Author : Halima Abdullahi K. Mashi Category : Thnovels
ta gama aman sannan ya karasa
da ita ta wanke baki da fuska a cikin bayin. Ya
ce,Ba ki d lfy ne?Ta soma Hawaye, Ka gani ko
Babn Walid,kila fa ciki ne da ni.Tun wancan Satin
ya kamata in ga al'aldata amma shiru. Ya ce, To
menene na kuka? Yi shiru,Allah ya inganta.Ta
harare shi Dana fa bai shekara ba.Ya ce,To dole
ne sai danki ya shekara sannan Allah zai baki
wata kyautar? Ta soma kuka,Ni dai zan je a
ciremin ne. ya hade fuska,Ban yarda da haka ba.
Ganin ta tada hnklnta tana cewa "Dama Hjyrsu ta
ce mata tabi a hankalu ta ki ji gashi nan yanzun
tana da wani ciki. Ya ce To kada ki damu kin ji?
Zamu je asibtin dn a tabbatar da cikin kafin a san
abnyi. Da za suje asibiti shi ne ya dage sai da
tayi wanka,dn d farko kaca-kaca ta dauko
mayafi, ya ce sai tayi wanka ta canza tufafi.
Gwajin farko ya tabbata tana da ciki,nan ta shiga
kuka. shi kanshi ya damu domin bai so ciki
yanzun ba.A son ranahi sai an yaye yaron kafin
wani cikin. Amma ba shi da ra'ayin
zubarwa,nashi ganin kyautar Allah ce,dn haka ya
amsa ya kuma gode. Ya lallashe ta da cewa,ta yi
hkr su amshi kyautar Allah dn haka wani na nema
da kudi bai samu ba. likita ya ce,Kada ta
damu,taci gaba da bai wa danta abnci tana hada
mishi da nonon,a hnkli zata yaye shi bana farat
daya ba. Bayan ya kaita gida ya kuma
lallashenta,saiya nufi gurin Umma. Bayan sun
gaisa,ta tambayi iyalanshi ya ce "Daga asibiti ma
muke da Bishira." Umma ta dube shi da
sauri,Waye ba lfy? ya ce, Ita ce.Sai kuka ma take
yi wai dn an ce tana da ciki. Umma ta ce, Ikon
Allah, to Allah ya inganta.Sai dai kuma kada
Walid ya sha ciki. Abba ya ce,likiya ma ya yi
mata bayanin yadda za ta yi masa,hr ta janye shi
daga nono cikin hikima.Umma ta ce, Da za ta
yarda ma an kawo mana shi nan. ya ce,Ai dama
nan zan kawo shi da zarar an yaye shi Umma.
Sam bai fada ma Bishira nufinshi na baiwa Umma
Walid ba,dn yasan ba zata ta6a laminta ba.Sai
dai itama tasan dole hakan zai yi. Don haka ta
garzaya gurin Umman Bashir ta shaida mata
cewa sunje asibiti,dk ta fada mata komai,sannan
ta ce ita danta take tunani kada ya dauka ya
kawo wa Ummarshi ita ma a mallake mata yaro.
Umman Bashir Ta ce Wannan a zaune take,sai
dai in ko ba a kai shi ba.Amma ki bari daga kin
kula ya daina damuwa da nonon ki janye shi,zan
zo in taho da shi wurina. Bishira taji dadi tare da
cewa, Hakan dai yafi. Sabuwar kazanta ta
samu,Bishira dk abn bi bangon daki an tofe da
yawu.Rashin wanka sabo,kai abn nata sai
addu'a. Ibada kuwa ba a mgn,domin dai tuni ta
aje Sallah a gefe,Azumi dai tana yi amma in ta
sha bata ramawa.Allah ya shirye wanda ya 6ata.
Abba ya dai yanzun tuni ya yafe abincin
gidansa,matsawar ba shi da kanshi ya girka
ba,don kuwa dama can shi mutum ne mai
kyankyani. In zata fita takan wanke kafafunta ta
dauki kaya ta saka,sai ka rantse tayi
wanka.Amma da zata matso kusa da kai,nan za
ka ji kauri na tashu da karni da kuma wari. Dole
ya hkr da laluranshi ta aure a gurinta,domin in
yaje shimfidarta ba zata ki ba,amma wari da
zarni suna hana shi yin komai cikin nutsuwa. In
kuma dakinshi ya kirata ko bata kwana ciki ba
har gari ya waye yana jin warin jikinta a
shimfidarshi don haka lokuta da yawa yake
hakura da ita. *********** . Ummi tana kwance
kan gadonta,yayin da Khadija da Safiyya suke
zaune bakin gadon Safiyyan wadda ke kallon
Ummi. Hirar masoyinta take basu,Safiyya bata ko
gajiya da zancensshi. Khadija ta ce,ita ma da
zata taho har kuka nata Saurayin ya yi. Sai lkcn
Ummi ta dube su,"kuka Khadija?Khadijata
ce,"Riris Kuwa. Ummi ta ce, Hu'um ba namijin shi
yasa nike da za6i a kan irin mijin da zan aura.
Safiyya ta ce,"ke banza,dk cikin so ne. Ummi ta
ce Ban damu da sai namiji yaso ni ba,in dai ya
tara abubuwan da nake so ga namiji to zan yi
amfani da kasantuwata 'ya mace in koya mishi
Sona. Khadija ta tashi ta dawo kusa da Ummi,Kin
san me ki ke fada?Koda yake sanar damu yadda
ki ke son mijinki ya kasance? Ummi ta ce "Na
farko mai son Addini,Mai Ilimi duka 2,mai hakuru
,sannan yana da saurin fushi,mai kuzari da
kwarjini. Ma"abocin tsafta da tsantseni,wandadk
tufafin da yasa sai sun kar6e shi,mai biyayya ga
iyayensa,sannanmai kula da gidansa,baki mai
tsare gida,ga yawan Ibada, Safiyya da khadija
suka kwashe d dry,Khadija ta ce, Ina za ki samu
dk mai wadannan lissafin da ki ka yi??? Safiyya
ta ce, Kuma fa bata gama lissafin ba ke ba ki ji
ana cewa dan Adam tara yake bai cika goma ba?
Ummi ta ce,Akwai shi,Ya Abbanmu haka
Halayansa suke. Yanzu ma da ni ke lissafin shi
na ke kallo a idona.Khadija ta ce,To ba dan
uwanki ba ne da shi kenan kin samu a gida.Ummi
ta ce,Wuu fitina Road,wannan ya mugun tsanata,
ina son dai me irin halayarshi ds
dabi'unsa.Khadija ta ce,Har da kamaninsa? Ummi
ta ce,sosai ma. Saitaga sun sa dry.Safiyya ta ce,
Malma shi ki ke so,kuma dk yanda a ka yi ba
shakikin ki ba ne,da aure a tsananinku. Umma
tayi Shiru tana kallonsu,Khadija ta ce,Habiba
kenan,wai har saurin fushinshi tana so. Ummi ta
6ata rai tare da cewa,Tunda kun kasa fahimtata
shi kenan.Ya zan yi in ce ina son Ya Abba yana
da matarsa? SAfiyya ta ce,ke dai in da aure
Tsakaninku kada ki tsaya "ZURFIN CIKI, kizo a
karshe kina da kin sani. Ummi ta ce,A bar
zancen. 32... Sai dai kuma a daran ranar ta
tsinduma duniyar tunani.Tabbas zuciyarta da
shisshiga take,tunda ta rasa wanda zata so sai
Ya Abba. Wanda ya yi mata muguwar tsana.Afili
ta ce,Duk kauce-kauce da kewaye-kewaye ba za
su kai ni ba,Ya Abba nake so. Hawaye Suka
soma sintiri daga idanunta. Wannan lkcn ziyarar
da yazo Abba da Umma d Tsohuwa da Alhj
Karami dk suka zo. Dadi ya kashe Ummi,ta rasa
jikin wanda zata fara fadawa don dadi. Alhj
karami ta soma kamkamewa sannan
Umma,Tsohuwa kam ai tana manne jikinta hr
suka zo tafiya.Shi ko Ya Abba yanzun kunyarshi
take ji,dn haka tunda suka gaisa mgn bata kara
hada su ba. Sai dai jife-jife suna satar kallon
juna,in sun hada ido sai ya dan daure
fuska.Safiyya da khadija sun gaisa da su sannan
sun yaba da yadda a ke ji da Ummi. Da za su tafi
kuwa Ummi kuka Tsohuwa kuka,sai da Abba ya
ce ba za a sake zuwa da su ba,Sannan Ummi tayi
shiru.Sun tafi sun barta d kewarsu,Kamar yadda
suma suka tafi suna kewarta. ********** . Bishira
da kanta ta dauki Walid ta kai ma Umman
Bashir,domin ta san zai kai ma Ummanshi ne.
Abba ya rufe ta da fada lkcn d y tambayi dan ta
ce ta yaye shi ta kai ma Umman Bashir. Ya ce To
je ki dauko mn yarona,dn ba can nayi niyyar kai
shi ba,Ta rike kugu,kaje mana da kanka,tunda ba
ka son zamn danka hannun mahaifiyarka to ni ba
zan yi saken da Mahaifiyarka tayi ba a ka raba ta
da danta ina fata ka fahimci karatuna? Kallo
kurum ya bita da shi,sannan yaja tsaki tare da
cewa,Dube ki kmr wata Bauna,jiki sai tsami yake.
Ta ce,Eh dk abn da zaka ce kace. Ya juya ya fita
rai 6ace. Umma ya Samu ya fada mata, ta ce, To
menene na bata rai Abba? Can din da nan ba dk
daya ba ne? ai ba za su cutar da shi ba. Ya ce, ki
fahimce ni Umma,ba ina nufin zai cutu ba
ne,amma can da yara kanana,nan kuma babu.
Sannan......... ...... Sai kuma ya yi shiru tare d
cewa,Shi kenan. Umma ta ce,Yauwa bana son
kana daga murya kan abn da bai kai ya kawo ba.
Allah ya raya mana shi ya kuma sauketa lfy.
Abba Ya ce Ameen. Gidan (T.V)sun kira Abba sun
masa (intervier)da kusan wata 2,dmn ya cire ran
samun akin, ko da yaje suka ce sun dauke shi
aiki. Abn d yasa suka yi jinkiri daukarshi,suna
canza tsarukan aikin ne sannan sun sake
tantance ma'aikatansu. Litinin Abba ya soma
zuwa aiki kmr yadda a ka bukata,dakin watsa
labarai a ka kai Abba. Sam bai samu matsala
ba,dk d shi na mai yawan surutu ba ne,amma a
cikin sati 1 ya goge da aikin,km an yaba da yadda
yake watso labarai. Yana yi da Hausa minti sha
biyar da turanci minti sha biyar,ana sakawa karfe
7 na yamma. Abba ya kama aiki cikin sa'a nan
da nam sai farin jini cikin abn d bai fi wata ba ya
nemi izinin a bashi fili koda mint 15 ne don
gabatar da wani fili da ya yi masu don matasa.
filin yana kiran shugabannin matasa na
unguwanni suna hira da su akan halin da matasa
suke ciki na shaye- shaye da sace-sace da kuma
rashin sana'a. Da turanci a ke shirin,sannan a kan
baiwa sauran matasa na gida su bugo waya su
fadi nasu ra'ayin,game da abin da ya kawo
hakan,da kuma hanyoyin da za a bi don magance
su. Haka nan ya kan samu lkc ya shiga cikin
matasan musamman ma su shaye-shayen da
marasa sana'a dn jin ra"ayoyinsu,da dalilan
fadawarsu cikin harkar. Kafin wani lkc filin ya yi
suna kuma kullum yakan tallata filin kan cewa ya
kamata Gwamnati ta dauki nauyi filin don yana
taimakawa mata wurin inganta rayuwar matasa.
Cikin ikon Allah sai gashi Gwamnati ta yaba da
filin,ta dauki nauyin shirin kuma an sa shi hr
fannin Radiyo. Lallai Abba ya shigo da kafar
dama,Sannan hukumar gidan Radiyo tayi Matukar
farin ciki da zuwan Idris Aminu Idris,wannan
Ma'aikata. Sannan sai Abba ya zama wani sabon
tauraro wurin Al'umma,dk in da a ka ganshi ya
zama abn kallo. Matsalar shi daya gidanshi,in ka
ganshi a waje Sam ba za a kayi tsammanin haka
zaka samu gidanshi ba,Dattin ya karu,musamman
da ya kasance yanzun ba shi da lkcn kanshi
ballatana ya yi sammakon share gidan. Wankinshi
mai kaiwa yake yi,haka nan nasu ya ce ta dinga
kaiwa makota gidan wanki. Amma kafin ta hada
ta kai aiki ne ita dai tayi kallo ko a shiga makota
hira. Sam Abba ko adreshin Zai bada ya
gwammace ya bada na gidansu Ummanshi dn ba
ya so aje gidanshi ************* . Kwanci tashi
Ummi suna ta fana da jarabawa zuwa (SS2) cikin
ikon Allah suka gama. ranar da aka yi musu hutu
kamar ta sani bata tsaya jiran Abba ba,Ta nufo
gida. Shi kuwa lkcn suna kici-kicin kai Bishira
asibiti zata haihu,amma yana sane da cewa yay
Ummi zata dawo kuma hnklinshi na can. Motar
wani Salis Abokin aikinsa ya aro ya kai su
asibitin ita d Ummanashi. Bayan ya ba d dk wani
abu da suke bukata ya ce Umma za shi dauko
ummi. Umma ta ce,Ka barta tukunna in matarka
ta sauka lfy gobe sai kaje tunda tana mkrnt ne.
Ya yi-ya yi Umma ta ki,dole ya hkr. sai bayan
la'asar sannan ta haihu,Nurse ce ta zo tayi musu
albishiri an samu 'ya mace. Bayan an kintsa
uwar,sannan a ka kaita dakin hutu,su kuma a ka
kawo musu 'yar.Nurse din da ta kawo 'yar ta ce
d Umma ke ce Mamanta? Umma ta ce,'Eh."Nursr
din ta ce "kazantar yarinyar tayi yawa,kafin ta
haihu sai da likita ya korata ta yi wanka,muka yi
mata aski ko'ina jinkinta datti. Gsky Mama
mijinta yana kokari,yanzun kuje ku dafa ruwan
dumi ku kawo mata tayi wanka. Abba ya yi tsaki
ya ce, kin ji ko Umma,Allah ya kara.Umma ta
ce,Yanzun kaje gida ka dauki babban filas dina ka
shiga wurin Umman Bashir ka ce Mata ta dafo
ruwan Zafi,daga nan ma sa ji haihuwar. Yana
shiga gidan tun daga zaure ya jiyo Muryar
Tsohuwa tana cewa,Naji shiru-shiru kin ga dai hr
yanzu. Yana saka kafa a tsakar gidan muryar
Ummi ta daki dodon kunnanshi.in da ta ce,Kila
kuma ta haihu yanzun. jinin jikinshi ya tsinke dn
jin Muryae. Ya nufi dakin.Tana zaune tana shan
rake. Ya dubeta, ita ma shi take kallo dn tunda ta
diro ba wanda take muradin Gani irin shi,cikin
sanyi murya ya ce,Ummi ke da wa ki ka taho? Ta
sunkuyar da kai,Ni da wasu 'yan mkrntrmu ne
muka dawo. Ya ce '"Good,tashi ki dafa ruwan zafi
ki zuba a babban flask. ya dubi Tsohuwa da take
ta tambayarshi ko mai dakin nashi ta sauka? Ya
ce, Eh ta haifi 'ya mace. Tsohuwa cikin takaici ta
ce,Sai yanzu kaga damar bani amsa?Dan
walakanci kawai? Kai mai sunan Malam ka gyara
halinka. Abba ya ce,Yi hkr Tsohuwa dk na gaji
ne,Nan kuma ina yi wa Ummi mgn. Ta ce kana
mata fadan ka dai. Ya ce,Tsohuwa wai ni hr
yanzun ba zan wanku a wurink ba game da
Ummi? ta ce, Ina fa zaka wanku?Har abada mai
sunan Malam kai ba me kaunar takwara bane. .
Yace to naji a bar maganar yanzu dai kishiyarki
ta haihu.an samu ya mace.tace Allah ya raya
mana. Yana jingine da bango yana kallon ummi
tana ta shige da ficen daura ruwan zafi.komai
cikin tsafta da natsuwa take yi. Sai da tasa
ruwan zafi ta wanke flask din kasancewar anjima
ba'ayi amfani dashi ba.ta tafasa ruwan tazo ta
bashi,ya ciro wayarshi ya mika mata. "sa min a
caji naga nepa sun kawo wuta" ummi ta jona
waya sannan ta ci gaba da girkin dare don tasan
Alhaji bai cika son wani abu da dare ba sabanin
tuwo. Ta gama wanka sannan tayi sallar
magariba tana kwance gadon tsohuwa tana
tunanin abba. Tsohuwa nata lazimi in tayi
magariba bata tashi sai tayi isha sannan taci
abinci.ummi ta tuna wayar da yaya abba ya bata
ajiya. Da sauri ta tashi tare da cewa "ke tsohuwar
nan anzo tayaki hira kin share mutane" ta mike
ta nufi daki ta dauko wayar ta kunna HEHE KIN
MANTA YAYA ABBA KENAN?" Sakwanni ne sukai
ta go slown shigowa sannan sai kira tashin farko
data daga wayar muryar mace taji, ta ce "dawa
nake magana" wadda ta kira ta ce "ina mai
wayar?" ummi tace "dq matarshi kike magana,ke
din wacece?" waccac n ta ce "in yazo ki
tambayeshi? yasan me lambar." nan da nan sai
ummi ta samu kanta yana juyawa,tayi tsakita
kashe.ta shiga duba sakonnin da yawansu na
mata ne masu sonshi,daidaikune na maza masu
nuna yabawar aikinsa.hankalin ummi ya tashi
ganin yadda mata suke farautar abinda take
tsananin so.ta kashe wayar cike da nadamar
kunnata Hankalin Ummi ta samu kanta yana
juyawa,tayi tsaki ta kashe.Ta shiga duba
sakonnin da yawansu na mata ne ma su
sonshi,dai-daiku ne na maza ma su nuna
yabawar aikinsu. Hankalin Ummi ya tashi,ganin
yadda mata suke farauta abnda take tsananin So.
Ta kashe wayar cike fa nadamar kunnata. Sintiri
ta dinga yi a tsakar dakin,Sallamarshi ce ta, katse
ta.Ta amsa ciki,sannan ta zauna ba tare da ta
kalle shi ba. Ya ce,Bani wayata da abinci 'yan
asibiti. Ta mike ta dauko masa abncin,sannan ta
bashi wayar.sai dai tana yin komai ne fuskarta
daure. Ya ce,Lafiya na ganki wani iri?ta dago ido
ta kalle shi,ta sake tsuke fuska. lfy lau.Ya ce,shi
kenan na tafi Sam bata tanka ba. Yana fita ta
mike a kujera,so takeyi a lkcn ta samu makanta
mafita,shin ko dai ta tare shi ne ta fada masa?
wata zuciyar ta ce,In ko ya dinga kwallo da ke
sai kin rasa mai cetonki. Ta tashi tare da
cewa,Bari kawai in fada ma Tsohuwa.Zuciyarta ta
sake rayawa.Tsohuwa fa ba zata yarda ba, domin
kullum tana bada shaidar tsanar da Ya Abba ya
mata,ta koma ta zauna. Sai ta samu kanta da
fashewa d kuka,tana fadin wannan wace irin fitina
ce ta same ni?me yasa zcyt ke son tozarta ni?
Me yasa zata so wanda ya tsane ta?Ta mike ta
shige uwar daka. Gado ta hau tana son ta lallashi
zcyrta,dn ta daina son Ya Abba. Shi kuma yana
tafe a mashin zcyrshi na mitar bata gaji da ganin
Ummi ba,yadda take ta kai kawo ya ke gani a
idonshi. Lkcn da ya kai musu abnci me jego ta
gyare,dama ta zubar d jini ne shi yasa suka ki
sallamarta,sukace sai da Safe. Ya samu kannanta
sun zo da wata 'yar Babnsu.Sun gaisa an yi 'yar
hira sannan suka ta fi lkcn ya dauki 'yar ya yi
mata kallon sosai. Ya dubi Umma kin san
yarinyar nan da wa take min kama?Ta ce,A'a.
Bishira ta tsare shi da ido,ya ce lkcn d Ummi na
karamarta sak wannan. Umma ta ce,Kana nufun
d Ummi take kama?ya ce,"Eh,Bishira ba kunya ta
ce,Allah ya kyauta ni 'yata bata kama da wata
can wai ummi. Umma tayi saurin cewa,Dama
zolayarki yake ba suyi kama ba.Shi kuma ya
kalleta.Ko ki so ko kada ki so yarinyar nan sak
take kama d Ummi. Ya mika ma Umma ita,yana
ci gaba da fadin Maman Walid kina bani
mmki,kina zaton zan ki raba 'ya'yanku d Ummi?
Ya girgiza kai"Sun hadu hr abada ,domin in kin
tsaga jikin 'ya'yanki dole za ki ga jinin Ummi. to
ya ya ma ki ke tsammanin zan so wanda ba ya
son Ummi? Ta ce, "Oho! Ni ba ka sona kenan?To
in da na gode ma Allah dk dyniya ta san cewa
Ummi bata kaunarka.dk da kana wanta.Ba ita ba
ce silar kariyarka?ko an kashe ka ma bata da
asara. Umma ta ce,'Abba jeka ban son in kuma
jin bakinka in na isa. / ZURFIN CIKI book 2 part 7
ZURFIN CIKI book 2 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:16
Ta samu an saka ranar auren fati da saurayinta
Fahat,nan fa Alhj ya ce dama ke ni ke jira uwata
ki dawo. A masu sonki ki fito da daya a hada
auranku da 'yar uwarki Fati. Hankalin Ummi ya yi
matukar tashi,ranar kasacin