Chapter 6 Reading ZABIN MAHAIFIYATA Book Complete BY ESHAAT.txt Arewa Novels

ZABIN MAHAIFIYATA Book Complete BY ESHAAT.txt

Author :  ESHAAT SMILER Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   6 / 7

15K to 18K   out of 20.8K words

min kunne da surutunku, kun hana na fahimci abinda ake fad'a a news d'in. Yana maganar yana satan kallon salma da take jifansa da murmushi duk dan ta k'ular da humaira.


humaira da ranta ya gama b'aci ta kalle shi ta fara magana ta ma manta da batun wani plan tace "wallahi duk abinda na tsara shi za'abi, koka manta haka akeyi aduk lokacin da kayi aure? kaine ka bani damar tsara duk yanda nake so dan haka yanzuma haka nake buk'atar ayi.


kallonta salma tayi tana murmushi tace "Aunty menene abin d'aga hankali anan? kawai dan zan dinga yima mijina hidima ai ba wani abu bane....


Keee!... Badake nake yiba da wanda ya ajiyeki nake magana. humaira ta fad'a tana huci kamar kububuwa

Look humaira kinsan fa ban cika son hayaniya ba, please kowa ta tafi d'akinta banson tashin hankali.


Mik'ewa salma tayi fuskarta cike da murmushi ta wuce d'akinta. itama humaira tashi tayi ta dube shi tace, "Abdul nika wulak'anta a gaban wancan banzan ko? to wallahi se nayi maganinku daga kai har ita. ta wuce shi ta shige d'aki"

Tsaki yaja ya kashe kallon ya nufi d'akin salma, hakanan yake jin ya rage tsoron humaira yana ganin yanzu bazai d'auki rashin mutuncin ta ba.

kuyi hakuri da wannan wallahi har nayi ya goge.

Readers naji k'orafin ku zan dingayi kullum insha ALLAhu, wanda ba'abi ra'ayin ku ba ina me baku hak'uri.


🌳🌳UMMU AFFAN🌳🌳
[1:36PM, 2/7/2018] β€ͺ+234 808 677 7945‬: 🌳🌳🌳🌳🌳
ZAB'IN MAHAIFINA
🌳🌳🌳🌳🌳

Written by SADIYA ALHASSAN (Ummu Affan)

🌐HAJOW πŸ“πŸŒ

πŸŒπŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS ✍🏾✍🏾✍🏾🌐

Dedicated to PRINCESS ESHAT AYSM
AYSHA BICHIKI

Page 21

Sistr eyshert Aysm ina miki murna da fara sabon novel d'inki (WAZAN SO) ALLAh ya k'ara d'aukaka,yanda kika fara lafiya ALLAh yasa ki gama lafiya. Inayin ki sistr irin sosai d'innan.😘


Akashe ya samu wutan falon amma yana iya hango d'an haske ta cikin bedroom d'in. Sallama yayi sannan ya shiga d'akin a kwance ya sameta ta bama k'ofar baya, tayi nisa a tunani da alama batasan mutum ya shigo d'akin ba.

Gefenta yaje ya kwanta ya juya mata baya,sannan yaja bargo ya lullube jikinsa. ya kashe bedsite lamp dake gefenshi, se a lokacin salma tasan ya shigo d'akin. Cikin sauri ta mik'e zaune ta ce mallam lafiya zaka shigo min d'aki ba ko sallama,

Ko juyowa beyiba bare ya nuna yasan tana magana. duk da haka batayi shiru ba, gaskiya ka tashi ka koma d'ayan d'akin dan ni bansa ba kwana da wani namiji a cikin d'aki d'aya ba.


Batare daya juyo ba ya fara magana "Nan gidana ne ina da ikon shiga duk inda naso a kowani lokaci, kuma ya kamata kisan banbancin dake tsakanin da da kuma yanzu, ki iya bakinki saboda yanzu a k'ark'ashin iko na kike, ba k'ark'ashin ikon iyayenki ba. Agidana kike ba gidanku naje ba.


Shiru salma tayi batare da ta sake cewa komai ba ta mik'e domin ta koma d'ayan d'akin. Muryar shi taji yana bata umurni koma ki kwanta, dan ni bana raba makwanci da matata ki kiyaye ko saboda gaba, komawa salma tayi ta kwanta amma ta gagara runtsawa saboda fargaba da rashin sabo, ga sanyi da takeji.

Shima ba baccin yakeyi ba, tunani ne ya cika kwakwalwar sa, ya rasa me yake damunsa ga wani feeling dayake ji wanda be tab'a jin irinsa akan wata 'ya mace ba.

Sauk'ar numfashinta yaji abayansa alamar bacci ya d'auketa, juyowa yayi yana kallonta tana baccinta cikin kwanciyar hankali, ta dunk'ule jikinta waje d'aya. Tsintar kansa yayi da rungumota zuwa jikin sa, a tare suka sauk'e ajiyar zuciya, itakam cikin bacci ne ba tare datasani ba, yayin dashi kuma najin dad'in jinta dayayi ajikinsa ne.

Kallonta yakeyi be tab'a sanin tana da kyau sosai haka ba, tayi mishi kyau datake bacci, sleeping beauty ya furta a hankali.


Jawo bargon yayi ya lullub'a musu gaba d'aya, yayi addua ya shafa musu. abinda ya juma beyi ba wato addu'an kwanciya.

Cikin dare salma ta farka tajita a jikin mutum, hannu takai ta kunna lamp d'in dake gepenta, zuba mishi ido tayi tana kallon fuskarshi ga kwantaccen sajen shi wanda ya kwanta a fuskar shi, ya k'arama fuskar shi kyau da kamala gaskiya ta yarda Abdul me kyau ne.

Hannun shi ta kalla wanda ya zagayeta dashi tunani takeyi ta yanda zata cire hannun batare data tashe shi, gashi so take yi ta tashi ta d'auro alwala tayi sallan nafila.


A hankali ta zare jikinta a cikin nashi ta nufi toilet domin ta d'auro alwala, k'aran bud'e kofar toilet d'inne ya tashe shi. Yana kallonta ta cikin hasken dayake d'akin, ta fito ta d'auki hijab d'inta ta tada kabbara.


Raka'a hud'u tayi tadad'e a sujjadarta ta k'arshe tana kaima ALLAh kukanta kafin ta d'ago ta sallame.

bayan tayi zikiri tayima annabi salati,ta d'auko alqur'ani ta fara karatu cikin sanyin muryanta. Duk abinda takeyi A.A yana kallonta nan take farin ciki ya rufeshi, Salma itace irin matar dayake burin ya aura tun farko. Haka kawai shima yaji yana sha'awar yin nafilan koda raka'a 2 ne, idan be manta ba rabonshi da ya tashi sallah da daddare tun kafin yayi aure. mik'ewa yayi ya shiga toilet d'in ya d'aura alwala,ya fito ya shimfid'a sallaya ya tada kabbara.

Bayan ya idar yayi addu'o'inshi, sannan shima ya d'auko alqur'ani daya gani a gefe ya fara karantawa. Salma tabar karatun da takeyi ta juyo tana kallon shi jin yanda yake k'ira'ar sa kamar sudes, A.A daya kammala karatun shi ya juyo ya kalleta jin dayayi tayi shiru da barin karatun.

Gani yayi ta zuba mishi ido da alama hankainta baya wajen. hure mata ido yayi, yace "yadai 'yan mata kallon fa?" cikin sauri ta kauda kanta cike dajin kunyar kamata da yayi tana kallon shi.


Rufe qur'anin tayi ta mik'e ta cire hijabin ta ninke ta adana shi, sannan taje ta kwanta, Shima tashi yayi yaje ya kwanta ya jawota jikinsa, ya lullub'a musu bargo suka koma bacci.


ASUBA TA GARI SAL-AZEEZ.


Humaira kuwa tana shiga d'akinta ta d'auki waya ta kira lina ta fad'a mata duk abinda ya faru, masifa lina tahauta dashi,tace bakiji abinda boka ya fad'a bane? yace fa idan kikayi wasa ita ce silar tonuwar asirinki. gashi kin jawo har yana miki musu a gabanta. humaira tace "wallahi lina rainane ya b'aci shiyasa" humy sefa kinyi hakuri kin daure zuciyar ki kafin komai ya tafi yanda muke so. dad'a bata shawari lina tayi sannan sukayi sallama

Shiru-shiru humaira bataga A.A ya biyo bayanta ba kamar yanda ya saba, tashi tayi ta leka falon gani tayi bakowa da alama d'akin salma ya tafi. dawowa tayi d'aki ta kasa zama duk tunanin kar wani abu ya shiga tsakanin su, gashi ba daman taje d'akin Saboda kar plan d'insu ya wargaje. A tak'aice ranar haka humaira takwana tsabar kishi kamar zatayi hauka.

Da asuba ya riga salma tashi, saida yayi alwala sannan yazo ya tasheta ya shimfida sallaya yayi raka'atainil fajri.

Bayan salma ta d'auro alwala yaja su sallar asuba, bayan sun idar sukaci gaba da karatun alqur'ani har gari ya k'arasa wayewa.


Salma ce ta gaishe shi ya amsa fuskar shi d'auke da murmushi, dan jinshi yake cikin farin ciki.

Mik'ewa tayi tashiga toilet ta had'a mishi ruwan wanka ta fito ta fad'a masa, binta yayi da kallon mamaki da tunda suke da humaira bata tab'a had'a masa ruwan wanka ba dan komai da kansa yake yi.

thanks yace sannan ya tashi ya nufi toilet d'in ita kuma ta nufi kitchen dan ta d'aura musu breakfast


dankali ta soya musu da kwai, tayi musu farfesun kayan ciki, se ruwan lipton dayaji kayan k'amshi. bayan ta kammala ta debi kayan breakfast d'in takai babban falo dan tana da tabbacin humaira bata tashiba a lokacin.


d'ayan bedroom d'in ta shiga do tayi wanka. A.A ya fito daga wanka daga shi se towel a daure a k'ugunsa, se k'arami a hannunsa yana goge sumar kanshi. gaban mirror yaje yana k'arewa mayukanta dake kan mirron kallo. hannu yasa ya d'auko wani lotion me k'amshi ya shafa.

Fitowa yayi yanufi d'ayan d'akin dan ya shirya, saboda akwai sauran kayanshi daya manta be kwashe ba a d'akin.

shigarsa tayi dai-dai da fitowar salma daga wanka, tana d'aure da towel wanda ko cinyoyinta be gama rufewa ba. Daskarewa yayi a wajen, ganinta d'aure da towel ya d'aga masa hankali, takowa ya farayi zuwa inda take tsaye, salma data kasa yin gaba bare baya tsabar kunya daya rufeta kamar k'asa ta tsage ta shiga haka takeji.

Ganin yana nufota ne yasa ta juya a guje ta koma toilet d'in ta rufo kofa. murmushi kawai yayi ya girgiza kai.

kan mirron d'akin ya nufa ya shafa ma sumar sa mayuka ya fesa hairsprayer. sannan ya nufi wall drop ya ciro kayan da zai saka. Black jeans ya ciro da farar t-shirt me guntun hannu, a gaban rigan an rubuta HANDSOME da bak'ak'en harufa. Ya saka farin takalmi cover shoe se bak'in jacket daya d'aura akan kayan kasancewa lokacin hunturu ne. turaruka ya d'auka ya fesa san ya bar d'akin ya nufi part d'in humaira



Salma saida taji fitar shi ta fito ta koma d'ayan bedroom d'in ta shirya cikin doguwar rigar material fitted gawn bata d'aura d'ankwali ba se tayi rolling da siririn mayafi kalan kayan, ta fesa turarukanta ta fito ta nufi falo.

Bata tarar da kowa ba, zama tayi akan kujeran dining d'in ta fara had'a tea dan baza ta iya zaman jiran su ba.

bata dad'e da zama ba A.A ya fito da alama har yanzu humaira bata tashi ba, hanyar fita taga ya nufa ta d'an d'aga murya tace "ga breakfast d'inka fa"

Juyowa yayi yana kallon ta shi abin natama ya dena bashi mamaki se burgeshi da takeyi. Yaushe rabon da yayi breakfast a gidansa ai harya manta, se dai kullum idan yaje office ya aika a siyo mishi a restaurant, indai kaga ya karya a gidansa to ranar weekend ne shima se 11:00am. shi harya ma saba, duk lokacin da zai tafi office harya shirya humaira bata farka daga bacci ba bare ta bama mai aiki umurnin abinda za'a girka(mata dan ALLAh mu gyara)

K'arasowa yayi ya zauna, cup ta d'auka ta had'a mishi tea ta d'auki plate ta zuba mishi dankalin da farfesun. be wani ci da yawa ba ya tashi duk da abincin yayi masa dad'i. briefcase d'insa ya d'auka ya nufi hanyar fita daga falon,

"A dawo lafiya ALLAh ya tsare ya bada sa'a" salma ta fada tana bin bayansa da kallo. Juyo wa yayi, yayi mata k'ayataccen murmushi dan har a ransa yaji dadin adduar datayi masa, sannan ya juya ya fita,



muje zuwa




🌳🌳UMMU AFFAN🌳🌳
[1:36PM, 2/7/2018] β€ͺ+234 808 677 7945‬: 🌳🌳🌳🌳🌳
ZAB'IN MAHAIFINA
🌳🌳🌳🌳🌳

Written by SADIYA ALHASSAN (Ummu Affan)

🌐HAJOW πŸ“πŸŒ

πŸŒπŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS ✍🏾✍🏾✍🏾🌐

Dedicated to PRINCESS ESHAT AYSM
AYSHA BICHIKI

Page 22










Tattara wajen salma tayi, sannan ta dauki plate ta d'ebama me gadi ta hada masa tea ta fita domin takai masa.

A zaune ta tarar dashi yanajin radio, bayan sun gaisa ta mik'amishi, karb'a yayi yanata zuba mata godiya. Salma ta kalle shi tace "Baba dan ALLAh za'a samu ganyen magarya anan kusa?" eh baza a rasa ba, akwai anan baya bari naje natsunko miki. Godiya salma tayi masa sannan ta koma ciki.

Tana zaune a falo taji ana sallama tashi tayi ta lek'a, taga me gadin ne ya dawo hannunsa d'auke da bak'in leda, mik'amata ledan yayi "hajiya gashi ansamu amma d'anye ne" karb'a tayi tana murmushi bakomai baba daman nafi buk'atar d'anyen, godiya ta sake mishi.

part d'inta ta koma ta tsinki ganyen magaryan guda 7 ta zuba a wani roba ta jik'a da ruwa, ta tofa ayoyin shifa aciki da wasu adduo'i ta barshi ya jik'a. Zob'onta ta hada me dadin gaske,da ruwan addu'an ta saka a fridge.

Falon ta koma ta tattara kayan da sukayi breakfast wanda suka bata, ta wanke ta maida komai yanda yake. Ta gyara part d'inta ta fesa room fresh, ta kunna turaren wuta a burner, ko ina ya dau kamshi.


Humaira ta fito tayi wankan ta tayi kyau ba lefi se dai idanunta sun kumbura da alama taci kuka ta k'oshi. dining taje tayi breakfast sannan takoma kan kujeran falon ta zauna.

k'arfe 11:00 salma ta d'aura abincin rana, shinkafa da miya tayi wanda yaji naman kaza, tayi had'in coslow. ta zuba shinkafar a cooler, coslow d'in ta zuba awani d'an tangaran ta rufe da farin leda ta saka a fridge



Tunanin wanda zata samu yakaima A.A office takeyi, knocking taji anayi mata, zuwa tayi ta bud'e humaira tagani a tsaye " malama kizo kinyi bak'i, ta juya abinta fitowa salma tayi tabi bayanta. Ita dai bataga kowa a falon ba, waje ta lek'a ta tarar da drivern gidansu A.A tare da wata yarinya wanda baza tafi 14years ba. Bayan sun gaisa yake fad'a mata hajiya ne ta aiko shi ya kawo mata 'YAR AIKIN. Ya mik'o mata wani leda yace "ga wannan tace zakiga bayanin komai a ciki. karb'a tayi tace yace ta gode, harya juya zai tafi ta tsayar dashi "dan Allah ko kasan wajen aikin Alh. Abdul?"Alh. gidan nan? ya tambaye ta "eh shi nake nufi" salma ta bashi amsa.

Nasani ranki ya dad'e, dan Allah aika zan baka ka kai mishi idan bazan takura ka ba.salma ta fad'a, A'a hajiya bakomai ki kawo sena kai mishi.

Hannun yarinyar salma ta kama suka shiga ciki bata tarar da humaira a falonta ba, Abincin ta had'a acikin basket ta d'auko had'in zob'onta wanda yayi sanyi ta zuba a jug, ta d'eba ma yarinyar abinci a plate ta bata sannan ja d'auki basket d'in takaima drivern.





Manage with this





🌳🌳UMMU AFFAN🌳🌳
[1:36PM, 2/7/2018] β€ͺ+234 808 677 7945‬: 🌳🌳🌳🌳🌳
ZAB'IN MAHAIFINA
🌳🌳🌳🌳🌳

Written by SADIYA ALHASSAN (Ummu Affan)

🌐HAJOW πŸ“πŸŒ

πŸŒπŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘§HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS ✍🏾✍🏾✍🏾🌐

Dedicated to PRINCESS ESHAT AYSM
AYSHA BICHIKI

Page 23

Ledan da aka kawo mata tadauko ta bude,turaruka ne masu kamshi na jiki, se hadin zuma ,dabino da ridi, se mad'i da sauran kayan mata masu inganci. Kowanne an rubuta yanda zatayi amfani dashi ajikin takarda.


Mayarwa tayi cikin ledar aranta tana raya mezatayi dashi, ita tagaji dashan irin wadannan abubuwae, dan tun tana gida Aunty hadiza take d'ura mata su. gwanda ma turaren xata iya amfani dasu.

dauka tayi takai cikin dakinta, ta bude wall drop dinta tasa a ciki ta rufe. ta dawo falon ta tarar da yarinyar ta gama cin abinci. zama tayi akan kujera ta kalli yarinyar tace "menene sunanki?" sunana jamila, yarinyar ta amsa mata. To jamila zaki dinga yimin wanke-wanke da shara se mopping, iya kacin ki falo da kitchen banda cikin d'aki wannan zan gyara da kaina. ina fatan zakiyi aikin ki ba tare dakin bani matsala ba?

Insha Allahu aunty zan kiyaye, zaki sameni mebin umurninki. to shykenan yanzu kije kitchen akwai wanke-wanke se kiyi, amsawa tayi sannan ta mike ta shiga kitchen din domin ta aiwatar da aikin da aka sata.

tananan zaune har yarinyar tagama ta fito, mik'ewa tayi tace"dauko kayanki muje na nuna miki yanda zaki zauna.

B.Q takaita dakunane guda 2 kowanne da toilet a ciki se falo a tsakiya, se k'aton kitchen a gefe da alama shine manda ake girki a ciki. daki daya blessing ne a ciki, d'ayan d'akin wanda ba kowa salma tace ta shiga, ta juya ta koma part d'inta.

Toilet ta shiga ta d'auro alwala tayi sallar azahar. ta dawo falo ta zauna ta kunna tashar arewa24, ta samu suna hasko film din dawo-dawo.


Tana zaune taji an turo k'ofarta an shigo ba neman izini, d'aga kai tayi dan taga waye me k'arfin halin shigo mata d'aki haka.

Blessing ta gani 'yar aikin humaira, cikin b'acin rai salma ta daka mata tsawa "Ke!.. baki da hankali ne? da zaki shigo min d'aki ba neman izini, haka aka koya miki a gidanku?" Jikinta yana b'ari ta durk'usa tana bawa salma hakuri.

Fuska ba fara'a salma tace "me kikazo yimin a d'aki?" cikin girmamawa ta amsa hajia babba ce ta aiko ni nazo na karb'a mata abinci a wajenki.

shek'ek'e salma take kallonta tace kije kice mata ban girka da ita ba. cikin sauri ta mik'e ta fita

Bugo kofar akayi aka shigo, humaira ce cikin masifa ta fara magana " ke salma ina abincina?" ban girka dake ba salma ta fad'a. kutman uba..πŸ™Š ina cikin gidannan kiyi abinci kice baki girka dani ba? to wallahi baki isa ba, da wani tsugudidin ne yasa kikace zaki dingayi da kanki?

kallonta salma tayi tace "ai da nace zan dingayi da kaina bance hardake zan dinga girkawa ba, wa mijina nace zan girka. Alfarma d'aya zan iya miki, shine zan dinga yi dake safe da dare, da rana kuma seki nemi abinda zakici. Hakan ma albarkacin mijina kikaci, dan haka karki sake zuwa kice na baki abinci danni ba 'yar aikinki bane.

Dubanta humaira takeyi cike da mamakinta,yarinya k'arama ta tsaya tana fad'a mata magana , wanda inda tana da k'anne tayi k'anwa ta 2 da ita, lalle ta samu waje da yawa tace " wallahi salma ina tausaya miki, ni humaira nayi alk'awarin sena LALATA (littafin sad-naf) miki rayuwa, se kinyi nadamar shiga gonata da kikayi.


Tab'e baki salma tayi tace " ni nafi k'arfinki wallahi, idan kina takama dabin malamai ne to

6 / 7