Author : Hafsat C Sodangi Category : Romantic Hausa Novels
/>
da zai bukata idan ya fito daga
wankan.
Na dawo dakin inda na bar su
Tasi'u suna nan inda suke, kallon
cartoon din da na saka musuna
Kiddies world suke yi har yanzu.
28
Ban dade da dawowa ba Bala ya
shigo da aiken da aka yi mishi babbar
leda cike da kayan kwalama.
Ya ajiye ya juya na kira shi na debi
mai yawa na ba shi saboda sanin da
nayi yana da yaya suna kuma zaune
ne a boys Quarters din gidan.
Godiya sosai yayi ya juya. Na bai
wa su Tasi'u wanda za su iya ci na kai
saura fridge na ajiye saboda Ice
Cream din kada ya narke.
Ganin da nayi hankalinsu ya yi nisa
yasa na koma wurin Ahmad ya gama
shirinshi har ya fito falon yana
kokarin fitowa na ce, "Ai abincinka
nazo na baka ya ce mu koma wurinki
na ci a can, na ce to."
A falona yaci abincin shi muka ci
gaba da hirar mu, su Tasi'u ma suna
harkokinsu har suka yi barci. Na
29
dauke su naje daya dakin nawa na
kwantar da su na dawo in da Ahmad
yake.
Ya jawo ni jikinshi ya kwantar da
ni a kan kafafunshi yana shafa gashin
kaina.
"Tun da ki ka zo gidan nan ina
kallon ki ba ki taba yin kitso ba." Na
ce, Ai ban san inda za a yi mun
kitson ba ne a unguwar nan."
Ya ce, "Eh mai yi ma su Zainab
tazo tayi miki gobe. Na ce, "To."
A dakinamuka kwana ya ce
saboda su Tasi'u kada a bar su su
kadai. Sammako sOsai yanzun nake yi
saboda karyawar Ahmad tunda na
lura ba son shayi da biredi yake yi ba.
Pizza na mishi na hada mishi da
ruwan lipton saboda complain din da
30
yake yi akan tebar shi da take kara
habaka.
Duk da na gaya mishi ni bana
ganinta. Sai da na sallame shi ya tafi
sannan na dawo na shirya su Tasi'u
cikin sababbin kayansu muka karya
muna 'yar hirarmu cikin raha da ban
dariya suna bani labarai.
Su na tambaya abinda zan girka
musu suka fadaa na shiga nayi musu
muka ci tare sannan na dauko Ice
Cream din su na jiya na ba su suka
sha suka ce mun za su je wasa a waje.
Kamar na hana su sai dai naga kada
na takura su tunda yara ne.
Tashi nayi na nuna musu wurin da
yara suke wasa sannan na dawo
dakina na hau gado na kwanta.
Ban dadc sosai da kwanciya ba sai
ga dan aika daga kasuwa Ahmad ya
31
aiko shi da sakon su Tasi'u. Na karba
ina dubawa.
Kaya ne masu asalin kyau yan
kanti set uku-uku, sai takalma sandals
na asali.
Na ajiye kayan na leka don na kira
su daga nesa na hango su a kan lilo,
don haka na dawo na bar su suka ci
gaba da wasan su.
Ni kuma na shiga kicin don fara
shirin abincin dare. Ihun da nake
jiyowa ne yasa ni saurin fitowa, don
kuwa ya yi mun kama da na Tasi'u.
Sai dai kafin na fita waje har sun
shigo dakin cikin tsananin rudewa na
kwallara kara tare da fadin "Inna
lillahi wa inna ilaihi raj1'una."
Jini ne kawai har ya rine rigarshi
gaba daya. Waje nayi da gudu saboda
rudewa.
32
Daga nesa Bala direba ya hango ni
ya taho cikin sauri "Lafiya, lafiya? 99
Na ce, Zo ka gani. Na taho dakin
har ya zauna a kasa cikin saurin shi
ya sunkunci Tasi'u nima na bishi a
mota ya saka shi zuwa asibiti.
Ban jira dawowansu ba bin su nayi.
Ba karamin jin ciwo Tasi'u ya yi
ba, don kuwa sai da aka yi mishi
dinki a keyarshi a ka yi dressing din
wurin aka yi mishi allurai sannan
muka dawo gida wajen karfe shida da
rabi na yamma.
Har dakina Bala direba ya kawo shi
kan kujera ya ajiye shi. Muryar shi
har ta dishe saboda kuka. Na tsaya a
kanshi ina kallon shi saboda tausayin
da ya bani.
Na koma bandakina na dauko
sandar goge-goge na goge duk jinin
33
da ya mannu a tayels din na saka
dettol na sake gogewa sannan na
shiga kicin cikin sauri don na dan yi
wa Ahmad abincin da zai ci.
Sai dai ko dorawa ban yi ba sai ga
motarshi ta shigo gidan, duk da haka
ban fasa ba saboda nasan ba wurina
zai wuto ba.
Cikin kankanin lokaci na yi mishi
fried rice da coleslaw salad, sannan na
dawona dauki Tasi'u da barci ya riga
ya dauke.
Naje nayi mishi wanka da ruwa
mai zafi saboda ya ji dadin jikinshi,
na hada mishi tea na ba shi sannan na
ba shi magungunan da Likita ya ba
shi.
Naje na kwantar da su ban wani bar
su suka tsaya kallo ba.
34
Ahmad ya shigo lokacin ne nake
wanka amma kafin na fito ya tafi
dakinshi, don haka sai kawai na bi shi
can.
Shi ma wankan na samu yake yi
don kuwa dabi'arshi ce vin wanka, da
zarar ya idar da sallar Isha'i yana cin
abincin shi yana dan kallona.
Zuwa can dai ya kasa yin shiru ya
ce, "Menene ya faru ne amarya?
Na ce "Me ka gani? Ya ce, "Ba
haka na saba ganinki ba. Kamar nayi
shiru don kuwa abin da zuciyata take
ta gaya mun kenan sai dai na kasa.
Abin kawai da na sani shi ne,
Sabi'u ba zai yi mun karya ba, don
kuwa yana wurin da abin ya faru ya
kuma tabbatar mun da Ziradat ce ta
wurgar da Tasi'u akan liie ya ji
wannan ciwon.
35
Na share hawayena da na gama yi
mishi bayani, ya ce "Yanzu yana
ina? Na ce, Ya yi barci. Mikewa
yayi ya taho dakin da nake kwantar
da su har yanzu wata irin ajiyar
zuciya yake yi.
Duk da nisan da barcin shi ya yi ya
zuba mishi ido yana kallon lafcecen
bandejin da aka toshe ciwon da shi,
ya juya ya fita.
Shiru naji bai dawo ba, na mike
zan fita sai na hango shi yana tahowa
daga sashen Hajiya, duk da ban san
me ya faru ba gabana ne ya fadi da na
kalli fuskarshi.
Na kauce na ba shi hanya ya shige
daki ya kwanta, ni ma kwanciyar nayi
ban ce mishi komai ba, tunda shi ma
bai ce mun ba.
36
Washegari sai da ya gama shiri zai
fita ne ya kalle ni.
"Kiyi hakuri Hauwa'u, zan so ki
dauke shi a matsayin tsautsayi duk da
dai nasan ganganci ne kawai irin na
yara."
Na ce, "Babu komai." Ya fita, Na
shirya kamar kullum na shiga sashen
Hajiya don na gaisheta.
Kallon kawai da ta yi mun ne ya y1
matukar sanyaya mun jikina.
Na gaisheta ta amsa sannan ta ce,
Ko da wasa kada ki kuskura ki kara
kai karar yaran nan wurin Babansu na
gaya miki kada ki kara.
Ba a yi mun haka, kada ki shiga
gonata saboda bana son abinda zai sa
na saba miki. Tashi ki bani wuri."
37
Dawowa dakina nayi, nayi
sumukwi nayi tsit saboda sanyin da
jikina ya yi.
Ban yarda na mayar da su Tasi'u
gida ba kamar yadda naso nayi sai da
ya ji sauki sosai har aka cire mishi
bandejin.
Ahmad kuwa siyayya ya yi musu
mai ban sha'awa har da Kekuna ya ba
su, sannan yasa Bala ya mayar da su
gida.
Na riga na saba duk ranar Litinin
da Alhamis Hajiya tana Azumin
nafila, tunda nazo kuma duk da cewar
da tayi na daina saka mata abinci idan
nayi bai sa na fasa yi mata girkin
abincin buda baki a wadannan
ranakun ba.
Tun tana hanawa har tayi shiru,
kasancewar yau Alhamis sai na shirya
38
mata farfesun danyen kifi mai hadi
sannan nayi mata lafiyayyen alcle na
ganye da kunun gyada na danyar
shinkafa.
Na hada wuri daya ina nufin dauka
na kai sai ga wayar Ahmad ya aiko
dan aike na ba shi takardar da ya bari
a kan bed side din shi da ke cikin
dakinshin.
Hakan ne yasa nayi waya sashen su
don Larai tazo ta dauki abincin, sai
aka ce bata nan, don haka na ce
Zainab tazo ta dauka.
Na shiga na dauko wa dan aiken
sakon shi na ba shi, sannan na dawo
na ci gaba da harkokin abincina.
Sai da na kammala komai nayi
wanka nayi kwalliya tare da sallar
Magriba sannan na fito wurin Hajiya
don nayi mata sannu da shan ruwa.
39
Ina shiga Ahmad yana fita saboda
sallamar da aka yi da shi a waje.
Na durkusa gefe na gaisheta tana
amsawa kamar kullum yanayinta ta
kuma yi mun sannu. Na mike zan fito
sai naji an kira sunana.
Na waiwayo da sauri don ganin
mai maganar. Tun da nazo gidan yau
ne naji Zainab tayi magana da ni.
Tana rike da kofar dakinsu da
hannu daya yayin da dayan kuma
take nuno ni da shi.
"Kada ki kuskura ki sake yin waya
ki ce a turo ni ki aike ni kin ji na gaya
miki. Ba na daukan raini idan kin lura
za ki gane tunda ki ka zo gidan nan
ban taba shiga harkarki ba.
Idan me aika ki ke so, to gayawa
wanda ya ajiye ki ya nemo miki." Ta
juya ta koma dakin da ta fito.
40
Ina tsaye a bakin kofar dakin ko
ina a jikina sai tsatsafo da gumi yake
yi.
Murmushi Hajiya tayi ta ce "Kai
Zainab kenan, ina dai yi miki addu'a
Allah ya shirye ki. Je ki abin ki
Hauwa'u rabu da ita."
Na juyo na dawo daki raina a
cushe. Har lokacin da Ahmad ya
shigo na rasa yadda zan yi na saki
raina.
Duk wani abinda na saba yi mishi
na mishi sai dai da muka kwanta
Juyawata nayi na rabu da shi, don
kuwa abin har yanzu yana cina.
Yayi tambayar har ya gaji wai na
gaya mishi abinda ke damuna na ce
babu komai. Ya ce, haka kawai ki ke
mun irin wannan abin.
41
Nayi shiru naga zai ja mun wata
matsala na ce mishi ba ni da lafiya, ya
ce Idan ba ki da lafiya ba za ki yi
magana ba sai kawai ki juya mun
keya?
Juyowa nayi na ba shi hakuri,
sannan aka zauna lafiya.
Duk wani kokari da nake yi na gani
ban shiga sabga r 'ya'yan Ahmad ba
nayi shi, amma hakan bai sa sun bar
ni ba tare da su suna shiga tawa
harkar ba.
Babu ma dai shaidaniya irin
Ziradat, haka kawai yarinyar bata
kwanta mun ba. Gara Zainab bata
kallon inda nake bata yi mun magana
amma ita ko baki nayi to sai tasan
yadda tayi ta yi musu abinda ransu ya
6aci.
42
Duk wanda tayi wa rashin
mutuncinta hakuri nake ba shi tunda
ko a gaban Hajiya ne hakurin zataa
bayar sai ko bin su da take yi da
addu'ar shiriya.
Ba ni da wata matsala daga wurin
mijina, muhimmmin abu kenan a
wajena.
Wata irin iska mai karfin gaske aka
yi da daddare, wacce ta bugo satelite
dish din sashen su ya fado kasa.
A lokacin nan Ahmad baya nan,
don haka ba a gyara ba. Tun da abin
nan ya lalace sai suka dawo kallon su
Wurina.
Ziradat da Zinatu safe, rana da dare
a dakina suke wuni, ba na sawa ba na
hanawa.
Sannan ga su da ciye-ciye duk
abinda suka ci kuma to a wurin za su
43
yar da bawon shi ko kuma su bar
kwanon a wurin ko da wacce irin
shara ko gyara na yi wa gun.
Ban taba daga ido na kalli abin da
suke yi ko na gaji nayi musu magana
ba.
Abin dai da na sani shi ne, ya kusa
wucewa tunda maigidan ya dawo a
jiya da daddare bayan tafiyar da yayi
ta wajen sati biyu.
Na gama aikina tas da yamma na
gyara dakina da na Ahmad na duba
babu wani abin da zan yi.
Don haka nayi wanka na gyara
kaina, nayi kwalliya ta burgewa
sannan na dawo falona da yake ta
kanshi na zauna ina kallon
programme din (Ask Huda) da ake yi
a Huda TV.
44
Kan wata tambaya dangane da jinin
Haila da ake amsa ta wacce ta dade
tana daure mun kai.
Sai kawai Zinatu ta shigo dakin
nan da sauri ta dauki remote ta canza
zuwa kidsco wai zata ga cartoon.
Wani gululun takaici ya taso min,
ban san yadda aka yi na daka mata
tsawa ba.
Na ce, "Meye haka? Dalla can
mayar mun inda ki ka same shi."
Iyakacin abinda na ce kenan yarinyar
nan ta tayi jifa da remote dinnan ya
daki bango ya wargaje.
Sannan ta falla a guje tana kurma
wani irin ihu, sai ka ce wacce ya
yanke wa wata gaba a jikinta.
Wani sabon takaicin ya sake kama
ni, ganin remote din ya ki aiki na
tattara shi na aj1ye.
45
Na shiga dakina na bi lafiyar gado
ina 'yan sake-sakena.
Larai ce tayi sallama ta shigo, wai
in je Hajiya tana kirana. Na fito bayan
na lullube jikina da gyale.
"Me ya hada ki da Zinatu ki ka
bugeta?" Na kalli yarinyar yadda ta
takure a jikin kujera har yanzu kuka
take yi.
Na ce, "Hajiya ban bugeta ba." Na
fara kokarin yi mata bayanin abin da
ya faru.
Ta ce, "Dakata! Kin ga yadda muka
fara zama cikin fahimtar juna? To ba
na so wani abu ya shigo daga baya,
don idan nayi niyyar daukan mataki
akan mutum abin ba ya yi mishi kyau.
Kada na sake jin an ce ko kallon
banza kin yi wa wani da a cikin gidan
46
nan, ballantana har ta kai ga kin saka
hannu a jikinsu.
Ki zauna a matsayinki su zauna a
matsayinsu. Ni bana dukan yarana
tunda ubansu ma a haka na
tarbiyantar da abina.
Duk wanda ya ce ba zai yi hakuri
da su a haka har kafin su fahimci kan
al'amarin duniya ba, to sai yasan
nayi.
Ba na so, kada kuma na sake jin
don sun je wurinki sai kiyi mata haka
har tana sulewa saboda razana? Ai
nan gidan ubanta ne tana da ikon
shiga duk inda take so ta wala."
Na dawo dakina nayi alwala nayi
sallar magriba har aka yi Isha'i ban
tashi daga wurin ba.
Don haka na mike nayi sallar Isha'i
tare da shafa'i da wutiri. Motsin
47
Ahmad naji a wurin shi ne na dauki
abincin shi na kai mishi.
Ina ajiyewa ya ce, "Me ya hada ki
da Zinatu ki ka yi mata irin wannan
dukan? Wato kin gane ko? Ni da ki ke
gani ina matukar tsoron tashin
hankali.
A waje ban huta ba, babu abin da
nake bukata irin na shigo gida dan
hutun da zan yi da iyalina na yishi
cikin kwanciyar hankali da farin ciki
ba.
Menene haka? Tun farko na gaya
miki kiyi kokarin zama ba tare da
wani abu ya hada ki da wani yaro ba,
saboda nima hakuri nake yi da su.
Hajiya kuma ina matukar kokarin
ganin bacin rai, bai same ta ba
ballantana a ce sanadina ne,"
48
Naga fadan nashi zai yi yawa
saboda wani abu bai taba hada ni da
shi makamancin haka ba, a tsawon
zaman da nayi a gidan na watanni
shida.
Na ce, Ban fa bugeta ba." Ya
watso mun ido "Ba ki bugeta ba? Na
ce "Na rantse maka ban bugeta ba."
"Me ki ke nufi kenan? Kina so ki
ce mun Mahaifiyata tayi miki karya?"
Nan da nan na fara kuka saboda jin
inda ya mayar da abin.
Nan take kuma fadan yafi na dah
wai na karyata mishi uwa. Ga gaskiya
nan kiri-kiri jikin yarinya ya rure har
zazzabi ya rufeta amma kina karyata
mahaifiyata.
Mara kunyar yarinya, tashi ki ba ni
wuri."
49
Na tashi na dawo dakina nayi kuka
har na gaji, idanuna suka yi luhu-luhu
saboda rashin barcin da ban yi ba.
Na gama abin karyawa kamar ba
zan shiga sashen nashi ba, tunda
korata ya yi jiya sai naga kada na
karawa kaina matsala.
Na dauka na kai mishi na ajiye na
juyo abina, tunda a da wannan damar
tayin gaba da wani ina dai bin doka
ne kawai. To da haka wanna ya wuce.
Ba karamin taka tsantsan nake yi
da yaran Ahmad da mahaifiyarshi ba,
saboda ina son aurena.
Gashi kuma cikin kankanin lokaci
sai na mallaki abubuwan kadara irin
Su,gold da zinari saboda yawan
tafiyar da yake yi.
Kuma shi mai sakin hannu ne.
matsalata a kullum ba daga shi ba ne
50
sannan babu fashi sai dai idan bai yi
tafiya ya dawo ba sai an ce nayi kaza
nayi kaza.
Ita kuma Hajiya ta ce aja mun
kunne, to garin aja kunnen sai ya
zama tashin hankali, ina batawa
mahaifiyarshi rai.
Sannan babu damar nayi musun
ban yi ba sai laifin nawa yayi yawa,
na karyata mahaifiyarshi, don haka
kullum a haka muke.
A daidai wannan lokacin ne ta
bayyana ina dauke da juna biyu har
na shiga wàta na uku.
Hakan ne ya matukar takura ni naa
kasa yin Azumin watan Ramadana,
saboda tsananin laulayin da nake yi.
Ba Ahmad ba ma har Hajiya a
wannan lokacin ta sassauta mun, don
51
haka babbar matsala a yanzu
laulayina ne da kuma yaran.
Tunda yanzu ba barina suka yi da
karata wurin Babansu duk da laulayin
da nake yi bai hana ni kiba na murje
ba.
Shirin sallah sosai ake yi don kuwa
gidan ma a cike yake da mutane 'yan
uwan su da suka zo daga kauye da
kuma babban dan Ahmad Zubair.
Wanda yanzu ne muka san juna da,
shi.
Shi kam babu laifi yana da hankali
don Aunty ma yake kirana. Haka nan
nima duk da sanin da nayi suna buda
baki a wurin Hajiya hada mishi nake
yi da Babanshi.
Sannan ganin shi yasa hatta Zainab
ta saurara da wasu abubuwan
ballantana su