Author : Jeeddah jao Category : A Books
Jauda suna tsaye sun zuba musu ido ,d’ayar tace ” ke!! Benaxir fa ta dawo !!! Kika shigo da Wannan bakya tunanin zata iya 6ata miki rai in ta ganta ko??!” Murmushi Jauda tayi sannan tace ” babu komai Aisha ai zamu fita ta baya in Mun gama aiki !!” Aisha de bata sake tanka mata ba ,Jaseena tace ” Wacece Benaxir har kuke tsoron ta haka ? D’ayar da tun farko bata tanka mata ba tace ” Wannan bai shafe ki ba !!:roll:” a tare Jauda da Aisha suka daka mata tsawa gami da k’iran sunan ta Meenah!!! Wai ke me yasa bakya son mutane ne kin cika bak’in hali !!? ” Aisha ce ta k’arasa maganar……
Jaseena tayi murmushi tace ” ni zan koma ,nagode da kyautata wa da kuka yi min ” Aisha tace don Allah ki tsaya mana yanzu zamu gama aiki mu tafi fada ,yau akwai tseren doki a fada kuma Kowa zai halarci gurin domin fidda gwani a wajen sarrafa doki ,kuma fa har akwai fad’a da zaki ,kowacce shekara yarima Haidar ke gaba a duk fannin.!! Kinsan yarima Haidar da son mutane ! Ai shine ma sadaukin Wannan masarauta Kowa yana karrama shi ,ba kamar mahaifin shi sarki Hasheem ba ,bai d’auke shi a kan komai ba ,Kinsan Haidar abokin mu ne tun muna k’anana tare muka taso har yanzun nan da kika gani ,ko lokacin da muka miki dariya a hanya ma ai shi ya hana mu in ba haka ba da abun ya fi haka ,ko wacce a cikin mu na da labari mai ban tausayi tun yarintar mu kuma labari mai ban tausayi amma da Sannu zaki san komai amma kafin nan ko zaki iya bamu labarin rayuwar ki da yadda akayi kika tsinci kanki cikin Wannan masarauta ta Ramali?? ”
Nan Jaseena ta kwashe duk labarin rayuwar ta ta fad’a musu har yadda akayi ta fito daga dutsen da had’uwar ta da shi Haidar ,duk sun tausaya mata matuk’a , Jauda ta mik’e tsaye tace ” toh ai duk labarin d’aya ne duk fa akan mulki aka k’ask’anta mu kawai don an fi k’arfin magabatan mu toh yanzu zama zamuyi a dinga cin kashi a kan mu ne??!! Aisha ta mik’e tace ” inaaaa!! A’a Sam bazai yiwu ba dole mu kwace hak’k’kin mu da kan mu mu tashi muyi yak’i mu k’watar ma kammu y’anci!!! ” Jauda ta sa hannu tace ” wa yake tare da ni??” Duk suka d’aura hannayen su a kan nata gami da cewa “ni!!” Duk suka maida dubansu ga Meenah da ko motsawa bata yi ba ,ganin duk sun sa mata ido itama ta d’aura nata hannun” Jaseena ta rasa Wannan wane irin hali ne Meenah take da shi kwata kwata batada fara’a a fuskar ta. A tare suka watsa hannayen sama kowannen su yana murmushi irin na masu k’arfi a jika 💪🏼
💞🏵 Jaseena. 🏵💞
Guri ne babba na gaske amma mutane duk sun cika gurin an zagaye makeken filin wanda Hasken farin wata ya cika shi fal! Gurin da mutanen suke hawa hawa ne ga fitilu nan ta ko ina sun haska benen dake sama sosai shine inda sarki Hasheem ke zaune shi da wata Kyakkyawar mata tasha ado na zinare ,gefe d’aya kuma sarakuna ne da matan su wayanda suka zo suma da y’an wasan su ma’ana sadaukai na k’asar su don suma su fafata a cikin gasar ,akwai gefen sarki Hasheem wanda duk cikin guraren ya fi ko ina k’ayatuwa ,wani sarki ne bashi da haske sosai amma da ka ganshi kasan ya dama ya shanye a sarauta ,gefen shi wani kyakkyawan saurayi ne ya sha ado gwanin sha’awa fuskar shi babu almuru ga dukkan alamu d’an sarkin ne ,ga kuma wani ta bayansu a tsaye da alama sarkin yak’in su ne don sanye yake cikin kayan yak’i saidai ya manyanta sosai don dattijo ne….
Toh masu ku biyo ni a episode na gaba don jin wainar da zata toyu a Wannan fili na gasa ,ina godiya masu karatu love you all!!💞
🏵Jeeddah ja’o🏵
[3/23, 9:15 AM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016
🐚🏵jeeddah ja’o🏵🐚
4⃣6⃣⏭5⃣0⃣
Haidar ne a kan doki suna Jere shi da wasu ,yayan sarakuna ,Jaseena da ke zaune a bene na farko kuma na k’asa ita da su Jauda kawai ta mik’e ba shiri ,su Aisha ma suka mike suna tambayar ta ko meyasa ta zabura haka? Fuskar ta babu almuru tace ” tabbas na san wancan !! Shine Rizwan d’an sarki Jalalud-deen !!! Me kuma yake yi anan ? Duk yadda akayi sarki Jalalud-deen ma yana nan !!” Aisha tace ” kice ba mu muka je neman su ba su da kansu sun kawo ‘kafar su inda ya dace!!” Duk suka bushe da dariya ,chan kuma sai Jaseena tace ” toh amma ai in an gama gasar yau gobe zasu tafi ko ?” A tsare Meenah tace ” sati biyu ake yi ana wasannin lallai muna da dama ” duk suka jinjina kai ,yayin da Jaseena tayi murmushi cikin ranta tace ” lallai Wannan Meenah d’in y’ar ganin dama ne !!.
Tun da aka fara tseren dawakai Haidar ne ke Jan ragamar Kwatsam sai dokin shi tayi wani irin ‘kara ta tik’a shi da k’asa ta yi gaba ,yarima Rizwan wa wuce shi yana masa wata muguwar dariya gami da cewa “Wannan karon kam baka isa ba!!! ” dokin Haidar da ya fita a guje ya zagayo ta inda su Jaseena ke zaune kawai se ta mik’e tayi tsalle ta fad’a kan dokin ” Hyaaaa!!! ” ta sa gudu ,ganin yadda ta kusa cimma Rizwan yasa sarki Jalalud-deen ya mik’e tsaye yana zare idanuwa.
Gudu suke daf da daf da ita yayinda Rizwan ya kasa mai da hankalin shi kan tseren ,abunka da mayen mata ,ya tsura mata ido ita kuwa ta sakar masa da wata hadaddiyar murmushi wanda ya sa sai da ya kusa tsaya wa. Sai da ta tabbatar ya gama rud’ewa kawai taja linzamin dokin ta kara gudu har ta tsallake Jan layin da aka zana ,ta zo na d’aya ,bak’in ciki ya sa Rizwan ya gagara k’arasawa yayin da idon Jalalud-deen suka rine tsabar haushi ace duk shirin da suka yi na ganin sun ci amma hakan bai yiwu ba?
Mutanen gari aka hau ihu ana Jaseena! Jaseena !! Jaseena!!! ,Wannan sunan da aka kira yasa sarki Jalalud-deen d’agowa cikin sauri yana kallon Jaseena !tabbas babu maraba tsakanin ta da mahaifiyar ta ,saidai a tunanin shi wata’kila idon shi ne ke mishi gizo sai yayi tsaki ya juya ya bar wajen ,yayinda Rizwan da sarkin yak’i Amjad suke taka mishi baya.
🏵Jeeddah ja’o🏵
[3/24, 7:40 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔
🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚
5⃣1⃣⏭5⃣5⃣
Haidar kuwa murmushi kawai yayi ya nufo inda take ,kanshi a k’asa yace ” nagode jarumar mata!!! ” Wannan sanyin Muryar tashi ta sa Jaseena lumshe idanuwa tana murmushi ba tare da ta tanka masa ba,shi ma yadda yayi maganar ba wanda zai gane magana yake yi ..
🐚. Gurin duk an watse Kowa ya koma gida, daga Aisha ,Jauda, Jaseena sai Meenah da Haidar, suna ta hirar su cikin nishad’i Meenah ce kad’ai kamar bata gurin. Jauda tace “Jaseena mu zamu tafi dare na yi sosai Kar Benaxir ta rufe k’ofa Kinsan ba mutunci gareta ba! Nan suka yi sallama suka bar ta da Haidar. Ganin sun share mintina babu wanda ya tanka wa wani yasa Jaseena ta mik’e tana kad’e rigar ta tace ” sai da safe yarima ,idon shi cikin nata yayi mata wani murmushi ba tare da ya tanka ba ,ganin shiru yasa ta juya zata tafi…….
Mahaifina sarki Mahmoud shine mai mulkin Wannan masarautar mutum ne wanda bai yadda ya ci ya sha ba tare da ya tabbatar jama’ar k’asar nan sun wadatu ba kullum burin shi yaga na gefen shi cikin walwala koda shi zai rasa ,hakan ne yasa ya fita daban da sauran yan uwan shi wanda kuma sun kasance ba uwa d’aya suke ba domin shi d’aya mahaifiyar shi ta Haifa kuma halin shi ma babu mai irin sa kasantuwar ,kakan mu mata biyu gareshi…..
Da sauri Jaseena ta juyo ta dawo inda yake ta nemi guri ta zauna don ta jiye wa kunnen ta ……. Yerima Haidar yaci gaba da cewa ” duk mahaifina ne babba a ciki domin mahaifiyar sa itace ta fari daga baya ne zaliha (ta biyun ) ta haifi maza biyu Hasheem ,Hayatud-deen ,da kuma mace d’aya Saleemah. Duk cikin su ukun Saleemah kad’ai ke son baba na don sun shaqu sosai hakan ne yasa tun tana y’ar shekara goma ,mahaifiyar ta Zaliha ta bada ita aure a wani masarauta Wai shi Kalahari aka daura mata aure da d’an sarkin garin yarima Jalalud-deen , wanda hakan yasa bata ‘kara zuwa ko da ziyara nan masarautar ba,Domin shine hud’ubar da mahaifiyar tata tayi mata.
Jin haka yasa Jaseena ta mik’e a razane ta ce ” Kalahari?? Jalalud-deen?!! ” shima Haidar ya mik’e yace “eh! Kin san su ne? Nan ta kwashe labarin rayuwar ta ta fada masa yayinda ya cika da mamaki ” haka Allah yake abin shi!! Shine abunda Haidar ya iya cewa kenan ,ya dubi Jaseena yace “Kin ga yanzu dare yayi ,ki je ki kwanta ki huta gobe in shaa Allah zan sanar da ke dukkan labari na. A nan suka rabu da alkawarin zai sanar da Jaseena komai game da shi washegari……………..
🏵Jeeddah ja’o🏵
[3/25, 12:20 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔
🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚
5⃣6⃣⏭6⃣0⃣
Tafiya take tana ta fama da y’ar doguwar rigar ta ,tazo wucewa ta gurin fada kenan taji kamar maganar mutane,ta d’an lek’a daya daga cikin tagogin fadar don taga su waye a fadar cikin Wannan dare. Tana lek’a wa idanuwan ta suka yi karo da sarki Jalalud-deen da kuma sarki Hasheem suna tsaye ,koda ta kasa kunne don tajiye wa kunnen ta abunda suke shiryawa……
” Ai Wannan ba komai bane ni a gurina domin a kan sarauta babu abunda bazan aikata ba !!! Ko yarima Haidar da ka gani ban barshi a Wannan masarautar ba saida na tabbatar cewa yana da nak’asa sannan kuma ban daukeshi a kan karon komai ba !!! Duk da ma de Y’ata Meenah bata k’auna ta Sam !! Amma Wannan karagar mulkin da ita ya dace ba Haidar ba!!!” Sarki Hasheem ne yayi Wannan maganar hannunshi rik’e da kofin zinare. Sarki Jalalud-deen ya mik’e yayi wata y’ar muguwar dariya yace ” lallai abokina baka da wayo !! Ai sai da wuta ake shan Zuma!!!domin dan hakin da ka raina shi zai tsone maka ido ,yaran yanzu da ka gani ,zamani ya chanja domin babu wata dabara da basu sani ba ,bar ganin shi da nakasa ,kaga fa yadda ya mamaye zukatan al’umma ! Abun yi kawai shi ne ka kawar da shi kwata kwata domin in baya nan tare da kai babu yadda za’ayi Meenah ta ‘ki kar6ar mulkin Ramali ,ka duba fa ka gani ,mace ce mai kwarjini ga jarumta bai kamaceta bama a ce Wai ta bar daular dake cikin wannan masarautar! Ni ina da shawara ,me zai hana a had’a su aure da d’an wajena Rizwan? Kaga zasu yi mulkin Ramali cikin kwanciyar hankali ,kasan ko d’ana Rizwan bashi da masaniya akan abubuwan da nayita tufkawa a masarautar Kalahari , don na lura yan da son gaskiya shi yasa na ci gaba da 6ata shi da sakalci don in har ya gano ni ba mai gaskiya bane ,Rizwan zai iya juya min baya kasan duk da ba Saleemah bace ta haife shi amma goyon ta ne shi yasa nayi duk yadda zan yi su daina ganawa da juna kullum!!” Duk suka bushe da dariya Hasheem yace ” baka da dama abokina!! Shikenan! Na amince da shawarar ka!! …..
Jaseena ta toshe baki da hannayen ta ,ganin fitowa zasuyi yasa ta ruga a guje ,bata ankara ba taji an fizgo hannun ta cikin wani d’aki an rufe k’ofar ,zata yi magana yasa hannu ya toshe bakin ta yace , “ki nutsu” tana juyawa tayi ido hud’u da Rizwan:oops: tace ” kai!!! Sake min hannu na !!! ” ta fisge hannunta daga rik’on da yayi mata ,ta bud’e baki zata ‘kara wata maganar ya ce ” naji duk abubuwan da suke shiryawa !! Kamar yadda kema kika ji su ‘ da na zaci ni ne asalin wanda ya cancanci sarautar k’asar Kalahari ashe ba sarauta ta bace ta wani ne ! Duk rashin mutunci da cin amanar da nake wa mutane ashe de duk a banza ne , duk kuri da gadara da mulki ashe ba ta mahaifina bane !!! Kaicho na wlhy nayi nadamar samun irin wannan uban ,wanda kawai son zuciya ya saka a gaba ,kuma yanzu na tabbatar ba sona yake ba don yana turanine cikin halaka !! Wani hawaye ne ya biyo kumatun Jaseena tace ” hakane yaya Rizwan amma ai babu komai akwai Allah!! Tana kai wannan ta fice tana goge hawaye ,tabar Rizwan yana tunanin dalilin k’iran shi da tayi da yaya Rizwan ; cikin ranshi kuwa sai tambayar kan shi yake ,dama akwai ranar da zata zo har zai zubar da kwalla da kuma jin tsananin tsanar mahaifin shi?
Da sassafe Jaseena ta shirya cikin irin shigar da ta saba ,ta fice don gari ko gama wayewa bai yi ba ,bata zame ko ina ba sai inda sukayi alk’awari zasu na had’uwa ita da Haidar ,amma abun da ya d’aure mata kai shine tun da taje tana masa magana ko kallon inda take bai yi ba ballantana ya amsa mata ,da gani kasan ranshi a 6ace ne. A fusace ya tashi zai bar gurin ta sha gabanshi da gudu tace ” Wai ni laifin me nai maka ne!?tun d’azu ina maka magana ka min shiru kamar da gunki nake magana alhali na tabbata kana ji na “! Bai saurareta ba ya bi ta gefenta zai wuce ta sake tare shi ,cikin tsawa yace ME KIKE YI JIYA A DAKIN RIZWAN!!! ” shiru tayi tana kallon shi ido da ido ta ce ” me kake nufi Haidar ? Me kuma zanyi a d’akin Rizwan ,chan ta juyo tace ,yaya Haidar !! Yaushe muka fara haka da kai? Me yasa bazaka fad’a min ba? Me yasa kake boye min ? ” Haidar yayi sauri ya tari bakin ta yace ” Jaseena ban fahimce ki ba ” tayi murmushi wanda yasa hawayen da ke idanuwan ta suka zubo ba shiri tace ” ka kasa fadamin kana sona ko” ka kasa kuma bawa zuciyar ka hak’uri har ta fara zuga ka,ka fara zargin abin da kake k’auna kuma sannan ka kasa daurewa! ” Haidar ya juyo yana kallon cikin idonta” yayinda ta juya zata bar gurin. Haidar yace ” na soki Jaseena kuma har abada zan soki ” ya durk’usa k’asa yace ” kiyi hak’uri ya ke Kyakkyawa ! Ki taimaka min da zuciyar ki domin tawa ta riga ta kufce min ! Ban kuma san yaushe zata dawo gareni ba don ta fita farautar abunda tafi mata komai soyuwa ne!”
🏵 Jeeddah ja’o🏵
[3/25, 10:45 PM] Jeeddah ja’o🏵: ⚔🦃JASEENA🦃⚔ 2016
🐚🏵Jeeddah ja’o🏵🐚
6⃣1⃣⏭6⃣5⃣
Jaseena ta juyo idanuwan ta duk sun yi ja ,tace “Na baka !! Na baka ya Haidar!! Ka kula da ita domin taka ta riga ta iso inda zata tsaya da farautar kuma bani da tabbacin zata koma gareka !!” Haidar ya mik’e yace ” nagode kyakkyawa !! Jaseena tayi murmushi tace ” akwai maganar da nake son sanar da kai ne ” Haidar yace” ki fad’a mana ko ma menene. Ta kwashe duk abubuwan da ya faru a daren jiya ta sanar da shi har abunda yasa ta shiga d’akin Rizwan. Haidar ya sake bata hakuri ,sannan ta gyara zama ta ce ” baka k’arasa min labarin ka ba” ya d’an yi murmushi sannan ya ci gaba……..
🕸🐚🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸🐚🕸
A lokacin ina da shekaru goma sha shida ne ,k’ anin babana wato Hasheem ya bi rud’in uwarsa na cewa Kar ya kuskura ya bar babana da rai don in har ya tsufa a kan karagar mulki nine zan gaje shi na zama sarki , don shi a cewar shi ni ba komai bane in ya kawar da mahaifina, da duk wani mai ji dani, kasantuwar kullum da safe muna fita daji ni da kakana yana nuna min nau’in ganyayyaki da amfanin su ,hakan yasa ya shirya mana gadar zare.
Mun yi Nisan kiwo nida kaka har bayan la’asar sannan muka iso gida ,muna shiga wasu mutane a kan dawakai su kuma suna fita ,ga gari duk ya turnuk’e da hayak’i ko da muka k’arasa cikin fada nan muka tarar da gawawwakin iyayena da kuma na k’annen k’ anin Hasheem Hayatud-deen , Hasheem ya kwanta a kansu sai kukan munafurci yake yi kamar da gaske ,a nan ne zuciyar kakana ya buga take rai yayi halinsa , bayan kwana uku da faruwar hakan ,kawu Hasheem ya na’da kanshi a matsayin sarkin Ramali ,duk dattijawan da basuyi Na’am da hukuncin da ya yanke ba sai ya sa aka kwashe su aka kai su masarautar Kalahari aka rufe ana basu horo mai tsanani ,daga cikin wadannan dattijawan sun had’a da mahaifan Aisha da kuma Jauda ,kamar yadda na fad’a miki Meenah itace d’iyar kawu Hasheem amma tun tana y’ar shekaru tara ne abun ya faru don duk sa’anni suke da Aisha da Jauda kinga kuma k’awaye ne hakan yasa ta baro fada ta zab’i zaman bauta a gidan Benaxir har ta girma ta kawo lokacin nan da kike gani….
Ni kuwa tun lokacin da abun ya faru na daina magana da Kowa da na gano hakan kawu Hasheem ya ke so sai na nuna mishi ma kwata kwata bana magana na daina yi ko da da wasa ,a haka shi da mabiya bayansa suka zata na riga na zama miskini. Kin ji yadda rayuwa ta ta kasance kullum cikin k’ask’anci amma ko a jikina domin na san dole ne wata rana sai gaskiya tayi halinta!!” Amma tunda haka abun yake toh mu zamu fara wargaza mishi rayuwar sa” Jaseena ta goge d’an hawayen fuskar ta sannan tace ” lallai ka shiga k’uncin rayuwa Haidar !! A nan ne Jaseena ta kwashe labarin ta ta bashi ta kuma sanar da shi ko wanene sarki Jalalud-deen. Sun dad’e suna shan hirar su ,kafin nan suka nufi gidan Benaxir don yin