Author : Sakina Yazid Category : Top Hausa Novels 2025
tafukan hannunta ta fashe da kuka. Wannan wane irin wulakanci ne, tana murna ya saki kishiyarta amma kullum suna tare, ita kuma tana nan ya kulleta a gida. Wannan wace irin musiba ce? So take ta ware rana taje ta sami Khadeejan a office din nata ta tara mata mutane amma dai tana tsoron kada Mustapha ya saketa a kan hakan; don yanzu taga kamar ma ba a haiyacinsa yake ba. To yanzu babu aure a tsakaninsu yana mata wannan tsohon nacin idan kuma ta dawo ya za ayi? Ita menene makomarta ya dawo da rabin ransa me kaunar ‘yayansa.
Ta dora hannu a ka ta sake rushewa da kuka.
END