BAHIYYA HAUSA NOVELS COMPLETE BY OUM AMEER.docx

Author :  Oum Ameer Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   9 / 14

24K to 27K   out of 39.2K words

mata komai da ya wakana tsakanin ta da Bahiyya da kuma irin rashin mutuncin da Baban Amed ya gurza mata. Ƙarshe tace.

“Kin ma san wani abun takaici Hanifah? I'm 6weeks pregnant, cikin ɗoki yace min dole zai zaɓi wata ƙasar mai daɗi muje muyi renon cikin a can har na haife sai mu dawo na ce masa ban amince ba ya bari dai idan cikin ya kai term sai mu tafi,shine yace ya amince amma idan muka tafi sai babyn ya kai 2years zamu dawo nace na amince nima, a haka muka tsaya amma wai shine don yayimin baƙin ciki wai yanzu yake faɗamin in shirya gobe zamu bar ƙasar.”

Cikin Mamaki Hanifah tace.

“Ke ma dai Rasi kina bani mamaki wallahi yadda kike iya tolerating nonsense ɗin namiji, kuɗin sa ne? In da ace kuɗin sa ne don ya hana ba matsala ba ne...”

Wani murmushin takaici Rasi ta saki wanda yafi kuka ciwo tana girgiza kai tace.

“Hmm! Up to now you don't know men Hanifah, but bet me, one day one time sai namiji ya gurza miki watarana I promise you this, a lokacin zaki gane cewa maza maza ne kuma ba zaki iya yin komai ba a wannan lokacin, shiyasa nike gayamiki kiyi amfani da damar ki tun kina da lokacin ki”

Dariya ce ta suɓucewa Hanifah tace.

“Rasi, for get about it because wannan ranar ma ba zai taɓa zuwa ba”

“Hanifah bazan kira ki da yarinya ba, 8years in marriage kin wuce a ce baki san minene aure ba. while I don't blame you Saboda ba rayuwar auren tsantsa kike practicing ba daga ke har mijin ki baku san ma daɗin auren ba. But idan kika shirya rayuwar auren ta gaske watarana zaki ce na faɗa miki haka”

Taɓe baki Hanifah tayi tace.

“Rasi! yanzu dai duk abinda kike so nima shi nike so, tunda har Abdulfatah ya katangeki daga taimakon wannan yarinyar, me I will do that Ko don na kare miki mutuncin ki daga idon ta”

Cikin tsantsar farin ciki Maman Khadijat tace.

“Thank you, thank you Hanifah, wallahi ban san taya ya zan iya gode miki ba, thank you so much”

“Mention not Rasi, kinfi haka a wurina, tunda kin ƙi ki kore ta ya na iya, dole in so abinda kike so”

Rungume ta tayi tace.

"Naji dai, thank you matar Farooq.... Oya! Tashi muje bana so a tsaya wani jinkiri kuma kada wani abu yazo ya biyo baya”

***************

BAHIYYA

Tun ina zaune har sai da na kai ga gincirawa ba tare da na kawo komai a raina ba na zauna zaman jiranta, tunda har mijinta ne dole na san zata tsaya sai ta gama da shi sannan tayi ta tawa. To kuma ina nan zaune sai naga Ƙawarta ta shigo, hakan yasa na ƙara gyara zama domin na san dole itama sai ta bata time ɗin ta kafin ni.

Ganin har lokacin sallar Asr yayi yasa na miƙe naje na ɗoro alwala na zo na gabatar da sallah. Ina zaune Ina addu'a suka shigo tare da ƙawar ta ta.

Gaishe su na ƙara yi tare da baza kunne ina jira in ji tace na tashi mu tafi,sai dai ganin sun samu wuri sun zauna yasa ni jin wani abu ya ɗan ɗarsu a zuciyata.

“Bahiyya!”

Ɗagowa nayi na kalli Maman Khadijat nace

“Na'am”

“Tun ɗazu ina ciki da Baban Amed banki na yaƙi ya fitar da wannan kuɗin mai yawa, nayi ta gwadawa yaƙi bayar da haɗin kai shi yasa kika ga na jima ban fito ba, amma Alhamdulillah! Ga Ƙawata nan Hanifah in sha Allahu zaku tafi tare ita ce zata biya kuɗin babu wata matsala”

Rusunawa nayi inata gode musu wanda har sai dai Maman Khadijat taji tausayi na ya ƙara sarƙafe mata zuciya. A hankali tace.

“Bahiyya ba buƙatar duk wannan please, fatanmu dai shine Allah ya bata lafiya....” Sai kuma tayi murmushi tace.

“Bahiyya kin san ɗan Adam da kuɗi, tunda kuɗin nan yaƙi fita a banki na naji Zazzaɓi yazo ya kamani lokaci guda, bana jin daɗi jikina a yanzu ba zan iya fita ba, saboda haka kice ina gaida maman ku kinji ko, Allah yasa ayi cikin nasara. Tashi kuje”

Duk da cewa ban san abinda ke faruwa ba, wani irin abu naji mai sanyi ya mamaye zuciyata da gudu naje na ƙanƙame maman Khadijat ina ta rusa kuka tare da sakin sabbatunda ni kai na ban san mi nake cewa ba.

Daga haka muka tashi muka tafi a motar wadda ta kira da Hanifah.

Har muka isa asibitin ni da ita babu wanda yayi magana kowa da irin abinda ya ke saƙawa a cikin ransa.



Bayan mun isa bakin asibitin na miƙa hannu da nufin buɗe motar tace min.

“Dakata, akwai maganar da nike so muyi da ke..............”

*OUM AMEER*

💝 *BAHIYYA*💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*BY*

*AMINA IBRAHIM*

*(OUM-AMIR)*

*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*

*FREE PAGE*

*BABI NA GOMA*

........... Kafeta nayi da Fitilun ganina tamkar zan karanto wani abu daga allon fuskar ta.

“Daina kallo na haka da waɗannan idanuwan naki”

Jin ta furta haka a gare ni yasa nayi saurin saukar da idanuwana ƙasa da sauri kamar yadda ta umurceni, a can ƙasan raina kuma sai naji wani iri domin kalmar tayi min kama da ta muzantawa duk da cewa ban san abinda yake ranta ba.

Mun jima shiru kafin ta iya buɗe bakinta tamkar wadda aka tilasta akan dole sai ta yi min magana tace.

“Zan biya kuɗin aikin Mahaifiyarki kamar yadda Rasi tayi miki alƙawari, but sai dai ina da wata 'ƴar ƙaramar buƙata zuwa gare ki, idan kin amince fine, zan biya ko da sun kai million ɗari ne ba tare da ɓata lokaci ba...”

Ban tsaya nauyin baki ba kaina na ƙasa tunda ba taso na kalle ta nace.

“Zanyi koma mine ne kika buƙata muddin zaki biya kuɗin aikin mahaifiyata, ita kaɗai ta ragemin a duniya sai ƙanwata”

Gyaɗa kai tayi tace.

“While, ba wani abu bane mai wahala, kawai dai zaki tayani renon ciki ne zuwa wata tara daga zaran ya fito duniya sai kiyi tafiyar ki kawai aikin ki ya ƙare...”

Cikin azama na tare numfashin ta nace

“Na amince! in don ɗan waɗannan aikin ne tabbatas na amince”

Murmushi tayi wanda har sai da na jiyo sautin sa sannan tace.

“Ki dai ƙara tunani, kije kuma ki yi shawara na baki daga nan zuwa jibi....”

Hawayen da suka zamomin abokan rayuwata ne suka fara zarya akan kuncina, girgiza kai na na fara yi ina magiya nace.

“Dan Allah Hajiya ki taimaka min, in dai akan mahaifiyata ne babu wani tunanin da zan tsaya yi, duk da yanzu cewa an ɗora ta akan magani likita ya gayamin cewa rayuwar ta tana cikin haɗari aikin nan da wuri shine maslaha, bana son in rasa mahaifiyata dan Allah ki bada kuɗin ko aikin da yafi wannan ne ni na amince miki zanyi matuƙar zaki biya mata kuɗin aikin nan, kuma zan yi ta gode miki har in koma ga Allah ba zan manta da alherin ki gare ni ba”

Ajiyar zuciya ta sauke a hakankali tace.

“Shi kenan. Gobe da safe zan zo, amma Kuma aikin namu ba a nan ƙasar zamu zauna ba ƙasar waje ne zamu tafi”

Daga haka naji ƙofofin motar sun ce ƙitt! Alamar cewa sun buɗe daga nan na buɗe tare da ƙara yi mata godiya na sauka cikin tsantsar farin ciki na shige cikin asibitin.

Ina shiga na cimma Malama ta kawo abinci kamar kullum,Daman bayan ta taso daga makaranta idan mai aikin ta tagama girki sai ta shirya ta wuto asibitin tare da abincin.

Spoon ne riƙe a hannun Nuhaira tana bawa mama da ke jingine jikin pillow abinci a hankali tana mai ƙureta da kallo. Jin sallama ta yasa duk suka juyo, Nuhaira da malama suna rige rigen tambaya ta ina na shige duk yinin yau, domin ban faɗamusu in da zanje ba.

Da sauri naje na karɓi spoon daga hannun Nuhaira nace.

“Bani spoon ɗin Nuhaira, duk yinin yau ban hidimta mata da komai ba, bani ko wannan ladar na samu.”

A hankali na shiga bata abincin tana mai kafeni da ido wanda nasan ko bata furta ba itama tambaya ta take daga ina nake.

Kauda kanta da tayi shi ya bani tabbacin cewa abincin ya ishe ta daman ba wani abun kirki ta ke ci ba. Ruwa na bata sannan na tambaye ta ko akwai abinda ta ke buƙata, girgiza kanta tayi alamar ba komai sannan na miƙe na tattara kayan na dawo.

Gajen haƙuri ne yasa malama sake jefomin tambayar daga ina na ke.

Zaunawa nayi ina mai sakin sassanyar murmushi na kalli malama nace.

“Malama kin san daga ina na ke kuwa?”

Tsuromin na mujiyarta tayi tare da girgiza kanta alamar a'a.

Nace.

“Gidan Maman khadijat naje”

Cike da mamaki tace.

“Gidan Maman Khadijat Bahiyya! Kina nufin gidan Hajiya Rasi'a?”

Gyaɗa kaina nayi nace.

“Eh malama. Wallahi ko da na bar asibitin nan ɗazu bansan ina na nufa ba, sai daga baya tunanin zuwa gidanta ya ɗarsu a zuciyata....”

Nan na shaida musu duk yadda nayi da maman Khadijat da kuma wadda muka zo tare da nufin gobe zata zo ta biya kuɗin aikin baki ɗaya.

Kabbara Nuhaira ta ɗauka tare da zuwa ta ƙanƙameni ta saki wani kukan farin ciki tana mai faɗin

“Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! Haƙiƙa dukkan wani tsanani yana tare da sauƙi Aunty Bahiyya da yardar ubangiji, waɗan nan mutane Allah ubangiji ya saka musu da mafificin alkairi. Amin.”

A hankali Mama ta runtse idon ta hawaye na sauka daga gefen kuncin ta, bakinta sai motsawa yake tana ta jera kabbara da yabo da nuna godiya a wurin Allah.

Malama itama rungume ni tayi cikin farin ciki tace.

“Haƙiƙa kin cika jajirtaciyya 'ƴa mai nagarta Bahiyya, kin saka kaifin hankali da basira wanda ni kaina tunanin hakan bai zo min ba, Hajiya Rasi'a mace ce mai taimako sosai, gaba ɗaya Allah ya mantar da ni da tunanin zuwa wurin abokan hulɗarki. Mungode mata sosai in sha Allah zan je har gida na yi mata godiya...”

Dariya ce ta suɓuce min bayan tunawa da Yarjejeniyar mu ni da Hajiya Hanifah na kalli malama nace.

“To amma kun san wani abu? Ita wannan hajiya Hanifah ɗin sai da mukayi wani sharaɗi a tsakanin mu, cewa wai zan taya ta renon cikinta idan ta haihu sai in dawo gida, nace mata ba matsala, wai harda cewa naje nayi shawara, ban san lokacin da na saka mata kuka ba, nace ba wata shawara ni na amince kawai tazo ta biya mana kuɗin.”

Cikin mamaki Malama tace

“ renon ciki kamar yaya? Ke da ba mijin ta ba taya zaki taya ta renon ciki? Kuma na san dai tana da masu aiki birjik duk basu ishe ta ba sai ke?”

A wauta irin tawa ban kawo komai a raina ba nace.

"Malama kin san halin masu kuɗin nan shegen son jikin tsiya ne da su, kuma mijin dole ya fita wurin sabgoginsa na yau da kullum, to wata ƙila ko ruwa tafi so a bata a baki, ni kuma ba ruwa ba ko wanka tace in yi mata wallahi tsab zan iya ina ruwana..”

Dariya Nuhaira ta fashe da ita tace.

"Kai Aunty Bahiyya wanka fa?”

Nima dariyar nayi nace.

" Wallahi Nuhaira da gaske na ke, ko wanka ta ce in riƙa yi mata zan yi matuƙar buƙata ta zata biya, biyan buƙata ai yafi dogon buri. Su masu kuɗin nan kawai idan tsabar jin daɗi yayi musu yawa haukacewa ma su ke, har a rasa mima za'a yi da kuɗi”

Murmushi Malama tayi tace.

“Abu ɗaya muke fata, Allah ya sa ayi aikin nan cikin nasara ya tashi kafaɗunta ”

Duk muka amsa da amin.

***************

HANIFAH

Bayan fitowa ta daga motar wani farin ciki ne ya lulluɓeta domin ba ƙaramar sa'a ta taka ba. Ainahin dalilin zuwanta gidan Rasi'a shine; bayan fitowar ta daga asibitin Nicholas direct office ɗin Farooq ta wuce cike da farin ciki ta sa mesa ta shaida masa yadda suka yi. Nan fa suka hau daru yace shi sam bai yarda ace Christian ce zata ɗaukar masa cikin ɗansa ba, ai addinin mu ya faɗamana cewa tun a ciki yaro yake fara koyon abubuwa kafin ya fito duniya, kuma ya kan ɗauko halayya da ɗabi'u saboda haka ba zai yi farin ciki ba ace wai ɗansa zai fito daga tsatson da addinin su bai zo ɗaya ba. Matuƙar tana so ya amince to ba zai yarda ayi dashen ɗansu a mahaifar Agnes ba, sai dai a fasa. Wuta sukayi sosai da shi. Ƙarshe cikin fushi ta baro Office ɗin direct ta nufi gidan Aminiyarta Rasi'a don ta koka mata matsalar ta sannan ta nemi shawarar ta akan ina ya kama ta a samo wadda za'a yi wannan aikin da ita. Kwatsam cikin sa'a sai gashi tayi katari da wannan damɓarwar tsakanin Rasi da Mijin ta. Cikin ƙwarewa da iya kanta ta jefi tsuntsu biyu da dutse Ɗaya.

Tasan idan ta faɗawa Rasi manufarta akan Bahiyya a yanda taga tana ƙaunar yarinyar nan ba zata amince ba, amma cikin ruwan sanyi gashi buƙatar ta zata biya. Addu'a take a cikin ranta Allah ya tabbatar da tafiyar su a gobe ɗin shi kenan itakam hankalin ta kwance.

Bayan ta gama nazare - nazarenta ta umurci drivernta akan ya nufi hanyar gida.

Tana shiga cikin sa'a kuwa taci karo da farooq ɗin ya dawo, masallaci ya wuce bai dawo ba sai bayan sallar Isha.

Har ɗaki ta samesa bayan ya fito daga wanka tayi murmushi ta ce.

“Welcome!”

Shima murmushin ya mayar mata yace.

“Thank you Hanifah. Ina kika je ne? Na je har office ɗin ki bakya nan?”

Murmushi tayi tace.

“Ina da wani sauran hutu ne bayan nasan cewa ban cika maka muradin ka ba. Na je neman matar kamar yadda ka buƙata...”

Runtse idanunsa yayi tare da girgiza kai yace.

“Hanifah! Hanifah! You are there stressing your self. Ni fa abun ma ya fara fita daga kaina...”

Cikin shagawaɓewa tace.

“But I have already found the woman, musulma Mai addini kamar yadda ka buƙata. Dan Allah Farooq ka karɓi abun nan da zuciya ɗaya please”

Kafaɗar sa ya ɗaga tare da ware hannayensa alamar shi kenan.

Hugging ɗinsa tayi tare da narke masa tana sakar masa sabbatu, shi kuma daman can in dai Hanifah zata biye sa to yafi ƙaunar wannan rayuwar soyayyar fiye da komai a duniya . Duk son sa da abinci haka suka lalace a wurin suna ta abu ɗaya.

***************

BAHIYYAH

Firah muka sha sosai muna ta tsara yadda zamuyi da likita kamar yadda ya faɗa mana cewa da zaran an samu kuɗin zai shige mana gaba a shirya yi mata aikin. Mama ma jefi jefi ta kan ɗan sako bakinta kaɗan. Gaba ɗaya da ka kalle mu kasan cewa cikin kashi saba'in kashi talatin na daga cikin damuwar mu ya tafi da ikon Allah.

Sai da aka gama sallar Isha mijin malama yazo ya gaida Mama, malama ta faɗa mishi abinda ake ciki ya nuna farin cikin sa yayi mana addu'a sannan suka fita zuwa gida.

A bakin get ɗin asibitin na tsaya nace.

“Malama dama akwai maganar da nike so in sanar miki.”

Tsayawa tayi shi Kuma uncle Idris yayi gaba wurin mashin ɗinsa ya tsaya jiran mu.

Kallon ta nayi tare da marairece murya na riƙe hannun ta nace.

"Malama akwai abinda na ɓoye ban faɗa muku ba. Matar tace ba a ƙasar nan zatayi renon cikin ba kuma dole in amince in tafi tare da ita, to na san idan na faɗa kai tsaye hankalin Mama na iya tashi ni kuma bana son abinda zai ɗaga mata hankali a halin yanzu”

Jinjina kai Malama tayi alamar abin babba ne tace.

"Dole kuma sai tare da ke Bahiyya? Anya zan yarda da wannan matar kuwa?”

Cikin magiya nace.

“Malama dan Allah kada ki ce a'a please, wallahi nayi imani ba zata cutar dani ba, gobe fa da kanta tace zata zo nan, kuma na faɗa miki babbar Aminiyar maman Khadijat ce idan har ba ta kirki ba ce maman Khadijat ba zata haɗani da ita ba. Malama wannan hanyar ita kaɗaice hanyar da zan iya ceto rayuwar mahaifiya, ba zan iya bari wannan damar ta wuce ni ba, domin idan Mama ta mutu wallahi ni kaina rayuwata tazo Ƙarshe, kawai abinda nike so da ke shi ne ki tayani da addu'a kuma ki kula min da Mama ta da Ƙanwata, shekara kamar kwana ce take cikin Ikon Allah zaki ga shekara ta zagayo, in sha Allah kuma zaku same ni mai kiyaye wa”

Ajiyar zuciya ta sauke sannan tace.

“Bahiyya duk don saboda mahaifiyar ki kika yarda da ɗaukar wannan kasadar, dole zan kirashi da kasada domin ba ki san ina zaki ba kuma baki san mi zaki tarar ba, amma koma minene ina miki fatan tsarin ubangiji a duk inda kike, tunda har saboda mahaifiyarki kika ɗauki wannan nauyin in sha Allah ubangiji zai saka miki da abinda baki yi tsammani ba domin uwa ta sha gaban komai da albarkar ta zaki yi nasara a rayuwar gwagwarmayar ki in

9 / 14