Author : Oum Ameer Category : Romantic Hausa Novels
dawo gida. Bayan mun shigo gida nabawa malama Rabi kuɗi tace min a'a in riƙe duka nawa ne itama ta sallameta. Nuhaira uwar kaɗaɗi ita ta buɗe ledar bayan Malama ta tafi. Turmin atamfa ne da kayan cusmetics masu tsada na 'ƴan gayu. Kuɗin kuma da ta ban daban dubu ashirin ne cif. Mamaki ya kasa ɓoyuwa akan fuskokinmu musamman Mama, zunzurutun dubu ashirin da biyar kai tsaye kamar tsintuwa. Addu'a tayi ta min ni dai Nuhaira tana yi mana fatan alheri wanda hakan ba ƙaramin daɗi yake min ba.
*************
Jumeirah Lakes Towers (JLT)
Dubai, UAE.
Ranar Friday itace wadda ta kasance ranar ƙaddamar da center Hanifah kamar yadda tayi buri.
Wurin ya ƙayatu iya ƙayatuwa fiye da yadda bata zata ba, Daddy ya shirya mata taro wanda har a cikin ranta taji ta ƙayatu ainun sannan kuma ya fitar da ita kunyar baƙin ta. Babu abinda zata cewa daddy sai godiya................
*OUM-AMEER *
💝 *BAHIYYA* 💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*AMINA IBRAHIM*
(OUM-AMIR)
*WATTPAD:*
*@UMMU-AMEER*
*PAID BOOK 500*
*3132703269*
*FIRST BANK*
*AMINA IBRAHIM*
*08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA BIYAR*
............... A makare ya iso wurin shiyasa bai samu haɗuwa da ita ba sai a filin taron. Tunda ta tunkaro shi ya kasa ɗauke idon sa a kanta domin ba ƙaramin kyau ta masa ba. Wata arniyar Maroon Red carpets gown ce mai jela a baya a jikinta wadda ta bi jikinta ko ina ta manne tamkar an bita da fenti, an yi mata tsaga daga guiwar ƙafarta ta ta dama a ta gaba zuwa ƙasa, wuyan rigar V shaped ne yayin da ɗayan hannun rigar yake dogo duk an bishi da tsagu sai kuma ɗayan aka yi shi guntu cure da chipom. Gashin kanta kuma yasha gyara wanda aka nannaɗe wuri ɗaya a bayan ƙeyar kanta. Ta sha kyau sosai mutane sai yabawa suke. Daga inda Mahi yake zaune yana hango ta ji yake ranshi yana mishi wani iri, wai wannan matar Farooq ce, wai nan ita musulma ce mai sallolli guda biyar, kuma ƙarin abin haushin ma wai ga iyayenta a wurin duk suna kallon ta kuma ko a jikin su, sai kuma ya juya ya kalli dressing ɗin mamar ita kanta da kuma ƙanwar ta Hamrah kawai sai naga yayi murmushi tare da girgiza kai a ranshi yace wata Wayewar dai in dai haka take Allah ya tsare mu da ita.
Murmushi suka sakarwa juna ita da Farooq ɗin ta , a hankali ya tare ta tare da bata wani hurt hugging a hankali cikin shauƙi ya ɗora soft lips ɗinsa akan bare neck ɗin Hanifah yayi kissing ɗinta sannan yayi taking deep breath ya shaƙi ƙamshinta Mai ɗadi sannan ya janye ya saita idanuwansa a nata a hankali ya furta mata.
“ I so much miss you Hanifah, without you my life is going to be miserable. You look very beautiful and adorable wife, I'm really proud of you, Ina yi miki fatan nasara da fatan albarka ga duk abinda kika sa ma gaba Indai na alkaiiri ne, Grand Ma Itama tace in faɗa miki haka”
Hawayen farin cikin da suka gangaro mata ne tayi saurin sharewa tare da jin daɗin Kalaman mijinta with so much happiness tace.
“Thank you Farooq, you are the best husband ever, I really appreciate, a yanzu na gama sakankancewa da cewa duk abinda ka ke min da zuciya ɗaya kake yinsa a matsayi na na matarka, ka bani matsayin da ba kowa ne irin namiji ne ya ke iya bawa matar sa ba, I'm proud of you for being my lovely and caring husband, ban san ta ya zan iya gode maka ba....”
Ɗan yatsan sa ya ɗora akan lips ɗin ta yace.
"Shhh! kullum ni kawai abinda ni ke so Hanifah muddin zaki ƙaunace ni ki So ni, ni hakan ma is ok for me. I love you”
Hugging ɗin shi tayi tana murmushi tace.
“I love you so much Farooq”
Kawai ji sukayi ɗakin ya ɗauki tafi raf-raf-raf. Ana ihu ana yi musu kirari. Bayan like 20mnt haka aka gama shirya komai, aka shiga gudanar da ƙayataccen bukin yadda ya kamata.
Farooq bai san Mahi na wurin ba sai bayan da aka gama taron duk rabin mutane sun watse sannan ya gansa kawai yana masa murmushi. Ba ƙaramin mamaki ya bawa Farooq ba har bai san lokacin da yace.
“Mahi you are the most crazy friend in this world, when did you arrived here?”
Dariya Mahi yayi yace.
“While tunda Baban Soyayya ya kama Hanifah ya riƙe ta kamar zai cinye ta”
“Mahi I have every right because she's my wife, so don't judge me, kayi Abinda ya shafe ka”
Hannayensa ya ɗaga sama yana dariya yace.
“I rest my case”
Murmushi Farooq yayi yace.
"Better.” sai kuma ya sake kallon Mahi ɗin yace.
“ And thank you for coming, I really appreciate your presence.”
“Kafi haka a wurina Farooq, Ina Hanifah murna...”
Da sauri Farooq ya ɗaga masa Hannu tare da ciro wayar sa a pocket ɗin sa yace.
" Wait! Let me call her she's around here Sai ku gaisa zai fi”
Cikin mintunan da ba su gaza sha biyar ba ta iso wurin. Hannunta ta saƙala cikin wuyan hannun Farooq tana murmushi ta kalli Mahi tace.
" Mahi welcome”
Murmushi yayi yace.
“Congratulations Mrs Mai-gishiri, Allah ya sanya alheri yasa rai aka yiwa, ya kuma ƙaro dimɓin nasarori”
“Amin, thank you Mahi”
Daga haka ta juya ta ci gaba da sallamar baƙin ta. Su ma su Farooq ɗin daga nan suka wuce wurin nasu yi.
Washe gari ya zo gida ya same ta, bayan sun gama gaisawa da Momma ya wuce zuwa ɗakin da take, Hamrah na zaune akan couch ita kuma Hanifah tana tsaye tana saka kayan ta bayan ta gama mulke jikinta da mayuka. Da sauri Hamrah ta miƙe tana murmushi tace.
“Good morning Yah Farooq”
“How are you Hamrah and studies?”
Tace.
“I'm doing great Yah Farooq, Ina ta yaku murna da ƙarin wannan nasarar”
Yace.
“Thank you Hamrah. Allah ya albarkaci rayuwar ki...”
Hanifah ta karɓe zancen tana dariya tace.
“Ya kuma bata miji mai nagarta kamar Farooq ɗina”
Dariya Hamrah tayi tace.
“A'a fav. Sis wanda yafi shi ma zaki ce”
Dariya suka saka su duka ukun sannan Hanifah tace.
“Ina ga kin fara shan ƙwaya Hamrah, because ba zaki taɓa samun mijin da yafi shi ba... Oya get out please allowed couples to have some privacy”
Taɓe baki tayi tare da ɗaga shoulder tace.
“OK oo! Hamrah doesn't have problem with that, I can excused you love bird”
Daga haka ta fice ta barsu. Kamar jira yake Hamrah ta fita saboda ba ƙaramin jan hankalin sa Hanifah tayi ba, da sauri ya matsa in da take ya rungumeta ta baya gam-gam ya ɗora fuskar sa akan wuyanta tamkar ya haɗiyeta haka ya keji.
Tana murmushi tace
“Do you missed me?”
Yace.
“what! Wife are you teasing me? Common you too you know word can't express how much you I missed you”
Daga haka ya yi turning ɗinta tayi facing ɗinshi a hankali ya shiga kissing ɗin lips ɗinta romantically with his hand rubbing every part of her body passionately.
Ba laifi itama tasan cewa tayi missing fitinanne mijin nan nata saboda haka bata hana shi ba sai da taji ya fara ɓalla hook ɗin bra ɗinta da sauri ta janye tana kallon shi tace.
“Please don't...”
Cikin wani irin mawuyacin hali ya watsa mata rinannun idanuwansa da suka rikiɗe suka canja launi, murya a dishashe yace.
“Please Hanifah allowed me, idan kika hanani ban san ya zanyi ba.... Dan Allah Hanifah”
“Farooq I'm sorry, yanzu haka ina da muhimman mutanen da suke jirana a Office beside the whole staff are there waiting for me Idan na bar su hakan bai kyautu ba. Kayi haƙuri kawai har na dawo gida dan Allah tunda ba tsere maka zan yi ba.”
Jingina bayansa yayi a jikin wardrobe ɗin ɗakin with so much heart break yace.
“Buht I thought we are going back together Hanifah?”
“What! No gaskiya kaima kasan komawa na gida yanzu ba zai yi yu ba, I have to ensure that everything has fall apart kafin na koma gida”
Wani zafi yaji zuciyar sa nayi masa, ya tabbata idan bai yi da gaske ba Hanifah zata saka mishi ciwon zuciya. Cikin jin haushi yace.
“Hanifah ya ya kike so in yi da rayuwata ne? Shin shi wannan aikin na zuwa lahira ne? Of all the time that you have spend with out me ke ko kaɗan baki ji cewa a ranki ya kamata kiyi min adalci ba, Hanifah ke ba yarinya ba ce atleast ya kamata ki riƙa tunani irin na matan aure saboda you are not alone, you are married remember ni ba saurayin ki bane, ni mijin ki ne, hakan kike yi zunubi ne Hanifah Allah baya so....”
Hannayenta ta sanya a waist ɗinta tayi burning face tace.
“OK! Halin ku na maza yau kake so ka nuna min Farooq? What's the big deal here? Ban San nayi maka wani abun da har zaka ji haushi ka fara ihu haka ba. You are my husband but I know that I have my right too, you have no right to force me akan abinda banyi niyya ba ka gane?kuma magana ta ƙarshe I'm not going back with you Idan na gama settling business ɗina zan dawo”
Daga haka ta ɗauki purse ɗin ta ta wuce ta ƙyale shi, tana ji yana ta ihun kiran sunan ta amma ko sau ɗaya bata waiwayeshi ba.
**************
Abuja
Nigeria
Tunda ya dawo gida yake kwance bashi da lafiya, sai da Mahid yazo gidan yaga situation ɗinsa cikin gaggawa ya kira masa family doctor ɗinsa wato Dr. Nicholas. Zazzaɓi mai zafi ne ya kama sa, Dr. Nicho yayi mamakin ganin Mai-gishiri a wannan yanayin. Ba ɓata lokaci ya bashi taimakon gaggawa bayan ya samu bacci ya ɗauke sa ya shiga tambayar Mahi Ina Madam Hanifah ne, shine ya faɗa masa ai taje wurin familynta, shine ma ya saka Farooq ɗin Zazzaɓi. dariya ce ta kama dr. Nicho ta yaya za'a ce don matarshi ta tafi zai kamu da irin wannan zazzabi haka to idan haka ne ko duk zata tafi ya kamata ya riƙa binta suna tafiya tare. Bayan sun gama firah suka tafi tare ya karɓo masa magani ya dawo gidan yasa cook suka shirya abinci ya kai mai ɗaki amma har yanxu bai farka ba.
Ya daɗe har kusan yamma sannan ya farka yana buɗe ido yaga Madinah a gefen sa.
Cikin mamaki yace.
"Madinah! Yaushe kika zo?”
Matsowa tayi tare da share hawayen idanunta tace.
“Sannu Faruku, dan Allah kayi min alƙawarin ba zaka sake kwantawa ciwo ba, wallahi ba zan iya jurewa ba”
A hankali ya tashi zaune yana murmushin ƙarfin hali ya share mata hawayen ta yace.
“Ji wannan tsohuwar waye yace miki bani da lafiya da har zaki zo ki na min kuka a nan?...”
“Don't joke with me Faruku, I'm serious”
Hannunta ya sanya cikin nashi yace.
“Calm down please, you know that I'm a strong person, kawai guntun zazzaɓi ne kuma in sha Allah shikenan na warke daga yanzu ma”
“Allah yasa haka. Ga abinci kaci, mi kake so in zuba maka?”
Yace.
“Duk abinda kika bani Madinah zan ci, na gode”
Da kanta ta shiga bashi abincin a baki kamar sanda yake ƙarami, bayan ya gama ta zauna kusa da shi tana shafa suman kansa can cikin zuciyar ta kuma fal take da tausayinsa.
Shiru ne ya ratsa tsakanin su na dogon lokaci sai daga baya ya kira sunan ta yace.
“Grand Ma”
Tace.
“Na'am Faruku”
“A karo na barkatai kuma na ƙarshe ina roƙonki da ki faɗamin su waye mu?”
Gyara zamanta tayi da kyau tace.
“Yanzu kuwa zan faɗa maka abinda na daɗe ina ɓoyema. Asalin sunana Rebecca Samuel ne, mijina kuma Carlos Ishaya, Asalinmu mu en jahar Enugu ne, mu Christian ne gaba da baya lokacin da ƙaddarar kasuwanci ta kawo Carlos Kaduna sai muka dawo nan da zama a hankali sai muka karɓi addinin musulunci na canza suna zuwa Madinat Carlos kuma ya canza zuwa Modu garba, kuma mun sani cewa zunubi ne daga cikin dangin mu duk wanda ya canza addini to daga ranar ya fita daga cikin family har abada za'a ɗauka cewa mutuwa yayi, muna nan zaune lafiya har na haifi Azizat wato mahaifiyarka muka yita renonta cikin kulawa tayi karatu har ta gama Ss3 sai ga wani mutumin Nijar yazo neman aurenta har ni na ce ban amince ba amma Kakan ka yace sam tunda shi take so dole shi zamu bata dole ba dan na so ba aka yi mata aure da Lawali Mai-Gishiri. Bayan auren suka tafi can Birnin Yamai har Allah yasa ta samu cikin ka aka haife ka bayan kayi shekara biyu suka shirya suka zo nan sai da tayi wata biyu a gida tana shirin tafiya na nace da magiya akan dole sai ta barmin kai bata tsaya jayayya ba ta haɗa dukkan ka yanka ta ajiyemin sannan baban ka yazo ya ɗauke ta suka tafi, a wannan ranar muka samu mummunan labarin cewa sun yi haɗarin mota sun mutu haka aka kawo muna garwasu domin basu yi nisa da barin garin Kaduna ba accident ɗin ya faru muna nan kuma muna rainonka ni da Kakanka shima tsakanin sa da Azizat 3years ne. Mijina yayi fice sosai domin sannannen ɗan siyasa ne kuma ɗan kasuwa. Da Dukiyar da ya tara na ci gaba da yin business ina kula da kai a hankali na buɗe Almadinah Textile and more a nan Kaduna, daga nan kuma bayan ka gama secondary nasan kasan da wayonka na ɗauke ka mu ka koma UK kayi karatuttukanka Daga baya muka dawo gida Nigeria. Dangin Mahaifinka basu san in da muke ba kuma har yau babu ko tsuntsu da ya taɓa zuwa ya ce min yazo neman Lawali da Azizat. Kaji yadda rayuwar mu ta kasance Faruku.
Cike da Mamaki yace.
“To miye abin ɓoyo a nan Grand Ma? Ko wane bawa ai da irin ƙaddarar sa”
Sai kuma yayi hugging ɗinta yace.
“Da kin sani da baki wahalar da kanki wurin ɓoyen wannan maganar ba har zuwa tsawon lokacin nan, Allah ubangiji yaji ƙansu da Rahma mu kuma ya kyautata tamu idan ta zo.”
“Amin. Ni ɓoye maka ne kada kayi ta jin ba daɗi”
Yace.
“Nothing like that Madinah, Dan Allah ki daina wannan kukan da kike wallahi bana so, Allah shi ne mai yadda yaso da bayin sa, sannan ina alfahari da ke, ko ban samu wasu dangi ba ke kaɗai da Hanifah kun ishe ni farin ciki, you meant so much to me Madinah, I love you. Kawai dai Ina so in san ina ne tushen mu kuma yau naji shi kenan”
Tace
“Hakane, Allah yasa mu dace. Tashi ka lallaɓa kaje kayi Sallahr magrib wata ƙila ma ko asr da zuhr ba kayi ba. Ni na san kana da sakaci da Sallah Faruku bafa abune mai kyau ba”
A hankali ya sauka yana faɗin.
“in sha Allah Grand ma zan gyara”
**************
Washe gari da Mahi yazo duba shi suna zaune Parlourn sa bayan sun gama gaisawa kamar ba zai yi magana ba sai kuma yace.
“Mahi please ka bani shawara mi zanyi Hanifah ta fahimci irin rayuwar da nike so da ita? Can you imagine Hanifah telling me that she knows her right ni ban Isa komai da ita ba, bayan nasan ni mijinta ta ne”
Gyaran Murya Mahi yayi yace.
“Da farko ina baka haƙuri Farooq, kasan wasu matan basu san abinda ya kamata ba sai an lurar da su suke ganewa, kayi haƙuri Kayi ta lallaɓata kana nuna mata hanya in sha Allah watarana zata fahimce. Abu na biyu kuma shawarar da zan baka nasan ba lallai ne tayi daidai da ra'ayin ka ba, amma Ina mai baka shawara zama a haka ba zai sa ku samu ci gaba a rayuwar auren ku matuƙar ba haihuwa kuka yi ba, wato Farooq ina so kasan wani abu, ɗaukar cikin ɗanka da mace zata yi har ta haife shi yana ƙara muku bonding da kafa wata ƙauna ta musamman ko don 'ƴa' ƴan nan. Duk wannan borin da take yi maka daga zaran kun in sha Allah zaku samu fahimtar juna da ita, sannan kuma Farooq ko don tsohuwar nan ya kamata ka tausaya mata ta samu yaran da zatayi wasa da su kafin ta koma ga Mahaliccin ta, zata yi matuƙar farin ciki. Dan Allah kayi tunani Farooq I'm not forcing or commanding, ni kawai Mai bayar da shawara ne. Yara farin ciki ne, rahama ne Farooq.”
“Sannan abu na gaba Farooq, Wayewar Hanifah tayi yawa, wallahi idan baka yi wasa ba sai kun shiga wutar Jahannama domin kuwa ku musulmai ne, kasani a cikin Alƙur'ani mai girma Allah yace ku tsare kawunan ku da iyalanku daga shiga wuta. Farooq ji irin shigar fitsarar da matarka take yi ta gaisa da wannan namijin ta rungumi wannan namijin duk da sunan wayewa. Ka riƙa yiwa matarka nasiha kana gayama ta gaskiya domin ku tsira ranar gobe alƙiyama”