Author : Autar Manya Category : Romantic Hausa Novels
shi riƙe da Tabar sigari Yana zuƙa ya haɗa ƙaramin Hadari acikin Falon Kunnen shi maƙale da waya wadda yake sauraran Muryar Zainab Budurwar shi wadda aka sanya musu ranar aure nan da wata Biyu masu zuwa.
Dawowar shi kenan daga wajan training ɗin koyar da dabarun yaƙin da suke wa ƙananun sojoji, waɗanda za'a tura Rinduna Shida kwantar da tarzoma a wani ƙauye dake zamfara Wanda har dashi acikin posting ɗin wanda shine ya kasance mai jagorancin rindunar farko kasance warshi ƙwararran captain ɗin soja wanda yasan ta kan dabarun yaƙi sosai.
"Baby yau she zaka shigo Kano ya kamata ka shigo wannan satin Momy nata tambayar ka sabida shirye shiryen auren mu"
Muryar Zee cikin iyayi take masa maganar.
Ya lumshe idanun shi cikin tsananin son da yake mata shima ji yake kamar yayi tsuntsu ya ganshi a kano don ya ganta yau kimanin watanni Biyar kenan baije Kano ba sai dai suyi waya da ƴan gida dakuma Zee ɗin shi.
"Nima ina ishir war son ganin ki My zee matsalar kawai yanayin aikin namu ne, amman idan kika yi haƙuri Very soon zamu kasance tare"
Ya faɗi maganar cikin dakakkiyar Muryar shi ta jaruman maza.
Kuka ta soma yi masa tana buga ƙafarta a ƙasa cikin yanayin shagwaɓarta dake ƙara narkar dashi cikin tafkin Kogin sonta.
"Ni yanzu kenan bazan ƙara ganin kaba sai kazo Biki fisabilillahi ka min adalci kenan? zuciyata da gangar Jikina son ganin ka suke amman kai ka zaɓi Ka nesanta kanka dani?"
Ta faɗa tana turo baki gaba tana zubar da hawayen Missing Ɗinshi.
Ya Shafa kanshi tare da aje Tabar Hannun shi bayan ya kashe ta, ya ɗauko cingam Guda ya jefa cikin bakin shi yana taunawa a hankali sautin muryar shi ke Fita wanda yake bata haƙuri.
"Kimin uziri My zainab idan kika yi haƙuri ma kwana nawa ne suka rage mu kasance tare"
Ya faɗi maganar Cikin rashin sabo da yawan magana.
Ya jima yana kwantar mata da hankali Cikin kulawa ta musamman wanda ita kuma sai faman Botsare wa take tana zuba masa Complain kala kala Daga ƙarshe ma cewa tayi Zato zo ita ta ganshi In baze zoba shi.
"What! Zainab baki da hankali ne zaki ce zaki zo wajena To mu a tarbiyar mu hakan ba daidai bane ga Yarinya Budurwa, Look zainab Kada ki ga ina lallaɓa ki kice zaki min sokon ci ranki zai ɓaci yanzu"
Ya faɗa yana kashe wayar Cikin takaici Yasan Zainab tana Masifar Son shi amman bai son son nashi ya zama hauka ba da har take Tutiyar biyoshi lagos Jiyay zuciyar shi na rawa akanta da sauri Ya kori shaiɗan tare da tashi ya Nufi ƙaramin Kicin ɗin shi ya tsiyayi Coffee a cup ya nufi Bedroom Yana kurɓa duk yadda wayarta Ke Shigowa cikin tashi wayar Bai Ɗaga ba Yama barta a falo tana ta faman Ringing laptop ya janyo tare da zama saman Sopa ya jona cajin laptop Ɗin sannan ya kuma Fita ya Koma falo lokacin wayarta Tagama Ringing Ya ɗauka baibi takanta ba ya shiga Neman Layin mahaifin shi domin su gaisa.
*************
*KANO*
Unguwar Jambulo.
Cikin ƙaton gidan mahaifin Zainab Alhaji Idiris Mai kwano Dattijon arziƙi Mutumin ƙwarai mai taimako Domin Allah Ba domin duniya ta yaba mashi ba.
Ƙaton Falo ne wanda ya sami damar lashe manyan saitunan Kujerun Royal har Guda Biyar Babbar Mace Zaune A saman One seater tana danna wayar dake Hannunta Hajiya Zahra Kenan Uwar Gida kuma amaryar Alhaji Idiris mai kwano Haifaffiyar Jahar sokoto Mahaifiya Ga Zainab Wadda Zainab Ɗin kaɗai Allah ya basu a kaf Duniya Duk yawan arziƙin su da tarin Dukiyar su Basu da wani ɗa inba zainab ba wadda suka ɗauki Son duniya suka ɗora mata.
Daga Alhaji Idi har hajja zahra mutanan sokoto ne kasuwanci ya kawo Alhaji idi kano wanda yake zaman sa anan Jambulo ya gina ƙaton gidan shi, Wanda kullum gidan baya rabo da jama'a da yake taimakawa Haka zalika matar shi Hajiya zahra bata da matsala ko kaɗan matsalarta ɗaya shine taga ƴarta Zainab Cikin damuwa.
Zainab Itama bata da wulaƙanta Mutane tana da kirki matiƙa haka in kaga tana wasa da masu aikin su sai ka rantse Ba ƴar gidan bace gaba ɗaya karatunta Na likitanci tayi shine a ƙasar Indiya yanzu haka tana a matsayin Cikakkiyar likitar mata a asibitin Malam Aminu Kano Zainab tana da Mugun kuɗi in ka cire na mahaifanta itama kanta mai kuɗin kanta ce.
Zainab bata da wata damuwa Ko Matsala a rayuwarta sama da Aikin ta Na asibiti da take dan tana masifar son aikinta , Sai kuma Ahmad wanda ta ɗauki son duniya ta ɗora mishi tana mai wani irin maitar So wanda ji take kamar ta lashe shi ta mayar dashi Cikinta,In kaga zainab tai kuka akan Ahmad ne in kaga Zainab tai dariya akan Ahmad Ne tana Masifar son shi tana mugun jin tsoron shi bata da dama akan Ahmad, Zainab tana da ƙawaye sosai ƴaƴan manya kasancewarta Mace mai son jama'a da kwashe kwashen ƙawaye Shiyasa bata rabo da su ko gida ko Office matsalar Zainab ɗaya ce tana da mugun Zargi Daidai da ruwa ka bata in bata yarda dakai ba bata sha mace ce mai zargin gaske sai dai Duk zargin nata akwai ta da saurin ɗaukar shawarar ƙawaye kasancewarta Ita kaɗai a gidan su bata da abokin shawara sai Hajiya Babarta wadda take masifar son ƴar tata tamkar tsoka ɗaya a miya, Da wuya kaga Zainab taiwa Hajiya laifi sabida bama cika zaman gidan tayi ba sai week end.
Ita ma Hajiyar da wuya kaga taiwa Zainab faɗa sai dai in tai abun da baya cikin tsari wannan tana ƙoƙarin kai son nesa tai mata faɗa amman ba sosai ba.
Cikin sauri Zainab ta fito daga Cikin ƙayataccen ɗakinta harta tana Tuntuɓe Ta nufi wajan Hajiya mahaifiyarta Jikin zainab sanye ike da riga iya gwiwa da dogon wando kanta babu ɗankwali Doguwa ce fara siririya mai far'a da Sakin Fuska.
A jikin Hajiya ta zauna tana Tura bakinta gaba kamar wata ƙaramar yarinya Duk da Zainab ba yarinyar Bace don zata kai shekaru talatin da Biyu aduniya ( 32 ) amman tsabar Hutu da gogewa ya hana a gane yawan shekarunta.
"Yaya akai Abuwata?"
Da yake sunan da Hajiya ke kiranta dashi kenan.
"Hajiya Ahmad Ne ina ta kiran shi bai ɗauka ba Kodai yana tare da wata Ne?"
Da sauri Hajiya ta ƙwaɓe mata baki tare da cewa.
"Kull kada na kuma ji kina zargin Mijin da zaki aura, Dan Allah Abu ki dinga rage kishin nan da zargi kina son ɓata imanin ki babu fa mai yi sai Allah babu kuma mai hanawa sai Allah"
Kuka Zainab tasa.
"Amman Hajiya danna ce masa zanje nai week end wajan sa zai hauni da masifa dan yaga ina son shi"
Salati Hajiya ta soma tana tafa Hannu
"Ah dole ya hau masifa yace miki Kin haukace ai a garinku na Shasha shai aka ce ana zuwa wajan wanda ba'a aura ba a kwana ko? tashi ki bani waje wadda bata da girma sai na jikinta"
Zainab ta Rumgume Hajiya tana cewa.
"Hajiyata ban da fushi mana Allah ya Huci Zuciyarki"
Hajiya tace.
"Na kasa gane kanki akan yaron na dan Allah ki dinga kama kanki Ina gudar Miki wulaƙancin Ɗa Namiji idan ya gane mace ce tafi damuwa dashi akan shi"
Kuka Zainab tasa tana Birgima a ƙasa wai Hajiya tai mata Baki Ahmad ya wulaƙantata.......
*Unguwar Ɗan bare gidan*
Amatullahi...........
Auta 09022260850.
*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*
BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*004*
A hankali sautin ƙarar shigowar Motar shi cikin gidan ke kaɗa mata hanjin Cikinta, Daga cikin Ƙirjinta Kuwa dokawa yake da ƙarfi wanda In mutum yana kusa da ita tsaf zai ji sautin dokawar da Ƙirjin nata yake.
Tun Bayan fitar Ameerah daga gidan take zaune a falo ita ɗaya gaba ɗaya tsoron dawowar Imran gidan take wanda hakan ya zame mata al'adar Rayuwarta Koda yaushe In ya fita Tana cikin Raha da Nishaɗi amman da zarar Ya dawo to duk wani Ɓurɓushin Farin cikinta Gushe wa yake yi.
Tsayin watanni tara kenan da auran su da Imran amman har zuwa wannan lokaci ta Kasa samun farin ciki kamar ko wace mace acikin gidan Mijinta.
Curewa take a waje ɗaya tana haɗe jikinta tamkar mai jin sanyi, A hankali Taji sautin shigowar sa cikin Falon bada ban tayi da gaske bama da bazata ji sallamar tashi ba.
"Sannu da dawowa"
Ta faɗa masa kanta yana ƙasa.
Yayi mata banza kamar bada shi take magana ba.
"Amatullah"!
Ya kira sunanta a dake.
Ta ɗago tare da zuba masa Manyan Idanunta tana kallon shi kafin daga bisani tace masa.
"Na'am Yallaɓai"
Ya ɗan gyara tsaiwar shi yana soke Hannun shi a cikin aljihun wandon shi.
"Taso Muje gidan ku anwa baba aikin Idanu daga nan muje shoping"
Ya faɗi hakan yana wucewa ɗaki Minti biyar ya fito sanye da wasu kayan na daban.
Ta miƙe tana Ƙoƙarin gyara Hijabin Jikinta.
"A,a Je maza ki shafa Powder sannan ki ɗan saka wannan maiƙon naku na leɓe"
Sosai Abin ya bata mamaki amman sai ta wuce taje tayi yadda yace Ɗin daga bisani ta dawo Har ya wuce waje abin mamaki ba wannan Motar daya Shigar da ita gida ya Shiga ba ashe akwai wata a waje mai kyau sabuwa ya buɗe mata gidan gaba ta shiga ta zauna Yaja suka hau Titin Rijiyar Zaki inda anan layin Rumfar shehu gidan su yake.
Sai da ya tsaya a wani Store yasai kayan abinci aka shigar dasu Motar sannan ya shigo suka ja Suna tafiya ita bata ce mai ba shi bai ce mata ba har suka ƙarasa layin.
A bakin Ƙofar Gida Yay parking bata jira shiba ta ɓalle murfin ta fita wajan ƙatuwar tabarmar Su Alhaji Babba ta ƙarasa wanda Suke zaune suna shan Iska sallama tayi agaban su ta tsugunna tana gaishe dasu.
Kafin Imran ya ƙaraso shima ya tsugunna yana gaishe dasu.
Cikin Jin daɗi Alhaji Babba yace.
"Ma sha Allah! Amatullah kece da wannan Lokaci barka barka da zuwa naji daɗin Ganin ki Allah ya ƙara zaunar mana dake lafiya, Koke fa da kika kwantar da hankalin ki"
Aranta tace Alhaji ba zaku gane yaran ba, Nidai zan cigaba da haƙuri.
Amman a fili sai tace.
"Nagode Alhaji"
Nasiha sauran ƴan uwan mahaifin nata sukai mata kafin ta miƙe tabar wajan ta nufi Cikin gida.
Babban Gida mai sassa da dama acikin sa wanda ya haɗe ƴaƴa da jikoki sashin su ta shiga da sallama a bakin ta.
Umma tana zaune tana bawa Baba ayaba a bakin shi ta ɗago cikin sakin fuska take amsa wa Amatullah Sallama.
"Kece da wannan daran dafatan dai lafiya?"
Amatullah ta dubi Ummah da mamaki sannan tace.
"Tare dashi muke yace ne nazo na duba Jikin Baba"
Bata kai ma da rufe bakinta ba Umma ta miƙe tsaye tare da Nufar Ƙofar Gida da sauri Amatullah ta riƙe Hannun Ummah tana gyaɗa mata kanta.
"Ummah yanzu fa zai shigo Gidan Dan Allah ki Koma ki zauna"
Ta Doke hannun Amatullah tana cewa.
"Cikani Dan ubanki so kike Su hure masa kunne a waje ko? Su roƙe mashi Kuɗi a banza"
Amatullahi ta sunkuyar da kanta cikin takaicin Halin Ummanta batace Mata komai ba Umman na ƙoƙarin Fita Imran ɗin ya shigo.
Sosa kai Umma tayi tare da cewa.
"Lale maraba da zuwan ka Imirana daman yanzu take cewa tare kuke"
Ya zauna a saman dardumar daya gani a shinfiɗe cikin jin kunya yake cewa.
"Eh Muna tare dasu Alhaji ne muna gaisawa"
A take ilahirin annurin fuskar Umma ya ɗauke dan bata ƙaunar wani ya raɓi surukin nata bare yaci arziƙin sa.
Tana ƙoƙarin yin magana ƙannen Amatullahi Hassan da Hussaini suka soma shigo da kayan abincin daya siya a hanya Bakin Ummah kamar Gonar auduga.
Sai albarka take shiwa Imran wanda yake ta sakin murmushi mai tarin ma'anoni da yawa.
Sam Ummah bata tambayi Amatullahi yaya zaman su da Mijinta ba bare ta jata ajiki ta shigar da ita ɗaki su ɗan zanta irin na ɗa da mahaifi sai ma mayar da hankalinta kan Imran datai suna ta hira.
Ganin Haka yasa Amatullahi taja Jikinta zuwa wajan Babanta wanda yake kwance.
Ta ƙarasa wajansa ta zauna tana kallon shi shekara Kusan Biyar yana kwance ga matsalar ƙafafu da basa takawa ga matsalar Idanu damma yau an masa aikin Idon wanda aka sanya masa glass a idanun nashi ba wani tsufa yayi ba, Amman lalura ta saka girma ya hau masa da wuri.
"Sannu baba Allah ya baka lafiya"
Jin Muryar ƴar tasa, a kusa dashi yasa ya kama hannunta yana cewa.
"Amatuna kece a gidan?"
Ta ƙaƙalo murmushin dole kana tace masa.
"Baba tun Ummah na baka ayaba nai sallama baka ji bane?"
Yayi murmushi yana cewa.
"Banji ba Amatuna, Kinga mijin ki ɗan albarka ya biya min kuɗin aikin idanu yanzu Ganin ba kamar da ba"
Tayi murmushi tana cewa.
"Damma yau akai amman nan da kwana biyu ma zaka fi haka gani, Nina ɗauka ma kana asibiti Allah dai ya sawaƙe"
Baba yace.
"Ai Amatuna baki ga asibitin ba, na masu hannu da shuni ne, Daga an maka aikin kai ƴan awanni zasu sallame ka"
Amatullah tace.
"Baba Allah yasa an yi a sa'a Amin"
Baba ya kuma karkatowa ya dube ta.
"Amatuna mijin ki yaron kirki ne, Ki haƙuri ki zaman ki agidan ki, Allah ya ƙara muku zaman lafiya"
Gabanta ya faɗi Imran ya siye baba kenan da idan tazo gida da maganar zaman auren ta baba yana ƙoƙarin fahimtarta to shima yau Ga shi nan yana yabon Imran fiye da zaton ta.
Hawaye masu zafi suka Zubo mata a saman Kuncin ta bata bar kowa ya gani ba ta share su, Ta sunkuyar da kanta Baba ya cigaba da yi mata Nasiha mai ratsa Jiki.
Har wajan taran dare suna Gidan Kafin ta miƙe tace wa Ummah zata Leƙa sashin Matan Kawun nan ta su gaisa.
Ta Dubi Nana ƙanwarta wadda Daman su biyu ne mata ita da Nana sai Ƴan Biyu maza dake binta, Nana take bi musu, Tace mata tazo ta rakata Ɓarin su Ameerah su gaisa da sauran sashin Nana ta Tura baki tana cewa.
"Ni bana shiga sai kin dawo"
Ga Mamakin Amatullah Ummah batai wa Nana magana ba, Sai ma kuma jan hirar da tayi da Imran kamar ba surukinta ba.
Amatullah ta yi waje tana Jinjina halin ummanta na son abin duniya wanda shine jagora ga halin Ummah na farko.
Sashin Su Ameerah ta soma zuwa sukai gaisa da Anty babar su Ameerah sama sama.
Ta fito Ameerah ce ta rakata Sauran sassan ƙannan mahaifinta Guda Huɗu, Sannan suka Nufi sashin Su Yaya Ahmad wanda shine na farko ma daga ka shiga Gidan.
Mamaki sosai Amatullahi tayi yadda taga an ƙere sashin kamar ba'a cikin Gidanba ga hasken ƙwan sola kota Ina bata sha mamaki ba sai da ta shiga falon Mama wanda yaci uban saitin Kujeru masu kyau ga ƙatuwar Tv sai faman aiki take Iskar fanka kota ina.
Sallama sukai Ƙannen shi ƴammata Su Biyu Waɗanda basuyi aure ba suka amsa musu cikin sakin fuska Zama sukai a ɗaya daga cikin kujerun Sannan Surayyah autar su ta nufi Bedroom ta gayawa Mama.
Minti kaɗan Mama ta fito Cikin wata dakakkiyar shadda tana tafe tana taƙama.
A ran Amatullah tace ashe har yau Izzar tana nan.
Ba yabo babu fallasa suka gaisa sannan suka baro sashin wanda Naja'atu ƙanwar shi wadda suke sa'anni ta rakosu hanya.
Anan suka haɗu da Ƙanin Ahmad Kamal suka gaisa yana ƙoƙarin Shiga ɗakin shi.
Sai da su Ameerah da Naja suka rakata har bakin sashin su, sannan suka koma Ɓangarorin su.
Koda ta koma ma Imran har ya miƙe suna sallama da Ummah wanda ya ɗauko damin Kuɗi ya bata ta saka hannu ta amsa Jikinta har yana Ɓari Takaici Baƙin ciki sune suka wa Amatullah ca a zuciyarta.
Haka suka Nufi Mota yaja suka tafi ya biya Ta wani super market yayi mata uwar siyayyah.
Sannan suka wuce Gida.
Wanka tayi bayan ta shigar da siyayyar tata.
Kana ta koma Ɗakinta ta saka kayan bacci ta kwanta bayan ta kashe ƙwai.
A hankali Imran ya shigo ɗakin Jikinsa sanye da Guntun wando da singlet ya raɓa Jikinta ya kwanta aran shi yana ayyana tabbas Yau Burin sa zai cika Tabbas sai ya fitar da maitar shi ta san Neman ta tabayan ta.
A hankali ya haɗe jikinsa da nata yana shafo mazaunanta ta baya yana fitar da wani Irin nishi.
Cikin Baccin daya kwasheta taji yana shafa mata jikinta.
Tsoro fargaba tashin hankali sune suka dirar mata a zuciyarta mai Imran yake Nufi tsayin wata tara tana rayuwar gidan shi bai taɓa kusantarta ba sai sau ɗaya Tun daran farkon su, Kullum burin shi ya nemeta ta bayanta Allah bai bashi Iko ba shine yau ya ritsa ta a wannan daran zai ƙara far mata Innalillahi wa'innah ilaihirraju'un rana zafi Inuwa Ƙuna ta faɗa a ranta kafin da sauri kuma ta Miƙe zaune........
*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake