Author : Maimuna Tijjani Iyam Category : Romantic Hausa Novels
ɗau lokaci ba ta tanka mini har na faɗa tunanin na tsallake iyakata ta hanyar faɗa cikin abin da bai shafe ni ba kuma bai kasance hurumina ba. Har na cire rai da samun amsa daga gare ta sai kuma can na ji ta ce"Amatullah".
"Na'am". Na amsa da shi cikin nutsuwa da kulawa.
"Kin taɓa yin soyayya? Kin taɓa son wani irin son da kike ji tamkar ba za iya yin rayuwa ba tare da shi ba? Kin taɓa tsintar kanki cikin ƙangin so mai dabaibayi? Kin taɓa ɗaukar so da ƙauna kacukam kika ɗaura akan wani ɗa na miji? Kin taɓa yin soyayya mai zurfi da sarƙarƙiya?".
Sai da na sauƙe numfashi mai nauyi kana na sama zarafin cewa"Ranki ya daɗe duk abubuwan da kika lissafa babu ko guda ɗaya da ya taɓa faruwa da ni. Hasalima ban taɓa yin soyayya ba a cikin rayuwata".
"In dai abin da kika faɗa haka ne tabbas ba za ki taɓa fahimtar duk abin da zan bayyana miki ba, Amatullah so wani mungun abu ne. Wallahi ko maƙiyina ba na masa fatan Allah ya jarabce shi da makauniyar soyayya".
"Don ban taɓa yin soyayya ba ai ba hakan ne zai sa na kasa fahimtar halin da kike ciki ba, sai dai na Hajiya ni na san ban kai na ji damuwarki ba amma in sha Allah na yi miki alƙawarin zan taya ki da addu'ar Allah ya kawo miki mafita da sauƙin halin da kika tsinci kanki a ciki". Ina dasa a zancen nawan na tashi na tattare kwanunkan da su Ayan suka gama cin abincin na kai kicin na wanke su, duk da ina jin yunwar kuma ina buƙatar na saka wani abu a cikin cikina, amma na kasa cin abincin sa boda yadda na ga Hajiya tana zubar da hawaye. Duk da ban san takamammen abin da yake damuwanta tare da yi mata ƙaiƙayi a cikin ranta ba, amma na tabbatar da cewar abin azimun.
A lokacin yarinyatata duk macen da na gani tana rayuwa a cikin babban gida, tana saka suturar da take so sannan ta hau manyan mota. Gani nake yi tamkar a duniya dai kam ba da ta wani matsala kuma sun gama dace wa a cikin duniya sai dai a yi fatan dace wa a gobe ƙiyama. Ashe kallon kitse nake yi wa dogo, sai yanzu da hankali ya ratsa jikina ma fahimci ko wani Bawa da irin na shi damuwar kuma mai ɗaki shi ya san inda yake yi masa yoyo.
"Idan tunanin za ki tsaya zauna kina yi ai da kin ui zamanki a can gida ba zai kin zo nan ba". Muryar Altine shi ya dawo da ni cikin duniyar zahiri daga karatun wasiƙan jakin da nake yi, ban ɗaga ido na kalle ta ba balle na ce da ita wani abu na tashi na je na rufe abincin na wanke hannuna na fita.
Har yanzu Hajiya tana nan zaune inda na bar ta ba gusa ba wnda a iya tsawon kwanakin da na yi a cikin gidan. Na lura ba ta cika sama a falon ƙasan ba rai da rai yana sama indai ba wani abun ba ne ya sauƙo da ita ƙasa shi ma tana gama wa take kowa wa sama.
Har na yi gaba zan wuce sai na ji ta ƙira sunan na dawo da baya na zo na durƙusa a gabanta kaina a ƙasa ina sauraron zancen da take yi cikin amo mai rauni.
"Amatullah ki ba ni shawara na rasa da yadda zan ɓutowa wannan lamarin gabaɗaya kaina ya kule. Tunanina ya tsaya a waje guda cak".
"Ranki ya daɗe ai ban san abin da yake damunki ba balle har na yi tunanin shawaran da ya dace na ba ki".
Ta ɗan yi jim ta ce"haƙiƙa Allah ya jarabce ni da tsananin son mijina. Hasalima ni na fara ganinsa na ce ina sonsa har kuma Allah ya ƙaddara za mu yi aure su haifa Ayan da Aryan. Su biyu iyayensu suka haifa daga shi sai ƙaninsa Saifullah da muke zaune tare da shi a cikin gidan, ba su da wani dangin kusa illa junansu hakan ya sanya suke matuƙar ƙaunar juna. Mun yi aure da Saddam amma sai bayan auren na fahimci ya aure ni kawai sa boda ya sama wacce za ta taya sa sanya ido akan ƙaninsa kasancewar sa ba mazauni ba, tun da muka yi aure da shi bai taɓa yin sati guda cur a cikin gidan nan ba. Ya yi wuta shi ne ya zo ya yi kwana biyar ya koma daga nan kuma sai ya sanda ya ƙara waiwayo mana. Soyayyar Saddam ta rufe min ido ta hanyar ba na iya ganin aibunsa kuma ba na ganin laifinsa akan komai duk da kuwa ni ma kaina na san yana cutar da ni".
"Hajiya ba kya tunanin cewa kuma yanayin aikinsa ne yake hana sa samun lokacin da zai zo gida? Kin ga fa ya wadata ku da komai na buƙatar rayuwa bai bar ku da yunwa ba, bai bar ku da ƙishi ba haka nan bai bar ku cikin tsumma ba komai na buƙatar rayuwa yana yi muku".
Ta saki wani sakakken murmushi kafin ta ce"ba za ki fahimta ba. Duk waɗannan abubuwan da kika lissafa ba su ne jin daɗin rayuwar duniya mussamman a cikin gidan aure. Aure ba na mutum ɗaya ba ne na mutane biyu da ake buƙatar ko wani ɓangare ya ba da na shi gudumawar, ban yi dogon karatun addini ba amma iya sanin da nake da shi na san cewa ƙissan rayuwar Sayyada Khadijatu da Ma'aiki sallallahu Alaihi Wasallama, ita ta fara ganinsa ta ce tana sonsa sa boda ta yarda da shi kuma ta yi na'am da kyawawan halaye da ɗabi'unsa. Shin ni na yi laifi don na yi koyi da macen da tarihi ya tabbatar da cewar ta hidimtawa addini da ƙarfinta kuma da dukiyarta? Mene ne lafina don na gan sa na ce ina son sa shin addini ya haramta hakan ne da na cancanci wannan azabtarwan?".
Na yi shuru ina tunanin ta inda zan fara kafin can na soma cewa"ki miƙa lamurranki zuwa ga Allah don shi kaɗai ne zai kawo miki mafita da sauƙin halin da kika tsinci kanki a ciki. Duk duniya babu wanda zai iya yaye miki damuwarki sama da wanda ya ɗaura miki. Ki yi sallan dare ki kai goshinki ƙasa ki yi Allah kuka ki sanar da shi damuwa da matsalolinki, ki roƙe sa cike da yaƙinin cewar zai amsa miki kuma ya yi miki zaɓi mafi zama alkhairi a gare ki. Ki yi azumi ki yi sadaka sannan ki yawaita karatun alƙur'ani don yana samar da nutsuwa a zuciyar da babu ita, ya haifar da kwanciyar hankali da salama a ciki ruhin da babu ita sannan ya na wanke ƙwaƙwalwa ya kuma daidata tunani".
Ta sauƙe wani gauron ajiyar zuciyarta da har sai da na ji sautinsa kafin ta ce"na gode in sha Allah zan yi duk yadda kika ce. Na gode sosai da wannan shawaran".
Ina ɗago kaina idanuna suka sauƙa akan Altine da take ƙarisowa inda muke ta murtuƙe fuskarta marar annurin nan tamau, da hakan ya ba ni cikakken tabbacin ta saurara duk abin da muke zanta da Hajiya.
"Hajiya sannu da hutawa, daman na zo mu yi wata magana". Ta yi zancen yayin da take zauna wa kusa da ƙafafun Hajiyar.
"Ina jinki".
"Ki ɗan ba mu waje ko". Murmushi kawai na yi na tashi na ba su waje na koma cikin ɗakin Altine na zauna, ganin zaman ba zai kai ni ko'ina ba. Hakan ya sanya ni ɗaukar alƙur'anin da na gani ajiye dirowa na fara karantawa.
Ban yi nisa ina yi ba Altine ta shigo ta amshe ƙur'anin daga hannuna ta rufe ta ajiye shi a gefe guda, ta zauna tana fuskantana tare da haɗe hannayenta wajen guda.
"Amatullah kike ko?".
"Ƙwarai ba ki yi kuskure Amatullah nake".
Ta gyaɗa kanta"ina so na yi miki gargaɗi na farko wanda shi za kasance shi ne na ƙarshe da zan yi miki wanda matuƙar ki na ƙaunar ci gaba da zama a cikin gidan nan dole ki yi bi abin da zan gindaya miki. Kin ga wannan shishshigewan da kike yi wa Hajiya da zummar samun wajen zama babu inda zai kai ki, sai dai ma ya sauƙe ki a tashar ƙasƙanci. Na ji har wani banzan shawara kike ba ta ke a dole kin cika kin batse, to daga yau na ja miki jan layi tsakaninki da Hajiya iyakan cin ki da ita gaisuwa ce daga nan kuma sai gobe".
Tun da ta fara zancen nake bin ta da kallo har ta tsaya a madakata. Ban yi mamaki don izuwa yanzu in da sabo ya ci ace na saba da halinta. Murmushi kawai na yi na ce"yadda kika ce haka za a yi ranki ya daɗe". Ina rufe bakina na tashi na je na yi alwalan sallan zuhur na zo na gabatar da salla a daɗe zaune akan sallayan har sai da na ji wani bacci-bacci ya soma ɗauka ta kana na tashi na ɗauki alƙur'anin na ci gaba da karatuna ban daga wajen ba sai da na yi sallan asr, na fita kicin na haɗa abincin rana na zo na jere shi akan dinning table lokacin Hajiya ba ta cikin falon, haka nan ban ga su Ayan ba Wanda na fi kyautata zaton ko su na can wajen Saif. Don na leƙa ta taga na ga motarsa tana cikin gidan da hakan ya ba ni tabbacin cewar bai fita ba.
Sai da na ci nawa abincin kana na fito falo na kuwa yi sa'a lokacin Hajiya ta fito sai dai da alamar fita za ta yi don mayafinta yana saƙale a bisa kafaɗunta. Na duƙa na yi mata sannu ta amsa mini fuskarta babu yabo babu fallasa.
"Hajiya daman mun gama duk wasu ayyuka ne shi ne nake son na je gida. Inda wani abun zuwa an jima sai na dawo".
"Ba damuwa ni ma daman fita zan yi yanzu, Su Aryan suna ɗakina suna bacci sai ki sanarwa Altine ta na duba su".
"To in sha Allah, a dawo lafiya".
Har ta yi gaba sai kuma ya dawo da baya"an kai abincin Saif ne?". Na jijjiga mata kaina alamar a'a da hakan ya ba ta damar zarce wa da faɗin"ya kamata a kai masa sai a fito da kwanukan safen". Kaina kawai na gyaɗa mata da hakan ya ba ta damar ficewa daga cikin falon, na fita da kallo har sai da ta ɓace wa ganina kana na juya na je na haɗa masa abincin na ɗaura akan tray na nufi sashinsa. Haka kawai a duk sa'ilin da na nufi sashin nake tsintar kaina cikin matsanancin faɗuwa gaban da ban san dalilinsa ba.
Sai da na ja dogon numfashi kana na sama ƙwarin gwiwar tura ƙofar falon haɗe da sallama na shiga ciki, yana nan kwance inda na same shi da safe da dukkan alamu tun da na bar shi bai gusa daga wajen ba, na ajiye abincin kana na ɗauki tray ɗin da na kawo da safe. Na ga alamun ko buɗe wa ba ayi ba balle a ci.
"Ranki ya daɗe a fitar da abincin safen nan tun da ga na rana an kawo?". Na yi tambayar jikina yana rawa. Na yi shuru bai tanka mini ba hakan ya sa ni buɗe plate ɗin don gani da idona cikin rashin sa'a ya zame ya faɗi zuwa ƙasa take ya tarwatse ya yi ɗaɗɗaya. Ƙarar ya gigita ni har sai da na runtse idanuna na ajiye tray ɗin hannuna ina tattare wanda ya fashe ɗin.
"Ranka ya daɗe ka yi haƙuri kuskure ba da niyya na yi ba". Tsit na ji ba a amsa mini har na gama tattarawa na zuwa a gefen tray na juyo na ga yana nan inda yake kwance bai motsa.
Haka kawai na ji ƙirjina ya buga na zo na tsaya a gabansa ina ƙiran sunansa amma shuru bai ko motsa ƴatsunsa ba, balle wani gaɓa daga jikinsa.
Ina janye matashin da ya rumgume a ƙirjinsa na ga hannunsa ya faɗo ƙasa jikinsa ya sake, ban san lokacin da na yi jifa da matashin ina sakin salati da sallallami ba tsabar gigicewa da kiɗimewar da na yi.
[12/7, 1:15 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
©️ Maimuna Tijjani Iyam
______________________________________
Page 6️⃣4️⃣
Na rasa abin da ya dace na yi sai kai komo nake yi a cikin falon rumgume da hannayena a bisa ƙirjina, na rasa wanda zan je na sanar wa halin da yake ciki ga shi Hajiya ba ta nan ta fita, na zo na tsuguna a gabansa ina bubbuga hannun kujerar da yake kwance a kaina tare da ƙiran sunansa.
"Ranka ya daɗe don Allah ka tashi ka buɗe idanunka". Shuru bai amsa ba kamar yadda bai motsa ko da ƴatsun hannunsa ba, hakan ya ƙara gigita dukkan nutsuwar da ya yi saura a gangar jikina da har ban san lokacin da hawaye suka ambaliya a bisa dakalin fuskata ba.
Altine ce ta faɗo mini a ciki raina na yi zumbur na miƙe da nufin na je na sanar da ita halin da na zo na iske shi a ciki, har na tashi na ji wayarsa da yake ajiye akan teburin ta soma ruri kamar ba zsn kula ba sai kuma na ɗauki wayar ban tsaya duba wanda yake ƙira ba na kara wayar a kunnena ina magana ciki sarƙafewar harshe da cushewar numfashi.
"Don Allah ku taimaka mini Yallaɓai ne ba shi da lafiya. Gashi nan ko motsawa ba ya yi kamar ma ba ya yin numfashi".
"Ina mai wayar? Ina shi Saifullah ɗin?".
Aka jeranta mini tambayar a haɗe sai da na juya na kalle shi har yanzu bai motsa ba kafin na ce"ga shi nan a shi da lafiya ne".
"Yana ina yanzu?".
"Yana gida a cikin sashinsa".
Aka ɗan yi shuru kafin can aka ce"ki karanta suratul Baƙara a cikin wuta ki shafa masa a fuskarsa, sannan idan inda yake akwai fanka ki kashe su sannan ki rufe tagogi, ki aiwatar da abin da na ce miki ba tare da kin katse ƙiran ba".
Tamkar ina gabansa haka na gyaɗa kaina alamar duk na saurara abin da ya faɗa kuma na fahimta, na je na ɗauki ruwa na karanta ayoyi goma na farkon Suratul Baƙara na tofa a cikin ruwan, na sa hannuna na ɗeba na yarfa masa a fuskarsa na yi hakan har sau uku amma bai ko motsa ba balle na kai ga saka ran sai buɗe idanunsa har numfashinsa ya dawo.
Ban san lokacin da na fashe da wani kukan ba ina rarumar wayar na mayar da ita kunnena ina faɗin" ka ga har yanzu fa bai tashi ba, ko buɗe idonsa ma bai yi ba". Da ƙyar na ƙare zancen sa boda wani gigitaccen da ya ƙwace mini.
"Ki nutsu ki kwantar da hnakalinki sai mu yi tunanin mafita. Kin rufe tagogin?".
"A'a yanzu zan rufe". Na furta ina miƙe wa na je na rufe tagogin kana na kashe fanka.
"Ki lulluɓe masa jikinsa da bargo mai nauyi sannan ki zauna a kusa da shi ki na ci gaba da karanto masa karatun".
"Ka na ga zsi tashi kuwa?". Na jefa masa tambayar cikin sarewa da kuma cire tsammani.
"In sha Allah ke dai kawai ki yi abin da na ce".
Ban iya amsa masa da kalmomin da baki kan iya furtawa ba, na hanzari na haura sama na shiga cikin ɗakinsa na ɗauko bargon da na gani akan gadon na fita. Garin sauri na zame daga matattakalan benin sai ji na na yi a ƙasa tim, ƙuguna ya bugu sosai da har sai da na runtse idanuna ina cije leɓena sa bosa azabar zafi da zogin da na ji ya ratsa cikin kwanyata.
Da ƙyar na tashi ina dafe jikin gini har na iso inda yake na lulluɓa masa bargo a jikinsa tun daga ƙafarsa har zuwa kafaɗuna, na zauna a ƙasa kusa da kansa ina ci gaba da karatun a hankali cikin muryar kuka.
Ban gushe ina karantun har sai da na ga ya soma motsa ƙafafunsa zuwa hannayensa, sai dai har izuwa lokacin bai buɗe idanunsa ba. Wasu hawayen suka gangaro daga cikin koramar idanuna, zan iya cewa tun da Uwata Hafsatu ta haifo ni cikin wannan duniyar ban taɓa ganin irin wannan rashin lafiyan da numfashin mutum zai ɗauke gabaɗaya, jikinsa ya sandare kamar itace ba. Tun ina karatun da tunani da burin zai buɗe idanunsa har na soma karaya na ɗauki wayar da nufin ƙiran lambar da muka yi waya da mai ita. Na ga wayar da lambobin sirri da hakan yake nufin ba zai iya aiwatar da komai da ita ba, tagwayen ajiyan numfashi na sauƙe tare da ɗaura kaina jikin kujerar da yake kwance akan ta, na koma yin karatun a cikin zuciyata don baki ya yi mini da hakan ya hana ni furta ko da kalma guda.
Rurin da wayar ta soma yi shi ya sanya ni zabura na ɗauko kaina zan ɗauki wayar idanuna suka sauƙa akan fuskarsa. Yana zaune akan kujerar ya jingina bayansa a jikin kujerar tare da cije leɓansa. Idanunmu suka sarƙafe cikin na juna wani kukan ya ƙara kubce mini mai haɗe da farin cikin ganin ya buɗe ido har ya tashi ya zauna.
Wayarsa da yake kusa da ni ya kai hannu ya ɗauka da hakan ya tilasta mini janye idanuna daga gare sa.
"Za mu yi magana an jima kaɗan yanzu ba na jin daɗin jikina inna dawo daidai zan ƙira ka".
Ban san me ye aka ce masa daga ɗayan ɓangaren ba sai ji na yi ya furta"waye ya sanar da kai ba ni da lafiya Sultan?". Ban san amsar da aka ba shi ba a taƙaice ya ce"ok". Daga haka ya datse ƙiran ya ajiye wayar yana lumshe idanunsa tare da furzar da zazzafan iska da bakinsa da har sai da na ji sautin fitarsa.
Muryarta a shaƙe na ce"sannu ranka ya daɗe ya jikin?". Bai amsa mini ba illa idanun da ya tsura mini kamar zai cinye ni