Author : Afrah Category : Home Of Novels
dadi, at last zata ga yaya habun su, tace Allah ya kaimu.
Har yamma neena na sashen mami, suna kicin da zarah, abba yasa ta hada masa danwake, amma bata iya ba, sai tayi inviting neena ta taya ta, suna gama kwabin su, amir ya shigo da gudu, yaja hannun neena, anty anty, zo muje papa dina ya zo, neena tace ka bari muje anjima little master, amir ya dunga janta yana cewa noo noo muje yanzu, zarah sai dariya take musu.
Prince duk ya gaji da kwanciyar, ji yake kamar an dauke masa wani dutse mai nauyi daga kansa, tsana kyama da dana sani duk yake akan ikram.
Amir ya shigo da gudu, papa papa, ya fada akan jikin prince, prince ya rungume shi, my boy kaine haka, ka zama big boy fa, amir yayi dariya yace papa, ka manta dani, kullum anty neena sai tace min zaka zo, zaka zo, amma baka zo ba, prince ya dago kansa, ya kalli neena dake tsaye, ta kura masa ido, gaba daya tausayin shi take, yadda duk ya rame.
Prince ya kura mata ido shima, gaba daya ta canza, ta kara girma tayi wani irin kyau, yayi saurin dauke idon sa, ya shafa kan amir my boy am sorry koh, ka yafe wa papa, amir yace na yafe maka papa, sukayi hugging junan su.neena tayi murmushi itama.
Da daddare mum ta zauna kusa da prince, ta riko hannun sa, ka yafe min na'im duk ni na jawo maka....
Prince ya katse ta , noo mum bake bace, haka Allah ya kaddara, yayaB ce ta shigo tana fadin ina angon ikram?,
Mum tace yayaB bama son jin sunan nan a gidan nan, yayaB ta zauna itama, tace sannu na'im, prince ya kada mata kai, ta kalli mum , yanzu ya za'ayi da auren?
Kinsan dai ba sakin ta yayi ba, mum tace sai gobe akayi maganar dasu dad dinsu, yayaB tace hakane, sannan ta mike, su na'im gara dai a maida jiki, dan jibi sallah, kadan fito da fasali, amma dai ko abinci bata baka ma ko?, prince ya mike yana kumbure fuska, kije yayaB ki tafi hakanan, surutun nan naki zai sani ciwon kai, yayaB na dariya ta fita, mum ta mike itama, inshaAllah bazan sake matsa maka da maganar aure ba, prince yace mum kada ki dauki wannan al'amarin ya faru ne saboda ke, Allah ne ya kaddara zai faru, mum tace toh my son, ka kwanta kayi barci ka huta.
Neena a kicin, ta hada wa amir hot milk dinshi, zuby ta shigo daukar ruwa, ta dauki roban hot milk din da yayi ragowa, yau dai rabona ne, neena tayi saurin kwacewa, anty zuby akwai mai shi, zuby ta tsaya kallon neena, da mamaki, dan ita take bawa sauran ko ta kai wa deeja, toh yau koma wa zata bawa?,
Zuby tace neena na waye, neena ta shiga zare zaren ido, uhm uhm na na, ya........prince
Zuby ta kalle ta baki bude, ya prince.?? Zata kara magana, mum ta kwala mata kira..
Ta fita da sauri, neena ta sauke ajiyar zuciya.
Sannan ta dauki cups din guda biyu ta fita.
Ta kaiwa amir nashi, sannan ta zauna da dayan ta rasa ya zatayi ta kai wa prince, amir yace anty wannan naki ne? Kisha mana kada yayi sanyi.
Neena ta mike, ba nawa bane, ina zuwa little master, ta fice da sauri.
Tazo bakin kofar dakin ta tsaya, sai dataji kamar wani na tahuwa tayi saurin bude kofar ta shiga.
A kwance ta iske shi, yana karatun wani novel, yana jin bude dakin ya kalli kofar, yaga neena a tsaye.
Neena da kyal take daga kafar ta, prince ya mike ya zauna, yace lafiya?
Neena ta miko masa cup din hot milk, wannan na kawo maka, prince ya dan kalle ta, ya miko hannu zai amsa, neena tace da zafi, prince ya nuna mata kusa dashi, zauna, neena ta kasa gardama dasshi dan tausaya masa da takeyi.
Ta zauna, prince yace sai ki bani nasha , tunda ke baya miki zafi a hannun, neena ta kalle shi, taga ita yake kallo shima, tayi saurin dauke idon ta, tace toh.
Prince yayi mamakin ta, ta kuwa miko masa cup din a baki, amma bata bari sun hada ido ba, yakai bakin sa yasha, wani dadi yaji sosai, baiso yasha dayawa ba, amma hakanan ya samu kansa dashan madarar sosai, yana sha yana kallon neena.
Har saida madarar ta kare sannan neena ta mike, bata lura da akwai ruwa a kasa kusa da ita, sai dai taji lema a kasan, ruwan ya rube, skirt dinta ya tadiye ta, ta fadii luu akan gadon, kuma a jikin prince.
Gabadaya sai da sukaji wani yarrr, neena ta kasa tabuka komai, shi kuwa prince , wani yanayi ya shiga, kirjinsa na bugawa da sauri, har neena sai data ji ma....ta kalle shi da sauri, zaton ta ciwon sane, ta mike da sauri.., tana cewa badai jikin bane ko? Prince ya girgiza mata kai, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta dauki cup dinta ta fice...
Aka°•○sultana
[8/9, 8:44 AM] .: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
_*YAR*_
🎃 *TALAKAWA*🎃
By→afrah
Episode→1⃣0⃣1⃣
To
→1⃣0⃣2⃣
Washegari da safe, duka family ana falo, neena da amir sun tafi school.
Dad ya gyara zaman sa yace, na'im ya jikin naka?
Prince yace da sauki dad.
YayaB tace ni yanzu maganar matarsa za'ayi, mum tace dazun munyi waya dama mummy din ikram din, ta bada hakuri sosai, tace bama da sanin ta bane, ikram ta aikata wannan danyen aikin.yanzu ma halin da take ciki ya ishe ta ishara, dan suna asibitin mahaukata..
Duka falon aka hau salati, prince dai dauke kai yayi kawai, shi da zasu taimaka masa ma dasun daina ko ambatar sunan ta.
Abba yace ashsha, Allah ya kara tsarewa, ni ina ganin mu barwa na'im komai a hannunsa, idan yaji zai iya yafe mata suci gaba da auren toh, idan kuma ya gaji sai ya bata takardarta.
Dad yace gaskiyane, yayaB tace, zaman na'im da wannan jahilar yarinyar ya kare...
Mum tace kwarai kuwa, gaskiya bazan sake yarda a kara cutar min da daba..
Mami tace nima dai ina ganin rabuwar zata fi.
Dad yace kudai ina ruwan a ciki, miji da matarsa..
Abba ya kalli prince, na'im kaje kayi shawara kafin gobe kaji.
Prince ya kada kai,ya mike ya fita, mum ta bisa da kallo, kodai bai dawo hankalinsa, miye abun tunani aciki, kawai ya bawa ikram saki kowa ma ya huta.
Ranar gaba daya neena na school, sai da yamma ta dawo, cikin sauri ta shirya, ta shiga dakin mum, ta sanar mata zuwa gaida yaya habu, dan ya iso ranar daga jordan.
Amir yayi yayi ta tafi dashi amma taki, dan motar haya zata shiga.
Cikin murna ta shigo gidan, salamu alaikum, ina babban yayan yake?
Umma da sadeeq suka fito, yayi wani haske, ya kara kyau sosai, ya kara wayewa, ga kayan jikinshi ma sun mutukar amsar sa, ya aje kasumba, sai murmushi yake sakarwa neena, shima din ba karamin ganin girman ta yayi ba, dan ma zuby na aika masa pics dinsu.
Neena ta ware idanun ta, umman waye wannan arab man din?
Umman tayi dariya, waye kuwa, yayankine.
Neena ta rike kugun ta, like seriously? , yayana kaine kuwa?
Sadeeq yayi dariya, kaji yarinyar nan, harkin ma manta da yayan naki kenan?,
Neena tayi dariya tayi saurin zuwa ta rungume sa, well come back yayan, sadeeq yayi murmushi yace my sis kin ganki kuwa, kinga yadda kika koma yan mata.
Neena ta rufe fuskarta da tafin hannun ta, kai yaya ni har yanzu yarinya ce ko umma?
Umma na shiga daki tace, ni rabani da shiga karyayyakin ki,
Neena ta riko hannun sadeeq, muje ka bani tsaraba ta.
Sun shiga dakin umma, sai fira sukeyi, cikin nishadi da barkwanci.
Neena ta matsa wa sadeeq sai ya bata tsarabar ta, yace kin cika damun mutum wallahi, oya jawo min akwatin can.
Neena cikin zumudi ta jawo ta kawo masa a gaban sa, ya bude ya ciro wasu laces guda biyu da set din sarka da yan kunne masu tsadar gaske, ya mikawa umma.
Umma tace harda ni kuma, toh an gode Allah yayi albarka.
Ya ciro wasu materials guda uku, da arebians gowns guda biyu, sai indian set of yan kunne da sarka, sai waya kirar samsung A4.
Neena tace woah wooah , yaya duk nawa ne,?
Sadeeq ya harareta, yace ga naki, materials daya, set din yan kunne da kuma waya A4 , neena ta daka tsallen murna, wayyo yaya nagode...
Sadeeq ya dan yage muryar sa, wannan na inlaw dinki ne, da zara'u..
Neena tace woow sun gode sosai, amma zaka zo gaida su dad ko?
Sadeeq yace eh, nama kirasu na sanar dasu dawowa ta, faruk yace deeja ta haihu, yaushe ne sunan ma?
Neena tace saura kwana uku.
Umma tace ina ta cewa nazo barka, amma kuma sai ga, shamsiyar , jamila ta haihu itama, ina zuwa tayasu aiki.
Neena tace ba damuwa ai, zan fadawa su mamin.
Sunsha fira sosai, sai karfe bakwai neena ta baro gidan, dan gobe sallah, kuma mum tace ta dawo.
Mai taxi ya ajiye ta a gaban gate, ta biyasa kudin sa ta shigo, ta gaida mai gadi, tayi ta bayan gidan.
Hango ta yayi tana tahuwa cikin tafiyarta mai daukar hankali, prince ya kura mata, daga inaa take ?
Ita neena bata ma san yana ta wajen ba, sai tafiyarta takeyi, dauke da ledojin kayan da sadeeq ya basu, sai murna takeyi yayanta ya dawo, kuma har waya ya siya mata.
Bata ankara ba , Sai dai kawai taji an jawo hannun ta, ba karamin tsorata tayi ba.
, jikin bango ya jinginar da ita, ta kware baki ta saki ihuuu, ga wurin duhu ya mamaye bata ganin kowa sai inuwa.
Wayyooooo,ta furta a tsorace..... taji ansa hannu antoshe mata baki...
Aka°•○sultana
[8/9, 8:44 AM] .: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
_*YAR*_
🎃 *TALAKAWA*🎃
By→afrah
Episode→1⃣0⃣3⃣
To
→1⃣0⃣4⃣
*LOVE* _oh yeah dis_ _+2347010902548
Episode is all abt soyayya_..
_Muje zuwa_....
Ta ware manyan manyan idanunta, kirjin ta kuwa kamar zai bullo, fitsari kawai ya rage tayi, a tunanin ta barawo ne ya shigo musu gidan.
Prince ya jawo hannun ta da karfi, sukayi tafiya har wurin da kawai haske.
Neena kuwa sai bin sa kawai take, gashi ya juya mata baya, bata gane ko wanene ba.
Har sai da suka iso bangon kusa da kicin din mum, ya sake jawo ta ta dawo gaban sa, ya jinginar da ita da bango kamar dazun.
Sai lokacin neena ta ganshi, amma har lokacin a tsorace take, mai ya prince keyi anan?
Bata idasa tambayar kan taba, taji yace da silent voice dinshi, ina kikaje?
Yayi maganar yana daure fuska, neena tayi blinking(kyafta) idonta sau biyu, ta nuna kanta da yatsan ta, Ni?
Prince yace a'a ni, neena ta hadiye yawu da kyal, gaba daya ya dawo mata prince dinshi.
Yayi two steps, sai gashi dab da ita, bude kofar sukaji za'ayi , yayaB ce, ta fito rubar da ruwan zafin data gama kasa kafarta..ai ni zubaida kada ma kimin magana, har nace miki kizo ki kasan kafa, ki wani turo dan bakin ki kamar biro, dan kina amsa waya ko.....
YayaB na maganar ne tana shirin fitowarta....kuma dole ne idan ta fito ta gansu.
Prince ya rike hannun neena, ya fisgota sukayi baya sosai, ga wurin yayi duhu sosai, ya jingina da bango, sannan ya jawo ta jikin sa, neena ta kware baki, dan yayaB taji ta, ta taimaka mata, a zaton ta prince sai ya bata punishment din dawowar dare da tayi, dan ta taba jin su zarah da zuby na fadin, idan sukayi dare ya prince na cin uban su.
Prince ya daure fuska yayi saurin rufe mata baki, ya sa dayan hannunsa a lips dinsa, meaning tayi masa shiru
Gaba daya ta kasa sukuni, sai neman kwace wa takeyi, prince yayi dan tsaki, ganin yarinyar zata tona shi, gashi wannan yayaB din surutu kamar radio. .yasan ta gansu, kowa ma sai yaji a gidan...
Ya sake janyota sosai, har suna jin lumfashin juna, hancinsu na gogar na juna, idanunsu na kallon juna, take neena ta nutsu, dan wani irin kyau da kwarjini da prince yayi mata..
Shima prince dai kawai controlling kansa yake, ya kasa dauke idonsa daga kallon cute face din neena, (shes darm a pretty dude) zuciyar prince ta fada masa... (ni kuwa afrah dake tsaye ina kallon ikon Allah,, nace make I play aashiqui song 4 dem"sunn raha hai" lolz).
Sai da sukayi minti 10 a haka , sannan sukaji rufe kofar yayaB, lock lock ta saka key ta rufe gaba daya tana cewa, sai ayi ta barin kofar nan a bude, bacin kowa na ciki mtsw, ta fice daga kicin din tana kashe wutar kicin din....
Neena ta fisge da karfi, daga rikon da prince yayi mata, tayi saurin karasawa wurin kofar tana bubbugawa, ta leka ta window tana kiran sunan zuby! YayaB! Amir! Mum!... amma shiru ba wanda yasan ma tanayi....
Kamar zatayi kuka, ta saki kayan hanunta, tayi tsaye hawaye na fita, wayyo yau a waje zata kwana kenan?
Gashi bata da waya a hannunta, wanda ya sadeeq ya bata kuma ba caji bare simcard...🙆
Prince kuwa tsaye yayi, sai data gama nata rakin , sannan yazo, ya murda yaji gam, yaja tsaki, ya leka windows yaga an ma rufe kofar kicin din, yazo wurin neena.
Yace, ya zamuyi kenan? Neena kamar ta shake shi, duka bashi ya jawo ba, da yanzu tana daki abunta, ta rufa da bargonta mai laushi, dan sanyin wajen nan yayi yawa, gashi bata son sanyi...
Bata san ma hararar prince takeyi ba, tana tunanin nan, shi kuwa, burge shi ma ta kara yi...har taso ta basa dariya, yadda duk ta wani shagwabe fuska, zata kuka..
Neena tace ya prince ka kira zuby please, prince yace gud idea, ya saka hannun sa cikin aljinu, yaji wayam...
Neena ta kura masa ido, tace badai ka manta wayan a ciki ba?? Kamar zata fashe da kuka tayi maganar...
Prince ya kada mata kai, neena ta kwashi kayan ledojin ta, bari naje sashen mami na duba ko basu kulle ba...
Ta tafi da sauri, prince ya saka hannunsa a aljihu ya koma , wurin rumfar garden , ya zauna.
Neena taje taga sun rufe suma, kamar ta fasa ihu, ta sake dawowa, ta hango prince a zaune abunsa, mtsw shi bai ma ko damu ba, dan yana da jacket dinshi zata rage masa jin sanyin nan, ni fa, ta kalli jikinta...
Gown ta saka, mai guntun hannu, sai gyele bamai kauri bane sosai, ko dan kwali bata daura bama, tana zangin zuwa wurin yaya habu...
A sanyaye tazo ta zauna itama, prince ya jinginar da kanshi a kujera ya lumshe idon shi.
Neena tasa gyelen ta, ta rufe jikin ta, still tana danjin sanyin, ta takure sosai...
Sai data dauki minti sha biyar a haka, duk tsoro takeji, amma tana kallon prince taji she's save, tunda yana kusa, tayi murmushi , sannan tasa kanta a table, barci yadan dauke ta...
Prince ya bude idonsa a hankali,
Ya taso yazo wurin ta, gashin ta yadan sauko a fuskarta, sai barcin ta takeyi, amma a takure da gani dai tana jin sanyi..
Prince ya cire jacket dinshi, ya rufe mata jiki, sannan ya jawo kujera, ya zauna dab da ita, ya sa hannun sa, yadan janye mata gashin daga fuskarta, ya kura mata ido, tun daga idanunta, gashin idonta masu tsayi, zuwa hancinta, medium, yayi fitting din fuskarta, zuwa cute pink lips dinta, suma sunyi daidai da fuskarta.
Prince yakai hannunsa ya shafi lips dinta, take ya sauke ajiyar zuciya...
Ya mike kadan, ya sumbaceta a goshin ta, a hankali ya motsa bakin sa.
Zai furta.......
Fans na bar muku amsar abunda prince zai furta....
Lols sai naji guesses dinku zanci muku gaba😜
Love u all muah....
Aka°•○sultana
[8/9, 8:44 AM] .: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
_*YAR*_
🎃 *TALAKAWA*🎃
By→afrah
Episode→1⃣0⃣5⃣
To