ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

Author :  Maryam Abdul Category :  Old Hausa Novels

Chapter   4 / 30

9K to 12K   out of 88.3K words

da damuwa ne"?

" Um nagode sosai Allah ya saka da Alkhairi" still Kanta a k'asa itakam har yanzu tsaronsa takeyi da gaske.

"Hmm damefa"?

Bata ansa ba sai Ledar da ta Mik'a mishi " gashi ka kaima Aunty Zainab ina gaida ita sosai " duk cikin sanyayyiyar murya take maganar.

"Allah ya kiyaye" tana fad'a ta juya ba tare dataji me zaice ba, binta yayi da kallo harta shige, Shafa Kansa yayi tare da smiling harda lumshe ido (tofa me kenan Dr?)...........

Zainab taji dad'in kyautar Laure kuma ta nuna hakan a fuskarta wanda hakan ba k'aramin dad'i yayi ma Abdool ba, amma kuma k'asan ranta tanajin kishi sosai saboda zuwa yanzu ta gane itace dai 'yar fillon da yake magana, to amma meyasa ta damu da yawa batada tabbacin sonta yake ko tausayinta, dan tasan Abdool da tausayi a d'an zaman da sukayi yana d'aya daga cikin hayensa dake k'ara nutsata a k'aunarsa, amma kuma tanaji a jikin ta na Laure ya wuce tausayi to amma meye mafita saboda a gaskiya tana matuk'ar k'aunar sa tare da kishinsa (tofa Zee u say something oo).

"Sir pls idan zakaje Skk dis week zan bika ka ragen hanya"?

Saida yayi Jim sannan yace "OK".....


*End of week....*

Har k'ofar gidansu ya taho d'aukar ta, sanye ta fito cikin Arabian gown black tayi rolling da light blue d'in kashka, light make up tayi, tayi kyau ba k'arya.

Tunda ta fito ya bita da ido for d first time daya k'are mata kallo, tayi masa kyau amma kuma bata a zuciyarsa maganan gaskiya, dan ya dad'e da harbo jirginta musamman a d'an lokacin nan da take shige masa yasan sonsa takeyi, kuma har cikin ransa yana tausaya mata saboda yanzu shima yasan dafin so.

Tunda suka gaisa suka d'auki hanya bamai cewa uffan kowa da abinda yake sak'awa a ransa.

K'ira'a ya kunna musu ta *Shaik sudais* cikin suratul bak'ara, cikin kwarewa yake tuk'in yana bin karatun a hankali cikin daddad'ar muryarsa mai killing d'in Zainab, aiko lup tayi a kujera tanajin inama su couple ne, direct gidansu zasu wuce yanzu sai imagining takeyi a ranta tana murmushi( boyar Allah).

Batama san sun iso ba saida taji yana fad'in " ina muka nufa" cikin kasala tace.

"Mabera" gidane mai kyau madaidaici dan Baban ta yana da hali dai2 gwargwado, saboda ma'aikacin gwannati ne kuma ba laifi yanada salary, Zainab CE babba 'yarsa sai k'annenta 4, yana ajeta har zai ja mota tace "pls sir ka shigo Ku gaisa da Momy na".

"Oh! Sowie Zainab I'm urgent now but i promise zanzo when I'm free".

Godiya tayi masa sannan yaja motarsa zuwa family house nasu.............





*na shiga busy, ga matsalan b3, kuci gaba da hak'uri Dani* one love friendsd'=?M?



=؄? Meryerm Abdool=؄?
[7/17, 12:08 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?


*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*

_baya shiga aljannah mai yankewa(yana nufin mai yanke zumunci)_

*to 'yar uwa nidake dasu muyi k'ok'ari muga mun sada zumunci, musamman wanda yayi nisa, ba wai sai zumunci na jini, Aa harna musulunci saboda dukkan musulmi d'an uwan musulmi ne.*

Allah yasa mudace =?O?



```Double love belong 2 u, ina yinku =?
? momma (Ayshat garkuwa, neighbour(zee Yabour), indon kauye, Fashuna, swerry, Husna, ummyn yusrah, momyn ihsan, Maman khadija, Seemaluv, Rufy, ummimi, eshat asym, ummu safwan, ummi garkuwa, zarah adami, maskurah, Ayshat hanwa, shukrah, ummihaneefa. Pls wad'anda ban fad'a su tsumayeni next page love u all dearest=?
?=?
?```





=??? *Episode* 46--50



'Yan dubiya sai zuwa Suke ciki harda jauro anzo kamar mutumin kirki hadda wani duk'awa waishi a dole ladabi yake, Ardo dai kallonsa kawai yayi, yasan dai ba Wanda ya isa ya Aurar da Laure sai shi, ya barsu da shirmensu, 'yar ledar dubiya sai ciki yaje da ita ya bawa Iya Hari, dan ya k'asa ba Ardo.

Ita kuma mai kwadayi baki har kunne ta ansa tana shi masa Albarka, ita da Lanti sai rawar kai Suke, Shatu dai idone kawai nata, Laure ita harta manta dashi d'an kwana daya da basu had'u ba, data ganshi kamar ta hadi zuciya, shiko gogan naka dad'i kasheshi yaga rayuwarsa gata cikin kayan 'yan birni ji yake awa ya d'auke ta ya tafi, ba laifi shima yayi shigar arziki yau anzo dubiyar suruki cikin manyan kaya hadda hula, kamar abin arziki, saidai idonnan kam nanan kamar garwashi (chain! d'an kwaya baiyi ba, Allah ya karemu da zuri'armu Ameen).





Abdool yana isa b'angaren kakansa ya shige, yana zaune kamar kullum yana duba littafan musulunci, gaisawa sukayi cikin fara'a tare da tambayarsa yanayin aiki ya ansa da komai qlau, nan sukayi barkwancinsu da suka saba tare da tab'a hira, sannan ya shiga ciki ya gaidasu kamar kullum kakarsa fuska ba annuri suka gaisa, sannan ya dawo ya gayama Alhaji zai isa inda Hakeem dan zasuje Argungu ne.

"Madallah Hakeem yaron kirkine kullum sai yazo dubani ga dawainiya, Allah dai ya sanyama abotarku Albarka kuci gaba har abada ".

" Ameen Alhaji, ai indai Hakeem zaiyi abinda yafi haka" ya fad'a da murmushi dan yasan abokin nasa sarai akwai kirki matuk'a (shi akeso aboki na gari Allah yasa mudace).




~~~~~~~~~~~~~~~~~~






Hakeem ne kwance parlour gidansa sai bacci yake cikin kwanciyar hankali, Ac sai sanyaya sa takeyi, Abdool tsaye kansa ya kama k'ugu kamar mace yana tunanin kalar tasuwar da zai masa.

Saidai ya daddage yakai mishi bugu a baya, aiko sai gashi zaune yana Sosa bayan saboda yaji bugun sai raba ido yake kamar Wanda yayi k'arya.

Abdool kuwa dariya yake masa, dariyarce ta sanar da shi mai aikin, harara ya watsa masa "kaidai anyi mugu wallahi, mutum na baccinsa kazo ka tashesa fisabilillah".

"Kaiko idan ba wauta ba, meyasa ka kwanciya a parlour kuma k'ofa a bud'e salon a saceka ka bani aiki".

Dariya ya basa " imaging a saceni fa? Meye amfanin securitys d'in? A side ma waya kwanciyar bakai ba tun ten na shirya ina jiran ka, amma shiru kaman an aiki bawa garinsu" ya fad'a tare da K'ara da dalla mishi harara.

Siririyar dariya yayi tare kwanciya a seat hadda lumshe ido "hmm ka Bari kawai dude d things are much fa".

" Hmmm ba wani things lover boy, kadai kace love na nuk'urk'usarka period, wai ina labarin 'yar fillo taka"?

"Hmm! Wani bunch of surprise, ina last time da muke waya nace maka ina guest? Kakanta aka kawo emergency....." Nan dai ya bashi labarin duk abinda ya faru.

Hakeem hadda buga k'afa saboda dariyar k'eta "I told oo ur in love, lallai makashin maza, mazane ke kashesha, ina zanga Shukrah da Memzy alhakinsu ya fita.

" kaifa matsala dakai kenan! Ana maganan arziki kanata tsiya, ai kaima kasan ban musu walak'anci ba, an rabo lafiya wata kil ma sunyi aure, whatever dai yanzu meye way out"?

"Hmm kana sonta ka Aureta kawai".

" what! In aureta fa kace, kasan me kake fad'a kuwa?"

"Na sani mana, meye ribar soyayya idan ba aure?"

"Abinda nakeso ka gane, yarinya ce sosai inaga ko sa'ar Nihal batayi ba, sannan gata tsorona takeyi, abar maganar wannan ma ina matuk'ar tausayinta da alama tana cikin damuwa kamar yadda na gayamaka kullum cikin damuwa zaka ganta koda kuwa tana fara'a ne zaka tsinkayo damuwarta".


"Kaji Smart! Well tunda kakanta Nada saukin kai inaga ka fake da zuwa dubashi daganan sai kud'an saba, kaga kamai zaizo da sauk'i".

" wow good idea friend, hakan za'ayi".

"Hhhhhh toya maganan Zee kuma?"

"Kaji wata kuma ai ina gayamaka tare muka taho da ita nayi dropping din ta, hmm taso ta kaimi cikin gida na zille mata".

Dariya sosai yaba Hakeem yanayin yadda yayi maganan " kaji na 'yar fillo da Zainab".

"Fad'i ka k'ara ai gwandani nayi kasuwa kaifa?"

"Hhhh ba komai dai".

" amma kasan me? Ina tausayawa Zainab fa, saboda yanzu nasan rad'ad'in so".


"To ka auresu duka mana".

" caff! God forbid, bazan Iya ba".

"Nidai kaika Jiyo, kaga tashi muje time is going".

" oh zuwa Argungu is no big deal fa, nan da one hour mun isa, kuma ai bayau zamu dawo ba, yawwa ina sak'ona, dan bazan dawo tanan ba".

"Au abin 'yar hakane" Hakeem ya fad'a yana bashi wata k'aramar Leda, dama ya fito da kayansa shi kawai yake jira, ta motar Abdool suka tafi......

Tarba mai kyau suka samu daga kakannin nasa na Uwa, da Kawunsa, gaisawa sukayi cikin fara'ar ganin jikan nasu, bayan sun hutane Abdool ya d'auki Hakeem ya zaga dashi gari, dan yasan garin sosai, kamar su gidan Al'adu, matan fada, mala, grand fishing, da dai sauransu basu suka dawo ba sai magrib, bayan sunyi sallah kuwa suka dasa firar yaushe rabo da kakannin NASA.....


Washe gari ma sake fita sukayi dan garin ya burge Hakeem sosai( ai dole ne Hakeem, Argungu garin nabame kowa sarki, gari mai ni'ima da dinbin tarihi, garin sarautar gargajiya data zamani, kabawa ikon Allah Ku adda ruwan nan) lolz.

Basu suka baro Argungu ba sai bayan la'asar tare da tsarabarsu ta kifi.

Anan yabo suka rabu Hakeem ya shiga motar baya zuwa Skk, kamar yadda Abdool yace hakan yayi akayi.

Wanka kawai yayi ya canja kaya, ya d'auki hanya kilgori dan ganin mintin zuciyarsa...........







_manage pls_ =??




=؄?Meryerm Abdool=؄?
[7/18, 10:05 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?


```#one love # just for u guys,=?
? Aunty kausar, Aunty khady, Suhana, Ummu khady, sisin Mama, fateey nashuka, Meryerm mukhtar, Lemancykhan, Salma(momma), samrah, Biebie die, biebie, sumyn bash, Rafe'at, Ayshat Yabour, waleeda wazir, deeja wazir, beebah wadata, Nana fa'ad, miss Hafsy, miss feedy. Heart u guy, d'Allah yasa ban manta kowa ba=?"?```








=??? *Episode* 51--55




"Ke bakiga yadda nirrud'e ba jikina sai rawa yake, awa i???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?n saki hitsari cikin wando, da nigga nai".

" hhhh hhhhhh dama nasan haka za'ayi ainayi mamaki da nigga ya dawo daku daga asibiti, ahe dama likita na? Hi yassa ni matsu mu had'u in ha labari".

"Yo nima bansan likita na ba, na aza d'an sanda ahe likita na, keni koda munka shiga Yabo hankali na bai tare dani kwata-kwata bangane komai ba saida nigganai nittuna ai nan niya na munka ganehi ranar".

" toya kunka k'are miya hwada ma su Ardo?"

"Ke walle bansani ba danni gidan wata 'yar binni ya kaini nikkwana, Ashe sunada kirki kala biyu ta bani irin na binni, kuma tabbani abincinsu mai dad'i ke shima yanada kirki bakiga hidimadda yayima su Baffa b.........." Nan dai taci gaba da zuba kamar 'ya'yan kanya dan Laure badai surutu ba idan ta had'u da wadda ta saba, dan ma a gida batada abokin yine sai Ardo, ga tambaya amma ai dole fillo akwai tambaya. Lolz



Tun daga nesa ya tsinkayo su da tuluna akai, da alama firar da Suke tayi musu dad'i sai kwasar dariya Laure takeyi, rungume hannuwa yayi a k'irji ya jingina da motarsa sai faman kallonta yakeyi, Ashe tana fira haka? Ashe tana dariya haka? Yake tambayan Kansa.

Dan ba k'aramin kyau tayi mishi ba yadda take dariyar gwanin sha'awa komai tayi burgesa takeyi, komai nata unique ne (oh Dr ka fad'a da yawa fa).

Har sukazo suka wuceshi sam basu kula dashi ba, da yake suna right shikuma yana left.

"Hmmm ki bari Abukkiyata Jauro ya dameni ya hani jin dad'i kamar nid'ai a macce".

" ai bakiga komi ba kwana gudan da kikayi bakyanan baki ga zarya ba wai sai in hwada mishi ina kikaje wai yaje gidan ba kowa, seda niyyi ta yimai rantsuwa sannan ya yadda".

Ta bud'e baki zatayi magana kenan.... " 'yan fullo masu tulu aka" ya fad'a cikin daga murya saboda su jiyoshi ai kuwa sunji, k'irjinta ne ya harba, dan ta gane mai muryar tome yazoyi kuma? Ta tambayi Kanta.

Itakam Delu tuni ta jiya ganin mai kiransu tana ganin shine ta tab'o Laure datak'i juyowa "Laure mutumunki ne hwa".


Takowa yayi har inda Suke, cikin girmamawa suka gaidashi, tuni bakin surutu ya d'inke kamar ruwa ya cita " daga ina haka?" Delu ce ta ansa "daga rahi debo ruwa".

" Baba na nan?" Ya fad'a yana kallon Laure, data wani takure saboda bako hijab sai wani siririn mayafi, duk ta jita wani iri dan dama bata saba fita hakan ba, yauma bala'in Hari ne ya fitar da ita ba shiri.

"Um yana nan" ta ansa kai tsaye.

Kowama yayi gurin motarsa yayin da su kuma suka nufi gida, saida yaga sun bace ma ganinsa sannan yaja motarsa.


Yana zaune kamar kullum yana duba littafansa na addini, jin tsayuwar mota yasa ya d'ago, yayi mamakin ganinsa, amma bai nuna a fuska ba, da fara'a ya taresa, bayan sun gaisa, ya shiga ciki yasa. Aka kawo masa fura wacce taji damu da nono fara k'al, yasha sosai dan dama favorite d'insa ce.

Booth yaje ya fito da kayan fruits shake a Leda, sannan ya d'akko wannan ledar sak'on daya ansa gun Hakeem.

"Baba dama maganine na kawo maka wannan in heeler ce da kaji alaman asthma ka shaka ta baki ta saurin saukar da ita, wad'annan kuma magungunan hawan jini ne...." Nan dai yayi mishi bayani yadda zaiyi amfani dasu, godiya Sosai Ardo yayi tare da sanya masa Albarka, shidai yana ganin hankalin yaron sosai har yana raya Wani tunani a ransa game dashi.

Cikin firarsu ne yake cewa yanayin garin na matuk'ar burgeshi, zaiso yad'an zaga garin.

"To ai Bari in kira Ramlatuna ta d'an nuna maka gari, kafin magriba kad'an ga wasu guraren" zanso kuga zuciyar Abdool farincikin bai misaltuwa, dama haka yakeso.




" " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " " "



A k'afa suka fito tana gaba yana biye da ita, suna tafe kamar gumaka ba mai cewa uffan, ja yayi ya tsaya yak'i tafiya, saida tayi d'an nisa taji alaman ba'a binda aiko tana juyowa ta gansa tsaye abinsa.

Dawowa tayi inda yake ba tare da tayi magana ba, ganin tsayuwar bamai k'arewa bace ga marece na k'ara yi yasa yace "a haka zaki nunan garin muna tafe kamar kurame? Idan ba zakiyi magana ba mu koma kawai" ya fad'a tare da had'a rai.

Rau-rau tayi da ido tare da turo baki "yo ai Kaina baka dariya, sai had'e huska, ni tsoronka nake".

Dariya sosai ta bashi yanayin yadda take maganar, aiko dariya yayi hadda tafa hannu, itakam tsuru tayi tana kallonsa, saida yayi mai isarsa sannan yace.

"Wama sunanki"?

" Laure" ta fad'a a tak'aice.

"Aa ba shine sunanki ba, ni bazan ringa kiran ki dashi Wanda Ardo ke kiranki dashi nike nufi".

Saida tayi murmushi dan ita Kanta tafison sunan " Ramlatuna " ta fad'a.

Shima murmushi yayi yace "yawwa shi amma Ramlah luv zan ringa kiranki kinaso ko?"

D'aga masa kai tayi dan ita batasan me luv din yake nufi ba "yawwa zamu zama abokai daga yau kin yarda?"

Namma kai ta d'aga mishi "daga yau mun zama friend zakina ringa bani labari?"

"Au wallah zan baka, badai kanaso ba?"

"Inaso sosai".


Haka suka tafi suna hira tana ta bashi labarai barkatai shidai biye mata kawai yakeyi duk inda sukaje tana masa bayanin gurin, aiko yasha labarai sai mamaki yake Ashe haka take da surutu, ada bayason mutum mai surutu shiyasa yake kwaban Nihal saboda itama akwai surutu, amma surutun Laure burgesa yayi duk da kuwa mafi yawa duk shirme ne sa soki burutsu.

Sai ana daf da magarib suka dawo ransa fal farinciki ji yake kamar kada su rabu, shikam Allah ya d'ora masa k'aunar Ramlah, anan yayi magrib tare da Ardo bayan sun dawo ya wuce, yana tafe yana tuk'i tunaninta kawai yakeyi yana murmushi a gaskiya dole ya sanya ranar yau a cikin tarihinsa dan babbace a gurin sa yayi enjoyed nata ba kad'an ba....


Sannu-sannu shak'uwa mai k'arfi ta shiga a tsakaninsu duk da har yanzu Ramlah batasan meye so ba, amma tanijin da Abdool a ranta. Duk k'arshen sati yake zuwa, suje su zaga gari daga nan su dire rafi, inda yake koya mata kara2, dayake tw bashi labarin tayi primary har 4 iya Hari ta fidda ita, zuwa yanzu ba abinda bai Sani ba game da ita da irin musgunawar da Iya Hari take mata, yanajin tausayinta sosai k'aramar yarinya da ita amma tasan wahalar rayuwa, duk abinnan da akeyi Jauro baida labari, saboda irin ranar bai zama gari suna jeji gurin farauta (kome zai faru idan ya sani? Allah masani).

Iya Hari kuwa cewa tayi dama daga ganin wannan likitan dan iskane yana fama da gilashi awa dan daudu, yazo yaba malam kud'i ya saida mutunci jikarsa, sannan tace "yo dama ai zani ce ta cimma muje dama can tsohuwar sana'arta ce" duk ta yadda ta yadda ta debo musu ciki saidai suk'arasa ita da makwad'aicin kakanta.

Haka taita sakin magana ba dad'in ji, sudai kunnensu kawai suka dad'e, suka barta da Allahu.

B'angaren Zainab kuwa ta d'age da gayawa Allah buk'atarta ba dare, ba rana, shikam Abdool tausayi take nashi, dan yasan dafin so, shiyasa yake d'an sake mata fuska kota samu sassauci (Allah sarki Zee, ba komai kina tare da Allah.)...........
.







=؄?Meryerm Abdool=؄?
[7/20, 9:59 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?


=?-?=?-? *kulli nafsin za'ik'atil maut(each and every soul should test d bitter of dead) may ur gentle soul rest in perfect peace, may jannatil firdous be ur final home sisto Hauwa'u (Aunty 'yar gande) may Allah bless ur children's, Ameen=?O?





=??? *Episode* 56--60






Kwatsam aka samu wani munafiki ya gayama Jauro, aiko kuzo kuga kunfar baki, kaman yayi hauka wai Laure da wani, gidansu yayi sa'a kuwa Ardo bayanan, nan ya hau Iya Hari da masefa ai duk laifinta ne da take bari tana fita amma zaiyi maganin ko wane shegen ne.

Bud'ar bakinta sai cewa tayi "Yo ai ba laihinshi naba, ita ka biye mai kuma ai da sanin malam shiya d'aure Musu gindi wainan gari taka nuna mai."

Cikin muryan 'yan tasha "wai wane d'an kazar uba ne?"

"Hehehe likitan Malam na, yana kawo musu mai dad'i da mask'i ai dole baki ya mutu(kamar bada ita ake ci ba).

" to nidai ko shi'a asibiti ba likita ba billahillazi

4 / 30