Allon Sihiri Book 3 By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt

Author :  Abdulaziz Sani Madakin Gini Category :  Arewa Pen

Chapter   2 / 3

3K to 6K   out of 7.2K words

dinnan
rana
daya jal,kuma mu saki jikinmu dashi har mu gaya
masa sirrinmu?Shin baka tsoron cewa zai iya
cutar
damu ko kuma yayi amfani da sirrin namu sami
Damai-Akala?Kawai muyi amfani dashi wajen
cika
burinmu in yaso mu a tsakaninmu mu sasanta
yadda kowa zai amfana.Koda jin haka sai
Sarauniya
Akisatul Sauwara tayi murmushi tace tabbas
kazo
da shawara mafi alheri,shi kuwa Yarima Lubainu
sai
ransa ya baci ya dubesu su biyun yace,ni kam
daga
yanzu na fita daga cikinku domin bazan iya baku
yarda da amanata ba,tunda har zaku iya yin
karya
da yaudara,gwara na baiwa wannan bakon
jarumin
amincina saboda akwai alamun cewa zaifiku iya
rike
amanata.Koda gama fadin hakan sai Yarima
Lubainu
ya juya ya bar wajen su Sarki Darmanu ya nufi
inda
Bakon Jarumin da dan wada Dazyan ke
tsaye.Koda
ganin haka sai Sarauniya Akisatul Sauwara ta
ruga
izuwa gareshi tasha gabansa tace haba yakai
wannan dan Sarki,ka tuna irin halaccin danayi
maka
lokacin dakazo gareni bisa neman taimakona.Ka
tuna yadda na dauko ALLON SIHIRI NA kuma na
biyoka a cikin wannan tafiya mai hadarin gaske
don
kawai na taimake ka ka sami nasarar samo
lafiyar
jikinka ka koma ga matarka kuma masoyiyarka
YAZARINA?Idan ka tarwatsa mini nawa shirin
saboda
cikar burinka kaci amanata kuma ka nuna mini
cewa
kai
ba dan Halak bane!Koda Sarauniya Akisatul
Sauwara
tazo daidai nan a zancenta sai Jikin Yarima
Lubainu
yayi sanyi kuma hankalinsa ya dugunzuma har
idanunsa suka dan ciko da kwallah,amma daya
sake
tuno da nasihar da aka bashi kafin ya baro gida
ta
rike gaskiya,amana da alkawari sai ya dubi
sarauniya Akisatul Sauwara yace,kiyi hakuri akan
fadin gaskiay saidai kice naci amanarki.Yana
gama
fadin hakan ya tunkari bakon jarumin gadan
gadan
yana shirin ya isa daf dashi sai dan wada Dazyan
yai
sauri ya shiga tsakiyarsu ya dubeshi a fusace
yace,doka ta farko ba a kusantar maigidana don
yin
magana dashi.Na gaya muku cewa ba kurma
bane
ba,don haka ko daga nesa zaka iya fadin duk
abinda
kakeson fada masa.Koda jin haka sai Yarima
Lubainu yayi murmushi yace hakikanin gaskiya ni
neman magani ne ya fito dani daga kasarmu.Nan
take Yarima Lubainu ya kwashe labarinsa kaf ya
zayyane bai boye komai ba harda batun
soyayyarsa
da YAZARINA wacce ta haddasa gaba a
tsakaninsa
da abokinsa YARIMA MANGUL har sukayi gasar
neman aurenta ta hanyar yakar juna ya cirewa
Yarima Mangul hannun daya shi kuma yayi masa
asiri ya kashe masa Mazakuta.Yarima Lubainu ya
cigaba da bayani akan fitowar da yayi don neman
ALLON SIHIRI ya karantashi don ya gano inda
KOGIN
BAHAR IMFAL yake yaje cikinsa ya tsinko dan
itaciyar da zata warkar da wannan cuta tasa
domin
ya koma gida a matsayin Namiji lafiyayye yaci
gaba
da ZAMAN AURE da masoyiyarsa
YazarinaLokacin da
Yarima Lubainu yazo nan a labarinsa sai bakon
Jarumin da Dazyan suka ji sun kamu da tsananin
tausayinsa.Bakon Jarumin yayi shiru yana tunani
da
nazari izuwa tsawon dan dakiku kadan sannan ya
dubi Dazyan yayi masa zancen kurame.A Sannan
ne
Sarki Darmanu da sarauniya Akisatul Sauwara
suka
taho garesu da sauri domin suji abinda bakon
jarumin zaice.Dazyan yayi gyaran murya sannan
yace,yakai wannan dan sarki kayi sani cewa
shugabana yace inda zaka yi imani da
UBANGIJIN
MUSULUNCI ka karbi addininmu zaka iya samu
lafiyarka a rana guda a cikin dakika guda daya
ma jal
ka yankewa kanwa duk wahalar dake gabanka.To
amma ya fuskanci cewa zuciyarka da ta
wadannan
Abokan Gaba tana da rauni akan yin imani da
ubangijin musulunci saboda kun yarda da Addinin
iyayenku da kakanninku,kuma kuna gani kamar
addinin naku shine addinin gaskiya,saboda kuga
zahiri kuma ku gamsu cewar addinin musulunci
shine na gaskiya mafin inganci da daraja akan
naku,shugabana ya amince zai ci gaba dayin
wannan tafiya tare daku amma duk inda akaje zai
barku ku jarraba kafin sihirinku da na damtsenku
wajen ganin cewa kun kawar da kowacce irin
masifa
da aka riska sai bayan kun kasa sannan shi ya
kawar da masifar da taimakon ubangijin
musulunci,amma fa sai idan kun dauki alkawarin
cewar bayan anzo karshen tafiyar zakuyi imani
da
addinin musulunci,idan kuma baku yarda ba da
wannan sharadi ba,to zai cigaba da binku kawai
a
cikin wannan tafiya ya zaman dan kallo ba tare
daya
taimaka muku da komai ba.Koda Dazyan yazo
nan a
jawabinsa sai hankali Sarki Darmanu dana
Sarauniya
Akisatul Sauwara ya dugunzuma ainun fiye da ko
yaushe suka rasa abinda yake musu dadi a
duniya,shi kuwa Yarima Lubainu sai farin ciki ya
lullubeshi ya dubi bakon jarumin cikin murmushi
yace tabbas ni na yarda da wannan sharadi
naka.Koda jin hakan sai Bakon Jarumin yayi
maganar kurame ga Dazyan shi kuma Dazyan sai
ya
dubi Yarima Lubainu yace mai gidana yana
murna
dajin bayaninka.Dazyan ya juya ya dubi Sarki
Darmanu da Sarauniya Akisatul Sauwara
yace,maigidana yace ki kuma fa menene
ra'ayinku?
Cikin rawar murya da tuntuben harshe Sarauniya
Akisatul Sauwara tace babu matsala muma mun
amince da sharadin maigidanka to amma yanzu
yaza ayi akan batun ALLON SIHIRIN Boka
Darbusa
wanda mukazo nema a cikin gidansa?
pls Like nd comments
15 hrs · PublicALLON SIHIRI
Littafi na uku (3)
Part C
Batun ALLON SIHIRIN Boka Darbusa wanda
mukazo
nema yanzu a cikin gidansa.Koda jin wannan
tambaya sai Bakon Jarumin ya dubi Dazyan ya
sake
yi masa zancen kurame da hannu.Dazyan ya dubi
sarauniya Akisatul Sauwara yace maigidana yace
yanzu zamu bazama neman wannan ALLON
SIHIRI a
cikin wannan gida,amma ku ukun ne zaku fara
neman ALLON SIHIRIN da karfinku sihirinku,idan
kuka kasa sai mu roki ubangijinmu ya nuna mana
inda yake mu daukeshi da izininsa mu baku.Koda
gama fadin hakan sai Yarima Lubainu ya dubi su
Sarauniya Akisatul Sauwara yace to kunji yanzu
dai
shawara ta rage ga mai shiga rijiya.Sarauniya
Akisatul Sauwara da Sarki Darmanu suka dubi
junansu sukayi murmushi kuma suka budi baki
cikin
hadin murya suka ce muma mun amince da
hakan.Nan take Sarauniya Akisatul Sauwara,Sarki
Darmanu da Yarima Lubainu suka sake kunna kai
izuwa cikin gidan Boka Darbusa kowannensu na
karanta dalasiman tsafinsa a cikin ransa.Shi
kuwa
Bakon Jarumi da Bawansa Dazyan sai suka bisu
a
baya kawai suna kallonsu kuma suna neman
tsarin
Allah daga dukkan mugun abun dake cikin
gidan.Abu dai kamar wasa saida su sarauniya
Akisatul Sauwara suka shiga duk wani sako,lungu
da
dukkan dakunan dake gidan kuma suka caje
komai
da ko ina a cikin gidan amma har suka gaji likis
ko
alamar ALLON SIHIRI basu gani ba.Daga karshe
ne
suka ga wani daki mai katuwar bakar kofar karfe
a
kulle wanda ya rage basu shiga ba.Ita kanta
kofar
wannan daki ta isa abar tsoro domin anyi tane da
mulmulallen karfe mai kaurin gaske,sannan akwai
hoton KWARANGWAL din kan BIL'ADAMA da
kafafuwansa a jikinta alamar cewa wannan
daki,daki
ne me mugun hadari wanda mutum zai iya rasa
rayuwarsa a ciki.Koda sukayi arba da kofar
wannan
daki sai sarauniya Akisatul Sauwara,Yarima
Lubainu
da sarki Darmanu suka dubi junansu sukayi cirko
cirko suna kallon kofar.Kawai sai Sarki Darmanu
ya
dubi sarauniya Akisatul Sauwara yace ai sai fara
jarraba taki sa'ar mu gani.Ba tare da wata
gardama
ba kuwa sarauniya Akisatul Sauwara ta kama
kofar
taja da nufin ta budeta amma sai ta kasa kawai
sai ta
fara karanta wadansu dalasiman tsafi tana
tofawa a
kofar.Maimakon kofar ta bude sai wata irin iska
mai
karfin gaske ta fito daga cikin kofar ta doki kirjin
Sarauniya Akisatul Sauwara tayi sama da ita da
karfi,bayanta ya gwaru da jikin bango ta fado
kasa a
galabaice.Koda ganin abinda ya faru sai hankalin
Sarki Darmanu ya tashi jikinsa ya kama tsuma ya
dubi Yarima Lubainu yace saura kai.Yarima
Lubainu
ya numfasa yace shin ka mantane kai abinda
Sarauniya Akisatul Sauwara ta kasa yi nima
bazan
iya ba.Koda jin haka sai Sarki Darmanu ua ciza
lebe
sannan ya dunkule hannayensa biyu yayi nuni
dasu
izuwa ga kofar yana mai rintse idanu.Faruwar
hakan
keda wuya sai iska mai karfi ta fito daga cikin
hannayensa ta rinka duka kofar dakin tana
jijjigata
kamar zata burma ciki amma sai hakan ya
gagara.Maimakon ma kofar ta bude sai ta maido
masa da iskar hannun nasa ta sureshi sama ta
rinka
katantanwa dashi a sama ya rinka ihu yana
neman
hallaka.Koda ganin haka sai Bakon Jarumin ya
daka
tsalle sama ya riko rigar Sarki Darmanu.Take
iskar
tsafin ta dauke dif sarki Darmanu ya fado kasa
tim.Shi kuwa Bakon Jarumin sai ya diga a kasa
bisa
kafafunsa cikin koshin lafiya.Sarki Darmanu kuwa
saida hancinsa da bakinsa suka kama yoyon
jini.Bakon Jarumin ya dubi Dazyan yayi masa
zance
da hannu sannan Dazyan ya dubi sarauniya
Akisatul
Sauwara da Sarki Darmanu yace shugabana yace
zai
bude muku wannan kofa da izinin ubangijinsa
wato
ubangijin musulunci.Koda jin haka sai Sarauniya
Akisatul Sauwara ta dubi Yarima Lubainu da
Sarki
Darmanu tayi musu kallon ko menene ra'ayinsu?
Duk
su biyun sai suka sunkui da kawunansu
kas.Faruwar
hakan keda wuya sai Sarauniya Akisatul Sauwara
ta
dubi Bakon Jarumi tace mun baka dama.Dajin
haka
sai Bakon Jarumin ya tunkari kofar dakin kai
tsaye
ba tare da shakkar komai ba,da isarsa bakin kofar
sai ya dungureta da dan yatsansa guda
daya.Take
kofar ta bude a hankali tamkar yaro ne karami
wanda
baifi shekara hudu ba ya turata ta bude din.Saida
kofar ta gama wangamewa gaba dayanta sannan
su
Yarima Lubainu suka matso kusa da Bakon
Jarumin
suna leka cikin dakin jikinsu na tsuma saboda
tsoro
da fargabar ko wata masiface zata taso,amma
sai
suka ji shiri kamar maye ya ci shirwa.Koda ganin
cewa su Yarima Lubainu sun kasa shiga dakin sai
Bakon Jarumin ya juyo ya dubi Dazyan yayi masa
inkiya.Take Dazyan ya rugo ya bishi a baya,suka
kunna kai izuwa cikin dakin su biyu,ba tare da
fargabar komai ba.Duk da haka sai su Yarima
Lubainu suka kasa shiga dakinDaki ne babba mai
girman gaske tamkar wata karamar unguwa.Babu
komai a cikin dakin face durowa da tebura a jere
a
layi,layi kuma sahu sahu reras,iyakar ganin
idanun
mutum babu iyaka.Akan teburan da durowoyin
kwalabe ne birjik.Cike da RUWAN SIHIRI kala
kala.A
cikin durowoyin kuwa kayan TSATSUBA ne iri iri
kamar kahonni,Layu,Guraye,Kawunan Tsuntsaye
da
sauran sassan jikin dabbobi dana dan Adam dana
Aljanu.Shi kansa bakon jarumin daya shigo cikin
wannan daki saida ya cika da mamakin irin
abubuwan dake cikinsa da yadda akayi aka iya
tarasa.Koda Ya ga sun dan jima a ciki amma su
Sarauniya Akisatul Sauwara sun kasa biyosu
izuwa
ciki sai ya dubi Dazyan yayi masa maganar
kurame.Take Dazyan ya juya da baya ya ruga
waje
yace da su Yarima Lubainu maigidana yace ku
cire
tsoron komai a cikin ranku ku shiga ciki saboda
kune kuka san abinda kukazo nema,kuma akwai
rubuce rubucen sihiri da yawa a cikin dakin a
jikin
abubuwa da yawa wadanda ba zamu iya
karantasu
ba mu fahimta.
Koda jin haka sai Sarki Darmanu yayi wuf ya
wuce
gaba ya shige cikin dakin.Koda Ganin haka sai
Sarauniya Akisatul Sauwara da Yarima Lubainu
ma
suka bi bayansa da sauri.Shima dan wada
Dazyan
sai ya bisu da sauri sukaje suka riski bakon
jarumin
a tsaye a cikin tsakiyar daki.Da isarsu Dazyan ya
dubesu yace maigidana yace ya baku damar ku
dudduba ko za kuga abinda kukazo nema.Koda
jin
haka sai duk su ukun suka rarrabu suka rinka
bude
durowoyi suna duba kan tebura.Saida suka shafe
sama da sa'a daya da rabi suna neman ALLON
SIHIRIN Boka Darbusa amma basu ganshi
ba.Al'amarin dayai matukar dugunzuma
hankalinsu
kenan suka rasa abinda yake musu dadi a
duniya.Koda Bakon Jarumi yaga yadda hankalinsu
ya tashi sai mamaki ya turnukeshi yace a
ransa"Hakika iska na yawo da mai kayam kara!
Yanzu fa saboda kwadayin abin duniya ne yasa
wadannan mutane idanunsu suka rufe akan
neman
wannan ALLON SIHIRI?A cikinsu ma babu wanda
yafi
cancanta a taimakawa sama da Yarima
Lubainu,domin shine wanda aka zalunta kuma
ake
neman salwantar da rayuwarsa".Koda gama
Aiyana
hakan a cikin ransa sai bakon Jarumi ya tafa
hannayensa sau uku.Koda jin sautin tafin sai
Yarima
Lubainu,Sarki Darmanu da Sarauniya Akisatul
Sauwara suka tsaya cak ga barin binciken da
sukeyi
suka dawo inda yake tsaye.Da zuwansa sai dan
wada Dazyan ya dubesu yace,maigidana yace
tunda
dai kun kasa gano inda wannan ALLON SIHIRIN
yake
to shi zai bincikoshi da yardar ubangijinsa.Cikin
alamun karayar zuciya Akisatul Sauwara tace
shike
nan mun amince ya dauko ALLON SIHIRI.Koda
jin
haka sai Bakon Jarumin ya nufi inda jerin
durowoyin
suke.Har yabi layi na farko domin ya fara
bincikawa
sai ya tsaya cak,ya kirga layi na tara ya shiga
yana
kirgasu saida yazo kan durowa ta tara sannan ya
tsaya cak ya dubeta da kyau.Babu kofa a jikin
durowar kuma a rife take ruf.Babu alamar akwai
wani
abu a jikinta inda za'a iya budewa har aga abinda
ke
cikinta.Kawai sai ya daga hannunsa ya doki
tsakiyar
durowar take ta wargaje,ai kuwa sai ga ALLON
SIHIRI
kaso na uku a cikinta.Koda Yarima Lubainu,Sarki
Darmanu da sarauniya Akisatul Sauwara sukayi
arba
da wannan ALLON SIHIRI sai suka cika da
tsananin
mamaki.Kawai sai Sarki Darmanu da Sarauniya
Akisatul Sauwara suka yunkura cikin bakin zafina
nama duk su biyun a lokaci guda suka kaiwa
ALLON
SIHIRIN cafka,kowannansu na kokarin yariga
dayan
dauka,amma sai bakon jarumin yayi caraf ya
rigasu
dauka ya dubesu cikin murmushi yace,ai dama
nasan cewa sai hakan ta faru a tsakaninku.Da
zancen kurame yayi wannan bayani kuma Dazyan
ne
yayi musu jawabin.Bakon jarumin ya cigaba da
cewa
Kunga wannan ALLON SIHIRI dakuke gani duk
wanda
ya hada gudu uku a cikinsu bai isa ya iya rikeshi
ba
a hannunsa daidai da tsawon dakika goma
ba,amma
idan kuma shakkar hakan ku kawo ragowar bari
biyun dake hannunku kuga zahiri.Koda jin wannan
batu sai Sarauniya Akisatul Sauwara da Sarki
Darmanu suka kama muzurai suna duru duru
suka
kasa miko Allunan Sihirin nasu.Koda ganin haka
sai
Bakon Jarumi yayi murmushi kawai sai ya ajiye
ALLON SIHIRIN Boka Darbusa a tsakiyar dakin ya
koma gefe daya zura musu idanu.Nanfa
Sarauniya
Akisatul Sauwara da Sarki Darmanu suka kama
Kallon juna kuma suna kallon wannan ALLON
SIHIRI.Nan take kowannensu ya zaro nasa Allon
Sihirin kuma lokaci guda sai kowannensu ya daka
tsalla ya kaiwa Allon Sihirin Boka Darbusa
cafka.Ai
kuwa sai hannayensu suka cafki Allon Sihiri a
lokaci
guda.Nan fa suka mike tsaye a tare suka kama
naushin juna kowannensu na kokarin ya kwace
Allunan biyu ya hade da nasa.Gashi dai
kowannensu
yana dakuwa domin naushin junansu sukeyi a
fuska
da ciki amma saboda naci sunki yarda su saki
ALLON SIHIRIN.Shi kuwa Yarima Lubainu dama
ya
koma gefe daya ya zuba musu idanu kawai yana
jiran yaga yadda karshen al'amarin zai
kasance.Bakon Jarumin da dan wada Dazyan
kuwa
sai suka kara matsawa can gefe daya suka
zauna
akan wata doguwar kujera suna morewa
idanunsu
da kallon fadan da akeyi.Sarauniya Akisatul
Sauwara
da Sarki Darmanu na cikin kwarmazuwa sai
kawai
suka ga wata irin GUGUWA ta shigo cikin
daki.Nan
take ta suri komai na cikin dakin har da Sarki
Darmanu,Sarauniya Akisatul Sauwara da Yarima
Lubainu tayi sama dasu ta rinka gwara kansu a
jikin
bango.Amma bakon Jarumi da dan wada Dazyan
kuwa ko kusa dasu wannan guguwa batazo ba
kuma
suma suka ki suyi wani motsi suka cigaba da
zuba
idanu kawai.Cikin yan dakiku kadan su Yarima
Lubainu suka jigata suka fita daga
hayyacinsu.Sarauniya Akisatul Sauwara da Sarki
Darmanu basu san Sa'adda suka saki duka
Allunan
Sihirin uku ba suka fado kasa.Faruwar hakan
keda
wuya sai Allunan Sihirin suka hade waje guda
suka
manne da juna tamkar ba'a taba rabasu ba suka
zama babban Allo guda daya.Faruwar hakan
keda
wuya sai wannan guguwa ta rikide ta zama
wadansu
irin SAMUDAWAN BAKAKEN ALJANU dauke da
muggan MAKAMAN YAKI.Nan fa samudawan
bakaken aljanun suka ruguntsume da masifaffen
azababben yaki a tsakaninsu,ya zamana cewa
kowannensu na kokarin ya dauki ALLON SIHIRI
ya
gudu dashi amma duk wanda hannunsa yaki kan
ALLON SIHIRI sai kaga an dankara masa SARA
ko
SUKA ko kaga an mangareshi ya fadi can gefe
daya
sumamme,ko kallonsa babu mai yi saidai ma
acigaba da tattakeshi a kokarin gwagwarmayar
daukar ALLON SIHIRIN.Tunda aka watsar dasu
Sarauniya Akisatul Sauwara gefe daya a
galabaice
suka kasa mikewa tsaye suka cigaba da zama
dirshen a kasa suna kallon wadannan Aljanu
kawai
suna ganin masifaffan yakin da ake yi tsakanin
wadannan samudawan bakaken aljanun.Su kansu
sun san cewa basu isa su iya tarar wadannan
aljanu
da yaki ba bare su iya karbar wan
Nan ALLON SIHIRI daga hannunsu.Saida aka
shafe
sama da sa'a biyu da rabi ana yin wannnan
azababben yaki ya zamana cewa da yawa daga
cikin
aljanun sun zama nakasassu wasu ba
hannaye,wasu
ba kafafu,wasu ma an datse rabin jikinsu,amma
saboda taurin rai irin na aljanu basu fasa cigaba
da
kokarin daukar ALLON SIHIRIN BA.Koda bakon
jarumi yaga ana ta bata lokaci amma an rasa
wanda
zamo GWARZON JARUMIN da zai iya daukar
ALLON
SIHIRIN sai kawai ya mike tsaye zumbur daga
inda
yake tsaye yana mai kwalla KABBARA ya falfalo
da
gudu izuwa inda akeyin wannan gumurzun
yako.Da
karfin tsiya ya ratsa ta tsakiyar samudawan
bakaken
aljanun yana bankesu suna zubewa kasa tamkar
yana sassabe a gona.Koda yazo tsakiyar aljanun
sai
ya sake saka tsalle sama izuwa inda Aljanun
sukayi
tsiri sama wani kan wani domin sukai izuwa kan
wani Gansamemen Aljani mafi tsawo,kauri da
Kirar
SADAUKANTAKA wanda shi ne ya sami nasarar
cafe
ALLON SIHIRIN ya bude fuka fukansa yai sama
da
niyyar ya gudu,amma sai wadansu daga cikin
aljanun suka ruko kafafun nasa suna janyoshi
kasa
don ya fado,amma sai suka kasa saboda
tsananin
karfin damtsensa.A haka sadaukin Aljanin ya
cigaba
da fuffuka yana kai yakushi SARA DA SUKA da
faratan kafafuwansa.Lokacin da bakon jarumin ya
daka tsalle a sama tamkar an harboshi daha
cikin
baka sai da ya iso inda basamuden sadaukin
aljanin
yake,yana isowa daidai fuskarsa sai ya takarkare
ya
zabga masa wawan naushi a fuska.Saboda karfin
naushin take karan hancin aljanin ya karye ya
kurma
uban ihu sakamakon tsananin zafi da zogin da
yaji.Nan take ya dimauce bai san sa'adda ya
saki
ALLON SIHIRIN ba.Caraf sai bakon jarumin ya
cafe
Allon Sihirin da hannu daya alhalin su kansu
samudawan aljanun basa iya daga Allon Sihirin
da
hannu daya saboda tsananin nauyinsa.Koda
Aljanun
suka ga wannan bil'adama ya karbe ALLON
SIHIRIN
sai sukayi caa!a kansa suka yanyameshi suna
masu
kai masa sara da suka ta ko ina domin su
hallakashi.Ai kuwa sai ya tarwatsa su a lokacin
da
ya sake kwalla Kabbara ya zare takobinsa cikin
bakin zafin nama ya shiga kare kansa gami da
maida martani.Wohoho!wanda Allah ya kare yafi
gaban Magauta!Duk da tsananin yawa na
wadannan
samudawan bakaken aljanu da tsananin karfin
damtsensu da mugayen makamansu sai gashi
bakon jarumi ya zame musu ALAKAKAI,Sai gashi
yayi musu mummunar barnar datafi wacce
sukayiwa
kansu,domin kuwa duk aljanin da yayiwa duka
daya
tofa idan ya baje a kasa wanwar da kyar ma
yake iya
numfashi wasu ma kamar sun zama gawa.Kai!da
bala'i yakai bala'i sai gashi aljanun suna cika
wandunansu da iska suna ficewa daga cikin
dakin
da gudu.Kafin a jima duk sun tarwatse sun fice
daga
cikin dakinsu duka sun bar bakon jarumin shi
kadai
a tsaye rike da ALLON SIHIRIN a lokacin da dakin
yayi tsit tamkar babu wani mutum daya mai rai a
cikinsa.Yarima Lubainu,Sarauniya Akisatul
Sauwara
kuwa saboda tsananin mamaki bisa ganin irin
gagarumar jarumtakar da bakon jarumin yayi sai
suka kura masa idanu kawao suka kasa budar
baki
suce wani abu,kai mikewa ma tsaye sai ya
gagaresu.Koda ganin haka sai bakon jarumin ya
dubi dan wada Dazyan yayi masa wata inkiya,shi
kuma sai ya dubi Sarauniyar Akisatul Sauwara da
Sarki Darmanu da Yarima Lubainu
yace,Maigidana
yace bazai baiwa dayanku wannan Allon Sihiri ba
face an zauna an tattauna kuma koda ma ya
baiwa
dayanku shi bazai sami damar karantashi ba bare
har ya cika burinsa saboda masu farautar Allon
Sihirin suna da yawa kuma sunfi ku karfin damtse
dana Sihiri.Wadannan Bakaken Samudawan
Aljanu
da sukazo yanzu maigidana ya fatattakesu Yaran
Boka Darbusa ne anan gaba kuma akwai sauran
Manyan MATSAFAN DUNIYA da MANYAN
JARUMAI
dazasu fito farautar wannan ALLON SIHIRI.Kuma
shi
kanshi Boka Darbusa ba hakura zaiyi ba zai
cigaba
da kokarin karbarsa ne.Yanzu sai kowa yaje ya
nemi
dakin da zai kwanta a cikin wannna fada domin
ya
huta tunda dare yayi in yaso gobe da safe mu
tattauna akan abinda muke ganin cewar shi ya
kamata ayi.Gama fadin hakan keda wuya sai
Bakon
Jarumin ya juya domin ya fice daga cikin
wannan
daki,amma sai Sarauniya Akisatul Sauwara tayi
wuf,ta mike tsaye kuma tayi gyaran murya
tace,yakai
wannan JARUMIN JARUMAI kayi sani cewa mu
muna
cikin tsoro da fargaba don haka bazamu iya
sakin
jikinmu ba har mu kwanta a cikin wannnan fada
ta
Boka Darbusa mu iya kwana a cikinta saboda a
ko
yaushe zai iya kawo mana ZIYARAR BAZATO ya
cutar damu.Koda jin wannan jawabi sai Bakon
Jarumin yaji kamar ya bushe da dariya amma sai
ya
dake ya dubi dan wada Dazyan yayi masa zancen
kurame.Nan take Dazyan ya dubi Sarauniya
Akisatul
Sauwara yace,ashe bakuyi mamakin yadda
shugaban
ya iya yakar Boka Darbusa ba da dukkan
Aljanunsa?
Shin bakuyi mamakin yadda ya gano inda Allon
Sihirinsa yake ba ya daukoshi kuma har ya hana
wasu saceshi?To ku sani cewa zamanku anan
cikin
wannnan gida tare da shugabana shine kadai
abinda
zai baku kariya amma da zarar kun fita daga nan
to
fa komai zai iya faruwa a gareku,kuma abune
mayuwaci dayanku ya iya tsira da rayuwarsa
bare
har ya sami damar cika burinsa.Koda gama fadin
hakan sai Bakon Jarumin ya saba ALLON SIHIRI
a
hammatarsa ya juya ya fice daga cikin wannan
daki
Dazyan na biye dashi.Koda ganin haka ai
Sarauniya
Akisatul Sauwara,Yarima Lubainu da Sarki
Darmanu
suka bishi da sauri cikin alamun tsoro suna ta
waige
waige,gani suke kamar ma a koda yaushe Boka
Darbusa ko wakilinsa zasu iya kawo musu hari a
ko
yaushe. kuyi hakuri dangane da jinkirin post yauALLON SIHIRI
Littafi na Uku (3)
Part D
LOKACIN da Bakom Jarumi ya fita daga cikin
wannan daki na kayan sihirin Bokab Darbusa sai
ya
tunkari inda turakarsa ta barci take,kai tsaye sai
kace
dama can yasan kowanne lungu da sako na
gidan.Da isowarsa kofar turakar sai ya tsaya cak
sannan ya juyo baya.Take yayi arba dasu
sarauniya
Akisatul Sauwara suna biye dashi.Cikin matukar
mamaki ya dubesu sannan ya dubi Dazyan sukayi
magana kamar yadda suka sabaDazyan ya dubi
su
Sarauniya Akisatul Sauwara yace shugabana
yace na
gaya muku ba zai taba yiyuwa ba ya kwana da
dayanku a cikin

2 / 3