Author : Hafsat C Sodangi Category : Romantic Hausa Novels
kaita
kunnena.
"Ranki shi dade barka da shan ruwa."
Na ce, "Ai mnu nan bamu sha ba
tukunna, wanene mai magana?"
85
"Ahmad ne."
Na dan yi shiru ina tunani, to ni kuma
ina nasan wani Ahmad? Na ce, Kayi
hakuri ban gane ba."
Ya ce, Mutumin da ki ka yi sayayya a
shagonshi kwanakin baya. Na ce, Au, haka
ne ina wuni?
Muka fara gaisawa, ya ce Nayo ta so na
kira to wani uzuri ne ya same ni shi ne
dalili na kuma kira ne a yanzu don na nemi
wata alfarma da fatan kuma ba za a ki yi
mun ba?
Na ce, mecece alfarmar da ka ke nema?
Ya ce, So nake a bani izinin zuwa gida.
Na ce, Aiya, ai bana ma gari. Ya ce, Eh
naso nayi zaton hakan da ki ka ce mun ku
ba ku sha ruwa ba, kina wane gari ne
yanzu haka?"
Na ce, Ina Birnin kudu. Ya ce, Au ki ce
kusa da garinmu kenan. To sai yaushe ki
ke ganin za ki dawo?
86
Na ce, Gaskiya sai gab da sallah ko ma
bayan sallah. Muka yi sallama da shi na
ajiye wayar.
Ni shaf na ma manta da shi gaba daya.
Baba Ladi ta ce, To shi kuma wannan
wanene?
Na ce, Wani ne. Naja bakina nayi shiru,
ta ce Kya dai ji da gulmarki.
Ina zaune a sashen kannen Babana
muna aikin abincin buda baki wayata tayi
kara.
Na dauka ina dubawa, Ahmad ne. tun
bayan da müka yi waya da shi kwanai
takwas kenan cif, ba mu sake ba sai yanzu
da ya kira ni.
"Ranki shi dade."
Na ce, "Tare da naka." Yayi murmushi
ya ce, To amin ya azumin? Na ce, Mun
gode Allah. Ya kasuwa? Ya ce kullum
muna godiya ga Ubangiji.
87
Na kira ne na shaida miki ayi abin buda
baki da ni don ina kan hanya. Cikin
mamaki na ce, Gaskiya ko wasa?
Ya ce, Akwai wasa ne a tsakanina da
ke? Shiru nayi. Ai maganata da ke babu
wasa a cikinta, abinda na kudura a raina
kenan kuma kema ina fatan ya zama haka
a wurinki.
Sammani na tura ya taho da Ahnmad
daga inda ya tsaya, sannan ya shigar da shi
dakin su da ke zaure na samarn.
Muka fara gaisawa yana dan tambayata
wasu abubuwa ina ba shi amsa.
Na ce, Nayi mamaki sosai da ka ce mun
kana hanya, sai daga baya na tuna ka ce
mun kusa da garn ku ne.
Ya ce, Eh kusa da garinmu ne amma ai
da nisa a tsakani koda dai ba sosai ba.
Ni dan Kano ne Challawa. Kuma
saboda rashin adalci irin naki sai ki ka yi
tunanin garinmu na zo ba wurinki ba.
88
Na dan yi murmushi na ce, A a ni
haka nake nufi ba. Ya ce, To me yasa ki ka
yi riko da wannan hujjar idan ba haka ki
ke nufi ba?
Na taso ne takanas nazo wurinki don k1
tabbatar da duk wata magana da zan yi
miki ko kuma wacce zata biyo baya.
Ina kuma fatan ba zan samu matsala
daga bangarenki ba. Shiru nayi ina
sauraronshi tare da yin wani tunani a cikin
raina.
Ba zan son na sake yin gaggawa a cikin
zancen neman aure ba, da koma wayea
yanzu nafi bukatar fahimtar juna farko
tukunna.
Don kuwa babbar matsalar da na gamu
da ita a gidan Ishak kenan, koda dai a
lokacin ban san komai game da zaman
aure ba. Don haka yanzu daban.
Shirun da ya ji nayi shi ne yasa shi ci
gaba da magana.
89
"Na riga nayi booking din wurin kwana
a cikin gari, don haka zan dawo gobe don
mu ci gaba daga inda muka tsaya.
Zan iya shiga na gaidamutanen gidan?
Na ce, Eh bari nayi musu magana. Ya ce,
To.
Kasancewar su Baba dan Juma ba sa
nan sai kawai ya gaisa da su Baba Ladi ya
wuce.
Kwana nayi ina tunane-tunane ranar
saboda ban taba yin zaton cikin dan
Rankanin lokaci zan fada cikin harka ta
zancen aure ba.
Koda Babana ya tabbatar mun ba zai
yiwu na koma Makaranta ba sai nake
tunanin a kalla zan shekara ko ma fin
hakan kafin kuma na sake yin wani auren.
Ko ma don na dan huta wasu abubuwa
na 6acin rai da fargaba da ke cikin aurén.
Don haka maganar da na tsayar kawai a
raina ita ce ba yanzu zan yi wani auren ba,
don kuwa zan fi son idan nayi aure nan
90
gaba nayi zamana ba tare da na sake
fitowa ba, tunda dai ba jeka ka dawo ba
ne.
A Kamar yadda ya ce haka din kuwa ya
yi, karfe sha daya daidai ya yi sallama.
aKwalliya mai sauki nayi ta atamfa
(Cote Divoire) sai gyale mahadinta. Muka
gaisa ya ce, Ina fata dai ban bugo
sammako ba ko?
Na ce, "A'a haba. Ya ce, To ai ban sani
ba don kuwa da kyar na iya bari goma da
rabi tayi.
Ya ce, To me ki ka ce Hauwa'u? Tunda
kin ga matafiyi nake dole ina so na koma
gida a yau in Allah ya yarda saboda
mahaifiyata.
Don haka nake so ki taimaka ki bani
amsar da ki ka yii alkawari don 1na san
halin da nake ciki.
Na ce, To a gaskiya ni bana son
maganar aure ta zamo cikin gaggawa, in
91
da hali ina son fahimtar juna ta zam0
farko.
Tunda shi din abu ne da ake yi ba da
nufin rabuwa ba. Zuba mun ido yayi yana
kallona.
Zuwa can ya ce, Kin yi magana irin ta
manya, na kuma yaba da zurfin tunaninki.
A matsayin da ki ke a yanzu lokaci
kamar yaya ki ke so a bai don ki fahimci
mutum, shekara daya ko biyu ko fiye da
haka?
Amsar da tia kasa ba shi kenan saboda
na gane gatse yake yi mun. Kina ganin
mutum kamar ni zan iya yi miki irin
wannan neman?
Kuma nema na aure? Ni ba karamin
yaro ba ne ina da 'ya'ya ina da mahaifiya,
bayan haka kuma ina zaune ne a yanzu
bani da iyali.
A irin kallon da nayi miki da iya abinda
na fahimta a tare da ke a yanzu bana zaton
92
iyayenki za su bar ki zuwa wannan tsawon
lokacin ba tare da aure ba.
Na dade kwarai ban ji wani abu game
da wata mace ba kamar yadda ki ka zamo
mun Hauwa'u.
Don haka kada kiyi mun rashin adalci
wajen zartar da hukunci a kaina. A hankali
na ce mishi to ka bari na dawo gida
tukuna.
Ya ce, To shi kenan yadda duk ki ka ce
mai neman a ba shi ai ba ya fushi.
Atamfofi masu kyau ya kawo ya baiwa
su Baba Ladi dukansu ya ce su ci sallah.
Mun ci gaba da yin waya da Ahmad,
kullum yake kirana safe da yamma muna
gaisawa.
Cikin dan kankanin lokaci sai muka yi
sabo sai kuma na fahimce shi don kuwa ko
a waya sai na gane yana da bambanci da
Ishak.
Don kuwa shi mai barkwanci ne. ban
shirya dawowa gida ba sai ana azumi
93
ashirin da biyar kenan sallah saura
kwanaki hudu.
Tsaraba sosai aka yi mun, Baba Ladi da
kishiyoyinta kaf dinsu tsarabarsu ta Umma
ce.
Don kayan Siyarwarta irin su kuka,
bushasshiyar kubewa, daddawa, barkono
da dai sauransu tsaraba sai da naki diba
saboda sanin da nayi dole sai na biya
kudin motarta idan nazo tasha.
Amma duk da haka ban tsira ba, don
kuwa kudi mg yawa suka karba saboda
bugun shinkafar da suka hado ni da shi.
Tun ina hanya Ahmad yake kira har na
kusa sauka.
Muna gab da motarmu zata shiga tasha
ya kira ni.
"Ga Direbana zai zo ya dauke ki zuwa
gida. Na ce, "A'a ayi hakuri yallabai
kada Babana ya kore ni a gidan. "
94
Ni dai har yanzu ban daina mamakin
Ishak ba. Ashe ya iya magana cikin
tsanaki yi ne ba ya yi.
Ya yi mun alkawura masu yawa amma
duk wadanda kudi ne za su aiwatar da su
shi kwata-kwata ma bai fahimce ni ba
kenan tsawon, zaman da nayi da shi.
Ya manta bai yi mun alkawarin ba zai
sake dukana ba zai ba ni lokacin shi ya
nuna mun so da kauna da kulawa da
tausayawa wadannan abubuwan sune
manyan abubuwan da na rasa a gidan
Ishak.
"Kiyi mun magana Hauwa'u don
Allah."
Na ce, "Ishak! Ka saurare ni ka ji abin
da zan gaya maka, kaje ka samu wata
matar ka aura ko kuma ka maida wata
daga cikin matanka na baya da ka saką zai
fi maka akan zuwa kofar gidanmu da ka ke
yi ka ke sawa ana kirana.
113
Auren da zan yi aure ne na SOsai da
sosai da zuciya daya ba tare da wata
manufa ba, ina son Ahmad ina kuma fatan
auren da zamu yi ya zamo mana alheri a
duniya.da lahira.
Kai kuma ina yi maka addu'ar Allah ya
kara maka hakuri ya kuma baka mace
wacce zata iya zama da kai kuma ta
kwarai ko don dana da ke gidanka.
Ina kuma rokonka da kada ka sake
zuwa gidan nan ka kira ni don gudun bacin
rai."
Zama nayi na yi wa Umma bayanin
abin da ya faru tsakanina da Ishak ta ce,
"To! Haka Allah ya kaddara amma
wannan al amari.
Hirarmu ta yi nisa da Uma har na rinka
bata labarin abubuwan da suka rinka
faruwa da ni a gidan Ishak, wadanda ko
sau daya ban taba fada ba.
114
Ta ce, "Ikon Allah, ai shi yasa aka ce
wai MAI DAKI shi yasan inda yake yi
masa yoyo."
Na ce, "Shi yasa na yi matukar mamaki
da yazo yake kokarin naje na kashe aure
na dawo gidanshi."
Umma ta ce, "To ke dai sai kiyi a
hankali, ki kuma yawaita addu'a shi
wannan din ya zamo miki alheri, shi kuma
Isiyakun Allah ya ba shi wacce zata zame
mishi alherin shi ma.
Ai shi yasa wani lokaci sai abu ya same
ka kayi ta bakin ciki sai daga baya ka gane
alheri ne abin.
Ba gashi ba da yanzu kina can a
wannan halin tunda mai hali ai ba ya
fasawa kuma maganar gaskiya ita ce zama
da miji mai duka abin akwai matukar
wahala.
Ki kuma kudura a ranki za ki yi zaman
auren ki da zuciya daya."
115
Shirin aure sosai nake yi da Umma,
kudin hidima da Ahmad ya bani shi ne
nayi amfani da shi wajen yin kayan daki.
Sai kawai dan cikon da aka yi akai
wajen siyan asalin kayan kamfani dan odar
da kuma na'urorin kicin.
Duk wani nawa na gayyace shi ciki har
da Hindu da Momi, abin ya yi musu dadi
ba kadan ba, Momi ce kuma ta kawo mun
guzurin littafin girki na turanci (Woman
and Home) da ya kunshi girke-girke iri-iri
wajen kala dari biyu.
Kayan aure na musamman Ahmad ya yi
mun tunda ai ko Hausawa ma sun ce wai
masu abu da abunsu. Don kuwa komai a
cikin kayan na asalin mai kyau ne.
Mutanen birnin kudu kuwa kamar ajiyar
garin suka bayar don kuwa wadanda ba su
zo ba kadan ne.
Da addu'ata fal baki da zuci na sa kafa
na shiga gidan Ahmad.
116