Chapter 2 Reading MAITAR IDO COMPELET DOCUMENT BOOK By Mrs Sadauki .txt Arewa Novels

MAITAR IDO COMPELET DOCUMENT BOOK By Mrs Sadauki .txt

Author :  Mrs Sadauki Category :  Documentary

Chapter   2 / 7

3K to 6K   out of 20.5K words

ce “Leemat ban son haka fa” dariya ta yi tare da ci gaba da yi min sharri,tsabar iskanci ma da za su tafi haka ta sa yatsa a fuskata ta na dirzawa ta na cewa “wallahi duk baƙin ta ne na zata ko dauɗa ce” na ture hannunta ina hararenta ta dungure min kai ta na sa tissu ta goge yatsanta ta ce “na shafo dauɗa” sai ta kai yatsan ga hanci ta na sunsuna wai wari nan fa suka shiga yi mini dariya,ni kuma kawai sai na fashe da kuka bayan tafiyar su ne anty Sailuba ke ce mini “ke wasa fa take yi miki kawai don a yi dariya” sai dai duk yadda ta so shawo kaina ƙin yarda na yi kawai dai na haɗe abin a zuci na kammala mata aikin da zan yi kafin na wuce wurin sayar da abincin.


Yadda na ga dandazon mutane duk sun yaɓe anty Hinda sai abin ya bani mamaki don mun sha yin kwantai sai mun dawo da abinci gida yau kuma abun mamaki tururuwa saya ake.Ashe farkon mamakina ne ban ma ga komai ba,sai da na ƙarasa na soma taya ta sayarwa hatta yadda ake zuba abincin an rage awo amma haka muka sayar da shi tasss sai wanda ta zuba mini .Sai da na wanke robobin da aka ci abinci sannan na zauna na soma cin abincin hannu baka hannu akushi,daga nan gida na wuce amma har yanzu Kaka ba ta nan ganin haka na koma saloon ba ni na koma gida ba sai wajen taran dare.
A zaune na tarar da Kaka ta na sauraren rediyo ,bayan na gaishe ta tare da tambayar inda ta je na samu wuri na zauna.Amma sai na ga Kaka ta ƙure cikina da ido,ban kai ga tambayar ta lafiya ba kuma na ji ya fara mirɗa mini.Maimakon in yi zawo a'a kumfa ne ya soma fito mini ta baki kamar akuyar da ta haɗi leda.Kaka ta yi ƙyaci kafin ta bani magani na sha nan na soma amai kamar zan amayar da hanjin cikina,“haba Hinda da ni kike zancen!” ta sake yin wani ƙyacin.....








*Gajeren labari ne*🌚
[27/07 à 16:37] MRS SADAUKI 👑: *MAITAR IDO*👁️
👁️👁️👁️👁️👁️
HoRrOR story☠️


Na
© Chamsiya Laouali Rabo
#MRS SADAUKI💫✍️


*FCWA ☀️*




*NB:* Maitar ido iri-iri ce akwai ta tsafi,akwai kuma wacce ake haifar mutum da ita irin tace wacce in mai ita ya kalli abu da ya burge shi ko akasin haka sai kuka abin ya lalace.Itaciyar bedi ta sha mutuwa silar Maitar ido,wasu sun san su na da ita wasu kuma ba su sani ba.In sha Allah a sannu zan faɗi alamominta da kuma yadda mutum zai yi rabu da ita.




5-6




Na sha baƙar azaba sosai kafin na samu aman ya tsaya,Kaka ta ce “je ki kwanta ” ban musa ba na haye katifa a gajiye,sai dai tuna abin da Leemat ta yi mini yasa na ji baƙin ciki ya rufe ni.Na yi ƙwafa kafin na ce “wai Kaka don Allah baƙin nan na wane ne na kwaso? Tsakanin Inna da Abba waye baƙi?”


Abun mamaki tambayar tawa ce na ga ta razana Kaka,sai ta kasa bani amsa sai motsi take da baki ni kuma na ƙara jin haushi na ce “a gaskiya ko ma dai wane ne na biyo ya cuce ni,yau an wulaƙanta Ni an tozarta ni saboda kawai ni BAƘA CE(Sajida Nijar)”


Kaka ta ce “mi ta yi miki? Sannan wane mataki kike son a ɗauka kanta?”
Jin abin nema ya samu har da tashi na yi zaune ba tare da na san wannan ne farkon jefa rayuwata a cakwalkwalin ruɗani,na ce “so nake ta zama baƙa kamar dai ni,sannan gashin kanta wanda ta yi mini gori a ɓata shi ya zamana nawa ma ya fi nata kyau da tsayi”


Kaka ta saki murmushi wanda a cikinsa na hango tsantsar farin ciki kafin tace “Sarah kin tabbata ki na son haka?”
Ba tare da wani tunani ba na ce “eh sosai ma Kaka”
Ta ce “kin shirya?”
“A shirye nake ai” na faɗa ba tare da na san shirin mi Kaka ke nufi ba,ta ce “to babu damuwa yau za mu je ki ɓata rayuwarta da kan ki,don haka kwanta ki yi bacci tun kafin dare ya tsala ”


Cike da murna na kwanta ina tunani ƙila acid za mu je mu watsa mata sannan mu datse gashinta,da haka bacci ya ɗauke ni.Na ɗauki lokaci mai tsayi a cikinsa kafin na ga Kaka na yi min irin wannan abun na jiya,wasu ruwa ne take yayafa min ta na yin wasu surkullen da ita kaɗai ta san ma'anar su.Abu guda na sani shine bacci nake,amma kuma abun mamaki sai na irina ta miƙe tsaye ta na tambayar Kaka “har lokacin tafiyar tamu yayi?”
“Eh fito mu tafi jirgi na jiranmu” sai ta ja hannuna muka fito,ni kuwa sai ware ido nake na ga inda zan ga jirgi sai dai ina abin ya wuce tunanina.Turmi Kaka ta kada kwance hannuna na cikin nata muka shiga turmin nan kawai sai gani na yi ya tashi da mu sama.Da mamaki na tambaye ta “amma Kaka dama turmi ya na iya tashi sama?”
Ba ta bani amsar tambayar da na yi mata sai bayani ta soma yi mini,“leƙa ƙasa ki ga yadda duniyar da muka baro take” na je na kama bakin turmin na leƙa sai na duk ga gidajen mutane nan da kuma ababen hawa,na waro ido ina mamaki na ce “ya na ga garin duk yayi duhu alhalin nan sama kuma hasken rana?”


“Duniya biyu ce mabanbanta,daren can shine safiyar wannan duniyar.A sannu za ki saba za ki ji wannan ɓoyayyar duniyar ta fi waccan daɗi,tun tuni nake son kawo ki amma kika ƙi bani haɗin kai sai yau da zafin ɗaukar fansa ya ci galaba a kan ki” ina shirin yi mata wata tambayar ta ce “shuuut! Mun kawo Dutsen Muradi ki nutsu ki aiwatar da komai yadda ya kamata”
Kan wani ƙaton dutse jirginmu na turmi ya sauka,yanzu ma Kaka ce ta kama hannuna muka fito “ ki faɗi abin da ya kawo ki mana kin yi wani tsaye” Kaka ta faɗa ta na kallona,“ to ai ni ban san ya zan yi ba” na faɗa ina ƙyafƙyaf da ido.


“Sunan ta za ki kira ”


“Leemat!” na faɗa cikin rawar murya,wani haske ne ya soma sauko wa daga sama mai gamar gajimare kafin ya tsaya a gabanmu,ta cikinsa nake hango Leemat a kwance jikin wani matashin saurayi sai shafar mata gashin da aka kitse yake.


Maimakon muradin gashin ya zube kamar yadda na zo da niyyar,a'a sai na canza ƙudiri na kafe tsorayen da ido ina mai cewa “ ku zama macizai ta yadda saurayin kawai zai iya ganinsu” ko baki ban rufe ba kuwa tsorayen suka fara motsi kafin su zama macizai su na fiddo halshe.Saurayin ya fasa ihu tare da koma gefe ya na rawar sanyi tuni fitsari ya soma yi masa zuba,sai haƙuri yake bai wa Leemat kar ta cutar da shi ita kuma ta na tambayar mine ne gashin kanta yake yi mata nuni wanda yasa ta nufi madubi don dubawa sai dai kafin ta isa ne Kaka ke ce min “ da zarar ta isa ga madubin mutuwa za ta yi don shi mirror bai ƙarya ki yi saurin dakatar da ita”
Take na ruɗe jin zan yi kashin kai na ce “ ta yaya Kaka? Ya zan tsayar da ita ?” kafin kuma ta bani amsa na ƙure ƙafar Leemat da ido nan take ta ɓangwale ta faɗi ƙasa timmm daidai nan kuma Kaka ta yi wani furuci komai ya tsaya cak ciki kuwa har da tsintar kaina kan katifa kuma numfashina ya dawo gangar jikina.




A firgice na tashi ina dafe zuciya,sai kuma na yi saurin sauka na ɗauko ruwa na sha ina mai cewa “ na yi mummunan mafarki ” don ni duk a tunani mafarkin ne na yi ba gaske ba.Kan shimfiɗa na je kwanta,sai kuma na shiga tambayar to ina Kaka ta tafi cikin daren nan ƙila ko banɗaki.Ban kai ga samo amsa ba na ji wata uwar ƙara rudududuuu kamar ta sama za ta faɗo,tsoro ya kama ni na ƙanƙame jikina.Ina cikin wannan yanayi Kaka ta buɗo ɗaki ta shigo cakwal-cakwal da ƙafafunta na kaza,ido na murza na dai ga har yanzu ba su canza izuwa na mutane ba sai kuma na tuna tun jiya fa haka suke har lokacin da anty Sailuba ta zo ta ja ni muka tafi saloon.




Na buɗe baki da niyyar tambayar ta “ Kaka wai...” amma sai ta katse ni ta hanyar cewa “ rufe mini baki tun da ke ba ƴar goyo ba ce,na taimaka miki don ɗaukar fansa shi ne kika baro ni can don ki nuna mini wuyan ki ya isa yanka ƙarfin ikonki(ƙarfin tsafi shine sai miyagu ke ɓoye shi su ce ƙarfin iko) ya ma fi nawa.Ina ce dai ni ce nan na raine ki tun ki na tsuman goyo,kuma ki sani daga yau na raba hanya da ke sai ki yi abin da kika ga dama tun da kin ishi kan ki.Sai dai ki sani tsohon kai ya fi sabon kai dafi ” ta na gama faɗa ta yi gaba ta nufi wani ɗan lungu da muke aje kaya.Wani ƙaton bindi na ga ya na yi mata reto kamar jela,duk ɓaɓatun da gama yi sam ban fahimci abin da take nufi ba don har zuwa yanzu duk na ɗauka mafarki ne na yi.


Kayan jikinta ta canza sannan ta raɓa gefe na ta kwanta,hakan ya bani damar ganin salewar da gefen fuskarta yayi kamar wacce aka ƙona ga wuta.
“Mi ya same ki kuma haka?” na yi tambayar ina shirin ɗora hannuna kan ciwon amma sai ta yi amfani da nata wurin buge ni tare da ɗora min yatsunta sak irin na mage don firgici har sai da na yi baya “ in kika kuskura kika taɓa ni zan yayage miki fuska” a tsorace na kai kaina na jingine ga bango.


Ƙiri-ƙiri yau Kaka ta fito mini da ɓoyayyar siffarta,“ don Allah ki yi haƙuri ni ban mi na yi miki ba” na faɗa a tsorace ,“hum” ta yi wani ƙyaci kafin ta juya min baya ƙaton bindinta kuwa sai wani motsi yake kamar yadda mage ke yi.
Muƙut! Na haɗiye wasu yawu kafin na ce “ wai Kaka wannan duk mine ne? Ƙafafuwan kaza ga kuma bindin mage a bayan ki?”




Ba ta juyo ba ,amsa ta bani kai tsaye “ iya nawa kawai kika gani? Ke naki fa?”
“Ni ai banda ƙafar kaza”
“To ki duba wane kala gare ki” ta bani amsa .
Furucinta yasa na tashi zaune don duba ƙafafuna sai dai mi zan gani? A madadin ƙafafu wani shabcecen bindi kifi ne tun daga wajen ƙuguna zuwa ƙasa na kifi ne.Ban san lokacin da na fasa wani uban ihu ba ina motsa bindin mai ɗauke da wasu ababe kamar mafarfeci.


Ihun da na yi yayi daidai soma zubar ruwan sama masu mugun ƙarfi kafin ƙyaftawar ido ɗakinmu ya cika da ruwa.Hankalin Kaka a tashe ta soma tsalle-tsalle don kamar yadda mage ba ta son ruwa to ita ma haka take,ni kuwa maimakon ace na ji tsoron ruwan a'a sai na ji kamar ma na zo gidana ne .Ko kaɗan ban ji irin wannan yanayin ba na son fiddo kai waje,hasali ma wutsilniya na soma yi cikin ruwan ina yawo kamar wata ƴar ruwa.Munduwar wuyana ce ta soma fitar da wani haske mai ƙuna ,tsabar yadda hasken ke da ƙarfi har sai yasa na wani abu ya caki kwanyata da kuma daidai saitin zuciya ban ƙara sanin abin da ya faru ba sai a washegari na tashi tuni kuma rana ta fito wantsar.Na yi miƙa na tashi zaune ina hamma,Kaka ta shigo ɗakin ta na mai cewa “sai yanzu kika ga damar dawowa?”
Ban fahimci tambayarta ba hakan yasa na ce “Kaka ni da ke bacci ina kuma na je? Bari na yo fitsari na baki labarin mafarkin da na yi cabbb wai Allah na gode ma da mafarki ne” sai na sauka daga katifar na fita waje abun mamaki duk ruwa ne a kwance.Buta na ɗauka na raɓa ta inda babu ruwan na je na shiga banɗaki,ina fitowa na wanke fuska da ƙafafuwana sannan na koma ɗaki ina tambayar Kaka “wai ruwa aka yi jiya? Kuma ba lokacin damina ne ba”
“Sarah kar ki raina mini hankali ki dinga yin abu kamar ba ki san mi kike yi ba,wuce dai ki tafi tun ɗazu Sailuba ke ta aikowa kiran ki” ficewa na yi na nufi saloon.Ina shiga na tarar da Leemat zaune a ƙasa yayin da kuma ƙawarta Watsima ke kwance kitson da aka yi mata jiya sai faman faɗin “washhh! Washhh” take yi yayin da ita kuma anty Sailuba ke ta masifa ta na cewa “ in ba abun ki ba Leemat daga saurayi ya ce kitson bai yi ba shikenan sai ki kwance?Allah duk da kin biya ni na ji zafi fa”
“Anty Sailuba wallahi a rayuwata dama ban son kitso ,saboda na ci kuɗinsa ne na zo kika yi mini amma don wulaƙanci ba ki yadda ya fita daga ɗakin a guje ba kamar ya ga wata aljana”
Watsima ta ƙyalƙyace da dariya ta ce “In dai ya baki kuɗin iPhone ɗin ai shikenan ”
“Ai ban yarda ma na raɓe shi ba sai da ya damƙa mini ita ga hannu,ta na can na baro ta a caji yanzu in gama wanke mini zan je na kunna ta na yi ta selfie ”


Daga wannan ban sake sanin abin da suke tattauna wa ba sakamakon duniyar tunani da na lula ‘ kenan dama ba mafarki ne na yi ba a daren jiya?’ na tambayi kaina kafin kuma na yi wani makirin murmushi na ƙara cewa a zuci ‘ in dai haka ne kuwa Leemat ba zan bari ki yi selfie ɗin nan ba,wato za a yi mana burga da dogon gashi ’
Ina nan zaune ina ɗinka hulla aka gama kwance mata gashin,anty Sailuba ta wanke mata shi ta saka mata kwarkwaro sannan ta je ta zauna kan kujera aka ɗora mata tukunyar busar da gashi.
Sai da na kwatanci gashin ya kusa bushewa kafin na ƙurawa tukunyar ido ina bata umarnin ta ja gashin Leemat ya shige can ciki ko minti biyu ba a yi ba kuwa tukunyar ta soma yin wata irin ƙara ta na fitar da haƙi haɗi da ƙauri.
Hankali tashe anty Sailuba ta je za ta cire wayar lantarkin da ganga na kalli ƙawarta na ce ‘ɓangwale ki faɗi’ ji kake timmmm anty Sailuba ta faɗi tuni Leemat ta soma kuka haɗi da ƙoƙarin tashi amma ta kasa saboda yadda tukunyar ta riƙe gashin gam.Hayaƙin da ya soma fita na baiwa umarnin ya ƙara farashi ai kuwa shagon ya turniƙe da hayaƙi,Watsima sai tari take ta na cewa ta shiga uku ba ta ganin komai yayin da kuma anty Sailuba ke kukan ƙafarta.Sai a lokacin na miƙe na nufi Leemat,daidai gabanta na tsaya kafin na ƙuwara casque ido sai komai ya tsaya cak na jawo ta ina cewa “yi sauri ki tashi tun da an samu kin fito”
Anty Sailuba da Watsima sai salati suke yi su na taɓa hannu ganin yadda gashin Leemat duk yayi wani iri kamar an kaɗa taliya ƴar murje.Kan kujera anty Sailuba ta zauna da Leemat wacce ke ta matsar ƙwallla,ɓarin mai aka yi mata iri-iri kafin a soma shatar gashin nan take ya soma zubewa ya na faɗuwa ƙasa sai ga Leemat da ƙwaiƙwayayen gashi....
[28/07 à 06:36] MRS SADAUKI 👑: *MAITAR IDO*👁️
👁️👁️👁️👁️👁️
HoRrOR story☠️


Na
© Chamsiya Laouali Rabo
#MRS SADAUKI💫✍️


*FCWA ☀️*




7-8




Wani irin daɗi yake ratsa ni ganin Leemat na kuka ta dalilina, wannan kuma bai rasa nasaba da MAITAR IDOna don duk wani mugu ya na jin daɗin mugunta musamman ga waɗanda suka taƙile shi.


Leemat za ta kwashe gashinta don tafiya da shi amma anty Sailuba ta yi saurin hanata “ haba ke kuwa in kika tafi da shi a zai dinga tuna miki baƙin ciki,bari na baki mai ki dinga shafa wa gashin in sha Allah zai dawo normal” cike da siyasa anty Sailuba ta yi mata wayo ta karɓe gashin ta haɗa ta da mai ita kuma doluwar ta karɓa ba tare da ta san sayar da shi za a yi ba.
Ko kuɗin gyaran gashin ba ta karɓa ba suka yi tafiyar su,ita kuwa anty Sailuba tamkar ma ta yi murna da hakan .Ƙaton gwangwanin da take ajiyar gashi ta buɗe ta zuba kafin ta juyo ta kalle ni ta tuntsire da dariya ta ce “ ikon Allah! Ki na ga fa jiya Leemat ta yi ta miki sharri yau ita ma gashinta ya koma irin naki ”
Na saki murmushin ni ma kafin na ce “anty yunwa nake ji”
“To acici ga abincin ki can tun ɗazu na ajiye miki shi” ta nuna mini da yatsanta na je na ɗauko.


Zazafen tuwon shinkafa ne da miyar kuɓewa sai ƙamshi yake da alamu kuma girkin gida ne,ido kawai na ƙura ina kallon abincin wanda zuciyata ta shaida mini ‘an saka maganin mallaka’ da mamaki na ɗago na dubi anty Sailuba na ce “wai anty tuwon nan tun na yaushe ne?”


Cike da masifa ta ce “babu ruwana da iskanci kamar ya na yaushe ne? Na sunan haihuwata.”
“Daga tambaya?”
“Ni na girka shi da kaina,kin samu ma na zuba miki sauran abincin mijina duk da uban kishin da nake da ”


Anty Sailuba ta na da aure sai dai kusan shekara biyar ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba,ta na da mugun kishi sannan ta na son mijinta sosai kamar ta mutu.Duk in ta ji labarin yayi sabuwar budurwa haka za ta samo lambarta ko kuma ta je har gidansu yarinyar ta ci mata mutumci.
A zuci na ce ‘shikenan Bilal ka shiga uku , Allah kaɗai ya san bayan maganin mallaka wane iri ake baka kuma’ a zahiri kuma cewa na yi “a'a gaskiya ba zan ci tuwon nan ba,yo ai in na yi hakan kamar na nuna raini ne a gare shi ” na kuwa rufe abincin.
Anty Sailuba ta ƙure ni da ido kafin ta ce “ki ɗauka ki ci babu ruwana da

2 / 7