RABON KWADO Book 2 By Nana BMB.txt

Author :  Nanah BMB Category :  Love Story

Chapter   2 / 9

3K to 6K   out of 24.3K words

koh kidena zama da yunwa yanzu cikinki zefara zafi kada kizauna jiran ya mujaheed domin yau busy dinsu yafi nakullum balallae suzo da ranaba sezuwa dare nasan zezo seya baki nadaren kici abinda kikeso dae kenan koh, donhaka kisauko yanzu kona kira miki mom nasanar mata,
Turo baki kawae mimi tayi jin zara ta ramfota ga haushinda yacikata sam bataga mujaheed ba yau dukse takejin haushi,kamar tayi kuka tace nifa nakoshi kawae nidae ki kiraminshi awaya,sakin baki zara tayi tana kallonta sannan tace wlh bazan kirashi yanzuba suna tsaka da tarbar mutane sedae nakira miki mom barima kigani wayanta tadauka tayi kiran ganin dagaske take yasata saukowa tasoma tsakuran abincin tana hararan zara takasan ido, ita drym tabata ana daga wayan tayi sallama takuwa marae raece fuska tace pls zara bagashi inaciba kada kigayamata,murmushi tayi mata tacigaba da maganarta tace sis yataron biki andaura aure yanzu koh,inty tashaida mata andaura komae lpy, to masha allah yasanya alkhairi yabasu zaman lpy ya albarkaci rayuwar aurensu,tace ameen
Zara ina mutuniyata i hope dae tanajin sauki sosae zara tasaki murmushi mesauti takalli mimi tanata juya spoon din hannunta alan dole ita abinci takeci,sannan tace inty mutuniyarki lafiya tananan tanata zuban rigima harda harara naki kira mata mutumin,kinsan yau basu zoba,dariya inty tayi sosae tace kema laifinkine waya gayamiki ana shiga tsakaninsu zaki iya ganinshi yanzun nan kuma kiji kunya,haba zara tarike tace wlh sister naga alama domin mitanen nakifa ana zazou segodiyan allah,murmushi tayi tace wlh ni wlh burgeni sukeyi sosae meenal da ya mujaheed suka dace dajuna inason meenal dayawa jinake dama inbiyoku hospital dinma,murmushi maryam tayi tace a ah kitaho kuma kiyi yaya dabakin namu bari dae nabaki ita kuyi magana,mika mata wayan tayi ta ansa tana tura baki suka gaisa yacca take mata maganarma suduka setabasu dariya,inty tace meenal kada kidamu kinji yanzu zannemo miki ya mujaheed dinki yazo gareki kokyadena fushin nan ay kuwa mimi tasaki murmushi tace to nagode tamikawa zara wayan sukae sallama suna dry.
Suna zaune tayi jugum shi kawae takeson gani duk haushi yacikata saboda yaki zuwa itakuwa zara charting take abinta suna haka,yaturo kofan yashigo da sallamarsa tayi saurin daga kanta kuwa suna hada ido tasauke ajiyan zuciya because yayi kyau matuka yasha kananun kaya abinshi bakake tuni yacire manyan kayan na dauren aure saboda zafi hannunshi dauke da juice dayan hannun kuma wayanshice yarike murmushi kawae yake zuba mata harya karaso yazauna gefen bed dinnata, sam beji sallamar da zara take amsa masaba ma,ko ina kamshinsa yagauraye room din sosae farin ciki yallubeta naganinshi datayi, amma seta turo baki itafa anbata mata rae se atime din yajuya suka gaisa da zara tacigaba da danna wayanta haka shima ya aje juice din yana danna tashi wayan, habawa takaeci kuwa yacikata tasa musu kuka,
Hanzarta ajiye wayar yayi yakamo hannunta yana cewa sorry my dear meyay zafine haka nazo ko kulani ma kinkiyi,kara tunzura baki tayi tace to bakae bane kaki zuwa inda nake kuma kazo shine kashareni,hadiye dariyarsa yayi is ok sorry kinji kinsan yadda aiki yamana yawa yau yanzuma nikadae ne bazan iya jurewaba na aje komae nataho sameer yanacan yacedae namiki sannu, ina fata dae kinci avinci baki zauna dayunwaba?
Shiru tayi masa, zara tace inafa kaema kasan bazata ciba tunda baka zoba tundazu nake fama da ita takici wae saina kiraka, saboda nakine tundazu aketa antayamin hararan kasan ido,wani farin cikine yaziyarci zuciyansa yasaki lallausan smile yace aida kinkirani zara don meenal tafi min komae agurina ay, murmushin jin dadi kuwa mimi tayi har beauty point dinta suka lotsa wanda sam bekae na meenal ba ita intana magana har bayyana suke,amma sam bawanda ya ankara acikinsu gwalo tajuya taewa maryam alamun an gwaleta, bani abincin zara yanzu zataci kuwa takoshi mikewa tayi tadauko abincin tabashi tafita abinta domin answer waya,bata abincin yake cikin nutsuwa tana karba harta kusan cinye abinci tashagala da kallonsa hankalinshi yanakan abincin koda yadago zemata magana yaga yadda takafeshi da ido shima kanshi yana mamakin yadda meenal kemasa irin wannan kallon haka murmushi yaymata ya hura mata iska a fuskanta yace yadae,murmushin kawae tayi tasunkuyar dakanta,meenal yanzu kinacin abinci sosae nagode allah sosae su mummy nasan zasuji dadin hakan seda takoshi kadan yarage abincin,sannan yasoma bata lemun daya shigo dashi tanasha wayarsace tafara ruri alamun ana kira kallon wayan yayi besaniba yasheka mata ajikinta jin saukan ajiyan heart dinta yayi lemun dasanyi gashi yana ratsata,dafe goshinsa yayi yace sorry meenal tissue yaciro yasoma goge mata lemun dadan sauri sauri yakeyi don kiran yakara shigowa besaniba yagoga maga kan kirjinta gurin ciwonta tasaki siririyar kara, koda yakkalleta yaga idonta tafda kwalla yamutse fuska yay cikin tausayi yace ya allah wlh namanta kinada ciwo duk muhammad dinkine yarudani kwana biyu yahanani sakat sena hadaku awaya so banason kowa yasan abinda yafaru shiyasa banbashi ke kunyi maganaba, yanzuma ina rokonki idan kunyi magana kada kigaya masa kinji kisaki jikinki sosae kada yagane,ay mimi cikinta wani kadawa yayi tana masa kallon rashin fahimta zuciyanta nabugu to waye kuma muhammad....


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2


NA NANA BMB


page 9 -10
Koda yadago yana kallonta yaga yadda tazuba masa idanu cikeda tsoro setaso bashi dry ma hannunta daya matsane yasata dawowa cikin tunaninta,murmushin karfin hali tamasa yace yadae kada nakirashine kasa bashi amsa tayi tanadan kallonshi kamar mara gaskiya tambaya yajeho mata wae ina kikasa wayankine agidansu inty koda ita kika tafine tafadi ahanya, yace yanata kiran wayanki akashe haka su aunty suma,dan saisaeta kanta tayi tadukanda kanta don tarasa bakin magana,yana sauke idanunshi kan kirjinta yaga dan jini yabata mata saman rigarta kadan dake milk ce cikin damuwa yace hasbinallah meenal haryanzu baki warkeba agurinnan kallonshi tae taga meyake magana akae taga yana kallon kirjinta tayi ssurin maida kanta kasa kuwa, bazato ba tsammani taga yakae hannu kan kirjin nata gefen rigar yadan janye yana kallon karcewar da tayi yana yamutsa fuska kanar zeyi kuka yanzunma dayatsansa daya yadan shafi gurin yace ina maganin dakike shafawa agurin?lumsassun idanunta tabude tayi masa nuni da inda inda suke a ajiye yadauko yazauna kuwa dakanshi yasa tissue yagoge mata gurin yashafa mata maganin harya gama idanunta yana lumshe, gyara zamansa yayi sannan yakira muhammad koda yakara waya akunne yace sorry muhammad gata ay yanzu nashigo ne,mika mata wayan yayi ta ansa hannunta narawa tamkar anmata dole tace hello! cikin fada kuwa yace wae baza ah bawa meenal wayanba ne bae rufe bakiba yaji tace ina wuni,bae amsataba kawae yace bawa mujaheed wayan mika masa wayan tayi jikinta asanyaye,tsaki yay ya anshi wayan yace to meye kuma,mujaheed nizaka rainawa hankali ina meenal take,da mamaki mujaheed yace bangane ba ayni haka raenawa hankalin bagata tanama maganaba kace tabani gata ni cikin haushin yamika mata wayan,koda takara wayan akunne sunan daya kirata dashine yasa zuciyarta rudani sweety yakara kiran sunanta, cikin sanyin muryanta tace na am dan shiru yayi sannan yace meyake damunkine kifadamin gaskiya,babu komae babu abinda yake damuna dama yamata tambayarne donyakarajin muryanta,bashi wayan shine kawae abinda yafurta tabashi wayan kuwa ta lula duniyar tunani shin towaye wannan kwalla taf a idanunta,yankewa tunaninta yayi jin mujaheed yayi sama da ita abakin kofa yasauketa yasaurin zura mata hijab dinta na sallah yakama hannunta suka fita harcikin mota yasakata sannan yakuma kiran muhammad amma vidio call ya aje mata wayan kan cinyarta yazauna gefe shima yazuba mata ido, ya allah koda suka hada ido tacikin waya kasa kuma kallonsa tayi dagashi se gajeren wando iya gwiwa,dakyar ta iya kakalo murmushi tace sannu yaya kana lpy baima jitaba saboda irin kallonda yake mata,cikin tuhuma yace ina wayanki kika kaeta?tayi shiru cikin jin haushin hakan yace badake nake maganaba ne, yaya bansan inda takeba wlh,yayi kyau bakisan inda takeba sam babu abinda yadameki saboda kinsamu freedom na yawo ko bakidamu da halinda zamu shigaba kullum zuciyata cikin fargaba take da tunani marasa dadi akanki daddy yakikkira kinki daga wayan karshe wayannaki akashe su nana harsun gaji dakiranki ma, ko awayan mujaheed base ki kiramuba wani irin haline kikeson daukane yanzu?
Kayi hkr yaya bazan sakeba tayi maganar idonta tafda kwallah zatayi kuka har mujaheed seda yayi mamakin yadda takewa muhammad magana,MEENAL! yakira sunanta zuciyarshi tabda tambayoyi kala kala, meyake damunki?yanzunma bata dagoba tace bakomae,sosae tabashi haushi kawae yakashe wayanshi ma,
Da mamaki mujaheed yace meenal meyasa zakiyi masa magana ahaka ne sokike yagane bakida lpy,tagirgiza masa kanta,to kada kikuma amsashi awannan mood din pls kisaki jikinki,yanzunma kae kawae tadaga masa yakama hannunta suka koma cikin hospital din se kallon ko ina take harda wae waye saboda time dinda aka shigo da ita cikin asibitin bata hayyacinta sun shiga room din datake zara tana zaune tayi tagumi tana ganinsu kuwa tasaki murmushi tace ya mujaheed ina kukajene ina nan har tsoro yasoma kamani,murmushin yamata shima yace nakaeta motane tayi waya da yayanta kinsan basusan abinda yafaruba bawanj guri tajeba ay, wae zara kinsan inda wayan meenal takene,tagirgiza masa kae alamun a ah, bewani zaunaba yay musu sallama yatafi don jiranshi su sameer sukeyi,
Tana kwance duk ta rame tabushe dakyar take bude idonta haka zama ma gagararta yakeyi saboda yunwa ta dagazata ruwane kawae take iya samu tasha abayi,numfashintama dakyar yake fita bata kara ganin mutuminba tundaga ranar hawayene kawae yakebimata fuska data lumshe idanunta lapiyayyaen abinci take hangowa tana hadiyar yawo,cikin wahalalliyar muryarta take cewa ya allah kadauki raena kozan huta dawannan ukubar sun tafi sun barni da yunwa ko kukama kasawa tayi,baccin wahale yadauketa kamar amafarki kuwa taji shigowan mutumin tabude ido ahankali taba wanan gardin mutumin shine dae yadawo hannunsa daukeda bindiga dakuma cup tayi saurin tashi zaune cikin tashin hankali take kallonsa harya karaso ya tsugunna agabanta, batare dayayi maganaba yamika mata cup din hannunsa, bamusu kuwa ta ansa fresh milk ce aciki batajira meze ceba takafa baki tas tashanyeta dataga hakan bematabama tasa hannu tana lashe kofin, yadda takeyi nema tabashi dry yay murmushi,cup din ya anshe yamika mata waya takuwa ansa takara akunne dukda hankalinta yanakan bindigar dayake nunata da ita,hello! tacikin wayan kuwa taji kukan wata mata tana cewa mimi ina fata dae basuyi miki komaeba nakasa bacci diyata narasa inda zan tsoma rayuwa, shiru meenal tayi saboda yadda kukan matan yake taba mata zuciya basuyimin komaeba tacewa matan, to nagode allah mimi kiyi hkr kinji allah ze kubutar dake kullum cikin addu ah muke yimiki, kasancewa meenal ba itabace mimi yasa hawaye zubuwa daga idanunta masu zafi kafin tayi magana kuwa ya anshe wayan yakashe tasoma binsa da kallon tsana,da murmushi yamike yace madarar dakikashace tasaki jin kwarin gwiwar yimin rashin kunya kiyi kome kikeso duka kwana nawane yarage miki aduniya,ficewa yayi abinsa,tabishi da harara sam tadena tsoron mutuwar ma ko kadan muryan matarne kawae yake mata yawo ajiki, mikewa tayi tayo alwala tazo tasona sallah abinta don ayanzu itace mafita agareta, tana idarwa tasoma rero karatun Alkur ani,
washe gari
Su sadiyane sukazo yiwa meenal sallama zasu tafi gida domin biki yakare jiya anmika ango dakinsa,duka dasu mom akazo da inty, gashi harda zara za ah tafi hakanne yasata samusu kuka wlh ita se ansallameta, mujaheed azuciyansa yace daman nasan za ah rina haka, lallabata yasomayi cewan tabari tadan sami sauki,mom tace a ah mujaheed kira doctor dole amata abinda takeso aitamayi har aka gama biki tana asibiti,zara tayi dry tace kinji mom itama banata bikin takeyi anan bah suduka sukasa dry kuwa banda mujaheed dayayi murmushi kawae yana kallonta ta tura baki gaba tana hararan zara,sunsha hira sosae sanan doctor yasallamesu suka tafi gida da murnarta se kallon gari take abinta. ...


TAKU A KULLUM NANA BMB.


08147110349
[7/28, 8:20 AM] Nana BMB: 💝💖💝💖
RABON KWADO....
BOOK 2

NA NANA BMB


page 11 -12
Koda suka karasa gidan kowa yanata shirin tafiya gida abinsa ita kuwa mimi tayi lamo tanata kallon gidan don yau ta taba zuwansa seda su zara suka gama shirinsu sannan tazauna gefen meenal tace to meenal zamu tafi sae allah yakaemu naki bikin muzo musha shagali,murmushi mimi tay batareda tadagoba tace hmmm,inty ma murmushin tayi tana kallonta,sosae tafiyar su zara tasa sukaji babu dadi ga mimi bata wani magana sedae kallo kawae gidan yayi shiru bakaman jiyaba wayar meenal inty tadauko tace meenal gawayanki koda naga miss calls dayawa sena kashe miki wayan tunda ya mujaheed yace bayason asan bakida lpy,murmushin karfin hali tayi mata ta ansa tana godiya tasoma juya wayan ahannunta yinin ranar inty tafuskanci meenal tacanza sam batason magana ko ana hira sedae tai murmushi, kasa jurewa tayi tace pls meenal menene yake damunkine sam bakyason magana yanzu murmushi tamata tace wlh babu abinda yake damuna, to ko inkira miki ya mujaheed?setabawa mimi dry tagirgiza mata kae tace a ah, tom shikenan muje mukwanta kikara hutawa anjima gidan ya sameer zamuje ku gaisa da amarya don shima yace gobe zaku wuce gida,
tunda mimi ta anshi wayan meenal takeson ganin abinda yake cikin wayan amma da security awayan dole takashe wayan ta ajiyeta,bayan ishah su inty suka tafi gidan sameer mujaheed yana driving dinsu mimi nagefenshi se inty abaya suna ta fira har suka karasa bakarya kam gidan sameer yahadu haka auntie salma matarsa tanada kirki sosae se nan nan take dasu tanatama mimi sannu don sameer yabata labarin komae koda yatambayi salma ina sameer tashaida masa ay yana bedroom dinsa, kae tsaye yawuce dakin nasa sukuma ancikasu dakayan ciye ciye,
Akwance yasamu sameer yana danna laptop dagashi se boxer murmushi yayi kawae yazauna kusa dashi yakae masa duka abaya kamar yasani kuwa yazille, yajuyo yazuba masa uwar harara,dry mujaheed yay donya fahimci abinda sameer yake nufi,hannunshi yahade guri daya yarike baki yace oh ni mujaheed shin sameer duka yaushe kasan zakin amarcin nan ne dazaka dinga turomin baki harda hararata munzo mun katsema jin dadi koh inkayi hakuri dagayau bazaka sake ganinaba dakudi seka nemeni,
murmushi sameer yay mesauti yagyara kwanciyarsa yajuyo yana kallonsa yaharde hannayensa abayan kansa yace mujaheed bazaka ganeba ne yau nakeson fara cin amarcina amma don iskanci irinnaka karasa sanda zaka kawomin su inty seda daddare don mugunta irintaka duka sameer yakae masa saboda dariyar dayakeyi masa dan iska ainasan dama dabiyu kaimin haka,saeda nujaheed yay dariyarsa son ransa sanaan ya tsagaita yace kace amarya wanaka takeyi shiyasa naganka duk ba adaidaeba,kallon kafafun sameer yasomayi har zuwa sama,yakuwasa hannu yature masa fuka yace munafiki mekakeson kallone juyawa yay yakifa akwance abinsa yana dariya shima,
Jinjina kae mujaheed yayi yace tabdijan babbabar magana dole ka kasa fitowa kagaisa dasu inty wlh amarya tarufawa kanta asiri tabada kae bori yahau,mintsininshi sameer yafara yana cewa allah yashiryaka mujaheed bansan sanda ka kara zama hakaba duk jarabata ay ban kaekaba tundani bana rawar sanyi dashan magani ehe! kamakalewa 'yar yarinya ai meenal zatae fama da ..... Saurin toshe masa baki mujaheed yayi yace to mara mutumci naji bari nabarma dakin kasan yacca zakayi wlh kafito don bayanzu zamu tafiba, cije baki sameer yay yana girgiza kae yace habawa mujaheed zan ramane,
Mujaheed yana fitowa yasamu salma takunna musu TV sunata kallo abinsu inty tana ganinshi tace kae ya mujaheed harka fito badae tunyanzu zamu tafibah, girgiza mata kansa yayi alamun a ah yana murmushi haka salma itama murmushin jin dadi tayi jin bayanzu zasu tafiba mujaheed na ankare da ita azuciyansa yana cewa habawa yarinya zakiyi bayani ne,fitowansa da dan jumawa sameer yafito shima yazumbula babbar rigarsa ta daurin aure se muzurae yake yazauna kujeranda mujaheed kezaune wanda yaketa faman dry kasa kasa, gaisawa sukayi yanata ma mimi sannu da jiki yalura da dariyar da mujaheed kemasa matsawa yafarayi kusa dashi mujaheed namatsawa shima yana kara matsawa harya kureshi akarshen kujeran seya seya mike yay waje yana murmushi yasan yanzu ze iya kunyatashi gaban kannensa,
Duka hankalinsu nakan TV basusan mesukeyiba sameer yay dry yamike yabi bayanshi yana cewa karamin dan iska dakatsaya kaga meze faru,haka kawae kazomin gida kahanani sakewa,
Awaje suka cigaba dahirarsu gwanin burgewa har lokaci yajama basu saniba intyce tafito tanata kwala musu kira takuwa hangosu zaune saman mota kiran da take musune yasa dukansu suka zuba mata idanu tayi tace ya mujaheed mom ce tace mutaho gida dare yayi,
Cikin masifa sameer yace wani irin shashancine wannan zaki dinga yimana irin wanan kiran ni nazacima wani abune yafaru wlh sim sim itadae takoma ciki, murmushi mujaheed yay yazo dafda kunnensa yace kwantarda hankalinka aibacazatai dakae wani abu yasamu amaryaba daze hanaka cin amarcinka yau bare kasauke mata kwandon masifa yana gama fadin hakan yay saurin dirowa akan motan yay ciki tunkan sameer yay magana, kwafa yayi kuwa yabishi abaya kayan azziki salma tahadawa su inty suna shirin tafiya sameer yace wae meenal meke damunkine naga kinyi shiru kawae abinki, caraf inty tace ay tunda tadawo haka take bamagana gida takeso ay,kallon inty tayi tace allah sis bagida nakesoba kawae maganan ne baya kaena,sameer yay murmushi yacewa mujaheed to inkun koma yaushe zaka maidata gidannasu kenan,ay mimi tanajin haka taji cikinta yabada wani kara jin ashema ba agidansu ya mujaheed takeba, tabdijan babbar magana!
Maganar mujaheed dinne ya katse mata tunani yana cewa muna komawa bawani jumawa zamu tafi ay hutun nasu yakusa karewa sunkusa komawa school don muhammad ma yanata azalzalata,lebe sameer yarike a ah kaji masu kanwa fah jarababbe yanzu dae munji sit abinmu tunda yabar kasar saura shekara nawa yadawone,mujaheed yay dariya yace kaidae bari masifaffen bah saura shekara daya da rabi yadawo, time dinda yashekara biyu ba irin faman dabanyi dashiba yadawo gida yay hutu amma yaki yace wae inya dawo baze kuma komawa ba,sameer yace to kada yakoma mana shifa yayiwa

2 / 9