TASWIRAR KADDARA BOOK COMPLETE PDF .txt

Author :  Mrs A.M Category :  Top Hausa Novels 2025

Chapter   2 / 32

3K to 6K   out of 94.4K words

sallama nai masa na shiga gidan, ba kowa a tsakar gidan hakan yasa na nufi palour don nasan suna zaune ynxu tunda an kawo wuta.


Da sallama na shiga palourn duk suka amsa min, Zama nai a gefen kafar baba ina cire hijab din jikina.


Kallona Umma tai tace "kin biya gurin cilla neh koh don nasan yadda kika dade din nan sai dai in kun hadu dashi"


Sosa keya ta nai nace "Umma a kofar gida muka hadu fa shine kawai muka gaisa"


Girgiza kai Umma tai tace "ni na rasa me yasa kike Kula wannan yaron wallahi sam baya ji tubarkalla"


Abba ne ya ce "A'a Umman Aysha ki bisa da addu'a kawai shima dana Allah ya shirye sa da dukkan zuri'ar musulmai baki daya"


"Ameen" muka hada baki gaba daya muka ce, mike wa nai ina fadin "sai da safe Baba gobe da school kuma ina son na fara shiga school din su Mimi"


Khalil ne yace "Ya Batul zan raka ki in zaki kaita"


Harara na sakar masa sannan na juya na nufi dakin mu nida Aysha, akan katifar mu 6 by 6 na ga Mimi tana sanye da rigar baccin ta kanta sanye da hula, murmushi nai na karasa gurin wardrobe dinmu, kayan bacci nasa na hauro kan katifar addu'a na fara ma Mimi kafin nima nayi, janyo ta jikina nai na rungume ta hawaye masu dumi suna zubo min a fuska tabbas a duniya Mimi ce rauni na ita nake kallo nake tuna *TASWIRAR KADDARAR* data same mu shekaru 5 baya.


Lumshe idona nai ina ina tuna abubuwan da suka faru shekarun baya lokacin ina da shekara 14 gashi ynxu ina 18 amma abun kamar ynxu ya faru......






**********


Kallon Haidar Azlan yai yana tabe jajayen lips dinsa yace "in baxa ka kaini club dinba sauke ni in karasa ai ina da kafa"


Girgiza kai Haidar yai yace "Azlan kayi ma kanka fada Kai ynxu ya dace ma ace kullum kana hanyar zuwa club gurin Yan mata"


Shafa gemun sa yai yadan lashi jajayen lips dinsa kafin yace ina ruwan Ka Mata ai abin nishadi neh kuma don naje AI ba budurcina zan basu baaaa.......
















Comments Nd share plz🥹








Mrs A.M🥰❤️


[04/08, 20:17] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️


*TASWIRAR KADDARA*


♠️♠️♠️♠️♠️




Written by
Mrs A.M🥰


Page 3


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM


Assalamu alaikum Fans ina muku albishir din mai da Book din Taswirar kaddara free Book, Allah y bar kauna🥰


Tsaki Haidar yai yace wallahi gaba dayan Ka dan iska ne, ynxu kai sbd takadari ne baka da aiki sai maganar budurci daga anyi magana sai kace kana tattala budurcin Ka.


Dage gira daya Azlan yai kawai yana tsotsar lips dinsa hayaniyar ta ishe sa shiyasa kawai yaja bakinsa yana tsotsa, kallon sa Haidar yai ganin yana tsotsar lips dinsa hakan ya nuna masa cewa baxai sake magana ba kuma yan miskilan cin sun hawo knn, shima Jan bakin sa yai yai shiru ya maida hankalin sa kan titi.


Tafiya mai dan nisa sukai kafin Haidar yai parking motar juya wa yai ya kalli Azlan daya kwantar da kansa a jikin kujerar motar yana gyada kai a hankali, bai yi magana ba sai bude motar yai kawai ya sauka ya tafi don tarar Keke napeo ya mai da shi gida.


Sai da Haidar ya fita tukun ya bude idonsa a hankali yana lasar lips dinsa, fitowa yai ya shiga gurin driver sit yana tabe baki, a guje ya fisgi motar yana sharara gudu a hanya ikon Allah ne kawai ya kaisa club din lafia.


Parking motar yai a cikin katon compound dn club din tun daga yanayin motocin dake fake a gurin zaka San cewa club din sai wane da wane ne suke zuwa gurin, cikin tafiyar sa ta jarumta ya nufi cikin club din dake tashin Kida kamar zai tsage ginin Amma su wadanda suke ciki ba abinda ya dame su harkokin su kawai suke.......






************
Da safe ina tashi bayan nai sallar asuba wanka na shiga nai ina fitowa Aisha ta shiga itama don da asuba dukan mu muke wanka, bayan na shafa mai doguwar riga na zira na fito kitchen gas na kunna na dora ruwan tea don hakan ya zamar mana al'ada kullum sai mun sha tea da safe.


Ina gama fada tea din na juye a flask doya na dafa mana fara na dauki ragowar miya dake fridge na dumama, sai da na gama duka na kai palour sannan na shiga daki don dauko Mimi nai mata wanka.


A zaune na same ta tana hamma sai murza idonta take alamun ynxu ta tashi, murmushi nai da ya fito da wushirya ta na karasa gurin ta zama nai akan katifar mu na janyo ta jikina, cikin kaunar ta da baya boyuwa a fuskata nace "Morning My baby"


Murmushi tai dimple dinta na gefen kumatun ta na dama yana lotsawa, kwantar da kanta tai a jikina tana fadin "Good Morning MAA dita"


Dariya nai na girgiza kai ganin in na tsaya biye mata zamu iya makara yasa na mike na cire mata kaya, towel dinta na sa Mata naja hannun ta zuwa toilet dinmu dake tsakar gida, wanka nai mata kafin na bata ruwa na sata tai alwala.


Daki muka shiga na shirya ta cikin uniform dinta Riga da wando light blue sai karamin hijab dinta dark blue, socks na sa mata muka fito Palour karya wa mukai muna yi muna hira har muka gama na sa mata takalmin ta, Nima daki na shiga na shirya cikin uniform dina ringa da wando sai hijab Wanda ya kusa zuwa min har gwiwa ta, jaka ta na rataya na dakko ma Mimi jakar ta itama.
Ina fitowa naga Abba da Umma a zaune suna Shan tea gefensu su Khalil ne a zaune Suma suna karyawa, gaishe su nai na janyo Mimi ina samata hijab dinta, kallon Abba nai nace "mun tafi Abba"


Murmushi yai cike da dattako yace "ynxu dai sai kin je makarantar su Mimi din"


Turo madaidaicin baki na nai gaba nace "Abba in ban je ba haka malamar nan tasu zata dinga ma Mimi maganar meye ma'anar sunan da take using gwanda naje nai reporting in ba haka ba tun Mimi bata damuwa har sai abin ya soma damun ta tunda ynxu tace har classmate dinta sun fara tambayar ta Suma"


Daga kai yai yace "kuma hakane amma bar ya ni sai naje na musu magana kinga kema student ce ba lallai su baki wani muhimmanci ba amma In suka ga babba yaje zasu fi saurara koh"


Murmushi nai ina sakin hannun Mimi nace "Haka ne Abba Allah ya kara arziki da wadata ya Kara muku lafia"


A tare suka amsa da Ameen, sunkuya wa nai nayi ma Mimi kiss a kumatun ta sannan na mike na fita don na kusa makara ma karfin hali ne irin nawa kawai yasa ni cewa sai na fara raka Mimi school din su don na fara gajiya da tambayar da Aunty dinsu take mata akan meye ma'anar sunan babanta sbd tana Amfani da Khadija B ne a school shine Auntyn su kusan kullum sai ta tambaye ta meye B din yake nufi, ni kuma inaso naje na yi reporting wa headmaster dinsu tunda ai ba dole ne sai ta san ma'anar B dinba...


Ban dawo ba sai karfe 4:30 na yamma a gajiye na shigo gidan jakata a hannu na saukin tama daga yau na daina zuwa makarantar mun gama lesson ranar Monday zamu fara waec, a tsakar gida na samu Umma da Aysha suna hira sai Mimi dake zaune a cinyar Umma suna hira.


A gajiye na zauna a gefen tabarmar ina gaida Umma, a dakile ta amsa ni tana kauda kanta gefe, hannu nasa na tallafo kumatuna ina kallon ta kafin na kalli Aisha dake dariya tana kauda kanta.


Marairaice fuska nai nace "Ummana me kuma nayi ko Aisha ce ta hada min bom a gurin ki don taga bana nn"


Dariya Aisha tai tace "ba ruwana wallahi Ya Batul dazu ne aka aikowa Umma wai Manniru ba Shi da lafia machine ya kade sa ya samu targade a hannu shine fa Umma tace tasan aikin cilla ne kuma ke kikasa Shi yai ma Manniru targade tunda an hana kisa a karya sa"


Zaro madaidaitan idona nai nace "Umma ni kuma ina ruwana da wani Manniru ai kince kar nasa a karya sa kuma Umma ai Shi Mannirun bai ce cilla bane naji Aisha tace machine ne ya kade sa"


Kallona Umma tai kafin ta girgiza kai tace "Allah ya shirye ki in kin huta sai ki leka ki duba sa don dama Yakumbo tana min mitar ynxu kin dena leka ta"


Dariya nai nace "Ameen Ummana anjima sai na leka din Insha Allah"


Janyo Mimi jikina nai ina fadin "babyn wace wannan" dariya ta kalkale da shi da suka fito da jerarrun hakoran ta tace "babyn Maa ceh"


Murmushi nai ina jan kumatun ta daga kanta nai daga cinyata na mike don zuwa watsa ruwa gashi yunwa nake ji sosai, bayan nai wanka na chanja kaya dama nayi sallah a makaranta, kitchen na shiga na zubo shinkafa da wake nasa salad akai, Kan tabarma na zauna ina ci muna hira da su Umma har na gama, wanko hannuna nai na shiga daki nasa Hijab dina har kasa, hula na Sawa Mimi na shiga palour na dakko wa Yakumbo robar zobo guda daya da robar kunun ayar da nake na siyarwa, don Alhamdulillah ina Sana'a ta daidai gwargwado ina siyar da zobo da kunun Aya Allah yamin baiwar iya hada zobo da kunun Aya sosai shiyasa nake na siyar wa kuma Allah yasa ma abin albarka ana siya sosai wasu ina zubawa a roba wasu ina kullawa a leda har fridge Dan karami ne dani Wanda Abba ya siya min nake sa kayan zobo na a ciki, ga kuma cake ina yi shima don na iya sarrafa flour.


Fitowa nai hannuna rike da ledar dana Sama Yakumbo zobo, hannun Mimi na rike mukai ma Umma sallama muka fita daga gidan, cikin nutsuwa muke tafiya muna hira da Mimi tana ban labarin school dinsu har muka karasa Babban gida, ba nisa tsakanin mu da gidan a farkon layin mu gidan yake.


Muna Kiran sa babban gida ne sbd family house ne anan Yan uwan Abban mu suke zaune da matansu, muma da a bangaren da Yakumbo take ynxu anan muke da Zama da lokacin da nake da shekara goma Abba ya bar gida sbd sam Umma bata Jin dadin zama a gidan sbd Uwani matar Kawu Nasiru da kuma Hama matar Kawu Kabiru, su uku yakumbo ta haifa Kawu Nasiru ne babba sai Abba sai Kawu Kabiru.


Da sallama na shiga dogon soron gidan ina hade fuskata direct bangaren Kawu Nasiru na nufa hannu na rike da na Mimi, sallama na karayi a kofar bangaren nasu da ba kofa, shiga nai a tsakar gida na gansu zaune a kan tabarma Manniru yana kwance daga shi sai dogon wando, hannayen sa an dora akan pillow, a tsaye na tsaya ina kallon uwani dake bina da wani mugun kallo, Nima kallon da take min shi nake mata kafin na dauke kaina a kanta na maida kan Manniru da yai kalar tausayi, karkace kaina nai nace "ya jikin naka ashe hatsari Ka samu ALLAH ya kiyaye gaba"


Cikin rawar murya yace "Ameen Ya Batul" kallon Mimi yai yace "Mimi ba magana"


Murguda karamin bakin ta tai tana fari da ido tace "ai dukana kake yi wani lokacin shiyasa baxan ma sannu ba"


Karya wuya yai yace "baxan sake ko hararar ki ba Mimi ai ni ynxu kin zama kanwata ko Baki so na dinga siya miki alawar madara"


Washe kananun hakoran ta tai zatai magana na katse ta gurin fadin "Allah ya kiyaye gaba Uwani" daga haka naja hannun ta muka fita daga sassan zuwa sassan Yakumbo.


A Palourn ta muka same ta tana zaune a kasa ta mike kafafun ta da dukkan alamu iska take sha duba da rigar dake jikinta, anan muka shantake da hira don jinin mu yazo daya sosai da yakumbo duk cikin jikokin ta munfi dasawa da ita muyi fada muyi dadi haka muke lokacin da muke babban gida yawanci a dakin ta nake kwana ma sai da muka bar gidan sannan na rage zuwa gunta sbd Umma bata son muna yawan fita...






***********


Kallon Abie yai kafin ya lashi jajayen lips dinsa yace "A gidan su Haidar na kwana"


Cikin bacin rai Abie yace "ban hanaka amma kwana a waje ba na fada ma ba so daya ba ba so biyu ba duk daren da kai Ka tabbatar Ka dawo gida Ka kwana a gida"


Karkatar da kansa yai yace "Amma abie Shi Junaidu ai a waje yake kwana daki daya da mace ma watakila ma a kirjin sa take kwana me yasa shi baxa kace masa ya dawo gida ya kwana ba"


Sunkuyar da kai Junaid yai cikin tsananin kunya baisan yaushe Azlan zai nutsu ya daina iskanci ba.


Girgiza kai Abie yai duk da shima maganar Azlan din tasa shi jin kunya amma kuma ya saba da yanayin maganar sa haka yake bashi da kunya.


Girgiza kai Abie ya kuma yi yace "Ka fara mantawa cewa Shi Junaid yana da aure koh Kai kuma gwauro ne dole zai kwana a gidan matar sa kai kuma tunda baka da matar ai sai Ka kwana a gidan ubanka koh".


Dage gira yai kafin yace"nima aure xanyi na dinga kwanciya akan kirjin matata kawai" ya fada yana lumshe idonsa.


Mikewa Mami tai kawai ta shige dakin ta tana girgiza kai lokaci daya tana murmushi.


Kallon Junaid Abie yai yace duba min yaron nn ko ya sha wani Abu kafin ya shigo gidan nan.....
















Comments Nd share plz










Mrs A.M🥰
[06/08, 18:23] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️


*TASWIRAR KADDARA*


♠️♠️♠️♠️♠️




Written by
Mrs A.M🥰


Page 4


BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM




Kallon Junaid Azlan yai ya saki wani killer smile sannan ya juya kansa gefe yana shafa gemun sa, girgiza kai Abie yai kawai kafin yace "wallahi Azlan kar ka kara kwana a waje in ba haka ba sai na Saba maka wallahi"


Lumshe idonsa yai kafin ya bude su a kan Abie din, cikin kasa kasa da murya yace "insha Allah" daga haka Abie ya mike ya bar palourn.


Kallon sa Junaid yai yace "me yasa baka Jin magana ne wai Azlan kai kafison kullum Ka dinga batawa Abie da Mami rai koh, ynxu sbd tsabar rashin kunya a gaban su kake cewa mace na kwanciya akan kirjina.."


Zakudowa Azlan yai daga kan kujerar da yake ya kalli Junaid yana kankance idonsa daya sha kwalli rambadadau don shi baya ware idonsa gaba daya shiyasa ake masa kallon rikakken dan iska, tsuke karamin bakin sa yai kafin yace "ai gani nai ba karya nai ba koh abinda kuke yi knn masu auren kullum matan ku suna kirjin ku shiyasa naga nima zan maida hankali nayi auren nan ko naji abinda kuke ji"


Girgiza kai Junaid yai yana kallon Azlan kawai don shikam dama tuni Azlan yafi karfin sa, mikewa Azlan yai yana gyara wandon sa daya sassako sannan ya kalli Junaid yace "Ka gaida Mai dakin Ka ni zan wuce gurin tsoho"


Da ido Junaid ya bisa har ya fita kafin shima ya mike ya nufi part din Mami don yana son magana da ita akan tafiyar da yake son yi India akan matsalar rashin haihuwar sa...




********

Ban koma gida ba sai bayan Isha'i don Saida na gyara wa Yakumbo bangaren ta tsaf duk da ba wani datti kasancewar Yakumbo macece mai tsafta, bayan mun koma gida ban samu Umma a Palour ba nasan maybe tana daki hakan yasa nima na kwantar da Mimi da tai bacci a daki, addua nai mata sannan na fita zuwa kitchen don dora zobo na so nake nayi shi tun da daddare nasa a fridge kafin safe yayi sanyi.


Nida Aisha ne muka shiga kitchen din muna hada zobon muna hira tana bani labarin school dinsu fadan da akai yau akan wani saurayi, girgiza kai kawai nai cikin takaici ina mamakin yadda mata suke zubar da ajinsu da kimar su ta diya mace suna fada akan namiji, tabe baki nai takaici kamar zai kashe ni don haushi cikin saurin magana ta nace "ke ni ki daina bani labarin nan haba bakomai a ciki sai kayan takaici"


Dariya tai tace "dama nasan haka zaki ce ai Ya Batul don ba a gaban ki sukai damben bane ba wallahi nasan da sai kin kusa kuka kinga yadda suka yagawa juna hijab kuwa, kuma abin takaicin Wanda suke damben akansa yana zaune yana kallonsu amma ko uhm bai ce ba daga karshe ma mikewa yai ya tafi ya barsu agun irin su kashe junan nan nasu ma"


Cije lips dina na kasa nai cikin takaici nace "taya suke tunanin ma zai ga darajar su ita mace ai MAI DARAJA ce ynxu alal misali ko da ace a cikin su yana son wata wannan zubar da mutuncin da sukai a bainar jama'a ai dole ma yaji baya ra'ayin su"


Gyada kai Aisha tai tace "kuma a haka fah wai su basu yadda ba sun burge sbd sunyi fada akan abinda suke so sai hura hanci suke nidai banga karshen yadda aka kare ba na taho kar Umma tai min fada tace na dade Amma wallahi Ya Batul Allah Allah nake gobe tayi naje naji yadda ake kare"


Tabe baki nai nace "anan kika fi kauri ai son Jin gulma da munafurci"


Turo baki tai tace "ynxu ya batul nice nake da son gulmar"


Kallon ta nai nace "toh in bason gulma ba ina ruwan ki da son sanin yadda fadan ya kare"


Gyada kai tai tace "Hmm Ya Batul knn"


Kamal ne ya shigo hannun sa rike da leda yar madaidaiciya, kallona yai yace "Ya Batul yau tun da muka dawo daga school ban ganki ba ina ta tambayar Umma tace kina kin je babban gida"


Zobon dana kulla a a leda na ajiye nace ina can naje duba Manniru sai kuma na tsaya gurin yakumbo daka sani ai daka shigo gurin nata tana ta min mitar baka zuwa wai khalil ne kullum sai yaje amma banda Kai"


Dariya yai yace "rikicin tsufa ne kawai yake damunta Allah amma ko ranar Monday fa sai da naje na gaishe ta nine ma na kai mata abincin da Umma ta bayar a kaimata"


Miko min ledar yai yace "gashi inji Mansur Mai shago wai cake din ya kare nan kudin cinikin

2 / 32