BAKON LAMARI HAUSA READ NOVELS By HASEENATU.txt

Author :  Autar Manya Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   4 / 11

9K to 12K   out of 30.4K words

da baƙin ciki da munafurci a cewar ummah wannan tasa tunda Ummah taga Anty na shigewa jikin mama yasa Ummah ta dena shiga hulɗar su dan ko cikakkiyar magana Ummah bata yi musu.

Sauran matan gida kuma gulma ita kuma Ummah bata gulma barta da son abin duniyarta wannan yasa bata shiri da kowa a gidan take sabgarta ita ɗaya Ita ko Anty maman su ameerah kusan Kullum ma tana sashen mama wadda maman ta ɗauki Anty a matsayin aminiyarta akaf gidan babu wadda mama ta yarda dashi kamar Anty sabida yadda Anty take wa mama Biyayyah tare da nuna mata zahirin ƙauna.

"Kawo kayan a saka mata"
Cewar mama bayan ta shafe Jaririyar da mai Da sauri Anty ta miƙe tana bari ta je ta ɗauko kayan a ɗaki wanda Amatullah tasan ba domin Allah ta faɗi hakan ba kawai dan ta shiga taga ƙwaƙwaf ne.

Minti kaɗan ta dawo da akwatin ƴan kayan gaba ɗaya wanda mamaki ya cika Amatullah haka ta zazzage kayan waɗanda ba yawa gare su ba Matan gidan ko wacce tabi kayan da kallo banda Mama data ɗauki Riga mai kyau ta sanyi ta Sinke ƴar.

"Amatu bakya bata Nono hala?"
Da sauri Amatullah ta ɗago tana Bin mama da kallo kamar su da Ahmad har tai yawa sannan taji ta gaya mata sunan da ɗanta yake gaya mata.

Batai magana ba tai ƙasa da kanta.

"Amsheta ina zuwa"
Mamar ta faɗi.
Da kanta ta miƙe ta haɗowa Amatullah tea mai kauri nan da nan ta rufeta da faɗa tana ce mata.
"Gidan ki babu abin da zaki nema ki rasa cikin sa baza ki ci abinci ba Laifin Hadiza ne ( ummah ) tunda ita ba zata tsaya ta lura dake ba haihuwar fari ce in bata tsaya akanki ba zaki lalace shiyasa nacewa Mijin Hafsa ya kawon abata in watan haihuwarta ya kama"

Amatullah ta amshi tea ɗin ta kafa kai tana sha wanda Anty ta amshe maganar.
"Ai mama yaya hadiza sam ta gyara halinta ace mu ta mayar damu ababan gaba fisabilillahi rayuwar haka zata tafi Ace kaf matan gidanmu sai tazo da kanta taiwa Amatullah wanka"

Mama tai murmushi tace.

"Rabu da maganar Lami bata da amfani Allah dai ya ganar da Hadiza kawai"
Daga haka taja bakinta tai shuru bata bawa Anty ƙofar taba da haka zata ja gulmar Ummah ai tayi da matan gida.

Har la'asar suna gidan anan suka ci abinci ban da mama da take azumin alhamis.

Haka har ranar suna tazo ƴan uwan Amatullah basu yanke ba umma tai mitar zuwan nasu amman Amatullah tace mata arziƙine kuma tun daga wannan Dubarar shan tea da mama ta nuna mata shikenan ruwan Nono ya kawo yarinya ta sami abinci.

Anyi suna lafiya Yarinya taci Sunan Ummah Khadijatul Iman amman Iman ɗin za'a ke ce mata.

Kuma har lokacin Babu wani daga cikin ahalin imran daya zo gidan Amatullah bata sami fuskar tuhumar shiba a daddafe umma tai zuwan sati bayan suna.

Daga nan kuma Amatullah ta koma cigaba da kula da yarinyarta.

Lokacin datai kwanaki ashirin agidan Imran ya soma Tsiro mata da wasu halaiya na daban Son kusantarta acikin Jinin Biƙi ji wani jahilci ƙin amincewar da tayi shine ya tsiri hanata abinci tare da Kulleta a ɗaki tun safe har sai ya dawo zai Buɗeta..........

_EKEJA BARRACK LAGOS STATE_...........
*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*





*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami  ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah  ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE  muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko  uwargida  ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*

BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE  @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }

*NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

*007*

Juyi kawai yake a saman kujera hannun shi riƙe da wayar shi yana duba posting Ɗin da aka turo mishi yanzu na zuwa Kano wanda zai ɗauki watanni kusan uku acan, Shine zai jagoranci rindunar sojoji ta farko da zasu shiga wasu daga cikin ƙauyukan Kano waɗanda ake tunanin wasu mutane da ba'a san ko su waye ba suna haurawa cikin dare suna kwashe musu dabbobin su tare da ƙona musu Gidajen su wannan tasa Aka buƙaci sojoji kusan Rinduna Biyar don ta shiga ƙauyukan ta bawa mutanan dake ciki kariya.

Duba Map ɗin ƙauyukan ya shiga yi wanda suke Cikin Ɓangareron Kano maso kabashin Gudu Batare da wata shakka ba ya tura shaidar Gani tare da aje wayar tashi yana Cike wata takarda dake gaban shi.


Tura Ƙofar Office ɗin nashi akai tare dayin sallama Abokin Aikin shi Captain Khalil ne ya shigo sanye Cikin kakin su na soja Miƙa masa hannu yayi suka gaisa sannan ya nuna masa Kujerar dake kallon Shi.

"Khalil yanzu nake ganin Wani posting letter ko kai ma ka gani?"

Captain Khalil yaja tsaki tare da cewa.

"Kai dai Bari Makama nagama Shirin tafiya zamfara kasan Gida ce amman Mutanan nan suka sauya mana rinduna"

Murmushi Ahmad yayi tare da cewa.
"Au kaifa gida aka tura ka ko? to ka sani Ko kanon ce alheri gare mu?"

Khalil bai yi magana ba ya janyo wayar shi yana nunawa Ahmad cikin ta.
"Kaga nan zamu sauka a Bakabo barrack fa na can janguza wannan posting sam bai min daɗi ba wallahi"

Ahmad yace.
"Na gani mana Allah ya zartar mana da alheri haka kwanakin Baya Nai shirin katsina naga an mayar dani Barno haka na tafi kasan a rundunar mu ni kaɗai nayi rai"

Haka suka ɗan tattauna akan tafiyar tasu wadda Shida Abokin aikin sa Khalil sune zasu jagoranci Rindunar sojojin ɓangaren su, sauran tawagar ukun daga wata tawagar ta daban take.


Bayan gama maganar tasu Khalil ya tashi ya koma office ɗinsa.

Bayan sallar azahar suka soma training da tawagarsu sai wajan yamma ya koma gidan shi duk ya gaji haka ya watsa ruwa ajikin shi ya kwanta agado yana mai jin wayar shi tana ringing!

Idanun shi a rufe ya ɗaga wayar yana sakin ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya.
"Tunda mukai magana rannan Shikenan ka share ni ka manta dani wato dani da Babu duka a ɗaya a rayuwar ka Ko Baby?"

Muryar Zee wadda take maganar cikin shagwaɓar da take masa a koda yaushe idan suna waya.

Ya janyo pillow ya matse a kirjinsa ya gaji Hutu yake buƙata amman yasan idan yace mata haka wata rigimar ce zata kuma tashi.

"Kiyi haƙuri zainab wallahi ayyuka ne suka sha kaina yanzu ma haka".....

"Ni babu wani ayyuka kawai kace dai ka sami wadda ta fini"
Ta tare mashi maganar daya ke Niyyar gaya mata.

"To shikenan ƙarya zan miki tunda ni maƙaryaci ne ko?"
Ya faɗa a zuciye yana ƙoƙarin datse wayar.

"Kayi haƙuri nima bai laifi na bane laifin zuciyata ne data ke maitar son ka"
Ta faɗa muryarta na rawa kamar zata yi masa kuka!
Zuciyarshi ta karye sam baya son jin kukan ƴa mace yana mugun sanya mishi rauni.
"Shiii! ya isa Bana son jin kukan ki Nama kusa zuwa kano In sha Allah ki tare ni nan da kwana ki Uku"


Wata ƙara ta saki tana Ihun murna duk azaton ta, ta ɗauka sabida ita zaizo jin ƙarar tai yawa yasa ya datse kiran yana mai kashe wayar Baki ɗaya ya mirgina ba jimawa bacci yay awan gaba dashi.

Bai tashi ba sai magariba yayi sallah ya kuma fita Filin training wanda anan suka ɓata Lokaci har zuwa isha'i sallah kawai yayi ya soma haɗe tarkacen sa yana addu'ar In sha Allah daga wannan tafiyar yabar lagos gaba ɗaya In sha Allah arewa zai koma koda ba Kano state ba.


Zainab.
Ta rungume ƙawarta Rahma tana cewa.
"Alhamdulillah naji daɗin zuwan ka my love"
Rahma ta tureta tana cewa.
"Dallah ajikina kike ba ajikin sa ba mayyar Ahmad ni wallahi har kin soma bani haushi nifa a rayuwa bana son naga mace ta zaƙe a soyayyar namiji sabida ƙarshe sai yayi breaking heart Ɗinta"

Zee ta harari rahma tana cewa

"Ramcy zamu yi faɗa akan Baby wallahi ban haɗa soyayyar Baby data kowa ba rannan da Hajiya tai min baki akan Ahmad sai da nai kwana Uku ban ci abinci ba sabida haka kema zamu ɓata akan shi nina san Baby baze ci Amana taba yadda yake sona har yayi yawa"

Ramcy tabi zee da kallo tana mamakin rawar kanta akan wannan Ahmad mai wa mutane kallon banza.
Dan ita tunda tagan shi sau ɗaya taji baya burgeta sabida kama gidan shi yayta wani haɗe rai yana wani shan ƙamshi kamar wani basarake!


A gurguje Zainab taiwa Rahma Sallama ta wuce Gida ta ɗauki sabon kaya takai Ɗinki tun a ranar ta umarci masu Hidimar Gidansu akan su soma ƙara gyara gidan na musamman don akwai babban baƙon da zai zo.

Ranar haka zainab ta Ishi Hajiya da Dadyn ta da maganar Ahmad wanda suka Biye mata suna taya ta Murnar zuwan Masoyin nata don Dadyn ta har kuɗi ya kuma ƙara mata yace ta gyara Jikinta da kyau.
Washe garin ranar kuwa Zee ta wuce gidan gyaran Jiki wanda aka gyare mata Jikinta daga nan ta wuce wajan Mai make up tai Booking wanda zata je ranar da Ahmad zai sauka in an mata ta wuce airport ta ɗauko shi dan tuni tai masa waya akan cewa ita zata ɗauko shi idan ya sauka daga nan ta wuce dashi Gidan su inya Ci Abinci ya Huta sai ya wuce nasu Gidan ( kuji fa )

Shiko Ahmad koda zee tai masa wannan maganar kawai yaji tane batare daya bata amsa ba don shi tuni Yayi wa Kamal ƙanin shi waya wanda shine zai ɗauko shi don shi baze bi tawagar suba daban zai tawo sa haɗu a filin daga.

Burin shi ya ganshi a gaban Maman shi dan yayi masifar Missing ɗinta Ji yake kamar yay tsuntsu ya janyo Jibi ya ganshi a kano.

Itama kuma Maman tun da yay mata waya zaizo take hidimar tarban shi dan takanas zata shiga Kicin ta shirya masa abinci na musamman wanda rabon ta da kicin tun da Ahmad yabar gida don baya cin abincin kowa sai nata wannan yasa tunda yabar kano ƴammatan ta ke mata girki sai yanzu da yace zaizo Jibi take Hidimar haɗa masa abincin da zai ci idan Allah yasa yazo ɗin wanda zatai mai abincinmu na gargajiya don yafi son shi fiye da kowani abinci.

*ƊAN BARE*

Yau tunda Imran yabar Gidan bai dawo ba sai Cikin dare gaba ɗaya ran shi a ɓace yake sabida haka komai ya gani a gidan ball yake dashi sakamakon Maganganun da Uban gidan shi ya gaya masa.

"Ina son ka Imran wannan auren da kayi ma dan babu yadda zanyi ne amman duk ranar dana tabbata ka kusanci matarka daga ranar zaka gane kuranka kasan ba'a yaudarar Tani Ɗan Manu"
Wannan maganar da Tani ɗan manu ya gayawa Imran shine ya sanya Imran bacin rai ba kaɗan ba Tsoro fargaba ɗimuwa shine ya ke ɗawainiya da IMRAN DARE ƊAYA sunan da jama'a ke kiran shi dashi kenan.
Tsoron shi ɗaya shine kada Tani Ɗan Manu ya gano fa ya kusanci matar shi har ta haihu wanda Auren ma sai da Imran yakai ruwa rana sannan tani ya bar shi yayi sabida a tsarin su tani babu auren wani jinsi wannan alƙawari ne sukai da ƙungiyar su koda yabar Imran ma yay auren dan babu yadda zai da son Imran ne wanda shi kuma Imran Mahaifiyar shice ta matsa masa akan sai yayi auren wannan tasa yayi aure akan sharaɗin babu kusantar matar.

Zama yayi akan Kujera yana saƙa wa da kwancewa na matakin daya dace ya ɗauka akan Amatullah da ƴarta ji yake kamar ya kasheta ya Gudu yabar Gidan.

A fusace ya Nufi ɗakin daya kulleta ya sanya Key ya buɗe ya shiga cikin sa.........
*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*





*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami  ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah  ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE  muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko  uwargida  ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*

BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE  @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
     { Eternal love }

           *NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

                     *008*

A razane Amatullahi Ta ɗago tana kallon Imran wanda ya tsaya akanta yana Huci tamkar kumurcin maciji Ƙamƙame Iman tayi ajikinta wanda nan da nan jikin nata  ya ɗauki Ɓari tana mai bin Imran da kallo Ruwan hawaye yana Ta wanke mata fuskarta.

Ya dube ta a wulaƙance tare da ƙara taku Biyu a gabanta sannan yaja ya tsaya.
"Kije gidan iyayen ki, Ni bazan sake kiba Kuma bazan dawo dake gidana ba haka zan jinginar dake da aure na akanki har ki koma ga Allah! ta yadda wani baze taɓa Neman auren ki ba, Nayi alƙwari kamar yadda kika ƙi aminta da buƙata ta Nima haka bazan taɓa bada takardar sakin ki ba Kije kita zama a kusa da wannan shegiyar kwaɗayayyar uwar taki mai kama da Mayu"

Kuka! ne mai ƙarfi ya ƙwace mata yi take ta ƙi dai na shi bakinta yayi nauyi bata da wata kalma da zata iya furtawa.
"Kuka yanzu kika soma so nake na bar Muku darasi a rayuwarku, dake da mahaifiyar ki da mahaifinki ina son Ku ɗanɗana baƙin ciki da Ƙuncin rayuwa na har abada bana muku fatan samun sassauci"
Ta ɗago da sauri Muryarta duk ta dashe tace masa.
"Imran tsakanina dakai sai sakayyar Allah tunda nake auren ka ban taɓa samun farin ciki ba kai Min ciki na haihu batare daka Nunan wani daga cikin dangin kaba, Rabon dana san  wani naka tun a neman aure na, sannan kazo kace naje gida ba tare da shaidar saki ba Nan gaba idan ƴata ta tashi wa zan nuna mata a matsayin mahaifinta Ni kenan a haka zan cigaba da rayuwa ta cikin Ƙunci? dan kawai na bijirewa saɓon Allah In sha Allah Imran ƙarshen ka baze yi kyau ba"
Ta ƙarasa maganar cikin Kuka!
Dariya mai ƙarfi ya saki wadda ta sanya Iman farkawa da wani gigitaccen Kuka wanda ta ke yin sa da iya kacin ƙarfin ta Amatullah bata da zaɓin daya wuce itama fashewa da kukan.
Wannan wace irin rayuwa ce wannan wace irin ƙaddara ce ke bibiyar rayuwarta tabbas idan Haƙƙin wanda ka zalunta haka yake saurin Bibiyar bawa da anrage Cin Amana a duniya.

"Na baki mintuna Goma idan har na dawo na tarar dake a gidana tabbas zan sauya Miki kalar halittarki da yadda idan kinje gida mahaifan ki ba Zasu gane kiba"
Ya faɗa a gadarance yana mai Juyawa yabar ɗakin da mugun sauri.

A garin saurin miƙewa daga wajan yasa Ta yarda Iman a ƙasa wadda ta kuma canyarewa da kuka kamar wadda ake Mintsini Abu goma da ashirin ya haɗar mata Nan da nan jikinta yahau rawa kaya kala Huɗu ta ɗauka Sai ƴan kayan Iman haka ta fita daga ɗakin tana share hawayenta a garin Ta goya Iman ma ta kuma Faɗuwa yarinyar sabida rashin sabon goyon da bata saba ba


A daren ta fita daga Unguwar ga hannunta babu ko sisi tafiya kawai take a ƙafa ga Uban Hadarin daya haɗo sai faman iska ake Titi duka sahu ya ɗauke Tana zuwa daidai Rijiyar zaki layin Muhalli aka tsuge da ruwa wanda kafin ta ƙarasa Gida Ruwan yayi musu duka ita da Iman Lokacin da taje layin su kuwa dare yayi sosai dan an rufe Ƙofa haka ta saka Dutse tahau dukan Ƙofar wanda ta jima tana Duka kafin taji Muryar Alhaji babba yana cewa.
"Wanene ke Bugu haka lafiya?"
Cikin rawar ɗari tace.

"Nice Amatullahi Alhaji"
Da sauri Alhaji ya zare sakatar Ƙofar yana haskata da Tourch light.
"Subuhanallahi Amatullah da wannan dare kusan ƙarfe ɗaya lafiya dai?"

Fashe

4 / 11