Author : Oum Ameer Category : Romantic Hausa Novels
💝 *BAHIYYA* 💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*Amina Ibrahim*
(Oum-Amir)
Follow me on wattpad:
@Oum-Ameer
*FREE PAGE*
*BABI NA ƊAYA*
Kaduna Road
Suleja Niger state.
BAHIYYA
A irin yanda jikina ke ƙyarma yana mazari tamkar ana kiɗamin goge a gidan 'ƴan bori shi zai tabbatar maka da irin tsananin tashin hankali da firgicin da ni ke ciki marar misaltuwa, ga wani irin zufa da yake fetsomin tun daga tsakkiyar kaina har zuwa tafin ƙafa ta kamar na haɗiyi kunama. Ban tabbatar da cewa fitsari na ke ba sai da wani jibgegen basamude ya kwashe ni da marin da sai da ya sani ganin wasu taurari, murya cike da ban tsoro yace.
“Don ubanki fitsari ma kika sakar min har ya gangaro zuwa ƙafata ko”
Wani irin ciri jikina ya ƙara ɗauka tamkar an jona ni a shocking, da sauri na shiga girgiza kai na cikin matsanancin kuka ina faɗin.
“Kayi haƙuri ban sani ba ne”
A irin dukan da suka yiwa Babanmu banyi tunani zai iya sake motsa ko da ɗan yatsan sa ba. Amma cike da jarumta irin ta tsayayyen uba ya ɗago da ƙyar yana faɗin.
“Dan Allah duk abinda zaku yi min kuyi amma ina roƙonku kada ku taɓamin mata ta da yara na, ku tafi dani kamar yadda kuka buƙata amma dan Allah kar ku cutar min da iyali n.....”
Daram! Muka ji saukar wata mummunar ƙara mai hirgita ruhin mai numfashi tamkar saukar aradu haka ta dirar mana a masarrafar sauraronmu, ashe harbin bindiga ne ya sauka akan ƙirjin Baba kai tsaye suka kashe shi har lahira.
Wani irin gigitaccen ihu na saki tare da zubewa akan gawar Baba somammiya.
Kalma Mama ta ɗauka tare da durƙushewa akan ƙafafunta tana faɗin.
“La'ilaha illallah - Muhammadur-rasulullah sallallahu alaihi wassalam! .Allahumma ajirni fi musibatina wa akhlufni hairan minha. Shi kenan Malam Jafar ka yi shahada ka tafi ka barni a duniya ni da Bahiyya da Nuhaira....”
Nuhaira da ta duƙunƙune kanta a jikin Mama ta runtse ido gam ko kaɗan bata sake motsawa ba sai kukan da take wanda yake bayyanar da tsantsar tsoro da tashin hankali. Ganin baba shimfiɗe a ƙasa matacce yasa lokaci guda taji tsoron ya fita daga zuciyar ta ta faɗa kan Baba tana kuka mai ban tausayi.
Daga haka suka tattara duk kuɗin da suka karɓa daga hannun Baba da Mama suka fita kai tsaye suka bar gidan.
“Babaaaa... Dan Allah ka tashi Baba, wayyo Babaaa....”
Da ƙarfin tsiya Nuhaira ta shiga jijjigani tana faɗin.
“Anty Bahiyya! Anty Bahiyya dan Allah ki tashi mafarki fa kike yi”
A zabure na miƙe zaune tare da saka dukkan ƙarfina na cakumeta na rungume gam,Ina faɗin.
“Nuhaira Baba...Baba an fita da gawar shi shi kenan ba zai dawo ba...”
Hankaɗo ƙyallen ɗakin namu Mama tayi tare da duba agogon da ke kan screen ɗin ƙaramar wayar hannun ta, kusan ƙarfe ɗaya saura na dare ya nuna mata,ƙara sa shigowa ɗakin tayi tare da dakamin tsawa tace.
“Wai Bahiyya ke ba zaki fawwalawa Allah al'amarin ki ba ne? Ubangiji shi yake jarabtar bayinsa yadda ya so, ya baka ko ya hana ka duk yana daga cikin ikon sa. Jafar bawan sa ne shi ya kawo shi duniyar kuma ya ɗauke abinsa, kukan ki, ihun ki, duk abinda zaki yi wallahi ba zai dawo da malam duniyar nan ba, gwara ma tun wuri ki sauya tafiyar ki”
Cikin gunjin kuka mai ban tausayi na shiga girgiza kaina still ina lafe a jikin Nuhaira ina faɗin.
"Wallahi Mama ba laifi na bane, babu wani dare da zai zo min in kwanta bacci ba tare da nayi mafarki da wannan baƙar ranar da aka kashe Baba ba, wadda har in koma ga mahalicci na ba zan manta da ita ba....”
Jikin Mama ne yayi sanyi. A hankali ta zo ta zauna kusa damu tare da kwantar da murya tace.
“Bahiyya! Ki yi haƙuri, na san da ciwo sosai, amma wanda ya mutu komai zaki yi ba zai dawo ba, na sha faɗa miki ki riƙi azkhar ya zame miki abokin hira, duk za ki shiga bacci ki yi alwala kiyi addu'a, ki tashi cikin dare kiyi sallah ki roƙa masa gafara a wurin Allah, shi kadai zaki yi masa ki tabbatar masa ya bar 'ƴa' ƴa masu yi masa addu'a, idan kuma kin wayi gari ki yi haƙuri ki saki ranki kiyi walwala kamar yadda 'ƴar uwarki ta ke yi, rayuwa ba za ta ci gaba a haka ba. Dole ki koyi rayuwa a duk irin yanda ta zo miki. Tabbas mun rasa jigo, mun rasa linzamin kamawa amma ya zamuyi? Wannan ita ce ƙaddarar mu kuma ya zama dole mu amshe ta hannu biyu muyi godiya. Sannan mu sake shirin yanda zamu rayu domin mu ci gaba da rayuwa cikin aminci,
saboda haka kiyi haƙuri Bahiyya ki rage wannan damuwar a ranki, shekara ɗaya har da watanni ya ci ace kin haƙura saboda kin fi kowa sanin wanda ya mutu ba zai dawo ba”
Miƙe wa nayi na fita waje jiki a saɓule nayo alwala na dawo na shimfiɗa sallaya na fara nafila, duk mama tana zaune tayi tagumi ita ma da irin abinda ta ke saƙawa a cikin ranta.
Ganin na duƙufa yasa ta miƙe ta wuce ɗakinta, Nuhaira ma gyarawa tayi ta kwanta abinta tare da lumshe ido tana nazarin rayuwar mu ta baya har ɓacci ɓarawo ya sace ta.
************
Washe gari mun fito ni da Nuhaira muka yi duk wani morning routine ɗin mu, bayan mun kambala naga kusan ƙarfe goma amma Mama bata fito ba yasa na shiga ɗakin ina faɗin.
“Mama wai lafiya har yanzu baki fito ba, ga kunun ki har ya soma yin sanyi”
ɗago kanta tayi tana daga kwance tace.
“Bahiyya ciwon da na faɗa muku ina ji a ƙirjina kwana biyu fa yau ya so ya matsamin”
Cikin damuwa nace
“Subhanallah! Sannu Mama, bari to in fita wurin mai chemist in samo miki magani, Nuhaira sai ta tafi kasuwar tunda naga kayan miyar duk sun ƙare kuma mutane sai shigowa nema su ke, ba zamu iya kaiwa ranar kasuwa ba kayan miyar ba”
“To wa zaiyi niƙar injin ɗin naji yara sun taru waje?”
“Daman ni ce da niƙa yau Nuhaira kuwa bada Kayan miya, amma sai suyi hak'uri su kai niƙan wani wuri har zuwa yamma mu gani..”
Lallaɓawa tayi ta miƙe zaune tace.
“A'a, tafi ki samomin maganin in sha, idan ciwon ya faɗamin sai in niƙe musu ke kuma ki je kiyi wa Malama kitsonda ta aiko tun jiya tana neman ki”
Miƙewa nayi ina faɗin.
“Af! Ni wallahi har na manta da zancen kitson malama, bari to in yi sauri in dawo”
Bayan ficewa ta Nuhaira ta shigo ɗakin da kuɗi a hannun ta tana faɗin.
“Sannu Mama ya jiki?”
Mama ta amsa.
“Jiki Alhamdulillah Nuhaira. Naira Nawa ne nan kika haɗa?”
Tana ƙara murza kuɗin tace.
“Dubu goma sha ɗaya ne da ɗari bakwai na ɗanyun kayan miya, dubu bakwai kuma na magi da kayan tarkace”
“To yi maza dan Allah Nuhaira kada ki tsaya ko ina, ki yi ki dawo kada mutane su tsaya suyi ta jira”
Hijabi ta zuba ta fita tana faɗin.
“In sha Allah kamar walkiya Mama zaki ga naje na dawo yanzu, kiyi min addu'a”
“To Allah ya tsare ya sa a dawo lafiya”
Cikin mintuna da basu gaza ashirin ba na dawo gidan. Kunun na ɗauko mata tasha na ɓalla mata magani na ƙwaya da na ruwa tasha sannan na shirya na ce mata na tafi gidan Malama Rabi.
Cikin ikon Allah ko a hankali taji ciwon ya washe, hakan ya bata damar tashi ta shiga niƙawa yara abubuwan da suka kawo. Mama er hustlen ce ko can baya lokacin da baban mu yana da rai, yana da shagon sa itama bata fasa nema ba. Yanzu ma da ya kasance baya nan dole ta ƙara ƙaimi wurin nema domin ta kula damu.
**************
Life Camp.
Abuja Nigeria
Hanifah
Kwance ta ke akan rantsatstsen makeken cushion ɗin palourn ta tana kallon wani Korean film cike da nishadi da kwanciyar hankali. A yadda ta natsu sosai ta zuba Fitilun ganinta akan tvn nan tana murmushi, ko ina na parlourn tsaf yake sai walwali yake tamkar yanzu aka halitta shi saboda tsabtar sa, ga sassanyar Acn da ya gauraya da sihirtaccen ƙamshin turaruka masu azabar ƙamshi da wanzar da kwanciyar hankali ga wanda ya ke ɗakin. Ga laptop da wayoyinta nan zube a gefen ta, yadda tayi ɗai-ɗai tana kallon tana nishadi shi zai tabbatar maka da cewa ba ta da wata sauran damuwa a duniya.
Jin motsin fitowar mijin nata yasa ta miƙe da sauri tana wani irin murmushi mai kama zuciya ta nufe shi tana faɗin.
“Har ka fito?”
Tsadadden agogon da ke ɗaure a tsintsiyar hannunsa ya duba shima yana mai mayar mata da murmushin yace.
“Getting to 9:00am Hanifah, I'm already late and I have told you since yesterday that the meeting is 10:00am, but sai da kika san yanda kika yi kika sakani yin latti, Mahi is waiting for me, so ki bar breakfast ɗinki kawai na gode, ki sa a nema min lunch kafin na dawo”
Dariya tayi tace.
“Sure! But Ko da ma ace ka dawo baka same ni ba, the food will be ready, am gonna meet with Rasi'ah, akan zancen tafiyar nan tamu Cyprus....”
Side hug ya bata tare da kissing forehead ɗinta yayi gaba da sauri yana faɗin.
“Let's catch up on phone Hanifah, Mahi sai Kirana yake”
“OK bye”
Kallon shi take har ya ɓace wa ganinta, murmushi ta saki tare da komawa kan cushion ɗin taci gaba da kallon da ta ke a tv.
**************
Farooq
At around 1:30pm bayan sun dawo daga sallahr zuhr, suna cin lunch ɗin da Mahid yasa aka kawo daga gidan sa,ya kalli Farooq ya ce.
“I never thought the meeting would go smooth like this Wallahi, Saboda yanda naga mutanen nan zuwan farko sai a hankali”
Dariya Farooq ɗin yayi yace.
“That's the challenges of life. We must plan on how to deal with our business partners always, along the line ka shirya shirin amsar faɗuwa duk lokacin da abubuwa ba su zo maka kamar yadda kayi expecting ba. A fuska sam kamar ba zasu yi daɗin hulɗa ba amma daga baya dubi yadda muka ƙare da su”
Gyaɗa kai Mahid ya yi yace.
“Haka ne fa, bari in maka ta karin maganar malam bature yace wai 'do not judge a book by it's cover'. While Ya Madinah ta ke? Kwana biyu”
Wani irin sassanyar ajiyar zuciya ya saki yana murmushi yace.
“Madinah is doing Good Mahi, Ina missing ɗin tsohuwar nan kwana biyu wallahi, gashi aiki ya hana min zuwa ganin ta, ita kuma ƙiri-ƙiri taƙi Abuja wai ba zata zauna da ni ba”
With full confidence ya Kalli Farooq ɗin cikin idonsa yace.
“Farooq mi yasa zata zauna da kai? Zama ba zai yi tsakanin ta da Hanifah ba, dama ace kun haihu ne, ko don saboda yaran zata zauna ko kuma ta riƙa zuwa a kai a kai”
Taɓe baki yayi yace.
“Haihuwa? Ba saboda haihuwa ba dai kawai bata so zuwa ba ne...”
“Farooq! Madinah ko bata furta maka ba nasan a cikin ranta tana da burin ganin 'ƴa' ƴan ka a duniya. Aure shekara bakwai! At least ka saka hankali da lissafi a cikin wannan maganar, kai kaɗai ta raina ƙwallin ƙwal nasan abu mafi farin ciki yau ta gan ka da 'ƴa' ƴa....”
Hannu ya ɗaga mishi alamar baya son zancen yace.
“Mahi please! Mubar wannan maganar, Hanifah ta ishe ni rayuwa ita da Madinah, ni ka ɗai ne na rayu a duniya ta sai yanzu da na samu Hanifah, babu kalar farin cikin da bata bani, babu abinda muka nema muka rasa....”
Miƙewa Mahid yayi tare da dangwarar da spoon ɗin hannunsa akan plate ɗin abincin da kwata kwata basu yi masa cokali uku na kirki ba, cike da jin haushi yace.
“Farooq ka daina yi min zancen banza a nan, aure ba 'ya' ƴa miye ribar sa? Manzon Allah S. A. W ya faɗamana cewa muyi aure mu hayayyafa zai yi alfahari da hakan ranar gobe ƙiyama. Sannan ya sake faɗa mana a cikin wani hadith ɗin cewa, yayin da ɗan Adam ya mutu dukkan ayyukan sa zasu yanke, fa ce abubuwa guda uku zasu rakasa zuwa ƙabarinsa, bayan an binne sa dukkan su zasu dawo ɗaya ne kawai zai tsaya tare da shi a cikin ƙabarinsa,kasan mi ne ne shi? Aikin sa walau Hairan ko Sharran. Abubuwan da ya bari kuma a doron ƙasa waɗanɗa ba zasu yanke ba matukar ya gina su a lokacin da yake raye a ban ƙasa su ne:Sadaka mai gudana, na biyu waladun salih yaro na gari wanda zai riƙa yi masa addu'a a lokacin da baya raye, na uku ilimin da ya wanzar a ban ƙasa mutane na ci gaba da amfana da shi. Ka gayamin idan baka haihu ba ta ina zaka samu yaron da zai riƙa yi maka addu'a idan ka mutu? Tun wuri ina kiran ka da babbar murya ka aje wannan banzar aƙidar yahudancin da ka ɗaukar wa kanka tun lokaci bai ƙure maka ba ka haihu, 'ƴa' ƴa su ne farin ciki sanyin idanuwan iyayen su matuƙar sun taso akan turba madaidaiciya”
Daga haka ya kwashe kayan sa ya juya da nufin ficewa daga Office ɗin.
Cike da ɓacin rai Farooq ya ce..............
Ki biya 500 ki sha karatu sister
3132703269
First Bank
Amina Ibrahim
💝 *BAHIYYA* 💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*FOLLOW ME ON WATTPAD:*
*@UMMU-AMEER*
*PAID BOOK 500*
*3132703269*
*FIRST BANK*
*AMINA IBRAHIM*
*08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA BIYU*
“......... Mahi ji yanda kake magana dani tamkar ni ba shugaban ka bane, what's your problem about my marital life kana da matsala da hakan ne?”
Juyowa Mahid ya yi yace.
“Kai mai gidana ne saboda ina aikin a ƙarƙashin companynka and again don't forget I'm also a friend to you. So if you want zaka iya cewa na ajiye maka aikin ka saboda na faɗa maka gaskiya amma ba zaka iya datse iyakar abotar mu ba Farooq”
Daga haka ya juya ya fice daga ma'aikatar baki ɗaya ya nufi gida, yana ƙara jinjina al'amarin Farooq da matar sa Hanifah. Abu wasa wasa tun yana ɗauka amarci ne kawai suke morewa idan suka gama za su nemi su haihu amma sam a iya yanda ya fahimci Hanifah sam bata kawo zancen haihuwa ko kaɗan idan aka yi mata kuma ko da wasa bakin gaskiyar ta zata kafe cewa, 'ya' ƴa problem ne saboda haka ko babu su mutum zai iya rayuwa, kuma yayi farin ciki.
Mahid Baffa abokin Farooq ne tun a UK Allah ya haɗa su wurin karatu, sosai ta su ta zo ɗaya wurin halayya da mu'amalantar juna. Shi Mahid ɗan Kano ne yayin da Aiki yanzu ya kawo shi Abuja tare da Farooq ɗin.
*************
BAHIYYA
Sai kusan ƙarfe biyar na yamma na dawo ma gidan ina mai faɗuwa zaune a gindin bishiryar da suka shimfiɗa tabarma suna zaune na ce.
“Wash Allah! Wallahi duk na gaji jikina ji ni ke tamkar an naɗa min duka, aikin lalle da kitso wallahi akwai wahala...”
Nuhaira tana dariya ta ce.
"Amma kuma akwai kama naira ba. Ko da yake mutanen basa son biyan kuɗin ƙwarai sai dai kayi musu dan Allah dan zaman tare”
Girgiza kai Mama tayi tace.
" Ku dai har yanzu yara ne, ko naira goma ake samu ai yafi maganin zaman banza kuma yau da gobe in dai ana saka haƙuri sai naira gomar ta koma naira ɗari.”
Cike da zumuɗi Na ce.
“Ai Mama na manta ma in yi miki albishir, Malam ta ce zata riƙa zuwa dani cikin gari domin in riƙa yiwa mutanen ta kitso da lalle tunda Maryam ta yi aure. Tace kullum sai damunta su ke yi da kira wai ta kawo musu mai lalle da kitso...”
Shewa Nuhaira tayi tare da tafa hannu tace.
“Shikenan Aunty Bahiyya Allah ya kawo miki hanyar samun biyan kuɗin kitso da lalle mai tsoka domin su mutanen nan sun san darajar wahalar mutum, kamar yadda Maryam ɗin ta ke faɗa. Ki ji fa yanda cikin unguwar nan a ke ta zagin ta wai ta cika girman kai yanzu kowa ba ta iya yiwa lalle da kitso a yankin nan namu saboda tana zuwa manyan gidaje cikin Abuja tana kama kuɗi. Amma ji dan Allah irin sayayyar kayan kitchen ɗin da tayi....”
Katse ta Mama tayi da faɗin.
“Nuhaira wuce ki duba mana sanwa kinji”
“To lallai kam, daga fara magana kin a re kin yafe kamar ke nike faɗawa maganar. Ni mi kike dafa mana ne yau? yunwa ma ni keji”
Daga bakin Murhun Nuhaira