Author : Oum Ameer Category : Romantic Hausa Novels
ne nagan su wasu iri domin ni ba kayan da sukayi daidai da tsari na bane, gaba ɗaya kayan daga riga da wando sai riga da skirt, sai kuma Abayas sun kai shida, to suka ɗai ne nikejin a raina cewa zan iya sanyawa amma su kam waɗancan haram shan giya a gidan Malam, mamaki na babu atamfa ko kala ɗaya a ciki.
Da dare ma haka na kwanta a kan gadon tare da janyo bargo na rufe jikina saboda sanyin ACn da yake ratsani.
Sati ɗaya na kwashe a gidan ba tare da na sake sanya Hajiya Hanifah a ido na ba, wannan matar da a yanzu na saba da ita Nafisat itace kaɗai ni ke gani, ta dage sosai wurin koyar da ni abubuwa waɗanda tuni nayi nisa sosai a iya wasu abubuwan wasu kuma sai dai a hankali, ni kaina idan na kalli madubi na kan yarda da cewa jiki na ya canza sosai ba kamar yadda na zo ba, tsabar hutu da cin kayan daɗi iri iri,ko gashin kai na ban san cewa ina da dogon gashi sosai mai santsi ba sai yanzu da ya ke shan gyara a wurin Aunty Nafisat domin haka tace in riƙa kiranta.
A kwana na takwas ne ina zaune, bayan na gama sallar azahar ina tunanin su Mama a raina sai ga Aunty Nafisat ta shigo tacemin in shiryo mu tafi madam tana nemana. Lokaci guda annurin fuskata ya ɓace tare da jin wani irin faɗuwar gaba take na hau karanto addu'o'i. Daman nayi wanka already, wata Abaya ce maroon colour na ɗauko na saka tare da ɗaura ɗan kwalin na sake zura hijabi na a kai na cimma Aunty Nafisat Parlour muka tafi.
Wani parlourn ne na daban mai faɗi gaske ta nuna min yayin da ta juya daga bakin ƙofar ta koma abinta. Sai da na tsaya na gama sai ta kaina sannan na shiga ɗauke da sallama a baki na.
Ganin ta yau tare da wani wanda da alama mijinta ne yasa na tsaya tun daga nesa na tsuguna a ƙasa gaba na sai tsananta faɗuwa yake tamkar wadda za'a yanka naman jikin ta.
Na jima tsugune a wurin yayin da sukayi tamkar basu ganni ba suna ta maganar su a ƙasa ƙasa. Sai daga baya ta kalle shi tace.
“Farooq she's our surrogate...”
Sai kuma ta kalle ni tace.
"Hey! Look here. Kallo nan, tashi tsaye ya ganki”
Miƙewa nayi tsaye tare da kallon in da yake zaune kamar yadda ta umurce ni, sai dai daga ƙasƙantaccen kallon da naga ya fara bi na da shi ne yasa naji jikina yayi sanyi, kallo ne wanda har in koma ga Allah ba zan manta da shi ba duk da cewa ban san manufarsa ba. Wanda har cikin raina na ji na muzanta na kuma kunyata.
Cike da izgili ya zare ido ya kalli Hanifah yace.
“What! Oh no! It can't be possible Hanifah.Look at her Fa, wannan tsuntsuwar mi zata iya? daga ganin wannan ma abinci bai wadaci jikin ta ba, saboda haka she can't carry my baby gaskiya....”
Da sauri Hanifah tace..............
*OUM AMEER*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JDbgcC7yQyC5NhQw9Q1jFl💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA GOMA SHA HUƊU*
.......... “She can do it Farooq, I have already started preparing her, da shawarar doctor Nicholas ni ke amfani, he planned all the necessary nutrients for her so that she and our baby will be in good condition. Beside we are gonna stay together with her, So is our duty to take good care of her”
Girgiza kan shi yayi tare da kallon Hanifah yace.
"Hanifah! Hanifah har yanzu kina ganin cewa akan daidai kike?”
With full confidence tace.
“I'm 100% sure love, in sha Allah everything will go smoothly beyond your expectations”
Taɓe baki yayi tare da sake kallo na a karo na biyu, tun daga ƙasa na har sama sannan yace.
“While tunda har kince hakan yayi miki is ok. You can ask her to leave”
“Ki tafi”
Abinda na ji kenan ta faɗa, hakan yasa na juya na fice zuciya ta na wani tuƙuƙin baƙin ciki. Wai shin mi masu kuɗi suka ɗauki kan su ne a duniyar nan? ba fa saya ta suka yi ba ballantana suce yadda suka ga dama za su yi dani, ji wani kallon wulaƙancin da ya ke min tamkar an tilasta shi dole sai ya kalle ni banza a banza kawai, idan kuna taƙamar kuɗi ai Allah ba ruwan shi da wannan da zukata yake aiki ba jiki ba ko wani abin mutum mtsww! Wai harda Kirana Tsuntsuwa tsabar raina halittar Allah ko miye marabar matarsa da ni Oho! Don itama naga ba wani jikin a zo a gani ne da ita ba. ita kuma wannan matar bana tunanin ma cewa ta san suna na domin ko da wasa ban taɓa jin ta kira ni ba tsabar wulakanci, ni sai a yau nayi baƙin cikin rashin jin yaren nasara da bana ji kuma bana iya mayarwa, ɗan abinda nikeji da wanda nike iya mayarwa ɗin banji sunyi ko ɗaya ba ballantana in ce na fahimta domin da ina ji nasan tabbas zan fahimci ina suka dosa miye suke magana a kai. Kuma ai ban tilasta ta ba itace ta zaɓeni idan ban musu ba su mayar dani gidan Mama na mana. Tsaki na ja sai kuma a raina nace, ko ma dai miye ni dai buƙatata ta biya tunda har Mama ta samu lafiya ai shi kenan. Maimakon in ganni na ɓilla ƙofa ta kawai gani na nayi a wani wurin na daban, cikin ruɗewa na fara zare ido na rasa ina zan nufa, ga shegun mutanen har masu aiki wai turanci suke yi tsabar kinibibi da sanabe, domin duk wacce naga zasu yi magana da Aunty Nafisat da turanci suke yi so ba ni da halin in tambayi wani. Ina nan tsaye kamar an dasa Icce sai Aunty Nafisat na gani tana faɗin
“Bahiyya ina zaki je ne? Kin sani sai faman neman ki ni ke”
Dariya nayi kamar wata sakarya nace.
“Wallahi Aunty Nafisat manta hanyar nayi, kawai sai na tsinci kaina a nan”
“Eyyah sorry. To yanxu biyoni muje”
Babban kitchen ne ta jani wanda tunda ni ke ban taɓa ganin kitchen irin shi ba,komai an shirya shi bisa tsari gwanin burgewa. waigowa tayi ta kalle ni tace.
“Mi kike so ki ci yanzu?”
Cikin Mamaki na ce.
“Ai ban jima da cin abinci ba ko kin manta”
Girgiza kai tayi tace.
“Ban manta ba, Hajiya ce tace ki riƙa cin abinci time to time ba dole sai kina jin yunwa ba”
Cikin rashin fahimtar zancen nata nace.
“Bana jin yunwa, amma ki bani madarar nan mai daɗi irin ta ranar sannan ki haɗamin da naman kaza dafaffe”
"OK to muje in rakaki kada ki ƙara manta hanyar, Yanxu zan kawo miki”
************
HANIFAH
Bayan fitar Bahiyya zaunawa tayi kan cinyar sa tasa hannu tana yamutsa sumar kansa da ta sha gyara sosai tana murmushi tace.
“Ba lallai suna samun abinci mai gina jiki yadda ya kamata ba, but mu a nan zamu iya bata, Nafisat is taking good care of her, sannan Kuma wani gefen halittar jikin ta ne haka, kada ka damu. Gobe in sha Allah we will go to the hospital together for possible investigation, Idan an gama screening ɗinta Sai mu wuce kawai, you will become a father soon as you wish”
Kallonta yayi yace.
“Hanifah ya zamuyi da su Daddy ya zamuyi da Madinah?”
Murmushi tayi tace.
“Wannan duk mai sauƙi ne, We are going to surprised them, daman can 2years back Momma ta taɓa tambaya na cewa har yanzu bata samu jika ba, nace mata sai time yayi, to since then bata sake tambayana ba kuma, so we will plan to hide it for them, it will serve as a secret, after she put to bed Sai mu kira su mu faɗa musu cewa na haihu, ita kuma sai ta tafiyar ta, har Grand Ma Itama.”
Gyaɗa kan shi yayi tare da ɗaga ta daga kan thigh ɗinsa ya miƙe tsaye yace.
"It's ok. I have meeting tomorrow morning, so zan je zan tattauna da Mahi...”
Wani faɗuwar gaba taji wanda bata san dalili ba saboda kawai taji ya kira sunan Mahi.
Da sauri tace.
" Wait.. Wait..!”
Tsayawa yayi yace.
"What?”
Kai tsaye tace.
“Please let it be secret, don't tell him anything pls”
Ɗan jim yayi kaɗan sai kuma ya Gyaɗa kai yace.
“Ok”
Tana ganin ficewar sa ta koma daɓas kan kujera ta zauna tare da sauke wani nannauyan ajiyan zuciya tana girgiza kai a ranta tana faɗin. I hate you Mahi! I so much hate you with passion, you are the cause of all my stress, we have plan and build our life simple and understandable with so much love and care, duk abinda na faɗawa mijina yarda yake bai taɓa fushi dani ba, but daga lokacin da ya fara zama da kai sai ka shiga canja sa a hankali ya fara dawowa mijin bahaushiya, ya fara yi min magana cikin ihu da nuna shine a gaba ni bani wani right, I promise you Mahi Sai na ɗaukeshi baki ɗaya daga ƙasar nan ka daina ganinsa.
Sai kuma ta ja guntun tsaki tana ƙara tuna yadda yanzu Farooq ya canja baki ɗaya, komai na sa ya dawo na ganin laifi, gashi yanzu two-four bai da wani zance sai na haihuwa. Taya zata iya yafewa Mahi Madinat, a yanzu ta gama yarda a duniya bata da wasu maƙiyanda suka wuce mutum biyu ɗin nan.
*************
BAHIYYA
Zaune nake na baje ina kwasar wainar ƙwai da shayi mai bala'in kauri ga dankalin turawa daban ga farfesun kayan ciki sai tashin ƙamshi yake,a gaskiya ina jin daɗin rayuwar da nike ciki a yanzu, amma da zaran na tuna da kalar masu gidan sai in ji komai ya fita kaina kuma.
Sallama Aunty Nafisat tayi ta shigo ciki tare da sakar min murmushi tace.
“Sannu Bahiyya, idan kika gama ki shirya zaku fita da Hajiya...”
Cikin damuwa nace.
"Ina zamu je kuma”
Aunty Nafisat tace
“I don't know”
Nace
" To tare da ke zamu tafi”
Girgiza kanta tayi tace.
“A'a, ki yi ki shirya she's waiting for you, don't waste her time”
Cikin zaƙuwa nace.
“Aunty Nafisat dan Allah ko zaki koyamin turanci nima in riƙa ji ina mayarwa kamar ku?”
Dariya tayi tace.
" Kai Bahiyya, kina nufin baki iya turanci ba? A ina kika makaranta?”
Taɓe baki nayi nace.
“A garin mu na da Zamfara, government ce nayi kuma kin san karatun can sai a hankali ba kamar na nan ba ne, sannan gashi na shiga Ss3 ba daɗewa muka dawo nan,nan ɗin kuma ban ci gaba ba”
“OK! Idan mun samu time zan riƙa koyar da ke ta baki da kuma rubutu”
Cikin jindadi maganar ta nayi mata godiya sannan ta juya ta tafi. Ina jin daɗin Aunty Nafisat a gidan nan, ban san matsayin ta ba amma tana da kirki sosai.
Miƙewa nayi domin abincin gaba ɗaya ji nayi ya fitar min a kai, amma kuma sai da naci naman tukun sannan na tashi, domin ni a gaskiya ina son nama ba wasa.
Wanka nayi shaf-shaf na fito na mulke jikina da mayuka na sababbi sannan naje gun kayana na buɗe na saka sabbin undies cikin waɗanda aka kawo min na zaɓo wata Abaya onion color na saka sannan na zuba black hijab ɗina a kai na sanya black shoe na fito.
Da Aunty Nafisat naci karo ta yi min murmushi ta juya na bita har bakin mota,ta buɗe na shiga sannan ta koma, wanda a raina na rasa gane wannan kulawar ko ta miye domin abin har mamaki yake bani. Ko a motar nafi minti talatin da ni da direba muna zaune sannan ta ga dama ta fito.
Tana shigowa na kalle ta kaɗan cikin tsoro tsoro nace.
"Ina kwana”
Ba tare da ta ko kalli in da nake ba tace.
" Lafiya”
Daga haka ta fitar da wayar ta ta fara latsawa cikin harshen turanci na ji tayi wa direban magana shi kuma na ji yace OK Ma.
Tsaki naja cikin raina nace shegu kawai idan na koyi turancin ai sai inga tsiyar ƙarya duk in da ta kwana.
Duk da ba'a faɗamin ba na gane cewa asibiti ce. Asibiti? Mi kuma zamuyi a asibiti? Tambayar da na yiwa kaina kenan wanda nasan cewa bani da amsar ta sai dai in zuba na mujiyata in yi kallo.
Bayan munyi tafiya naga mun shiga wani babban wuri mai girma gashi ya sha kyau kamar ba asibiti ba. Wani office muka shiga wanda naga wani likita zaune ya tsuke cikin suit baƙa mai blue ɗin necktie.
Da sauri ya miƙe suka fara gaisuwa su biyu bayan sun gama ya zauna tare da kallona yana murmushi yacemin.
“Welcome, please have a seat”
Murmushi nayi masa kamar yadda ya yi min na zauna akan kujerar da naga ya na nunamin.
Ba wata doguwar magana sukayi ba sai naga ya miƙe yace in biyo sa, ba musu na tashi na bi shi, zuciya ta sai bugawa take akan tsoro.
Jinina aka fara ɗiba, sannan aka kaini wani ɗaki ana ta min wasu abubuwa na gwaji kamar mai wata rashin lafiya, tambayoyi ne suke cizon raina bani da kuma wanda zan tambaya, domin duk basa jin Hausa. Mun jima sosai a asibitin sannan daga bisani na fito ni ka ɗai likitan ya rakoni har bakin mota, sai da na shiga na zauna sannan yace min.
“Sai Anjima Beautiful”
Ji nayi kamar na kafa masa mari ɗan iskan, wai daman yana jin Hausa amma yayi kamar baya ji, tsaki naja tare da juya fuskata nayi masa banza.
Daga haka ya rufe motar direban yaja muka tafi.
Bayan mun koma gida abun still yana raina, Ina ganin Aunty Nafisat nace.
"Aunty Nafisat mi yasa ta kaini asibiti hala?”
Cikin mamaki tace.
" Miya faru ?”
Nan na gaya mata duk abinda aka min na gwaje-gwaje da kuma Jinina da aka ɗiba.
Tace min ba komai nasan harakar masu kudin nan sunfi son komai suyi shi akan ƙa'ida.
Daga haka na wuce ciki na yi wanka nayi sallah sannan na ci abinci na zauna aikin kallo, domin shi kaɗai ne aikina a yanzu, daga ci sai kwanciya sai kallo sai Sallah.
Washe gari ma haka akayi, Ina zaune tace in shirya zamu fita, biye nike ni dai aka kaini wurin yin passport na shirye shiryen tafiyarmu, tafiyar da ban san dalilin ta ba, ko da yake renon cikin zan tayata dole su yi min gwaji kada ace ina ɗauke da wata cutar da zan iya shafa mata ita da ɗanta.
Bayan mun gama wani babban shopping mall muka tafi, a can na tarar da Aunty Nafisat mamaki duk ya gama kamani. Dariya tayi tacemin muje in zaɓi duk abinda nike so a nan. Ƙarshe dai ita ce ta shiga zaɓar min domin ni ban san komai ba, ganin ban taɓa saka wancan kayan ba yasa ta ƙara jibgamin Abayas masu uban yawa, da kayan shafe shafe muka koma gida.
A yanzu kam na saba sosai da Aunty Nafisat domin ina zagewa muyi ta fira, yawancin firar kuma duk akan turancin ne akan na dage dole sai ta koyamin ni kuma ko da bala'i na ƙuduri sai na iya.
Muna cikin firar mu naji an kira ta a waya ta ɗauka cikin ladabi tana magana daga Ƙarshe ta yanke bayan sun gama.
Kallona tayi tace.
“Bahiyya muje na ta yaki ki shirya kayan ki gobe zaku tafi”
Murya a sanyaye nace.
"Gobe kuma? To da ke zamu tafi ko Aunty Nafisat?”
Girgiza kanta tayi tace.
“A'a.”
Daga haka ta wuce na bi bayanta zuwa ɗaki na.
Trolley biyu tayimin babba da ƙarama sai wata jakar handbag da muka siyo ranar wadda sai dai na riƙe don passion domin ban san mi zan saka a ciki ba.
Muna nan tare da ita har lokacin tafiyar ta gida yayi na rakota har bakin motar ta har da guntun hawaye na duk da nasan cewa gobe da ƙila kafin mu tafi da wuri zata zo amma ina jin kewar ta sosai a ciki raina.
Da dare bayan na kwanta, bacci kasa ɗaukata yayi, tunanin Mama ne kawai a raina da kuma Nuhaira, sai yanzu naji takaici domin ba riƙe numbern Mama ba da kuma ta Malama sannan banyi azancin rubutawa na riƙe ba, sai yanzu na gane cewa nayi shirme babba, taya zan yi shekara ba tare da jin muryar Mama ba? Ga matar nan er renin hankali, ban gama damar ta balle na tambaye ta. Yanzu dai idan muka tafi sai inga wa kuma zata samu wanda zai riƙa yi mata magana da ni tunda bata so tana magana dani, wanda ban san dalilin hakan ba.
Washe gari ma da na farka, sukuku na tashi tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.
Ina cikin shiryawa sai ga Aunty Nafisat ta shigo da murna naje na rungume ta.
Nan muka yi ta fira ta sai kuma ta tashi