Author : Hadiza D. Auta Category : New Hausa Novels 2026
ba.
Sai kawai na daga kai tabbacin eh.
Ya ce "Ikon Allah ban yi zaton akwai lokacin da zaki ce soyayyar da kika wanzu kina yi masa zata zama ta kuruciya ce ba. Lallai yau na sake fahimtar al'amarin mata da kuma kuruciya babban al'amari ne da ba zaka ganesu ta dad'in rai ba."
Abida ta sake ce wa "Kasan tun akan auren da Yaya Faruku ya yi na karaya da lamarin Bilki. Domin ranar da muka dawo ta samu labarin ya yi aure kukan da ta yi ba kad'an ba ne. Sannan sai wanccan term din fa ta yarda suka shirya take kula shi. Gabadaya boye masa take yi. Shima sai da sharadin ita ba budurwasa ba ce"
Yaya Asad ya saki gauron numfashi ya ce "Allah ya kyauta. Amma dai ki dage da karatu, kar ki yarda ki jefa kanki a cikin had'arin soyayya. Idan kika yi Ilimi maza da yawa zasu so ki kala kala. Sai ki ga har da manyan mutane masu rik'e da mukamai daban daban ko manyan Alhazai y'an kasuwa".
Abida ta sake ce wa "God forbid auren d'an kasuwa, basu iya komai ba sai ra'ayin ruk'au, da dunkufe cigaban mace".
Cikin kaduwa ya ce "Autar Momi gaskiya kin kerewa tunanina, wato saboda kun girma ba'a gabana ba ya sanya giggiwar ki ta yi yawa ko?
Ki tabbatar a gidana zaki yi karatun ki na jami'a, na ga alama sai na sake sanya ido akan ki k'warai da gaske."
Yana rufe baki ta yi maza ta ce "Haba Yaya ai idan sallar daren da nake yi akan Baba ta karbu ai abroad zan wuce na yi karatuna. Sola zaka dauka ka saka mata ido tun bata daukowa kanta mijin kara da kiyashi ba".
Kan dole ya yi shiru yana mamakin yadda k'ananun yara suka girma tashi guda. Ya numfasa yana tuna shekarar haihuwarsu ya kammala karamar sakandire.
Har suka k'arasa garin Bakori bai bar mamakin wayewar da ya gani tare da Abida ba. Haka nan shiru shirun Bilki da yake ganin ya yi mata yawa tun tana k'arama ya fahimci ya bita har kan girmanta da alamun rashin wayo a tare da ita, amma kuma ya fahimci tana cikin mata masu tsananta soyayya masu tsananin kishi. Wanda hakan alamun mace na cikin kalubalen fad'awar gararin rayuwa. Domin abubuwane guda biyu da mace ba zata iya tsallakewa ba. Na farko soyayya ta zama mahadi ne na rayuwar kowanne bil-adama har ma da wasu halittun irinsu jinnu da dabbobi.
Sannan kuma kishi shima wani gini ne da ba zai yiwu mace ta rushe shi daga jikinta ba.
Shi a yanzu da yake da shekaru shida da aure matarsa bata huta da saka masa ido ba, bata hutar da zuciyarta zullumin kada ya so wata ko ya kula wata macen ba. Duk da babu wata k'ofar da ta ga ni na ce wa yana soyayya da wata macen. Shi a karan kansa ya k'yamaci polygamy domin yana kallon artabun da ake yi a tsakanin yan'uwan da suka fito daga mabanbanta iyaye mata. Mahaifi kuwa kullum a cikin zargin yafi karkata a wani bangare yake, mafi yawa iyaye mazan da suke da mabanbanta iyalai sun fi saurin tsufa da gajiyawa sabida tsananin zullumi da fargabar yadda ahalinsu suke a wargaje.
Bayan hakan y'aya'n kullum a cikin artabu suke da matan uban, haka matan uba a cikin dauki ba dad'i ake da su akan y'aya'n da ba nasu ba. Wadannan dalilan ya sanya ya k'i polygamy ya k'udire mace guda ta ishe shi rayuwa kamar yadda ya taso ya ga iyayensa maza da mata guda guda. Shiyasa zumunci da soyayyar gidansu ta sha banban da ta kowanne ahali.
Amma matarsa bata gane hakan ba, kullum cikin tsanantawa kanta take, har fad'i take yi, jikinta na fad'a mata kamar watarana zai samo yarinya sa'ar Aysha d'iyarta ta farko ya aura. Da haka gara ya yi yanzu ba sai ta tsufa ya dauko mata yarinyar da zata zo ta rainata ta hanata sakat a gidanta, saboda tak'amar tana gamsar da miji da kuruciyarta ba. A duk sadda take irin wadannan kalaman dariya yake yi tare da ce wa "K'arin aure ai zuwa yake yi, idan an k'addara mini zan k'ara da kaina ne zan fad'a miki. Ki daina tayar da hankalinki akan abin da yake gaibu ne".
Amma a k'asan ransa baya da ko sha'awar ya k'ara din, amma bai san me yasa tsayin Bilki ya yi masa ba, yadda take a tsaye cak, mai fadadden k'ugu zata dace da matar jarumin d'ansanda irinsa.
Sai dai kuma yana ganin yarinyace k'ankanuwa da bai kamata ya bijiro da wannan maganar a tsakaninsu ba, mussaman da yake ganin Faruku yafi shi cancantar ya yi amarya da ita.
Daidai lokacin ya isa cikin harabar babbar makarantar gwamnatin tarayya ta Bakori.
Ya tayamu sauke kayanmu, ya damkawa kowacce sabbin y'an d'ari biyu guda goma, dubu biyu d'aya ke nan, wanda a wanccan lokacin dubu biyu kudi ne mai auki.
Ya mana nasihar mu kame daga k'awayen banza, mu kuma dage mu fito da result mai kyau ta yadda zamu samu gurbin shiga makarantar gaba.
Muka yi masa godiya, ya ja motar ya tafi.
Yana fita, motar gidansu Basma ta shigo. Muka rungume juna da ihun murna. Tare muka biya leburori suka kwashe mana kayanmu zuwa hostel.
Daren ranar bana mantawa da shi domin da k'yar barci ya sure ni. Ba komai ya hana ni sukuni ba, illah yadda na ga mutanen gidanmu sun gasgata soyayya muke yi ta gaske da Yaya Faruku. A farkon kam lokacin da ba ni da wayo ina sonsa, da na shiga sakandire na gane soyayya tabbas ina jin sonsa har raina duk da shi zolayarsa ba zata bari a gane gaskiyar alqiblarsa ba. Haka dai muke tafiya a shine saurayina, domin duk sadda zan hakaito saurayina a duniya to Yaya Faruku ke zuwa mini, komai da komai nasa yana burge ni. Amma daga lokacin da ya yi aure na ji a duniya na tsani ko kallonsa na yi. A yanzu da nake yin hankali sai na fahimci ba sonsa nake yi da aure ba, kawai shakuwa ce, da kuma yadda yake girmama lamarina, shiyasa zuciyata ta bashi wani babban matsayi da ya zarce kowa a gidanmu har yan'uwana da muke ciki guda kuwa.
Amma tsakanina da Allah an jarrabe ni da ƙin auren zumunci. Ba dan komai ba ni dai a tsarina ne bana so, ban ga kuma wadda zan iya aura ba cikin ƴaƴan Baba Babba. Ko Yaya Usman da na ga take taken cewa zai yi yana sona tunda Faruku ya yi aure, nan da nan na canja masa fuska ko gaishe shi na daina yi, dan kada ma ya samu fuskar tunkarata ko bayyana maganar. Da ya fahimci bana ra'ayinsa ko kadan sai ya haƙura cikin salin alin.
Baki da baki Baba ƙarami ya nuna mini yana son ya bawa Yaya Usman aurena da zarar na kammala sakandire, bayan auren na cigaba da karatuna a dakina.
Ban ji nauyi ko shakku ba na ce "Baba bana sonsa, na ro'ke ka kada ka furta wannan kudirin naka wani ya ji".
A sanyaye ya ce "Ba zan miki auren dole ba, Allah ya had'aku da abokan arzikinku daga ke har shi. Na rufe magana tunda dama shi bai fad'a mini ba, amma nasan tabbas yana sonki, duk da yana iyakacin k'ok'arinsa wajen dannewa tunda bai ga fuska a wajen ki ba."
Na bata rai na ce "Na rufe k'ofar da zai furta, Yaya Faruku kad'ai zan iya karba, shima kuwa tunda ya yi aure magana ta k'are da ikon Allah ba zan yi auren zumunci ba. Ina jin tsoron kada zumuntarku mai k'arfi ta shiga tasgado".
Ya yi dariya sosai ya ce "Bilkisu babu yadda za'a yi akan d'ana na bata da d'an-uwana. Kin san kuwa yadda muke son juna da Baba babba? Mu kad'ai mahaifiyarmu ta haifa, kuma bamu tab'a rayuwa ba waje d'aya ba, ban da aikin da nake zuwa Katsina na yi kwanaki bamu tab'a rabuwa ba, domin ko makarantar kwana tare muka yi a Barewa duk da ya zarta ni aji sosai.
Har yau ban haifi d'an da zai shiga tsakaninmu ba, tunda dai ba kya so, to na bar maganar domin Annabi ya ce "Kada mu aurar da ku sai kuna so, sannan yayunki da aka aurar babu wacce muka yiwa tilas, ke ma kuwa ba za'a yi miki ba.
Na kama baki a zuciyata kuwa na ce me ma zaisa na yi tunanin zai iya ce wa yana sona don na fasa yi da Yaya Faruku?
Me zan yi da mutumin da ya ba ni shekaru kusan sha shida.
Da kaina na yiwa kaina dariyar hasashena.
*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*
*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*
*08163761797*
✍️
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: https://wa.me/c/2347020695644
07
*Kun tuna Umm Nihla mai yadinkan Yan gayu da Yabin Bulkacuwa ta yi ta kece raini da su?*
*Tana nan tana kawo muku su zuka zuka, na alfarma, amintattu, akan farashi mai rahusa*
*Malaysianfabricsng*
07020695644.
Kwanaki k'alilan na manta komai na durfafi karatuna. Bana biye wa rashin karatun Abida domin na riga da na san ba kwanyarmu d'aya ba.
Kwanci tashi muka dawo gida rubuta jamb.
Kwanaki biyu muka yi, muka sake juyawa dan rubuta jarabawar karshe.
Ranar 9 ga watan 9 muka kammala jarabawar karshe wanda ta zama ranar murna da doki hadi kuma da zullumin rabuwa da junanmu.
Ni da Basma sai kuka muke yi, Abida kuwa sai hidimarta take yi wanda Babu alamun kuka ko wata damuwa mai yawa.
Da ta gaji da ganin kukanmu sai kawai ta ce "To ku koma s.s.1 mana."
Basma ta zabura ta ce "To mu koma tare y'ar sarkin BAK'AR TA'ADAR cabawa mutane magana."
A banzance Abida ta ce "To na gaji da kukan munanfincinku. Haba da munsan junanmu? Allah ya had'amu, dukkanmu kuma munsan adadin zaman da zamu yi mu koma inda muka fito. Da lokacin ya yi muna da ranmu da lafiyarmu mai ya kamata mu yi?"
Ba wacce ta tanka mata. Ta numfasa ta ce "Sai mu yi fatan duk inda rayuwa zata kaimu mu kasance cikin aminci, ya kuma bamu sa'ar samun sakamako mai kyau. Mu da muka yi sa'a ma daga jaha d'aya muke, duk runtsi zamu dinga haduwa."
Jikinmu ya yi sanyi domin bamu yi zaton Abida zata sauko ta yi magana cikin kwanciyar hankali haka ba.
Basma aka fara zuwa d'auka. Har jikin motar na bita tamkar ba zamu rabu ba. Da k'yar muka bari direban ya ja suka tafi.
Abida tana daga kan akwatin kayanta ta ce "Ni fa Bilki na gaji da wannan kusancin naku da Basma. Ban son na ga mutane sun cika dagewa k'awance irin haka. Wallahi da bamu yi kandi ba sai na saka an bibiyeku haba wannan makalewar da kuke yiwa juna ta yi yawa "
Duk yadda na ji haushin kalamanta haka na daure na guntse baki ban tanka mata ba.
Domin na sani nice a ruwa, saboda ta fini harshen zaro magana.
Ilai kuwa ta kaikace ta ce "Da ni ce ke, murna zan yi, zan bar wajen da ake ce mini sola. Ke gabad'aya wata iri ce Bilki, har rasa ajin da zan saki ki nake yi."
Na sake matsewa ban ce komai ba.
Ita kuma ta kasa hak'uri ta sake fad'in "Wannan shiru shirun naki da kuttu yake sola."
Ko motsi mai k'arfi na ƙi yi, balle na biye ta. Kan dole itama ta kame bakinta domin tasan ba kulata zan yi ba.
Tsawon lokaci muna zaune jugum jugum sai na ji ta ce "Wato Bilki kina da hak'uri, kina da gudun mu yi faɗa. Albarkacin baƙin cikin da nake ta nausa miki idan na haihu zan ba ki abin da na haifa dan ki ta tunawa da ƙuruciyarmu da yadda nake miki sababi amma ki jure, kina sona na shaida, nima kuma ina sonki fiye da Yaya Munira da Yaya Faruƙu ".
Hawaye ya zubo mini na ce "Na gode sosai Abida, idan kuma Allah yasa kika ba ni ɗin wani a duniya ba zai ji ba ni na haifa a bakina ba, ba zan taɓa nuna banbanci da wadanda na haifa ba."
Ta matso kusa da ni tana share mini hawayen da yaƙi tsayawa ba tare da na shirya faruwar hakan ba.
Da ƙyar na yi jarumtar shanyen kukan na ƙaƙalo murmushi na ce "Amma so nake ki soni fiye da Yaya Asad".
Ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "Ban iya ƙarya ba, ban iya yaudara ba, ban so wani cikin yan'uwana sama da shi ba. Dan haka ki yi haƙuri kawai Bilki".
Na dara kaɗan na ce "Na yi hak'uri Abidan Baba".
Ba jimawa Yaya Faruku ya zo, shi ya zuba kayan a but bayan mun je ya karbo mana pass din tafiya.
Na kasa sakewa na nuna masa farincikina na kammala sakandire, bare na bashi labarin abubuwan da suka faru.
Gabaɗaya alhinin rabuwa da class mate ya taɓa ni. Sannan Abida ta yi matuƙar sanyaya mini zuciyata da gangar jikina gabadaya. Haka nan sai nake ganin tamkar akwai wata ƙaddara da take ɗamfare a tsakaninmu. Tunanina ya tsananta, da na ga lallai ba fahimtar komai zan yi ba,sai kawai na hau yin istigifari.
Kan dole Yaya Faruku ya haƙura da rashin kuzarina, haka Abidan ma bata da karsashi kamar yadda ya santa da guntsi fesa. Da tuni ta ishe shi ya sayi jaridarta. Shi kuma da hanzari yake siya domin yasan mafi yawa labaran jaridarta nawa ne.
Baba ƙarami muka tarar a harabar gidan yana dakon isowarmu
a dalilin Baba babba ya je Lagos taron da gwamnatin tarayya ta shiryawa masu samar da Madara a ƙasa.
Ya karbemu da murna.
Muka tsugunna a gabansa muna gaishe shi domin shi din ba shi da haba haba irin baba Babba.
Ya amsa cikin sakin fuska tare da yi mana fatan alheri a cikin kammala karatun da muka yi.
Ya kuma ce "Yanzu ne zaku fara gwagwamarya da rayuwa, na roki kada ƙalubalen rashin samun abin da ake so ya sanya ku canja kyawawan ɗab'iunku, sannan duk inda rayuwa zata kai ku to ku zama wakilan addini musulunci da Hausa Fulani na gari abin koyi".
Murya babu amo muka ce "In Sha Allah Baba!
Kaitsaye sashenmu muka dosa domin kuwa mun riga mun san Baba babba baya tab'a yarda ya yi tafiyar da yasan zai wuce kwana biyu ba tare da rakiyar Momi ba.
Gabadaya Baba babba bature ne. Ma'ana a bayyane yake nuna soyayya ga ahalinsa. Baya yarda da al'adun bahaushe akan sha'anin aurensa. Duk inda zashi momi na gefensa. Amma Baba k'arami kuwa shine asalin d'an gargajiya gabadaya irin wannan rayuwar bata dame shi ba. Ga shi har digirin digir gir ya yi.
**
A wannan shekarar muka samu gurbin karatu.
Dukkanmu a A.B.U Zaria. Abida ta samu nasarar samun MBBS din ma'ana burinta na zama likata zai tabbata.
Yayin da ni na samu Nutrition and dietetics. A wanccan lokacin ban so kwas din ba, domin ba shine zabina ba, amma na hak'ura tare da fatan ya zame mini alheri, tunda ba zai yiwu na ce zan sake neman wani kwas ba.
Basma ma ta samu nasarar shiga jami'ar sai dai ita jami'ar Bayero ta samu, inda zata karanci lab science.
Baba k'arami tare da Baba Babba suka kaimu har cikin makaranta, bayan nasiha da jan kunne iri iri.
Ba abin da ya tsaya mini irin yadda Baba k'arami ya fito da al'amarin da yake ciwa iyayen yau tuwo a kwarya.
Da kakkauran murya ya ce "Tunda kuka iso duniya bamu huta da hidimarku ta kowanne bigire ba, har zuwa yau dinnan bamu huta da dawainiyarku ba, ba kuma mu tab'a gazawa ba. Bayan hidimar da muke yi muku da aljihunmu da k'arfinmu haka nan bamu tab'a gajiyawa wajen yi muku addu'ar shirya da samun nasarar rayuwa ba.
A yau da zamu kai ku jami'a wajen ka zo na zo, wajen da babu kwaba. Abun da zamu fad'a muku d'aya ne tal. Ubangiji ne wakilinmu akan tarbiyar da muka wanzu muna yi muku, idan kun taimaki kanku kun k'are mana mutunci kun kare naku, to kun tsallake kalubalen rayuwa mai yawa, idan kuwa kun ha'incemu kun watsar da tarbiyar da muka d'oraku a kai, kun jefa rayuwarku cikin garari da tashin hankali hadi da bak'in ciki marar yankewa. Ubangiji kuma zai mana sakayya. Ku kiyaye, ku kiyaye, kada ku kusancin zina bare ta baku sha'awa ku afka mata, masifarta yawa ne da ita, naso take yi.
Kun isa aure duk wacce ta had'u da namijin da ya yi mata, ya nuna zai aure ta ta turo mana shi, zamu aurar da ita babu jinkiri."
Gabaɗaya mun yi laƙwas kunya ta dabaibaye mu domin Baba ƙarami cire kunya ya yi sosai ya ding faɗin "Mun san sha'awa halitta ce, kuma kun kai shekarun da zaku buƙaci namiji amma kuma bata gurbatacciyar hanya ba, kada ku yi sanadin da zamu kunyata mu mutu da baƙin ciki dan Allah."
Nasihar ta yi matukar ratsamu, gabaɗaya kuka muke yi, har Abida da ta fini taurin zuciya.
Sun jima tare da mu a makarantar tare da Yaya Munira da a lokacin ta shiga ajin ƙarshe inda take karantar (Law) shari'a kevnan.
Haka suka barmu cikin jan kunne da nasiha iri iri.
Ba bangarenmu ɗakunan kwananmu ɗaya da yaya Munira ba.
Amma muna haduwa akai akai, yayin da muke ɗaki ɗaya da Abida haka abincinmu a haɗe tamkar muna F.G.C Bakori.
Sannu a hankali muke karatun har muka cinye shekarar farko. Yaya Munira ta kammala cikin nasara. Mun yi kewar rashinta a kusa da mu, domin sosai take yi mana alheri da saka ido a kanmu.
Cikin sa'a a wannan shekarar jamiar zata yi bikin yaye dubban ɗalibai(convacation).
Sosai muke ɗoki da murnar yaya Munira na cikin waɗanɗa suka yi sa'a baza su yi dogon zama kafin a yi bikin ba.
Kusan kowa ahalin gidanmu ya halarci bikin inka dauke Yaya Asad da bai