Chapter 5 Reading BAHIYYA HAUSA NOVELS COMPLETE BY OUM AMEER.docx Arewa Novels

BAHIYYA HAUSA NOVELS COMPLETE BY OUM AMEER.docx

Author :  Oum Ameer Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   5 / 14

12K to 15K   out of 39.2K words

*OUM AMEER*

💝 *BAHIYYA*💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*BY*

*AMINA IBRAHIM*

*(OUM-AMIR)*

*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*

*FREE PAGE*

*BABI NA SHIDA*

Jingina bayan sa yayi a jikin cushion ɗin tare da lumshe idanunsa relaxing himself yana digesting shawarar da Mahi ya basa.

Shi kuwa Mahi ganin ya ƙi ce masa komai yasa ya miƙe tsaye yace.

“Ni zan tafi I'm leaving to Ghana in sha Allah, kai kuma sai ka shirya kayi scheduling time ɗinda zaka gana da mutanen nan da na faɗa maka sun iso tun shekaranjiya, sunce ba za su gana da kowa ba sai kai”

Daga haka ya juya ya fice daga gidan.

Farooq kuwa yafi hour a haka duk wanda ya gansa zaiyi tunanin cewa bacci yake nan ko ba baccin da yake kawai matsalolin gidan sa yake ta lissafi yana neman hanyar warware su.

Miƙewa yayi ya shiga ɗakin da Madinah ta ke, gefen window ya sameta tana tsaye tana kallon waje amma ganin quick action ɗinta tana goge Hawaye ya tabbatar masa da cewa kuka take, cikin mamaki yace.

“Wai Madinah minene? Why have you been crying since yesterday ? da na san cewa tilas taki ki amsamin tamboyoyin zai sa ki yi ta kuka da na haƙura kawai,ko dai akwai wani abin ne bayan wannan ? Please idan har kina da wata damuwa just tell me”

Matsawa yayi in da ta ke tsaye ya rungumeta cikin nuna kulawa yace.

“Madinah Farukun ki ne idan akwai wani abu dan Allah ki faɗamin, idan ina ganin ki kina kuka zuciya ta ba zata iya daurewa ba”

Murmushi tayi tace.

“Haba ba fa komai, kawai dai tunawa da nayi da Azizat da Modu ne yasa zuciya ta ta kasa daurewa”

Cikin tausayawa yace.

“Nasan ba zan taɓa fahimtar yadda kike ji ba domin ke kika rayu tare da su ke kika san zafin su da muhimmancin su a rayuwar ki, to amma ni kuma da na san ke kaɗai ce rayuwa ta dole zan damu idan kina cikin wata damuwa, kiyi haƙuri”

“Na gode Umar”

Sake tambayar ta yayi yace.

“But Grand Ma, is that only my Mom you gave birth to?”

Gyaɗa kai tayi alamar eh sannan tace.

“Bayan haihuwar Azizat nan ma wata Azal ɗin ce ta sake faɗamana ni da Modu, bayan wata shida da haihuwar ta na je wajen wani spiritualist shima daga garin mu Enugu ya fito na san shi tun daga gida, buƙata ta na faɗa shi akan ina son maganin tsayar da haihuwa kafin yarinya ta ta girma saboda bana so inyi ciki da goyo, ya tambayeni sunan Mijina da kuma sunan da na canja nima na faɗa mishi, daga nan ya tashi ya shiga wani bukka sai da ya ɗauki lokaci ya fito ya ce min an gama aiki,aikin na binnewa a cikin ƙasa saboda haka duk lokacin da na ke buƙatar haihuwa in zo daga zaran an to ne shikenan. Hmmm! Faruku ban sake komawa wurin mutumin nan ba sai da Azizat ta cika shekara biyar cif a duniya, ko da naje na riski labarin da har in koma ga Mahalicci na ba zan manta da shi ba, domin kuwa ko da naje mutumin ya mutu shekara biyu da suka wuce, wurin nashi ma gaba ɗaya an rushe shi anyi gini kamar bai zauna a wurin ba. Kuma asirin an riga an binne sai idan an tone zan iya sake haihuwa, to kaji yadda mahaifiyarka ta kasance a gare ni ita kaɗai, nayi kuka nayi kuka har na gode Allah na riga na aikata kuskuren da ba zai gyaru ba, a duk lokacin da naga abokanan hulɗa ta da yara fiye da uku huɗu sai na ji zuciya ta ta tsinke in yi ta kuka ina istigfari. Hakan yasa ni da kakan ka muka ɗauki son duniya muka ɗorawa Azizat bayan ta mutu kusan zaucewa na kusa yi, hakan yasa da soyayyar kaka da jika da kuma soyayyar mahaifiyarka duk muka haɗa muka baka har Modu ya mutu ya bar mu daga ni sai kai”

A labarin jiya da ta bashi bai ji abinda ya girgiza shi irin na yau ba, haƙiƙa ya tausayawa wannan tsohuwar matuƙa.

Shiru ne ya ratsa tsakanin su bayan some minutes ya ce.

"I'm so sorry Grand Ma”

Murmushi tayi tace.

“thank you. Ka je ka shirya ka zo ka kai ni gidan Victoria nayi mata alƙawarin watan watarana zan zo tare da kai idan damar hakan ta samu”

“Wace Victoria?”

“She's my old friend since from child hood we were from the same state”

"OK.”

Bayan ya gama duk abinda yake suka shirya around 12:00pm suka bar gidan.

Sun samu tarba mai kyau gidan da suka je, sai 4pm suka dawo.

Madinah tayi hakan ne domin ta rage masa damuwar da take damun sa, Mahi yayi mata duk bayanin da yake ciki to amma ba zata shiga al'amarin gidan sa ba, zata dai taya shi da addu'ar da ta saba yi masa kullum, kuma shi ma bai damu da ya sanar mata ba saboda duk lokacin da ya mata lodging wani complain tsakanin shi da Hanifah sai dai ta ba shi haƙuri tace yayi haƙuri Hanifah yarinya ce watarana zata daina.

A haka tayi ta ɗau ke masa hankali suna yawon kai ziyara na tsawon kwanaki daga baya kuma ya warware ya koma Office, amma Kullum kwanan duniya da matarsa yake kwana a rai da ita yake tashi.

***********

BAHIYYA

A 'ƴan watannin nan na samu kuɗi ba laifi domin Malama Rabi ta sama min customers da nike wa aikin lalle da kitso sun fi a ƙirga kuma kowa da kalar irin biyan da yake min na karamci. Hakan yasa muka haɗa kuɗi kusan dubu saba' in Mama ta baiwa Malama akan mu tafi tare a samu makaranta private dai dai da matsayin mu a sanya Nuhaira kafin zuwa wata shekara ni kuma a biya min kuɗin WAEC.

A ta dalilin rashin samun Baba Maharazu a waya shine sanadiyyar da Malama ta shiga gaba gaba aka yiwa Nuhaira komai har uniform har komai ya kama kuɗi dubu saba'in da huɗu termly kuma Dubu ashirin da biyu. Ss1 to Ss3.

Malama ta kasance maƙociyar mu ce tunda muka dawo nan garin Kaduna Road suka haɗu da Mama, da ita da mijinta duk malaman makaranta ne suna da yara huɗu, bariki ba kamar gida ba ne namiji zai bar matarsa ita ma ta fita ta nema domin su taru su rufawa juna asiri matuƙar zata iya, hakan yasa Malama bayan aikin koyarwa ta shiga hulɗa da mutane daban daban tana kai kayan mata cikin gari da kuma sauran State tana kuma da shago ƙofar gidanta. Ta iya kanta sosai shiyasa duk yadda kake tana iya zama da kai tana kuma da kirki irin nata.

Sanadiyyar komawar Nuhaira school yasa aiki ya taru ya min yawa ni da Mama in kuma na fita cikin gari ita kaɗai tayi ta wahala shiyasa na nema mata almajiri mai taimaka mata.

Yauma haka nayi ta bada kayan miya idan an kawo niƙa kuma in tashi in yi domin Mama ta ɗan fita unguwa, ƙarfe uku nayi na yamma na shirya na fita islamiyya nabarwa Sharifu almajiri sauran aikin kafin Nuhaira ta dawo daga school domin sai uku da rabi suke tasowa kafin ta iso gida kuma huɗu tayi shiyasa take zuwa islamiyya yanzu a makare.

Ko da muka shigo gida ana kiran sallar magrib ganin banga mama a waje ba na shiga ɗaki na tadda ta kwance a duƙunƙune da sauri muka isa gareta ni da Nuhaira muna rige rigen tambayarta mike damun ta,ko iya ɗaga kanta ba tayi hakan yasa hankalinmu ya tashi sosai na cakumota da ƙarfi nace.

“Mama mi ne ne? Mi ya same ki?”

Sai tin zuciyar ta ta shiga nuna min da hannu alamar nan ne yake mata zafi. Cikin ruɗewar kuka nace.

“InnaLillahi! Wannan ciwon zuciyar ya matsa miki Mama. Tashi ki daure mu tafi chemist, yau da ke zan tafi domin ya duba ki.... Nuhaira ɗauko mata hijabi da mukulli mu tafi”

Da sauri Nuhaira tayi yanda nace muka rufe gidan a hankali muka lallaɓa da ita wanda ko a chemist ɗin kasa zaunawa tayi sai da na zauna ta kwanta a jiki na. Tambaya ta mutumin yayi mike damunta.

Kai tsaye na share hawayena na ce.

“Ta daɗe tana complain cewa ƙirjinta yana ciwo, to duk lokacin da abin ya tasar mata sai inzo in sayi mata magani ko nan ko kuma wani wuri in bata tasha, to yau dai bama nan ko da muka dawo kuma mun cimmata a haka”

Nidai ganin nayi ya ɗauko wani abu ya ɗaura mata a hannun ta sannan ya saka wani a kunne bayan ya gama. Ya kalle ni yace min hawan jini ne da ita kuma ya hau sosai fiye da ƙima.

Cikin tsantsar mamaki ni da Nuhaira muka haɗa baki wurin kiran.

“Hawan Jini likita?”

Cikin kuka na sake cewa.

“Hawan jini ta yaya? Wane irin hawa jini dan Allah, muna zaune lafiya”

Mutumin yace.

“While, ba abin mamaki ba ne ai, musamman idan akwai wata damuwa tare da ita tana yawan tunani da rashin samun ishashshen bacci, amma...”

Sai ya juya ya hahhaɗo magunguna ya bani na kusan dubu goma sha ɗaya.

A nan ya buɗe ya bata maganin, sannan yace

“idan akwai abinda yake saka ta damuwa kuyi ƙoƙari ku ɗauke mata hankali a kai, ta riƙa samun bacci yadda ya kamata tana cin abinci mai kyau, in sha Allah zata ji sauƙi”

Daga haka na cewa Nuhaira taje gida ta ɗauko masa kuɗin shi, bayan ta dawo muka koma gida, kafin shiga bacci har mun samu taji sauƙi domin har ta tashi tayi Sallah taci abinci.

Washe gari bayan mun gama sallar Asuba muka je muka gaishe ta nayi sauri na haɗa mana break fast Nuhaira ta shirya ta fita makaranta ni kuma na kai mata abin karin nata ɗaki bayan ta ɗanci ba yawa na bata magani kamar yadda likita yace.

Bayan na kwashe kayan na dawo na zauna cikin tausasa murya na kalle ta nace.

“Mama miye yake damunki haka? Mi kike tunani da har ya sa miki hawan jini nan take? Dan Allah Mama ki gayamin”

Girgiza kanta tayi tace.

“Ni dai ban san ina da wata damuwa ba Bahiyya, gaskiya ban sani ba.....”

Cikin rashin gamsuwa da maganar ta nace.

“A'a Mama, dan Allah ki gayamin minene damuwar ki,irin wannan ciwon ba zai kama mutum ba muddin ba damuwa ce a ransa ba.”

“Ni kam bani da wata damuwa Bahiyya”

Juyin duniyar nan nayi amma Mama ta kafe tace min babu abinda yake damunta dole na hak'ura na ƙyale ta ina faɗin.

“To tunda kince ba abinda yake damunki, dan Allah ki kwantar da hankalinki idan ma akwai wani abinda ba zaki iya gayamin ba kiyi haƙuri ki cire sa a ranki, bana so mu koma wurin likitin bayan kwana biyu ya aunaki yace min ga wata damuwa, idan wani abu ya sameki Mama ban san ya zamuyi ba. Kece ƙwarin guiwar mu, kece kaɗai muke da, ke kika zama bangon jinginar mu idan wani abu ya sameki ban san in da zamu shiga ba. Mama ke ce fa kullum kike min faɗa akan in dai na damuwa, in zama mai tawakkali, yau kuma ace kece wai hawan jini ya kama, mi kika nema kika rasa? Idan ma mutuwar Baba ce ya kamata ace kin saba kamar yadda kike faɗamin Mama...”

Hawayen da suka gangaro min na share tare da Miƙewa tsaye na fita waje jin sallamar yaro ya shigo gidan namu.

Mama kuwa mirginawa tayi ta kwanta akan pillow wasu hawaye masu zafi na bin gefen kuncin ta. Haƙiƙa mutuwar Jafaru ta nakasa mata zuciya ta yadda ma bata yi tsammani ba. Idan tace tana samun wadataccen bacci tsawon shekarar nan tayi ƙarya, babu abinda take tunani sai mijinta da kuma rayuwar marayun 'ƴa' ƴan ta mata guda biyu, waɗannan mutanen da suka kashe mijinta sunyi mata illar da har ta kwanta damanta ba zata warke ba. Domin shine jigonta shiya kawo ta wannan ƙasar ta Nigeria ba tare da tasan wani mutum na daban ba bayan shi. Gashi har ya koma ga Allah ƙasar ta sa ta gagare shi komawa akan wani dalilin banza na son zuciya irin na mutanen yau. Har baro garin Gusau tayi ko zata samu sauƙi ta manta da rayuwar su ta baya amma abin ya ci tura. To kuma yanzu ga ƙarin wata matsalar ta kunno kai tunda likitan ya faɗa mata tana da hawan jini damuwar ta da fargabar ta suka ƙaru, damuwa ta ƙara baibaye ta fiye da ta baya.

Ita tsoron ta kullum idan ta mutu a wane halin rayuwar 'ya' ƴan ta za su kasance? Sannan idan suka isa aure wa zai aure su idan akaji cewar ba su da dangin uwa babu na uba suka ɗai ne su uku suke rayuwar su.

Bayan kwana biyu kamar yadda likitan yace, na shirya na cewa mama ta shirya mu koma wurin mai chemist kamar yadda yace, ƙin amincewa tayi ta kafe kai da fata tace min taji sauƙi ba sai mun koma ba. Ƙarshe ma faɗa ta rufe ni da shi wai duk laifi na ne, daman su mutanen nan matuƙar kana ziyartar su to kullum cikin kira maka matsala suke, da ace na siyo mata maganin ta tun ranar tasha da yanzu kowa na nan hankalin sa kwance, to ita babu in da za ta je ta warke.

Dole na na kama kaina na ja baki na nayi shiru na ƙyale ta, amma Ina kula da ita sosai duk wani motsin ta yana kan idona, sai dai daga baya na gano tabbas Mama bata samun bacci kamar yadda likita yace, akai akai idan na farka naje ɗakin ta zaune nike samun ta kan sallayah.

Tun daga wannan lokacin na bata shawara ta riƙa sai ta lokaci idan ma tashin zatayi na dare to ta ta shi amma ta rage ɗaukar dogon lokaci.

Haka mukaci gaba da rayuwa, Mama ta samu sauƙi sosai a gaban idanunmu kamar yadda take nuna mana idan abin ya tasar mata sai ta tafi can wani chemist ta sayi magani ta dawo gida ta ɓoye tana sha don kar mu gani hankalin mu ya tashi. Nuhaira taci gaba da karatun ta, nima ina yawon lalle na da yanzu na ƙara yawan customers.

*************

Hanifah

Ko bayan rabuwar su da Farooq sai da ta sake share wata biyu da sati biyu a Dubai sannan ta wuce Egypt ta sake yin sati biyun ta masu kyau sannan ta dawo.

Duk iya yanda Farooq ya ɗauki fushi da ita kasa daurewa yayi dole ya dawo kiranta a waya yana jin muryarta amma bai taɓa tambayar ta cewa ina take ba, mi take yi ko yaushe zata dawo. Iyaka suyi wayar su idan sun ƙare su kashe. Sau biyu tafiya tana kama shi zuwa Dubai bai taɓa attempting na cewa ya je wurinta ba. Ya ƙyale ta har lokacin da ta ga dama ta dawo don kan ta.

Ko da ta iso ma baya ƙasar yana Saudiyya tare da Madinat sun je aikin Umrah sai da tayi kwana huɗu da dawowa sannan ya dawo.

Tare da Madinah suka shigo gidan, tunda yayi rashin lafiyar nan ta zo bata koma Kaduna ba. Cikin murna tazo ta tare shi tana faɗin.

“Welcome”

Kamar wanda yake mafarki haka yayi hugging ɗin ta back yace.

“Am i dreaming?”

Dariya tayi tace.

“No! Not at all. Is your Hanifah”

Ƙara riƙe ta yayi gam a jikin shi yana faɗin.

“Welcome back home my love”

“Thank you”

Ganin Madinah yasa tayi saurin janye jikin ta taje gareta with soft smile on her face ta bata side hug tace.

“Welcome Grand Ma”

Cikin Kalaman hikima Madinah tace.

“Thank you Hanifah. Da fatan an dawo lafiya”

Hanifah tace

“Lafiya lau Grand Ma”

Madinah tace

“Ya kasuwa? Ya familyn ki? Da fatan komai lafiya?”

Hanifah tace

“Everything is fine, my family are doing good”

“That's nice to hear.”

Madinah tace tare da kama hanyar zuwa masaukinta,luggage ɗin ta da suke hannun shi da kanshi ya wuce har ɗakin ya kai mata, daman tun a mota da suka sauka ya hana kowa ɗaukar kayan yace aikin shi ne saboda haka shi zai kwashe kayan.

Yana fitowa ya zarce ɗakin shi ya je yayi wanka ya shirya itama Hanifah da sauri taje ta sake yin wanka ta shirya cikin riga da wando da suka amshi fatar ta sukayi raɗau, sai wata hular net da ta saka ta naɗe kanta da ita tayi matuƙar kyau. Daman kuma kafin ta shiga ciki sai da ta saka Nafisat cook ɗinta cewa ta shiryawa Farooq table kafin su fito.

Ta riga shi fitowa hakan yasa ta wuce ɗakin shi direct ta sa meshi ya gama shiryawa yana tsaye jikin window yana kallon waje, hannayensa soke a cikin trouser pocket ɗin shi.

A hankali taje ta rungume shi ta baya tare da ɗora kanta a bayan shi tayi lamo, dukkan su babu

5 / 14