ZAWARCI BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Mrs Sadauki .txt

Author :  Mrs Sadauki Category :  Love Story

Chapter   7 / 13

18K to 21K   out of 37.3K words

ta binne kurwar jariri can ƙasan zuciyarta ta furta ‘ zuwa dare zan zo na tone’ haka suka isa gida.






Ta kuwa ci sa'a Daddy bai fita ba,Murjanatu ta gaishe shi ya amsa tare da yi mata barka kafin ya maida dubansa ga Hajara wacce sai raba ido take kana gani ka san ba ta da gaskiya.


“ Hakan da kika yi daidai ne? Don dai ba ni ne na haifi Murjanatu ba shine kika koro Habibah daga asibiti? ”




“Ka yi haƙuri ba koro ta na yi ba,na dai ce ta dawo gida tun da ba za a barin mai jego ita ɗaya ba a gida”


“Mi yasa ba ki kira ni kin shaida min zancen haihuwar ba? Ban cancanta ba ne ko me?”


“Ka yi haƙuri Daddyn yara,yanzu dai ka kira shi mijin nata ka shaida masa zancen haihuwar ”


Bai amsa mata ba ya fice,sai a lokacin Habibah ta fito idonta kan jaririn wanda ke baccin wahala.Cike da tausayinsa ta ƙarasa ta ce “ barka Murjanatu Allah raya shi kan sunnah”
“Amen na gode” ta amsa tare da miƙa mata jaririn,Habibah ta karɓe shi tana mai zaunawa kan kujera ta shafi sumar gashinsa tana kallonsa da kyau ta tabbata kurwarsa na gidan yari ba a cinye ba sai dai ba ta san a ina aka binne ta ba.Haka ta gaji da binciken ta miƙa shi ga uwarsa ta miƙe suna ƴar kallon-kallon ita da Hajara wacce idon nan nata suke wiƙi-wiƙi na maras gaskiya.




A sanyayye Habibah ta koma ɗakin Safeenatu,“ ya dai Gwaggo Habibah lafiya na gan ki duk kin yi wani iri?” Feenat ta tambaya.


“ Babu komai Safeena,bacci Baseerat take?”


“Eh ba ta jima da rufe idon ba”


“Mu gan ta” Habibah ta faɗa tare da yin zama, Safeenatu ta ɗora mata jaririyar kan cinya.Hannunta mai safa ta kamo ta cire sannan ta soma shafa shi ,zuciya cike da rauni ta soma yin magana “ ki tausaya ki ceto jaririn da bai san komai ba,ki sani shi ma tamkar Basheer yake mai rauni ne.In kuma har yanzu kuna cikin fushi ne shi yasa kuka hana ta ɗauki mataki ku yi haƙuri,amma dai a duba lamarin” tana gama faɗa Baseerat ta buɗe idonta taram cikin na Habibah,ita kuwa ta shiga kallon abubuwan da suka faru bayan ta bar asibitin a cikin ƙwayar idon jaririyar ta ga komai har inda Hajara ta binne kurwar.Tana gama gani Baseerat ta maida idonta ta rufe, Safeenatu dai na gefe a yanzu ma kallonsu take ba tare da ta ce komai ba.






Habibah ta ja ajiyar zuciya ta sakar mata murmushi ita kuwa kai ta ɗauke,tana mai jawo wayarta ta kunna data so take ta yi bincike don gano shin abubuwan da suke faruwa zai iya kasancewa ko kuwa ƴarta ce kawai ke da shi.








Tunanin ta watsar ta shiga WhatsApp ta fara duba saƙonnin mutane masu yi mata barka kafin kwatsam ta ganta cikin wani group.A hankali ta soma biyayar abubuwan da ke faruwa sai ta ga amsoshin tambayoyinta kan wani posting.


```“M” CIKIN TAFIN HANNU,MAUME HAND/PAUME DE MAIN


Chiromancy wata daɗaɗiyar hanya ce ta hango makomar mutum da kuma fassarar halayyar mutum daga dalilin layukan hannu. Wani lokaci waɗannan layuka na iya samar da lambobi da haruffa. Ɗaya daga cikin waɗannan wasiƙun na iya zama wasiƙar M, ma'anar wacce mystics da dama suka yi nazari a kanta.


Kamar yadda mutane da yawa suka yi imani, layukan da ke kan tafin hannunmu suna bayyana halinmu da ƙaddararmu. La lettre M est attribuée à des personnes vraiment spéciales(The letter M is assigned to truly special people). An ba su kyakkyawar fahimta kuma suna wakiltar abokan haɗin gwiwa akan dukkan wasu kasuwanci.


Idan mutanen da kake so suna da wasiƙa ta musamman M a cikin tafin hannu ya kamata ka sani cewa ba za ka iya raina masa hankali ba kuma ta wata hanyar ba za ka iya yin ƙarya ko yaudarar wannan mutumin ba. Kasancewar shi mai dubara da hankali da tsantsar lura sosai, mutamin da ke da harafin M a tafin hannu cikin sauƙi zai fahimci cewa ana yi masa ƙarya ne ko yaudara.




``Matan da suke da harafin M a tafin hannunsu suna da zurfin tunani fiye da maza, har ma da waɗanda suke da wannan wasiƙar. Ana yi musu baiwa da ikon sarrafawa da shawo kan duk wani cikas a rayuwa, kuma sun san yadda ake amfani da albarkatu da damar da ake da su.
Harafin "M" a kan tafin hannu ma na iya nufin:
• Ƙwarewar shugabanci
• Iko wato power/pouvoir```




Zuciyar Safeenatu banda bugawa babu abin da take yi har sai da ta ajiye wayar ta je ta ɗauki ruwa masu sanyi ta sha .Ta dawo ta zauna don ƙara duba saƙon sai dai hatta shi kansa group ɗin ya ɓata a wayarta babu shi sam .Kamar mahaukaciya haka ta miƙe ta je ta yi wani gurwanau a gaban net ɗin da aka saka Baseerat,ta zuge zip ɗin ta kalli ƙofar toilet inda motsin ruwa ke ta zuba da alamu Habibah wanka ta shiga ba tare da ita ta san yaushe ta shiga ba .


Murya a ɗan kasalance ta ce “ Baseerat ni ce mahaifiyarki,ni na haife ki.Duk wani wanda bai son ganin kin cutu to tabbas sai dai ya biyo bayana,don haka kar ki ga kamar ban son ki a'a wallahi zuciyata raunk ne da ita.Magana nake son yi miki game da abin da na gani cikin wayata,shin kina da masaniya? In dai tabbas ke ƴar baiwa ce kamar yadda saƙon nan ya bayyana to ki buɗe idonki ki kalle ni” ko rufe baki ba ta yi ba kuwa Baseerat ta buɗe idon sai da Safeenatu ta dafe ƙirji saboda tsoro.




“Mine ne wai?” daga bayanta Habibah ta tambaya ,zip ɗin net ɗin ta mayar tana mai cewa “ babu komai Gwaggo Habibah,na yarda na aminta da lamarin nan gaske ne ana samun ƴan baiwa to Allah bata ikon yin amfani da ita ta hanyar ƙwarai” ruwan sama ne suka fara sauka a daidai lokacin da Safeenatu ta rufe bakinta.






Gwaggo Habibah ta yi wani ɗan ihun murna tare da rungume Safeenatu ta ce “ kin ga ko? Ƴarki ta musamman ce ancestor/ ancêtre suna tare da ita”


A wannan daren cike da zullumi da tunani Safeenatu ta yi shi,da ta samu bacci ya ɗauke ta mafarkai ta yi barkatai akan goben Baseerat.
Washegari tun da safe kukan jaririn Murjanatu ya cika gidan kamar wanda ake cirewa rai.




“Jaririn can ba dai kuka ba” Safeenatu ta faɗa .
Habibah ta ja baki ta yi shiru tana tuna jiya irin gumurzun da suka yi ita da Hajara akan kurwar yaron.Dakyar ta yi nasara ta tone ta tare da saka Hajara don doli ta mayar masa abarsa wacce tuni ita kanta kurwar ta yi rauni,kukan da yake yi kuma saboda ciwon jiki ne.




★A kwana a tashi babu wuya wurin Allah yau ne sunan Twins ɗin Safeenatu waɗanda dangin Bashir suka yi bajinta sosai wurin yankan manyan raguna uku biyu na BASHEER ɗaya kuma na BASEERAT .A wannan rana ta farin ciki Safeenatu ta rakuɓe wuri guda tana ta yin kuka,ga shi dai ta sha ƙunshi da kitso ga kuma gizner ta gani ta faɗa amma rashin masoyinta ya dawo mata daram musamman yadda ake ta faɗar an yi masa madadi da kuma addu'o'in da mutane ke yi.
Da wannan damar Gwaggo Hajara ta shirya mugunta wacce take kambacin fansar da ta yi niyyar ɗauka akan Habibah da hana ta rawar gaban hantsi.Sai da ta bari duk hankalin mutane ya ɗauku,sannan jarirai duk an fitar da su can tsakar gida saboda zafin da ɗakin ya ɗauka sannan ta nufi ɗakin Safeenatu.Duk da akwai mutane hakan bai hana ta gwada sa'arta ba,“ ungo Safeena Gwaggonki Habibah ta ce ki ci abincin nan kafin ta zo ta yi miki ta ƙarfi tun da dai ke ba ki jin magana kina jego amma kin ƙi cin abinci ” Hajara ta faɗa tare da miƙa mata plate mai cike da nama ya sha jar miya,ta karɓa tana turo baki tare da soma ci don ita duk a tunaninta gaske dai Habibar ta bata.Cike da murna Hajara ta bar ɗakin ta je ta kasa kunne tana jiran sakamako.




Da rana mutanen arziki sun cika gida, Safeenatu ta shiga Toilet ta yi wanka da canza kaya daga shadda zuwa less.Kamar wacce aka yi wa wankin ido haka take ganin ƴan biki tsirara tamkar babu kaya jikinsu,zuciyarta ta yi wani mugun bugawa ganin ta soma ganin hanjin cikin mutane yayin da kuma take jin wani abu a bakinta da ba ta san mine ne ba.A daidai nan free page ya ida,duk mai son ci gaba za ta biya kuɗi domin shiga PAID GROUP.


*FREE PAGE/ PAGE NA KYAUTA YA IDA*


Detail 500 via 6042551755
Hassana ibrahim
Keystone bank DM +22795045822
In kin san ba ki shirya saya ba kar ki min magana,ga detail nan kawai ki tura kuɗin ki turo min evidence ta WhatsApp.


*NB:* daga lokacin da ya kammala ya zama complete zai koma 1000.






01 octoba 2024


#CHAMSIYA LAOUALI RABO
MRS SADAUKI 💫
[01/10 à 12:03] MRS SADAUKI 💫: *IBRAHEEM*
```soldier man```


© Chamsiya Laouali Rabo
#MRS SADAUKI💫✍️


*FCWA ☀️*


#Sadaukarwa ga duk waɗanda suka taɓa rasa wani jigo nasu a soja.Allah jadadda rahama a gare ka Yayana AbduRashid😓




*Ƙirƙiraren labari ne,bai faru ba a gaske .Ban yarda a juya shi ko a mayar da shi audio doli sai da izinina*




1-2




A nutse nake sauraren mahaifiyata ido a lumshe,tun da ta fara nasihar nake daɗa jin nutsuwa na sake samun gurbi a zuciyata har sai da ta zo da furucinta na ƙarshe wanda yayi tsananin razana ni har ban san lokacin da na furta “mi kika ce Ammy?” na yi tambayar da tunanin ko kunnena ne bai jiye min daidai ba.


“A yau an ɗaura aurenka da Maryama ina so ka riƙe amana zuwa gobe in sha Allah zan kawo ta da kaina” ta sake maimaita wa,shiru na yi ina jin wani yanayi marar misaltawa.


“Ibraheemu haƙuri za ka yi, wannan ne kawai gatan da za mu yi wa Maryama don nuna soyayyarmu gare ta da kuma jadadda girman alƙawarin da na ɗaukar wa mahaifiyarta kafin ta bar duniya” yanzu ma dai shiru na yi ba don ban ji ba sai don abubuwa da dama da suka dinga gwaro a kwanyata.


“Heemu ka na ji na kuwa?”
“Na'am Ammy ina ji” na faɗa ina jan ajiyar zuciya,ita ma ajiyar zuciyar ta sauke kafin ta ce “ ina Daddyn ka?”
“Ya fita tun jiya bai dawo ba”
“Okay sai an jima ”
“Ammyyy!” na faɗa da sauri,sai ta tsaya da ƙoƙarin kashewar ta ce “ ya aka yi yarona ina jin ka?”
Kamar mai koyon magana na ce “ki bar ta nan wurin ki har zuwa wani lokaci ”
“Saboda me?”
“Kawai Ammy ”
“Sai mun zo” ta faɗa tare da kashe kiran na furzar da huci ina jin duniyar na juya min.Screen ɗin wayar na ƙurawa ido ina kallon hotonmu wanda shine hoton ƙarshe da muka ɗauka tare da ɗan uwa kuma abokina.


«Zo mu ɗauki hoto ina jin a jikina kamar ba zan fito daga wannan yaƙin ba»cewar Abakar ya na dariya,wacce ba ta kai ga gushe wa ba na yi amfani da wayata na ɗauke mu selfie.Hoton na shafa yayin da kuma muryarsa ke yi min amo a dodon kunne,da sauri na miƙe na nufi ɗakin motsa jiki na soma training.Na shafe kusan awa biyu kafin na fito na wuce bedroom wanka na yi na shirya cikin t-shirt ta soja da wandon kaki.Key ɗin mota na ɗauka kafin na sauko ƙasa inda ƴan aiki ke ta shawagi,su na gani na suka soma gaishe ni kamar kullum da kai kawai na amsa masu na fita zuwa harabar gidan.




Inda motata ke parker na nufa direct, ɗaya daga cikin escort ɗin ne ya rugo ya na tambaya ta inda zan je.“ Ni kaɗai zan tafi babu buƙatar rakiya ko ba ga cikin kayan da nake ba?”
“Sorry mai gida yalɓai ne ya bada umarnin duk inda za ka je mu yi ma rakiya” ya faɗa cike da girmamawa.
“Yi tafiyar ka” na faɗa tare da shige wa ciki na yi wa motar key,wurin fita ma sai da sojawan da ke tsaron ƙofa suka ɓata min lokaci kafin su bar ni na fita.




A hankali nake gudu ina duba yanayin garin da yadda al'amurra ke tafiya,a haka har na isa barikin soja.Daidai ɗakinmu na yi parking,na jima sosai kafin na fito ,key nasa na buɗe ƙofar na shiga a nan take duk wani tsohon tarihi ya dinga dawo min.Dakyar nake cira ƙafa ina takawa izuwa ciki,daidai akwatinsa na je na tsaya tare da buɗa shi na ciro kakinsa mai ɗauke da sunansa Abakar.Na rungume rigar ina jin ƙamshin jikinsa na ratsa hancina,karon farko da na ji idona sun cika da hawaye tun bayan dawowar mu daga yaƙin da ya zame mana shamaki ni da abokina.


Sosai nake hawaye ina jin dutsen da ya jima da yin gini a zuciyata na motsawa haɗi da zubar da tururi .


“Ibraheem!” ya kira sunana a dake,duk da na san ko wane ne bai sa na juyo ba har lokacin da nake jin takunsa na matso ni.
“ Mi yasa ka fito alhalin na ce ka zauna gida? Shi ne kuma ka hana escort su take ma baya,mi yasa ba ka jin magana ta? In fa wani abu ya same ka?”


Sai a lokacin na juyo muna facing juna,ban ce masa komai ba sai idona masu cike da baƙin ciki da zafin ɗaukar fansa na ƙura masa.
“ Wannan zuciyar da kake ji da ita kar ka manta ni ka gado amma shine don tsageranci za ka ƙure ni da ido ka na kallo kamar sa'an ka.Abakar ya mutu ba shine sojan farko da ya taɓa rasa rayuwa ba a wurin yaƙi amma duk ka bi ka adabi mutane da hauka,shi Abakar ɗin wa ya fi ne da ba za a kashe shi b...”
“Daddy???” na faɗa a zuciye kafin kuma na juya na mayar da rigar C
cikin akwati na rufe na sungumi akwatin na fito,don yanzu shi ne kawai abin da ya rage min nasa.




Bayan mota na saka shi,sam ban damu da tarin sojawan da suke tsaye ba waɗanda na san tare suke da mahaifina.Ko ɗakin ban koma na rufe ba na yi wa motar key,ina tafe ina tunanin ƙiyayyar da Daddy ya ɗorawa Abakar dare ɗaya wacce a can farko ba haka suke ba.
Na ja wani huci ina mai danganta abin da don ya fito gari guda ne da mahaifiyata,a haka na isa gida can sama na haura da akwatin na ajiye shi bisa bed ɗina.


Gaban mirror na je na yi tsaye na ƙurawa fuskata ido wacce ta ƙara yin ja don ɓacin rai,baƙar sumar kaina mai tarin yawa na hargitsa ina kai wa ƙaton ƙirjina duka ina mai yin wata hargowa kamar kumurcin zaki har manyan damatsana su na masu motsawa.




Wayata ce ta ɗau ruri sai da ta yi na uku kafin na ciro ta na ɗauka haɗi da karawa a kunne.
“Ka sauko ƙasa ina son yin magana da kai” shi ne abin da ya faɗa kafin ya kashe, toilet na shiga na wanke fuska ta kafin na sauka ɗin.A zaune na tarar da shi ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya,shi ma sanye yake cikin na soja mai ɗauke da adon galolin yabo birjit.Kujera mai facing tasa na zauna ina mai sunne kai saboda sai yanzu ne na ji ban kyauta ba game da abin da na yi masa.
“Ibraheem ka ɗago ka kalle ni” yayi furta cike da kulawa,ƙin ɗagowar na yi saboda kallon tsakiyar idon Daddy sai mutum ya shirya,na sha jin sojawa na faɗar su na shakkar kallon nasa wanda ni ma shaida ne ba a ko wane irin yanayi ba ne nake iya kallonsa.




“Mine ne damuwar ka? Abakar?”
Sai a lokacin na ɗago na dube shi,murya cike da rauni na ce “ Daddy shi ɗin abokina ne tun na ƙurciya ina mugun sonsa,tamkar yadda Wa ke son ƙanensa...” shiru na yi ina jan ajiyar zuciya.




Daddy ya ce “ saboda mutuwarsa ce nake ganin rauni a idon ka? Ka gaji ne da aikin sojan na tsige ka?”
Wani irin halbawa zuciyata ta yi,da sauri na ce “ haba Daddy ya za ka ce haka? In na bar aikin soja mi zan yi ?”


Ya miƙe tsaye ya na cewa “to in ka na son ci gaba da zama a ciki,ka fidda Abakar a ranka ko sunansa kar na sake jin ka ambata” har ya kai bakin ƙofa kuma sai ya juyo muna kallon juna kafin ya ci gaba da cewa “zuwa an jima sabuwar mahaifiyar ka za ta tare ban son jin wata matsala ta fito daga gare ka” ya na gama faɗa ya fice.


Tsakanin baƙin cikin sharaɗin da ya gindiya mini da kuma kishin Ammyna da nake yi jin zai kawo wata mace matsayin mata sai na rasa da wanne zan ji.Ɗaki na koma na kunna karatun Alkur'ani ina saurare,a haka bacci ya ɗauke sai wuraren sallar zuhur na farka.Na yi wanka haɗi da alwala na saka jallabiya na wuce masjid da ke nan cikin gidanmu,ni na ja su sallah bayan mu gama na zauna nan na ci gaba da lazumi ban fito ba sai bayan sallar Asar.




“Babana yau mi za a girka ma na buɗa baki?” Granny ta tambaye ni,mahaifiyar Daddy ce a nan gidanmu take zaune tun kafin ma a naɗa shi komanda sojoji.Muna gane wa juna ni da ita don ni ɗaya ne kaɗai jikanta,kaf ƴaƴanta kuma tun su na jarirai suke mutuwa Daddy kawai ya tsaya.


“Tsohuwa mai ran ƙarfe ina kika shige duk yau ban gan ki ba” na faɗa tare da nufar ta ina ta ƙoƙarin ƙaƙalo murmushi.
“Ina ɗakina,ai ba ka neme ni ba tun jiya ƙafar nan ta matsa min da ciwo” ta faɗa ta na nuna min ƙafar wacce ta ɗan kumbura.
Kan capet na zauna na soma matsa mata ƙafar,cikin sigar zolaya na ce “ko sai an yanke ƙafar nan dai?” ta dungure min kai ta na mai cewa “ka ji min shashanci in an cire gobe da mi zan tarben amaryar ka?”
Fuska na kwaɓe ina mai kallonta,ta sakar min murmushi ta ce “Ammyn ka ta kira ni ai ,t sanar da ni yadda kuka yi da ita.Ka na ji Babana ita wani sa'in rayuwa ita ke tsara mana yadda za mu yi,ba kowanne lokaci ba

7 / 13