Author : Yusrah Musa Abubakar Category : Hausa Novels 001
sa daga nesa zan baka irin kayan dana kawo masa ka gani biscuit da coculate muje maza ka kaini".
Da sauri almajirin ya wuce gaba mk ya bishi a baya da wani murmushin mugunta daga nesa da gidan suka tsaya almajirin yace" ga gidan can wancan malamin me rawani da yake zaune a tsakiya to shine baban ta gurinsa aka aiko ka" kai mk ya daga yana cewa" na gode kaji yaro toga caculate din taka" .
Karba almajirin yay yana tafiyarsa mk kuma ya zubawa baffa ido ko ba'a fada ba wannan mahaifin Safah ne ga dogon hancin ta nan ya gani juyawa yay yana komawa wajen motar sa bai karasa gurin baffan ba.
Mrs Al'ameen Ahmad ce,๐
Till we meet
Thank for your support๐น.
Typing
๐ Yusrah Musa Abubakar Gimba
Ayi hakuri da typing error๐จ banjin dadi๐ข kwana biyu.
๐ซANNURI ๐WRITER'S ๐ชASSOCIATION๐ซ
๐กHome of ๐คHospitality and ๐Harmony
๐SAFREEYYAH๐
๐๐ Zarah Musa dan adam
๐๐ Naja'at Musa Abubakar
๐๐ Kubrah Sani Muhammad.
#YUSRAHMS#
NO.47 ๐ 48
Safah kam na can tana shan lalle a gidan wata mata wacce itama yarta ta dawo daga birni gurin yan uwan su ta koyo acan tazo tana yi.
Da gudu Aisha ta shigo gidan tana guda kamar hancinta zai cire cikin dariya tace" ahayye ayyuruyuri nanaye anayi muna jin dadi ana bari muna jin haushi ta yaya murtala ikon Allah bada kanki a sare kije gida kice ya fadi kai jama'a Safara'u irin wannan kyau haka lallai kice gobe ango zai shana jifa wani kamshi da kike kamar kin fada a rijiyar turare meye ne sirrin fada min naji kafin nawa yazo kinga na kware".
Harararta Safah tay" idan kin gama shashancin zaki iya bani sakon dana aike ki" dariya Aisha tay" beban komai ba yace bashi da kudi kiyi hakuri" wani kallo Safah tay mata tana cewa" me kika ce"? Cikin tsokana Aisha tace" yace bashi da ko kwandala duk kin cinye masa kudi"
Au haka ma yace dama in yana da kwandala ma me zatai mai sake min lallen nan Furera na dawo" jin haka yasa da sauri Aisha ta fito da dubu biyu tana mika mata tace" gashi nan ya bani kar kisa yanzu yazo ya zane ni da bulala kowa yana biki jikinsa a ware ni ina dingishi kamar gurguwa"
Ke kika sani can da yawar ki debo min ruwa ni nayi wanka mu tafi gida" bokiti Aisha ta dauka tana cewa" yanzu ma kuwa amaryar mu bayan yayana za'a burge naki debowa bani minti daya ina dawowa ta shagonsa zanbi ya sako kwalbar turare guda daya a ruwan" tana fadin haka ta fita dan daga murya Safah tay yadda zata jita tace" banda lokacin shashancin ki nidai burina ki kawo min ruwa malama".
Bayan sallar isha dukkan nin kawayen Safah sun hadu zasu taya ta cin tsire suna zaune a karkashin bishiyar zaitun din cikin gidan su sun taru yan kamun amarya su Asabe sai juyi ake ana gadara ansha sabon dinkin da Safah tayo mata a Adamawa gefe guda tukunya ce babba akan wuta ana dafa abincin yan kamu.
Safah suna zaune a daki itada baffa cikin nasiha baffa yace" Safara'u tun yau base gobe ba zan fara miki nasiha ki rike darajar auren ki murtala yarone me hankali kuma kinga ke marainiya ce baki da uwa baki da me baki shawarra saini din dai dan Allah Safara'u idan Allah ya tashe mu lafiya gobe za'a daura miki aure kije dakin mijinki ki zama me hakuri da juriya ki rike Allah ki roke shi zai amsa miki ki tsaya a kofarsa zai karbeki ki nufe sa zai cire ki daga cikin kunci da damuwa ki dogara dashi ya isar miki ki kula sosai ke kadaice 'yata ina son ki amma dole aure shine zai raba mu inai miki fatan alkhari Allah yayi miki albarka ya tsare ki a duk inda kika tsinci kanki".
Safah da hawaye ke zarya a kuncin ta da 'kyar muryarta na rawa tace" amin baffa nagode lallai kai ubah ne nagari wanda kowacce d'iya zatai alfahari da kai".
Kai baffa ya jinjina zaiyi magana suka ji anyi sallama a kofar dakin wani yaro na cewa" wai ance Safara'u tazo a waje".
Kallon juna sukai itada baffa kafin tace" kaje kace wai inji waye"? Dakatar da yaron baffa yay yana cewa" baki sani ba ko murtala ne kije ki gano mana amma karki dade kinga kin bar kawayen ki kuma na ji kina cewa a gurin maryama zaku kwana dasu" eh baffa acan zamu kwana bari na dawo" fita tay yayin da sukai karo da Aisha.
Dan dafe goshi Aisha tay tan acewa" wash saurin me kike haka zaki lagarta ni"? tura ta gefe Safah tay tana cewa" ke matsa mana kin wani tare min hanya murtala ne yake kira na" dariya Aisha tay" oh wannan shine angon zumudi inace gobe iyanzu an raka ki amma yaudin ma bazai barki ki huta ba" kallonta Safah tay" kinga ban hanya kar yaga na dade" matsawa Aisha tay" inye cankadi kaga masu miji gaskiya kar yaga kin dade duk da komai kikai burgeshi yake ke amarya ce bakya lefi ko kin cinnawa shagon angon ki wuta zaice kuskure ne ki karbo kudin tsiren tare dani dan Allah" banza Safah ta mata tana fita a gidan.
Ganin bata ga murtalan inda ya saba tsayawa ba idan yazo gurinta yasa ta cewa yaron" kai yana ina ne ban ganshi ba" dan tafiya sukai yaron yace mata" yana waccan bishiyar yace ki same shi" to tace yaron kuma ya juya abin sa.
Cikin mamaki Safah ta nufi bishiyar domin ta gano shi a zaune amma me yasa yau sai nan bayan koda wasa bai taba yin hakan ba ita kadai take tunani a zuciyarta harta karasa gurin da sallama tace" haba murtala yau kuma shirar harnan bayan layin mu me yasa baza ka karasa ba"?.
Mikewa tsaye mk yay yana cewa" wannan hamsim ne ba murtalan da kika sani bane barka da zuwa big girl nasan kinyi mamakin gani na amma ina tunanin kinsan abinda kika aikata min jiya kodan ba lallai ki tuna ba tunda karamar kwakwalwa gareki me kike tunani a kaina dama saboda rashin hankali da kike cemin wata rana zaki,tona min asiri gurin mahaifana da gaske kike? yayi kyau saidai karki manta abinda nace miki a waccan lokacin cewa idan tsautsayi yasa kika tona min asirina zan kashe ki kuma ban fasa ba yanzu ma abinda ya kawo ni kenan fatan kin shirya amsar hukuncinki big girl idan harkin shirya to nima a shirye nake".
Duk jikin Safah rawa yake saboda tsoro dan ja da baya tay tana kallon sa tace" ban fadawa hajiya don tayi maka wani abuba nafada mata ne tayi maka fada kuma ka shiryu ka gane cewa abinda kake bashi dakyau amma tunda kaidin batacce ne sai ince Allah ya shiryar dakai kuma kayi hakuri abinda ya faru na roke ka mk ba wata alaka tsakani na dakai ka rabu dani nayi rayuwa gobe ne daurin aurena karka bata min shiri bani da wani hadi dakai ka dauka ban sanka ba ka manta da komai ka gyara halin ka kanemi yafiya a gurin wanda ya halicceka ka daina saba masa kai mutum ne baudadde mara kyan hali kayi kokarin gyara halinka tun lokaci bai kure maka ba".
Kara bude idanuwan sa yay akanta jin abinda tace yana jijjiga kai yace" humm big girl kina ban dariya kuma kina bata lokacinki amfada miki wa'azi nazo kimin idai haka kike tunani to kinci kai babu abinda ya kawo ni wannan jakin sokon kauyen naku sai daukar fansa akan ki baki gane bane amma yanzu zan ganar dake ".
Cikin dakewa Safah tace" me kake nufi"?.
Fito da wuka yay yana kallonta yace "ga abinda zanyi kasheki zanyi na shafe tarihin ki a rayuwa shine babban burina".
Matsawa Safah tay tana kallonshi tace" karya ne wallhi nafi karfin ka wulakanta ni kaidin banza".
Jin abinda take cewa a fusace ya zare wukar daga cikin gidan ta ya nufo tada iya karfinsa ganin da gaske yake kashe ta zaiyi yasa a guje ta juya zuwa gida amma tayi rashin sa'a yasha gaban ta yana huci yace" ina kuma za kije ashe dai ina da zarra ki tsaya mana tunda kince kinfi karfina".
Ganin ya sake tahowa gurin ta gadan-gadan yasa da mugun gudu ta juya yayin da yabi bayan ta da iya karfinsa.............
Tofaaaaa muje zuwa..... ga mai son cigabansa sai a tuntu'be ni tanan.
+234 816 098 3083
#400
Account no:2410673902
Yusrah Musa Zenith bank๐ฆ.
MINISTER ASHRAF #300
ME KAMAR SARKI #300
ROYALTY 500
Ga masu bu'katar siya Kuna iya kumin magana da wancan WhatsApp number Nawa ta sama.
YMA DUTSE NEW WORLD๐๐.
๐น๐๐น๐๐น๐๐น๐๐น๐๐น๐๐น๐
๐ต๏ธ๐น๐ผ.