Author : Hafsat C Sodangi Category : New Hausa Novels 2026
ciro daga cikin kwai saboda
laushi da kyau.
Dama gani ba fara ba haka nan ba baka
ba. Kalar jikina ita ce tafi daukar hankali,
amma ba ya ga haka bani.da tsawo sai dai
kuma idan ba tsayuwa kusa dani kayi ba.
46
Zai vi wuya ka gane haka, don kuwa
gabo6ina suna da zubin na dogayen
mutane.
Lubabatu ce tayi sallama ta shigo ta
zauna muna gaisawa tana tambayata
shirye-shiryena, ina yi mata bayani.
Zuwa can ta ce, To ai gaskiya
Hauwa'u ni dai hakuri za kiyi ba zan samu
zuwa ba shi yasa naga da ki ga shiru ban
zo ba gara na gaya mii kawai.
Na ce, Saboda me Luba? Ta ce, TO
Yaya Abdussamad ne ya hana ni ya ce,
idan kuma nazo to zai lauki kwakkwaran
mataki a kaina.
Nayi shiru ina dan tunani a raina na
rasa abin da na yiwa Abdussamad da yake
sa shi yin irin wadannan abubuwan da
yake yi mun a wannan lokacin.
Na ce,To babu komai Luba na gode,
amma kin san wani abu? Ni fa ban san
abinda na yi wa Abdussamad ba, amma
zan shigo gidan naku dan anjima kadan.
47
Ta ce,A'a rabu da shi kawai. Ni na
riga na fahimce shi, shi a tunaninshi
sauraron shi da ki ke yi Jira yake yi ya
gama karatu kuyi aure.
Wanda Umma ma ta gaya mishi ke
mace ce ba tun yanzu ba to bai yarda ba.
Yaushe za'a ce ke kin jira shi, shi da yake
aji uku na Jami'a a yanzu ko bautar kasa
bai je ba, ballantana har ya samu aiki kuyi
aure?
Na ce, "Duk ba haka ba ne ma Luba, ni
bai taba ce mun yana sona ba, mutunci ne
kawai na dauka a tsakani."
Ta ce, "Tabdijam! Ke kenan amma
kowa ya sani."
Bayan tafiyar Luba shiru na yi ina
tunani ban san abinda ya hana ni fahimta
ba sai a yanzu ne nake fahimtar wasu
abubuwan.
To amma koda na gane hakan tun farko
ko kuma ace shi ya gaya mun da kanshi
48
zai yiwu na jira shi? na yi wa kaina
tambayar.
A take kuma na baiwa kaina amsa ba
zai yiwu ba don kuwa a yanzu ma auren
nawa ya dauro ne saboda wasu dalilai.
Da dai ace muna da wadatar da zan yi
karatuna ne ba tare da wata matsala ba to
da sai in ce zan yi ta jiran Abdussamad har
ya yi karatunshi ya gama muyi aure.
Don kuwa wane mutum na ce bana
sonshi dan gaye ne. Duk da iyayenshi ba
masu kudi ba ne Abdussamad dan gata ne.
Haka nan shi ne dan farin namiji a
gidansu. Nayi maza na cire tunaninsu shi
da kanwarshi a cikin raina, na ci gaba da
harkokina, saboda hakan shi yafi mun.
Kayatacciyar walima aka shirya ana
gobe daurin aurena. Babu abin da bai ji ba
a wurin walimar.
Ana cikin walimar ne kuma 'yan uwan
Ango suka iso da La'asar aka farata ba a
gama ba sai gab da sallar Magriba.
49
A wurin su Sadiya nake jin labarin irin
kawataccen kayan auren da aka y1 mun
kamar zan yi dokin gani sai kuma naga to
al ma nawa ne, dokin me kuma.
Na tsaya cewa Ishak ya kawata bikin
nan ma tamkar na bata ne. Nayi kwalliya
iri-iri ba a magana.
Ranar Asabar da aka daura aure aka kai
ni gidan aka watse saboda wadanda suka
zo daga wasu garuruwa da za su koma a
ranar Lahadi don samun damar komawa
wuraren aikin su wadanda suka saura daga
yan biki kawai, yan uwan Umma ne da
yan uwan Babana wadanda a gidanmu
suke.
Na bude idona ina kallon dakin
shiryayyen daki na zamani irin wanda
mafarkina bai taba nuna mun shi a
matsayin nawa ba.
A takaice dai gidan yayi matukar
haduwa daidai da rayuwar 'yan boko. Bani
50
kadai ba nasan Ummana da Babana ma za
Su samu nutsuwa a yanzu.
Naci amarcina yadda ya kamata, abin
ba a cewa komai ga kuma karin nutsuwa
da na samu ta bangaren abinci da kuma
wurin zama sai abin ya hadu ya sani nan
da nan nayi wani irin canzawa, nayi kyau
ba kadan ba.
SKullum idan 'na tashi nake tsab tace
gidana na fara da abincin karyawa wanda
shayi ne da biredi wani lokaci ya ce da
kwai zai ci wani lokacin kuma ya ce da
sauran farfesun dare zai ci.
Kasancewar kusan kullum yana kawo
kaji ko kuma kifi ko nama ya dai danganta
da abin da yake so sannan na fara gyaran
dakin kwanciyarmu wanda kullum na
gyara shi sai na tsaya na kare mishi kallon
saboda sha'awar da yake bani.
Kullum kuma burina Umma tazo ne
taga inda nake kwana amma har yanzu
wajen watana daya shiru bata zo ba.
51
Sai na tsabtace toilet din da ke cikin
bedroom din na kalkale tiles din bango
zuwa na kasa yayi tas, sannan na fito falo.
Nan ma haka kafn na shiga kicin, nan
ma na gyare shi na goge tiles din shi nayi
wanke-wanke na goge cabinet sannan na
fito na wanke tsakar gidan nan tas.
Nasa sandar goge-goge nayi mopping
din ko ina. Bana gajiya saboda yadda yin
hakan yake yi mun dadi a cikin raina.
Bayan duk na gama hakanne sai kuma
na dauko kayanmu da muka cire na wanke
su na goge.
Ban cika yin abinci da rana ba saboda
baya dawowa da rana sai dare, don haka
sai kawai na sha shayi ko dan wani abu
mai sauki sai da daddare ne nake yin girki
Kullum cikin raina dai ina tsara yadda
zan rinka tafiyar da al'amuran gidana ne,
idan na koma Makaranta.
52
A yau kuma nayi nufin yi mishi
maganar tunda idan ba batan lissafi nayi
ba, to ina cikin wata na uku ne da aure.
Sai da na gabatar mishi da abincin shi
shinkafa da miya da salad na ajiye mishi
kunun zaki a gefe, sannan na koma na
zauna na ci gaba da kallon abinda ake yi a TV.
Ishak ba mutum ba ne mai hira zan iya
cewa abinda aurenmu ban sani ba ko da
can kafin auren ban lura na gane hakan ba ne.
Kullum dai idan zai dawo to ka'idarshi
zai yi guzurin Jaridar da zai karanta ta
ranar kafin zuwan shi wurin kwanciya.
Idan kuma ya kwanta ranar ba shi da
bukata ta to zai yi juyawar shi ne ya kalli
bango nima nayi tawa kwanciyar ban
kuma taba daukan hakan a matsayin wata
matsala ba.
Idan kuma ranar sati ne to kuwa haka
zai wuni yana kallon Jaridar shi ta sati,
53
idan kuma yamma tayi to zai fita ba zal
dawo ba sai sha daya ko da rabi idan ya yi
dare kuwa har sha biyun dare.
To zan iya cewa wannan ita ce babbar
matsalata da shi amma nauyinshi ya hana
ni yi mishi magana.
Sai dai maganar Makaranta ta ce a yau
nayi nufin yi mishi magana saboda tafiyar
lokaci.
Saida ya gama cin abincin shi na
kwashe kwanukan sannan na dawo na
zauna can gefe na ce mishi cikin ladabi.
"Don Allah ina so ne nayi maka wata
magana idan ba za ka damu ba." Ya dan
kawar da Jaridarshi daga kan fuskarshi ya
ce, "Uhum ina jin ki."
Na ce, Dama maganar Makaranta ta
nake so nayi maka don yanzu na kai wata
shida bana zuwa kada lokaci ya yi ta
tafiya."
Yayi shiru zuwa wani lokaci da har na
fara gundura da shirun nashi sai da ya
54
daga Jaidar ya ci gaba da dubawa sannan
ne ya ce "Ba yanzu ba."
Na ce, Na'am!" saboda yanayin da
amsar tashi tazo mun. Na ce miki ba
yanzu ko da matsala ne?"
A hankali na ce, "A'a babu." Ya ce,
To madallah." Sannan ya ci gaba da
kallon Jaridarshi. Daki na shiga na kwanta
sai dai na kasa hana kaina kukan da yazo
mun.
Ba yanzu ba sai yaushe? Sai dai ba zai
yiwu nayi mishi irin wannan tambayar ba.
To waye zai tambayan mun shi? Ai sai
daini din don kuwa ni ce nake zaune tare
da shi. Hakan ne yasa ni mikewa daga kan
gadon na fito falon na sake neman wani
wuri na zauna.
Na ce To yaushe ka ke ganin ya dace
kenan na koma Makarantar? Ya janye
Jaridar daga fuskarshi ya zuba mun ido
yana kallona.
55
"Ke! Tashi ki bani wuri, ke kuma
wacece da za ki yi mun titsiye? Shashashar
yarinya kawai.
Wadanda ya zamarwa dole ma ba su
tsaya sun ga kin yi karatun ba ballantana ni."
Mikewa na sake yi na hau gado na
kwanta. Har aka kira assalatu ban runtsa
ba, kuka kawai nake yi kukan sharbe.
Wane irin abu ne kuma haka meke
faruwa ne? Shin me Ishak yake nufi? Na
mike daga kan gadon na nufi bayan gida
nayi wanka sannan na dauro alwala.
Har yanzu barcin shi yake yi cikin
kwanciyar hankali. Nayi sallolina na nafila
raka'a biyu sau uku sannan na zauna na
dan yi karatun Kur'ani.kafin aka fara kiran
sallah.
Lokacinne ya tashi ya shiga bayan gida
yayin da ni kuma na tada sallar nafila ta
raka'atul fijri, sannan nayi sallar asubahi.
56
Na durkusa na gaishe shi kamar yadda
na saba sannan na shiga kicin don kokarin
yin abin karyawa kada ya makara.
Ba tun yauba na sha yin tunanin shiga
gidajen makwabta da muke unguwa daya
da su saboda mu'amalla da Jama'a.
Ban kuma samu damar yin hakan baa
duk kuwa da cewar su sun shigo ba sau
daya ba ba sau biyu ba. Haka nan ma
yayan su.
Baran ma dai Hindu wacce nasan ko
bata gime mun ba to zamu yi sa'a da ita
don a yanzu a SS 2 take kenan da muna
tare a Makaranta.
Don haka ko a yau da nayi nufin na sha
kunun gyada da safe sai na tashi domin na
leka sudaga nan kuma na samu wanda zai
siya mun gyada da kamu.
Ba a yi hanzarin tambayar Ishak ba
amma a a raina sai na kuduri aniyar idan ya
dawo daga wurin aiki sai na sanar da shi.
57
sNa fito na rufe ko'ina na cikin gidan
sannan na nufi gian su Hindu wanda yake
kallon namu gidan nayi kyakkyawan
sallama a tsakar gidan wanda hakan yasa
Momy mahaifiyarsu ta leko.
"A'a'a Amarya ce yau a gidan namu?
To shigo daga ciki mana." Na bita muka
shiga falon na zauna a kasa ta ce "A'a
zauna a kan kujera mana."
Na mike na gyara zamą a kan kujerar
sannan na gaisheta cikin girmamawa ta
amsa tare da yin yar hira kadan wacce
mafi yawancinta kan al'amuran gida ne.
Na ce, Hindu bata nan ko? Ta ce, "Eh
ba su dawo daga Makaranta ba, saboda
tana tsayawa lesson."
Ban. wani tsaya bata lokaci ba na mike
don dawowa gida har kofar gida ta rako ni
da yar leda a hannunta ta miko mun nayi
godiya na nufi gida ina tunanin inda zan
samu abin da na fito nema.
58
Wanda ba zai yiwu kuma na kara yin
gaba ba. Wani abin mamaki shi ne ban
lura na hangi motar Ishak ba sai da nazo
shiga gida.
Wani irin mummunan faduwar gaba ne
ya same ni sai dai kawai sai naga to ai ba
nisa nayi ba sai nayi mishi bayani.
Na shiga dakin cikin murmushi na ce,
Lah ban yi zaton zaka dawo yanzu ba, shi
yasa... " kan na gama maganata ya ce
"Dama idan na fita yawon ki ki ke tafiya?
lye? Inà ki ka je? Na ce miki daga ina ki
ke, kaga mun shegiya 'yar matsiyata.
Raina yayi mummunan baci na ce "A'a
ni kada ka sake zagina ka hada da iyayena,
me nayi da zafi haka?"
Ya ce, "An zage su matsiyata me za ki
yi iye na ce me za ki yi idan an zage su su
din banza su din wofi."
Wannan shi ne na farko kuma na karshe
na gaya miki idan ki ka kuskura ki ka sake
59
ita na dawo gidan nan ba kya nan sai nayi
miki abinda ba ki yi zato ba."
Ya juya ya fita ina jin shi ya sakala
kwado ya rufe gidan ta baya. Na zauna a
wurin nayi kuka irin wanda ban taba yi ba
a rayuwata.
Dama haka auren yake? Na san iyayena
talakawa ne wadanda ba su da komai
amma ba haka yana nufin Ishak ya zage su
ba ne tamkar sun dauke ni sun ba shi ni
auren da ko wata biyar bai yi ba.
Tausayin Babana ya sake kama ni,
mutum mai kokari da bai taba zuwa kofar
gidan wani neman taimako ba, ya dogara
ga Allah ne da kuma dan abinda yáke
samu a wurin aikinsa.
Hakanne yasa mutanen unguwarmu har
da ma su kudin suke matukar girmama shi.
Na lallaba na mike da nufin shiga kicin
nayi girkin abincin dare. Na kuwa samu ya
kawo wani cefanen abinda a yau ya daina
birge ni.
60
Na dauko na fara rarrabawa, ina ajiye
komai a wurinshi, na zaro ledar da naji
danshi, kifi ne manya masu kyan gaske
guda uku.
Na bude frizer na ajiye guda biyu na
fara gyaran dayan da alama shi yake son ci
da daddare.
Farfesun kifi nayi mishi wanda bai yi
romo mai yawa ba, sai nayi coconut fried
ice na ajiye a food flask ganin har na
gama bai dawo ba duk kuwa da daren da
nayi sabodamakarar da nayi wajen
farawa.
Har nayi sallar Isha'i shiru bai dawo ba.
Bai saba yin dare a waje ba idan ba
kwanakin sati ba ne wato Asabar da
Lahadi.
Tun ina sa ran dawowan shi har na
hakura na hau gado na kwanta. Can cikin
dare na ji motsin shi.
Na mike na same shi tsaye yana cire
riga da niyyar canzawa don kwanciya.
61
Na fito falo na dauko abincinshi na
kawo mishi, bayan nayi mishi sannun da
ko kallona bai yi ba.
Na ajiye abincin da farfesun na koma
gefe na zauna yadda na saba yi. Ya gama
shirin shi ina tunanin zai zauna yaci
abincin ne sai kawai naga ya hau gado ya
kwanta.
Na dan daure na ce ba za ka ci abincin
ba ne? Bai ce mun komai ba duk kuwa da
nasan idonshi biyu saboda haka sai na
tattara na kai kicin na zuba cikin wani abin
na saka a fridge don gudun kada ya lalace.
Na dawo dakin na gyara na sake
kwanciya sai dai a yanzu kam ban samu
yin barcin ba.
Kan kace meye wannan sai na fara jin
saukar numfashin Ishak yau ma haka na
kwana ban yi barci ba.
Sai dai duk tsawon lokacin tunani nake
yi na ya kamata naje gida naga iyayena
62
haka nan na sanar musu da abinda yake
faruwa.
Hakanne yasa da na gama gaishe shi da
safe na roki ya bani izinin zuwa gida bai
bani amsa ba haka nan bai tsaya karyawa
ba yayi ficewarshi.
Da wani bacin ran na wuni wanda yau
duk da dadin da gyaran gidan nan yake yi
mun yau haka ya zauna sai da naga
La'asar tayi sannan na mike don shirin
abincin dare.
Shaf, na mance da abincin jiya da Ishak
bar ci ba, don haka na nufi kofar gida don
na samu yaran da zan baiwa abincin.
Sai dai a kulle na ganshi ta baya. Sai
kawai na dawo na kama aiyukana. Kamar
yadda jiya bai dawo ba sai tsakar dare
haka nan yau ma.
Sannan bai ci abincin ba ya sake
kwanciya. Gari ya waye na sake yi mishi
maganar zuwa gida yau ma bai ce mun
komai ba, ya fita ba tare da ya karya ba.
63
Na dai lura idan nace zan zauna ina
kunci da bakin ciki to zan nakasa kaina,
sai kawai na nemi samun saukin
damuwata ta wata hanyar.
Ni ba ma'abociyar kallon fim ba ce,
amma yau sai na shiga laluben drawer da
ke jikin TV stand din don neman kaset din
kallo.
s1Na yi dace da wani mai suna Why did I
get married too?' sunan shi ne ya dauki
hankalina da na saka kuma sai na samu
kaina da nutsuwa don yin kallon.
Kawaye ne guda uku sai dai kowacce
da irin matsalar aurenta. Na dan ji dadin
yin kallon don ya rage mun damuwa.
Ban ki yin abinci ba don ganin ba ya ci
kuma ina ta tara shi a fridge. Tuwo nayi
miyar kubewa bushasshiya na ajiye kamar
yadda na saba.
Ban kwanta ba zama nayi na jira
dawowarshi. Shima yau bai vi dare sosai
ba, don kuwa sha daya da kwata ya dawo.
64
Babu irin tunanin da ban vi ba amma ina
kasa sanin abin vi a kan matsalar. Zaman
auren da nayi ba mai yawa bane
ballantana har nayi wayon zama da miji.
Amma sai na kudure a raina a yau idan
ya dawo zan san abin yi akai shi ne kuma
na ba shi hakuri.
Ganina da yayi zaune a falon bai tsaya
ba wucewa yayi zuwa cikin daki yadda ya
saba.
Na bishi na sake yi mi1shi sannu, sannan
na tsugunna a gefe na ce Don Allah idan
nayi maka laiti ne ka yafe mun abinda nayi
maka. Ba kuma zan sake ba da ikon
Allah."
Wannan magiyar da nayi mishi ita ce
tasa shi ajiye rigar barcin da ya dauko zai
saka ya kalle ni.
To kenan har kin isa na zage ki ki
rama. Iye! Ke kuma wacece a cikin mata?
Duk da bacin ran da maganar tashi ta sa
ni wacce a take kuma na kasa danne
65
hawayen da suka fara zuba a idona
hakurin na ke ba shi kafin daga baya ya ce
ya wuce amma kadá ki sake ko da wasa."
Hakan bai sa yaci abincin ba, amma bai
dame ni ba. Na hau gado na kwanta.
Washegari na lura ba shi da niyyar buga
sammak0 irin