ZAWARCI BOOK COMPLETE HAUSA NOVELS BY JAMILA MUSA.txt

Author :  Jamila Musa Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   9 / 33

24K to 27K   out of 97.5K words

shiru tana addu"ar Allah ya tsallaketa, tun tana zaman bayi na marmari ha zaman ya fara isarta, tun tana kukan zuci har ta fara mai ƙarfi, shi kuma kabir sai maganar batsa yake, raihana tanajinshi amma ta kasa magana,

Har aka kira azahar kabir bai fita ba kuma bai dawo mata da zaninta ba, kam wasa sabon fari, tana cikin bayi har yanxun tana kuka, tana tsine ma kabir albarka, tana nadamar zuwanta gidan nan tare da nemar ma duk macen dake faɗin duniya Allah ya rabata da *zawarci* duk inda ka samu ka raɓa kayi haƙuri wata rana sai labari, idan kuwa kace zawarci zakai lallai yanxun ka fara ganin wulaƙanta, dan baka da mutumci da kima da daraja a idon kowa raihana tace yanxun da ina da aurena mima zai kawoni gidan nan har inyi wanka?"" koma nazo nayi wankan ai bai isa ya wulaƙantani haka ba, wani irin ihu raihana tayi kamar mai shirin hawa bori, kabir dake zaune yaji ƙarajin data yi, yace kiman alkawari idan zaki ban insha nono, raihana tace Allah ya tsine maka albarka wallahi banƙi yau an gitta gawarka ka mutu ba, kabir yace ban mutuwa wallahi harsai na samu abinda nake so a wurinki, ina samun abinda nake so yauma in mutu banajin komai,

Kiran sallar la'asar raihana taji an fara, wayyyo Allahna na shiga ukku na lalace nk raihana, kabir dan matsayin manzan Allah S. A. W ka bani zanina dan girman ubangiji kasa sai kiran Allah nake a cikin bayi, ka rufa man asiri, kabir yace yarinya dani kike zance, baƙin ciki yasa raihana tayi shiru, ta koma kuka ƙasa ƙasa, ga ta gaji da tsayuwa amma babu damar ta zauna cikin bayin dan tsikar jikinta ma a tashe take,

tana cikin kuka taji anyi sallama, gabanta ya faɗi tace Allah kasa ba umma bace, lokacin da hawaye ya sake zubo mata daga idon ta , gaishe da kabir tayi sannan tace don Allah raihana tana nan?"" kabir yace bata nan, daga cikin bayi raihana tace zulaihat ina nan ƙarya yake rufa man asiri kada ki fita daga gidan nan don girman Allah, kasan cewa zulaiha ba ita ɗaya bace taxo, su ukku ne, itama ɗaga muryarta tayi sannan tace kina inane?"" raihana tace gani nan a bayi shiga ɗakin ki ɗauko man kayan sawa, har zata shiga ɗaki kabir yace bar munafika gafa zanin nan ta bani riƙo da zata shiga wanka, anshi ki miƙa ma baƙar munafika kusa dashi zulaiha ta matsa ta karɓi zanin ta miƙa ma raihana ta ɗaura ta sako hijabinta sannan ta buɗe bayin ta fito,

tana fitowa da gudu taje ta rungume zulaiha ta fashe da kuka tace Allah ka raba kullihin musulmi da zawarci, ƙawayen zulaiha suƙa amsa da amin bakin ɗayansu, kabir kuma sai hararar raihana yake, alwalla tayi sannan suka shiga ɗaki baki ɗayansu,

suna shiga raihana ta fara sallah ko gaisawa dasu bata tsaya yi ba, saida ta gama sallah sannan ta shirya ta saka kayanta, ta kalli zulaiha tace yau kin ceci rayuwata, ta kwashe kaf abinda ya faru ta faɗa masu, ƙawar zulaiha tai dariya tace ke ai mai sauƙi ne, shi yasa kin ganni nan na rufa ma kaina asiri dana fara zawarcin nan mijina yana shaye shaye mutane suka matsa man in kashe aure na, na kashe auren na koma gida, sai gashi ni ƙanin kishiryar mamana zaiman fyaɗe,

tsaki raihana tayi tace Allah dai ya sawaƙe, kawar zulaiha tace idan dai kana zawarci wulaƙanci iri iri sai ka fuskance shi, ni wallahi dana ga mace tana halbe halbe a gidan mijinta sai nace ta rufa ma kanta asiri, tayi haƙuri tayi zaman ta,

raihana tace gaskiya aini yanxun idan nayi aure ko mijina ya ƙoreni babu gidan ubandaa zanje, bare ma insha Allah bazan mashi abinda zai ɓata mashi rai ba, tarairayarshi zanyi in kula dashi bazan bashi abu daga tsaye ba, zan girmamashi sai yaji daɗin aurena wallahi, dariya sukai baki ɗayansu, raihana tace bansan wulaƙanci fa, dukansu sukai dariya baki ɗaya,

raihana tace zulai waye ya faɗa maki ina muna na gidan?"" tace dana je gidan da kuke haya baku nan sai naje na tambayi gwaggo tace tanajin kina gidan ummanki, raihana tace ashe tasan muna nan?"" zulaiha tace Eh, raihana tace ina yaranki ne?"" tace hmm na maiyar dasu kamar yanda kika ce,.ke raihana matarshi kinsan bata taɓa aihuwa ba, ko?"" to tace bata riƙe mashi "ya"yanshi, tayi yaji tana gidansu, yau yazo gidanmu yace ma baba ayi haƙuri yana biko,

Raiha a tayi dariya, sannan tace kinji ita kuma banzar zatai ma kanta, mu mata muna da matsala dasai ta kama yaran ta riƙe to miye a ciki?"" zulaiha tace baƙin ciki zaki man?"" kibar banza ta tafi ai duniyar sai wani ya rasa wani yake samu, raihana tace ba baƙin ciki bane, gaskiya ce, dake da ita babu wanda ya kawo wani kiyi haƙuri kuyi zaman ku, zulaiha tace kr barta can ita ta sani,

Raihana tace to yanxun ya aka ƙare zulaiha tace da aka kirani maganar komawa cewa nayi gaskiya bazan koma ba, raihana ta taɓe baki tace shegiya dama ni na samu damarki wallahi da komawata zanyi dariya zulaiha tayi sannan tace ke jan ajin nan ne, su duka suka kwashe da dariya, raihana tace wane aji yarinya?"" ai aji cikin gida ake janshi , bari ki shiga daga ciki sannan kina shi, idan yaga zaki raina mashi hankali saiya haƙura dake kinsan suma mazan da nasu halin, amma ki lallaɓa kawai ki koma tunda dama ta samu kafin ta wuce, zulaiha tace insha Allah, hada ceman ai laifinki yasa na ƙara aure tana kwaikwayon maganar mijin nata, duk suka sake sheƙewa da dariya,

zulaiha tace kai ku tashi mu tafi idan muka biye raihana anan zamu kwana kinga har an fara kiran sallah magrib, lokacin da suka tashi baki ɗayansu,

hijabi rainaha tasa danyi masu raki, tunda tace su tsaya suyi sallah amma sunce sai sunje gida,

bayan ta raka su ta dawo, bata shiga gidan ba, ƙofar gida ta zauna, tana jiran wanda zai shiga gidan, tana nan zaune ƙofar gida babu alamar wanda zaizo, kabir ne ya fito daga cikin gidan, ya kalleta sannan ya wuce, miƙewa tayi da sauri ta shige gidan tana shiga ta kulle ƙofar, shi kuma yana ganin ta shiga ya fara bubuguwa, raihana tasa ko masu gidan ne suka fara dawowa, tana zuwa tace waye?"" yace ubanki ne, buɗe mana gida tunda ba gidan ubanki bane, raihana tace anƙi a buɗe sai masu gidan sun dawo, yace na ranste maki idan na biyo ta sama kashinki ya bushe, raihana tana jin haka da sauri ta ɗaga kanta dan ganin kantangar ganin zai iya shigowa yasa ta yanke shawarar buɗe mashi amma sai ta koma ƙofar gida, tana magansr zuci taji yace baki jina ne dan kutumar ubanki?"" da sauri raihana ta buɗe ƙofar tana ƙoƙari fita yana ƙokarin shigowa, da sauri ya riƙeta, ya lallatsa mata nono tace wayyo Allahna na shiga ukku matse ta yayi jikin bango da ƙarfin bala"i shi ƙoƙarinshi ya rufe gidan ita kuma sai yage baki take tana jama"a ku kawo ɗauki, daɗe mata baki yayi da hannushi yace shegiya sai kin tara mana mutane, ni ban taɓa ganin wanda baisan arxiki irinki ba, ana ƙoƙarin rufa maki asiri ke kuma kina so ki tona ma mutane ko, hannunshi ya sake kaiwa saitin mamanta da sauri ta zame, tana ƙoƙarin fifa dan ƙafarta ɗaya harta taka sumintin ƙofar gida, ya jawo mata wuyan hijabi ƙiyyyyyyy ya dawo da ita ciki, dukiyar fulaninta ya sake kai hannunshi kafin ya ƙara taɓawa raihana tayi kukan kura takai bakinta saitin hancin shi tayi mashi wani irin cixo, shi kuma lokacin da yaga ta buɗe bakinta ta nufo fuskarshi tunaninshi kisss zatai mashi saboda haka ya saki baki,

lokacin daya ji cizo kundai san hanci baya san a taɓa shi kabir jinshi yayi a duniya yake ko a lahira, tana ganin ya rufe idonshi yana ihu tayo waje da gudu, tana fitosa suka haɗu da umma..................€€
💦💦💦💦💦
💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦

*Page* 2⃣3⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA*

*jinjinar ban girma ameenci fans, wannan page in nakune , Asmeenat Xeeyan tace a baku shi*

*****

*U*mma ganin raihana ta fito da gudu ta tsaya tana tambayarta lafiya?"" bata gama rufe bakinta ba, saiga kabir ya fito cikin 360 yana cewa yau sai kinci ubanda ya haifeki,

Ganin umma yasa ya tsaya, umma ta fara tambayar lafiya?"" da gudu raihana taje ta faɗa saman kafaɗar umma tana kuka tace umma muje bana san gidan nan mu tafi don Allah, tana sake farkewa da kuka,

Hankalin umma ya tashi tace miye wai?"" hannu raihana ta shiga girgizawa tana cewa muje umma mu tafi don Allah,

Umma ta kalli inda kabir yake tace lafiya kabir?"" kabir kallon raihana yayi raihana tace umma muje muje don Allah na tsani gidan nan, mu tafi kada mu dake komawa gidan nan,

Umma tace wai miye ne?"" kai kabir laifi tayi maka ne?"" kabir yace umma zagina tayi, da sauri raihana ta ɗago daga saman kafaɗar umma ta kalli kabir, umma kuma tace miya haɗaku?"" kabir yayi tsuru tsuru dan baisan amsar da zai bawa umma ba, umma tace ummmm Allah ya kyauta dai,

Raihana cikin kuka tace umma kin samo mana gdan?"" umma tace ban samu ba, raihana tace ina kika je kika daɗe?"" umma tace inacan neman gidan , umma tace muje ciki, raihana tace wallahi bazan sake shiga gidan nan ba,

Umma tace to ina zamu?"" raihana tace ki zauna gidanku nima zan tafi gidanmu, tana faɗin haka ta fara tafiya, umma tace raihana zo nan!"" raihana ta tsaya ba tare data juyo ba, umma tace raihana ina ne gidanku?"" raihana tace wallahi gidan gwaggo zanje, umma tace to kije da safe ki dawo ina nemanki, raihana tace to, sannan ta wuce daga wurin,

Umma na ganin tabar wurin tace kila halin nashi ne yayi mata, bawar Allah ubangiji ya baki miji na gari ubangiji ya kawo maki sauƙin wannan *zawarci* mutum ya rasa inda zai raɓa, ajiyar zuciya tayi sannan ta shige gida, shi kuma kabir wuri ya samu ya zauna yana tsine ma raihana da maiyi abinda yasa ransa yayi ba,

raihana tafiya tayi sosai kafin ta iso gidan gwaggo, lokacin data iso ƙofar gida suka haɗu da gwaggo da alama daga unguwa ta dawo, raihana tace gwaggo daga ina haka?"" gwaggo tace daga unguwa nake, raihana tace nazo gaisheki ne, gwaggo tace to, ta buɗe gidan suka shiga, ɗaki raihana tabi gwaggo suka shiga, suna shiga raihana tace bara tayi sallah gwaggo tace to, buta ta ɗauka ta fita, bayan tayo alwalla ta dawo tayi sallah, data gama suƙa sake gaisawa da gwaggo sun ɗan daɗe suna fira, daga baya gwaggo tace ma raihana ki tashi ki tafi gida dare ya fara, raihana tace ina nan yau anan zan kwana, gwaggo tace saboda mi zaki kwana anan?"" raihana tace haka kawai nayi ra"ayi, gwaggo tace idan uwaki ta nemeki fa?""

Raihana tace ai nace mata na dawo nan gidan kwata kwata da zama, harsai Allah ya bani mijin aure, ido gwaggo ta zaro tace nidai ban zama dake raihana tace ai bake zaki zauna dani ba nice zan zauna dakai, gwaggo tace baki isa ba, raihana gado ta tashi ta haye, bayan ta kwanta tace gwaggo da safe ko waye zaije can gidan ya anso man kayana?"" gwaggo tayi ma raihana shiru , duk maganar da raihana tayi gwaggo bata , bata amsa, baki raihana ta taɓe, sanan tace gwaggo kenan,

Raihana gyara kwanciyarta tayi sannan ta fara tuno abinda ya faru tsakaninta da kabir, ajiyar zuciya tayi sannan tayi addu"ar Allah ya tsare na gaba, haka dai tayi ta tunani iri iri har bacci ya ɗauketa,

****
*G*ari na waye wa, gwaggo ta tashi ta ɗora dumamen tuwo, lokacin da raihana ta farka, dan sallahr asuba tayi ta koma bacci, to lokacin data farka jikinta ta wanke ta shirya dan tafiya wurin kiran da umma tace da safe ta dawo,

tsakar gida ta fito tayi ma gwaggo sai ta dawo, tace kada ki dawo gaskiya nidai kiyi zamanki can, raihana ta juyo ta kalli gwaggo sannan tace gwaggo kiyi haƙuri don girman Allah kada ki manta ada wannan gidan ba naki bane, mahifinmu yake dashi baki taɓa zaton zaki sameshi ba, ita rayuwa hawa da sauka ce kiyi man alfarma dan Allah in zauna na wani lokaci kafin mu samu gidan zama, bance da umma zamu dawo ba ni kaɗai zan zauna, taci gaba da cewa gwaggo kefe mai riƙeni ce yanxun da maifiyata bata da rai haka zaku barni inyi ta tangariri a duniya?"" hawaye ya zubo daga idon raihana tace kiyi haƙuri rayuwa juyawa take sai kiga wata rana na gaba ya koma baya, amma duk abinda akai haƙuri dashi sai ya zama labari,


gwaggo cikin sanyi tace to ai kema ki fito da miji kiyi aure amma kin tsaya ruwan ido , raihana tace ba ruwan ido nake ba Allah har yanxun bai kawo man wanda zai aureni ba, dana samu zanyi aure kiyi haƙuri, ki barni in zauna tare dake kada wannan raɓe raɓen da nake yasa ni faɗawa cikin wani hali,

Jikin gwaggo yayi sanyi raihana ta bata tsauyi, tana tunani taji raihana na cewa ki taimaka man don girman Allah ko yau muka samu gida dani da ummana bama zan dawo ba, amma idan bamu samu ba zan dawo ki taimaka man ko a tsakar gida sai in riƙa kwana, gwaggo tayi shiru,

raihana taci gaba da cewa nayi imani da "ya"yanki ne a wannan rayuwar zakiji tausayinsu duba kiga jarawar da Allah ya ɗora man ya kamata a tausaya man gwaggo duniyar duka guda nawa take?"" baki da tabbas ma idan na fita zan dawo da rayuwata kila kuma saƙon mutuwa ta zaizo maki, ki taimakeni gwaggo yanxun nake buƙatar taimako don Allah

gwaggo tace tsaya kici tuwo, raihana tayi murmushi sannan tace na ƙoshi, gwaggo tace mi kika ci ne?"" raihana tana cikin tashin hankali sai yanxun ta tuna rabonya da abinci tun ruwan kokon data sha jiya da alewa, tanajin yunwa sosai amma tunda gwaggo dama tun baba yana raye bata san taci abincin gida yasa ta haƙura ta matse yunwarta tace umma ta ajiye man kalaci,

sai na dawo gwaggo, gwaggo tace jira in baki mabuɗi guda ɗaya ko kinxo bana nan sai ki buɗe, raihana tace ah ah barshi idan nazo baki nan zan jira a waje harsai kin dawo,

tana faɗin haka tayi waje, tana fita take magana a ranta tace muda gidan gadonmu amma ƙarfin ya cinye mana, hawayen daya zubo mata a idonta tasa gefen hijabinta ta goge, haka ta daɓi sayyada har gidansu umma,

Lokacin data isa a ƙofar gida ta tsaya ta samu yaro tace ya shiga yace a na sallama da umma fati, bayan wani lokaci yaron ya dawo yace gata nan zuwa, godiya raihana tayi mashi sannan ta samu wuri ta zauna tana jiran fitowar mahaifiyarta ,,,,,


ba"a wani ɗauki lokaci ba, umma ta fito, inda raihana take zaune taje ta zauna , bayan ta zauna raihana ta gaisheta, umma ta amsa sannan ta kalli raihana tace kuka kikai?"" murmushi ta ƙaƙaro dan tana cikin damuwa, sannan tace ma umma mi kika gani?"" umma tace naga idonki yayi ja, wasu sabbin hawaye suka zubo ma raihana wadda ta kasa maida su, ta kalli umma tace nidao zanje ince ma yusufa ya aiko idai zai aure ni, umma ta zaro ido tace mata haba raihana kiyi haƙuri tunda ya daina zuwa wurinki saiki barshi, kiyi fatan Allah ya baki wani wanda yafi shi alkairi,

raihana tace umma haƙuri na nidai bama ƙarewa yayi ba mutuwa yayi ta sake ɓarkewa da kuka umma taji tausayin raihana sosai, ita umma tunanin ta raihana abinda yasa take so tayi aure kila dan ta taɓa auren ne ko tana buƙatar namiji a kusa da ita,

Ita kuma a ɓangaren raihana tana so tayi aurene saboda ta rasa mataɓa, dan ita babu wani abu daya taɓa shiga tsakaninta da wani namiji, dan ko aminu daya aureta duk zan da sukai saidai ya ɗanyi wasanni da ita,

Umma ta kalli raihana sannan tace to tunda kina ganin haka ne mafita kiyi ma yusufan magana kiji, tayi ma raihana hakane dan kada taje ta saka rayuwata a wani halin ,,,,

Raihana ta kalli umma tace umma kinyi kalaci ne?"" umma tace ni ɗan kuɗaɗen nawa ma an sace, raihana tace subahanallah""" garin ya?"" umma tace nima wallahi ban sani ba , raihana tace to mi kikaci yanxun?"" umma tace ba komai, raihana tabi mahaifiyarya da kallo cikin tausayi

Umma tace ke ban maki albishir ba, raihana tace nami?"" umma tace na samu aiki wani gida, gaban raihana ya faɗi, tace haba umma, sai ki tafi kina aiki aje ayi ta ɓata maki rai?"" ni wallahi bansan aikin gidajen nan, tace ke wannan basu da wulaƙanci wallahi mutanen kirki ne, raihana tace to Allah ya tsare ,

Umma tace ameen sannan tace to ya kuka ƙare da gwaggon?"" raihana ta ɓoye ma umma dan kada ranta ya ɓaci, tace gwaggo tace wai hadake mu dawo gidanta, dan tasan umma baza ta koma ba, raihana taci gaba da cewa nace mata ah ah, nidai kaɗai zan zauna ke kince baza kixo ba, umma tace kwarai kuwa ko babu sauran gidan zama a duniya,

Dariya raihana tayi sanann tace umma bani kayana kinji inje inyi wanka gidan farida zanje, umma tace wane iri zan ɗauko maki, raihana tace masu kyau zaki bani kala biyar dan saina kwana biyu ban sake dawowa ba, umma tace to,

tashi tayi taje ta ɗauko mata kayanta sannan ta kawo mata, raihana tayi mata bankwana sannan ta tafi,

raihana tafiya take a galabaice yunwa ta isheta har bata ganin gabanta saboda azabar yunwa, daƙel ta iso gidan gwaggo lokacin data iso ta samu gwaggo ta fito zata fita, gwaggo tace har kin dawo ne?"" raihana tace Eh gwaggo tace to ga mabuɗin gidan raihana tace a,a barshi kije ki dawo, gwaggo tace saboda mi?"" raihana tace ai nima gaba zanyi, gwaggo tace to sai kin dawo, raihana ta miƙe da "yan kayanta tayi gaba,


a ranta take magana tace

9 / 33