Author : Autar Manya Category : Romantic Hausa Novels
da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*
BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*12*
Lokacin daya fito daga Palon mama kusan ƙarfe taran Dare ne, sabida haka alwala yayi ya wuce masallacin dake kallon ƙofar Gidansu yayi sallar Isha'in daya rasa Yana fitowa daga Masallacin suka haɗu da Kamal wanda yake Buɗe Gate zai shigar da Motar Shi daya kai masa wanki Tun jiya sabida Haka dakata wa yayi Kamal har ya shigar da Motar Cikin Harabar Gidan sannan ya Miƙo masa Keyn Motar.
Amsar Keyn yayi sukai sallama da Kamal ya Nufi Cikin Gida shi kuma Kamal ya Juya da tashi Motar dan ya kaita gareji sabida Harabar Gidan bazai ci mota Biyu ba dan haka iya ta Ahmad ce kaɗai ta sami wuri a harabar Gidan.
Hadari ne keta haɗowa a garin sabida yanayin na damuna ne iska mai ƙarfi tana Kaɗawa wanda ya bawa Ahmad damar Ƙara sauri wajan shiga Gida sabida baya son ruwa ya taɓa shi Gudun zazzaɓin daya ke haifar masa Kuma ya lura Hadarin dab yake da zubar da ruwan sama.
Kukan Jariri ke tashi cikin kunnen shi Lokacin daya kai ƙofar shiga sashin su A hankali yake ƙara matsar da Kunnen shi zuwa Inda yake Jin sautin fitar Kukan Jaririn Tabbas ba Gizo Kunnen shi ke yi masa ba Ƙofar Sashin Kawun sa Sha'aibu anan yake Jiyo Kukan jaririn wanda har takai ga jaririn ya sarƙe yana tari Kukan yaƙi Fita ta daɗi.
Da sauri ya ƙarasa Cikin sashin Abin mamaki harya tura Ƙofar da aka karo ya shiga tsakar Gidan amman babu wanda ya fito daga ɗaki bare yasa ran sallamar daya ke yi za'a amsa masa.
A hankali yake Bin sahun Inda yake Jin kukan jaririn Bai sha mamaki ba sai da ya tsinci kansa a Ɗakin daya haɗu da tarkacen Itace Duhu Dumɗun acikin ɗakin babu alamar Haske Hannunsa har rawa yake wajan Ɗauko wayar shi dake aljihun jallabiyar shi.
Yana mai kunnata ya Haska ɗakin da fitilar wayar tashi
Wanda idanunshi yakai masa Duba wajan Jaririyar Yarinya ɗanyar haihuwa yashe a ƙasan wani ƙaramin zani sai Kuka take Duk ta ɓata Jikinta da Dattin Sumuntin Ɗakin.
Cikin zafin nama ya ɗauke Jaririyar yana jijjigata ajikinsa har Lokacin bata daina Kuka ba sai cilla ƙafafu take.
A hankali ya saka mata harshen sa Cikin bakinta wanda ta kama tana mamula kamar ta sami Nono sai Kukan ya tsaya ta kama ajiyar Zuciya.
Haska yarinyar yayi sosai yana ƙare mata kallo tausayi da Soyayyarta a take suka Kama masa Zuciyarsa.
Hannunta ya kama wanda aka saka mata ƙaramar azurfa a ɗan ƙaramin yatsarta Da sauri ta saki harshen nasa ta canyara Kuka Har tana ƙwarewa.
Ya Kuma Ɗorata a kafaɗarsa Kallo ɗaya yayiwa hannun yaga Ya kumbura har yaja Ruwa.
Ya zaro idanunsa waje yana mamakin Rashin Imanin uwar yarinyar da bata san ya rayuwa take Ciki ba amman an barta cikin tsananin azabar Ciwo a hannu ba tare da an kula ba.
Amatullah.
Tunda suka fita da Sabuwa bata dawo gida ba sai da akai Sallar isha'i Lokacin da suka je Gidan Alhaji Idris mai kwano masu gadi suka hanasu shiga sabuwa taita Kiran Number Hajiya Zahra bata same taba sabida Haka sai kawai suka Juya Koda suka juya Ɗin a hanya Amatullah ta sanya wa Sabuwa Kuka akan cewar bata da Daidai da Kuɗin Maganin sauro bare abin da zata ci Ruwan Nono ya kawo Yarinyar ta tasamu Tsananin tausayin ta ya kama sabuwa sabida haka sai kawai tai Rijiyar Zaki cikin tasha Da Ita wajan Wata Hajiya Balki mai Abinci akan ta ɗan yi mata aiki ko naira Ɗari biyar ta bata Cikin Ikon Allah suna zuwa tashar ma Hajiya Zahran ta Kira sabuwa Sai dai ganin Magariba ta kawo kai yasa sabuwa tace mata Gobe
Zasu dawo Basu ma sami Hajiya Balki ba sai yaranta dan haka sai suka Juya Gida to sai sabuwan tace wa Amatullah ta Bita Gidanta taci abincin dare sai ta koma Gida Sabida Sabuwa tana jin tausayin Amatullah sosai.
Hakan akai Suka Nufi Gidan sabuwa Anan taci Abinci har akai isha'i sannan tayo Gida Bayan sunyi sallama da sabuwa.
Koda ta Koma gidan Bata sami tarbar arziƙi a wajan Ummah ba bare ta sami Darajar tace mata daga ina take sai ma ɓacin rai data riska dan Nana ta ɗaukar mata kayanta Kala ɗaya takai gidan Ɗinki an rage mata ta sanya su ajikinta Koda tai magana Nana tahau Gaya mata baƙar magana Hussaini Ƙaninta shine mai cewa sai ya ɓallata ya ɓalla banza sai da ƙyar Hassan ya riƙe Hussaini Amatullah tasha Kuka a ɗaki Sannan ta aje Iman a saman zaninta ta Ɗebi ruwan sanyi a rijiya ta shiga Banɗaki domin tai wanka Duk da ba Omo bare sabulu amman tasan Ruwan sanyi zai mata Maganin zafin daya Isheta.
Tajima tana kallon Gefen cikinta wanda tsargiyar ɗinkin da akai mata na C's Ta cire tsaf wajan yayi Kyau babu alamun wata matsala Jan ajiyar zuciya tai aranta tana Godiya ga Allah daya sa wajan bai sami wata matsala ba ya warke ras.
Duk Budirin Kukan da Iman take sam bata jiba sabida Bayin yaɗan shiga Loko Haka ta gama wankan ta ɗauro zani ta Fito kanta Ko ɗan kwali babu.
Sai dai koda da fito Ɗin Ta tsinci kanta da tsananin faɗuwar Gaba sakamakon wanda ta gani a tsaye Riƙe da Iman A hannun shi yana jijjigata Tsananin tsoro da faɗuwar gaba ne suka Kuma ƙaruwa acikin zuciyarta Ko shekaru nawa zatai bata gan shiba bazata mance Kamannin saba YAYA AHMAD.
Ta faɗa aranta da sauri Kuma ta raɓe shi tai ɗaki har tana Bugewa da bango.
Da kallo ya bita yana mamakin Ramewar da yarinyar tayi tome ke damunta?Ya girgiza kan shi yana mai juyawa Ya fita da Iman A hannunshi Wajan motar shi ya nufa ya Buɗe tare da aje Iman aciki ya zagaya ya buɗe Gate sannan ya koma ya fitar da Motar Sannan ya dawo ya rufe Gate Ɗin ya Koma Cikin Mota yayi mata key yaja ya bar layin.
Kai tsaye wani ƙaramin Private Clinic ya kaita wanda Nurse suka karɓi Iman domin su duba Hannun ta kamar yadda yayi Musu Bayani Rintse Idanu yayi yana jin zafin yadda Ƴar ƙaramar yarinyar Keta tsala Kuka Lokacin da Nurse ke gyara mata Hannun nata wanda tace masa Buguwa ne tayi bayan an gyara aka shafa mata magani a wajan Ya biya Kuɗi sannan ya Shiga Mota sai da ya biya ta wani super market ya sayi madara ta Jarirai ya tambayi yadda ake haɗawa tare dasu pampers dasu Pida sannan ya ƙara Saya mata Riguna masu kyau sai yayo Gida.
Lokacin daya ƙaraso Gida tuni an soma ruwa da sauri ya shigar da Motar ya Kulle Gida sannan ya fito da Iman da kayan daya siya yayi ɗakinsa da Gudu gudu, Batare daya Bi takan Amatullah ba bare ya kai mata yarinyarta so yake yaga Gudun ruwan Haukanta........
Bayan ya shiga ɗakin ya rufo ƙofar shi ruwan zafi ya haɗa yay wanka ya Rage daga shi sai Guntun wando da singlet Itama Iman Tawul ya Jiƙa da ruwan Ɗumi ya goge mata Jikinta tas sannan ya sauya mata kaya wajan saka pampers ne yaci wahala dan har Gumi sai da ya haɗa yana gama shiryata ya Haɗa mata madara a pida da ruwan Ɗumi ya ɗaga kanta yana bata Cafkewa tai tana sha tana ajiyar Zuciya Har ƙwallar tausayin yarinyar ce ta tarar masa a idanunsa tas ta shanye Madarar dake ƙatuwar Pidar Ya kwantar da Ita saman Ƙirjinsa yana shafa kanta mai cike da suma Kafin wani Lokaci tayi gyatsa ba jimawa Bacci yay awon gaba da ita sai Fitar Numfashi mai ɗumi take.
Anan ƙasan Carpet yaja Pillow ya kwantar da kanshi Shima da yake Gajiya na Cin Jikinsa bai Minti Biyar ba bacci mai Daɗi ya kwashe Shi Batare daya yi Tunanin kaiwa Amatullah Yarinyarta ba.........
Amatullah.
*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*
BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*13*
Cikin mutuwar Jiki take sanya kaya ajikinta gaba ɗaya tunaninta ya tsaya cak, Yaushe ya dawo Gida Ina zai kai mata Iman ita bata son duk wata alaƙa da zata Haɗa ta dashi Dan haka Koma Ina ya nufa da Iman dole ya dawo mata da yarinyarta Tafaɗa tana Danno Bakinta gaba kamar Yana kallon ta.
Tana kammala shiri ta Fita tsakar Gida ta zauna Yayyafin ruwan sama na Dukan Jikinta Idanunta Lumshe Tana shaƙar Mayen Ƙamshin Turaren shi daya bari a tsakar Gidan Tun tana Zaune harta Gaji ta Miƙe ta fita harabar Gidan Ƙofar Gida a rufe Haka nan Gate Ɗin ma a rufe Jingina tayi da Bango Hawaye yana zubo mata Wa zata Tunkara da Batun Ahmad ya ɗaukar Mata Iman ya fita?
Haka ta koma cikin Gida gaba ɗaya Jikinta yayi mata sanyi ɗaki ta wuce a wannan dare Bacci Ɓarowa shine yayi awon Gaba da ita daman Ga jikinta Duk ta gaji.
Wajan Asubah zazzaɓi Duk ya rufe mata Jikinta ga Nononta ya samƙame Ya ciko sabida Rashin sha da Iman batai ba zuwa asubahi kanta ya soma yi mata azababban Ciwo a daddafe ta Fita tsakar Gida tayo alwala ta dawo ta zauna tana azkar Ta jingina kanta Jikin itace wajan shiddan safe ta Fita ɗakin Baba ta gyara shi sannan ta koma ɗaki ta kuma zama ji take Kamar tai tsuntsu ta ganta a gaban Iman bata san tana son yarinyar taba sai da ya nisanta ta da ita.
Kuka take a wannan Lokacin domin ta kasa jure rashin Iman.
"Amatullah Lafiyar ki, kike kuka?"
Taji Muryar Ameerah a saman kanta wadda sam bata ji Sallamar da Ameerah ke mata a ɗakin ba.
Ta ɗago jajayen idanunta ta zubawa Ameerah Tare da cewa.
"Ba komai Idona ke min Ciwo"
Da sauri Ameerah ta aje kwanon abincin data shigo mata da shi a gabanta tare da zubewa a kusa da Amatullah Ɗin tace mata.
"Yaya naga Kina kuka da idanuna sannan Kice Idanun ki na maki ciwo Ina Iman ban ganta ba?"
Sai Amatullah ta kuma fashewa da kuka tana cewa.
"Tun jiya ya tafar Min da Ƴata ko ina ruwan shi dani Oho dan rashin Imani ya tafar Min da ƴata bai dawo Min da ita ba"
Da sauri Ameerah tace.
"Waye Imran? garin yaya?"
Tura baki Amatullah tayi tare da cewa.
"Yayah Ahmad Mana"
Jimm ameerah tayi Batai magana ba har tsayin wasu Lokuta Kafin tace.
"Meye Ya haɗa ki da shi da har ya Ɗauki IMAN ɗin?"
Cike da Mamaki Ameerah ta faɗi maganar.
"Oho mai"
Amatullah ta faɗa tana mai cigaba da kukanta.
Ameerah Danne abin da ke taso mata a zuciya tayi kafin ta shiga rarrashin Amatullah tana yi tana kawar da sharrin shaiɗan a zuciyarta.
Da Ƙyar ta Lallaɓa ta taci Indomie da ƙwan da ta da fo mata sannan Suka fita Ameerah na ce mata tazo suje wajan Mama ta gaya mata Ita kuma Amatullah taƙi tace yaje ya kwaɗanta Iman ɗin ya cinye.
Ranta Babu Daɗi ta fita daga Gidan tayi gidan sabuwa koda taje can ma sabuwa taita tambayarta meye ya kumbura mata idanu tace ba Komai Haka suka tattara don tafiya Gidan aikin nata.
***************
Da Gudu Ameerah ta shiga Cikin Gida tana yada kwanon tana kiran Anty wani azababban Kishin Ahmad na cin ranta.
Da sauri Anty dake haɗa ma Ƙanin Ameerah abinci ta fito tsakar Gida Tana cewa "Ke! Nifa nagaji da wannan ɗagamin Hankalin da kike jiya kin shigo min gida a firgice yau ma haka Uban me aka kuma yi Miki?"
Rungume Anty tayi tana cewa.
"Anty zuciyata raguwa ce na kasa lafawa duk wanda zai Raɓi Yaya Ahmad Anty zuciyata zata Buga Jina ke kamar zan Mutu in ban sami Yayah ba"
Anty ta shiga shafa kan Ameerah tana jin Raɗaɗi acikin zuciyarta na yadda da ranta da lafiyarta ƴarta ke neman rasa Nutsuwarta akan ɗa namiji.
"Ki shuru Ameerah kada Mutan gida suji me muke ciki wuce Muje Ɗaki maza"
Jikin Anty har yana rawa tama mance da wani Abincin da take zubawa suka nufi ɗaki suka zauna a saman Kujera Ameerah ta ɗago Fuskarta datai jage jage da hawaye tace.
"Anty jiya fa ƴar Amatullah a wajan sa ta kwana Fisabilillah meye haɗin sa da ita yanzu naje na tarar tana ta Kuka Da ƙyar na danne zuciyata na Dawo gida Anty Nifa bana son naga yana kula ko wace mace idan bani ba duk da nasan Amatullah ba zata ci Amanata ba domin tasan yadda nake son shi"
Anty ta zunduma wata irin ashar tana miƙewa tsaye.
"Dama kece Wawiya waya gaya Miki yanzu akwai amana ai wanda ka yarda dashi shiyake fara cin amanarka dama ni fa wannan tsinanniyar yarinyar bana ƙaunar ta bana son ta wato Har yanzu bai haƙura da ita ba kenan?"
Da sauri Ameerah ta Rufewa Anty Baki tana cewa.
"Nifa Anty bana zargin Amatullah kawai Kishin Abin naji acikin zuciyata amman wallahi kamar yadda yaya baya ranta itama haka bata na shi ran"
Anty Tayi juyi tana cewa
"Dama Yaya sai da tace min sai na tashi tsaye akan Ahmad sannan haƙar mu zata cimma ruwa sabida haka bana jin Ko ita waccan Ƴar mai kuɗin zan bari ya aura dan haka daga yau ki soma shiri Cikin ko wani yanayi zaki iya jin An ɗaura auren ki da Ahmad Ina shine Burin ki to kisa aranki wannan Buri naki cikakken Buri ne sai kin aure shi ita kanta uwarsa sai dai ta koma ƴar kallo"
Anty tana faɗin haka ta ɗauki wayarta ta shiga kiran Yayarta a waya ta shige ɗaki tabar Ameerah da nazarin maganar tata.
Mintuna kaɗan ta fito da mayafi tana cewa ameerah ta kula da gida zata Fita anguwa.
Amman taji zuciyarta tayi sanyi tana Jin Ahmad shine rabin rayuwarta ta yarda ta kowace hanya mahaifiyarta tabi Idan har Burinta zai cika ta sami Muradin zuciyarta.
*********************
Ya tashi da tsananin mamaki acikin Zuciyarsa na yadda Amatu tai ko in kula da ƴar Cikinta haka ya shirya ya fita yayi sallar asubahi ya dawo ɗaki Lokacin Iman ta tashi tana ta tsala Ihu Jin Kukan yake na juyar masa da kanshi da sauri ya ɗauketa da madararta yayi Falon Mama yana Kiran Naja'atu wadda ta fito da Hijabin sallah a jikinta ta zube tana gaisar dashi ya Miƙa mata Iman yana cewa ta bata madara ta Goyata.
Amsar Yarinyar tayi cike da Bin Umarninsa haka ta Juya ɗaki shikuma ya Nufi Ɗakin Alhaji Domin su gaisa.
Zaune ya tarar da Mama da Alhaji suna hira a ɗaki yayi sallama suka amsa ya zauna a ƙasan carpet yana gaishe dasu Bayan sun gaisa Alhaji ya dube shi Cike da kulawa yana cewa.
"Ɗazu muka gama maganarka da kawunan ka Ina ganin yau zasu je Gidan su yarinyar nan kawai zamu kai Lefe Jibi idan muna raye tunda Lefan ka daman yana ƙasa Idan yaso nan da wani satin in suna shirye a ɗaura aure matarka ta tare agidan ka dake Bayan layi abin da baka ƙarasa ba sai ka Ƙarasa Da wuri Tunda zaka jima anan Ɗin gwara ka zauna da matarka"
Tunda Alhaji ya soma maganar yayi ƙasa da kanshi Jin maganar yake daga sama Sam baze iya musu da maganar Alhaji ba amman yaso an ɗan ɗaga Bikin an barshi kamar yadda yake ada sabida yana da shirin da ze a ƙasa amman Tunda Alhaji yace ayi Ɗin hakan za'ai babu ja.
"Baka ce Komai ba Babana ko kana ganin abar shi kamar yadda yake? ni abin da yasa nace ayi Yanzu sabida naga ka sami Lokaci ka dawo Kano Komai zai zo maka da sauƙi"
Cewar Alhaji wanda yake maganar Cikin dattako.
"Alhaji ba wani abu abar shi hakan Allah ya ƙara Girma"
Daga haka yaja Bakinshi yayi shuru Mama ta bishi da kallo tana yaba tsananin Biyayyarsa.
Duk Yadda baya son abu idan suka umarce shi dayi baya Musu tana addu'ar Shima Allah ya bashi masu yi masa Biyayya kamar yadda yake Yi musu.
"Binta ke baki ce Komai ba?"
Cewar Alhaji.
Mama tayi dariya Ta kauda kanta Gefe.
Alhaji yayi dariyar shima yana mamakin wannan alkunya da Mama kewa Ahmad.
Ya jima suna ɗan tattaunawa da Ahmad ɗin kafin Suyi sallama ya wuce Ɗakin sa.
Alhaji ya kalli mama yace mata.
"Kinga yaron nan naki badai zurfin Ciki ba koda abu bai masa ba baze Fito fili ya faɗa ba