SANADIN KENAN 2 HAUSA NOVELS BY TAKORI KABARA.doc

Author :  Sumayya Abdulkadir Takori Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   10 / 11

27K to 30K   out of 31.5K words

ke".  Nima tunanina kenan Goggo .
Tuni ta yi wankanta na safe dama, ta soma tattara 'yan komatsanta cikin 'handbag' dinta da ta zo da ita, don yanzu bata dauko babbar jakarta in za ta zo, suna maganar suka ji dirin mota a kofar gida. Ilya baya nan daga ita sai Talatu da Goggo, suka yi sallama ita da Goggo da Talatu ta fito. Akilu ya bude mata kofar motar ta shiga, kullum bata gajiya da rokonsa kan ya daina fitowa ya bude mata kofa, amma ya ki bari.
Babu inda ake bincikarsu kamar koyaushe har suka tadda ginin da masu gidan ke ciki wanda shine a can karshen gidan.
Dakinsu ta nufa kai tsaye da jakarta a hannu, ba kowa a dakin, ta karasa ta aje jakar gefe ta zauna kan  resting chair tana taraddadi Allah yasa Ameena lafiya take.
Ya yi knocking hade da sallama Amina ta amsa, ya murda kofar sannan ya turo Ameena cikin kekenta suka shigo tare. Ta daga kai ta dube shi, idan har ba gizo idonta yake mata ba har wata  yar rama baban Amina yayi a idanunta cikin kwanaki biyun data yi bata ganshi ba. Tace a ranta watakila shine baya jin dadi. Ta karasa da sauri tana tattaba jikin little sai ta ji ya ce,
"Ki yi hakuri, lafiya kalau fa, na sa an dauko ki da wuri, duk da nasan ba mu kadai ke da bukatar ki ba akwai pigeons (tantabarunki), wasu abubuwan yau na kasa ne, I m weak today!".
Ta yi murmushi,
"Babu damuwa. Tunda Ameena lafiya take. An ba ta magungunanta na safe?"
"Na manta ban bata ba, rashinki a gidan ya dan maida ni upset, ga su ki ba ta".
Ya mika mata ledar magungunan. Ta karba da sauri, ba tareda ta yiwa maganarsa wata fassara ba, bata dube shi ba take magana, tana kokarin kwance ledar magungunan hannunta har rawa yake.
"Amma ka ga lokacin shan ya wuce ko? Ba haka muka yi da kai ba, kafin in yarda in fara bar maka amanar Amina".
Ya yi murmushi, ganin yadda ta ke maganar kamar mai yi wa kaninta fada, ba karamin jin dadin maganganunta ya yi ba masu nuna kulawarta a kan Ameena, don haka cikin kwantaccen sauti ya ce,
"Allah ya huci zuciyar Dr. Amina. Amma ina yin kokari fa, na cancanci a nuna appreciation ga kokarina, kula da Da sai uwarsa, da wanne zan ji? Ni ne messaging, ni ne ba da abinci a baki, ni ne amsa tambayoyin Amina a kan ina ki ka je, ni ne wanka da canza diapers, nine bada magani.
Ni ne zagaye da  yar ki a wheel chair, sannan gidan ya zama wani irin wawakeke (very wide) ba tareda ke ba. Dr. Amina, kin shaci fili cikin rayuwarmu da yawa cikin dan lokaci kalilan. Ban gane hakan ba sai a karshen satinnan da kika tafi kika barmu, gidan ya zamo incomplete. Ko mene ne sirrin?"
Da sauri ta juya ta dube shi, don ta tabbatar daga inda kalaman data ke ji ke fitowa, tanaso ta amincewa kanta da gaske da Ma'arouf Ji-Kas ta ke magana ko waninsa? Ko kunnuwanta ke jin gizo?
Wadannan basu yi kama da kalamansa ba, ba yau ta soma jin zantuttukansa ba these are odd, very different, sunyi nauyi da yawa cikin kunnuwanta, da gaske da Jikas din da fuskarsa ta karade fastoci da akwatunan talabijin da sauran kafofin yada labarai take magana. Shi din ne da gaske, ba wani mai kama dashi ba.
Wannan Kyakkyawan Ma arouf din mai wadatar jini a jika, ma abocin kwarjini da cikar zati da kamala. Bata da amsar tambayarsa, batada kowanne sirri. Abin da ta sani kawai shi ne ba zai taba iya yin abin da mace za ta iya ba, kuma ya ce ya ji ya gani ya daukar wa kansa aikin da ba nasa ba, saboda matarsa shafaffiya da mai ce.
Anya matar Jikas musulma ce mai zuciyar imani? Tausayin Ameena ya kara kamata. Ta kara jin son Goggonta, tana rokon Allah cikin zuciyarta ya bar mata ita (Goggo) su cigaba da rayuwa tare.
Maraici babban kalubale ne ga rayuwar dan adam balle ga karamin yaro, wanda bai gama sanin kansa ba. Shi kuwa me ya yi masa zafi da dole sai ya zauna da wannan matar tasa? Wadda bata tausayawa jininsa kiri-kiri haka? Bai yi kama da ragwayen maza ba, wadanda matan su suka fi karfin su, dole akwai wani boyayyen al'amari cikin auren nasa.
Amina ta nisa.  taimaka min ka kwantarda ita, zamuyi gashin kashi . Ta gujewa waccan tambayar da ya yi mata kenan, don ba ta da amsarta. Zuciyarta raurawa take, bata taba jin kwatankwacin wadannan maganganun daga kowa ba, don haka she becomes agitated!.
Ya ciro Amina daga keken ya kwantar da ita, ya samu wuri daidai kafafunta ya zauna, sai Dr. Ameena ta samu kanta da kasa yin gashin, ta koma wajen zamanta na dindin wato doguwar kujerar hutawa ta zauna, tana juya injin thermotherapy dinta a hannu. Kamar ance da ita ta dago ta dube su, ba kowa Ma arouf ke kallo ba har zuwa lokacin sai ita Ameena. Wani irin sanyi taji jikinta ya yi, ta maida kanta kasa ta sunkuyar.
Can saman kanta ta tsinkayi sautinsa,  raising pigeons is wonderful, (kiwon tantabaru abune mai ban mamaki) kin bawa Amina saura na Babanta, ina son yin babban kiwone irin naki, ki bani nima, in hada dana Ameena in cigaba da kiwonsu, they are progressing fiyeda tsammaninki .
Dr. Amina ta dan ciji lebe ta girgiza kai (showing resentment),
"gaskiya BABAN ya yi hakuri, I so much love my pigeons! (ina son tantabaru na)".
Sai bayan ta fadi hakan ne kuma taji a wani barin na zuciyarta kamar bata kyauta ba a karo na biyu. A zuciyarsa yace  musu na biyu . Girgiza kai yayi, cikin mika wuya ga sabuwar rayuwar dake faruwa dashi, baida tsimi bai da dabara face karbar ta da hannu bibbiyu don samun nutsuwar zuciyarsa. Gabadaya jinsa yake a hargitse, wannan halittar dake gabansa, ita kadai zata sa ya samu nutsuwa. Hakan kuma bazai faru ba, ba tareda ya ja ta a jiki ya shiga rayuwarta ba.
"Na yi hakuri da account number, ban kara tambaya ba. Yau watanni bakwai zuwa takwas kenan saboda gudun musun ki Dr. Ameena. Ban yi fushi ba, yau ma na sake neman wata alfarmar, a karo na biyu ban dace ba.
To ban hakura ba, wannan karon ina so lallai, kuma rabin gabadayansu za ki bani, wato mu raba daidai, a gidan gona ta zan zuba su in hada da na Ameena. Ko saboda ni ba abin tausayi ba ne sai Ameena? Shi ya sa komai na roke ki ba za ki ba ni ba? Shin akwai abin tausayi a duniya ma irina?"
Amina Ta dago ta kalle shi, so take ta hango ta inda za aji tausayin mutum kamarsa. Sosai ta ga ya zame mata abin tausayin a fannin da ba ta sani ba, Sai ta ji zuciyarta ta karye.
"Kana da mita!".
Abinda ta iya cewa kawai kenan.
"Kina da tsiwa!". Ya mayar mata.
Ta yi dariya har fararen hakoranta suka fito. Lokaci daya ta ji ba Tantabaru ba, za ta iya mallaka masa duk abin da ta mallaka in har hakan zai sa shi farin ciki. Muryarta ta yi kasa sosai a sanda ta ke cewa.
"Wane bayani zan yi wa Goggo? Cewa zan kyautar maka da rabin abin da na gada daga mahaifina haka siddan, na rene su shekaru goma sha biyar ban taba baiwa kowa ba? A matsayinka na wa a gare ni zan ce da Goggo?"
Murmushi ya yi, ya mike tsaye yana kokarin fita,
"Matsayin da ki ka bani shi za ki gaya mata. Well, ban san matsayin da ki ka banin ba. Ba kuma yanzu nake son sani ba. Ni dai ta fanni na ban boye ba na gaya miki, kin shaci fili mai fadi a rayuwarmu ni da Ameena cikin dan lokaci kalilan". Da wannan ya karasa ficewa daga dakin.
Amina ta yi dan jim! Na sakanni, sosai ta shiga duhu da maganganun Ma arouf, so take kwakwalwarta ta fassara mata su, sai kuma ta watsar da tunanin ta ci gaba da abin da ke gabanta. Bata son kwadayin sanin fassarar maganganun nasa, da tasirinsu ya katse ta daga abinda takeyi. Kai ita bata barin komai ya shiga cikin aikinta fa. Amma Baban Ameena na son ya kara kansa cikin ayyukanta karfi da yaji, ta hanyar baiwa kwakwalwarta zazzaffan aiki wanda ita ba ta shirya wa hakan ba.
Misalin karfe takwas na daren ranar, suna zaune a falonsu shi da Laila, ta ci ado ta kashe dauri kamar mai shirin zuwa gasar sarauniyar kyau. Tana rike da tambulan na gilashi mai garai-garai cike da tataccen inibi mai sanyi, kurba take a hankali kafarta daya akan daya first-lady sosai, ba sai an tambaya ba. Kowannensu da abin da yake yi cikin falon kamar ba ma'aurata ba.
Ita kallon talabijin ta ke yi, inda ake nuna ayyukan mijin nata a kananan hukumomi da kauyuka a Bauchi TV, wani alfahari na kara shigarta. Alfaharin cewa she s the only one that owned him. Lokaci zuwa lokaci ta kan yi murmushi. Shi kuwa na'ura mai kwakwalwa ce da takardu fal a gabansa, yana duba tsare-tsaren  budget' na sabuwar shekarar da za a shiga wanda ma'aikatar kasafi da tsare-tsare (ministry of budget and planning) ta gwamnatinsa ta tsara ta fitar ta damka masa don ya sa hannu. Ya na dubawa ne a nitse yana gyare-gyare kafin ya sa hannun.
Ya dago ya dubi Laila, wadda tunda ta dawo daga tafiyar da tayi ba ta tambaye shi ina little Ameena ba ko ya ya jikinta?
Abin fa yana yi masa ciwo ba kadan ba. A ce tsakanin jininka da matar ka babu jin kai babu tausayi balle karah. Haushi ya kama shi ganin yadda ta wani cokalo dauri a gaban goshi, bakin nan ya sha jambaki jajawur ram! Jagira har kusa da kunne fuska ta sha foundation tayi haske kamar rana. Ya sha gaya mata ba ya son ganin artificial make-up, bai saba ganinsa a Aisha Maman Ameena ba, in don shi ta ke yi ba ya so. Ta bar fuskarta natural hakan yakeso amma ta ki bari, a ganin Laila ita daban matacciyar matarsa daban kowa tabi ra ayinta.
Ba yadda za a ce mata biyu sun taru sun zama daya wajen ra ayi da akida a wannan zamanin. Karamin tsaki yayi, har sai da ya shiga kunnenta, ta dauke kanta daga akwatun talabijin ta dube shi.
"Ya ya dai?"
Ya hadiye haushinsa.
"Me ya sa ba kya gaisawa da physiotherapist mai kula da Ameena, idan Amina bazata samu alfarmar sannu daga gareki ba?"
Ba ta ce komai ba, baya ga cuno baki gaba, bai damu ba ya ci gaba da cewa, "nasan ko sunanta baki sani ba duk tsayin zamanta a gidannan. At times inaso muyi maganarta sai wasu abubuwan su mantar dani, ke kuma baki taba tuna min ba. Kamar bakisan da zamanta a gidan ba. Sunanta Dr. Amina to, suna zaune a dakunan downstairs na bangaren nan, amma kamar ba ki san da su a gidan nan ba Laila. Don ban taba ganin sawun kafar ki a inda suke ba, a cire Amina karama don dama bata cikin lissafi, amma ita wannan bakuwa ce dake aiki a karkashina, a matsayinki na matar gidan ta cancanci kulawarki ko da da gaisuwa ne.
Na hore ki da gaisuwar mutunci ta cigaba a tsakaninku. Zaman Ameena ta ke kadai ba na wani ba".
Laila ta sake cuno baki.
"A kan me zan dinga gaishe ta? Ni da ita waye a saman wani? Ta taba zuwa inda nake ta gaisheni? Ta fiya girman kai, ba ta taba nemana a gidan nan ta gaishe ni ba, sai ni zan zubar da girmana in dinga zuwa inda ta ke?" Cikin girgiza kai ya ce.
 nida ba ni da girman ai ni nake zuwa inda suke ina gaishesu . Daga haka ya yi shiru ya kyale ta, ya ci gaba da abin da yake yi. Ta kyabe baki a ranta tace  kai ka ga zaka iya .

*****
Wannan satin da Amina ta zo gida, Goggo ta lura da ta faya shiru-shiru, ta zama wata irin sukuku da ita. Ita kuma ba wani abu ke damunta ba kamar ta inda za ta dauko wa Goggo zancen Tantabaru, ga shi ba za ta iya kin ba da su ga Baban Ameena ba a kan dalilai masu yawa, wadanda ta sani da wadanda ba ta sani ba. Duk da ta san za ta kasance cikin kewa mai yawa idan ta bada rabin tantabarun nan. Amma abin mamaki zuciyarta ta ki zama lafiya idan ba ta bada su din ga Gwamna Ji-kas ba kamar yadda ya bukata. Kuma ba a kan ko sisi ba.
Da yamma tana dakin Goggo da manyan littattafanta a gabanta tana nazari, wanda bata rabo da yinsa sai dai in bata kadai ce ba, amma da aka dan jima sai ta rufe ta ture su gefe, ta zuba uban tagumi.
Goggo ta shigo ta ganta a haka, har ta dauki abinda zata dauka a dakin ta fita ta dawo Amina bata san anyi ba, ta karasa bakin gado ta zauna, yayin da Amina na zaune a kan kilishi, har Goggo ta zauna ba ta ganta ba, sai da ta kai hannu ta taba ta. Ta juyo firgigit ta dubi Goggo.
"Me ke damunki ne Amina? Tunda ki ka zo wannan satin nake ganinki cikin damuwa. Wannan uban tagumi na magani da mene ne?"
Amina ta ga cewa, dole ne ta gaya wa Goggo tunda dai ba za ta dauki tantabarun nan ba tare da saninta ba. Sai dai ba ta san ya ya Goggo za ta karbi maganar ba, kada ta yi wani tunanin otherwise. Duk da haka dai ta ga bata da mafita sai ta daure ta ce.
"Goggo, wai Baban Ameena ne ya ce na ba shi rabin tantabaruna".
Goggo ta dan yi shiru, kafin tace "rabin tantabaru? Me zai yi da su? Wace irin hira ku ke yi tare da har ki ka yi masa maganar tantabaru? Me ya hada ku ban da aikin 'yarsa?"
Ta bi ta tsattare ta da ido, cike da tuhuma sai da Amina ta daburce.
"Ba...... ba abin da ya hada mu Goggo, amma kullum kafin ya fita office da bayan ya dawo sai ya shigo ya ga lafiyar 'yarsa, in har yana gari. Farkon zuwana gidan ko kallona ba ya yi, ko inda nake ba ya kallo. Wani irin mutum ne shi din a lokacin da mahaifiyarsa kadai ke ganin hakoransa. Ko magana za mu yi a kan lafiyar yarinyar ba ya kallona, ni ma bana kallonsa muke yi. Sau uku Hajiyarsa ta zo ita ta sanya muka fara magana da juna, don cewa ta yi ya yi wa matarsa fada ta dinga zuwa inda nake muna gaisawa tana ganin lafiyar Ameena, to matar ta ki mu gaisa, ta kuma ki zuwa ganin Ameenar. Daga lokacin ne ya soma yi min 'yan tambayoyi a kan rayuwa ta ina ba shi amsa. Sai muka dan fara sabawa har na kan bashi shawarwari akan siyasarsa kuma abin mamaki yana dauka.
Rannan ya ce in dawo da wuri ranar wata lahadi, zaki iya tuna ranar Goggo? Na ce masa ba zai yiwu ba don ina kiwo, ya tambaye ni na me ye na fada masa, sai ya ce zai saya wa Ameena aure biyu na dauka na ba shi. Wannan satin kuma gabadaya rabi ya ce in ba shi".
Goggo da ta tsura mata ido ta nisa, ta ce, "Ni dai ina kara gargadinki da tsare mutunci a ko'ina. Ba ni da mummunan tunani a kanshi, a kwashe a ba shi, ai hayayyafa suke".
Amina ta ji kamar an sauke mata dutsen Dala da Goron Dutse daga kanta. Ta ce,
"To Goggo, zan gaya masa kin amince ya turo a kwashe".
Rana ta farko da Amina ta yi tunanin buga wa Ma'arouf waya a rayuwarta. Sai dai wani barin na zuciyarta na hana ta. Amma barin a yi kiran ya rinjayi na kada a yi kiran.
Yana tura Ameena cikin wheel-chair a wata farfajiya da ke cikin gidansa ya ji kira daga wayarsa da ya kunna yanzu-yanzun nan. Ya yi magana da Turaki ne, ya manta bai sake kashewa ba ya sanya a aljihu. Abin mamaki sunan da ya baiwa lambar da bai taba tsammanin kira daga gareta bane wato  Amina's Doc' ya bayyana a fuskar wayar. Ya amsa ba tare da ya ce komai ba.
Da dai ta fuskanci ya amsa, sai ta fadi sakonta kai tsaye,
"Goggo ta amince a zo a kwashi Tantabarunnan".
Murmushi ya yi mai sauti, "Babu gaisuwa sai sako kai tsaye Dr. Amina?"
Amina ta yi shiru, jikinta har rawa-rawa yake yi don wani tsoro-tsoro ma take ji na kiran data yi, a ganin ta ta zarce limit din da ya kamace ta (ta wuce gona da iri), bayan ganin kima da girmansa, he s someone she respect most! Maimakon ta yi gaisuwar sai bakinta ya subuce da fadin zahirin abin da ke zuciyarta.
"Ina Ameena? Ya ya ta ke? An yi messaging din yamma? An fito da ita shan iska? Ta sha magani?"
Murmushi ya yi. Ya dan russunar da gazing dinsa kan Ameenar da ke cikin wheel-chair zaune abinta, a zuciyarsa ya ce, '....Ameena kina da wadda ta damu dake da lafiyarki, bayan ni da Hajiya. How I wish Laila ce haka! Da gininnikan da na yi wa rayuwa ta ba su soma kokarin rushewa ba.......!.'
Ya lumshe ido ya bude, bai ce komai ba. Sai ya kara wa Ameenar wayar a kunnenta.
"Ameena ga Aunty".
Ameena ta yi magana da iyakacin sautin ta mara karfi, "aunty yaushe za ki dawo? I'm missing you... I prefer your messaging than Daddy's...(Ina kewarki, na fi son tausarki a kan ta Daddy)".
Dr. Amina ta yi murmushi, ta kara makale wayar a kunnenta na dama.
"Kin manta na ce kullum na tafi ki kirga kwana sau uku zan dawo?"
"Na kirga,

10 / 11