MAI DAKI BOOK 3 HAUSA READ NOVELS BY SODANGI.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   2 / 6

3K to 6K   out of 15.7K words

/>
da zai bukata idan ya fito daga

wankan.

Na dawo dakin inda na bar su

Tasi'u suna nan inda suke, kallon

cartoon din da na saka musuna

Kiddies world suke yi har yanzu.

28

Ban dade da dawowa ba Bala ya

shigo da aiken da aka yi mishi babbar

leda cike da kayan kwalama.

Ya ajiye ya juya na kira shi na debi

mai yawa na ba shi saboda sanin da

nayi yana da yaya suna kuma zaune

ne a boys Quarters din gidan.

Godiya sosai yayi ya juya. Na bai

wa su Tasi'u wanda za su iya ci na kai

saura fridge na ajiye saboda Ice

Cream din kada ya narke.

Ganin da nayi hankalinsu ya yi nisa

yasa na koma wurin Ahmad ya gama

shirinshi har ya fito falon yana

kokarin fitowa na ce, "Ai abincinka

nazo na baka ya ce mu koma wurinki

na ci a can, na ce to."

A falona yaci abincin shi muka ci

gaba da hirar mu, su Tasi'u ma suna

harkokinsu har suka yi barci. Na

29

dauke su naje daya dakin nawa na

kwantar da su na dawo in da Ahmad

yake.

Ya jawo ni jikinshi ya kwantar da

ni a kan kafafunshi yana shafa gashin

kaina.

"Tun da ki ka zo gidan nan ina

kallon ki ba ki taba yin kitso ba." Na

ce, Ai ban san inda za a yi mun

kitson ba ne a unguwar nan."

Ya ce, "Eh mai yi ma su Zainab

tazo tayi miki gobe. Na ce, "To."

A dakinamuka kwana ya ce

saboda su Tasi'u kada a bar su su

kadai. Sammako sOsai yanzun nake yi

saboda karyawar Ahmad tunda na

lura ba son shayi da biredi yake yi ba.

Pizza na mishi na hada mishi da

ruwan lipton saboda complain din da

30

yake yi akan tebar shi da take kara

habaka.

Duk da na gaya mishi ni bana

ganinta. Sai da na sallame shi ya tafi

sannan na dawo na shirya su Tasi'u

cikin sababbin kayansu muka karya

muna 'yar hirarmu cikin raha da ban

dariya suna bani labarai.

Su na tambaya abinda zan girka

musu suka fadaa na shiga nayi musu

muka ci tare sannan na dauko Ice

Cream din su na jiya na ba su suka

sha suka ce mun za su je wasa a waje.

Kamar na hana su sai dai naga kada

na takura su tunda yara ne.

Tashi nayi na nuna musu wurin da

yara suke wasa sannan na dawo

dakina na hau gado na kwanta.

Ban dadc sosai da kwanciya ba sai

ga dan aika daga kasuwa Ahmad ya

31

aiko shi da sakon su Tasi'u. Na karba

ina dubawa.

Kaya ne masu asalin kyau yan

kanti set uku-uku, sai takalma sandals

na asali.

Na ajiye kayan na leka don na kira

su daga nesa na hango su a kan lilo,

don haka na dawo na bar su suka ci

gaba da wasan su.

Ni kuma na shiga kicin don fara

shirin abincin dare. Ihun da nake

jiyowa ne yasa ni saurin fitowa, don

kuwa ya yi mun kama da na Tasi'u.

Sai dai kafin na fita waje har sun

shigo dakin cikin tsananin rudewa na

kwallara kara tare da fadin "Inna

lillahi wa inna ilaihi raj1'una."

Jini ne kawai har ya rine rigarshi

gaba daya. Waje nayi da gudu saboda

rudewa.

32

Daga nesa Bala direba ya hango ni

ya taho cikin sauri "Lafiya, lafiya? 99

Na ce, Zo ka gani. Na taho dakin

har ya zauna a kasa cikin saurin shi

ya sunkunci Tasi'u nima na bishi a

mota ya saka shi zuwa asibiti.

Ban jira dawowansu ba bin su nayi.

Ba karamin jin ciwo Tasi'u ya yi

ba, don kuwa sai da aka yi mishi

dinki a keyarshi a ka yi dressing din

wurin aka yi mishi allurai sannan

muka dawo gida wajen karfe shida da

rabi na yamma.

Har dakina Bala direba ya kawo shi

kan kujera ya ajiye shi. Muryar shi

har ta dishe saboda kuka. Na tsaya a

kanshi ina kallon shi saboda tausayin

da ya bani.

Na koma bandakina na dauko

sandar goge-goge na goge duk jinin

33

da ya mannu a tayels din na saka

dettol na sake gogewa sannan na

shiga kicin cikin sauri don na dan yi

wa Ahmad abincin da zai ci.

Sai dai ko dorawa ban yi ba sai ga

motarshi ta shigo gidan, duk da haka

ban fasa ba saboda nasan ba wurina

zai wuto ba.

Cikin kankanin lokaci na yi mishi

fried rice da coleslaw salad, sannan na

dawona dauki Tasi'u da barci ya riga

ya dauke.

Naje nayi mishi wanka da ruwa

mai zafi saboda ya ji dadin jikinshi,

na hada mishi tea na ba shi sannan na

ba shi magungunan da Likita ya ba

shi.

Naje na kwantar da su ban wani bar

su suka tsaya kallo ba.

34

Ahmad ya shigo lokacin ne nake

wanka amma kafin na fito ya tafi

dakinshi, don haka sai kawai na bi shi

can.

Shi ma wankan na samu yake yi

don kuwa dabi'arshi ce vin wanka, da

zarar ya idar da sallar Isha'i yana cin

abincin shi yana dan kallona.

Zuwa can dai ya kasa yin shiru ya

ce, "Menene ya faru ne amarya?

Na ce "Me ka gani? Ya ce, "Ba

haka na saba ganinki ba. Kamar nayi

shiru don kuwa abin da zuciyata take

ta gaya mun kenan sai dai na kasa.

Abin kawai da na sani shi ne,

Sabi'u ba zai yi mun karya ba, don

kuwa yana wurin da abin ya faru ya

kuma tabbatar mun da Ziradat ce ta

wurgar da Tasi'u akan liie ya ji

wannan ciwon.

35

Na share hawayena da na gama yi

mishi bayani, ya ce "Yanzu yana

ina? Na ce, Ya yi barci. Mikewa

yayi ya taho dakin da nake kwantar

da su har yanzu wata irin ajiyar

zuciya yake yi.

Duk da nisan da barcin shi ya yi ya

zuba mishi ido yana kallon lafcecen

bandejin da aka toshe ciwon da shi,

ya juya ya fita.

Shiru naji bai dawo ba, na mike

zan fita sai na hango shi yana tahowa

daga sashen Hajiya, duk da ban san

me ya faru ba gabana ne ya fadi da na

kalli fuskarshi.

Na kauce na ba shi hanya ya shige

daki ya kwanta, ni ma kwanciyar nayi

ban ce mishi komai ba, tunda shi ma

bai ce mun ba.

36

Washegari sai da ya gama shiri zai

fita ne ya kalle ni.

"Kiyi hakuri Hauwa'u, zan so ki

dauke shi a matsayin tsautsayi duk da

dai nasan ganganci ne kawai irin na

yara."

Na ce, "Babu komai." Ya fita, Na

shirya kamar kullum na shiga sashen

Hajiya don na gaisheta.

Kallon kawai da ta yi mun ne ya y1

matukar sanyaya mun jikina.

Na gaisheta ta amsa sannan ta ce,

Ko da wasa kada ki kuskura ki kara

kai karar yaran nan wurin Babansu na

gaya miki kada ki kara.

Ba a yi mun haka, kada ki shiga

gonata saboda bana son abinda zai sa

na saba miki. Tashi ki bani wuri."

37

Dawowa dakina nayi, nayi

sumukwi nayi tsit saboda sanyin da

jikina ya yi.

Ban yarda na mayar da su Tasi'u

gida ba kamar yadda naso nayi sai da

ya ji sauki sosai har aka cire mishi

bandejin.

Ahmad kuwa siyayya ya yi musu

mai ban sha'awa har da Kekuna ya ba

su, sannan yasa Bala ya mayar da su

gida.

Na riga na saba duk ranar Litinin

da Alhamis Hajiya tana Azumin

nafila, tunda nazo kuma duk da cewar

da tayi na daina saka mata abinci idan

nayi bai sa na fasa yi mata girkin

abincin buda baki a wadannan

ranakun ba.

Tun tana hanawa har tayi shiru,

kasancewar yau Alhamis sai na shirya

38

mata farfesun danyen kifi mai hadi

sannan nayi mata lafiyayyen alcle na

ganye da kunun gyada na danyar

shinkafa.

Na hada wuri daya ina nufin dauka

na kai sai ga wayar Ahmad ya aiko

dan aike na ba shi takardar da ya bari

a kan bed side din shi da ke cikin

dakinshin.

Hakan ne yasa nayi waya sashen su

don Larai tazo ta dauki abincin, sai

aka ce bata nan, don haka na ce

Zainab tazo ta dauka.

Na shiga na dauko wa dan aiken

sakon shi na ba shi, sannan na dawo

na ci gaba da harkokin abincina.

Sai da na kammala komai nayi

wanka nayi kwalliya tare da sallar

Magriba sannan na fito wurin Hajiya

don nayi mata sannu da shan ruwa.

39

Ina shiga Ahmad yana fita saboda

sallamar da aka yi da shi a waje.

Na durkusa gefe na gaisheta tana

amsawa kamar kullum yanayinta ta

kuma yi mun sannu. Na mike zan fito

sai naji an kira sunana.

Na waiwayo da sauri don ganin

mai maganar. Tun da nazo gidan yau

ne naji Zainab tayi magana da ni.

Tana rike da kofar dakinsu da

hannu daya yayin da dayan kuma

take nuno ni da shi.

"Kada ki kuskura ki sake yin waya

ki ce a turo ni ki aike ni kin ji na gaya

miki. Ba na daukan raini idan kin lura

za ki gane tunda ki ka zo gidan nan

ban taba shiga harkarki ba.

Idan me aika ki ke so, to gayawa

wanda ya ajiye ki ya nemo miki." Ta

juya ta koma dakin da ta fito.

40

Ina tsaye a bakin kofar dakin ko

ina a jikina sai tsatsafo da gumi yake

yi.

Murmushi Hajiya tayi ta ce "Kai

Zainab kenan, ina dai yi miki addu'a

Allah ya shirye ki. Je ki abin ki

Hauwa'u rabu da ita."

Na juyo na dawo daki raina a

cushe. Har lokacin da Ahmad ya

shigo na rasa yadda zan yi na saki

raina.

Duk wani abinda na saba yi mishi

na mishi sai dai da muka kwanta

Juyawata nayi na rabu da shi, don

kuwa abin har yanzu yana cina.

Yayi tambayar har ya gaji wai na

gaya mishi abinda ke damuna na ce

babu komai. Ya ce, haka kawai ki ke

mun irin wannan abin.

41

Nayi shiru naga zai ja mun wata

matsala na ce mishi ba ni da lafiya, ya

ce Idan ba ki da lafiya ba za ki yi

magana ba sai kawai ki juya mun

keya?

Juyowa nayi na ba shi hakuri,

sannan aka zauna lafiya.

Duk wani kokari da nake yi na gani

ban shiga sabga r 'ya'yan Ahmad ba

nayi shi, amma hakan bai sa sun bar

ni ba tare da su suna shiga tawa

harkar ba.

Babu ma dai shaidaniya irin

Ziradat, haka kawai yarinyar bata

kwanta mun ba. Gara Zainab bata

kallon inda nake bata yi mun magana

amma ita ko baki nayi to sai tasan

yadda tayi ta yi musu abinda ransu ya

6aci.

42

Duk wanda tayi wa rashin

mutuncinta hakuri nake ba shi tunda

ko a gaban Hajiya ne hakurin zataa

bayar sai ko bin su da take yi da

addu'ar shiriya.

Ba ni da wata matsala daga wurin

mijina, muhimmmin abu kenan a

wajena.

Wata irin iska mai karfin gaske aka

yi da daddare, wacce ta bugo satelite

dish din sashen su ya fado kasa.

A lokacin nan Ahmad baya nan,

don haka ba a gyara ba. Tun da abin

nan ya lalace sai suka dawo kallon su

Wurina.

Ziradat da Zinatu safe, rana da dare

a dakina suke wuni, ba na sawa ba na

hanawa.

Sannan ga su da ciye-ciye duk

abinda suka ci kuma to a wurin za su

43

yar da bawon shi ko kuma su bar

kwanon a wurin ko da wacce irin

shara ko gyara na yi wa gun.

Ban taba daga ido na kalli abin da

suke yi ko na gaji nayi musu magana

ba.

Abin dai da na sani shi ne, ya kusa

wucewa tunda maigidan ya dawo a

jiya da daddare bayan tafiyar da yayi

ta wajen sati biyu.

Na gama aikina tas da yamma na

gyara dakina da na Ahmad na duba

babu wani abin da zan yi.

Don haka nayi wanka na gyara

kaina, nayi kwalliya ta burgewa

sannan na dawo falona da yake ta

kanshi na zauna ina kallon

programme din (Ask Huda) da ake yi

a Huda TV.

44

Kan wata tambaya dangane da jinin

Haila da ake amsa ta wacce ta dade

tana daure mun kai.

Sai kawai Zinatu ta shigo dakin

nan da sauri ta dauki remote ta canza

zuwa kidsco wai zata ga cartoon.

Wani gululun takaici ya taso min,

ban san yadda aka yi na daka mata

tsawa ba.

Na ce, "Meye haka? Dalla can

mayar mun inda ki ka same shi."

Iyakacin abinda na ce kenan yarinyar

nan ta tayi jifa da remote dinnan ya

daki bango ya wargaje.

Sannan ta falla a guje tana kurma

wani irin ihu, sai ka ce wacce ya

yanke wa wata gaba a jikinta.

Wani sabon takaicin ya sake kama

ni, ganin remote din ya ki aiki na

tattara shi na aj1ye.

45

Na shiga dakina na bi lafiyar gado

ina 'yan sake-sakena.

Larai ce tayi sallama ta shigo, wai

in je Hajiya tana kirana. Na fito bayan

na lullube jikina da gyale.

"Me ya hada ki da Zinatu ki ka

bugeta?" Na kalli yarinyar yadda ta

takure a jikin kujera har yanzu kuka

take yi.

Na ce, "Hajiya ban bugeta ba." Na

fara kokarin yi mata bayanin abin da

ya faru.

Ta ce, "Dakata! Kin ga yadda muka

fara zama cikin fahimtar juna? To ba

na so wani abu ya shigo daga baya,

don idan nayi niyyar daukan mataki

akan mutum abin ba ya yi mishi kyau.

Kada na sake jin an ce ko kallon

banza kin yi wa wani da a cikin gidan

46

nan, ballantana har ta kai ga kin saka

hannu a jikinsu.

Ki zauna a matsayinki su zauna a

matsayinsu. Ni bana dukan yarana

tunda ubansu ma a haka na

tarbiyantar da abina.

Duk wanda ya ce ba zai yi hakuri

da su a haka har kafin su fahimci kan

al'amarin duniya ba, to sai yasan

nayi.

Ba na so, kada kuma na sake jin

don sun je wurinki sai kiyi mata haka

har tana sulewa saboda razana? Ai

nan gidan ubanta ne tana da ikon

shiga duk inda take so ta wala."

Na dawo dakina nayi alwala nayi

sallar magriba har aka yi Isha'i ban

tashi daga wurin ba.

Don haka na mike nayi sallar Isha'i

tare da shafa'i da wutiri. Motsin

47

Ahmad naji a wurin shi ne na dauki

abincin shi na kai mishi.

Ina ajiyewa ya ce, "Me ya hada ki

da Zinatu ki ka yi mata irin wannan

dukan? Wato kin gane ko? Ni da ki ke

gani ina matukar tsoron tashin

hankali.

A waje ban huta ba, babu abin da

nake bukata irin na shigo gida dan

hutun da zan yi da iyalina na yishi

cikin kwanciyar hankali da farin ciki

ba.

Menene haka? Tun farko na gaya

miki kiyi kokarin zama ba tare da

wani abu ya hada ki da wani yaro ba,

saboda nima hakuri nake yi da su.

Hajiya kuma ina matukar kokarin

ganin bacin rai, bai same ta ba

ballantana a ce sanadina ne,"

48

Naga fadan nashi zai yi yawa

saboda wani abu bai taba hada ni da

shi makamancin haka ba, a tsawon

zaman da nayi a gidan na watanni

shida.

Na ce, Ban fa bugeta ba." Ya

watso mun ido "Ba ki bugeta ba? Na

ce "Na rantse maka ban bugeta ba."

"Me ki ke nufi kenan? Kina so ki

ce mun Mahaifiyata tayi miki karya?"

Nan da nan na fara kuka saboda jin

inda ya mayar da abin.

Nan take kuma fadan yafi na dah

wai na karyata mishi uwa. Ga gaskiya

nan kiri-kiri jikin yarinya ya rure har

zazzabi ya rufeta amma kina karyata

mahaifiyata.

Mara kunyar yarinya, tashi ki ba ni

wuri."

49

Na tashi na dawo dakina nayi kuka

har na gaji, idanuna suka yi luhu-luhu

saboda rashin barcin da ban yi ba.

Na gama abin karyawa kamar ba

zan shiga sashen nashi ba, tunda

korata ya yi jiya sai naga kada na

karawa kaina matsala.

Na dauka na kai mishi na ajiye na

juyo abina, tunda a da wannan damar

tayin gaba da wani ina dai bin doka

ne kawai. To da haka wanna ya wuce.

Ba karamin taka tsantsan nake yi

da yaran Ahmad da mahaifiyarshi ba,

saboda ina son aurena.

Gashi kuma cikin kankanin lokaci

sai na mallaki abubuwan kadara irin

Su,gold da zinari saboda yawan

tafiyar da yake yi.

Kuma shi mai sakin hannu ne.

matsalata a kullum ba daga shi ba ne

50

sannan babu fashi sai dai idan bai yi

tafiya ya dawo ba sai an ce nayi kaza

nayi kaza.

Ita kuma Hajiya ta ce aja mun

kunne, to garin aja kunnen sai ya

zama tashin hankali, ina batawa

mahaifiyarshi rai.

Sannan babu damar nayi musun

ban yi ba sai laifin nawa yayi yawa,

na karyata mahaifiyarshi, don haka

kullum a haka muke.

A daidai wannan lokacin ne ta

bayyana ina dauke da juna biyu har

na shiga wàta na uku.

Hakan ne ya matukar takura ni naa

kasa yin Azumin watan Ramadana,

saboda tsananin laulayin da nake yi.

Ba Ahmad ba ma har Hajiya a

wannan lokacin ta sassauta mun, don

51

haka babbar matsala a yanzu

laulayina ne da kuma yaran.

Tunda yanzu ba barina suka yi da

karata wurin Babansu duk da laulayin

da nake yi bai hana ni kiba na murje

ba.

Shirin sallah sosai ake yi don kuwa

gidan ma a cike yake da mutane 'yan

uwan su da suka zo daga kauye da

kuma babban dan Ahmad Zubair.

Wanda yanzu ne muka san juna da,

shi.

Shi kam babu laifi yana da hankali

don Aunty ma yake kirana. Haka nan

nima duk da sanin da nayi suna buda

baki a wurin Hajiya hada mishi nake

yi da Babanshi.

Sannan ganin shi yasa hatta Zainab

ta saurara da wasu abubuwan

ballantana su

2 / 6