Author : Autar Manya Category : Romantic Hausa Novels
gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*
BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*005*
Gumi duk ya wanke mata jikinta duk da sanyin fankar dake kaɗawa acikin ɗakin.
Muryarta a dashe irin ta mai bacci ta dube shi tana mai zare manyan idanuwanta tace masa.
"Imran meye haka dan Allah ka rabu dani, nace dan Allah ka rabu dani wallahi Allah koda duniya zaka bani bazan taɓa Kaucewa Umarnin Ubangijina akan taka buƙatar ba"
Batai aune ba taji saukar Danshin bakinsa cikin nata wanda shine ya dakatar da ita daga ƙarashe maganar data keyi a haukace yake yamutsa Dukkan sassan Jikinta yana ƙara ribatarta zuwa Cimma muradin Zuciyar sa
Wani tsallan albarka tayi tare da bangaje shi tayi hanyar falo har Rigar Jikinta na zamewa ta faɗi ƙasa.
A haukace ya bita yana cewa
"Dan matsiyatan iyayenki yau babu mai rabani da ke sai Allah, an gaya miki a banza zan ke, kashewa iyayen ki kuɗi to maitar Biyan buƙatar kaina ita ke ingizani zuwa ga aikata koma meye akan mayun iyayen ki, wallahi Tun ranar dana fara ɗora idanuna a bayanki naji ina maitar Jin ɗanɗanon shi"
Ya faɗi a lokacin daya cimmata ya saka ƙafa ya taɗeta ta maku a ƙasan tiles.
Wata ƙara ta saki kafin Numfashinta ya ɗauke tsaf sai kuma Jini ya soma biyowa ta ƙafafunta.
Wanda ganin wannan yawan Jini shiya tsorata Imran yayi saurin ɗauko jallabiyar shi ya sanya ita ma ya zira mata riga da hijabi, ya ɗagata cak sukai mota ya shiga mazaunin driver yaja motar suka Nufi Asibitin kuɗi mafi kusa dasu.
Lokacin da suka ƙarasa ƙarfe Ɗayan dare amman kaman rana sai karɓar marasa lafiya ake, Abin ka da asibitin Kuɗi.
Duk wani cuku cuku yayi nan da nan aka sakata a emergency room wanda Babban likitan asibitin ya duƙufa akanta dan Ceto rayuwarta har asuba Likitan yana tare da Amatullah wadda take a tsakanin Rai kokai Mutu kokai Inji bahaushe.
Likitan ya fita yayi sallah a hanya suka haɗu da Imran wanda har ya Ɗan faɗa sabida fargabar Kada Amatullah ta rasu bai sami cikakkiyar amsa wajan likitan ba.
Sabida haka ya raɓe jikin motar shi, Shikuma likitan ya koma bakin daga.
Wayar shi ya ciro ya kira Umman Amatullah.
Idar da sallar Ummah kenan taji kiran wayarta Nana ta ɗauko mata tana ce mata Yaya Imran ne Mijin Anty.
Jikin Ummah yana rawa ta ɗaga bayan sun gaisa Imran ya sosa kai cike da makirci yace wa Ummah.
"Ummah Muna asibiti fa tun Jiya Amatullah ta faɗi take zubar Jini"
Salati Ummah ta saki tana cewa wani asibitinne gata nan bara ta gyarawa Baba jikinsa ta fito ta barwa Nana girkin Gidan.
Kwatance yayi mata sannan ya ƙara yin ƙasa da murya sosai yana cewa.
"Ummah ina ganin kamar na haƙura da Auren Amatullahi, Ummah tunda mukai aure sau ɗaya kaɗai ta bani haƙƙina Kullum nazo mata da buƙata sai Munyi dambe ganin bata so nake haƙura dan kawai Jiya nace ta tausayamin ta bani shine ta ɗauki wuƙa tace Koni ko ita to a garin na karɓi wuƙar ne yasa ta faɗi Jini ya ɓalle mata"
Yakai maganar yana dariya ta yadda Ummah ba zata ji ba.
Ummah ta kuma jan salati tana tafa Hannu tana cewa.
"Haka tai maka Imirana To bara nazo dan ubanta Shegiyar yarinya mai ƙashin tsiya tafi son na dauwa ma acikin gadarar faccaloli to wallahi ta kaso auren ta badai wannan gidan ba sai dai ta nemi wani Gidan Uban"
Imran dariya yake har yana ƙwalla Tunda yake bai taɓa ganin mayyar Kuɗi kamar surukar tashi ba haka ya kashe wayar yana ƙarasawa cikin asibitin.
Nurse ce tazo ta kira shi akan Likitan nasan ganin shi bayan ya shiga Office ɗin Likitan suka kuma gaisawa sannan Likitan ya tura masa takarda gaban shi yana mai cewa.
"Muna son ka saka hannu nan da Awa Uku za'a mata C'S don a ceci rayuwarta ita da Bebyn ta don faɗuwar data yi Jiya ya haddasa wa ɗan da ke cikinta juyawa ya koma wani ɓarin Mun samu mun dakatar da zubar Jinin da take yanzu kawai Hannu zaka saka a mata aiki A rabata da Abin da ke cikinta Duk da cikin yana wata takwas ne da kwana bakwai"
Har Likitan ya gama maganar Imran bai iya motsi mai kyau ba Ta yaya tai Ciki har ya isa haihuwa bai sani ba daga kusantarta sau ɗaya shine har zata ɗauki ciki kamar wata akuya.
"Ranka ya daɗe kabar takarda a gabanka kuma kaƙi magana"
Muryar likitan ta katse masa tunanin sa.
"Nifa likita ban gane inda ka dosa ba, wai anyi gabas da kare, yarinyar nan sau ɗaya tak na kusanceta a wata taran data yi agidana sannan kawai a wani zo ace zata haihu ni gaskiya bazan wani saka hannu ba ta Mutu kawai dan ni a yanzu bana buƙatar Wani ɗa a rayuwata"
Likitan ya dubi Imran sanda ya ƙarasa maganar Cikin gadara.
"Amman kai kam musulmi ne?"
Cewar Likitan.
Imran ya juyo a fusace zai magana likitan ya ɗaga masa hannu cikin zafin rai yace.
"To in kai jahili ne kaje kabi malamai akan Halaccin wannan cikin gare ka Yau inda baka taɓa kusantarta bane za'a ce ɗan na waje ne, amman Kai da bakinka ka bada shaidar ka kusanci matarka sau ɗaya, ka sani ko tun a daran Allah ya saka ƙwan haihuwar ka cikin mahaifarta,Wannan ɗa naka ne kuma koda baka saka hannu ba ni da kaina wallahi sai na saka sannan nai mata aikin bayan nan kuma na maka ka a kotun musulunci akan kana barazanar kashe matarka da ɗanka akwai CC camera a office ɗinnan duk maganar da mukai tana naɗe dakai wawa"
Jin Kotu yasa jikin Imran ya hau rawa don a wajan cike file har Hotonsa sai da ya saka yasan babu damar Guduwa sabida akwai cikakken bayanin shi da kwatancen sa a Files ɗin daya buɗe a cikin asibitin.
"Zan saka amman Ciki kamar na aljanu ba laulayi babu girma ni a iya zamana da ita babu ta yadda na gane Tana da ciki"
Likitan yace.
"Allah ne yaso ɗan ko ƴar su taka ƙasa shine yasa ya ɓoye sanin ka da jinka da ganinka akan cikin nata"
Daga haka Imran ya saka hannu ran shi a Matiƙar ɓace ya zama dole ya Ɓoye haihuwar nan sabida kada Uban gidan shi yaji wanda Ya nuna masa harkar da yake a yanzu wanda sai da sukai yarjejeniya akan babu batun kusantar Mace ta gabanta har abada sai ta bayanta............
Yana fita daga Office Ɗin yaci karo da Ummah wadda Ko Kallon arziƙi bata samu wajan Imran ba sai ma wuce tan da yayi ya nufi motar shi ya zauna aciki yana saƙa wasiƙar Jaki na yadda zai salwantar da Amatullah da Ɗan da zata haifa sabida Gudun tonuwar asirinsa a wajan uban ɗakin sa wanda ya mayar dashi kamar matar shi( wa'iyazubillah )
Ummah kuwa Babu abin da take aranta sai zagin amatullah sabida zatonta maganar Ɗazu ce na bijire masan da Amatullah keyi ya saka yaƙi mata magana, Sam Ummah bata ta lafiyar ƴarta sai ta jimamin kada ran Imran ya ɓaci ya sako mata Amatullah suka samu suga rashi.
Cikin Aminci da Yardar Ubangiji akaiwa Amatullah aikin wanda aka samu nasarar Ciro mata Yarinyar ta mai kyau kamar su ɗaya sak da imran sai dai kawai farar fatar uwar ta data ɗauko amman kama kam kamar ka tsaga kara da Imran.
Bayan an gyara yarinyar wadda ko kayan haihuwa babu Sai Likitan ne yacewa Nurse su samo tawul a naɗeta bayan an naɗe ƴar an yanke mata cibi sai akaiwa Amatullah allura aka aje mata yarinyarta a gabanta Likitan yace a barta ta huta har allurar ta saketa.
Koda da nurse ta leƙa waje don sanar da Imran bata ganshi ba kuma bata san Ummah ba sabida haka ta koma ta kuma gyara wa yarinyar kwanciya sannan ta rufo musu ƙofar........
*Wannan salon na da banne kuma ban taɓa zuwa da irin shi a rubutu na ba mai kike jira ki hanzarta biyan naki dan tuni masu biya sun yi nisa labarin ko rabi bamu shiga ba yanzu ma aka fara*
*BAƘON LAMARI! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.*
*Ina masu kananan nono?*
*Ina masu yaye?*
*Ina yammata da ake shirin aure?*
*Ina matan gida masuson gyara?*
*Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?*
*Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?*
*Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.*
BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679
IG Bintus-spa-nd-more..
*BAƘON LAMARI...!*🌹
{ Eternal love }
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*006*
Sannu a hankali allurar da aka yi mata ta soma sakinta Cikin nutsuwa take buɗe idanunta waɗanda sukai mata nauyi daga sama kuma suka kumbura sosai.
Da farko razana tayi da taga jaririya a gabanta idanunta Buɗe tana tsotsar Hannunta sai da ta yunƙura don ta tashi taji ba zata iya ba.
Bin jaririyar take yi da kallo sannan ta ɗauke idanunta ta mayar saman rufin ɗakin tana tuna tsayin lokacin data ɗauka bata Numfashi wato rabon ta da sanin inda kanta yake tun agidanta a ɗazu da Imran yaso yi mata aika aika tun daga nan kuma bata sake Sanin Inda kanta yake ba sai a yanzu data farka taga jaririya ɗanyar haihuwa a gabanta.
Ina ta sami jaririya? dan ita a iya saninta ba Ciki ne da ita ba bare ace ta haihu.
Sautin Kukan yarinyar shine ya saka ta Juyo da sauri tana bin yarinyar da kallo yadda take Buɗe maƙogwaro tana kuka kamar wadda tai watanni.
Da sauri Nurse ta turo ɗakin ta shigo Ganin Amatullah ta Buɗe idanunta yasa Nurse ɗin tace.
"Ma sha Allah, Amman allurar nan tayi saurin sakin ki sannu Ga babyn ki nan In mai gidan yana kusa sai ya siyo muku madara kafin ruwan maman naki ya kawo"
Gaban Amatullah ya faɗi ta kuma Bin jaririyar da kallo wadda har tari take sabida Kuka! Bakin ta ya gaza furta komai sai dai kawai ido da ta saka tana kallon yarinyar.
Bata san lokacin da hawaye ya jiƙa mata Ƙuncin taba har yana sakkowa saman kirjinta.
Bata shirya haihuwa da Imran ba, Bata so haɗa tsatso dashi ba domin tabbas tasan gaba ita abar turkewa ce wajan ƴaƴanta akan irin uban data Zaɓa musu Saka kanta tayi a saman Cinyarta tana Kuka wiwi sai ɗakin ya kaure da kuka biyu ita nayi ƴar tata tana yi.
Ko kallon yarinyar batai ba wani irin tsanar yarinyar taji har cikin ranta saboda Duk abin da ya danganci Imran bata ƙaunar shi.
Kuma adaidai nan Ummah da Imran suka turo ƙofar suka shigo.
"Yawwa daman ina mata magana akan a sai wa jaririyar madara kafin ruwan mama ya sakko sai ta saka Min kuka koda yake haihuwar fari ce"
Cewar Nurse ɗin wadda take gayawa Imran da Ummah.
Amatullah cikin ranta tana kuma jin al'ajabin cikin da babu laulayi bare alamun shi, hana rantsuwa dai Tunda taje gidan bata ga al'adarta ba wannan Kuma ta ɗauka ko fargabar Imran ce ta saka Jinin ma ya ƙafe ya daina zuwa kwata kwata ( Amatullah kenan ai fargaba tsinkar da jini take ba ɗauke shiba kedai Kice bakya cikin kwanciyar hankalin da zaki fahimci kwanakin Jinin ki )
Maganar Ummah ce ta saka Amatullah ɗago wa da sauri.
"Rabu da ita likita akwai abin da ke ranta na baƙin hali shiyasa take wannan Kuka kya kashe kanki a banza"
Amatullah ta ƙure Ummah da idanu wannan wace irin Uwa Allah ya bata marar tausayi.
Da sauri wata zuciyar tace mata shine kema zaki gwadawa ƴarda bata ji ba bata gani ba zuwan ta Duniya kenan
Cikin azama ta ɗauke ƴarta ta ɗorata saman Kirjinta tare da saka baki tana hura mata kunnenta wanda nan da nan Babyn tayi shuru tana Mayar da ajiyar zuciya.
"Ummah ki mata ahankali Please yau ta haihu kinsan akwai rashin sabo a tare da ita"
Cewar Imran Cikin kirsa.
Kafin yace bara yaje ya siyo madarar.
Ummah ta nemi gu ta zauna.
Dan a ɗazu da take zaune a waje ita take tambaye Nurse ɗin kota san ɗakin da aka kwantar da Amatullah shine Nurse Ɗin ta nuna mata tare da bata tabbacin Amatullah ɗin ta haihu wanda shine Umman taje ta shaidawa Imran da murnarta wadda take farin cikin sun haɗa iri da Imran zasu ƙara Cin dukiya dan ita asan samun tama Namiji Amatullah ta haifa ba mace ba.
Koda taje sai Imran ya nuna mata bai ma san Amatullan ta haihu ba bayan Kuma ya sani ɗin.
Haka sukai zama kamar na kurame a ɗakin har sanda Imran ya dawo da kaya niƙi Niƙi kayan jaririyar kusan kala Goma sai auduga da su pampers tare da madara haka ya dire Ummah sai faman yi masa sannu take wanda bata ma Amatullah kamar hakan ba, Dan ita ko arziƙin sannun ma bata samu ba sabida takaicin Maganar da Imran ya gayawa Ummah a waya har yau bata saki zuciyarta ba.
Haka Amatullah ta miƙe tare da taimakon Nurse Ɗin ta shiga Toilet ta gyara jikinta ta fito Nurse ɗin ce ta gyara Babyn wajan azahar ya kawo musu abinci mai rai da lafiya ummah sai saka masa albarka ake Kuma babu wanda ta shaidawa Amatullah ta haihu daga Cikin Gidan har zuwa Danginta haka suka kwana a asibitin washe gari aka basu sallama.
Imran yaso Su wuce da ita gidansu amman Ummah taƙi tace tai zamanta a ɗakinta.
"Ummah to waze zauna da ita ke ga marar lafiya?"
Cewar Imran wanda wannan furucin sai da ya bawa Amatullah kunya amman ummah mursisi tai da idanu tace zata dinga asubanci tana zuwa.
Koda suka koma ba laifi ta gyara Amatullah tsaf ta wanke jaririya ita Kuma amatullah daman babu batun wanka amman ta samu gyara mai kyau wajan Ummah koda ta koma gida ma da zata dawo ta zo mata da Maganin wanka wanda zata ke sha.
Sai dai me a kwanaki Biyu Amatullah ta sami sauƙi wajan Imran wanda zai zo su gaisa amman bai taɓa ɗaukar yarinyar ba, Sai dai ya rage mata cin zarafin da yake mata Kuma abun mamaki babu wanda yazo mata barka da sunan ɗan uwan shi.
A kwana na uku ne ya soma tsiro da sabon cin mutunci wanda zai zauna a falo yana zuba mata habaici akan kwaɗayin mahaifiyarta tai kuka ta godewa Allah amman da Ummah tazo sai yayta nan nan da ita yana shirga ƙarya kamar ragowar yaƙi.
Yau kwana Biyar da haihuwa Ameerah tazo gidan sosai takewa Amatullah faɗan cewar ta haihu bata gaya mata ba sai Jiya suka ji wajan Hassan ƙaninta Mamaki Amatullah tayi don laifin Ummah ne ba nata ba wannan zuwan na Ameerah tai mata kitso da ƙunshi sannan suka gyara gidan washe gari Maman su Ya Ahmad dasu Anty suka zo don Mama ce ma taiwa Babyn wanka, Dan ita mama barta da rashin son magana wadda ta zame mata kamar Izzah amman babu ruwanta da Munafurci kamar na sauran matan gidan.
Don tana kallon Anty babar su Ameerah na nuna mama da ido wa Matar kawu, Amman maman bata ɗaga idanu ta dube suba.
A iya zamanta da mama waɗan can Halaiyar nata ta sani amman yanzu taji Ameerah tace tana ɗaga musu kai dan Ahmad zai auri ƴar masu Kuɗi sannan tana danne duk Kuɗin da Ahmad yake turowa.
Ita dai bata san Maman da haka ba amman bata sani ba ko hakan ne tunda Aminiyar Antyn su Ameerah ce, ita daman basa shiri da Ummah saboda Antyn su Ameerah aminiyar mama ce kuma anty tana nuna wa Ummah hassada