BAKON LAMARI HAUSA READ NOVELS By HASEENATU.txt

Author :  Autar Manya Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   6 / 11

15K to 18K   out of 30.4K words

daga gani yana cikin kwanciyar hankali Anty dan Allah ki ƙara min ƙoƙari akan shi Anty tunda na tashi da soyayyar yaya na taso a rayuwata kina kallo bana kula kowani namiji sabida shi dan Allah kiwa Baffa magana akan shi koze sami Alhaji da maganar mu"
Ta ƙarasa maganar tana jan Numfashi mai ƙarfi.

Tsananin tausayin yarinyar ne ya kama Anty Ameerah ƴarta ce ta fari wadda tafi soyuwa fiye da dukkan ƴaƴanta acikin zuciyarta dan haka dole ta Bawa ƴarta abinda take so koda zata rasa komai nata ne a rayuwa.
"Ki ƙaran haƙuri Ami, munyi magana da uwarsa ki bari muga auran nashi daga nan sai muga gudun ruwan su, Babanki kuma kinsan baze magana ba kinsan haƙurin su yayi yawa dukkan su sanyi gare su dan haka kada ki damu nai miki alƙawari Ahmad Sai ya aure ki koda tsiya koda tsiya tsiya! dan na fahimci kamar da rainin hankali a wajan uwarsa kawai ta faɗan hakanne dan tasa hankalina ya kwanta, Shima kuma Ahmad bawai Ganin girma na yake ba Dan na fahimci Duk sanda zaizo Ko kallon sashin nan bayay bare yazo ya gaishe ni sai dai ya tari Baffan sa a waje su gaisa Duk yadda nake wa uwarsa baya gani Inma ya ganni a wajan uwarsa haɗe rai yake yayta janta da hira su barni zaune ni kaɗai"

Ameerah ta lumshe idanu tare da cewa.
"To Anty kawai idan tai niyya tasa ya haɗe mu rana ɗaya mana?"
Anty tace.
"Barni da Hajiya Binta, dani take maganar ta ɗauka yadda nake mata a fuska har zuciyata haka yake? to sai da na laluba nagano zamu kwashi dukiya wajan ɗanta sannan nai mata kwanton ɓauna na shiga Jikinta Burina Ahmad ya aureki koda baki ce kina son shiba dama da niyyar na haɗaku bare da bakinki kince kina son sa sabida haka ki kwantar da hankalinki Ahmad Mijin kine Uban ƴaƴanki ki aure shi ki hayayyafa Komai nasa ya dawo namu Hatta uwar tasa ma sai yadda kika ce zai mata Sabida a rayuwa ina baƙin Cikin Mutum Biyu Hadiza da Binta sun fini komai Ita hadiza mijin ƴarta daya tsaya mata wannan abu na ƙona Mini rai Shiyasa jiya danaji labarin auren ta ya Mutu yau sai da nai sadaƙa sabida Murna ita kuma Binta Duba kiga kaf ƴaƴanta mata Uku dake ɗaki bamai auren talaka Shima Ahmad jibi yadda Allah ya ɗaukaka shi a aikin shi Lokaci ɗaya ga kuma kasuwancin sa wanda naji ashe ƙatuwar plaza ya saya ya zuba kayayyaki kuma ance kayan ma daga ƙasar waje ake shigo dasu ya damƙawa kamal a hannunsa yake kula masa da komai na ɓangaren plazar,sannan ya sami yarinyar dazai aura ƴar manyan Mutane, Binta a yanzu tafi ƙarfin Komai a rayuwa Hutu da jin daɗi kullum ƙara Huda ta yake shiyasa Sai da nai yadda nai da Gulma da Kirsa na rabasu da Hadiza don Muddin Suka haɗa kai ni tawa ta ƙare Sannan Kuma nasan yadda nai nake amshe saƙon matan gidannan Wanda take bani tace a raba musu na wajan Ahmad nake riƙewa nakuma toshe hanyar da zataji Duk dan tai baƙin jini acikin su to Alhamdulillahi wannan tarkon nawa ya kama domin kuwa yanzu duk matan gidannan haushin Binta suke ji suna ɗaukarta mace mai son kanta da izza Yanzu tarkona na gaba ki Auri ɗanta daga nan kuma ta kaɗe har ganyenta wallahi"
Zare idanu Ameerah tayi har zufa na keto mata.
"Haba Anty dan Allah ki bar yin haka wallahi babu kyau ko kaɗan Sabida bakisan ranar mutuwar kiba"

wata dariya Anty ta kwashe da ita kafin tace.
"Ke yarinya ce Ameerah baki san dawan garin ba ada can ma kafin a haifeku Mijin Binta Nada kuɗi Mijin Hadiza nada kuɗi kafin ya kwanta ciwo Ni kuma mijina baya cas bare as suke mana komai har Allah ya bashi malamin makaranta Kina kallo fa daga Alhaji sai Sha'aibu sai babanki sai sauran ƙannen shi Biyu su waɗannan bana ta tasu dan basa gabana amman waɗannan faccalolin nawa guda Biyu sun tsayan araina yadda bakya zato bafa zasu fini da Miji ba sannan suzo su fini da ƴaƴa Ina sam Ita waccan suruki ita waccan ƴaƴa musamman ma Ɗanta mai son ta mai kashe mata Kuɗi wallahi sai ma kin shiga gidan shi daga yau ki ɗau ɗammarar kota kwana"
Anty ta faɗa har idanunta na sauya kala zuwa ja.
Ameerah tabi ta da kallo sam bata fahimci me take Nufi ba akan waɗancan maganganun nata.

"Kuma sannan ba waccan matsiyaciyar ta dawo ba ki dinga janyon ita wallahi bazan ɗauka ba Ki tattara ki watsar da ita ke Budurwa ce ita bazzawara sabida haka hanyar Jirgi daban ta mota daban wallahi bana ƙaunar Amatullah ko kaɗan a duniya"
Ameerah tai saurin tashi daga wajan tayi ɗaki dan aduniya Ameerah bata son taji Anty na zagin Amatullah sabida ƙaunar da take mata Shaƙuwace tun ta yarinta zama suke na so da ƙaunar Juna ada Ko bacci baya rabasu duk da iyayen nasu mata basa shiri haka koda Amatullah tai aure Ameerah bata haura kwana biyu bata je ta ganta ba wannan shaƙuwa tasu har tai yawa basa Ɓoyewa Junansu sirrin Juna musamman ma Ameera data fi Amatullah yawan magana.
**************

Ahmad Ɗakin shi dake daidai Ƙofar Fita daga sashin su ya karɓi Key wajan Kamal ya Buɗe ya shiga ciki, Ko ina na ɗakin Need babu datti sabida gyaran da yake sha wajan su Naja dan kullum sai sun Buɗe ɗakin sun share sun Goge kayan wutar dake Ciki wannan yasa ɗakin babu datti ko tarkace.
A falon daya sha manyan kujeru masu tsananin kyau da ƙatuwar Tv da Shinfiɗaɗɗan carpet kamal ya aje masa Jakar Shikuma Ahmad ya wuce Bedroom Domin yayi wanka nan ma a gyare yake tsaf dan hatta Bedshirt An sauya shi da wani fari tas mai kyan gaske Taka Luntsumemen carpet ɗin dake Bedroom Ɗin yayi zuwa gaban gado yana shaƙar ƙamshin turaren daya kama ɗakin ya sami muhalli aciki tare da soma Cire Botiran gaban rigar kakinsa.............
*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*








*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami  ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah  ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE  muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko  uwargida  ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*

BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE  @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }

*NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

*11*

Ya ɗaura faffaɗan tawul a ƙugunsa Ya shiga Bathroom.
Ya Jima aciki yana wanka kafin ya fito Ya shirya Cikin wata Black jallabiya mai gajeran Hannu wadda aka mata aiki da Golden Ɗin zare mai layi layi Daga gaban ta Kuma a buɗe yake wanda ya bawa Gashin dake saman ƙirjinsa wanda ya tawo har ta wajan wuyan shi damar bayyana a sarari.

Turare mai daɗin ƙamshi ya fesa sannan ya ɗauki wayar shi daya aje a saman gado ya fita daga Ɗakin Gaba ɗaya ji yake ya gaji,Jin ana kiran sallar magariba yasa ya Ɗaura alwala a famfon dake Bakin Ɗakin nashi ya fice masallaci Zaman jiran Jam'i yayi har aka taru a masallacin suka yi sallar magariba sannan ya fito ya Nufi cikin Gida.

Babban falon Mama ya shiga Bakin sa ɗauke da Sallama.
Jin Shuru a falon ya tabbatar masa da duka Ƴan gidan sallah suke Domin hatta Tv an kashe ta.
A hankali yake taka ƙafarshi A saman Shinfiɗaɗɗan Carpet Ɗin daya malale Falon Har ya sami damar ƙarasawa Bakin Ƙofar Bedroom Ɗin Mama sai da ya buga ƙofar sau Uku sannan tai masa gyaran Murya.
Murɗa Handle ɗin Ƙofar yayi ya shiga Cikin Bedroom Ɗin Bakin sa ɗauke da sallama yana mai Lumshe idanunshi wani irin haɗaɗɗan Ƙamshin Turaren wuta wanda ya haɗe da Iskar Fanka na ratsa masa dukkan sassan Jikinsa.

Gyaran Murya ta kuma yi masa sabida haka sai ya nemi Gefenta ya zauna wadda take zaune a saman darduma tana lazimi da ƙaton Carbi mai Dubu a gabanta.
Zaman kusan Minti Talatin Yayi kafin ta shafa addu'ar ta Ɗago da kanta Cikin murmushi tace masa.
"Barka da dawowa Ina maka fatan nasara a cikin rayuwarka"
Ta furta hakan cike da so da ƙaunar ɗan nata cike da Ranta da zuciyarta.

Wani irin ƙayataccen Murmushi Ahmad ya saki yana shafa saman kanshi da Hannun shi cikin nagartacciyar Muryarsa mai cike da Haiba da nagarta yace.
"Mun same ku lafiya Mama? Yaya gida da yara Ina Alhaji tun da nazo ban gan shiba ko a masallaci?"

Cikin Murmushin daya ƙi gushewa a saman Fuskarta tace masa.
"Alhaji ya fita Cikin gari Gaisuwar abokin sa, Gida kuma Alhamdulillahi da kowa da Kowa muna cikin Godiyar Allah"
Daga haka taja Bakinta tayi shuru.

Shima Sunkuyar da kanshi yayi a ƙasa bai Kuma cewa komai ba sabida Rashin sabon doguwar Maganar da bata fiye shiga tsakaninsu ba sakamakon Alkunya da Mama take masa ta ɗan fari.

Ɗakin yayi tsit kamar Babu mutum aciki.
"Kaje falo akwai abincin ka"
Daga haka ta kuma shuru.

"Mama Muje tare dan Allah yaushe rabona dake ai mayi Hirar yaushe gamo"
Ya faɗa yana dariya ƙasa ƙasa.
Ɗago kanta tayi ta zabga masa harara tana mai kawar da kanta Gefe ɗaya Sanin ba zata tanka masa ba yasa ya miƙe Yana cigaba da dariyar daya keyi wadda In ba a gaban maman ba babu mai samun arziƙin Ganin dariyar tashi.

Dining area ya Nufa wanda aka jere shi da manyan Food Flask ɗin abinci kamar wanda za'ai ƴar ƙaramar walima ya Kuma shafa kanshi yana Cigaba da Murmushi yasan aikin Mama ne wannan wadda take Masa Hidimar Cikinsa duk sanda yake Gida ba dare babu rana dan baya yarda da girkin kowa sai nata.

Yayi Bisimillah ya zauna a saman Kujerar Dining Ɗin ya soma Buɗe food flask ɗin waɗan da akai girki kusan kala Uku aciki, kuma kowanne kalar Girkin daze gani daban waɗanda Duka abinci ne Irin namu na gargajiya.

Ya Ɗauki plate da Spoon ya aje a gaban shi sannan ya ɗauki Sarving Spoon ya Buɗe Flask ɗin Dambun shinkafar daya ji gyaɗa da Zogale da Albasa da wadataccen Man gyaɗa da ƙananun Hantar da aka yanka aciki ya matsar da Plate ɗin gaban flask ɗin ya saka sarving spoon yana ɗiba wani haɗaɗɗan ƙamshin Dambun na dukan Hancin sa.

Ɗan kaɗan ya zuba sabida bai da yawan cin abinci sannan ya rufe flask ɗin, ya janyo na farfesun Ƙoda da hanta da Tumbin da akai wanda Aka yanka manyan albasa acikin sa shima sai ƙamshi yake ya zuba wadatacce a saman Dambun sabida Yana da son Naman kayan ciki A rayuwar sa.
Bisimillah yayi ya ɗauki spoon ya soma Juyawa yana ɗiba Haɗe da farfesun yana kaiwa Cikin Bakin sa Daɗi Mai ma'ana yana kaiwa ƙwaƙwalwar sa Ziyara A ranshi yana addu'ar Allah yasa Zainab Ta iya Girki Domin mace wadda tasan kan ludayi itace Mace Duk macen da bata iya Girki ba sunanta Sorry Bini Bini daya ci loma ɗaya zai ɗauki Cup ya tsiyayi ruwa a Roba ya kai bakin sa har ya kammala Cin Abincin yayi Hamdala Ga Allah tare da Ɗaukar tissue ya goge bakin sa Lokacin daya tashi daga saman dinnig Ɗin wayar zainab kusan ta Biyar na shigowa bai ɗauka bane sabida ƙa'idarshi idan yana cin Abinci Baya magana har sai ya gama Kuma Bashi kaɗai ba wannan tarbiyar Duk wani Ɗan gidan Mama ne.

Bin kiran nata yayi Lokacin daya ƙarasa Saman one seater dake Falon Mama ya zauna ya ɗaura Ƙafa ɗaya kan ɗaya yana girgizawa.
"Baby ina ta kiran ka baka ɗauka ba wai baka tawo bane ba?"
Ya shafo gemun shi tare da cewa.
"Zainab sau nawa ina gaya Miki Ni musulmi ne ki soma yi min sallama kafin ki fara Min magana"
Ya faɗa Muryar shi a dake.

"Kai haƙuri Ina ɗaukin Ganin kane Tun ɗazu nasa masu aiki suka maka girki Ni kuma naje Gidan Kwalliya yanzu Haka kai nake Jira kai Min waya nazo airport Ɗin"

Tausayin tane ya tsirga masa har Ranshi Zainab na son shi Haka Shima yana son mace mai Son shi wadda zata Nuna masa tattali da kulawa.
"Ina gida yan zu haka nagama cin Girkin Mama na"
Ya faɗa a dake.
"What!! Girkin wa? banji me kace ba haba Ahmad kana Nufin duk wahalar dana sha Na kwalliya da sakawa ai maka Girki ya tashi a banza kenan?"
Ta ƙarasa maganar tana Kuka!
"To ya za'ai kinsan Ni ba korarre Bane Ina da gidan mahaifa Kano ai gida ce Ki min uziri yau na gaji Amman Gobe zan Zo"
Ya faɗa Cikin kwantar da Murya.
Kuka kawai zainab take masa na takaici da Baƙin cikin abin da yayi mata.
Gajiya yayi da Jin kukan nata dan shi bai iya rarrashin mace ba sabida haka sai ya kashe wayar tashi Baki ɗaya.
Ya kwantar da kanshi Jikin seater Yana mai rufe Idanunshi.

"Har ka gama cin abincin?"
Yaji Muryar mama wadda take zama a kujerar dake kallon shi.
Da sauri ya zame daga saman Kujerar ya zauna a ƙasa.
"Na gama mama Amman ina son Baƙin shayi asa Kamal ya miƙa Min ɗaki"
Ta Jinjina kai tana cewa.
"Daman na dafa maka mai kayan ƙamshi sai ya miƙa maka idan ya shigo"
"Nagode Mama"

Ta kuma fuskantar sa taga yadda ya nutsu a gabanta yay ƙasa da kanshi sosai.
"Amatu tana gida fa Auren ta ya Mutu, wannan abu da shi na kwana na tashi dashi da Alhaji ya gayan Jiya duka yaushe akai auren nata amman yaron nan ya sake ta ga jaririya ina ga basu yi arba'in ba! sannan Ina son kaje kaga Jikin Babanka sha'aibu yakamata ai wani abu akan wannan Jiki nasa sannan Kuma ka ƙaro Kayan abinci Wa matan kawun ka da sauran matan gidan sai Kuma Kuɗin makarantar Yaran kawunka suma naji ance an koro su Jiya"
Dama a ƙa'ida idan sukai waya da mama tana gaya masa dukkan buƙatun Gidan da kuma abin da ya faru sabida shine Babba a kaf ƴaƴan gidan, Gudun kada a ce bata gaya masa Komai. To yau kuma ganin Allah ya kawo shi yasa take gaya masa waɗancan maganganu waɗan da dama tace zata bari In yazo ta gaya masa tun sanda yace mata zaizo.

"Sannan ina son Hafsa ta dawo gida ta haihu kaga haihuwar fari ce"
Ta kuma faɗin hakan duk da yayi shuru ya ƙi cewa komai.
"A,a mama ki barta a gidan ta kawai In yaso a ɗauki mai aiki ta kula da ita"
Ya faɗa batare daya ɗago ya kalleta ba.
"To shike nan hakan za'ayi"

"Mama dama Amatu ta haihu aini ba wanda ya gaya Min, Shi Mijin nata ɗan ina ne?"
Ya jefo mata tambayar.
"Kasan yadda auren yazo ai koshi Alhaji faɗan daya gama yi Jiya kenan ai Hadiza ta cuci Yarinyar nan Wallahi sam batawa haihuwa adalci ba"
Mama ta faɗa daga gani abun yay mata ciwo a matsayin ta na uwa.
Bai ce komai ba yaja Bakin sa yay shuru yana mamakin yau wace rana mama ta zage tana magana a gabansa wadda ko a waya bata jan doguwar magana dashi koda magana ce mai mahimmanci data gaya masa take kashe wayar.
Cikin haka Alhaji ya shigo wanda suka gaisa da Ahmad sosai kuma Suka tattauna akan aikin daya kawo shi wanda yace Nan da ranar Litinin Zai tafi can barrack Ɗin da aka Tura su wanda zasu haɗa team ɗinsu su shiga ƙauyukan sai dai zai na zuwa gida week end addu'a Alhaji yayi masa sannan ya Miƙe yana Musu sallama dan ya gaji bacci ne a idanun shi sallar isha'i kawai zai yi wadda tuni akayi babu shi sai ya kwanta...........*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*



*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami  ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah  ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE  muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko  uwargida  ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar

6 / 11