Author : Hafsat C Sodangi Category : Romantic Hausa Novels
/>
ni. Ta ce, To a dawo lafiya. Muka
fito.
A wani babban shago ya tsaya ya yii
siyayya mai yawa, sannan muka wuce
gida.
Hira muke yi sosai da Umma shi
kuwa yana wurin Babana ba mu dawo
ba sai wajen karfe goma na dare.
Tashi nayi naga jini kadan-kadan
yana fitar mun, sai dai ban kula na
gani ba sai bayan da Ahmad ya tafi
kasuwa.
Bana son daga mishi hankali, don
haka nayi nufin bari sai ya dawo naayi
mishi bayani.
Nayi ta aikace-aikacena ba tare da
wani abu a raina ba, tunanina dai bai
wuce laulayi irin na ciki ba.
77
Sai da na gama ayyukana na shiga
bayan gida da nufin yin wanka, sai
kawai na ganni kace-kace cikin jini.
Sauri nayi na fito na dauki waya na
sanarwa Ahmad cewa ina son Zuwa
asibiti, ya ce lafiya? Na ce ch, ba na
dai jin dadi ne kawai, ya ce to Allah
ya sauwake.
Bala ya kai ni asibiti sai dai tun
kafin nan a takure nake cikin sauri
aka kai ni dakin Likita sai dai gwajin
farko ya tabbatar mana cikin ya
lalace, ya fita daga mahaifa dole a
cire.
Duk da halin da nake ciki a haka na
daure na kira Ahmad.
Cikin kankanin lokaci ya iso
asibitin, sai dai duk da saurin da ya yi
har an shigar da ni don wanke mun
mahaifa.
78
Duk da kokarin da nayi tayi na
hana kaina kuka kasa daurewa nayi da
Ahmad ya iso kaina.
Wannan karon ma bari nayi na ciki
wata hudu har da sati biyu, kamar dai
wancan kenan.
Kwana nayi a asibitin kowa kuma
yazo duba ni har daga gidanmu.
Likita ya shigo saboda sallama ta da
za a yi Ahmad yana yi mishi wasu
yan tambayoyi.
Ya ce, To dai a fayil dinta na ga ta
samu matsala makamanciyar wannan
shima a watanni hudu, don haka
tunda ga abinda ka fada zamu sake yi
mata scarming don mu gani ko da
matsala.
Likitan ya jawo wata 'yar takarda
yayi rubutu ya bamu. Ahmad ne da
kanshi ya kai ni wurin scarning din
79
muka dawo Likita ya duba ya ce, "To
a gaskiya ta samu matsala ne a
mahaifa saboda jijigar farat-daya da
mahaifarta tayi a wancan karon.
Saboda irin faduwar da tayi, hakan
ne yasa mahaifarta ba za ta iya rikke
wani ciki da zai yi fiye da watanni
hudu a mahaifarta ba.
Saboda bakin mahaifarta da ya riga
ya bude. Kuma shawarar da zan ba ku
a yanzu shi ne, kafin a san matakin da
za a dauka a kan matsalar, ta dan yi
hutu.
Don kuwa idan tayi wani cikin ma
a yanzu abinda zai faru kenan.
Dawowa gida muka yi jikinmu a
sanyaye, ni kam Ciwo ne ya rufe ni
jinya sosai Ahmad kwata-kwata ranar
bai fita kasuwa ba.
80
Bai kuma fadawa kowa abinda
Likita ya ce ba. Kwana biyu ko
abincin da zan ci daga wurin Hajiya
ake kawo mun.
Kullum kuma Ahmad zai ba ni
hakuri saboda lurar da yayi na dan
saka damuwa a raina.
Duk kokarin da nayi kada ya
fahimci wani abu kasawa nayi. Yau
ma yana zama zai fara mun magana
kuka na kama yi.
Sai da nayi ya ishe ni sannan na
share hawayena, babu abinda ke tsaya
mun a rai naji zuciyata ta baci irin na
tuna 'ya' yan Ahmad ne suka yi mun
wannan sanadin.
To tambayar ita ce, shin idan da ni
ce nayi wa wani a cikin su haka anya
zan zauna lafiya kuwa?
81
Amma gashi nan ni sun yi mun sun
zauna lafiya, sun ma mancc in ban da
shi Ahmad da yake ba ni hakuri.
Duk da warkewan da nayi a duk
lokacin da na tuna ina jin wani iri na
kuma kasa sakewa nayi harkokina
kamar da.
Ko shi Ahmad din ya lura ya gane
hakan, don yau ma muna zaune a
falonshi muna kallon labarai ya Juyo
yana kallona.
Hauwa'u magana nake so nayi
miki. Na lura duk tsawon lokacin nan
har yanzu ba ki saki jikinki ba.
Na kuma tambaycki shekaran iya
ko wani abu na damunki ne kin ce
a'a, lafiyarki kalau.
Ina so ki san wannan abun ba ke
kadai ya samu ba har da ni, amma
82
kuma kin takura ni na rasa walwalar
da a da nake farin cikin samu.
Idan ni ne nayi miki wani abu ki
gaya mun na gyara, idan kuma a kan
matsalar nan ne ina so kiyi hakuri.
Ina kokarin a wannan watan da zai
kama idan zan yi tafiya mu tafi tare
saboda wannan matsalar, sai ki ga
Likita a Dubai."
Ban ce mishi komai ba, amma nayi
kokari wajen ganin na rage takura ko
don saboda Ahmad.
Sai dai har karshen wata yazo ya
wuce Ahmad bai yi tafiyar ba, bai
kuma ce mun komai ba.
Muna kwance a dakinshi da
daddare a daren da ya dawo daga
Legos dauko wasu kayan shi da suka
shigo.
83
Nayi mishi maganar tafiyar da ya
ce zamu yi don ganin Likita. Ya ce,
"Kiyi hakuri Hauwa'u, ina nan ina
wasu shirye-shirye ne kawai."
Sai dai ba a wani jima ba ya shirya
ya tafi Dubai ya dawo ba tare da ya ce
mun komai ba.
Na shiga dakinshi na same shi
zaune ya baje takardu, lissafi yake yi.
Na zauna a gefe ina jiranshi ya gama
shiru bai gama ba har na gaji' na mike
na kwanta nayi barci.
Washegari tun da Asuba yayi shirin
shi gaba daya alamar daga wurin
Hajiya zai wuce.
Haka ina ji ina ganin babu yadda
zan yi ya fita. Da daddare kuwa da ya
dawo sai da na gama mishi komai
sannan na kwashe kwanukan.
84
Wai kafin naje na dawo nayi mishi
maganar da ke Cina a zuciyata nan ma
dawowa nayi na samu wai Hajiya ta
ira shi.
Zama nayi daram a kan kujera ina
jiran shigowarshi, bai shigo ba sai
wajen karfe goma da kwata.
Har yanzu ba ki yi bacci ba?" Na
ce, "Eh kai nake jira." Ya ce, "Akwai
magana kenan? Na ce, "Eh."
Ya gyara ya kwanta ya ce, "To ki
barta gobe kafin na fita kasuwa sai
muyi."
Na ce, Idan kuma a wurina tana da
muhimmanci fa? Ya ce, "Komai
muhimmancinta ki barta sai gobe, don
a yanzu na gaji."
Wani irin gululun bakin ciki ne ya
tokare mun makogorona. Da kyar
nake iya numfashi.
85
Tashi nayi na dawo dakina na hau
gadona na kwanta. Sai dai ban iya yin
barcin ba.
Ji nake yi kamar na koma na samu
Ahmad muyi duk wacce zamu yi da
shi daren nan amma ba zan iya ba.
Ko wani sauraron shi ban yi ba da
safe haka nan shi ma bai bukaci ya ji
maganar da nake son yi da shi ba.
Da dai ya gama shirinshi ne zai fita
ya leko dakin.
"Hauwa'u ina son burabusko da
miyar bindi". Na ce, To babu tsakin
shinkafa." Ya ce, "Ki karba a wurin
su Hajiya." Ya tafi.
Babu abinda na tsana yanzu a
rayuwata irin zuwa wajen su Hajiya.
Tun da dai gaisheta ya zama mun
dole, to kullum da safe ina zuwa
86
amma baya ga haka bana komawa sai
wata safiyar.
Sai da aka yi sallar Azahar sannan
na dauki roba na shiga wurin Hajiyan
na gaya mata ina son tsakin shinkafa.
Ta kalli Zainab ta ce, "Zainaba
tashi ki debowa Mamanku tsakin
shinkafa."
Ta dago ido ta kalle ni, sannan ta
ce, "Maman wasu dai Hajiya, ammna
ban da mu."
Ta ce, "To naji bana dai son rashin
kunya, karbi ki debo mata. Kin dai
kusa tafiya Makaranta a huta."
Ta ce, "Ai idan na ganc tafiyata zai
sa wasu murna ma sai na cc na fasa."
Ta dawo da tsakin a hannunta ta
dangwarar a kasa.
Ban tsaya sauråronta ba, dauka
nayi na yi tafiyata.
87
Zainab a yanzu ta rubuta
jarrabawarta na gama makaranta
sceondary, Jami'a ake neman mata
har ma an samu.
Dawowa wajena nayi na shiga
kokarin ganin na kammala cikin
lokaci, kuma nayi sa'a yayi kyau ya
yi dadi.
Ga kamshi ko ina a cikin gidan. Ina
gamawa na shiga bandaki nayi wanka
na fito kenan naj1 motsi a falona.
Don haka na fito falon bayan na
sanya zulumbun hijabina don ganin
ko waye.
Zainab ce rike da tircn abincin
Babansu, gabaki dayan shi zata fita.
Sa hannu nayi na rike na ce "Yau
kam a'a, abin ya ishe ni haka ba zai
yiwu ba.
88
A duk ranar da ki ka ga kina da
bukatar cin abincina to rinka gaya
mun sai na rinka saka sanwa da ke.
Ba haka kawai idan na gama girki
ki saka hannu ki sunkuci na mijina
kiyi gaba ki bar ni da dora sabo ba."
Ta zuba mun ido tana kallona, nimna
ita nake kallo, don na lura su gaba ki
dayansu ba su san zuru ba.
Kuma a gaban kowa sai Zainab ta
caccaba mun magana ba za a ce
komai ba.
Ba tun yau ba lokuta da dama sai
na gama abinci sai tazo ta sunkuta
gaba daya ta tafi da shi wurinsu ta ci
1ya cinta ta rabar da saura.
Wani lokacin ma ko rabi ba a ci sai
ta bar shi haka ya lalace, sannan ba za
ta dauko kwanukan ta dawo da shi ba
sai dai ni nabi bayan su.
89
Sau daya Hajiya bata taba yin
magana a kan hakan da take yi ba,
duk da tasan abincin danta Zainab
take dauka.
Kallon da take yi mun ne ya ishe ni
nayi nufin karbe tiren, sai kawai
yarinyar nan ta kabar da tiren gaba
daya abubuwan ciki suka watse.
Abincin ya zube a kasa, sannan tayi
murmushi ta raba ta gefena ta wuce.
Zubawa abincin da ya tarwatse din
ido nayi ba na ko kyaftawa.
Ban taba ganin danyen rashin
mutunci irin wannan ba.
Cikin dakina na koma na sanya
doguwar riga na futo zuwa wurin
Hajiya don na gaya mata abinda ke
faruwa.
Na shigo na zauna a kasa zan fara
magana sai ta ce "Dakata! Yau kuma
90
abin naki har ya kai ma ki hana
Zainaba abinci?
Ta dauko kuma kin biyo ta kin
kifar. Me ki ke nufi da abinda ki ka
yin?
Kin taba siyo abinci kin shigo da
shi gidan nan ne da ki ka samu damar
hana wani?"
Na ce, "Hajiya..". "Bana son jin
komai daga bakinki, nasha gaya miki
ba sau daya ba ba sau biyu ba cewa
duk abinda za ki yi a gidan nan to ya
tsaya tsakaninki da wasu amma kada
ki tsallako hurumina, don ba za ki ji
da dadi ba.
Ya ya za ki hanata cin abincin da
ubanta ya kawo ya ajiye takamar kina
matarshi?"
91
Tun ina daurewa bacin raina har
ban san sanda na fara zazzago
maganganu ba.
"Ai tun farko da nazo gidannan na
fara kawo abinci sashen nan aka ce na
daina don kuwa akwai mai girki.
Me yasa tunda haka ne idan tana
son abincina ba za ta fada mun tun da
wuri ba sai na girka da ita, sai ta bari
na gama tazo ta dauke gaba daya
haka ake yi?
Duk hakurin da nake yi da yarann
nan bai isa ba kullum kokarinsu bai
wuce na ganin sun kure ni ba.
Menene na yi musu?
Tunda na fara magana har na gama
Hajiya bata sake cewa komai ba, sai
kallona kawai da take yi.
Zuwa can ta ce, Lallai kin isa, ni
ki ke gayawa irin wadannan
92
maganganun? Dama ai biri ya yi
kama da mutumn.
Tun kwanakin baya na gane ya ba
ki isasshen damar da ta wadace ki. To
amma ba laifinki ba ne.
Tashi ki ba ni wuri, bari yazo ya
same ni mu san wacce muke ciki da
nida shi."
Mikewa nayi na dawo dakina na
kara tsallake abincin a wurin na shiga
uwar dakina na zauna.
Ni kaina na gane nayi kuskure
amsawa Hajiya da nayi, to amma ya
ya zan yi da raina?
Rashin 'yancin yayi yawa, ace wai
har a kan budurwar yarinya mai
shekara goma sha shidda kamar
Zainab za a zaunar da ni a titsiye ni
wai nayi laifi!
93
Kawai takamar ina auren ubanta
bayan da za a bi Silsilar abin za a iya
fahimtar ba ni ba ce mai laifin.
To amma saboda daurin gindi da
Son kai sai ya zama komai suka yi
daidai ne.
A madadin abubuwa su gyaru
kullum kara cabewa suke yi?
Kamar yadda ya saba dawowa haka
ya dawo yau ma. Ko inda yake ban je
ba ballantana na ba shi wani abu.
Don kuwa babu, na kuma san an
gaya mishi komai da ya faru.
Karfe tara har ta wuce ina zaune a
kan sallayata da nayi sallar Isha'i a
kai ban tashi ba.
Jiran kawai abinda zai biyo baya
nake yi. Bai shigo dakin ba sai wajen
karfe goma na dare.
94
Yadda nayi zaton zai shigo ba haka
ya shigo mun ba. Ya karewa abincin
da har yanzu yake shimfide a kasan
falon da food flask din da kuma
fasassun plates din kallo.
Ya sunkuya ya kwashe plates din
da kofunan da suka faffashe ya zubar
a abin zuba shara na nan kicin.
Sannan ya fito ya dawo da abin
kwashe shara da tsintsiya yasa ya
kwashe ya gyara wurin tsaf, sannan
ya wanke hannunshi ya zo ya zauna a
inda nake muna fuskantar juna.
"Ba kya jin maganata Hauwa'u, ko
nayi miki magana ba kya ji. me ya
hada ki da Zainab?"
Nan take na fahse da kuka saboda
karayar da nayi. Nayi kukana sai da
na gaji nayi shiru, sannan nayi mishi
bayanin komai.
95
Tun daga lokacin da Zainab ta tsiro
da abubuwanta har zuwa yau abinda
ya faru.
Ya yi shiru zuwa can ya ce, "Me
yasa ba ki taba gaya mun ba? Na
kalle shi.
"Na gaya maka fa ka ce? Idan na
gaya maka me za ka yi? Na taba gaya
maka wani abu da aka yi mun ka
dauki mataki?
Sannan ko karata aka kawo
wurinka ko ni ce da gaskiya ko ba ni
ba ce ba ka taba saurarona ka ji ta
bangarena ba.
Ni dai a kullum ni ce maras
gaskiya, 'ya'yanka kuma masu
gaskiya. A ina ne aka ce a yi haka don
daidaita zaman lafiya?
96
Ni kenan kullum ina da matsala da
'ya'yan miji, to menenhe aibuna? Me
nayi musu?"
"Za ki iya zama a Kano?"
Tambayar ta yi mun kwatsam! Na bar
kukan da nake yi a take na kalle shi.
"Ina da gida a Kano, idan kin yarda
za ki zauna a can sai na mayar da ke
can tunda ina shirye-shiryen bude
wata harkar a Kano kwanannan.
Ina son zama da ke Hauwa'u. Ni
kaina nasan ina da matsala a cikin
gidan nan. Kiyi hakuri a yanzu ko
meye Zainab zata yi miki ki daure ki
jure saboda ni da ke mu samu biyan
bukatarmu."
Hankalina ya dan kwanta, ya ce
"Ina neman alfarma idan ba zan
takura miki ba?"
97
Na ce, "Ta meye?" Ya ce, "Abinci
nake so ki samar mun wanda zan ci,
yunwa ta dame ni."
Tashi nayi a daren nayi wa Ahmad
dan girki mai sauri yaci sannan muka
kwanta.
Tun daga nan na samu sassaucin
damuwa, sai dai Hajiya ta daina amsa
gaisuwata, duk da haka kuma ban
daina zuwa gaisheta ba.
Zan zauna na kai mintina goma
bata saurare ni ba. Shi ma na lura
yana da 'yar matsala amma tunda dai
bai bude bakinshi ya fada mun ba sai
ban tambayar shi ba.
Na dai tsaya tsayin daka wajen
ganin bai kuntata da yawa ba, don
nasan matsalar ba ta wuce ta Hajiya
ba.
98
Ba a fi wata daya zuwa kwanaki
arba'in ba sai shirin Ahmad ya
kammala na bude babbar harkarshi ta
kasuwanci a Kano.
Har yaje ya yi sati daya a can don
ya tabbatar komai ya daidaita, sannan
ya dawo.
Muna kwance a dakinshi yana bani
labarin yadda abin yazo cikin
gagarumar nasara, ni kuma dokina sai
karuwa yake yi zai bar zama da su
Hajiya da 'yan fitinannun jikokinta,
zan koma Kano tare da mijina.
Ina ta ayyano irin tattalinshi da zaan
kara yi da irin abubuwan da zan yi na
ci gaba don kaina.
Don kuwa nima yanayin
kasuwancin Ahmad yana ba ni
sha'awa, har nima na kan yi tunanin a
99
matsayina na mace idan zan gwada
babu mamaki nayi nasara.
Na ce, Kaga idan muka koma ni ma
sai na gwada kasuwancin mata na
cikin gida.
Kallona ya yi cikin mamaki.
"Kasuwanci kuma Hauwa'u?
Na ce, "Eh mana, na zannuwa da
gwala-gwalai irin naku ba."
Shiru yayi yana kallona, ya ce
"Ashe kina sha'awar kasuwanci?"
Na ce, "Eh, zama da kai ne yasa
hakan, da can ba na yi."
Ya ce, To bari kayan da nayi oda
wannan watan su zo sai na diban miki
a ciki ki gwada muga irin taki nasarar.
Kin san mata da yawa suna karban
kaya a hannuna kuma suna samun
riba ba kadan ba.
100
Amma abin da na lura da shi shi ne,
sai wacce ta iya rikici saboda siyan
kayan gida yawanci bashi ne.
Ke kuma ban ga wannan a tare da
ke ba."
Ba mu yi bacci ba sai karfe daya
saboda 'yan hirarrakin da muke yi.
Washegari bai kintsa da wuri ba
saboda bakin da yayi abokan
kasuwancinsa.
Sai kusan sha daya na rana. Ya
shigo dakina rike da mukullin
motarshi yana ba ni sakon da zan bai
wa Bala direba idan yazo, saboda
haihuwar da matarshi tayi.
Sannan ya shiga wurin Hajiya.
Kwanciya nayi don na dan yi barci
kafin Azahar tayi. Sai dai ban ko yi
nisa ba naji sallamar Larai.
101
Daga cikin dakin na daga murya
ina tambayarta ko