Author : Preety Sk Category : New Hausa Novels 2026
akan wannan ne ta hora kanta da yunwa.” Mom ta faɗa sai A'isha ta ce.
“Kunsan halinta ai, akwai sa abu a rai, Allah dai ya ƙyauta, duk da ɗaga wa mutane hankali a banza.” A'ishah ta faɗa tana nufan Kitchen dan haɗa ma kanta abinci, ita haka Allah ya yi ta, tun tana ƙarama in aka dafa abu aka ba ta ba ta ci sai dai in Mom ta yi, tana ƙara girma kuwa ita ke girka ma kanta abinci, haka take ko ina ta je ba ta cin abu sai in da ita aka yi making.
Ina shiga room ɗina na daka wani tsalle sai gaba mirrow, dariyar ce ta ƙwace min, ai kuwa nai ta yi kaman mahaukaciya, sannan na ce.
“Hmmm ai ƙwanciyar hankalinku shine ku turani *Lagos State University College of Medicine (LASUCOM)* Hahahahahah ga ni ga NOLLYWOOD...... Sai ni ƳAR NOLLYWOOD insha Allah.” na faɗa ina sumbatar kai na ta mudubi.
Ni fa tun ainiyi *HOLLYWOOD* shi nake so, amma nasan ba zan samu daman zuwa U.S ba balle na shiga *HOLLYWOOD* har na yi Film, sai kawai buri na ya dawo *NOLLYWOOD* kuma insha Allah ko Film ɗaya ne sai na yi.
_______Aisha complex ta haɗa, anan ta sha dan ita ba wani abinci take ci sosai ba, tana gamawa ta koma room ɗin ta, a al'adance kullum sai ta yi wanka da daddare, sannan ta yi sallah kafin ta kwanta, haka yau ma bayan ta gama komai ta kwanta, take yau ɗin ta ya faɗo mata, tabbas yau rana ce da ba za ta manta da shi ba.
Jin sautin S.M.S ya sa ta duba, ganin M.D ya mata reply da.
*GOOD NIGHT It’s just been a day that you are gone and already it feels like ages. There’s no reason left to wake up in the morning, please come back soon. Thank you so much Eeshert.*
Murmushi ta yi sannan ta kalla wanda ta tura mai.
*Hello! My name is Night. I came here to kidnap your stress; Kill your strain. My weapon is deep sleep and my path is Sweet Dream. So please kindly co-operate and handover yourself! Good Night My.....*.
Murmushi ta kuma yi sannan ta lumshe idanunta, tana hasasho fuskar Ayan, ƙyaƙyƙyawan sauri mai Capacity. take barci ya ɗauke ta cike da zazzafan soyayyar Ayan........................✍️
END
> Ƴar NOLLYWOOD 🙆🙆🙆 Inayah gagara kowa kenan, hmmm ko ya za ta kasance......????
> Ba ku yi comments da Likes shi yasa Update yake zuwa a haka.
Na so kuban haɗin kai da a 2week za mu kammala........😏😏😏.
#LIKES👍
#SHARE😁
#COMMENTS🥰👌
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
🕊️ *May Allah keep us united, uplift us, and make our pens a means of positive change.*
Much love and respect to each and every one of you. ❤️🔥
*Keep shining, JAW family!* 🌺
*JARUMAI WRITER'S TEAM📚✍️*
𝒀𝒂𝒓 𝑵𝒐𝒍𝒍𝒚𝒘𝒐𝒐𝒅
Story and writing✍️
```PRETTY SK```
~SAKINA ABDULLAHI~
> *PRETTYN JAJIRTATTU 💪✍️
✽»≿━༺🌹﷽🌹༻━≾»✽
E.P1️⃣1️⃣⏩1️⃣2️⃣
*BAYAN WATA BIYU*
A'isha ta ƙara shiga tafkin soyayyar Yaya Ayan, ba shi kulawa take kamar me, wasa-wasa shima yake kulata sosai, amma har zuwa lokacin ba ya jinta a zuciyarsa, sai dai yana so ya aureta ɗan abu biyu, na farko da soyayyar da take mai, na biyu ko dan ya kauce ma auren Ruma.
*GIƊAƊO MANSION*
____________Gaba ɗaya sun yi shuru suna sauraran Baba Musa dake tsaida lokacin auren su, su 8, an sanya nan da wata biyar ne kacal. Ayan dake kallon iyayen nasa rai a haɗe ya ce.
“Baba ina da magana.”
“Ayan ina jikin ka, yarona.” Sai da ya sosa kansa sannan ya saci kallon kowa ganin yarda suke binshi da ido, dakewa ya yi sannan ya ce.
“Kunfi kowa sani cewa banson Ruma...........wallahi banson ta da aure, sai dai ina sonta a matsayin ƙanwa, Ni ina da wacce na yi ma alƙawarin aure.” ya kai nan yana shirin miƙewa da sauri Baba Yusuf ya mai da shi ya zauna.
Idan ransu ya yi dubu ya ɓaci, balle ma Ruma da Mahaifiyarta.
“Me ka ce?.” baba Yusuf ya tambaya ransa a haɗe.
“Akwai wacce na yi ma.......” wani sanyayyar mari ya ji Abba ya sauke mai a kuncinsa.
“Kar ka mai da mu mutanen banza, wallahi idan na kuma jin irin wannan furucin a bakinka sai na saɓa maka. So kake mu yi watsi da wasiyyar mahaifin mu ko ya ya?.” ya kai nan yana ɗan huci.
Ayan dake dafe da wajen, ya ɗan yi murmushi sannan ya miƙe tsaye.
“Shike nan, amma idan har wani abu ya bayya wa ƴan jaridu, kune sila, ina so na kare mutuncin gidan nan ne, amma tunda haka kuka ce shike nan.” da haka ya miƙe, yana musu kwarjini sosai, babu wanda ya dakatar da shi har ya fita, kowa cikin maimaita maganarsa suke yi dan kuwa babu abin da suka fahimta.
Sun dai riƙe. “Ƴan Jaridu, mutumci."
Babu dai wanda ya yi magana a cikinsu. Ruma kuwa tuni hawaye sun fara gangaro mata masu zafi.....
Cikin wannan takun nasa wanda kai ka ce sarki ne ko shugaban ƙasa, haka yake taku ƙasa na amsawa.
Direct motarsa ya nufa sannan ya bar gidan, yau Sunday Babu school dan haka ya nufa gidansu Aisha wacce ta yi mai kwantan ce.
A bakin get ɗin gidan su ya yi parking, sannan ya kira wayarta.
“Ina ƙofar gida."
“Okay ganin zuwa.” ta furta, da haka ya aje wayar yana ji kamar an yi mata abu dan yarda ta yi maganar kaman ranta na ɓa ce.
Ilai sai ga ta fito fuskarta babu annuri duk da suprice ɗin da ya yi mata na zuwa babu notice.
Ta yi ƙyau cikin dogon Blue Black na hijab har ƙasa, fuskarta babu komai dan be ta ɓa ganin ta yi makeup ba.
Ba yarda ta iya ko dan rana ma sai ta shiga motar tana sallama, murmushi ya saki kafin ya amsa.
“Aisha bazata na miki amma naga kina cikin damuwa meya faru?.” ya tambaya yana jin babu daɗi da ganinta a haka.
Kai ta girgiza mai.
“No faɗa min dai kin ji.” sai ta saki ranta dan dai komai ya wuce.
“Yaya Ayan ba komai walla...........” da sauri ta tsaida da maganar sakamakon ya sanya hannunsa ya kulle mata baki.
“Shhhhhh. Magana na zo mu yi mai muhimmanci amma idan ba ki faɗa min abin da aka miki ba, wallahi ba zan faɗa ba, kuma sai na.....”
“Shike nan zan faɗa maka.” ta faɗa tana gyara zamanta, shi kuma ya zuba mata fararen idanunsa akanta.
“Shalele ce.” sai ya yi murmushi, be ta ɓa ganin Shalele ba amma yasan akwaita da rashin ji, babu rana da za ta wuce ba tare da ta ɓata ma A'isha rai ba.
“Nikam wannan Shalelen duk randa na ganta sai na sa an rataye min ita, tana takura miki da yawa, me ma ta yi miki?.” murmushi ta ɗan yi sannan ta ce.
“Yau Sunday tana gida, wallahi tun asuba ta fara damuna, yanzu ta mun abu jima haka ta yi wani, kuma ban da ikon mata magana yanzu sai Mom ta ce *ina takura mata* kalla yarda ta fasamin yawa, wallahi da ganganga ta yarda shi, da na yi mata magana sai ta hau kuka wai natseta, shine ta faɗa ma Mom, sai Mom.................”
“Yi shuru na fahimta.” ya katseta dan kuwa gab take da yin kuka, a zamansu abu abu ya sani dangane da A'isha shine saurin Fushi ga ɗaukan abu da zafi.
“Zan siya miki waya shike nan.”
“A'a na gode, ai tsaga ne kawai.” ta faɗa tana kallon wayar da ya fashe sosai, har ya taɓa screen ya yi baƙi gefe ɗaya.
“Gobe insha Allah zan tawo miki da waya. Yanzu dai babban magana ne ya kawo ni.” sai ta mai da hankalinta a kansa.
“Aisha.” ya faɗa cike da rauni mai haɗe da taushi.
“Na'am.”
“Nasan kina sona sosai, balle a yanzu da nake baki lokaci na, sai dai aure tsakanin mu abu ne mai wahala saboda wata *WASIYYA* ”
Take ya ba ta taƙaitaccen labarin *Giɗaɗo Family* tare da abin da aka yanke a gidansu yanzu.
Wani abu ta ji ya doki zuciyarta, ta sauri ta rintse idanunta tana maimaita duk abin da yace.
“Yanzu......a...a...aure za ka yi?." Sai ya yi murmushi.
“Nasan za ki ce me yasa na miki haka. Me yasa na fara kulaki ko?.” sai ta ɗaga mai kai.
“Ni kaina banson auren.........uhmmmmmm ina da shawara amma yana da wahala sosai, in ɗai za ki iya to aure tsakanina da ke kamar an yi.” buɗe dara-daran idanunta ta yi tana kallonsa kamar yarda yake kallonta.
“Akwai wahala.” ya sake faɗa kamar mai raɗa.
“Koma menene shi zan yi muddin zamu yi aure.” ta faɗa tana jin zafi a ranta har lokacin.
“Gidan mu suna da abu guda ɗaya, idan har akan mutumcin gida ne to za su iya komai dan ganin be zuba ba, nasan kunsan familyn sosai ko da a labarai, to akwai son riƙe mutuminci.............yanzu mu mafita ɗaya ne tak mutumcin Familyn zamu yi ƙoƙarin mu ta ɓa, idan muka musu bayani to za su yarda.”
“Bangane ba Yaya Ayan.” sai ya ja dogon numfashi sannan ya ce.
“Uhmmmmm........Mu'aluma matar da miji kafin aure.” zaro idanuwanta ta yi dan jin furucinsa, dan kuwa ba ta yi tsammanin jin haka daga bakin sa ba, kai ta fara girgiza mai hawaye na gangarowa daga idanunta sannan zuciyarta ta tsananta bugu cikin sauri-sauri........................✍️
END.
> Duk wasan yara muke, har yanzu ba mu shiga labarin ba.
Kar a manta Like 👍 and Comment. Ngd SOSAI.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
🕊️ *May Allah keep us united, uplift us, and make our pens a means of positive change.*
Much love and respect to each and every one of you. ❤️🔥
*Keep shining, JAW family!* 🌺
*JARUMAI WRITER'S TEAM📚✍️*
𝒀𝒂𝒓 𝑵𝒐𝒍𝒍𝒚𝒘𝒐𝒐𝒅
Story and writing✍️
```PRETTY SK```
~SAKINA ABDULLAHI~
> *PRETTYN JAJIRTATTU 💪✍️
✽»≿━༺🌹﷽🌹༻━≾»✽
E.P1️⃣3⃣⏩1️⃣4⃣.
“Na haƙura da auren.......... Wallahi bazan iya wannan abun ba, ai wannan mutumcin harda na wa, da iyayenmu, da yaranmu duk zai zube, a'a......aa....... a'a Gaskiya. ” takai nan ta fashewa da kuka.
Take ya kwashe da dariya, yana dubanta, ganin irin dariyar da yake yi yasa ta kai hannu za ta fita daga cikin motan da sauri ya sa luck.
“Ai sai ki tsaya kiji gaba ɗaya maganar, ke kinsan ina da ilimin addini, ba yarda zan yi na kauce hanya, balle Zina, abu mafi muni. Kawai zamu yi basaja ne akan mun aikata haka, kuma ke kince idan ban aureki ba, za ki faɗa ma duniya saboda kina ɗauke da cikina a yanzu.” zaro idanuwa ta yi tana cewa.
“Innalillah, ta ya zamu yi irin wannan ƙaryan, kai ba ka ganin zai zo da matsala?.”
“Ko ɗaya, ai maganar daga familyna zuwa kanmu ne kawai, nasan yarda suke son mutumcin kansu ba za su bari hakan ta faru ba, dan sun san waye Mahaifinki, abokin kasuwancin sune.” jinjina kai ta yi tana maimaita abinda ya ce, tabbas a baki ya ya sauƙin faɗa, amma kuwa yana da girma fiye da a mai da shi abun wasa.
“Za ka fuskanci matsala sosai kuma nima haka idan na shiga gidan na ku haka.” ta faɗa bayan kukan na ta ya tsaya.
Iska ya furzar daga bakinsa sannan ya ce.
“Na sani, kuma nasan sharaɗin ɗaya ne, dole su aura min Ruma.” shuru ya yi, itama haka sai can ta katse shurun da cewa.
“Hmmmmmm da in rasaka gaba ɗaya ƙwanda mu yi hakan kuma zan iya rayuwa da ita Ruma ɗin. Duk da ina da zafin kishi.” sai ta share hawayenta.
“Yi min bayanin yarda tsarin yake.” ta kuma faɗa, with confidence.
Murmushi ya yi sannan take ya koro mata yarda ya tsara, dan kuwa wannan tsarin na sa tun kafin ya fara sake mata ya yi shi.
Ita dai jin yarda ya koro zancen ne ya bata mamaki, kaman wanda ya shekara yana tsara plane.
Bayan ta fahimta ne suka canza hira zuwa na soyayya.
*Inayah*
___________Tsaki na ja, ina ganin ai A'isha ta jima da fita, gashi a waje ne balle in ce tana cikin gidan nan, duk na bi na damu, kallon Mom na yi dake cin abinci.
“Mom zan leƙa na dubota, karfa a ce sace ta aka yi, mu muna nan zaune” na faɗa ina nuna damuwa.
“Kin iya neman rigima ne ai, amma je ki.........” ai ba ta ƙarasa ba na yi waje da sauri.
Tabbas ina da neman magana dan kuwa yau tun safe nake ɓata ma A'isha rai, sai dai ba da gangan na fasa mata wayaba bisa tsautsayi ne amma A'isha ta wani hau min masifa.
Me gadi na ganina ya washe baki yana cewa.
“Shalele ina zuwa?.”
“Baba Rabe duba Aunty zan yi kar a sace ta.” murmushi ya yi yana miƙewa.
“Zauna ai ba fita zan yi ba, leƙawa zanyi.” sai ya zauna yana kai Radio wajen kunninsa.
“To shalele.” ya faɗa yana lumshe idanunsa.
Ta saƙon get na leƙa, wata arniyar mota na gani, kafin na yi wani yinƙuri har A'isha ta fito ta ɗayan ɓangaren.
Ɓangaren dake gefana na ga an buɗe shima, take na ji abu na min yawo a ƙafata, da sauri na kalla a ɗan tsorace dan ma ban saki ihu ba, ashe igiyar riga nane, tsaki na kuma ja, ina mai da idanuwana wajen.
Wani dogon namiji na gaji cikin manyan kaya har da hula, yana da faɗi sosai, kaman wanda ke ɗaga ƙarfe, ban ga fuskansa ba dan haka na taɓe ƙaramin bakina.
A gaban A'isha ya tsaya yana goge mata fuska, da wani abu wanda ban tantance menene ba, sannan yana yi mata magana, wanda ban jin komai.
Kallon rigar na wa na kuma yi ina jin kaman na yi dambe da rigar saboda ban samu ganin fuskar Saurayin A'isha ba, so nake na ba Mom labarin komai da na gani kuma inason na karanci yanayinsu.
Ƙarar motar ne yasa na mai da idanuna wajen, ashe har ya wuce, ai da mugun gudu na bi bayan ɗakin mu, kamar wacce ta ga mugun abu.
Ta ɗayan ƙofar Kitchen na shiga ina mai da nunfashi kamar wacce aka biyo.
Ina shigowa falo na ƙura ma A'isha ido wacce ke ma Mom magana, dan itama shigowarta kenan.
“Mom wallahi A'isha ta yi kuka, kinsan menene........dukanta ya yi a cikin mota, sannan ya mata kashedi akan dole ta aureshi. Na gaji ai, shine saboda rainin wayau ya fito yana ba ta haƙuri harda share............... ” da sauri Aisha ta janyo Ni kusa da ita, Ita dai Mom ko kallona ba ta yi ba, dan kuwa tasan halina.
Zama A'isha ta yi tana riƙe da ni, zaunar da ni ta yi sannan ta ce.
“Inayah, me yasa kike son ɓata min rai? Me yasa kullum kike sani magana? Ba ki sona ne ko mene, ban fahimta ba kimin bayani?." Ta faɗa cike da raunin da ya sa Mom ta mai da hankalinta akan mu.
“Ki faɗa min.......ina jinki?." Da sauri na miƙe tsaye ina girgiza kai.
“Aisha, ban tsane ki ba............”
“Karya ne Inayah.” ta faɗa tana share hawaye wanda suka zubo mata.
Da sauri na isa gabata ina mai ɗago fuskarta.
*“Ban da ƙannai wanda zan sanya kuka, banda wanda zan duka ya yi kuka...........kawai ina miki wasu abun ne saboda na samu abokin faɗa, ke kuma komai da gaske kike ɗauka...........shine matsalarki............wallahi A'isha Ina miki muguwar soyayya. Na yarda ni ina sanyaki kuka, amma wallahi.......wallahi.......wallahi duk uban da ya sanya ki kuka a rayuwa, bayan ni sai na sa shi shima, duk wanda ya ɓata miki rai wallahi sai na rama miki........koda ko waye, na fita ne dan ga saurayinki, so nake na fahimci waye shi, dan wallahi bazan yarda wani ya sa ki kuka ba................wannan alƙawari na ne duk wanda ya saki kuma sai na rama miki, kisa wannan a kanki............har abada.”*
Da haka ya bar musu falon, cikin zafi-zafi da ɓacin rai na haye stairs, saboda sauri, bibbiyu nake haɗawa.
Da idanu suka bi ni dan kallon yarinya suke min, amma a yanzu sai suka ji maganganuna suna shiga kansu.
Mom ta taso har zuwa in da A'isha take zaune, zama ta yi, da sauri suka rungume juna cikin soyayya.
“Mom wacce irin ƙanwa nake da ita?, sam ba a fahimtar ta, tana da shiga rai ga gundura, wallahi ni kaina ina mugun son Inayah.” ta faɗa wani kukan na kwace mata.
“Mu yi ta mata addu'a kawai, sai kace mai iska. Dama ina faɗa miki duk soyayya ce yasa take ɓa ta miki rai.”
“Hmmmmm Inayah.” Sai Mom ta saketa.
“Akwai in da sanya mutum damuwa ya zama soyayya?."
“To ku na ku haka yake.” sai suka yi murmushi suna ƙara jin soyayyar Inayah har cikin ɓargo da jininsu.............✍️
END.
> Hmmmmm karku manta furucinta dan nan gaba zai ƙara bayyana........a wata siga............
> Ayan da A'isha wannan wani irin ganganci ne, lallaikam.
> Me kuke tunanin zai faru?
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
🕊️ *May Allah keep us united, uplift us, and make our pens a means of positive change.*
Much love and respect to each and every one of you. ❤️🔥
*Keep shining, JAW family!* 🌺
*JARUMAI WRITER'S TEAM📚✍️*
𝒀𝒂𝒓 𝑵𝒐𝒍𝒍𝒚𝒘𝒐𝒐𝒅
Story and writing✍️
```PRETTY SK```
~SAKINA ABDULLAHI~
> *PRETTYN JAJIRTATTU 💪✍️
✽»≿━༺🌹﷽🌹༻━≾»✽
E.P1️⃣5⃣⏩1️⃣6⃣.
______________________________Ina shiga ɗakina na kwanta kan gado, gaba ɗaya na ƙosa result ɗina na waec ya fito, zaman gidan nan duk ya isheni, nasan saura lokacin kaɗan na tafi Legos Wanda da ƙyar Mom ta yarda, Ina fatan komai da na tsara ya yi yarda nake so.
A hankali na kulle idanunwa take wani ɓari na zuciyata ya min tambayar da tunda nake be ta ɓa min ba.
“Inayah.......kina so ki jefa kanki ga halaka, *NOLLYWOOD* ba wajen zuwan mata masu kammun kai bane, tsakani da Allah haka ya dace? Ko karatun islamiya ba ki so, why?.”
Shuru na yi ina maimaita maganar, da sauri na miƙe tsaye sai kuma na nufa jakkanta, takaddun Islamiya na fiddo da su, zan iya cewa na manta rabon da na yi maraja'a.
Na iya Arabic sosai, dan bama yin magana da Hausa a Islamiyya.
Ba laifi na yi karatun sosai, sai da na bi gaba ɗaya takaddun na,