Author : Rabi'atu Bashir Abdullahi Category : True Life Story
bazata maganar tazo masa don haka ya fara had'a gumi yana kaicon halinsa nason zuciya da cutar k'anwarsa mafi soyuwa a rayuwarsa.
Ni kuwa Ummu Maher Na ce so ko cuta.😏☹️
Da k'er ya had'e miyau d'in bakinsa wajen fara magana," Safiyya kinsan halina kinsan abinda zan Aikata wallahi ba nine na yi mata fyed'e ba,nima na yi mamakin irin sharrin da Umma ta yimin don dama matar bata kwanta min ba,tana da shishshigi sosai shiyyasa ban fiya shiga harkarta ba shiyyasa yanzu ta tsaneni tazomin da wannan zancen,Amman zanje har gida in San ta yadda zan Fara magana dasu Baba da Mama.
"Amman kafin nan inason yin magana da Jamila....."
"Wat wallahi baka isa kayi magana da Jamila ba su San yadda zasuyi wajen k'ara yi maka sharri to wallahi baza kaje ba,kuma tunda abin yazo da haka dole ne musan abinyi.
Deen da aikin asiri ya ke Kansa har yanzu don duk abinda Madam Safiyya ta tsara agidan shi a ke yi don har mutane sun fara gane yadda Deen ya zama mijin tace.
Dole yanzu Jamila tana shirya wani abin domin kuwa ni nasan ba zata zauna ta yi shiru haka ba,dole ta sanar da wannan maganar Amman nasan koda zatayi maganar to ba ayau ba sai zuwa gobe mu kuma a Daren nan zamu aikata duk wani shirinmu.
Sulolo Deen ya yi kamar wani wawa yana kallon Safiyya Jan hannunsa ta yi suka shiga d'aki.
Da k'er Umma ta shawo kan Jamila don ma Allah ya tai makesu da suka dawo Mama bata nan ta bada sak'o a gaya musu cewa taje dubiyar y'ar yayarta da ta haihu a kayi mata operation.
Baccin wahala ne ya yi awan gaba da ita Umma da Fatima suna kallon ta suna tausayawa rayuwarta don sun San Halin Jamila ba zata tab'a k'arya ba,Fatima CE ta k'ara shaidawa Ummanta cewar tabbas Deen d'in ya aikata haka duba da irin abubuwan da ya ringa yi mata tun kafin yayi Aure da yadda Auren ya koma kan Safiyya.
Sai dare sannan na tashi da wani irin mummunan mafarki wai wasu mutane suna bina.
Da alama mutanen Gidan sun da d'e da bacci abin mamaki koda na duba a gogo k'arfe 9 na dare ba wani dare ne yayi sosai ba.
Farlo na fito na zaunq har yanzu zuciyata babu dad'i Allah² na ke safiya ta yi don koma menene masu iya magana sunce ranar wanka ba'a b'oyen cibi.
Ruwa na gani kan fridge mai sanyi da alama kuma wanine ya d'auko bai samu damar sha ba har ya yi bacci,don haka na d'auko na kafa kai a gorar ruwan sai da na shanye ruwan tas sannan na ji wani irin jiri yana d'iba ta ban Ankara ba sai da naji na fad'i saman kujerar da ke farlon.
Deen da Safiyya suna d'auko Jamila suka fara tafiya akan titi suna sharara gudo,yadda Deen yasan gari shiyyasa kwata kwata baibi titi ba sai da sukayi nisa sosai,Y'an sanda kuwa masu patrol suka tsayar dasu don bin cike...
*MISS GREEN ce✍🏼*
_*🍇JÂMÊÊLÊR*_🍇
*💖NA*
_Ummu Maher(Miss green💚🌱_
*MATAR BASH💡*
Follow me on wattpad
*Rabiatu333*
14🟨15
.......A matuk'ar tsorace Deen da Safiyya suka kalli junansu ganin y'an sanda sunyi cirko cirko agabansu hanjin cikinsu ya kad'a,lokaci d'aya Wata irin zufa mai zafi ya fara karyowa ko wannensu,lokacin da y'an sandan suka lek'o su biyu ko wanne daga jikin windows d'in suna k'are musu kallo tare da nazartarsu.
Daga cen d'aya b'angaren wani d'an sanda Ya ce.
"Sir"
Da sauri suka juya suna kallonshi don jin me zaice.
"Sir ga wani mun kamashi da hudar iblis da daddaren yana Neman tsere da su" ya fad'i hakan yana numfashi don da alama ya sha wuya sannan ya kamasa,kuma da alama yaron d'an masu kud'i ne.
To fa ganin Y'an sandannan sun tafi wajen wancen me laifin sai kuwa su Deen da Safiyya suka saki murmushi tare da juya motar zuwa wata hanyar.
Sunyi tafiya me Nisan gaske a wannan Daren,ko tsoro ba sa ji kodon zuciyarsu ta k'ek'ashe ne oho?
Wani tafkeken ruwa naga sun nufa da alama ruwan ruwan me matuk'ar girma ne,don haka Deen ya fito Shida Safiyya suka d'auko Jamila a hankali har suka k'ara sa wannan tafkeken kogin suka jefar da ita saida suka wuwulata har sau uku yadda zata shiga ruwan sosai sannan suka cillata.
Da sauri suka shiga cikin motar suka bar wajen cikin sauri don kada wani ya kamasu.
Mlm Bashir ne a gefen babban wani ruwa yana aikinsu irin na Malamai Amman fa ba na tsibbo ba,wata baiwar Allah zai had'awa maganin Haihuwa,kuma da wata itaciya za'ayi aikin acikin ruwan take.
Koda yaga ba zai samu daga bakin ruwan ba kawai sai ya saka kayan ruwansa da ya ke sakawa aduk lokacin da zai yi irin wannan aikin.
Dube_dube ya ke acikin ruwan har Allah yasa ya sameta,sai dai me?Mutum ya ji yana tab'awa dai dai jikin Y'ar bishiyar da ke cikin ruwan.
Ya tsorata sosai Amman da yake a shirye yake,don Mlm Bashir baya wasa da addu'ah,don haka ya fara janyota har Allah yasa ya fito daga cikin ruwan.
Masha Allah!abinda Mlm Bashir kenan ya fad'a ganin kyakyawan budurwa,sai da ya kalli k'afafunta ne yaga jini na zuba sosai kodon da tana cikin ruwa ne oho?.
Da sauri ya saka ta acikin motarsa sannan yayi hanyar babban asibiti da ke jihar Bauchi,Suna shiga likitoci suka karb'eta hannu bibbiyu don sun San Mlm Bashir mutum ne Babba Wanda ajihar gaba kid'aya ake ji dashi don Mlm ne Wanda yasan takan magani kaka_kala.
Sai da aka samu kamar 1hr sannan suka fito mode d'insu gaba kud'aya ya canza.
Sun shaidawa Mlm MATAR tana da ciki,harma tayi b'ari sai dai har yanzu bata San inda kanta ya ke ba.
Dai dai nan Jamila ta fashe da wani irin kuka tana kallon namesake d'inta sannan ta ce in tak'aice miki sai da nayi kwana d'ai_d'ai har bakwai sannan nasan inda kaina ya ke.
Bayan na warke tsaf bisa kulawar likitoci da Matan Mlm don Mlm ya basu duka labarin abinda ya faru.
To tun daga nan na koma Gidan Mlm da zama,in tak'aice miki Jamila sai da nayi wata 1 agidan Mlm sannan na fara sakin jikina,don suna bani kulawa Sosai,don Amaryar Mlm macece mai matuk'ar kirki da Jan mutane ajiki.
"Kuma Jamila kin k'ara jin maganar gida kuwa?".
"Hmm".
"Tunda ganan ban k'ara jin labarin gidaba,sai dai har y'an gida ba,Amman ina matuk'ar jin tausayin halinda Masoyana zasu shiga musammam Mama,Baba,Fatima,da Ummanta".
Kuka sosai Jamila ta fashe da shi,Namesake d'inta na rarrashinta.
" Hmm Jamila kin gama naki labarin saura labarina domin idan kikaji nawa naki ba komai bane".
To sai Ku biyoni don jin labarin Jamila 2 itama.
*Miss green ce*
*_JÂMÊÊLÊR_*
Na💖
(Ummu Maher)Miss green💚
*MATAR BASH💡*
Follow me on watt pad
*Rabiatu333*
🟨10&11
Wannan ita ce rana mafi muni Dana fuskanta arayuwa ta,ranar da bazan tab'a mantawa da ita ba domin kuwa aranar ne Yaya Deen ya yimin fyed'e a gidansa kuma a d'akin Yaya ta Safiyya,kuka ne yaci k'arfin Jamila alokacin da take bawa K'awarta Jamila labarinta.
"Kiyi hak'uri Namesake komai yayi farko yana da k'arshe tun kafin ki k'arasamin labarinki tausayinki ya k'ara ninkuwa a zuciyata,Amman Yaya Deen bai kyautawa rayuwarsa ba".
" Hmm Jamila ki tsaya kiji k'arshen labarina domin kuwa haryanzu ban kai miki inda nakeson kaiwa ba,rayuwata cike ta da abin al'ajabi da ban mamaki,rashin tausayi,cin amana,tsantar yaudara.
Fatima tayi kuka ranar kamar ranta zai fita,saboda yadda na bata labarin yadda Yaya Deen ya b'atamin rayuwa,Naso na sanar da iyaye na abinda ya faru Amman tuno abinda zai faru nayi hak'uri, na danne abinda yake cikin zuciyata,na yi jinya ta a d'aki har na warke,tun daga wannan ranar ne na shiga cikin k'unci na rame na lalace duk akan fyed'e da Yaya Deen ya yi min.
Ana cikin haka ne fa na fara wani irin zazzab'in dare kullum sai na yi shi,ga tashin zuciya na shaidawa Fatima tace muje asibiti don ganin likita,har mukaje asibitin gabana yana fad'uwa don ban San me zai faru ba,ga wani irin fad'uwar gabar da na keji kiran sunan Allah na fara yi har sakamakon gwajin ya fito.
Shingin kad'an in fad'i jin mummunan labarin da Likitan yake fad'amin wai inada k'ara min ciki,harda rubutamin scanning.
Fatima ma kuka ta ke yi,don sai yanzu take Dana sanin b'oye maganar da sukayi ita da Aminiyarta Jamila,da k'er muka dawo gida dukkanin zuciyoyinmu kamar zasu fashe tsabar tunani da fargaba,muna shigowa Gidan da Yaya Deen muka fara cin karo alokacin da ya ke bud'ewa Aunty Safiyya mota,tana d'auke da d'an k'ara min cikinta daya fara fitowa,sai wani iyayi take koda ta hango mu nida Fatima muna tahowa saita k'ara shigewa jikin Yaya Deen tana wani shagwab'a.
Kallonsu nayi cikin wata kwalla da ta fara fitowa daga idanuwa na tausayin kaina,don na lura Yaya Deen ko tunanin abinda ya yimin ba yayi,ya yi k'ibarsa ya sake wani irin fari kamar bature ko balarabe,Fatima CE ta fara wucewa ko agaishesu ba ta yi ba,ta yi wucewarta nima hakan ne a nawa b'angaren don ko kallo basu isheniba,inajin Aunty Safiyya tana tsaki tare da zagina,ni kuwa ko juyowa ban yiba nabi bayan Fatima,don jin kaina na ke yi yana juyawa tsabar damuwa,ina shiga d'akinmu na mak'ale jikin bango sai sannan wasu zafafan hawaye suka zubomin,sai asannan Fatima ta shigo tare da Mamanta.
Gaba nane ya k'ara bugawa lokacin da na ji Maman Fatima tana yimin magana kamar haka.
"Yanzu Jamila meye amfanin b'oye wannan maganar da ki ka yi,ni banga abin buyewa acikin wannan maganar ba,yanzu wa gari ya waya da kin fad'amin idanma ba zaki iya gayawa Mamanki ba ai da sai ki gayamin in gaya mata".
Tunda ta fara yimin magana kuka kawai na ke yi don jin maganarta ta na ke yi kamar wata ta tsuniya don abinda ya faru ya Riga da ya faru don babu amfanin sake mai_mai ta ta.
" yanzu lokaci ya k'ure na gayawa iyayenki,Amman babu Wanda zai fitar dake sai Allah,sai Shamsudden don koma menene shine ya janyo miki shi,don haka dole ne yanzu ya Sani ba sai an b'ata lokaci ba kamar yadda ku kayi daga farko.
Haka kuwa a kayi Maman Fatima ta nemi alfarma wajen fad'awa Mamana CE wa zamu rakata unguwa, mama ta yi mana a dawo lfy.
Fatima ce ta kirawo mana shi don ta tambaye shi ko yana gida ne,ya ce eh yana gida yanzu ya dawo daga kai Safiyya asibiti,Fatima ta ce mai to gasunan Amman da zai yiyu ya zauna a babban falonsa na bak'i ummanta CE ta ke son yi mai magana akan maganar abokinshi da ya ke son shi,nan da nan ya bada ammuna yana mai sake godewa Allah daba maganar da ya yi tunani ba ce don haka ya tashi ya kashewa Safiyya Ac ba ki d'aya sannan ya fita,yana Fita Safiyya ta fito cikin sand'a_sand'a ta bishi haka kawai taji bata yadda da wannan maganar ba don ta gane da Mmn fatima ya ke waya.
Ummu Maher ce
_*🍇JÀMÈÈLÈR*_🍇
*💖NA*
_Ummu Maher(miss green💚🌱_
*MATAR BASH💡*
Follow me on wattpad
*Rabiatu333*
12🟨13
Sosai Umma ta yi nisa a maganar ta, tunkafin Ta k'arasa maganar da ta ke yi Yaya Deen Ya yi saurin ta shi tsaye yana muzurai k'asan zuciyarsa kuma tausayin Jamila ya ke ji Amman bazai iya zuba idanu yana ji yana gani ba mutuncinsa ya zube don haka cikin kakkausar Murya ya ce.
"Gaskiya ni bansan da wannan maganar ba don ni rabona da ita tun kafin bikinmu da Safiyya,Amman na yi mamakin jin wannan zancen don Jamila ta zubarwa da su Abba mutunci......
K'arya ka ke Yaya Deen,suka jiyo muryar Jamila tana faman kuka kamar iyayenta sun mutu,Wallahi tallahi Kaine kayi min ciki domin ban tab'a aikata b'arna ba Kaine kayi min fyed'e a ranar da nazo Gidan nan Mama ta aikoni kawowa Matarka sak'o."
Da k'er ta kai maganar tana numfarfashi,da sauri Umma ta rik'eta tana gaya mata maganganu masu kwantar da hankali,Fatima ma tana taya ta da sauri Umma ta ruk'o hannun Jamila suka fito daga gidan.
Da sauri Yaya Deen ya fito daga main farlonsa duk ya had'a gumi kana ganinsa kaga Mara gaskiya.
Safiyya da ke lab'e ta ji komai don haka ta share hawayen da suka zubo mata tana sauri don ta koma d'akinta,Muryar Deen ta ji a bayan ta yana kiranta,Cak ta tsaya awajen harya k'araso ya juyo da ita yana fuskantar ta.
"Yaya Deen da gaske ne Kaine ka yiwa Jamila ciki?".
A bazata maganar tazo masa don haka ya fara had'a gumi yana kaicon halinsa nason zuciya da cutar k'anwarsa mafi soyuwa a rayuwarsa.
Ni kuwa Ummu Maher Na ce so ko cuta.😏☹️
Da k'er ya had'e miyau d'in bakinsa wajen fara magana," Safiyya kinsan halina kinsan abinda zan Aikata wallahi ba nine na yi mata fyed'e ba,nima na yi mamakin irin sharrin da Umma ta yimin don dama matar bata kwanta min ba,tana da shishshigi sosai shiyyasa ban fiya shiga harkarta ba shiyyasa yanzu ta tsaneni tazomin da wannan zancen,Amman zanje har gida in San ta yadda zan Fara magana dasu Baba da Mama.
"Amman kafin nan inason yin magana da Jamila....."
"Wat wallahi baka isa kayi magana da Jamila ba su San yadda zasuyi wajen k'ara yi maka sharri to wallahi baza kaje ba,kuma tunda abin yazo da haka dole ne musan abinyi.
Deen da aikin asiri ya ke Kansa har yanzu don duk abinda Madam Safiyya ta tsara agidan shi a ke yi don har mutane sun fara gane yadda Deen ya zama mijin tace.
Dole yanzu Jamila tana shirya wani abin domin kuwa ni nasan ba zata zauna ta yi shiru haka ba,dole ta sanar da wannan maganar Amman nasan koda zatayi maganar to ba ayau ba sai zuwa gobe mu kuma a Daren nan zamu aikata duk wani shirinmu.
Sulolo Deen ya yi kamar wani wawa yana kallon Safiyya Jan hannunsa ta yi suka shiga d'aki.
Da k'er Umma ta shawo kan Jamila don ma Allah ya tai makesu da suka dawo Mama bata nan ta bada sak'o a gaya musu cewa taje dubiyar y'ar yayarta da ta haihu a kayi mata operation.
Baccin wahala ne ya yi awan gaba da ita Umma da Fatima suna kallon ta suna tausayawa rayuwarta don sun San Halin Jamila ba zata tab'a k'arya ba,Fatima CE ta k'ara shaidawa Ummanta cewar tabbas Deen d'in ya aikata haka duba da irin abubuwan da ya ringa yi mata tun kafin yayi Aure da yadda Auren ya koma kan Safiyya.
Sai dare sannan na tashi da wani irin mummunan mafarki wai wasu mutane suna bina.
Da alama mutanen Gidan sun da d'e da bacci abin mamaki koda na duba a gogo k'arfe 9 na dare ba wani dare ne yayi sosai ba.
Farlo na fito na zaunq har yanzu zuciyata babu dad'i Allah² na ke safiya ta yi don koma menene masu iya magana sunce ranar wanka ba'a b'oyen cibi.
Ruwa na gani kan fridge mai sanyi da alama kuma wanine ya d'auko bai samu damar sha ba har ya yi bacci,don haka na d'auko na kafa kai a gorar ruwan sai da na shanye ruwan tas sannan na ji wani irin jiri yana d'iba ta ban Ankara ba sai da naji na fad'i saman kujerar da ke farlon.
Deen da Safiyya suna d'auko Jamila suka fara tafiya akan titi suna sharara gudo,yadda Deen yasan gari shiyyasa kwata kwata baibi titi ba sai da sukayi nisa sosai,Y'an sanda kuwa masu patrol suka tsayar dasu don bin cike...
*MISS GREEN ce✍🏼*
_*🍇JÂMÊÊLÊR*_🍇
*💖NA*
_Ummu Maher(Miss green💚🌱_
*MATAR BASH💡*
Follow me on wattpad
*Rabiatu333*
14🟨15
.......A matuk'ar tsorace Deen da Safiyya suka kalli junansu ganin y'an sanda sunyi cirko cirko agabansu hanjin cikinsu ya kad'a,lokaci d'aya Wata irin zufa mai zafi ya fara karyowa ko wannensu,lokacin da y'an sandan suka lek'o su biyu ko wanne daga jikin windows d'in suna k'are musu kallo tare da nazartarsu.
Daga cen d'aya b'angaren wani d'an sanda Ya ce.
"Sir"
Da sauri suka juya suna kallonshi don jin me zaice.
"Sir ga wani mun kamashi da hudar iblis da daddaren yana Neman tsere da su" ya fad'i hakan yana numfashi don da alama ya sha wuya sannan ya kamasa,kuma da alama yaron d'an masu kud'i ne.
To fa ganin Y'an sandannan sun tafi wajen wancen me laifin sai kuwa su Deen da Safiyya suka saki murmushi tare da juya motar zuwa wata hanyar.
Sunyi tafiya me Nisan gaske a wannan Daren,ko tsoro ba sa ji kodon zuciyarsu ta k'ek'ashe ne oho?
Wani tafkeken ruwa naga sun nufa da alama ruwan ruwan me matuk'ar girma ne,don haka Deen ya fito Shida Safiyya suka d'auko Jamila a hankali har suka k'ara sa wannan tafkeken kogin suka jefar da ita saida suka wuwulata har sau uku yadda zata shiga ruwan sosai sannan suka cillata.
Da sauri suka shiga cikin motar suka bar wajen cikin sauri don kada wani ya kamasu.
Mlm Bashir ne a gefen babban wani ruwa yana aikinsu irin na Malamai Amman fa ba na tsibbo ba,wata baiwar Allah zai had'awa maganin Haihuwa,kuma da wata itaciya za'ayi aikin acikin ruwan take.
Koda yaga ba zai samu daga bakin ruwan ba kawai sai ya saka kayan ruwansa da ya ke sakawa aduk lokacin da zai yi irin wannan aikin.
Dube_dube ya ke acikin ruwan har Allah yasa ya sameta,sai dai me?Mutum ya ji yana tab'awa dai dai jikin Y'ar bishiyar da ke cikin ruwan.
Ya tsorata sosai Amman da yake a shirye yake,don Mlm Bashir baya wasa da addu'ah,don haka ya fara janyota har Allah yasa ya fito daga cikin ruwan.
Masha Allah!abinda Mlm Bashir kenan ya fad'a ganin kyakyawan budurwa,sai da ya kalli k'afafunta ne yaga jini na zuba sosai kodon da tana cikin ruwa ne oho?.
Da sauri ya saka ta acikin motarsa sannan yayi hanyar babban asibiti da ke jihar Bauchi,Suna shiga likitoci suka karb'eta hannu bibbiyu don sun San Mlm Bashir mutum ne Babba Wanda ajihar gaba kid'aya ake ji dashi don Mlm ne Wanda yasan takan magani kaka_kala.
Sai da aka samu kamar 1hr sannan suka fito mode d'insu