu iyayen Dr lafiya cikin karamci da walwala hakan yasa ta saki jiki har ta ce zatai wasu kwanaki. Tana saura kwana uku tafiyarta naƙuda ta kamata cikin gaggawa suka nufi asibiti tasha baƙar wahala ƙwarai har an fara tunanin za ai mata C.s sai Ubangiji ya sauke ta lafiya ta haifi twins. Murna ta kama Dr G.Y sai dai murna ta koma ciki domin awanni wajan biyu da haihuwar aka dawo da jariran a hannu Allah ya yi musu rasuwa, daman da aka haife su ba wanda yaga kalar su sai da suka rasu. Haka akai musu suttura ba tare da mahaifiyar su ta gansu ba. Lokacin da Rumaisa ta samu labari kusan hauka ta kusa yi uwa uba akace ba zata sake haihuwa ba Wannan dalilin ya sanya ta saka damuwa a ranta ƙwarai da gaske. Bayan sati biyu ta tattara ta koma Dubai hakan ya yi wa Bulama daɗi ya ƙara samun damar da zai zauna da Saudat, a lokacin ne kuma labarin rasuwar P.A ɗin Rumaisa ya riskesu ya yi hatsari ya rasu da shi da motar gaba ɗaya suka ƙone ƙurmus. Bulama ya sanya wa ransa samun dukiyar Rumaisa ko ta halin yaya ne ta zama mallakinsa. Lokacin guda ya shiga amsar kuɗi wajanta da niyyar zai buɗe wasu, kamfanoni wani lokacin yace kuɗin sun gaza wani lokacin ya ce za a ƙaro kaya, wani lokacin ya ce ta bashi rance. Yarda da amincin da tai masa sai ta kalle shi tare da yin murmushi ta ce "Wanne irin rance ya kai Yusuf dukiyata taka ce dani da duk abin dana mallaka naka ne" idan Rumaisa ta faɗi haka sai Dr Bulama ya rungume ta tsam a jikinsa tare da maganganun masu daɗi. Ganin abubuwa sun fara runcaɓewa Rumaisa ga P.A ɗinta ya rasu ya sanya ta ɗakko Abdullah ƙaninta ta dawo da shi wajanta, tare da ragama wasu gefe na dukiyoyinta yana kulawa dasu ta bashi matsayin sabon P.A Daga nan ganin Dr Bulama ya ƙara yiwa Rumaisa wahala a cewar shi aiki ne ya yi masa yawa sosai, lokacin kuma tuni Saudat ta samu cikin Meenal farin ciki wajan Bulama ba a magana, ya tattara ya manta da batun ya taɓa haihuwar yara bai kuma damu da rashin haihuwar Rumaisa ba. Da Meenal ta girma ya ƙara himma wajan kwashe dukiyar Rumaisa lokacin Abdullah ya tsaya tsayin daka akan kuɗin da ƙyar suke fita, sbd a kaso goma na dukiyar Rumaisa bai fi kaso huɗu ya rage mata ba. Babban dalilin daya sanya Rumaisa shiga tashin hankalin har ta saka aka rufe sabon companyn data buɗe. Wannan kenan. Waje ya yi shiru cikin kuka Rumaisa ta ce "Wace kuma Meenal daga ina aka sameta shin itama yarinya ta ce?" Dr Bulama ya kasa cewa komai zufa na yanko masa sosai. A hankali Adnan ya sauke numfashi yana ƙara rungume Little a jikinsa ya ce. "Ƴar ce wacce matar shi ta haifa masa" "Ƴa tare da wata matar Yusuf? Da gaske ne abin da ake faɗa Ya kai Yusuf kada kayi mini ƙarya na amince da kai" Gaba ɗaya mutanan parlourn suka zuba wa Ummi idanu cike da tausayawa ya aka ƙare da kishiyar daka sani ma balle wacce akai a bayan idanun ka, uwa uba auren cin amana anyi mata kishiya da kuɗin ta. Cikin gunjin kuka sosai Ummi ta ce "Yusuf ka cuce ni kaci amanata, kaci amanar yarda da amincin da nayi maka na tsayin shekara da shekaru, kayi aure da dukiyata without knowing everyone Wallahi Wallahi Allah.....," Da sauri Abba ya ce "A'a Hajiya Rumaisa kada ayi haka, kiyi haƙuri don Allah ai ba a tabbatar auren ya yi ba" ya juya kan Adnan yana nuna shi da hannu ya ce. "Kai kuma kada na sake jin bakinka manya na magana" "I'm sorry Abba" Abba ya watsa masa harara ya ce "sorry for yourself Adnan Aliyu Matawalle" Adnan yai shiru. Abbi ya sauke numfashi yana mamakin rayuwa yadda bata da tabbas ɗin nan cikin nutsuwa ya ce. "Yanzu Dr da gaske dai kana da wata mata bayan Rumaisa?" kan Dr a ƙasa ya ce. "Gaskiya ne ina da mata Saudat na aureta ba tare da sanin Rumaisa ba, amma ita Saudat ta san da zaman Rumaisa ina da yarinyar Meenal ita ce wacce nake cewa wani ma'aikacina bashi da lafiya" Ya juya gaba ɗaya zai magana Ummi ta girgiza kai tana ɗaga masa hannu alamar bata buƙatar jin komai. "Ina yarinyar tawa? Kuyi haƙuri na kasa jurewa" Murmushi kawai Abbi ya yi ya shiga faɗin "Daughter, Afra... Come here your parents are here" da gudu Afra ta fito daga cikin ɗaki kamar me jira. Tana fitowa Ummi ta miƙe tsaye hawaye na zuba daga cikin idanunta ta warewa Afra hannu muryar ta na rawa ta ce. "Masha Allah, Allahamdulillah ta'al ya ɗiyata" Ummi ta faɗa a bayyane farin ciki ya sanya Afra kasa motsa wa ta durƙushe a wajan ta shiga rusa kuka da dukkan ƙarfinta. Ummi da kanta ta kama Afra ta rungome itama hawayen take sosai. Bulama ya kasa koda motsi sbd matsanancin kunya da kuma tsoron matakin da Ummi zata ɗauka. Shi kansa kallon Afra yake yana ji tamkar ya rungume ta. Murmushin fuskar Abdullah ya kasa ɓoyewa kusan yafi kowa jin daɗi a yadda fuskarsa ta nuna, at least Yayar tasa zata samu nutsuwar zuciya. Bayan komai ya lafa Abbi ya kalli Afra ya ce "Daughter inama kika ce an tsinceki" tana jikin Ummi muryar ta har lokacin rawa take ta ce "Baba ya ce wai ko wata rana yaje daji neman wani magani aka fara harbe harbe ya labe wani waje ya daɗe a wajan kafin ya fito daga inda ya ɓoye, yana fitowa idanunsa ya sauka akan wani mafarauci wanda yake kwance anyi masa harbi wajan huɗu, daga gefen shi kuma yaga wata jaririya kwance tana kuka, hakan yasa ya ɗauki Jaririyar taho hanyar gida shi ne yaje wajan ƴan sanda amma ya ɓoye labarin kisan yace kawai tsinta ta ya yi" Adnan ya kalleta domin ba haka ta faɗa masa ba, kamar mai karantar zuciyarsa ta ce "Wannan shi ne gaskiyar maganar Baba ya ce na ɓoye duk wanda ya tambaya na dinga faɗar abin da ya faɗa mini, sai na samu iyaye na gsky zan faɗi gaskiyar Abin" Cike da gamsuwa Abbi ya jinjina kai ya ce. "Babu mal wanda suke kashe mafaraucin nan sune kidnappers ɗin da muka kama cikin daji a can muka samu Abra, har wani yace mini wancan tasu ce kada na taɓa ta babu ko shakka a wajansu ta rayuwa tsayin shekaru uku har ta samu matsalar kunne, Allah mai iko Al-hakkumu bowayi gagara misali Allah mai yin Yadda ya su, ina ganin matsalar mu ta zo kusan ƙarshe" "Gaskiya kam abin da yake ɓoye ya fito, saura nemawa Salmanun-faris auren Afra yanzu a gaban iyayenta" Abbi ya yi saurin cewa. "A'a ba za a yi haka ba, ina da wacce zan bawa Salman Please Alhaji Aliyu" "Shi Salman ɗin ya ce baya son Afra? Kai Salman kana son ta ko ya ya?" Ya faɗa yana kallon Salman wanda zuciyar shi ta fara harbawa da jin maganar ta Abbinsa. Kasa cewa komai ya yi sbd Kunya kansa a ƙasa. "Kaga ni ma kamar uba nake wajanka kada kaji komai yanzu zan amsar maka auren Afra da izinin Ubangiji" Salman ya ɗago kai suka haɗa idanu da Afra tayi saurin rufe fuskarta a jikin Ummi. Ya ce "E, Abba ina son ta and I want marry her" "Masha Allah Ubangiji ya sanya albarka" ya juya kan Dr Bulama wanda ya kasa cewa komai ya ce "Dr muna neman alfarmar wajanka, idan babu damuwa muna buƙatar ka yarje mana akan nemawa Salman auren Afra" kafin Dr Bulama ya yi magana Ummi ta ce. "Sannu Alhaji, yanzu ɗiyata bata da wani Uba wanda ya shige ni, ni ce uwarta ni ce uban ta, Abdullah zai zama waliyi a gare ta" "Kada ki yi making decision cikin fushi uba, Uba ne komai lalacewar shi" "Don Allah kayi mini wannan alfarmar zuciyata a kusa take" Abba ya ce "To shikenan Allah ya yi mana maganin komai sai haƙuri" Ummi tai murmushin baƙin ciki ta ce "Afra daman taku ce ni kawai ƴar kallo ce an baku ita halak malak" Da sauri Adnan ya miƙe tsaye tare da Aishatul-humaira da sauri Mami ta ce. "Adnan son Ina zaka da Mamana?" Kasa yi mata magana ya yi, ya nufi ƙofar fita tari na sarƙe shi ya fara yi babu ƙaƙƙautawa jini na zuba, Little ta fara kuka tana ƙanƙame mahaifin nata da sauri Abbi ya miƙe shi da Hajiya Mama. Mami ta karɓi Little tana faɗin "Subuhanallah sannu Son" Abba ya kasa motsa wa tausayin tilon ɗanshi ya mamaye zuciyarshi amma duk abin da ya same shi, shi ne ya kawa kansa. "Ya Salam sannu Adnan, Salman get the car immediately, zamu koma hospital" hankalin Hajiya Mama ya tashi suka nufi asibiti da Adnan Little na ihu tana buga ƙafa zata bi ubanta sbd ta fara gane shi. Abba ya dafe kansa da hannu bibbiyu fargaba da tsoro ya cika masa zuciya. "Daman bashi da lafiya ne? Allahu ya sauwaƙe" Mami ta cewa Ummi "Amin ga grandchild ɗin naki nata rigima" Ummi tai murmushi ko inda Dr Bulama yake bata kallo yana son cewa zai duba Adnan amma babu mai yarda da shi. Jiki a saɓole ya miƙe tare da yin waje ko zai samu peace of mind Yana fita wayar shi tai ƙara ganin number Saudat ya sanya ya yi tsaki jin kiran ya yi yawa ya ɗauka cikin faɗa ya ce "Wai ya akai ne?" Ta cikin wayar tayi dry sosai ta ce . "Oh calm down Dr Yusuf Garba Bulama" ya buɗe baki da kyau ya ce "Ni kike kiran sunana haka?" Ta ce "Daga lokacin dana san ka san su waye yaranka, ni ma na shiga nutsuwata kafin dani dakai duk mu rasa mu fara yawo a titi ya sanya na nemawa kai na mafita, while before i say anything zan fara da wanda zai girgiza maka lissafi, ni ce na sanya a kwashe Mini yaran da Matarka Rumaisa ta haifa, aka maye gurbin su da matattun yaran dana bada kwangila aka sato suma a ranar aka haife su, na shirya wannan plan ɗin da P.a ɗin Hajiya Rumaisa tare da alkawarin zan bashi miliyoyin kuɗi, dana tabbatar ya ɗakko yaran kuma bana da kuɗin nasa aka buge motar ɗaya ɗakko yaran babbar mota tabi da kansu, nayi mamakin yadda yaran suka kuɓuta domin an tabbatar da P.a da motar ƙonewa sukai, abu na farko daya bani tabbacin jininka na raye saƙon da aka bani na baka, ina buɗewa naga photon wata budurwa mai kama dakai, tare da wasiƙar cewa jininka ce" Tai dariya sosai kafin ta ce "Wannan ke nan, abu na biyu tunda yaranka sun dawo nasan kawo yanzu Matarka Rumaisa ta samu labarin aurena da kai da kuma ƴata Meenal, so dole zata ɗauki matakin cin amanar da kayi mata, kafin haihuwar guzuma ɗa kwance uwa kwance na kwashi rabona dana Meenal, duk wasu file na filayenka suna wajena wanda ka saka hannu da sunan Meenal kai da duk wani abu daka san ka mallaka, dan haka kayi ta kanka ina jiran takardar saki saduwar alheri" Kusan mutuwar tsaye Dr Bulama ya yi "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un" ya shiga faɗa tare da faɗin "Na shiga uku" yana tsaye aka fara masa messages an rufe dukkan wani acct bank ɗinsa, daga na gida zuwa na company har na asibitin wanda kuma aikin Abdullah ne ko Ummi bata sani ba ya fita zuwa baya ya shiga kiran ma'aikata. Dr ya fito da sauri daga room Abba ya kasa haƙuri ya ce "Dr ya jikan son me ya sa me shi ina ɗana" ya buga ƙafaɗar Abba ya ce "just pray for him Ita yake buƙata" Hajiya Mama ta saki kuka ta ce "Kaga abin da kake shirin jawa Adnan? Me ya sa ba zaka taya shi neman abin da yake so ba? Gashi nan zai rasa rayuwar shi yabi matar tasa" Abba dai ya kasa magana Abbi ya ce. "Insha Allah za a ba shi auren Afra indai a kanta ne" cikin sauri Abba ya ce. "Kasan Allah idan har ina raye Adnan ba zai taɓa Auren Afra ba" yana faɗin haka ya nufi office ɗin Dr ya same shi zaune bayan sun gaida Dr ya ce. "Adnan ya samu ciwon zuciya wani gefe har ya fara kumbura ayi ƙoƙarin nema masa abin da zuciyarshi ke buƙata kafin mu samu ya farfaɗo daga dugun suman da ya yi" Abba ya ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un yanzu sai yaushe zai farka?" Dr ya ce "for now ba zan iya cewa komai ba, sbd jikinsa ya yi tsanani da yawa anyi wasa da zuciyarshi" da sauri Abba ya fita waya kare a kunnenshi. Daƙiƙo na juyawa zuwa sekonni, sekonni na juyawa mintuna, mintuna na juyawa zuwa awanni, a hankali suke sauyawa zuwa yini daga yini zuwa kwana. Adnan ya ɗauki wasu kwanaki kusan arba'in a gadon asibiti ba tare daya farfaɗo ba. Har lokacin Ummi na ƙasar gidan Abbi, Bulama kullum sai ya zo Ummi bata kula shi bata nuna masa ta san Abdullah ya rufe komai nasa ba, shi ma Bulama ya kasa cewa komai. Saudat ya yi neman duniya ya rasa inda zai sameta daga ƙarshe ma wayarta baya shiga. A hankali ya shiga buɗe idanunshi wanda sukai masa sosai da sauri ya mayar da idanun ya rufe sbd hasken da ya yi masa yawa. Slowly slowly ya ƙara trying na buɗe idanun, har ganinsa ya sauka akan drip dake maƙale a jikinsa. Hannu ɗaya ya sanya ya dafe kansa dake masa ciwo a hankali ya zame hannun zuwa saitin zuciyarshi dake bugawa da ƙarfi yana jin ciwo sosai ta cikinta. "Allahamdulillah son ka farka?" Hajiya Mama ta faɗa tana yin waje kiran Dr da kuma Abba da Abbi da suke waje suna tattaunawa akan a fitar da Adnan ɗin ƙasar waje. Salman ya gyara tsaiwa ba tare da ya kalli Adnan ɗin ba, duk da cewa yana jin tausayi shi. Fararen idanunta ta ɗaga kaɗan tana kallon inda yake kwance da sauri ta ɗauke sbd wani abu mai kama da tausayi da taji.. Dr dasu Abbi suka shigo bayan Dr ya gama duba jikin ya ce. "Allahamdulillah yanzu saura a ɗora shi akan magani" Abba ya yi murmushi yana faɗin "thank you Dr" "Son ya jikin?" Cewar Abbi. Adnan ya buɗe idanu sosai kallon shi ya sauka kan Afra dake kusa da Salman, ya runtse idanun zuciyarshi na ƙara bugawa ya kalli Abbansa, da Hajiya Mama sai kuma Abbi. Ƙamshin da yaji a gefen shi na dama ya sanya ya juya dan ganin waye, ya zabura jiki na rawa ya miƙe zaune yana ƙara kallon wacce ke dab da shi, ya ƙara juyawa ya kalli ɗayar wacce ke kusa da Salman. Ya mustsika idanu tare da diruwa daka bed ɗin yana tsinke ruwan hannunsa. "Abba idanuna ya samu matsala me ya sa Afra ke rabewa gida biyu ne?" Abba yai murmushi ya ce "A Lallai mukan ras namu idanun suke, mata biyu ko wacce daban" Adnan da jikinsa ke rawa sosai ya ƙara kallon wacce ke can kusa da gadon shi ko ɗago kai ba tayi ba, ya sake kallon wacce ke kusa da Salman, ya juya ya kalli Abba. "Your wife Abra khamal Khamis" cewar Abbi Innalillahi da wani irin sauri Adnan ya nufi wajan wacce ke kusa da Salman yana zuwa Salman ya girgiza kai yana sakin murmushi ya ce. "No! Wannan is no longer your's. Is not your Abra is mine" Adnan ya juya ganin haka ya sanya wacce ke zaune kusa da gadon ta miƙe tana tsare shi da idanu sosai alamar "Don't ever trying to come" da wani irin sauri Adnan ya nufeta gadan-gadan tamkar mahaukaci..... Contact to subscribe 09047871750 [11/27, 12:18 PM] Abk: A gigice Adnan ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya sa ba kuma haukacewa zan yi ba, dan Allah ku tasheni idan bacci nake, ko dai nima mutuwa na yi ne, muka haɗu a lahira?". Abba ya ce "Ba mutuwa kai ba, da ranka abin da kayi ka ke girba, tunda an salameka sai ka tashi mu tafi" A rikice Adnan ya nufi Abra zai damƙota, amma ta zura da gudu ta ɓuya a bayan Abba, tana kallon Adnan. Afra ma tashi tayi ta koma kusa da 'yar uwatta, tare da riƙe hannun Abra , cike da so da ƙauna. Adnan ya kuma nufo su, Amma Abba ya tare shi, ya ce "Ai baka isa ba, yanzu kazo mu koma gidan Major, zamu gabatar da ita ga mahaifinta da kuma mahaifiyarta, sannan ka zauna ka gaya musu abin da ka aikatawa 'yar su". "Abba dan Allah kayi mini rai" Adnan yai maganar yana haɗa hannayensa biyu. Abba ba sani ba sabo, ya haɗe rai ya dinga yiwa Adnan tsawa, suna fitowa daga ɗakin, Salman ya kuma rungume Abra, ji yake tamkar mafarki ne, ga Abransa a kusa da shi, abu kamar mafarki haka yake ganin faruwar abubuwan, Abransa is alive. Wani baƙin ciki ya kishi ne ya mamaye zuciyar Adnan, zai yinƙura yai wajen su Salman Abba ya ce "Wallahi kai mini wani hauka, sai na ci mutuncin ka a wurin nan, wuce mu tafi" Duk in da Abra ta waiwaya 'yan uwane masoya ke ta farincikin sake ganinta. Suna zuwa gida, suka tarar da Mami, ta na ta rusawa Ammi kuka, tana cewa  akan me Major ya ɓoye mata Abra tana raye, ya jefa zuciyarta cikin ƙunci. Ai Abra ba tayi sallama ba, ta tafi da gudu, ta danne Mami tana wani irin kuka kamar wadda ranta zai fita. Kasa magana suka yi, daga Mami har Abra, tamkar Mami zata mayar da Abra cikinta,  falo ya cika ga Ammi ga Abba da mahaifin Abbi, ga su Inna da Yaya Musa, gida sai koke koke ake, Ammi ta tsare Abba da son jin dalilin da ya sanya, suka aikata musu haka a kan Abra. A hankali idon Abra ya sauka a kan Little da ke hannun Salima, Abra ta zubawa Little ido. Ammi ta ce "Kawo mata 'yar ta ta ganta, taji ɗumin 'yar ta" girgiza kai Abra tayi ta ce "Ni ba 'ya ta ba ce" Gaba ɗaya suka kalleta, Ammi ta ce "wane irin abu ne haka kuma?". "Ammi na barwa Adnan 'yar sa, ina son su fita daga rayuwata gaba ɗaya da shi da ita" tai maganar tana kuka. "Baki da hankali ne? 'yar ta ki kike cewa kin barwa babanta?". "Eh Ammi, nima haka na rayu ba iyayena, har gara ita tana da uba" Abbai zai tsawataraa Abra, amma Abba ya ce "Ƙyaleta Major, tayi mini daidai, amma muna dakon jiran wani albishir da zamu yi miki ne, kan mu fayyace musu yadda aka yi mu kai musu haka ba su sani ba". Harabar gidan Major ta cika da motoci, sai hayaniya ake ji ƙasa ƙasa tun daga harabar gidan. Falo ya cika ya batse da mutane. A tsawon Kwanakin da Rumaisa ta yi a gidan Major, taga gata da karamci, kullum Afra tana tare da ita, ga Salman da take jin shima kamar nata ne, ga kuma Little da aka ce 'yar ta ce ta mutu ta bari, gashi suka yi wani irin sabo da Na'ima, duk da zasu yi sa'anni da Naima, amma Rumaisa tana girmamata kasancewar ita ta riƙe Abra. Bulama yana nan garin Kano, kullum cikin sintiri yake gidan Major, dan ganin Rumaisa da 'yarsa da kuma jikarsa, amma sam Rumaisa tayi mursisi ta dinga surfawa Bulama rashin mutunci, dan babu babban abinda ya ƙara mata tsanarsa irin jin shine dalilin da ya sanya ta rasa 'yar ta a karo na biyu, bayan sace su da aka yi da fari. Rumaisa ta fito falon, jin yadda gida ya cika da mutane, sai dai babu zato babu tsammani idanunta suka sauka a kan Abra da ke kusa da Salman, ga kuma Afra a gefe guda. A gigice ta nufi wurin da Abra take tana sambatu. " 'ya'ya na, duk nawa me sun dawo basu mutu ba 'ya'yana ne, Abdallah zo ka gani" Rumaisa tayi maganar tana nuna Abra da Afra. Ƙurii Abra ta yiwa matar da ido, ko ba a gaya mata ba, tabbas wannan matar suna da alaƙa. Zuwa tayi ta rungumesu gaba ɗaya, ta dinga gunjin kuka, har mayafin abayarta ya cire, dogon gashinta bar tsakiyar bayanta ya sauka, tayi larabci, tayi Hausa tayi turanci. "Abra she's your Mum" Abbi ya faɗa yana kallon Abra. Wani irin zillo Abra tayi, itama ta rungume matar, tana jin wani abu ya ratsata ba tare da ta gane takamaimai menene ba. Bulama ne yayi sallama ya shigo, yana sunkuyar da kai tamkar munafuki, yana sunkuyar da kai, Yaya Musa me ya ce "Laa Inna, baki gane wannan ba?". Inna ta ce "Ina zan manta shi, baƙin tsinanne, aka kashe mini miji a Asibitinsa, shi kume meye ya kawo shi nan, baƙin Azzalimi, muna ji muna gani yaƙi zuwa kan bawan Allah nan har ya mutu" Waro idanu Afra ta yi ta ce "Kenan kai kayi sanadiyyar mutuwar Mutumin da ya riƙe ni kamar uban da ya haife ni?" Adnan ya ce "Ba mutuwar mariƙinsa kawai ba, har da kisan 'yar sa a Asibitinsa wadda ta kasance matata Abra, sai dai gata nan a gabana, na kasa gane mafarki ne ko zahiri". Bulama ya samu wuri ya zauna, ya sunkuyar da kai yana zubar da hawaye, ya ce "Haƙiƙa wannan ishara ce Allah ya nuna mini, mutane sun rasa rayukansu a saboda sakacina, da sa neman kuɗi a gabana fiye da lafiyar mutane mugun halina ya zame mini DARE DA DUHU, babu lallai 'ya'yana su ƙaunace ni, sakamakon kowacce na bar mata wani tabo mai tsayawa a zuciya, dan Allah ku yafe mini, dama hausawa na cewa, idan kana mugunta ba ka yiwa kanka ba, baka iya ba, na watsar da dangina, na zalunci matar da ta mini halacci, an salwantar da rayuwar 'ya'yana, wadda na riƙa da soyayya ta ci Amanata, gaba ɗaya rayuwata ta zama DARE DA DUHU, da bana tunanin garin zai wayewa wannan duhun dare nawa, ku yafe mini dan Allah". Rumaisa ta ce "Wallahi ba zan baka yarana ba, kuma ka tattara duk wata dukiya tawa ka bani abata, wadda ka cinye kuma, zamu haɗu a kotu, sai ka biyani" "Rumaisa duk hukuncin da kika ɗauka a kaina daidai ne, amma ni ya aka yi naga Abra, bayan an sanar da ni ta rasu?". Abba ya ce gyara zamansa sannan ya ce "Eh wannan bayanin duk shi ne ya tara mu a nan, Adnan ya auri Abra ne bayan ya gano 'yar ka ce, dan ya ɗau fansar abin da kayi masa, na sakaci mahaifiyarsa ta rasa ranta. Tsawon zaman da Abra tayi da Adnan... Adnan ya katse shi ta hanyar cewa "Dan Allah Abba kayi mini rai" A fusace Abba ya ce "Zan tsinka maka mari, ka mini shiru mutumin kawai". Abba ya ɗora da "Ya auri Abra, duk muna sa ran ya samu yarinyar kirki, suna zaune lafiya, ashe ba baka bane ba, sai ranar da Abra ta kusa rasa ranta, ya gigice ya dinga faɗar irin zaman da yai da ita, ya dinga azabtar da ita, bayan mun dawo daga wurin likita, ya bamu shawarar idan ta warke daga C.S ɗin da aka yi mata, a kaita India, saboda suna da ƙwararrun likitoci da Asibitocin da suka ƙware, a wurin bada kulawa ga masu ciwon, kuma tun da bata kai last stage ba, zata iya warkewa. Daga nan na fara processing yadda Abra zata tafi India, katsam Adnan da bakinsa ya dinga faɗar yadda ya rayu da Abra, bayan an mata C.S jikinta ya rikice, duk mun ɗauka ta rasu, a lokacin da shi mijint, da Salman da ita Maman Salman duk sun suma, Nurses sun basu ɗaki, likitoci suka zo suka dudduba Abra, ba su ce mana komai ba, suka dinga mata ƙoƙari, suna dannna ƙirjinta suna mata allurai, har Major yana cewa kar su wahalar da gawar Abra, suka ce masa bata mutu ba, suganta ne yayi ƙasa fiye da kima, jinint ma ya sauka. Cikin ikon Allah ta cigaba da numfashi, amma bata hayyacinta, a ranar na buƙaci Major, da kar mu kuskura wani ya san Abra bata mutu ba, saboda za'a kaita India ne babu tabbacin ta dawo da rai, dan haka kar musa musu rai, na ɓoye masa ainihin dalilina na rashin san kowa ya san Abra bata mutu ba. Muka tafi da Abra Abuja, na barota ita da Major, kwanan su ɗaya a General Hospital Abuja, suka tafi indiya, likitan da ya dubata ya mata cs, suka haɗamu da da likitocin Asibitin da za'a kai Abra. Cikin ikon Allah ana kaita suka karɓeta, muka biya komai aka fara bata kulawa ta musamman. Lokacin da Maman Salman ta farfaɗo mun sanar da ita, an kaita gidana an mata sutura a binneta, duk da tayi mita a kan danme za a rufe Abra ko sallama ba suyi ba. Haka Adnan muka tabattar masa da an kai gawar Abra Kano, an binneta. Major ya baro Abra a can india, amma duk sati biyu ko ni ko shi, muna zuwa mu dubata, a nan Nigeria kuma, mun saka anata saukar Alqur'ani, har umara muka biya akaje aka yiwa Abra ɗawafi, Allah ya bata lafiya, idan kuma ba zata rayu ba, Allah ya sa ta cika da imani. A cikin ƙudirar ubangiji sati uku, Abra ta fara samun Lafiya, na samu Abra na sata a gaba, ta gaya mini komai a kan zamanta da Adnan, dan da farko so tayi ta rufawa Adnan Asiri. Na roƙeta a kan kar ta gaywa Major, halin da ta zauna da Adnan. Cikin ikon Allah watanni biyar kan na shida, aka tabattar mana da Abra ta warke ras ba wata damuwa da take damunta Yanzu. Alhamdilillah, a jiya ni da Major muka ɗauko Abra daga airport, ta kwana a gidan wani abokinsa, da safe muka wuce da ita Asibitin da mijinta yake, muka taho nan, haƙiƙa mun ɓata muku na ɓoye muku gaskiyar cewa Abra na raye, amma dan Allah kuyi mana afuwa. Zan yi amfani da wannan dama, wajen karɓar takardar sakin Abra daga hannunka Adnan, ka rubuta saki ka bani na Abra, zan mayar da ita Makaranta". "Haba Abba, Wallahi nayi nadama ka duba halin da nake ciki, na san tabbas a kowane lokaci zan iya rasa raina, dan Allah ku bari mu ƙarasa rayuwarmu tare, ko dan saboda yarinyar mu*. Rumaisa kuwa cewa ta ke "Dan Allah ita dai in ya saki Abran, a haɗa mata kan yaranta ta tafi da su". Adnan a ransa ya ce "Ji wannan matar da son kai, Wallahi ba in da matata zata da Aurena". Bulama ya ce "Dan Allah Afra, da kuma Abra dan Allah ku yafe mini, ku kalleni a matsayin uba ko sau ɗaya a rayuwata, yanzu bani da wani abu da yayi mini saura idan baku ba, hatta 'yan uwana basa ta tawa, saboda Saudat ta rabani da su". Gaba daya duk ɗokin da Afra take a kan son ganin mahaifinta, taji baƙi cikin kasancewar wannan azzalumin shine mahaifinsu, ba zata manta yadda aka bata labarin yadda ya wulaƙanta Baba har ya mutu ba, gaba ɗaya bai bata tausayi ba, mussaman da aka bada labarin cin amanar da ya yiwa mahaifiyarsu.   Kowa da abin da ya dame shi a falon nan, kowa neman mafitar kansa kawai yake yi, gaba ɗaya kan Abra ya fara ɗaukar zafi, dan haka ta miƙe ta nufi ɗakinta, wanda Afra ce a ciki Yanzu. Kan gadon taje ta haye tana kuka, yau ranar farinciki ce a gareta, ko ta baƙi ciki? Ya aka yi suka fito daga tsatson azzalumi irin wannan mutumin? Duk yanayi na rashin lafiya da Adnan yake ciki, haka ya tashi yabi bayan Abra. Yana zuwa ya fara ƙoƙarin abin da zuciyarsa ke muradi, wato ya rungumi Abra a jikinsa. Duka ta fara kai masa ta ko ina tana kuka "Adnan ka cikani na tsaneka, Azzalimi sai ka sakeni ka daina wani pretending ma". "Abra nayi kewarki, harshe ba zai iya bayyana abin da ke cikin zuciya ba, dan Allah ki yafe mini, mu koma mu zauna na miki tanadin soyayya irin wadda baki taɓa tunanin akwai taba". "To hell with your fucking useless love Adnan, duk wata soyayya idan har daga gareka take iska ce da shirme, kuma aikin banza, maƙaryaci, mayaudari, kuma maha'inci, ka aureni ka cutar da ni cutarwa mai muni, na tsane ka ko ƙaunar ganinka bana yi". Cikin hawaye Adnan ya ce "Abra, nine fa Adnan, baban yarinyarki amma kike gaya mini haka?". "Kaje kai da 'yar na bar maka, bana son duk wani abu da ya shafeka, dan haka ka tafi da 'yar ka na baka, kar ka sake zuwa in da nake" "Abra dan girman Allah. "Dan Allah Adnan ka rabu dani, ka bar mini wurin nan, tun kan in maka illa, Wallahi na tsnake, baka da bakin da zaka iya bani haƙurin da zai wanke zaluncin da ka yi mini, rashin lafiyata ƙuruciyata da maraicina a wannan lokacin bai sa ka tausaya mini na tsira daga rashin imaninka ba, na dinga binka a kan gwiwowina ina kuka, amma sau ɗaya baka kalleni da idon rahama ba, kome nayi maka kai ka koya mini, dan haka ka rabu da ni" ta ƙarasa Maganar tare da ficewa daga ɗakin ta bar Adnan saroro yana kallonta, bai taɓa zaton Abra ta iya wannan rashin mutunci ba. Falo fa ya rikice, dan Bulama har da hawaye, amma Afra taƙi ko kallonsa, dan ko fuskarsa bata son gani, ga rigima ta kacame tsakaninsa da Rumaisa na sai ya dawo mata da duk dukiyarta, kuma ta saka rigima a kan da yaranta zata tafi. Salima dai ta zama 'yar kallo, komai ya kwaɓe ba mai jin kan wani. Abbi kuwa ya ce "Ko nan da airport babu mai zuwar masa da yaransa, ba za su bawa Rumaisa yaran nan ba" aikuwa ta sa musu kuka ta ce bata yarda ba. Abbi ya ce "Ba muna son mu rabaki da yaranki bane ba, amma kinga Abra tana da Aure, Afra kuma very soon za'a ɗaura mata aure, kinga ba zasu bar aurensu su biki ba, sai dai ki dawo ki zauna da mijinki, wato babansu a Nigeria, yadda zaki dinga ganinsu. Aikuwa Rumaisa tai tsalle ta ce ko ana ha maza ha mata, ba zata zauna da Bulama ba, itama wataran kasheta zai yi, ko ya dawo ya kashe mata 'ya'ya, dan haka kotu zata kai shi, a raba aurensu a bata yaranta, dan kar a kuma kashe mata su. Gaba ɗaya fa gida ya sake rikicewa, ana wannan turka turka, Adnan ya kuma dawowa falo, ya zube a gaban Abbi ya haɗa hannayensa ya ce "Dan Allah Abbi, na tuba nayi nadama, na san nayi wauta, amma dan Allah ayi haƙuri, ina cike da baƙincikin rashin mahaifiyata, da kusan aka kashe mini ita a kan idona, saboda sakaci da son zuciya na wannan mutumin" "Ka gayar kalamanka, kar ka sake ka kausasa harshe a kan mahaifina, duk lalacewar iyaye iyaye ne, balle babu lalacewa a iyaye, ƙaddara bata wuce kan kowa ba" Abra tayi maganar cikin rauni, tana kallon Bulama amma ta kasa jin ɗigon soyayyar Bulama a ranta, tabbas ya cutar da Adnan, mussaman yadda ya bada labarin a yadda mahaifiyar tasa ta rasa ranta. Abba ya girgiza kai ya ce "Adnan ka bani kunya, yarda da irin soyayyar da Abra take maka, ya sa na haƙura na aura maka ita, ba dan ina so ba, dan a son samuna tayi karatu, amma ganin tana sonka ya sanya na aura maka ita, amma kaci amana Adnan, ina son Abra a zuciyata fiye da yadda nake jin Salman ɗan da na haifa, dan haka nima ba zan takurata ba, ka rubuta takardarta ka bani kan ka bar garin Kano". "Mama dan Allah ki saka baki, Mami kema kiyi magana su bani matata dan girman Allah". Mami ta haɗe rai ta ce "A'a ka bar mini 'ya ta ta huta, gara ta dawo gabana ban gaji da ganinta ba, balle ka kashe ta a banza da baƙinciki a kan laifina da baita ta aikata ba" Wata irin Soyayar Hajiya Na'ima ta kuma mamaye zuciyar Abra, duk da irin wahalar da ta sha a hannunta, amma tana son baiwar Allah nan, saboda ta bawa ratuwarta gudunmuwa sosai. Hajiya Mama tace "Allah ya sa ya zame maka darasi, har kullum da laifukan da kake yiwa Allah, da su yake maka hukunci, da baka rayu yadda kake so ba, amma ka ɗau fansa a kan wadda ita kanta bata san waye mahaifin nata ba, kuma tai shiru ta rufa maka asiri, duk da tana ƙishirwar son sanin mahaifinta, amma hakan bai sanya ta tona maka asiri ba, lallai Abra ta cancanci yabo, ta soka tsakani da Allah amma ka rusa damarka". Abba ya ce "Ku kuka tsaya biye ta tasa, Salmanj kawo takarda ya saketa ta huta" aikuwa Salman ya zaro jotter da biro ya miƙo, tabbas da Adnan na kusa da Salman ba abin da zai hana ya fasawa Salman baki. Abba ya wurgo masa takardar ya ce "Saketa maza, daga nan ta wuce Dubai  wurin mamanta, ta huta itama" "Dan Allah Abba kayi haƙuri, ba zan iya ba"   Wayar Bulama tayi ringing babu adadi, ya ɗauko wayar a hasale ya ɗaga wayar. "Gwamnati ta rufe maka Asibitinka, kuma an turo maka sammaci daga kotu, an kai ƙararka da Asibitinka" [11/28, 8:05 PM] Abk: Muryar wani mutum ta doki dodon kunnansa a kausashe da faɗin haka. Rarraba ido ya fara yi cikin rawar murya ya ce. "Ban gane ba, wa..wake magana?" "Ba ka da buƙatar sanin hakan, kai dai kawai ka amsa kiran kotu, an je gidanka har sau uku ba ka nan, shi ya sa muka nemi lambar wayarka don mu sanar maka, takardar sammacin tana hannun mai gadinka." Daga haka aka katse kiran. Gumi ne ya shiga tsatstsafowa a jikinsa duk da ac dake parlour'n, gabaɗaya mutanen gurin kallon shi suke cikin neman ƙarin bayani. Taɓe baki Ummi ta yi cikin harshen turanci ta ce. "In dai bala'i ne yanzu ka fara ganin shi a cikin rayuwarka Yusuf, tunda ka fifita kuɗi fiye da komai a duniya, ciki har da tsoron Allan ka. Ka zaɓi rayuwar cin zali da rashin tausayi ga wanda ba shi da shi, a garin hakan har mutumin da ya riƙe maka ƴarka ya mutu, wallahi ka yi asarar rayuwarka." Ta yi maganar cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar shi. Girgiza kai Abba ya yi cikin Dattaku ya ce. "Yanzu me ya faru? Me aka ce maka a wayar?" Cikin raunin murya ya ce. "Daga court aka kira ni, an kama asibitina tare da turo mini takardar sammaci." "Subhanallahi, Ubangiji ya kawo maka mafita." Abbi ya faɗa cikin tausayawa Hawaye Bulama ya fara tare da faɗin. "Ko me ya faru da ni, ni na janyo wa kaina, na biye wa son zuciyata na yi ta aikata kuskure, duk da na san hakan ba daidai ba ne, Ubangiji kuma ya yi ta ba ni nasara, fiye da shekara ashirin ban taɓa fuskantar wani ƙalubale akan abin da nake aikatawa ba sai yanzu komai ya rincaɓe mini." Ya nisa sannan ya cigaba da magana. "Na rasa matata mai ƙaunata da ta ba ni dukkan yardarta, sannan na rasa soyayyar Ƴaƴana waɗanda duk duniya babu abin da na ji ina so sama da su a yanzu. Tabbas bahaushe ya yi gaskiya da ya ce. "Rana dubu ta ɓarawo, rana ɗaya tak ta mai kaya." Wani mugun kallo Adnan ya wurga masa cikin tsana, ko kaɗan bai ji tausayin shi ba, sai ma takaicin shi da ya ƙara cika zuciyarsa, saboda shi ne Ummul aba'isin duk abubuwan da suka faru. Kasa magana kowa ya yi, Abra Sarkin kuka sai hawaye take yi, zuciyarta ta karye, wani irin tausayin mahaifinta ya cika mata zuciya. Miƙewa Bulama ya yi ya kalli Ummi da su Afra ya ce. "Zan tafi cikin baƙin cikin tsana na da nake gani kwance akan fuskokinku, amma don Allah ina roƙon ku alfarma guda ɗaya, ku yafe mini, ku kuma kasance masu yi mini addu'a, domin na san da ƙyar mu ƙara haɗuwa, saboda abubuwan da na aikata na cancanci zaman gidan kaso na har abada, kotu za ta iya yanke mini hukuncin ɗaurin rai da rai." Kawar da kai Ummi ta yi cikin ƙoƙarin danne tausayin shi da ya taso mata, duk da cikin harshen Hausa ya yi maganar amma yanayin da yake ya karyar mata da zuciya. Tashi Abra da ta fi su raguwar zuciya ta yi ta rungume shi tare da fashewa da kuka. Duk lalacewar Uba, Uba ne, kuma hannunka ba ya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar. A hankali Afra ta tashi ta ƙarasa ta janye Abra, cikin ɗacin zuciya ta ce. "Wannan mutumin ba abun tausayi ba ne, kar ki bari wannan kalaman yaudarar tasa da marairaicewar da ya yi su yi tasiri a zuciyarki, domin shi bai san hakan ba ga al'umma, wallahi ba zan taɓa yafe masa mutuwar da Babana mai ƙaunata ya yi ba saboda shi, taho mu bar kusa da shi kar baƙin....." Da sauri Abra ta toshe mata baki da hannunta tare da girgiza mata kai ta ce. "Ki daina faɗar haka ƴar'uwata, duk lalacewar shi mahaifinmu ne, shi ya yi sanadin kawo mu duniya, ko da kowa ya ƙi shi bai kamata mu ƙi shi ba, kar ki manta da Uba ake ado, a lokacin da ba mu san shi ba muke cikin ƙishirwar ganin shi addu'a muke ko yaya yake Allah ya nuna mana shi, yau ga shi Ubangiji ya amsa addu'armu, bai kamata kuma mu butulce masa ba. Wannan halayyar tasa ƙaddararsa ce a haka da mu baki ɗaya, Ubangiji ya riga ya rubuta duk abin da ya faru sai ya faru, babu yadda za mu yi." Ta ƙarashe maganar cikin kuka mai taɓa zuciya. Rungume ta Afra ta yi cikin hawaye, kalaman ƴar'uwar tata sun tsinka mata zuciya. Babu wanda tausayin su Abra bai ratsa wa zuciya ba a gurin, musamman Ummi da take ganin kamar ita ce ba ta zaɓa musu Uba na gari ba. Kan Bulama a ƙasa cikin tsananin jin kunya da nadama ya fice daga parlour'n cikin harɗewar ƙafa tamkar mai koyon tafiya, Abra da Afra suka raka shi da ido cikin wani irin yanayi. Tasowa Ummi ta yi ta rungume ƴaƴanta suka cigaba da kukan a tare. Bayan sun nutse sun yi shiru Baffa da tun ɗazu bai ce komai ba sai nazartar kowa da yake ya gyara zama ya ce. "Alhamdulillah komai ya yi farko zai yi ƙarshe, kuma komai na rayuwa nan mai wucewa ne. Tashin hankali da rashin nutsuwar zuci da Yusuf Bulama ya tsinci kansa a ciki ya ishe mu ishara da sauran masu irin halayyar shi. Allah ya sa mu dace, ya sa mu fi ƙarfin zuƙatanmu." Gabaɗaya suka amsa da Amin. Abba da bai manta da batun sakin Abra ba ya dubi Adnan ya ce. "Yanzu kai kaɗai muke jira, ka ba mu takardar sakin Abra." Kuka Adnan ya fashe da shi zai yi magana Abba ya ɗaga masa hannu tare da faɗin. "Idan har ba ka yi abin da na umarce ka ba a yanzu to ka sani babu ni babu ka..." "Ashsha! Me ya yi zafi haka Alhaji? Duk abin bai kai haka ba, abi komai a sannu. Saki ai ba shi ne mafita ba, Ubangiji ma da ya halatta a yi shi ba ya son a yi shi, yanzu a bar wannan maganar don Allah, na roƙi wannan alfarmar, a taimaka a yi mini ita." Baffa ya katse Abba da faɗin haka. "Amma Baffa da ka bari ya sake tan, tunda yarinyar ita ma ba ta son shi a yanzu." "Idan ba ta so babu mai yi mata dolen sai ta koma, amma abun da nake so a ba ta lokaci ta huta ta yi tunani, idan har lokacin da aka ba tan ta ce ba ta son shi ni da kaina zan karɓar mata takardar saki a hannun Adnan. Don mu sulhu muke so ba ɓatawa ba." Cikin gamsuwa Abbi ya ce. "Haka ne, na gamsu da bayaninka sosai Baffa, a ba ta lokacin, ko dan darajar yarinyar dake tsakaninsu." Ajiyar zuciya mai ƙarfi Adnan ya sauke ya cillar da jorter da pen ɗin hannunsa ya rarrafa gaban Baffa ya dinga kwarara masa godiya. Murmushi Baffa ya yi ya shafa kan Adnan ya ce. "Ba komai yaron kirki, kai dai ka dage da addu'a da kyautata mata, hakan zai taimaka gurin kankare mikin da ka yi mata a cikin zuciyarta." Gyaɗa masa kai ya yi idonsa a kan Abra, wadda ke wurga masa muguwar harara. "Yanzu tsawon wanne lokaci za a ba ta kafin a ƙara jin ta bakinta?" Abba ya tambaya. "A ba ta wata guda." "Shikenan Allah ya kai mu lafiya, amma kafin lokacin ina son a yi bikin Salman da Afra." Dam zuciyar Abra ta buga, Faris ɗinta ne zai auri ƴar'uwarta? 'Ya Allah.' ta faɗa a cikin zuciyarta tare da yin ƙasa da kanta cikin wani irin yanayi na karayar zuci. Salman dake lura da ita ya sauke numfashi, so yake su haɗa ido amma ta ƙi ɗago kanta. "Please ku bar maganar auren nan? Ku ba ni na tafi da ƴaƴana can ƙasata." Ummi ta faɗa cikin hawaye. "Babu mai hana ki Ƴaƴanki duk duniyar nan, amma tunda suna son junansu ita da Salman ki bari a ɗaura auren sai ku tafi dukanku har shi, mun san kin yi haƙuri na zaman da kika yi a nan tsawon lokaci, ga ƴan'uwanki suna ta son ki koma don su gan ki dake Ƴaƴanki, amma ki ƙara wani haƙurin, ana ɗaura auren da sati biyu insha Allahu za ku tafi." Tana ganin mutuncin Baffa sosai kuma ba za ta iya jayayya da shi ba, kallon Uba take masa tunda ya haife ta, hakan ya sa ta ce masa ta amince. Tashi suka yi suka bar iya su Abbi a parlour'n suka ƙara tattaunawa, sun tsayar da lokacin bikin sati uku masu zuwa. Su Abra sun fito suna yi wa Abba da su tafi sallama Adnan ya kafe ta da ido, duk da tana jin kaifin idonsa a jikinta amma ta ƙi kallon inda yake. Ganin hankalin su Abba ba ya kansu Salman ya ƙaraso ya kama hannunta. "I'm sorry my angel." Ya faɗa kamar zai yi kuka. Ƙasa ta yi da kanta ba ta ce komai ba, damƙe hannunta ya yi a cikin nasa cikin raunin murya ya ce. "Ban yi zaton zan ƙara ganin ki ba a rayuwata, na sha wahala sosai dalilin rashin ki, daga baya Ubangiji ya sako mini dangana na haƙura, duk da soyayyar ki tana nan a cikin zuciyata ko ɗigo ba ta ragu ba. Shigowar Afra cikin rayuwata ya warkar da duk mikin rashin ki a cikin rayuwata, saboda ganin na samu madadin ki." Murmushi Abra ta yi cikin ƙarfin hali ta ce. "Wannan bayanin duk na mene ne bro?" "Na son da kike mini ne da wanda nake miki." Murmushi ta yi ta ce. "Da ni da Afra duk ɗaya ne, tunda tana son ka kana son ta ku yi auran ku, kuma ina son sanar maka na fi kowa farinciki da hakan." Cikin ɗaga gira ya ce. "Sure?" "Of course ɗan ƙanina." Ɓata fuska ya yi ya ce. "Yanzu ni ne babba ai, tunda zan auri yayarki." Cikin dariya ta ce. "Son girman naka har ya kai ka fitar da babba a cikinmu ba tare da an faɗa maka ba?" "Na san ita ce ai, jikina ya ba ni." "Shikenan na ɗauki ƙanƙantar Yaya Faris." Murmushi suka yi a tare cikin ƙaunar junansu. Adnan dake kallon su ya ji zuciyarsa na wari irin tafarfasa saboda kishi, a fusace ya taho zai zare hannun Abra daga cikin na Salman tare da ja masa warning, taku ɗaya ya yi tari ya sarƙe shi. Da sauri Abbi ya kama shi suka fita ganin ya fara aman jini. Taɓe baki Abra ta yi tare da shigewa ciki, Salman ya bi ta da kallo. Ya san Yayarsa tana son shi har yanzu shi ma kuma haka, amma shi ya fi son ta koma gidan Adnan ko dan little, ba ya son yarinyar ta taso ta ga iyayenta ba sa tare. Sannan Afra tana mugun son shi, a zaman da suka yi tare shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakanin su, idan ya ce Abra yake so ba ita ba za ta shiga mawuyacin hali. Ɗakinta ta shiga ta tarar da Ummi da Inna a zaune. Zama ta yi a kusa da Ummi dake sakar mata murmushi. "Allah ya yi muku albarka." Ummi ta faɗa tana shafa kanta. Cikin jin daɗin kasancewa da mahaifiya Abra ta ce. "Amin." Kwantar da kanta ta yi akan kafaɗar Ummi ta ce. "A Ina ƴan'uwan mahaifinmu suke a ƙasar nan? Ina son mu haɗu da su." Ɓata fuska Ummi ta yi alamun ba ta san zancen Bulama, amma duk da ƙin shi da take ta san ba ta isa ta raba shi da Ƴaƴansa ba. Kamar an mata dole ta ce. "Suna Adamawa, amma iyayensa duk sun rasu, sai ƙanwarsa guda ɗaya Murja da sauran relatives ɗinsu." Kafin Abra ta kuma magana Afra ta shigo da Little a hannunta. Ba tare da yi magana ta ɗora ta a kan cinyar Abra. Kawar da kanta ta yi duk da cikin ranta cike take da zumuɗin ganin fuskar ƴar tata. "Ki ɗauki ƴarki, wannan abin da kike yi ba daidai ba ne, tunda ba ta miki laifin komai ba, bai kamata kuma laifin mahaifinta ya shafe mata ba." Afra ta faɗa cikin sigar nasiha. Murmushi Inna ta yi a ranta tana mamakin hankalin da ƴar Baba ta yi a zamanta a gidan Abbi. Rungume little Abra ta yi tare da sakin ajiyar zuciya, ƙaunar yarinyar na ratsa ko wane saƙo na jikinta, ta ji duk duniya babu abin da ba za ta iya yi ba saboda ita. Haɗa su Ummi ta yi ta rungume gabaɗaya tana hawayen farinciki, Afra ta zo ta zauna a ɗaya b'arin ita ma ta rungume ta, ban da ajiyar zuciya da hawaye babu abin da suke. Haka rayuwa ta cigaba da garawa cikin farinciki ga su Abra, duk da tunanin mahaifinsu da halin da yake ciki yana damun su. Sun samu labarin har yanzu ana shari'a akan asibinsa ba a ƙare ba, kuma kotu ta ƙi bayar da belin shi yana can a tsare. Shirye-shiryen bikin Salman da Afra ya kankama, Abbi ya sa an ƙara gyara wa Salman guest house ɗinsa, a can za su tare shi da amaryarsa da suke cin soyayyar su babu tsinke. Abra ta kwantar da hankalinta, ta cigaba da kallon Salman a matsayin blood brother ɗinta. Aunty Murja ta zo tun saura kwana uku biki, Ummi ta kira ta, ta sanar da ita duk abin da yake faruwa, da yake suna shiri sosai. Amma fa ta sha ciwon bakin ƙin sanar mata Bulama ya ƙara aure da ta yi. Adnan yana can jiki ya ƙara rincaɓewa, kuma ya ƙi yarda a fitar da shi waje, ya ce maganin ciwon shi kawai Abra ce. Abba kuma ya ƙyale shi ya ce ya je jikinsa ne, shi yake shan azabar ciwo ba wani ba. Kullum sai ya kira Abra ba adadi, ita kuma ba ta ɗaukar kiran, mamakin ma inda ya samu numbernta take, saboda sabon sim ta sake. An yi biki lafiya an gama lafiya, ba a wani ja abun sosai ba, dinner kawai aka yi da ɗaurin Aure aka kai amarya gidanta. Ranar Afra ta sha kuka, na barin su Inna da kewar Baba, ta so a ce ya ga ranar aurenta kamar yadda ya ci buri, amma Allah bai yi ba. Abra ma ta taya ta kukan, don duk da ba su jima da kasancewa da juna tare ba amma ta ji ba daɗi sosai a cikin ranta, a gefe kuma ta taya ta farinciki matuƙa na auren Namiji Jarumi, Yaro da halin manya Salmanul Farisi. Washegari da safe Afra tana baccin gajiyar da Salman ya tara mata a daren jiya ta ji ana yi mata tafiyar tsutsa a ƙafa. A hankali ta buɗe kumburarrun idonta da suka ci kuka ta sauke a kan fuskarsa. Murmushinsa mai kyau ya sakar mata tare da ranƙwafowa cikin sanyin murya ya ce. "Morning princess." Juyar da kanta ta yi gefe tare da turo baki. Kissing lips ɗinta ya yi tare da faɗin. "Tun ɗazu nake jiran ki tashi ki yi breakfast kar yunwa ta illata mini ke, kuma bana son na tashe ki kanki ya yi ciwo." Cikin shagwaɓa ta ce. "Ai dama ciwon yake." Marairaice fuska ya yi ya ce. "I'm sorry dear, mu je ki wanka sai ki sha magani, idan bai daina ciwon ba sai mu je asibiti." Riƙe duvet ɗin da yake ƙoƙarin yayewa ta yi ta ce. "To ka bar ni zan tashi da kaina." Murmushi ya yi cikin ransa yana faɗin. "Wanne dare ne jemege bai gani ba." Ƙarar da ta saka ya sa shi saurin ɗago ta yana tambayar ta lafiya? Hawaye ta fara ta ce. "Na kasa tashi, ko'ina a jikina duk ciwo yake mini, ƙafafuwana kamar ba a jikina suke ba. Cikin tausayawa ya shafa kanta tare da faɗin. "Sorry, har yanzu jikin bai bar ciwo ba?" Gyaɗa masa kai tare da taune lips ɗinta saboda zugin da take ji a ƙasanta. "Okay bari na ga gurin ko da rauni." Kuka ta saka masa tare da ƙanƙame jikinta ta hana shi ganin abin da yake son ganin. Numfashi ya sauke a hankali tare da saka hannu ya fara goge mata hawayen fuskarta, ture hannun ta yi tare da ƙoƙarin tashi daga jikinsa. Riƙe ta ya yi sosai cikin rarrashi ya ce. "Har yanzu fushin bai ƙare ba? Na ce fa ba zan kuma fa, jiyan ma duk ke kika ruɗani da kyawun da kika yi da daddaɗan ƙamshin da kike." Ya ƙarasa maganar tare da tusa kansa a wuyanta yana shaƙar ƙamshinta dake saukar masa da kasala. Ajiyar zuciya suka sauke a tare da lumshe ido. Jin ya fara sassauke numfashi tare da yawo da hannunsa a jikinta ya sa ta buɗe ido da sauri tare da ture kansa, don ba ta manta bak'ar azabar da ta sha ba a hannunsa jiya. Bai ce komai ba ya ɗauke ta cak ya kai ta toilet. Littafin dare da duhu na kuɗi ne, mai so ya tuntube mu a wannan numbern. 09047871750 [11/30, 9:12 PM] Abk: Da yamma Salman na zaune a parlourn gidansa ya yi wani fresh alamar tun a daren jiya angwancin ya amshe shi, shi kaɗai sai murmushi yake lokaci zuwa lokaci yana ɗaga kansa tare da kallon ƙofar bedroom ɗin ta. A hankali ya miƙe tare da ajjiye remote ɗin hannunsa kai tsaye bedroom ɗin ya nufa daga shi sai trousers iya giwwa jikinsa ko riga babu. Kwance ya sameta har yanzu saman gado ta rufe jikinta da duvet barci take a wahale har yanzu. "Oh sweetheart barci har yanzu?" Ya faɗa yana saka hannu tare da zame duvet ɗin, firgigit ta farka tana buɗe idanunta wanda hawaye ya gama cika su. Hucin zazzaɓi na fita a jikinta Salman ya haura gadon baki ɗaya suna haɗa ido ta fashe da kuka sosai, domin gani take kamar yana sane yake mata komai haushin shi duk ya kamata. Cikin rarrashi yana jawota jikinsa baki ɗaya tare da shafa kanta ya ce. "Sorry wife double sorry ni ne ko?" Kai ta ɗaga masa alamar "eh" tana ƙara shigewa jikinsa saboda daɗi ɗumin jikin da take ji. Ya ya yi kissing lips ɗinta yana zame mata hannun duguwar jikinta a ƙoƙarin shi na son sake haɗa jikin nasu waje guda da kyau! Yadda za tafi jin daɗi domin ya lura da yanayin nata.. Gaba ɗaya ta juya tare da rungome shi sosai sbd bayyanar jikinta hannunta a ƙirji shi tana duka tare da ƙananun kuke ta ce. "Uhm Uhm zan faɗawa Abbi da Mami mugunta kake mini" Ya kwaikwayi muryarta yana sake riƙeta a jikin nashi tare da ƙoƙarin lalubar bakin da ya yi maganar ya ce. "Uhm to ai haka shi ne auren sweetheart wife" "Sure?" Ta tambaye shi tana kafe shi da maraitattun idanunta wanda suke ƙara kashewa Salman jiki da zuciya. Ya tarairayota baki ɗaya saman sa sun jima suna kallon juna cikin ƙasa da murya ya ce. "I love You Afra Yusuf Garba Bulama, ban san adadin son da nake miki ba, bani kuma da bakin yi miki godiya a bisa kyautar da kika bani, I am immensely thankful to you for deciding to marry such a stubborn person like me and for going forth numerous times just to assure I was happy. Wallahi Afra ina son ki so mai yawa, son da baki ba zai taɓa iya faɗa ba sai dai gangar jikina tayi aikin ta, The best part of my day is your smile. Being with you is the easiest choice I have ever made, and I'm so lucky I get to make it every day. I love you more every day. I love your honesty, your passion, your resilience, your courage, your partnership, and your smile" Manyan kalaman da suke fita daga cikin bakin Salman sukai wa Afra nauyi a zuciya da sauri ta juya ta rungome Salmanun-faris a jikinta tana shassheƙar kuka wanda babu tantama na farin ciki ne. "I love You Amore Mio, love you to the rest of my life" "Amore Mio?" Salman ya tambaya yana ɗago ta daga jikinsa, taƙi yarda ta kalle shi sbd Kunya a hankali tana ɓoye kanta ta ce. "My love" yana kashe mata ido ya ce "da wanne yare?" ta rufe idanu ta ce "French" ya ɗago ta zuwa jikinsa yana sauka kan bed ɗin tare da nufar parlour da ita ya ce. "Oh, ashe matar tawa ta iya speech shi ne take pretending" yana faɗin hakan yana kissing nata. Abra dake zaune a parlour shigowar ta kenan tai gyaran murya kunya ta kama Salman da ita kanta Afra, Abra tai murmushi hannunta riƙe da Little ta ce. "I'll pretend I didn't see anything". Salman ya shafa kai yana sauke Afra data kasa kallon Abra ya ce "Yaya" ta watsa masa harara ba tare data ƙara kallon shi ba, ba sabon au bane gare ta ganin Salman ba riga shi ya sa ba taji komai ba. Ya juya da sauri zuwa bedroom ɗinsa Afra kuma ta taka a hankali tana cije baki ta zauna tana faɗin. "Daughter mai kama da Maman ta" Abra ta gyara zama domin Adnan ta guduwa tun ɗazo yake gidan ya hanata sakat da naci. Kuma ba tai niyyar zuwa gidan nasu ba kawai bata da zaɓi ne. Abra na zaune bayan ta shirya cikin kayan barci ta ƙara fresh ƙirjinta ya cika sosai, tayi wani irin kyau kamar wacce batai jinya ba, fatar jikinta sai glowing take. A hankali ta zauna tana buɗe datar wayarta sbd littafin da take karantawa na IDAN BA KE ya gama tafiya da tunaninta, ita ba gwanar karatun hausa novels bace tafi ƙarfi a English. Kamar da wasa taga littafin a wattpad ta fara karantawa. "Ikon Allah Surry muguwa ce, wannan ai muguwar shawara ce take bawa Zahrah, ta ya ya mijinta zai amshi budurcin wata a matsayin nata?" Tsaki taci gaba dayi ganin littafin yaje ending na free pages, kuma tana son taji ƙarshen labari ta ya ya Aljani zai auri mutum harda haihuwa a tsakani. Da sauri ta duba number da akai dropping 08119237616 tai adding number a WhatsApp tare da yin payment ganin marubuciyar bata Online yasa ta kashe network ɗin wayar. A hankali idanunta ya sauka akan photon Sp Adnan Aliyu Matawalle ta sauke numfashi ta kasa tantance hukumcin da zuciyarta ke son ɗauka game da Adnan, duk da wulaƙancin da Adnan ya yi mata but till now yana da gurbi a zuciyarta tana jin tausayin shi. Tana tuna makomar Aishatul-humaira. "You're the reason behind anything Adnan, ka rusa zuciyoyinmu" "Uhm kafin ai ɗaran akai kwanɗi, kafin kace uhm ake taɗi" Abra ta juya da sauri ta kalli Mami ta ce "Me nayi Mami?" "Nace wani abu? Waƙa nayi, ZUCIYAR MUTUM, SIRRIN SA." Abra ta kwaɓe fuska ta ce "Kai Mami" "Ba wani kai Mami, kije Abbinki na kira" zuciyar Abra ta buga ta miƙe da sauri kamar zatai kuka abinka da shagwaɓɓiyya ta ce. "Mami me nayi, wayyo Allah" Mami ta saka hannu ta ɗauki Little tana faɗin "Zonan Mamana, wannan rigimar tafi ƙarfin ki muje ki yi barci" tana faɗin hakan tai waje domin ta lura da sauyawar Abra khamal Khamis ɗin. Jiki a sanyaye ta saka hijabi tare da saka Hermes slippers a ƙafarta ta fita zuwa Main parlour. A zaune ta samu Abbi da Mami, Sai Ummi da Abdullah da kuma Salima. Tare da Adnan dake durƙushe ya saka dakakkiyar shadda amy colour wacce ta ƙara haska baƙar fatarsa, sai baza ƙamshin Pur oud yake, Iya kyau ya zuba kyau sai ramar dake maƙale a jikinsa na azabtuwa da soyayyar Abra. Jikinta na rawa ta nemi waje ta zauna ta ce. "Gani Abbi" Ya gyara zama yana ɗan sakin murmushi ya ce. "Abra Daughter ga mijinki ada ya kawo abin da kike buƙata" Ta ɗaga kai da sauri ta kalli Abbi zuciyarta na harbawa tsoro da fargaba suka cika mata zuciya. Ta kasa magana sai sunkuyar da kai da tayi tana wasa da yatsun hannunta. "Allahamdulillah Adnan ya yarda da ƙaddara ya amince da abin da kike buƙata, ya kawo takardar saki i mean divorce papers, kuma zai tafi da yarinyar shi kamar yadda kika ce, dashi da ita bakya buƙatar su, ina miki addu'ar samun miji wanda ya fi shi, shi ma Allah ya bashi wacce ta fiki" Bata san mai ya faru da ita ba, amma tuni hawaye ya gama wanke mata fuska ta shiga gogewa ba tare da kowa ya lura ba. Abbi ya yi murmushi ya ce "ina tunanin ke kike son haka ko?baki da idda san haka na baki sati guda ki fito da miji ko na zaɓa miki wanda naga dama" Mami ta ce "Kayi mata haƙurin wata ina za taga wani saurayin yanzu?" Abbi ya ɗaga hannu ya ce. "Tunda ta ce mijinta ya saketa ai ta shirya fito da wani, ba wani wata da zan bata" ya juya kan Adnan ya ce "Allah ya yi maka Albarka Adnan da umarnin mahaifin ka da kabi, maza ɗauki Mamana Aishatul-humaira ku tafi" Muryar Adnan a sarƙe ya ya miƙe tare da faɗin "Na gode Abbi, Allah ya ƙara girma" ya faɗa idanunsa akan Abra wacce ta kasa motsi. Yana miƙawa Little hannu kamar mai jira ta ɗaga hannunta tana sakin dariya ya yi murmushi kaɗan tare da rungome ta. Da sauri Abra ta miƙe ta ce. "Ka bani ƴata ai ba kai ka haifar mini ita ba" Ummi dai kallon komai take hukuncin Abbi ɗin ya yi mata daɗi domin yanzu tausayin zaryar da Adnan ɗin yake take. Adnan ya kalli Abra wani abu na fisgar shi yana jin kamar ya rungome ta ya yi ta kuka ko zata sassauta masa, zuciyarsa har wani dunƙule masa take. "Ka bani ƴata Malam, ka fita daga cikin rayuwarmu, ka saki uwa me ƴa zatai maka kuma?" Mami zatai magana Abbi ya dakatar da ita, tare da nuna mata ta zuba idanu zuwa inda dramar zata ƙare. Adnan ya sassauta murya mai nuna ki tauyasa mini komai nayi kuskure ne ba son raina bane. "Na rasa abin da kike nufi? Kince na sake ki? Kuma kince na ɗauki ƴata dani da ita bakya buƙatarmu, mene laifina saki ke kika nema fa? Ƴa kuma ta wace" a fusace Abra ta wani lailayo zagi zatai komai ta tuna kuma Ohu! Taja baki tare da yin shiru. Idanunta ya yi jaa sosai ta juya wajen Abbi ta ce "Abbi kace ya bani ƴata? Tunda ya yi abin da zuciyar shi take so nima zan yi abin da nai niyya" "A'a ba ruwana Daughter,bana son rashin gaskiya ke kika bashi zaɓi kuma yabi, Son kada dare ya yi maka" Abra ta fashe da kuka sosai tare da shigewa part ɗin ta, ta shiga kiran number Abba da Hajiya Mama amma duk basu ɗauka ba kamar haɗin baki. Ta shiga rera kuka a yanzu babu abin da zuciyarta ke muradi da son kasancewa da ita irin Aishatul-humaira gashi Adnan ya yi amfani da maganar da tayi wajan rabata da gudan jikinta. MAGANA ZARAR BUNU. Tun daga lokacin Abra ta shiga gaba da kowa ta yini kuka ta kwana kuka, Salman da kansa ya bawa Abbi haƙuri akan a bawa Abra ƴarta. Amma Abbi ya yi masa korar kare. Ummi taja Abra jikinta ta shiga yi mata nasiha akan ta koma gidan mijinta daga nan ta ƙwato ƴarta ko kuma ta koma sbd yarinyar badan halin Adnan ba. Hajiya Mama ta ci-gaba da kula da Little yarinya mai shiga rai. Ɓangaren Salman da Afra soyayya mai zafi ake tun tana jin kunyar shi har ta daina ya shagwaɓata da tarin soyayyar shi da kalar nasa salon mai mantar da duk wanda ƴa mace duniyar da take ciki. Har ta kai idan ba shi sam ba zata iya bacci ba ta sama da rayuwar auren kamar yadda yake buri tattali take samu sosai cikin sati guda daga Salman har Afra suka ƙara wani haske da ƙima Masha Allah. Ummi da Abdullah suka koma Dubai bayan an mata al'ƙawarin zuwan twins ɗin nata, burinta na son tafiya dasu bai cika ba, Dr Bulama har yanzu yana tsare domin an gano manya-manyan laifukan daya aikata a asibitin shi da ɗaukan ma'aikatan wanda sam basu dace ba, uwa uba kuma Ummi ta ƙara sawa akai masa sammacin cinye mata dukiya da ya yi, domin har yanzu wasu kuɗin basu fita ba, tare da cewa ya bata takardar sakin ta. Wannan abu ya zaga ko'ina har kunan gwamna, aka shiga binciken ko wanne asibiti tare da tabbatar da ingancin ma'aikatan. Aka ƙi bada belin Dr Bulama yana tsare labarin ya ɗaga hankalin Abra da Afra duk da laifin na Mahaifinsu ne amma ta wani ɓangaren suna tausaya masa ainun. A week later. Tana durƙushe gaban Abbi tare da sauraran abin da zai faɗa mata, zuciyarta sai bugawa take.. Abbi ya gyara zama ya ce "kamar yadda na baki umarnin sati guda ki fito da miji, na zuba miki ido amma shiru, to a yau bayan sakkowa masallaci na ɗaura miki aure da wanda zuciyata ta amince da shi, ga sadakin" ya faɗa yana miƙa mata damin kuɗi a lokacin nan idanun zuciyarta yarinyarta Aishatul-humaira da tsohuwun mijinta Sp Adnan Aliyu Matawalle kawai suke hango mata, har bata gane mai Abbi yake ce mata. "Daughter?" Ya kira sunanta da ƙarfi ta saurin cewa "Na'am Abbi" ya kalleta da kyau ya ce. "Kiyi mini alfarma a matsayin na wanda na isa a gareki, duk mijin da kika riska a matsayin shi ne mijin ki, ki amince da shi don Allah Abrana, kada ki watsa miki ƙasa a idanu, a wannan karan miji mai nagarta na zaɓa miki wanda ya dace da rayuwar da kike mafarki, Kada kiyi baƙin ciki da duk wanda kika gani don Allah ki yarda dashi,ki bisa sau da ƙafa aljannar ki na ƙarƙashin shi, wanda kuma sai kin yi biyayya zaki same ta, maza tashi kije yana waje yana jiranki zaku shige ba zaki sake kwanar mini a gida ba" Abra ta rushe da kukan da ita kanta bata san na menene ba, a karon farko hukuncin Abbi ya yi mata tsauri, ba damuwarta wanda ya zaɓa mata ba, Kawai Aishatul-humaira take tunani. "Insha Allah Abbi, nayi maka al'ƙawari" "Allah ya yi miki Albarka" ta faɗa jikin Mami tana kuka kamar ranta zai fita. Salima murmushi kawai take wacce take ɗauke da jaririn cikin Abbi a jikinta. Mami taiwa Abra nasiha sosai mai ratsa jiki. A tare suka rakata waje idan akace mijin nata yana nan. Wani magidanci ta gani tsaye fari ba sosai ba, suka haɗa idanu haka kurum ƙunci ya kama zuciyarta a haka ta shiga mota suka ɗauki hanyar da ita kanta bata sani ba. Bata kula shi ba, bai kulata ba har bacci ya ɗauke ta. Sai dare suka shigo garin cikin wata hadaddiyar unguwa mai kyau da tsari, har cikin gidan ya yi parking ya fita, itama ta fito tana mamakin abin da yana mutumin magana ita ko sunan shi bata sani ba. Ya kalleta ya ce "Madam shiga ciki, ina zuwa just 10 minutes" bata ce komai ba ta nufi hanyar shiga gidan tun a parlour ta san Mai gidan Ubangiji ya hure masa arziƙi ba a magana. Ta zaɓi ɗaki guda ɗaya wanda ya haɗu sosai, ta jima zaune kafin tai sallah ta kwanta har barci ya ɗauke ta bata ji motsin Mai gidan ba. Can cikin barci taji an rungome ta tsam a lallausan ƙirji wani ƙamshi na ratsa hancinta, ya sumbaci labbanta masu taushi a hankali ya ce "Wake up My Queen, heartbeat, my rigimammiyar matata" yaja hancinta yana ƙarasa zame rigar jikinta cike da soyayya, yai holding nata very tight. Abin da taji ya sanya Abra ta buɗe idanunta, da sauri ta ƙarasa buɗe idanun mamaki ya kasheta muryarta na rawa ta ce "Adnan.... You?' ya ɗora bakinsa akan nata ya yi kissing sosai yana kashe mata ido ya ce "Yes My Queen waye yace zan iya rabuwa dake?" Ya faɗa yana mirgina ta zuwa ƙasa..... *🔥 IDAN BA KE 17🔥* Marubuciyar Tsintacciya (Published) Kwaila ce Moon Uncle ne Sirrin mu Zain Abeed (Published) Auren fansa Abu maleek Lamrat Jidda Juyayi Raino ne sila Sai na aureta Izzar so Dare da duhu The new emir Ban sani ba ko wannan zai samu daidaito a zuciyoyinku? Tafiyar ƙaddara ce wacce ban saba yinta zallah ba... A wannan karan nace me zai hana muyi labari zallah akan *SOYAYYA* *SOYAYYA TSAKANIN MUTUM DA ALJANI???* Idan kun taɓa ji to labarin zai zo da salo na musamman. *IDAN BA KE* zan kashe dubban rayukan jama'a,na kuma shirya kashe duk mai son raba tsakanin ruhina da naki.... Shi ne alwashin da *ALJANI PRINCE BILAL* ya yi. Labarin *IDAN BA KE* Labari ne dana share shekara a zuciyata ina tsara yadda zan labaranta muku shi, Labarin Babban Malami ɗan kimanin shekaru 34 da haihuwa wato *YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU* da yarinyar da *ALJANI PRINCE BILAL* ya aura. Waye zai ci galaba? An bashi shekara guda domin kare rayuwarta tunda ya dai na yi mata kallon matar shi ta aure da sunan tai masa ƙanƙata kuma *MATSAYIN ƳA* take a wajansa. Kwatsam sai ciki ya bayyana, cikin waye? *YAA SHEIKH KO PRINCE BILAL???* Yayin da ya gama lalacewa da soyayyar ta a zuciyar shi, a lokacin aka raba zuciyoyin su da ƙaddara mafi muni ta yadda sam bazu zatta ba. TAYAYA Suka fito daga *CIKI ƊAYA?* gaba ɗaya wannan a cikin labarin IDAN BA KE. Wanda bai karanta ba ya nema ya karanta. Mun jima da gama free pages GOBE 29/11/22 zamu ɗora da posting ga wanda suka siya iya PAID GRP. Hanzarta biya ta nan 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. Ka tura shaidar biya ta nan 08119237616.... Salon na musamman ne🔥TEAM HALISA DANEJO ROME a shirya masoya ALJANI PRINCE BILAL A shirya. tawagar YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU a shirya🔥🔥🔥 yanzu zamu fara... SARAUTAR MARUBUTA [12/2, 2:49 PM] Abk: A gigice Abra ta ce "Adnan, you again? Wai me ya dawo da kai cikin rayuwata, a kan me zaka kuma dawo mini, ka shirya sake ƙarasa ni har lahira kenan?". "No Angel, please understand me" "Shut up Adnan, you have nothing to tell me, babu abin da zaka gaya mini, in dai halinka ne sai dai na gayawa wani". "Wallahi Abra nayi nadama, dan Allah dan Annabi ki taimaka mini ki yafe mini" "Kaga saurara mini, ɗan cikani malam" Adnan ya sake marairaicewa ya ce "Abra please, dan girman Allah ki saurareni ki yi haƙuri". "Adnan ka rabu dani nace maka, haryanzu ina kan bakana bana sonka bana ƙaunarka, kuma har in koma ga Allah ba zan manta cin zarafin da kayi mini a rayuwar aurenmu ba, dan haka ka ƙyaleni" a zuciye tayi Maganar, wanda hakan ya tilasatawa Adnan cikata, bata saurari komai ba ta diro daga kan gadon, ta nufi hanyar barin ɗakin. Bashi da zaɓi illa ya bi bayan Abra yana faɗin "Dan Allah ki tsaya ki saurareni" tsaki tayi ta koma falo, ta hau kan doguwar kujera ta kwanta. "Shikenan, ba zan kwana a ɗakinki ba, zan kwana a ɗaya bedroom ɗin, ki koma ɗakinki ki kwanta Please". "Malam dan Allah ka rabu dani Adnan, meye haka ne wai, Wallahi ka matasa mini barin gidan zan yi a daren nan, ba sai zuwa wani lokaci ba" "Yi haƙuri na ƙyaleki, amma dan Allah kar ki kwana a kan kujerar nan wuyanki zai yi ciwo" ko kallonsa ba tayi ba ta gyara kwanciyarta, ta rufe idanunta, sai da ya bar falon sannan ta tashi ta koma ɗakinta, ta kulle ƙofar ta saka key. Adnan kuwa kasa bacci yayi gaba ɗaya, juyi kawai yake a kan gadon nan, zuciyarsa na masa wani nauyi, yana tuna irin abubuwan da ya aikatawa Abra, duk da a lokacin yana sonta, da yadda yake fama da ita yanzu, taƙi ta tsaya ta saurare shi, balle ta bashi damar da zai gwada mata irin son da yake mata. "Koma me kika zama laifina ne Angel, ni ne silar sauyawar halayenki, amma ki yafe mini, na shirya baki dukkanin farinciki Abra Khamal Khamis" ya faɗs yana ƙanƙame pillow a ƙirjinsa, yana jin wata irin kewarta na ƙara ratsa zuciyarsa, ya tuna yadda ya dinga zuwar mata kamar ba matarsa ba, ba shi da tabbacin a zaman da suka yi Abra ta san menene ma daɗin auren, saboda buƙtarsa kawai a gabansa. "Am sorry Angel, ki yafe mini mana, Allah yana son bayinsa masu afuwa da yafiya". Abra kam zullumi ta shiga da tunanin kar da wani sabon salon yaudarar Adnan ya kuma zuwar mata, amma yanayinsa ya nuna tabbas yayi nadama, kuma ta san su Abbi ba zasu zaɓa mata abinda zai cutar da ita ba, sai dai duk ƙoƙarin da za tayi wurin manta abinda Adnan ya aikata mata ta kasa, saboda girman tarin laifukansa a gareta, da haka wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita. Duk wata kulawa da ta dace mace ta samu a wurin miji, Salman ya dage yana nunawa Afra yadda ya dace, gaba ɗaya Salman ya mantar da ita tarin damuwa da ƙuncin rayuwa da ya samu kansa a baya, Yanzu haka shirye shirye sun yi nisa, zai koma china dan ɗora karatunsa daga in da ya tsaya, kuma tare da Afra zai koma, domin ita ma ta cigaba da nata karatun a can. Washegari da safe, Adnan ya tashi ya gyara komai, ya dafa tea da kansa ya sayo bredi, already akwai kayan tea dan duk wani kayan Abinci ya saya ya ajiye. A falo ya koma ya zauna, yana jiran Abra ta fito, dan yana tsoron kar yaje tasota ta kuma yi masa wulaƙanci. Sai wurin ƙarfe goma ta fito, ta fito cikin wata doguwar riga mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, rigar tabi jikinta ta kwanta luf. Kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kanta, shi kuwa gogan murmushi ya yi ya ce "Good morning my Angel". "Ina ne kitchen, zan samawa kaina abin da zan ci ina jin yunwa". "Ai na haɗa breakfast, gasu can a kan dining na ajiye komai, ga kazar kuma ki a fridge idan ita ki ke so, sai in warming ɗin ta ki ci". Ba ta bashi amsa ba ta wuce dining, ta zauna ta fara haɗa tea. Dining ɗin ya bi Abra ya zauna, yana satar kallonta da yadda ta ƙara kyau da ƙiba, wata irin kewarta na kuma ratsa shi, wannan dogon gashin da ya zube lokacin da tayi rashin lafiya, duk ya dawo. Yayi mata do tun daga gaban goshinta gashin yake, baƙi ƙirin ya kwanta a bayanta. Tana ankare da yadda ya zuba mata ido kamar bai taɓa ganin mace ba, ta fara karyawa tana kaɗa ƙafarta, kamar ba san da wanzuwar sa a wurin ba. Shima karyawar yake yi, amma hankalinsa gaba ɗaya yana kanta, can ba tare da yayi tsammani ba yaji ta ce "Ammm nace ba, ina ka kai mini 'ya ta ne? Ina buƙatar ka bani abata". " 'yarki tana nan lafiya" "Ba lafiyarta na tambaya ba, ina ka kai mini ita, ina buƙatar a dawo mini da ita". "Tana wurin... Bai ƙarasa ba, suka ji ana kaɗa ƙararrawar falo. Adnan ne ya miƙe ya tafi ya buɗe. Direban gidansu ne, ya kawo Abinci daga gida, wanda Hajiya Mama ta aiko musu da shi. Adnan ya karɓa ya maida ƙofar ya rufe ya dawo dining. "Angel kinga Mama ta aiko da Abinci, bari in ajiye a kitchen maci da rana ko?" Ba ta ko ɗaga kai ta kalleshi ba,balle ya sa ran zata amsa masa. Ya tafi kai fulasan kitchen kar ya dawo ta bar falon. Akwatunan dake ɗakinsa ya kwaso, ya kai ɗakin Abra, Akwatuna duga shida ya zube a gaban Abra, da murnarsa ya ce "Angel, ga kaya na saya muku ke da little, gashi nan naki akwatuna huɗu nata kuma biyu, dama sauran kayan lefenki na wancan gidan ma suna gidanmu, suma zan ɗauko miki su". Abra ta kalli Akwatunan ta ce "Madalla, little ta gode, ni kuma ka bar kayanka, babana na riƙo bai bar ni tsirara ba" "Abra Wannan ai wani abu ne na daban, wannan hakkina ne nayi muku". "Ka yiwa 'yar ka dai, ai ni ban cancanci ka mini ba, ni da nake jinin Bulama, ai bai kamata ka mini abin da zaka kyautata mini ba, tunda auren na fansa ne" Dafe kansa Adnan ya yi ya ce "Abra why, na gaya miki nayi nadama, mai yasa kika canza hali ne?". "Koma menene ai kai ka koya mini ba wani ba, a waccan rayuwar ka sanar mini zaman bauta zan yi, ka ɗau fansa, ban sani ba ko a wannan karon ma fuska biyu kake mini kamar yadda ka saba". Sunkuyar da kai ya yi, a hankali ya matsa kusa da ita, yana kallon yadda doguwar rigarta ta ɗage santala santalan ƙafafuwanta suka bayyana, ya dubeta tare da ɗora hannunsa a kan cinyarta, ya ce "Believe me please, ba zan sake cutar da ke ba Abra" Kallonsa tayi ido cikin ido, yadda suka samu kusanci da juna, har tana iya jin saukar numfashin sa a jikinta, ta kalli faffaɗan ƙirjinsa da take missing, ta cigaba da kallonsa zuwa kan lips ɗinsa, da idanunsa da suka yi jawur cike da nadama, ji tayi wani abu na taso mata, tsohuwar soyayyar Adnan na ƙoƙarin taso mata. Dakewa tayi a lokacin da wani sashi na zuciyarta ya gargaɗeta 'Me kike shirin yi ne Abra, kamar baki da zuciya?'. Haɗe rai tayi ta ce "Ka zo ne dan kayi abin da ka saba, ka biya buƙatar ka sannan ka koreni a wulaƙance, kar warin abin da na fitar ya hautsina maka ciki? Ko kuma fyaɗen kake ƙoƙarin sake yi mini, kamar yadda kayi mini a ranata ta farko da kasancewa da ɗa namiji?" Wata irin ajiyar zuciya Adnan ya sauke, ya dubi Abra yana tuna abubuwan da suka shuɗe, da wasu ya manta ma da ya aikata hakan. "Ba zan gaza da cigaba da baki haƙuri ba Abra, na san ni mai laifi ne a wurinki, dan Allah ina mai kuma sake baki haƙuri". "Can You excuse me please?" Abra ta faɗa in a serious tone, tana sake nuna masa bata buƙatarsa a in da take. Jiki babu ƙwari haka Adnan ya tashi ya bar mata ɗakin. Kwanaki biyu da tarewar Abra, Hajiya Mama da Abba suka zo gidan da daddare, tare da little kasancewar dama tana wurin Hajiya Mama. Abra tayi murna da zuwansu, tayi musu kyakywar karɓa cike da farinciki. Gefe guda ga murnar ganin 'yarta da tayi. Abba ya yi musu nasiha me shiga jiki, da mahimmancin yafiya da haƙuri a zamantakewar aure, da kuma sake kashedi da jan kunne ga Adnan, a kan mahimmanci amana da riƙon iyali da adalci. Abra nasihar Abba ta ratsata, amma ba ta iya ji a ranta ta yafewa Adnan muzgunawar da yayi mata ba. Da zasu tafi ta so Mama ta bar mata little, amma Mama ta ce ba yanzu ba, sai an kwan biyu tukuna. Labari ya ishe sauran 'yan uwan Bulama, a kan iftila'in da ya afka masa, amma babu mutum guda da ya iya jajanta halin da yake ciki, ciki kuwa har da 'yan uwan mahaifinsa, saboda yadda ya watsar da su, tun bayan aurensa da Saudat, da yadda ya daina zuwa inda suke, shi kuma babu wanda ya san in da yake zaune a cikinsu, dan haka babu wanda yabi ta kan a tallafa masa saboda yanayin da yake ciki. Hajiya Saudat kuwa Nijar ta gudi can wurin wata ƙawarta ita da Meenal, sai dai tun bayan aikin da aka yiwa Meenal, aka cire mata mahaifa, ba ta samu lafiya ba, take ta rashin lafiya, duk ta ƙare ta rame, saboda kullum cikin ciwon ciki da zubar jini take. 'yan sanda kuma tuni suka baza komarsu dan ganin an daƙumo Hajiya Saudat bisa ga laifin da ta aikata. Adnan yana ji yana gani, yana zaune gida ɗaya da Abra, amma tafi ƙarfinsa, saboda a wannan karon zama ne yake son su yi shi na soyayya wanda zai mantar da ita waccan rayuwar da suka yi, sam baya son takura mata gaba ɗaya. Abra ko aikin gida sai ta ga dama take yi, Adnan ne yake komai, sai dai tana yin girki ta ajiye masa, saboda ko a lokacin da suka yi wancan zaman bai barta da yunwa ba. Shiga sai wadda ta ga dama take yi, wani lokacin haka zai kalleta ya haƙura ya bar mata falon ya koma sashinsa. Maganar arziƙi bata haɗasu saboda yana gudun samun matsala. Gefe guda kuwa Abra damuwa ta fara yi mata yawa a kan halin da mahaifinsu ke ciki, gaba ɗaya media ta ɗauka kasancewar sa shahararren likita ne, har ga Allah duk da tarin laifukan da Mahaifin nasu ya aikata, tana jinsa a ranta, kuma ta fara tunanin tunda tana garin Kaduna, akwai buƙatar ta je ta ganshi, dan tuni an fara gabatar da shari'arsa, sai dai ana nema ayi defeating ɗin lawyoyinsa, saboda ƙwararrun lawyoyi ne suke tsagin gwamnati, kuma a yanzu babu kuɗin da Bulaman zai iya ɗaukar wanda zasu tsaya masa. Kwanci tashi asarar rai, a daren yau Abra taci karo da message ɗin Salman, yake sanar mata da cewa ta tambayi izinin Adnan, zasu je Dubai tare da ita suje wurin Ummi, ita ta dawo gida, su kuma su wuce China shi a Afra. Farincikin da Abra ta shiga ba zai misalitu ba, dan haƙiƙa ɗan zaman da suka yi da mahaifiyarsu bai ishe su ba, duk da ba wani sabo da shaƙuwa a tsakanin su. Shirinta ta fara yi, ba tare da ta sanar da Adnan batun tafiyarsu ba, sai dai ta lura kamar ba shi da lafiya, rashin lafiyarsa ya ɗan tayar masa, amma bai gayamata ba, ita ma kuma ba ta nemi ta sani ba, ta shirya kayanta tsaf tana jiran zuwan su Faris. Sam Adnan bai san da zuwan da su Salman ba, dan bata gaya masa ba sai ganinsu kawai ya yi a gidan, Abra ta rasa in da zata saka kanta dan murna, Afra ta ƙara ƙiba Salman ma haka, kana kallonsu ka san farinciki da kwanciyar hankali sun sami kyakykyawan matsuguni a tare da su. Adnan ya dake ya daure, ya ɗan sake suka gaisa da Salman. Gefe guda kuma yai ta tsokanar Afra 'Su 'yar fara an auri fari, ni kuma Allah ya dawo mini da matata wurin ɗan baƙinta" Afra ta tura baki tana murmushi. Ɗaki Abra ta janye 'yar uwatta, suka ƙule suna hira, Afra ta ce "Sister, wai haryanzu jikin baban little bai warke bane, naga sai kuma rama yake yi?". "Oho masa" Abra ta faɗa cikin ko in kula. "Ba dai kina nufin haryanzu ba kwa jituwa ba?". "Kinga mu bar wannan maganar, me zamu dafa ne?". "A'a magama ce me mahimmanci da Yakamata mu tattauna ta" Abra ta miƙe ta ce "Sai kuma kiyi ai" ta fice ta bar ɗakin, ko da ta dawo falo da Salman da Adnan duk basa nan, dan haka ta mayar da hankali wurin ƙoƙarin ɗora girki. Hankalinta ya yi nisa a kan aikin da take yi, taji ƙamshin turaren sa ya mamaye ilahirin kafofin hancita. A hankali ya tako har in da take ya tsaya yana ƙare mata kallo. "Chef Yaya, girki in bana ki ba ƙanzo". Abra tayi dariya ta ce "Allah yasa matarka ta jika" dariya yayi yace "Sarkin daru ba" ya cigaba da tsurawa Abra idanunsa, ta ɗago ta kalleshi ta ce "lafiya wannan kallon fa?". "Angel, lokuta da dama zukatanmu suka mato a so da ƙaunar wani abu, har mu dinga jin tamkar rasa wannan abu na nufin tawaya ko samun naƙasu ga rayuwar mu, sai dai kash, tun gabanin mu zo duniya Alƙalamin ƙaddara ya kammala zana mana ƙaddarorinmu. Sai dai muyi ta lalube a duhu da sanyawa zukatanmu burika daban daban, wasu su cika wasu kuma saɓanin haka, wanda wannan hikima ce ta ubangiji da ba a masa dole. Tabbas soyayya ba ƙarya bace ba, na rayu da soyayyar ki a lokacin da nake zaton, tsananin ƙauna ce ta 'yan uwantaka, sai bayan bayyanar wani sirri da ya zama makamin ruguza wancan tunani da nake a baya, ya sauya akalar wannan soyayyar da nake miki. Abra ba kiyi Mamaki ba, yadda abubuwa suka dinga faruwa cikin hukuncin ubangiji ba, sama ta ka Adnan ya kutso ratuwarki, cikin ƙiftawa da bisimillah soyayya ta sanya kika rusa burin Abbi a kanki yayi miki aure. Sai dai duk da Auren da ki kai da zimmar Soyayya yayi silar rabuwar duniyarki zuwa abu biyu, idan ki ka tsaya da tunaniki kika duba hukuncin ubangiji da yadda abubuwa suka dinga wakana tamkar shirin film, sai ki gano ashe Adnan shi ne ƙaddarar ki. Duk da ya cuzguna miki a baya, sai ki duba a silarsa kuma kin haɗu da farincikin da kuɗi ba zai saya miki ba, ga iyayenki kin gano, ga kuma a silarsa 'yar uwakki ta bayyana, a silarsa Allah ya yi miki kyautar ɗan mutum sukutum guda. Yayata, ke mace ce me yafiya, wadda muka rayu ta gini a kan raunin zuciya, haƙuri da kuma kawaici, Adnan be gaya mini meke tsakaninku ba, amma yanayinsa ya nuna yana cikin damuwa, kuma kin san bashi da cikakkiyar lafiya, kika iya yafewa Mami balle uban 'yar ki? Kiyi tunanin my Angel" Tuni hawaye ya wanke fuskar Abra, saboda tasirin kalaman Salman a a zuciyarta, cikin kuka ta ce "Faris, Adnan ya cutar da ni san..... "Shhh, a sanadiyar yafiyar da zaki masa, sai Allah ya yi miki abin da baki zata ba, ko kin manta shine masoyinki na farko? Am sorry to say Abra, mahaifinki ya cutar da zuciyar Adnan, duk da hakan ba hujja bane na ya huce a kanki, amma ke a kan kanki, ya faru a Asibitinsa, cikin duhun dare ba tare da ya san ke 'yar sa ba ce, idan aka ce uwa Yaya an gama magana, mahaifinki ya cancanci ya nemi yafiyar waɗanda ya cutar, ba wannan maganar muke ba, duk da shima ina son ki yafewa mahaifinki daga ke har Afra, dan kan mu wuce Dubai nake son, muje mu ganshi, dan Allah komai ya wuce yayata, musa a ranmu dukkaninmu Allah yayi mana zaɓi ne daidai da ƙaddarorinmu, da kuma abin da ya dace da mu" Tuni hawaye suka wanke fuskar Abra, Salman ya dinga share mata ya cigaba da rarrashinta, har ta ɗan samu nutsuwa ta cigaba da aikinta, har yana tayata. Bayan ta kammala girkin, har suka yi bidirn cin abincin su, Adnan na ɗaki bai fito ba, bata son Salman ya kuma magana, dan haka ta bi Adnan ɗaki, ta tarar da shi a kwance a kan gado, yayi shiri ya zubawa wuri ɗaya ido. Shigowarta ce ta sanya ya mayar da idonsa kanta, ta ƙaraso ta tsaya tana kallonsa "Ba zaka ci Abinci bane?". "Angel bana jin yunwa sam, kewarki ce ke damuna" taɓe baki tayi ta ce "Dama zan gaya maka ne, gobe in Allah ya kaimu ƙarfe huɗu, Dubai zamu tafi, zan bi su Salman, zamuje wurin Ummi muyi mata sati ɗaya sannan mu dawo" Cikin mamaki Adnan ya kalli Abra "Amma baki gaya mini ba sai yanzu?". "Amma dai na gaya maka ko? Ba ɗaukar jaka nayi na tafi baka sani ba" tai maganar tana harrasa up and down. Adnan ya jinjina kai ya ce "Haka ne, Allah Ya kiyaye hanya" ta amsa da Ameen ta fice ta bar masa ɗakin, yana cigaba da mamakin yadda gaba ɗaya Abra ta sauya, tamkar an canzo masa ita da wata. A gidan su Salman suka kwana, sai dai basu fuskanci cewar ba ɗaki ɗaya su Abra suke ba. Washegari tun azahar Abra ta gama kintsawa, saboda zasu je prison wurin mahaifinsu. A ɗaki ta tarar da Adnan yana kwance, da alama jikinsa ya tashi. "Zamu tafi, kuma na ga tun safe baka sake fitowa ba" "Angel bana jin daɗin jikina ne, dan Allah kar ki tafi ki barni". Idanunta ne suka cika da hawaye ta ce "Au kar in tafi in barka kace? Ai gara ni wurin iyayena zani, ka manta ni ranar da ka sa ƙafa ka tafi ka barni, kana ƙyanƙyamin jikina, saboda ƙazantar da ta fito a jikina?" Shiru Adnan yayi ya rintse idanuwa a hankali ya furta "Is ok Angel, Allah ya kiyaye hanya, ki gaishe mini da Ummina, ba zan iya driving ba da na raka ku, bari driver ya kai ku" Ya dafe ƙirjinsa a hankali ya miƙe, wani abu ne mai kama da tausayi ya fara fizgarta, amma ta maze. Adnan ya fito falo, yana murmushi ya kalli Salman ya ce "Malam shine kawai zaka ɗauke mini mata, bayan kai kana tare da matarka" Salman yayi murmushi ya ce "Ko zaka bimu ne? Kar mu gudu da ita?" Adnan ya ce "Ai ina ganin likita ne, muje driver ya kai ku" Suka ƙarasa har gaban mota, Abra na ƙoƙarin shiga motar, Adnan ya riƙo hannunta ta baya, ya saka bakinsa a daidai kunnenta ya ce "My Angel, ina sonki da yawa, Allah ya tsare mini ke ya dawo da ku lafiya, dan Allah Abrana ki yafe mini,. Ban sani ba ko kan ku dawo rai yayi halinsa, bana son in je wurin Ubangiji da hakkinki, dan Allah ki yafe mini" ya ƙarasa maganar hawayensa na zirarowa yana gangarowa daga wuyanta zuwa cikin rigarta. Da haka ya cikata, ya juya ya koma cikin gida. Jikin Abra yayi sanyi ƙalau, amma ba ta ji zata fasa tafiyarta ba. Prison suka fara zuwa, aka fito musu da Bulama, gaba ɗaya ya fita hayyacinsa, duk wannan gayun babu, jar fatar nan tasa duk tayi baƙi. Abra na ganin halin da yake ciki ta fashe da kuka, ta rungume Bulama tana ta shesheƙar kuka, Bulama ma rungumeta ya yi shima yana kuka har da majina. " 'ya ta dan Allah ki yafe mini, ke da 'yar uwakki dan Allah ku yafe mini" Afra ma dai kuka take yi, sai dai ta kasa zuwa in da yake. Abra ta shiga share masa hawayen fuskarsa ta ce "Daddy ya ake ciki da zaman kotun naka? Insha Allah zan fara halarta kuma Insha Allah zan shawo kan Ummi ta yafe maka" Kalmar Daddy da ta kira shi da shi, yafi komai faranta masa rai. "Daughter, dan Allah ki yiwa mijinki godiya, duk da munin laifin da na aikata masa, tun ranar da aka fara zaman kotu, kullum shikaɗai ne wani nawa da yake zuwa, sai abokaina, kuma ya ɗaukar mini ƙwararrun lauyoyi har guda uku da zasu kareni, kuma koda Yaushe cikin yi mini aike yake na kayan Abinci, mahaifinsa ma ya zo, iyayenki ma Major da mai ɗakinsa sun zo. dan Allah ki nema mini gafarar mijinki akan abin da na aikata masa" Shiru Abra tayi, sam Adnan bai taɓa gaya mata wannan maganar ba. Suna tsaka da magana ne, gandiroba ya ce lokaci ya yi, zasu mayar da Bulama, suka dinga kuka ƙarshe sai Salman ne yayi ta aikin rarrashi da basu haƙuri. Har suka isa Dubai, Abra na Mamakin a yadda Adnan ya tsani mahaifinta, amma ya iya taimaka masa, take taji kaso mafi rinjaye na haushinsa da take ji ya ragu a zuciyarta, dama can ƙasan zuciyarta tana jin tausayinsa dannewa kawai take yi. Ummi ta rasa in da zata saka kanta dan daɗi, ganin yaranta a tare da ita, ta dinga farinciki tana nan nan da su, shi kansa Salman tana matuƙar son yaron nan, saboda kulawarsa ga yaran nata, kamar yadda yayi mata alƙawari ya cika, ya kawo mata yaranta wurinta. Sai dai tayi ta mita, saboda rashin kawo mata Little. "Abra ina wannan mijin naki masifaffe, naji babanki wai shi suka kuma aurawa, koda yake mahaifinki ne ya janyo miki koma menene" "Ummi ni mijina ba masifaffe bane, wato ba kya son mijina sai wannan ɗan naki ko?" Tayi maganar tana tura baki. Ummi ta ce "Abra raina ya ɓaci da jin abinda ya yi miki ne, ban san me su Major suka gani suka kuma bashi ke ba, ni so nayi su bani ke in aura miki balarabe" Abra ta ce "Ni bana son farin namiji, Caramel nake so kamar baban little" Hira me cike da soyayya da ƙaunar juna ce ta shiga tsakaninsu, a haka Abra ta shigo da batun Ummi ta yafe wa Daddyn su, nan da nan Rumaisa ta haɗe rai ta ce "Ko dukiyarta zata ƙare, sai ta tabbatar an kai shi prison, kuma sai an nemo Matarsa an musu Shari'a a kan abin da ta aikata mata" Babarsu Abra na da sanyin hali, amma a wannan karon ta ɗau zafi da yawa, duk irin kukan da Abra tayi mata, fafur ta ƙi amincewa da yafewa Bulama. Duk da tattali da kulawar da Ummi ke basu, hankalin Abra na Nigeria wurin mijinta, saboda yadda yake haki lokacin da zasu rabu, ta san yana jin jiki matuƙa, ga kuma wannan abun alkhairi da ya yiwa mahaifinsu. Salman ya cigaba da yiwa Abra nasiha, a kan ta yafewa Adnan, mussaman duba da irin abin alkhairi da ya yiwa mahaifinta. Ita kanta ta san Adnan ya yi laushi na gaske. Sai da Abra ta kwan goma a daddafe, gashi ta nemi lambar Adnan da ya dinga kiranta kwanakin baya, amma ba ta gano lambar a wayarta ba balle ta kira shi a waya, ta ji ya yake?. Ranar kwana na goma sha ɗaya, suka rako Abra airport, Abra da Afra sun sha kukan rabuwa, haka Abra ta hawo jirgi zuwa Nigeria. Ƙarfe biyar na yamma ta sauka. Shatar taxi tayi zuwa gida, saboda bata da lambar Adnan balle ta ce ya turo a ɗauketa. Ba laifi gidan bai yi datti ba, amma Abra ta zage ta sake gyara ko ina. Ba ta ji motsin Adnan ba, dan haka tayi zaton ko baya nan. Haka nan taji tana matuƙar son ganinsa. Har zuwa magariba bayan ta kammala girki, ba tsammani ta ga Adnan ya fito daga ɗakinsa, ba tsammani kawai yaga Abra, duk wannan motsin da take a gidan bai ji ba, ita kuwa tsorata tayi, ramar da Adnan ya yi ya wuce misali. "Ya a kai kika dawo baki kirani a waya ba na zo na ɗauko ki? Ai da ko girki na miki" yayi Maganar yana kallonta. Kallon kansa ya yi ya kalleta ya ce "Ya naga kina kallona? Wani laifin na kuma yi?" Tausayinsa ne ya cika zuciyarta, ta girgiza kai ta ce "Bakomai, masallaci zaka ne?". "Eh, ya hanya ya su Ummi?". "Suna lafiya tana gaisheka" "Bari inje in salla in dawo" "A dawo lafiya" "Allah ya sa my Angel". Ɗakinsa ta nufa, ta gyara masa, ta kukkuna turaren wuta. Adnan da uban ledoji ya dawo gidan, ya sissiyo kayan ciye-ciye duk dan ya farantawa Abra rai. Ta karɓi kayan ta ajiye, ta ce "muje dininga ka ci Abinci, dan banga alamar kana cin abinci ba da bana nan" Wani irin farinciki ya kama Adnan ganin Abra na kula shi. Ba musu ya wuce dining, ta zuba masa Abinci, yana ci yana mata hira cike da farinciki. "Wannan jikin naka, ko dai ƙasar waje zaka a duba ka, ka rame da yawa kalli yadda ka ke numfashi fa" "Kar ki damu, ni dai ko ban warke ba, fatana ki yafe mini kan in mutu Abra" ya yi maganar idonsa fal hawaye. Bata amsa ba masa ba, ta janyo plate ɗin gabansa, ta ɗebo Abinci ta kai bakinsa "Maza ka ƙara Abincin nan, i want my well biuld body Adnan back, maza ka cinye" tana bashi Abincin tana zubar da hawaye. Fuskar Adnan ɗauke da hawayen shima ya ce "Please Abra, yafiyarki ita ce babban abin da nake fata kan bar duniya, ko na mutu na san Little ba zata yi maraici ba, na barta a hannun nagartacciyar uwa, dan Allah talk My Angel" Ajiye plate ɗin ta yi, ta tafi ɗakinta. Bayanta Adnan ya bi zuwa ɗakinta, amma ta rufe ƙofar ɗakin. Haka Adnan ya haƙura ya sake alwala zuwa Masallaci, dan gabatar da sallar isha'i. Bayan ya dawo yayi wanka ya kwanta a ɗakinsa, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa fiye da kima. Ya lumshe idanunsa hawaye na zuba ya ce "I deserve it, kome kika mini, ba zai kai wanda nayi miki ba". Ƙofar ɗakin yaga an turo, Abra ce hannunta ɗauke da robar ruwa da kofi, ta kalli Adnan ta ce "Mun yi waya da Mama, ta ce mini kana da magunguna da kake sha, suna ina?" Ya nuna mata side bed, ta janyo ta ɗauko magungunan, ta dinga miƙa masa ɗaya bayan ɗaya yana sha, idonsa a kanta ko ƙiftawa ba ya yi. Miƙa hannu tayi, ta ɗan ja gemunsa kawai ta yi murmushi. "Please Abra forgive me, a Wannan karon kalamaina daga cikin zuciyata suke, ina sonki abra ko a wancan lokacin ma, ina cikin ɗacin ran abin da mahaifinki yayi mini ne, amma nayi nadama Please my wife forgive me, ina ji a jikina kamar ba zan rayu ba, saboda yanayin ciwona, kar in mutu.... Abra ta toshewa Adnan baki, tare da kwantar da kansa a kafaɗarta, tana shafa bayansa. "Angel kin yafe mini?". "Mu bar waccan maganar, lafiyarka nake fata, bana son Little tayi maraici, ka daina kuka dan Allah" "Hawayena ba zasu tsaya ba, muddin ban ji daga gareki ba My wife" "Kaga kwanta, ka samu numfashinka ya daidaita". Ba musu Adnan ya kwanta, tare da ita a jikinsa. "Baby, kayi mini wani abu da ya cancanci in maka godiya, abin alkhairi da ka yiwa mahaifina duk da laifinsa a wurinka". "Angel ban yiwa mahaifinki haka dan ya zama makamin da zan amfani da shi ki yafe mini ba, sai dai daga ni har shi masu laifi ne, kuma yanzu ya zama uba gareni tun da na haɗa zuriya da shi, ni dai yafiyarki nake nema". "Ka daina kukan nan Please, baka da lafiya yi bacci kaji Baby" Murmushi Adnan ya yi ya ce "Ni ba wannan nake so ba, ki amsa mini". "Zan tashi in tafi idan ba zaka yi baccin ba". "Ba bacci zan yi ba, let me show you how much I missed you" Cikin shagwaɓa ta ce "Mhmm Daddyn Little, baka da lafiya fa, dan Allah ka bari" Adnan bai saurareta ba, sai da ya ƙara tabattar mata da yadda ya yi kewarta, da kuma irin tsananin ƙaunar da yake mata. "Allah ya sa mun samu rabo, wannan karon ki haifo mana twins" "Ba Ameen ba" Abra ta faɗa tana tureshi daga jikinta. Dariya yayi yana sake ƙanƙameta a jikinsa yana sake neman yafiyarta. "Hmm Daddyn Little kenan, daga abin da ba zan manta ba, irin ina amarya ka kawo mini karuwa gida" "Wallahi Wallahi Abra ba halina bane, nayi ne kawai dan in ɓata miki rai, hayota nayi. Amma kiyi haƙuri please" A nan ya sake bata labarin yadda aka yi mahaifiyarsa ta rasa ranta a sakamakon abin da Bulama ya yi. "Amma ai ka yafewa Daddyna ko?". "Wallahi na yafe masa Abra". "Hmm mutum ya ci sa'a he is my first love, kuma ina ɗan son shi kaɗan, duk da laifukan mutum akwai kuma alkhairansa ds ba zan manta ba" "Kin yafe mini Abra?" "Na yafe maka Baby, Allah ya ƙara mana zaman lafiya da ƙaunar juna" LITTAFINMU NA KUƊI NE, A BAMU HAKKINMU KAN A KARANTA ₦300 NE KACAL. 08081012143[12/4, 12:01 PM] Abk: Farinciki mara misaltuwa ya ji ya mamaye dukkan zuciyarsa, ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi tare da ƙara ƙanƙame ta a ƙirjinsa, yana jin tamkar an sauke masa wani abu mai nauyi da ya danne zuciyarsa tsawon lokaci. Lumshe idonsa ya yi yana jin sa tamkar wanda ya shekara a sahara da dakon ƙishirwa ya samu ruwan sanyi yake sha. "Thank you, thank you so much matata, Allah ya yi miki albarka." Ya faɗa cikin hawaye. Hannu ta kai ta fara share masa hawayen tare da faɗin. "Ba na son ganin hawaye ko ɗigo yana zuba daga cikin idanunka, ka daina ka ji, kai fa jarumi ne, wanda ko kallon ka aka yi sai zuciya ta girgiza." Murmushi ya yi cikin jin daɗin kalamanta ya ce. "Ni rago ne mai rauni akan soyayyar ki Angel, walwalata, farincikina da kuzarina duk sai zuciyata ta samu nutsuwa daga gare ki za su ɗore." Hannayenta ta saka ta saƙalo wuyasansa da su ta ce. "Zuciyarka ta samu nutsuwa, in dai Abra Khamal Khamis ce ta zama tata har abada." Ƙara ƙanƙameta ya yi tamkar zai mayar da ita ciki ya shiga jera mata kalaman soyayya masu tsayawa a zuciya, tare da zagaye dukkan jikinta da hannunsa, cikin wani irin salo mai cike da shauƙi. Daɗin yanayin ya sa ba ta san lokacin da ta ɗora hannunta a kan lallusar sumar kansa ta shiga yamutsa masa ba tana sakin ajiyar zuciya, hakan ya ƙara jefa Adnan a cikin buƙatuwa da ita. A hankali cikin nutsuwa ya ɗora soft lips ɗinsa a kan nata, numfashi ta ja ta fesar tana ƙara shigewa jikinsa, wani baƙon yanayi na ziyartar ta. Salon Adnan na yau ba ƙaramin birkita ta ya yi ba, ba ta son lokacin da ta fara mayar masa da martani ba. Bayan komai ya lafa tana kwance a jikinsa tana mayar da numfashi, shi kuma yana shafa gashin kanta da ya birkice. Cikin murya mai kama da raɗa ya ce. "I love You! I love You! I love You with all my heart!" Murya ƙasa-ƙasa ta ce. "Love You too my Baby." Kissing forehead ɗinta ya yi cikin tsananin nishaɗi, yana jin tamkar bai taɓa kasancewa a cikin damuwa ba a rayuwarsa. Tashi ya yi ya ɗauke ta cak ya kai ta toilet, tana rurrufe ido da turo baki suka yi wanka a tare, shi kuwa ban da murmushi da tsokanar ta babu abin da yake. Bayan sun fito suna tsaye a gaban mirror ya ware towel ɗin jikinsa ya saka ta a ciki. Waro ido ta yi cikin jin kunya ta ce. "Daddyn Little...." "Shiiiii." Ya katse ta tare da ɗora kansa a kan kafaɗarta, yana jifan ta da wani irin kallo na zallar ƙauna wanda yake kashe mata jiki ya ce. "From today da towel ɗaya za muna using." Ya ƙarashe maganar tare da kunce na jikinta ya yi ƙasa da shi. Saurin juyawa ta yi ta rungume shi, kamar za ta yi kuka ta ce. "Ni dai a'a, kowa ya yi amfani da nasa." "Da ni da ke ai duk ɗaya, don haka komai da ɗaya za muna using." Ya ƙarashe maganar tare da ɗago kanta ya yi kissing lips ɗinta." Lumshe ido ta yi tare da maƙe kafaɗa. Bai ce komai ba ya ɗauko lotion ya fara shafa mata. Turo baki ta yi lokacin da ya juyar da ita yana shafa mata a ƙirjinta, ƙura masa ido ta yi ta cikin mirror ganin yadda ramar shi ta ƙara fitowa. Cike da tausayawa da ƙaunar shi ta shafa kuncinsa ta ce. "Ka rame sosai Baby, Please ka cire duk wata damuwa dake cikin ranka." Hannunta ya kama ya ce. "Babu wata sauran damuwa Angel tunda kin dawo cikin rayuwata, fatana kawai Ubangiji ya ba ni ikon kyautata miki." Cikin sanyin murya ta ce. "Amin Babyna, I love You." Yana goga sajensa a gefen fuskarta ya ce. "Love You too ƴar Aljannah." Washegari da safe Abra ce tsaye a kitchen tana soya egg, sanye take cikin wata red ɗin riga mai ƙaramin hannu wadda ta tsaya mata iya gwiwarta, ta faka gashin kanta wanda ya sauka har gadon bayanta da red ribbon. Ta yi kyau sosai duk da ba make up ta yi, daddaɗan ƙamshi na tashi a jikinta. Sauri take ta kammala haɗa breakfast ɗin kafin Adnan ya tashi, don da ƙyar da dabara ta raba jikinta da nasa ta fito. Jin kaman ana kallon ta ya sa ta juyawa, yana tsaye ya harɗe hannunsa a ƙirjinsa yana kallon ta, babu riga a jikinsa sai ƙaramin wando da bai gama rufe masa cinya ba. Murmushi ya sakar mata lokacin da suka haɗa ido tare da ƙarasowa ya rungume ta, ta baya. "Morning my Queen." Ya faɗa a saitin kunnenta da murya ƙasa-ƙasa. Lumshe ta yi ta buɗe ta ce. "Morning Hero, how was your body?" "Alhamdulillah." Tana zare hannunsa dake kan cikinta ta ce. "Bari na yi sauri na gama ka samu ka ci abinci ka sha magani." Mayar da hannun ya yi tare da cusa kansa a wuyanta yana shaƙar ƙamshin jikinta ya ce. "Na warke fa Angel, ni na manta ma ba ni da lafiya, saboda ba na jin ciwon komai a jikina tunda na same ki." "Sure?" Gyaɗa mata kai ya yi tare da cusa hannunsa a cikin rigarta. Cikin shagwaɓa ta ce. "Girki fa nake Baby." Murya ƙasa-ƙasa ya ce. "Ki bar shi ki huta Wifey, na san Mama za ta aiko mana." Ciro hannun nasa ta yi ta ce. "Mu ya kamata muna kai mata abinci ba ita za ta dinga girkawa tana kawo mana, ka bar ni na yi Please ita kuma ta huta." Maraicewa ya yi ya ce. "No." Bai jira abin da za ta ce ba ya juyo da ita ya haɗe bakinsu guri ɗaya. Da ƙyar ta ƙwaci kanta ta cigaba da aikinta, tare da suka ƙarasa aikin yana manne a jikinta, duk a cewar shi taya ta yake. Bayan sun gama suna zaune a parlour tana manne a jikinsa ta ce. "Ka cinye abincin nan duka Please, ba ka cin abinci ne shi ya sa duk ramar taka ta yi yawa." Girgiza kai ya yi ya ce. "I can't dear." Ɓata fuska ta yi tare da barin jikinsa, janyo ta ya yi ya ce. "I'm sorry, amma ba abinci ne zai saka na koma yadda nake ba." "To mene?" Ta faɗa tana sakin fuskarta. Raɗa mata ya yi a cikin kunnanta, saurin waro ido ta yi tare da rufe fuskarta tana murmushi. Shi ma murmushin yake, ɗaukar ta ya yi ya ɗora ta a kan cinyarsa ya fara ba ta abincin a baki, duk spoon ɗaya sai ya yi kissing lips ɗinta. Ba su tashi daga gurin ba sai kusan azhar, saboda lalacewar da suka yi suna zuba soyayya. Bayan sun yi wanka tare Adnan ya fita Masallaci. Bai dawo ba sai bayan la'asar. Tana zaune a parlour suna chat da Afra ya shigo, ta ci kwalliya cikin English wears. Ɗago kanta ta yi a hankali tare da amsa masa sallamar da ya yi. Ware mata hannayensa ya yi cikin kewar ta, cikin nutsuwar ta ta miƙe ta ƙarasa ta faɗa jikinsa. A tare suka saki ajiyar zuciya lokacin da zagaye bayanta da hannunsa. "Welcome Baby." "Yawwa love ya gidan?" Ya yi maganar yana shafa gashin kanta. Shagwaɓe fuska ta yi ta ce. "Ina ka je ka daɗe ka bar ni, ni kaɗai? Kuma ka san ba ka da lafiya." "I'm sorry, wani guri na je." "I thought gidan Mama ka je." Yana shafa lips ɗinta dake zuba ƙyallin white lipstick ya ce. "Yanzu dai za mu je mu gaishe ta idan na yi wanka." Cikin murna ta ce. "To mu je ka yi wankan mu tafi kar mu ɓata time." "Ɓata time ya zama dole tunda kika yi wannan kwalliyar." Langwaɓe kai ta yi don ta gane me yake nufi ta ce. "Please Bab...." "Please Angel." Ya katse ta cikin kwaikwayar muryarta tare da jan karan hancinta. Kanta ta cusa a cikin ƙirjinsa cikin sigar shagwaɓa. Cak ya ɗaga ta don hakan da take ƙara birkita shi yake, dama ƙamshinta gabaɗaya ya gama ruɗa shi. Sai kusan Magriba suka fito tana zuba masa rigimar ya sa ta sake wanka da yamman nan, shi kuma yana ta lallaɓa ta. Rantsatstsiyar sabuwar motar da ta gani ya sa ta tsayawa tana yaba ta. Murmushi ya yi ya kamo hannunta ya saka mata key a ciki tare da faɗin. "It's yours my lady." Waro ido ta yi cikin mamaki da farincikin da suka yi mata rufdugu a lokaci ɗaya ta ce. "Sure?" Gyaɗa mata kai ya yi. Rungume shi ta yi ta ce. "Alhamdulillah, thank you, thank you Baby, Allah ya saka da Alkhairi ya ƙara buɗi mai albarka da amfani." Cikin jin daɗin addu'ar ya ce. "Amin Angel, You deserve more than this a waje na, and babu godiya a tsakanin mu, duk abin da na mallaka naki ne." A bazata ya ji ta haɗe bakinsu guri ɗaya tana ba shi wani zazzafan kiss, bayan ta zare bakinta daga nasa ta ce. "Tukuici na farko kenan, sauran sai mun haɗu later." "Mu koma yanzu ma a ba ni." "Um'um." Ta faɗa cikin dariya tare da yin gaba gurin motar cikin farinciki. A cikinta suka je gidan Hajiya Mama. Hajiya Mama ta ji daɗin ganin su cikin walwala da farinciki alamun sun daidaita kansu, Ta yi musu nasiha mai ratsa zuciya akan zamantakewar aure, Abba ma ya ɗora da tasa. Little ta maƙale wa iyayenta, duk inda Abra ta yi tana manne a jikinta. Haka Adnan da zai tafi masallaci ta dinga kuka sai ta bi shi, sai da Abra ta goya ta sannan ta yi shiru, daga nan ma bacci ya ɗauke ta, har suka baro daga gidan ba ta tashi ba. Daga gidan Mama ba direct gida Adnan ya yi da su ba, sai suka biya wani bakery suka yi siyayya sannan suka dawo gida. A parlour suka baje suka ci abubuwan da suka siyo cike da ƙauna da tattalin juna. Daren yau ma sun raya shi da nuna wa juna soyayya, sai a yanzu da suka kasance tare kowannen su ya gane ba ƙaramin kewar ɗan'uwansa ya yi ba. Washegari da safe Adnan yana gaban mirror yana shiryawa zai fita Abra ta fito daga toilet. Kallon ta ya yi yana murmushi ya ce. "Princess wai fushin ne bai ƙare ba?" Turo baki ta yi ta ce. "Ba na ce kar ka tafi ka bar ni ba ka ƙi, ni bana son ka yi nesa da ni ko na one second." Takowa ya yi ya zauna a bakin gado sannan ya ɗora ta a kan cinyarsa, yana shafa santala-santalan cinyoyinta ya ce. "Na ce fa ba daɗe zan yi ba, signing kawai zan je na yi na dawo." "To zan bika." Ta faɗa a shagwaɓe." Gefen fuskarta ya shafa ya ce. "No prob Angel, shirya mu tafi." Cikin farinciki ta dinga kissing duk inda bakinta ya kai a fuskarsa tare yi masa godiya sannan ta tashi ta shirya. Shi ya zaɓar mata kayan da ta kasa a cikin waɗanda ya siyo mata. Ganin irin kyawun da ta yi ya ɓata fuska ya ce. "Gaskiya Angel a canza kayan nan." Marairaicewa ta yi ta ce. "Za mu ɓata lokaci fa, kuma ka ce jiran ka ake." Janyo ta ya yi jikinsa ya ce. "Kin yi kyau ne sosai my Queen, ba na son ai ta kalle mini ke." "Babu wanda zai kalle ni fa." "Ni dai ban yarda ba." "Please Baby, kuma na san ko na saka wani kayan shi ma haka za ka ce ya yi mini kyau na cire." Ba don ya so ba ya kama hannunta suka fita. Shi kaɗai ya shiga headquarter ɗinsu ya yi abin da zai yi ya fito suka tafi, saboda wai kar a kalle masa ita. Ta ɗauka gida za su koma sai ta ga sun ɗauki wata hanyar daban. Sai da suka kusa zuwa ta gane prison zai kai ta gurin Daddaynta. Farinciki ya mamaye zuciyarta, ƙima da darajar Adnan suka ƙaro a idonta. Ba gurin da suka je ganin shi last time ta ga sun nufa, wani guri ne mai kamar Hospital suka shiga bisa jagorancin wani ganduroba. Suna shiga wani ɗaki ta hango Bulama kwance a gadon marasa lafiya. Da sauri ta ƙarasa ta kama hannunsa. A raunane ta ce. "Daddy ba ka da lafiya? Me ya same ka?" Cikin ɗacin zuciya ya ce. "Daga cikin sharrukan da na aika da su gurare da dama ne suka fara dawowa kaina, wani aka kawo prison ɗin nan jiya, ashe ya sanni wai mahaifinsa ya rasu a asibitina bisa gangancinmu saboda ba su cika kuɗin da aka buƙata daga gare su ba." Cikin kuka Abra ta ce. "Waye ya yi maka wannan zaluncin haka? Daddy fuskarta duk ta kumbura fa ta yi taruwar jini." Murmushi Bulama ya yi mai ciwo ya ce. "Na tabbata zafi da raɗaɗin da ya ji a cikin zuciyarsa lokacin da mahaifinsa ya rasu sun fi wanda nake ji yanzu a jikina, don haka ban ga laifin shi ba ko kaɗan, hakan da ya yi idan har ya huce ya yafe mini to na yi farinciki, ko ba komai ya rage mini nauyin haƙƙin mutane da na ɗauka ranar gobe ƙiyama." Sun ɗan jima a prison ɗin Abra tana ta kuka, da ƙyar Adnan ya rarrashe ta, ta yi shiru. Ya so ɗaukar mataki a kan wanda ya daki Daddy amma Bulaman ya hana tare da faɗa musu hukumar gidan ta ɗauki matakinta da kanta. Sanadiyyar dukan aka yi masa ya sa aka ɗaga shari'arsa har sai ya samu lafiya sosai. Bayan sun baro prison ba su koma gida ba, wani haɗaɗɗen gurin shaƙatawa Adnan ya kai su, yanayin gurin ya burge Abra ba kaɗan ba. Sun daɗe a can cikin kulawa da ƙaunar juna, hakan ya rage mata kaso mafi yawa na damuwar halin da ta ga Bulama a ciki. Sai daf da Magriba suka dawo gida. Bayan ta yi Sallah ganin Adnan bai dawo ba ya sa ta kira Ummi a waya, ringing biyu ta ɗaga tare da yin sallama, ta amsa mata tare da gaishe ta. Gyara zama Abra ta yi cikin karyar da harshe ta ce. "Ummi don Allah ki yi haƙuri ki yafe wa Daddynmu, ki janye ƙarar da kike ƙoƙarin shigar da shi, yana cikin mawuyacin hali, ki taimaka masa Please ki taimake mu ma." Ajiyar zuciya Ummi ta sauke ta ce. "Nur mahaifinku ya ci amanata, ya cutar da ni ya cutar da ku, bana jin zan iya yafe masa har abada." "Please Ummi, Ubangiji ma muna yi masa laifi ya yafe mana, kuma yana son bayinsa masu yafiya a tsakanin su, halin da Daddy yake ciki kaɗai a yanzu ya ishe shi ishara da masu irin halinsa." A sanyaye Ummi ta ce. "Shikenan na yafe masa saboda ku, amma aure tsakanina da shi ya ƙare." Ajiyar zuciya Abra ta sauke cikin maɗaukakin farinciki, ba ta yi zaton yadda Ummin ta ɗau al'amarin da zafi za ta sakko cikin sauƙi haka ba, godiya ta dinga yi mata kamar za ta ari baki. Tausayin su ita da ƴar'uwarta ne ya kama Ummi, duk lalacewar mahaifinsu a haka suke son shi da son ganin ya yi ingantacciyar rayuwa. Ita ma Afra bayan sun dawo ta kikkira ta tana cigaba da roƙon ta akan ta yafe wa Bulama. Sai da Adnan ya dawo ta ba shi suka gaisa da ummi sannan suka yi sallama ta katse wayar, dama a fitar da suka yi ɗazu Adnan ya loda mata kati a wayarta. Yau jikin Meenal ya yi tsanani fiye da koyaushe, tun cikin dare take bleeding, gabaɗaya ta fita daga hayyacinta ba ta san ma waye a kanta ba. Hankali a tashe Hajiya Saudat da ƙawarta suka ɗauki Meenal zuwa asibiti. Taimakon gaggawa doctor's suka shiga ba ta, bayan wani lokaci wani likita ya fito yana share gumin fuskarsa da alamun damuwa ya dubi Saudat dake gunjin kuka ya ce. "Ke ce mahaifiyar ta?" Ɗaga masa kai ta yi da sauri tare da matsawa kusa da shi ta ce. "Doctor ya jikin nata? Kun tsayar da jinin da take zubarwa, don Allah ku taimaka mini ta samu lafiya, ita kaɗai ce ƴata a duniya." "Sai haƙuri Hajiya, Ubangiji ya karɓi ranta." A gigice Saudat ta ce. "Ban gane ba wanne ran? Me kake nufi?" "Ina nufin ta rasu, Allah ya karɓi abarsa." *Littafin dare da duhu na kuɗi ne, mai so ya tuntuɓe mu a 09047871750* [12/7, 8:27 PM] Abk: Cikin tashin hankali Saudat ta ce "Meenal ta rasu? Wacce Meenal kuma ba dai tawa Meenal ɗin ba?" Dr ya girgiza kai alamar alhini ya ce. "Ki yi haƙuri Madam, yarinyar dai da kuka kawo Ubangiji ya amshi abar shi" Saudat ta ce. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, na shiga uku wayyo Allah na, yarinyar dana haifa ɗaya ta barni don Allah Dr kace ba Meenal ba ce" kuka sosai take tana ihu kamar zautacciyya. Mutuwar ya sanya mata tsoro da ladama mara adadi, yarinyar data haifa ta mutu cikin mugun hali tana mai aikata alfasha, bata tabbacin Ubangiji ya yafewa Meenal ko a a'a. laifi zina abu ne mafi muni, amma ita nata laifin fa? Data raba zuƙata biyu, ta raba uwa da yaranta sbd son zuciya. Da ƙyar ta samawa kanta nutsuwa aka amshi gawar Meenal tare da yi mata suttura. Saudat bata cin abinci ta lalace tunanin yadda rayuwar yarinyarta ya ƙare ya damu ranta, tazo duniya cikin kamala ta koma cikin tuzarci me yafi haka muni a rayuwa?. mafitar yadda haɗu da Ubangiji lafiya take a yanzu da kuma addu'ar samawa Meenal sassauci wajan Ubangiji. Kwana uku da rasuwar data zaune Halima ta kalleta ta ce "Saudat mai zai hana ki faɗawa mahaifin yarinyar cewa yarinyar ta rasu?" Ta sauke numfashi kafin ta ce. "Ni ma nayi tunanin haka, amma ban san yadda zai ɗauki abin ba, duba da yadda mukai uwar watsi da shi ba mu yi rabuwa mai kyau bane" "Duk da haka, ƴar sa ce kuma yana da hakƙi akanta, ya cancanci yasan halin da ake ciki gudun abin da zai je ya dawo" Ta ce "Shi ke nan bari na ɗauki wayar na manta rabon dana kunnata ma" ta faɗa tana miƙewa tsaye tare da barin wajan, bayan ta kunna wayar ta lalubi number Dr Bulama ta kira sau biyu not answering. A kira na uku ne aka ɗauka. "Hello" ta faɗa a sanyaye akai mata shiru ta ƙara cewa "Assalamu alaika" sai a lokacin aka amsa tare da faɗin. "Wslm waye?" Tai shiru alamar tunani can ta ce. "Sorry Saudat my name, Bulama's wife, who am I speaking with?" "Hello" ta furta jin anyi shiru can aka ce "Oh Saudat ya ɗan ajjiye wayar ne, yanzu lafiya?" Ta ce "Idan babu damuwa ina son magana dashi urgent ne". "Kiyi haƙuri, kina iya faɗar komai sai a faɗa mishi idan ya zo ko?" Rashin sani yafi dare duhu, Saudat na waya bata san cewa tracking number ta ake ba. "Shikenan ka faɗa masa, Allah ya yi wa yarinyar shi Meenal rasuwa yau kwana uku, idan ya zo ya kirani" mai maganar ta waya ya ce. "May her soul rest in peace" "Amin na gode" ta faɗa tana sauke wayar. Haka kurum taji gabanta na faɗuwa ba tare da sanin dalili ba, maimakon ta kashe wayar sai ta barta a kunne. Da daddare haka ta ƙara kiran layin wata friend ɗinta dake Nigeria. Washegari da yamma suna zaune suka fara jiyo jiniyar motar ƴan sanda kafin ta motsa wasu ƴan sanda mata suka shigo ta miƙe da sauri ta ce. "Madam lafiya me akai?" Officer ta ce "Wace Saudat?" Saudat jiki na rawa ta ce "Ni ce" "You're under arrest Saudat" ihu ta fasa ta ce "Na shiga uku me nayi muku, ku barni da abin da nake ji, ina cikin damuwa don Allah ku barni wayyo Allahna" tana kuka Halima na kuka haka suka tafi da ita.. _*3 mnts later*_ Ƙamshin turaren Pur oud da Abra ta shaƙa ya sanya ta miƙe da sauri zuciyarta cike da son ganin gwanin nata mutumin daya gama mamaye zuciyarta da salon tsaftacciyar soyayyar shi. Har a lokacin Abra mamakin yadda komai ya sauya cikin ƙaramin lokaci. Ta kalli inda yake tsaye ya dawo sak Sp Adnan Aliyu Matawalle data sani a lokacin baya, ya ƙara ƙima sosai fatar shi tai haske sosai irin hasken nan na baƙaƙe mai ɗaukan idanu. Uniform ne a jikinsa na aiki, wanda suka ƙara fidda kyan shi sosai. Abra ta ɗaga hannu sama alamar sarawa cikin ƙasa da murya mai daɗin gaske ta ce. "Your welcome love of my life, rest of my life" kasa jurewa ya yi da ɗan sauri ya ƙarasu wajanta yana zame hular kansa. "Uhm am speechless" ya faɗa yana jawota jikinsa tare da mannata da ƙirjinsa. Ta zagaye hannuwanta zuwa ƙugunsa tare manne gangar jikinsu waje guda ta ce. "Ina son ka Sp Adnan Aliyu Matawalle, i love You to the square of my...." Ya manna bakinsa akan nata wani hot kisses yake sakar mata ta ko'ina, wanda ya kashe mata jiki baki ɗaya. A hankali ya saketa ta manna fuskarta a ƙirjin shi tana shaƙar ƙamshin Pur oud wanda a kwanakin yanzu yake mata daɗin gaske. Kama hannunta ya yi zuwa kan kujera bayan ya zauna ya ɗora ta akan cinyarsa ya ɗora kan shi a bayanta tare da zura hannunsa a cikin rigarta ya shafa cikin kaɗan daidai kunnanta ya ce. "Ina tunanin nayi ajjiya fa" ta sauke numfashi idanunta lumshe idanun yanayin nayi mata daɗi sosai. Kamar bata son magana ta ce "Ajjiya kuma?" Ya ƙara shafu cikin zuwa ƙirjin tayi zillo ta ce. "Uhm Uhm" Allah ya sani a lokacin a matse take da mijinta, shi take buƙata haka kurum Ubangiji ya ɗora mata kewar shi bata gajiya da shi kwata-kwata. "Yes Madam, Aishatul-humaira ta kusa samun sister or brother, ko both ɗin ma" ta kwanta jikin shi tana mai jan gemun shi cikin shagwaɓa ta ce. "Uhm ni a'a Please ba wata ajjiya?" Ya ɗan ɗagata sama kamar baby ya ce "haba yarinya ai tunda naga kina langwaɓewa kina shaƙar ƙamshin mijinki nasan Adnan ya yi ajjiya a ɗan ƙaramin cikin nan, Wow Sp Adnan Aliyu Matawalle you're lucky ka cika namijin duniya a wannan karan ni zan amshi haihuwar matata da kai na" "Ni ban so Allah" ta rungome shi sosai tana rufe idanunta gaba ɗaya gajiya ta saukar mata. Ya ɗagata sama yana tashi tsaye ya ce "Na san me kike so, muje nai wanka naci abinci sai samu ƙarfi da kuzari da kyau" ta maƙale jikinsa tare da kissing matar kunnan shi. "Mijina" ya riƙeta tsam a jikinta ya ce "Matata ƴar Albarka, ƴar Aljannata" Bata ya haɗa ruwan da kansa ba, duk da kasalar da take ji sai da ta haɗa masa ruwan wanka. Tana ƙoƙarin fita ya fisgota suka faɗa cikin ruwan wankan. Bayan cin abincin suna zaune a parlour suna hira irin ta masoya rabin hirar, I love you ne. Da matata ko mijina, ko kasan ina sonka ai. Tana kwance jikin shi daga ita sai vest, da ƙaramin skert. Shi ma trousers ne jikinsa babu ko riga sai shafa kwantaccen gashin ƙirjinsa take. "Uhm" ya shafa kanta ya ce "ya akai?" Ta maƙale shi sosai ta ce "Kai ne" Ya gane me take buƙata dan haka ya share kawai ya ce "Wayyo me Adnan ya yi bawan Allah, zo nan zo naji" ta saki kukan shagwaɓa tana dukan ƙirjin shi ta ce. "Allah ka gane fa" "Ni ban gane ba" ta sauka jikin shi ta ce "To sai da safe" wani kalar murmushi ya saki yana jawo pillow ya ce. "Ok good night sweetheart, my Queen" Har taje bakin ƙofa ta kasa jurewa ita dai mijinta take buƙata ta juya da sauri tana kaɗa jiki ta nufi inda yake, yana ƙoƙarin magana ta faɗa jikin shi tare da kama fuskar shi, ta haɗe bakinsu waje guda ta kau da duk wata kunya ta ɗiya mace ta shiga bawa Adnan salon da shi kansa sai daya gigita masa lissafi bai taɓa tunanin zata iya haka ba, ɗaukanta ya yi da ƙyar ganin suna neman huce lissafi kai tsaye ya direta akan lafiyayyan royal bed ɗin shi. Washegari ya kama weekend ba tare da sanin Abra ba, Adnan ya zame jikinsa tun safe bai dawo ba sai azahar.. Ta bisa da kallon tuhuma ba tare da ta ce komai ba, ya langwaɓar da kai gefe guda yana riƙe kunnansa tare da faɗin "Double sorry Maa" Ta juya masa baya murya sake ta ce. "Ruwan wanka yana jiran ka Abou-Aisha" Ya san duk lokacin da ta ce Abou-Aisha to fushi take da shi. Ganin yadda ya tsaya yana kallonta ta taka sannu a hankali zuwa gare shi tana zuwa ta shiga ɓalle gaban rigar, ta zare ya rage sai singlet, ta sunkuya ta cire masa takalmi da safar ƙafar shi ta riƙe kayan a hannu. Juya tai da nufin shigewa ya jawota tare da manna bayanta da ƙirjinsa ya zagaye ƙugunta, yana sunsunar wuyanta ya ce. "Wannan sauyin fa? Akan me?" "Magana nake Madam" tai masa banza tare da riƙe hannunsa kai tsaye bathroom ta shige da shi, sai ta fara zuba masa ruwan a jiki kana ta fito ta barshi. Kayan shan iska ta fito masa dasu tana gamawa ta nufi dinning ta shirya lunch. Adnan ya shirya cikin Arewa ɗin data fito masa da ita, da trousers sai baza ƙamshi yake jikinsa ya ƙara buɗewa sosai. A dinning ya sameta tana ganinsa ta ɗauke kai bayan ta gama zuba masa abinci a plate zata juya ya riƙo hannunta yana zaunar da ita saman cinyarsa ya ce. "Ki yafe mini matata, nayi laifi ban ƙarawa wani abu ne ya taso mini cikin gaggawa, am sorry bana son shirun nan" Idanunta ya cika da hawaye tana kwanciya jikinsa ta ce. "Ka bani tsoro, ai ko message kayi mini?" "Nayi laifi ayi haƙuri a yafe wa mijin" tai murmushi ta ce "dole na" "Ina son ka" ta faɗa tana shafa fuskar shi. Ya matseta a jikinsa ya ce. "A duk sanda kika ce kina so na, ina jin kamar nafi ko wanne namiji sa a ne Abra, wallahi duk son da kike mini bai kai kwatankwacin wanda nake miki ba, Ubangiji shi ne shaida idanun zuciyata bai taɓa kallon wata ƴa mace ba da sunan soyayya sai a kanki, farin ciki, kwanciyar hankali, yarda da juna su ne abin da ake nema a zaman aure kuma mun samu a gidanmu, kece uwar yarana daga duniya har lahira Allah ya yi miki Albarka Matata" Hawayen farin ya cina idanunta ta kasa cewa komai sai rungome shi kawai da tayi tana sakin murmushi. Monday aka gabatar da Shari'ar su Bulama, bisa taimakon Allah da kuma jajir cewar Adnan. Dr Yusuf Garba Bulama ya kubuta, bayan binciken takardun makaranta da kuma na asibitin yabi komai bisa tsari, da kuma shaidar da aka samu na taimakon daya taɓa yiwa wasu daga cikin al'umma. Farin ciki wajan Bulama ba a magana, yana fitowa ƴan jaridu sukai masa caa ya kasa cewa komai kawai sai ya jawo Abra da Adnan ya rungome, idanunsa cike da hawaye. Gida na musamman Adnan ya bashi, bayan komai ya lafa ya faɗawa Abra rasuwar ƴar uwarsu. "Allah sarki babu rabon ganawa, Ubangiji ya jiƙanta ya yi mata Rahama" a sanyaye Dr ya ce "Amin Ya Allah, ya kamata Ku tafi gida haka, Allah ya yi muku albarka ya baku zuri'a ta gari" a kunya ce Adnan ya amsa da Amin. Suna zuwa gida suka tarar da motar Hajiya Mama da Abba parke a parking lot. Adnan ya yi parking tare da fitowa, hakama Abra suna zuwa Hajiya Mama ta fito hannunta ɗauke da Aishatul-humaira. "Sannu da zuwa Mama,Abba" Hajiya Mama ta ce "yanzu muke shirin juyawa sai gaku,muma munzu taya murna" Aishatul-humaira ta shiga tsalle a hannun Hajiya Mama tana miƙawa Adnan hannu. "Oh yaran zamani wai harta gane ubanta, shi ya sa na tattaro kayanta na dawo da ita" Adnan ya rungome Little wacce take gwaranci tana jan gemun shi. Sun daɗe a gidan cikin ƙaramin lokaci Abra ta shirya musu girki lafiyayye. Suka ƙara tayata murnar fitowar Bulama kana suka tafi. Adnan da Abra suka saka Little a tsakiya yau zasu kwana tare da ƴarsu wannan ya jawota wannan ya jawota. Haka suka kwana cikin farin ciki da ƙaunar juna, washegari ƙarfe 10 na safe jirginsu ya ɗaga zuwa Kano.... [12/10, 11:40 AM] Abk: Slowly Salman yake driving idanunsa akan titi daga airport zuwa gida, ya girgiza kai kaɗan yana sauraran maganar ƴar uwar tashi kuma yayar shi har abada.. Murmushi kawai ya yi speaking calmly ya ce. "A'a yaya,My wife had a miscarriage in four months" "Ya Salam yanzu Faris Afra tayi ɓari amma a rasa wanda zai faɗa mini?" Ta faɗa idanunta na cika da hawaye sbd tausayin Afrar tun kafin ta ganta. Ya numfasa kaɗan yana kallon Aishatul-humaira dake riƙe a hannun mahaifinta ya ce. "Jiya ne fa, kuma na samu labarin za kuzo ba shikenan ba?" Abra na hawaye ta ce. "Ba shikenan ba, daka faɗa mini ai ko a waya zan kira nai jaje ko?" Ya ƙara yin murmushi domin gani yake yafi kowa ciwon rasa gudan jininsa amma bai fidda rai ba zuwa wani lokaci, domin wannan ɗin ma bai san zai samu nan kusa ba. "Am sorry yaya nayi laifi to" Adnan ya ce "Ba wani sorry kawai ka saka mini matata kuka, ka kiyaye ni fa" a wannan karan drya sosai Salman ya yi cikin farin cikin ganin Adnan da Abra suna zaune lafiya ya ce. "To Yaya Adnan a yafe mini, amma kada a manta nima fa ba gwauro bane a to" a haka dai suka ƙarasa gidan. Suna shiga Abra ta tafi da gudu ta rungome Mami tana hawayen farin ciki. "Yau na shiga uku, wai ke kam komai na kuka ne, ɗaga ni to" Abra ta ƙanƙame Mami tana murmushi ta ce "Mami hawayen farin ciki ne fa" "To nutsu kada ki samu asara yanzu" Abra ta ce "Asara kuma Mami tame?" Kai tsaye Mami ta ce "ina nufin kada kiyi ɓari irin na ƴar uwarki" Abra ta zauna kusa da Mami ta ce "Ayya Mami ai ni bani da ciki" "Ɗan duma ne, zai bayyanar kan shi ai da zarar lokaci ya yi" murmushi kawai Abra tayi. Adnan ya zauna ya ce "Ina yini Mami?" Ta ce "Allahamdulillah, ya hanya" kansa a ƙasa alamar martabawa ya ce. "Allahamdulillah!. Allah kuma ya mai da na aike" murmushi kawai tayi tana kallon Aishatul-humaira wacce ta ƙara wayo sosai ga wani kyau da Allah ya zuba mata, ta luff a jikin mahaifinta sai barci take. "Mamana an zama ƴan mata, ta fara tafiya ne?" Abra ta ce "Tab ƴar aiki muka samu Mami, wallahi komai ta samu fasa shi take, haka ta fasa wayar Abou-Aisha ta lalace ga surutu" "Ah masha Allah, Allah ya raya mana ita" Salima ta fito tana musu Sannu da zuwa. Bayan sun gaisheta, Mami taiwa Abra farin ciki kuɓutar Dr Bulama sosai tare da ƙara jajanta lamarin. Daga nan ɓangaren su Salman suka nufa, dake bayan tafiyar Salman ɗin an sake gina sabon ɓangaren a gidan Abbi, kuma babu kowa ciki shi ne Salman da Afra na dawowa suka sauka a nan. Mami tabi bayansu da kallo gwanin sha'awa kana ta shiga kallon tilin kayan arziƙin da Adnan ɗin ya kawo musu. A zaune suka samu Salman rungome da Afra sai kuka take taƙi haƙura tana ganin kamar gangancinta ya sanya ta rasa abin cikinta. "Kai baka jin kunyarmu ko"? "Ni kam Yaya zanji kunya ko kai? Ku rufe idanunku idan ba zaku iya ba" Adnan ya kwantar da Aishatul-humaira a cinyarsa yana ɗan jijjigata sai gani ya yi ta fara ɗaga kai da ƙafa kamar wacce akewa wasa. "Babu abin da zamu gani wanda bamu san dashi ba, mun shige darasinku" Adnan ya faɗa yana zaunar da Little wacce take ƙoƙarin sakkowa zuwa wajan Salman domin tuni ta gane shi. Abra ta koma kusa da ƴar uwarta tana dungure kan Salman. Hira suka yi sosai kafin Abra ta janye Afra zuwa bedroom ta fara bata darasi mai zafin gaske. "Little Kinga mun rasa mijinki ko? Don't worry soon za a samaki wani" ya zauna yana mata wasa ina ita hankalinta na kan wayar shi. "Yaushe kuka dawo daga ƙasar wajan ne?" Salman ya ce "Cikin satin nan, muna tunanin ma hawa jirgi ya kawo ɓarin Allah dai ya barwa kan shi sani" "Ayyah Allah ya kawo ni soon" hira suka ɗan taɓa duk da Adnan hankalinsa yana kan Abra baya son tai nesa da shi baki ɗaya. Bayan sun yi sallah Mami ta aiko da lafiyayyan lunch mai tsari kala-kala. Fitowa tayi daga kitchen zata shige bedroom ɗin Afra ya yi saurin jawota jikinsa yana kissing wuyanta. Ta marairaice fuska tana kallon shi, ya manna lips ɗin shi akan nata tare da yin kissing kaɗan ya ce "kin barni kamar maraya, Allah zan faɗawa Hajiya Mama" Ta shafi gemun shi tare da wuyan shi ta ce "Please mana, yau ɗaya ka barni muci abinci da Afra kaji" ya langwaɓe tare da riƙe ƙugunta da kyau yana mannawa da nashi murya bata fita sosai ya ce. "Ki gama yanzu,ina son mu gaisa da ƙanin Little" ta rungome shi sosai shi kuma ya fara ƙoƙarin kissing bakinta.. Ƙafar shi yaji an riƙe ana miƙewa tsaye tare da bubbuga ƙofar. "Oh my God, jeki madam tunda little tazo ba za ai abin arziƙi ba, yarinyar nan kinawa babanki baƙin ciki yasin" ya faɗa yana miƙa hannu tare da ɗaukan ta, shi bai ma san yaya akai ta zo wajan ba. Dry sosai Abra tayi tana shafa kan Little. Da daddare Salman ya yi musu jagora zuwa gidan Ammi sosai taji daɗi, kamar ta ƙwace Little amma taƙi ta maƙale a jikin Salman sai ka rantse shi ne ya haifeta shi kam dry kawai yake, daga nan suka je gidan Uncle Shurem sun daɗe sosai, ko wanne gida sai Adnan ya ajjiye abin arziƙi. Ganin Salman ya ɗauki hanya daban ya sanya Abra faɗin "Faris ina zamu?" Ya ce "Gidansu Mami angel" Jin Salman ya ce angel ya sanya Adnan taɓe baki, yaci ace ya saba amma a kullum Salman ya faɗi haka sai yaji kishin Abra, yana dannewa ne kawai sbd yasan kawo yanzu babu komai a zuciyar Salman ɗin. Salman kuma ba zai taɓa iya cewa Abra kai tsaye ba, bakinsa ya saba da angel babban dalili kuma Abra is his first love, yana ganin girma ƙimar sunanta ainun, ba zai taɓa iya manta abubuwa da suka faru ba, da yawan lokaci yana tuna first kiss ɗin shi da ƴar mace kuma Abra ce sai ya yi saurin yin Asstagafirullah. Shi ya sa a kullum ba a son namiji ya ɗinga zaƙewa yana aikata abu ga mace, sbd rashin samun tabbaci kasancewar ta mata wajanka, idan bata zana matarka ba a kullum ka ganta sai abin ya faɗo maka. Bayan sun gaisa Anuty Suwaiba ta ce "Abra nayi miki abubuwa da yawa, don Allah ki yafe mini ina cikin jarrabar rayuwa, tun bayan aure na da rabuwar da mukai, har yanzu wani namiji bai taɓa cewa yana so na, don Allah ki haƙuri ki yafe ko zan samu sassauci da rahamar Ubangiji" Abra ta ce "na yafe miki har abada" haka Uncle Faisal, wanda ya auri mace bai san halinta ba, sai gashi ashe maza take bi har sukai auren bata dai na ba. Shima ta ce ta yafe masa babu komai, haka babar Mami. Daga nan shopping mall Salman ya shige ya dinga jidarwa Aishatul-humaira kaya kamar hauka, Adnan zai magana Abra ta ce ya rabu dashi ai yana da kuɗin kuma shima babanta ne, bisa dole Adnan ya yi shiru. A ɓangaren Salman aka bawa Adnan da Abra wajan kwana Mami kuma ta ɗauke Little. Cikin dare Adnan ya ɗauke Abra zuwa bedroom ɗinsa, a ranar bata samu barci ba sai da sukai sallar asuba, sosai Adnan ya tara mata gajiya ga yanayin cikin dake jikinta wanda kawo yanzu ta san da zaman shi. Washegari motocin Major Khamal Khamis suka sauka a gidan,yana shigowa yaci karo da Little da sauri ya ɗauke ta yana faɗin "Matar zuwan yaushe" ta dinga tsalle a jikinsa, Mami ta rungume shi ta baya tana cewa "Wlcm Man" ya jawota gaba yana riƙe hannunta. Sosai Abbi yai farin ciki ya ƙara sakawa ko wanne albarka, a nan yake cewa ya kusa ritaya daga aiki ya dawo gida baki ɗaya hakan ya yi wa su Mami daɗi. Adnan ya kwashi iyalan shi zuwa gidan abokinsa Fayyad sun jima suna hira.. Washegari gari jirgi ya ɗaga dasu zuwa Kaduna. Rayuwa kenan, komai ya yi farko yana da ƙarshe a hankali Ubangiji yake tafiyar da komai cikin iko da buwayar shi, sauyi da ci-gaba yana ta zuwarwa Adnan da matsayinsa ya juye daga kan S.p ya dawo Inspector General of Police. Zaman gida ya yi masa wahala sosai. Da nacin su Abra da kuma addu'a haɗi da magiyar da Dr Bulama yake Ummi ta amince suka mai da hankalinsu, amma ta kwashe komai nata, Adnan ya buɗe sabon asibiti babba ya mallakawa Dr Bulama. Da gudu manyan motoci ke shigowa cikin Bulama's twins privet hospital. Jijiya na tashi kota ina, wasu manyan jami'an tsaron suka buɗewa Adnan ƙofa ya sako da ƙafarsa zuwa ƙasa cikin sauri kuma ya fito sanye da blue ɗin uniform wanda suka amshi jikinsa. _Ag ISP Adnan Aliyu Matawalle Inspector General of Police_. Ya juyawa da sauri zuwa cikin hospital ɗin yana ɗagawa sauran hannu alamar su tsaya, kai tsaye emergency ya nufa, yana zuwa ya samu Hajiya Mama tsaye da Ummi wacce bata jima da zuwa ƙasar ba, Abdullah na zaune shi da matar shi Soumayyerh a gigice Adnan ya ce. "Mama where's my wife? Tana ina?" Da hannu ta nuna masa labour ya nufi shiga Mama ta hana shi bai tsaya ba yai shigarwar shi ciki, yana shiga idanunsa ya sauka akan Abra wacce take cikin halin ciwon naƙuda su duka sun tsorata domin cikin kusan watan shi goma sha ɗaya, da sauri ya rungume ta yana shafa kanta. "Sorry Beb, sorry sweetheart sorry" shi ne kawai abin da yake faɗa, kuka sosai ta saka tana riƙe Adnan zufa na yanko mata, iya wahala tasha Adnan ya yi zaman dirshan a gadon lokacin da Abra ta fasa ihu daidai lokacin data haihuwa shima ya saki kuka yana riƙeta sosai a jikinsa ganin ko motsi ta kasa, tausayinta ya kama shi sosai. Likitoci suka zare babyn wane yake ƙato dashi tubarkallah, aka shirya shi cikin wasu kayan sanyi masu laushi sbd weather garin. Itama Abra aka gyara ta tare da mayar da ita ɗakin hutawa. Adnan ya rungome Abra da baby boy ɗin, jaririn uban shi ya yo baƙi ne sosai sai jajayen laɓɓa da yake dasu sai motsi yake yana kai hannu baki, a hankali Adnan ya lumshe idanun tare da faɗin. "Allah ya raya mana Abdullah bin Adnan Aliyu Matawalle" Abra tai farin ciki sosai soyayyar Abdullah ta wanzu a zuciyarta musamman ganin kamar shi da Adnan. Akai taron suna lafiya kayan da Abra ta samu ɓata baki ne, rasa inda zata saka kanta tayi kukan farin ciki tayi babu adadi. _3yrs ltr_ Abubuwa da yawa sun faru, Salman ya gama karatu lafiya lokacin yana da yarinya ɗaya mai suna Roumaisah kyakkyawa da ita, wacce kai tsaye yayi alƙawarin bawa Abdullah aurenta ko bayan babu ran shi. Burin Salman ya cika domin a rayuwa babu abin da ke birge shi kamar siyasa kamar wasa ya fara neman takara, kasancewar mahaifinsa yana da manyan mutane Adnan ma ya tsaya masa, sai ganshi yau Salman shi ne ke mulkar jama'a matsayin gwamnan garin. Gov Salman Khamal Khamis as governor of kano State. Bulama hankali ya kwanta komai ya dawo daidai, baya taɓa ɗaukan wanda bai dace ba acikin asibitin sa. Salima ta haifawa Abbi kyakkyawar yarinya kai tsaye ya sanya mata suna Na'ima, Mami tai farin ciki soyayyar yarinyar ta shiga ranta sosai. Saudat na gidan yari har yanzu laifukan ta manya ne sosai, tunda har da laifin kisan P.a ɗin Ummi ne a kanta... Kaduna airport. A hankali suke tafiya hannu sarƙe cikin na juna, Adnan na riƙe da Aishatul-humaira wacce ta girma sosai kusan shekaru huɗu kenan, Abra kuma na ɗauke da Abdullah wanda yake kama da Adnan sak gashi da kuzarin shi sosai. Ciki so da ƙaunar juna suke hawa kan steps ɗin jirgin wanda suka samu zama can cikin vip, Adnan ya faki Idanun Aishatul-humaira ya mannawa Abra kiss ya ce. "I love You, babu abinda zan cewa Ubangiji sai godiya" ta ɗora kanta a wuyan shi tana sakin murmushi ta ce. "Kai ne garkuwata duk abin da na zama a rayuwa kai ne sila, burikanmu suna cika bisa saka hannun mazajanmu ko albarkarsu, kulawarka kaɗai ta isa ta zama bar gwatance, ina cewa nayiwa sauran mata zarrah, ina son ka mijina Loving you has been a beautiful dream I never want to wake from. You are a rare, beautiful soul. I love you so much" Ya matseta a jikinsa farin ciki na ratsa zuciyarsa daidai kunnanta ya ce "My heart beats for you. Your love is a soft breeze, bending me gently, refreshing my soul. Allah ya yi miki Albarka, ya baki dukkan abin da kike so duniya da lahira nikam tuntuni na ɗaga miki ƙafar shiga aljanna" Murmushi tayi tana jan gemunsa ta ce "Ina son ka, Ubangiji yaci gaba da kare mini kai ya baka arziƙi na halak ya baka ikon sauke hakƙin iyalanka da al'ummar da suke kan ka" Ya saƙalo kanta yana kallon cikin idanunta ya ce. "I need your warm kiss once again" gaba ɗaya sun manta da batun Aishatul-humaira yarinya mai shegen wayo da kaifin tunani, wani irin Fitinan nan kisses Abra kewa Adnan, ganin zata gigita masa lissafi ya zame bakinsa yana kallon idanunta ya ce. "Uhm love" Ta ɗaga masa gira tana faɗin. "I am the luckiest of all humans. When you look into my eyes, I see pure, beautiful love. My heart overflows with joy. I’m so blessed to be loved by you, handsome" "Ina son ki matata" kafin su magana Aishatul-humaira ta shige tsakiyar su tana faɗin "Ina son ku Ammi, Abbi." Adnan ya haɗa da Abra da Aishatul-humaira da Abdullah ya rungome a jikinsa baki ɗaya ya ce. “Allahamdulillah” *ALLAHAMDULILLAH* muma Bright pens muka ce baki ɗaya, anan muka sauke wannan littafin na *DARE DA DUHU* Abin da mukai kuskure Allah ya yafe mana, wanda mukai daidai Allah ya bamu ladan shi, Ubangiji ya sanya littafin ya zama hujja garemu ba hujja a kanmu ba. _Muna godiya da masoya wanda suka kasance damu, wasu Munyi musu kuskure wasu kuma munyi musu daidai, ko kalli labarin da idanun zuciyarku. Komai a tsari yake👌🏾 kasance damu a sabuwar shekara har Ila yau mu na dai *Na'ima sulaiman sarauta Nimcyluv, marubuciyar Tsintacciya, Idan ba ke❤‍🔥* tare da *Zainab Shehu kumurya marubuciyar Komai nisan dare, da Neehal* sai *A'isha Adam marubuciyar Gaba Da gabanta, Aƙidata*_ domin magana da Bright pens kai tsaye duba nan 09047871750. Ga samu wanda zai maye gurbin DARE DA DUHU a zuƙatanku littafin IDAN BA KE wanda Nimcyluv take rubutawa cikin salo na musamman. Domin jin labarin YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU DA MATAYEN SHI BIYU, DA MUTUMIN DAKE SHIRIN RABA SHI DA ƳAR FILLON SHI zaku iya biyan 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616. Bright pens Nimcyluv Ayushercool Zee kumurya ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 Thu/Dec/ 8