Author : Ubeera Category : Hausawa Novels
a kan santala santalan cinyoyin ummul waɗanda suke
jawur kamar ka taɓa jini ya fito gasu acike babu alamar rama ko bushewa a tare dasu.
Wani irin yammm zittt yaji acikin dukkan ilahirin sassan jikinsa ga wata irin baƙuwar kasala dake
kawo mai cafka bai da ikon koda ɗaga yatsan hannunshi.
Tsintar kanshi yayi da saurin sada kanshi a ƙasa tare da janyo ƙasan lips ɗinshi a wahalce yana
tsotsa tamkar ze cire shi. zazzafan huci yake fesarwa da sauri da sauri nan da nan idanunshi
sukai wani irin ja har wani ruwane ya kwanta a saman su.
Sannu a hankali kukan ummul ke tashi acikin kunnenshi wanda tana yinshine da iyakacin
gaskiyar ta domin yadda Dr ke matsar wajan data buge bada wasa take yi mata ba.
Dai dai sanda zata matsa mata saman ƙugun ummul ta cije taƙi yarda seta fara mata magiya.
"Dan Allah likita ki barni haka wallahi da zafi kin famo har inda bai yi"
Murmushi Dr fauza ta sanya na ganin sakarcin ummul wanda yake ɗauke da wata irin
shagwaɓa.
Kafin a hankali ta furta.
"Haba amarya kamar ba jaruma ba pls ki bari saura ƙiris na kammala miki bazaki ji zafin ba"
Tafaɗa mata hakan cike da son bata ƙwarin gwiwa domin ta tsaya.
Noƙe kafaɗa tayi tare da cewa.
"Umm umm! nidai ki rabu dani haka wallahi har zazzaɓin wahala nakeji"
Dariya dr fauza ta sanya tare da furta.
"Gaskiya wannan amaryar kin cika raki Yallaɓai kaɗan matso ka taimaka na gyara mata wallahi
ta bugu sosai barin wajan ze zame mata illah don wataƙil yama hanata tafiya idan ba'a gyara
ba"
Muryar Dr fauza ta fita lokacin data ke ƙoƙarin janye hannun ummul data ɗora akan ƙugun nata.
A hankali ya ɗago da idanunshi waɗanda suka ɗan ƙanƙance kaɗan, sabida yanayin daya tsinci
kanshi a halin yanzun kasance warshi mutum mai saurin shiga yanayin buƙata.
A hankali yaɗan matso kaɗan ya tsira ma fuskar ummul idanunshi wadda fuskar tata tayi wani
irin ja sakamakon kukan data ci har wani gumine na zafin azaba ya jiƙa mata saman rigarta.
Yawu mai ɗaci ya haɗiye tare da tattare hannun rigarshi, Kaɗan sannu a hankali yakai
hannunshi dai dai ƙugun ummul yaɗan matse kaɗan yana wani kawar da kanshi ganin hakan
yasa dr ta soma gabatar da aikinta inda ta cigaba da gyara mata wajan.
Kuka sosai ummul take duk ta gama matse shi batare data san ta aikata hakan ba murya cikin
kuka take furta.
"Wayyo bamu wayyo babarmu kizo zasu kashe miki ƴarki wallahi se Allah ya sakamin dukkan
ku mugayene"
Abin da take faɗi kenan tana ture Aliyu daga jikinta.
Baƙaramin dauriya yake ba sabida yadda take goga mai albarkatun kirjinta a jikinshi saukar
kukan ta kuma yafi kama dana wadda ake having sex da ita tana raki wannan yanayin dayake
ayyanawa shine yake ƙara jefa zuciyar sa da gangar jikinsa cikin wani irin shauƙin buƙatuwa
kasancewar shi namiji mai muguwar sha'awa ta gasken gaske! danshi daya rasa wannan guri
gwara ya rasa abincin daze ci.
Har aka kammala ummul bata daina kuka ba dr fauza miƙewa tayi ta shiga cikin wata ƴar ƙofa
tana zame safar hannunta inda shikuma ya tsinci kanshi da fisgo ummul ta zauna saman
cinyarshi.
Da wata irin taɓara ta shigar da kanta tsakiyar kirjinsa tana cigaba da kukanta.
Bai iya rarrashin mace ba don ko basmah itake rarrashin sa dan haka seyayi mata shuru yana
kokawa da nutsuwar shi kafin A hankali ya rankwaɓa tare da kai kanshi dai dai saitin kunnenta
ya wani buga mata hucin zafin bakin shi kafin ya aro jarumtar magana.
"Haba mana pls kibar kukan tashi mutafi"
Yafaɗi maganar kamar bai da niyyar furta ta.
Bata kula shi ba sema miƙewar datai ta kama hanyar barin office ɗin kuma har lokacin kukan
dai take bata dena ba.
Dr fauza ta fito hannunta ɗauke da ledar drugs ta miƙawa Aliyu tana dariya.
"Yallaɓai wannan amaryar taka ta cika raki wannan ruwan ɗumi za,a samu se a gasa wajan se
a shafa shi wannan kuma tasha sau biyu a rana Allah ya sawaqe"
Kamar baze magana ba seya miƙe ya zube hannun shi guda cikin aljihun wandon shi tare da
furta.
"Thanks"!
A ƙasan laɓɓanshi ya ɗauki ledar ya fice yabarta da mayen ƙamshin sa.
Lumshe idanu dr fauza tayi a matsayin ta na budurwa wadda ta jima batai aure ba kuma tana
fatan samun mijin aure nan da nan taji Wannan mutumin ya burgeta ba kaɗan ba cake biron
hannunta tayi tana wani irin lumshe idanunta.
Sedai akwai tsantsar izzah da taƙama a haka ta faɗa tunanin banza na wanda bai san tana
yiba.
Acan gaban mota ya iske ta har lokacin kuka take bata dena ba
Bai ko dubi inda take ba ya buɗe motar ya shiga.
Ganin ya shiga ya data yana kokarin barinta a wajan yasa ta kai hannunta ɓarin mai zaman
banza ta bude ta zauna har lokacin hawaye na zuba a idanunta.
Ƙarar kukan ta dame shi matiƙa ga basmah na kiranshi a waya rediyon motar ya kunna sannan
ya sami zarafin ɗaga wayar basmah magana suke yana faman sakin tsadaddan murmushinsa
yayi kamar ma ya mance da wanzuwar ummul a cikin motar tashi.
Wanda hakan ba ƙaramin ɓatawa ummul zuciya yayi ba dan haka ta ƙara volume na kukan ta
wanda yayi matiƙar ɓatawa Aliyu ranshi.
Saurin katse kiran basmah yayi tare dajan wawan birki ya dakatar da tuƙin idanun shi duk ya fito
dasu waje tare da kallonta fuska babu walwala ya furta.
"Fitar min a mota na"
Yafaɗa daɗan ƙarfi kaɗan.
Amai makon ta fita seta gyara zama tare da ƙara sautin fitar kukan nata.
Sunkuyar da kanshi yayi tare da sanya hannu ya toshe dukkan kunnuwanshi yana furta kalmar.
"Hasbinallahu wani'imal wakil,dan girman Allah ki saurara min hakan nan jina ke kaina kamar
zeyi bindiga bani son hayaniya da ƙara"
Yafaɗa idanunshi sunyi wani irin ja jijiyar kanshi ta tasa tai wani irin ruɗu ruɗu wanda hakan
seda yaɗan so bata tsoro.
Ganin gaskiyar maganar daya gaya mata cikin idanuwan shi yasan ya ta fara rage sautin kukan
nata.
A hankali ya kunna motar ya cigaba da tafiya cike da rashin kuzari.
Aranshi yana jin tsananin tausayin yarinyar don tabbas son dake masa ya zama son maso wani
ƙoshin wahala dan shikam daga basmah ya rufe ƙofar aure ko soyayya duk macen daze kula
sedai tausayi badai soyayyah ba..........
ANYA KUWA?
Muje zuwa........
Littafin *BA SON TA NAKE BA* Na kuɗine akan farashin Naira #300 kacal, 0078174806
starling bank shaidar biya tanan 08142105218, Idan kuma katin Mtn zaki Turo na 400
[8/2, 2:10 PM] ❤️❤️ : *BA SON TA NAKE BA*
{ Tausayi ne }
NA
*AUTAR MANYA*
ALHAMDULILLAHI INA TAYA ƊAUKA CIN AL'UMMAR MUSULMI MURNAR ZAGAYO WAR
SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI ALLAH YASA MUN SHIGA A SA'A AMIN HAPPY
ISLAMIC NE YEAR TO ALL MUSLIM UMMAH 1444.
*12*
Mayar da hankalin shi yayi ga tuƙin shi sedai ta cikin kunnen shi yana jiyo sautin fitar ajiyar
zuciyarta akai akai lumshe kyawawan idanunshi yayi ya kuma waresu bisa kwalta yana jin jan
ajiyar zuciyar tata har cikin ranshi.
Ba jimawa wahalallan bacci yayi gaba da ita ta langwaɓar da kanta a jikin kujerar motar tare da
cusa hannunta a tsakiyar cinyoyinta kamar mai jin tsananin sanyi.
Ta wutsiyar idanu yake kallon yadda take sauke numfashi da alamun kukan data yine ya
sanyata wannan baccin, sanya hannu yayi tare da ɗan ƙara ƙarfin na'urar sanyaya motar kana
ya kunna rediyo ya cigaba da bin karatun alkur'ani mai girman dake tashi ta cikin rediyon daya
kunnah.
Ahaka har suka ƙarasa cikin unguwar yayi parking a ƙofar gidan hajja Tare da kashe motar yayi
jugum sabida rashin sanin yadda zeyi wajan tashinta daga baccin data keyi.
Wajan mintina biyar suna zaune cikin mota ganin lokaci naja yasa a hankali ya soma kiran
sunanta kamar yadda ta gaya mai kuma hajja ma tagaya masa.
Murya can ƙasa kamar baya so yake furta.
"Khairy! khairy!! khairy!!! wanda seda ya kirawo har sau uku amman ummul ko gezau batayi ba
sema sabon fitar numfashin dake fita ta cikin hancinta.
Tsaki yaɗan ja kaɗan aranshi yana ayyana matsalarta yawa gareta.
Sannu a hankali yakai hannun shi saman fuskarta yaɗan taɓa kumatunta kaɗan da sauri kuma
ya janye hannunsa.
Tura baki tayi tana wani yamutsa fuska kamar yadda yara keyi idan suna mafarki cikin baccinsu.
Idanunshi ya tsira a saman fuskar tata yana kallon ikon Allah babu ko ƙiftawa yana mamakin
yadda wani bin idan tayi abu take komawa kamar ƴar ƙaramar yarinya.
A hankali ya kuma kai hannunshi saman nata dake tsakanin cinyoyinta ɗumi yaji a saman fatar
hannun wanda ya sanya yaɗan ji wani irin baƙon yanayi acikin jikinshi.
A hankali yasanya bayan hannunshi ya shafi saman fatar hannunta yana furta.
"Khairy wake up"!
Saukar sassanyar muryarshi taji acikin kunnenta tamkar cikin mafarkinta.
A hankali take buɗe kyawawan narkakkun idanunta waɗanda sukayi ɗan ja kaɗan suka
kumbura sabida bacci da kuma kuka se hakan yasanya fuskarta ta ƙara cika da wani irin
sahihin kyau mai shiga zuciya.
Cikin nutsuwa ta sauke ganinta a saman hannunshi daya ƙi ɗaukewa daga saman nata hannun
wata irin kwantacciyar suma ce a kwance ajikin hannun nasa sannan kuma hannunshi yafi nata
girma nesa ba kusa ba ahankali taɗan motsa kaɗan tana cino bakinta gaba kamar yadda take
ma hajja ko bamu. Kafin tayi wata irin hamma tare da ƙandarewa ajikin seat tana wata irin miƙa.
Da sauri ya ɗauke hannunshi a saman nata yana mai sosa kanshi da ɗayan hannunshi.
Ya wani basar tare da furta.
"Mun iso gidan hajja fitar min a mota"
Sannu a hankali ta wani juya kai tana kallon saitin windo babansu na waje yana wa yara faɗa
kirjinta taji ya bada sautin dam! da karfi kwalla ta taru cikin idanunta.
"Khairey kina ɓata min lokaci na"
Wani irin mutuwa jikinta yayi ta wani kwantar da kirjinta a jikin glass ɗin motar dama ze dauwa
ma yana kiran sunanta a haka tunda take bata taɓa jin wanda ya iya bawa sunanta haƙƙinshi
kamar shiba.
Tsananin faɗuwar gaban ganin abbanta da kuma sanyin jikin kiran sunanta dayayi yasanya
jikinta ya soma karkarwa ahankali sanyi ke ratsa saƙo da lungu na cikin gangar jikinta.
"Khairyyyyyy"
Ya kuma jan sunan a wannan karon daɗan zafin rai kaɗan.
Juyowa tayi tare da yin ƙwalƙwal da idanunta batare data iya furta mai ko kalma guda ɗaya ba
se faman girgiza mai kanta data ke faman yi
"Dallah malama kimin magana ko kifita ina miki magana zaki mayar dani mahaukaci yaushe na
zama abokin wasanki daga jiya zuwa yau zaki shiga rayuwata ki tarwatsan farin cikina"
Yafaɗi maganar tare da ware mata girman idanunshi masu sanya marar ji saurin nutsuwa.
"Dan Allah ka fita ka barni anan zuwa anjima babanmu ne a waje bani so ya ganni"
Tafaɗa tana wasa da yatsun hannayenta idanunta na zubar ƙwallah!!
Ɗan kallon ta yayi na mintina biyu kafin ya kawar da kanshi.
"Ni ban yarda ba ki fita kawai wani uban ne ze ƙi son yaga ƴarshi indai ba baki da gaskiya ba
wato laifi kika ma mahaifanki shiyasa na ganki a hotel ko? ƙilan baya son yawon da kike ne
shiyasa bakwa shiri"
Yafaɗa tare da kafe fuskarta da kallo yana son gano rashin gaskiyarta.
Rintse idanunta tayi don ko kaɗan bata son kallon daya ke mata hakan yana sanya zuciyarta
tsalle tamkar zata faso ta fito mata daga kirjinta sannu a hankali ta sakar masa kyakykyawan
murmushi mai ciwo tare da saurin ɓalle murfin motar ta fita.
Ya jima yana auna yanayin yarinyar kafin ya girgiza kafaɗun shi alamun su ta shafa tare da
ɗaukar ledar drugs ɗin ya fice.
ƙofar karamin gida mai ginin ƙasa na kusa da gidan hajja ya ƙarasa tare da ɗan rissuna wa
yana gaisar da wani dattijo fari dake faman masifa ga wasu ƙananun yara kamar ze duke su jin
muryar Barrister yasan ya yaɗan sassauta tare da miƙawa Aliyu hannu suka gaisa kallon
dattijon Aliyu yayi sosai wanda shigarshi ma kaɗai ta nuna talaka ne futik don babu alamar
wadata atare dashi sedai akwai tsantsar kamanni atare dashi da waccan yarinyar.
Miƙewa yayi daga rissunawar tare dayi mai sallama yabar wajan wanda har lokacin dattijon bai
dena masifar daya kema yaran ba.
Lokacin da ummul ta shiga gidan hajja ta tarar da wata mata fara zaune a saman kujera suna
hira da hajja da ɗan sauri ummul ta ƙarasa wajan matar wadda bazata gaza shekaru 40 ba ta
wani ɗane jikinta tare da sanya kuka tana furta.
"Bamu shine baki zo da wuri ba ko?"
Cikin tsananin tausayawa wannan matar da ummul ta kira da bamu take shafa kan ummul tana
furta.
"Kiyi haƙuri Umminah nima ban so nakai wannan lokacin banzo gareki ba to kinsan halin gidan
namu ne yanzu ma fakar idanun mutan gidan nayi na shigo"
Da sauri ummul ta ɗago tana furta.
"Aikam naga abba a waje yana sana'ar tasa wa yaran mutane"
Da alamar tsoro bamu ta ware idanu tare da furta.
"Hasbinallahu wani'imal wakil ya rabbi ka rufan asiri"
Tafaɗa tare sauri sanya hannu ta share zufar data karyo mata.
Dai dai nan Aliyu Dikko ya doko sallama cikin kamilalliyar muryarshi.
Duk suka amsa da hajja da bamu wadda ummul ke zaune ɗare ɗare saman cinyarta.
Ɗan rissunar da kanshi yayi tare da gaisar da bamu sannan ya mikowa hajja ledar tare da furta.
"Zani inda na sauka seda anjima zan dawo dan na makara a komawa gida yau"
Da sauri ya furta hakan kamar mai tsoron abin da ke kusa dashi.
Ba sakewa yabar falon hajja ta take mai baya tana furta.
"To bazaka tsaya kaci abinci ba?"
Murmushi ya sauke mai ƙayatarwa.
"Haba hajja wani abincin zanci kuma bayan wanda naci?"
Ɓata rai hajja tayi kana tace.
"Ai kace bakai kalacin safiya ba to kaga akwai na rana tunda wancan na safiya kaci ay"
Zira hannayen shi yayi cikin aljihun wandonshi.
Yayi taku ɗaya zuwa biyu
'zan dawo anjima kimin sakwara miyar agushi, waccan ledar kuma maganinta ne aciki za'a sami
ruwa mai ɗumi a gasa wajan sannan a shafa maganin ɗayan kuma tasha Allah ya sawaqe"
Yafaɗa tare da cigaba da tafiyar shi.
Godiya hajja tayi masa kana ta koma ciki da murna hajja ke gayawa bamu cewar wannan fa
jikanta ne Aliyu ɗan wajan ɗiyarta.
Sosai suka faɗa hirar Aliyu ita da bamu wanda ita kuma ummul ta lafe jikin mahaifiyarta tana jin
ƙaunarta na ratsa mata jikinta.
Seda akai la'asar sannan bamu taima hajja sallama tare da godiya ta wuce gida.
Da ƙyar ummul tayi sallah taci abinci taɗan kwanta dan wajan na mata zafi sosai.
Wajan yamma ƙannenta suka shigo a sace sukai mata sannu suka koma.
Abu kamar wasa ummul taƙi shan magani duk da irin faɗan da hajja ke mata ga uban zugin da
wajan keyi mata saka makon taɓawar da likita tayi, zuwa magariba zazzaɓi da ciwon kai ya
kamata har tana sheƙa amai hankalin hajja yayi masifar tashi dan ko sallar magariba ma
azaune tayi ta bayan ta idar ta jibga uban bargo ta kwanta saman gadon hajja tana rawar ɗari
har tana shiɗewa faɗan duniya hajja tayi shi wanda ita bata san daman ummul ciwonta haka
yake ba sam bata shan magani se taji kamar zata mutu.
Shiko Aliyu ya koma hotel cikin nutsuwa yayi wanka ya shirya cikin kayan shan iska coffee
yaɗan sha sannan ya kwanta bacci wanda bashi ya farka ba se wajan karfe huɗu alwalwa ya
ɗauro ya tayar da sallar la'asar bayan ya idar ya ɗauko system ɗinshi yana aiki da ita.
Bai tashi daga wajan taba se magariba alwala yayi tare da sauya kaya zuwa jallabiya fara ƙal
mai dogon hannu tare da baƙin 3qtr acikinta sallah ya tayar bayan ya idar ya zauna karatu
wanda a kwanakin nan kusan kullum seya yi.
Seda yayi sallar isha'i wajan ƙarfe 8:30 ya miƙe tare da nade sallayar yaɗan ƙara fesa turare ya
ɗauki wayarshi da keyn mota ya fita.
A hara bar hotel ɗin ya kalli sararin samaniya walkiya tana tashi hadari na haɗowa alamar
ruwan sama na gab da sauka.
Yana son yanayin damuna sedai baya son dukan ruwan sama dan muddin ruwa ya taɓa shi
seyayi zazzaɓi ko mura mai zafi
Da sauri ya shiga motar ya kunna ya ɗauki hanyar gidan hajja
Dayake yayi sauri yasa ya ƙarasa wajan ƙarfe 9:00pm sabida akwai tazara nesa ba kusa ba a
tsakaninsu parking ya gyara a kofar gidan tare da fitowa waje bayan ya kashe motar hadarin
unguwar su hajja ma har yaso yafi nacan inda ya baro ɗin tura gate ɗin yayi ya shiga daya ke
hajja tasan zezo shiyasa bata rufe gate ɗinta ba. Sallama ɗauke cikin bakinshi ya shiga falon hajja.
Da sauri hajja dake zaune tai tsuku duk al'amarin ciwon ummul ya ɗaga mata hankali ta ɗago
tare da amsa mai sallamar cikin kulawa.
Tsaida kallon sa yayi a fuskar hajja yana nazarin ta kafin ya furta.
"Hajja ta lafiya na ganki cikin rashin walwala? daman nace ma ammi a yaran can wani ya dawo
nan tace kinki amman zaman kaɗaicin bai da daɗi"
Yafaɗa yana mai zama a gefenta.
"Kai nifa salame na zuwa yau ma biki taje shiyasa bata zo ba,nifa duk damuwata akan ummi ne
kaganta can a gado se wani abu take gudu nake kar yarinyar mutane ta mutu"
Tafaɗa tana share hawayenta.
Ɗan jimm yayi tare da cewa.
"Au hajja bata sha maganin bane wani abunne kuma?"
Yafaɗa batare da ya