Chapter 29 Reading WADATAR ZUCI Complete Book by Aisha Alto.txt Arewa Novels

WADATAR ZUCI Complete Book by Aisha Alto.txt

Author :  Aisha Alto Category :  A Books

Chapter   29 / 38

84K to 87K   out of 113.4K words

zuba masa ido tana kallonsa sama da ƙasa, ganin irin mashahuriyar shigar alfarmar dake jikinsa ne ya ƙara gigita mata tunani.
Wani irin tsananin farin ciki mara misaltuwa yau Mama take jin kanta a ciki.
Karkacewa yayi gefe ya zura hannu cikin aljihun wandon tsadaddiyar shaddar dake jikinsa ya zaro kuɗi masu yawa ya zube a gabanta yana faɗin "Ga wannan ba yawa ayi haƙuri, sai na da ɗa zagayowa..."
Ko kafin ya gama rufe baki Mama ta fara tattare kuɗin tana faɗin "Haba ba komai wallahi, mai yawan kenan wannan ai kyautar manya ce..." Ta faɗa kai tsaye, kafin kuma ta shiga kwallawa Ilham da Amatullah kira tana faɗin "Amatu.. Ilham Ina kuke ne..? Maza kuzo ku gaida yayanku zai wuce..." Ta ƙarashe maganar lokaci ɗaya tana tattare kuɗin da hanzari ta tura a hijabinta.
Fitowa su Amatullah ɗin sukayi suka gaishesa, da murmushi a fuskarsa ya amsa musu, ganin ya zura hannu a aljihu yana ƙirgo kuɗi ne yasa Mama sake washe baki tana zuba masa godiya kamar bakinta zai yage saboda tsantsar farin cikin da take ciki.


Kuɗi masu yawa ya damƙo a hannunsa ya miƙa musu, da sauri Mama tasa hannu ta karɓe tana faɗin "A'a ranka ya daɗe kuma har da ƙarin wata wahalar haka..? Mun gode mun gode Allah ya saka da alkhairi, Allah yasa a gama da duniya lafiya mun gode..mun gode Allah ya raya zuri'a yayi musu albarka..."


Miƙewa yayi zai tafi, Mama ta miƙe da sauri itama tana ƙara kwarara masa godiya, a hankali ya zura takalmansa da tunda ya zauna Mama take gyara mai zamansu ta matsar mai dasu dai-dai gurin ƙafarsa ta yadda zai zura cikin sauƙi, miƙewa Fadwa tayi itama cikin rawar jiki ta rufa masa baya, Mama kuwa sai data rakosa har cikin zaure, sannan ta juya ta koma cikin gida cike da tsananin farin ciki, su kuma suka fita shida Fadwa.


Jiki na rawa Mama ta zauna ta miƙe ƙafafu bayan ta zube kuɗin duka a gabanta ta hau ƙirgawa.


A ɓangaren Fadwa kuwa koda suka ƙarasa gurin motarsa bai wani tsaya dogon zancen da ita ba ya buɗe mota ya shiga ya zauna kana ya buɗe mata ɗayan gefen itama yace ta shigo, ba tare da wani tunanin komai ba kuwa ta zagaya da sauri ta shige tana ji tamkar ta taka rawa saboda tsabar murna.


Juyowa yayi ya ɗan kalli fuskarta da har lokacin take ɗauke da fara'a, kafin a hankali ya kamo hannunta ya riƙe a nasa wanda kamar dama Fadwa jira take ya riƙe hannun nata, ta ƙara matsawa jikinsa sosai ta kwantar da kanta a kafaɗarsa, ɗan murmushi yayi tare da ƙara damƙe hannunta a nasa kafin kamar daga sama taji muryarsa yana faɗin "Baby ina matuƙar sonki ina ƙaunarki, zaki aureni...?" Ya faɗa cikin wani irin salo da shine kaɗai yasan ma'anarsa.


Zaro idanu Fadwa tayi cike da tsantsar mamaki da kaɗuwa tana faɗin "Why not ranka ya daɗe..me zai hana...?" Ta faɗa kai tsaye tana tsaresa da manyan idanuwanta waɗanda ke cike da tsantsar farin ciki da jin daɗi.


Numfashi yaja a hankali kafin ya zame hannunsa a nata yana faɗin "Ok ba matsala, ni zan wuce ki bani numbern wayarki zan kiraki sai mu ƙarashe maganar a waya...."


Jinjina masa kai tayi cike da farin ciki tana washe baki, kafin taga ya buɗe wani guri a cikin motar ya ɗauko kuɗi sabbi fil rafa guda ya miƙa miƙa mata yace "Gashi ki siya kati da kayan kwalliya, kafin insa ayo miki odern wasu daga Dubai..."


Karɓa tayi tana masa godiya tamkar zata zube ƙasa dan farin ciki, fitowa tai. daga motar ta nufi cikin gida yayinda shi kuma yaja motar ya bar unguwar.


Da ihun murnarta ta shigo cikin gidan, Mama dasu Ilham suna zaune har lokacin a tsakar gida Mama nata lissafin kuɗi.
Murmushi kawai Fadwa tayi ta zauna tana duban Ilham da itama itan ta tsare da idanu tana kallonta.
Kwaɓe fuska Fadwan tayi ta taɓe baki kafin ta juya ta miƙawa Mama kuɗin dake hannunta tana hararar Ilham data tsare ta ido, tana faɗin "Kinga inda ake harkar arziki ko Ilham...? Amma kullum ki damu mutane da zancen in koma gidan Ya Azeez duk kibi ki damu mutane da zancen sa saboda baki san ɗumbin alkhairin dake kirana ba kikeso ki ƙara turani gurin tsiya sai kace wata uwar abun na tsinta a auren nasa da har kike min sha'awar komawa in cigaba da zama dashi, shegiya mai baƙin halin tsiya da munafunci. To kiga dai harkar arziki yau yau ɗin nan daga ganina mutum ya biyo ni har gida ji bi abun alkhairin da yayi mana nida ku..? Amma sai ki ta damun mutane da maganar wani banza can Ya Azeez sai kace ƙanin uwarki kona ubanki..." Ta ƙarashe maganar a zafafe tana watsa mata harara.




Kauda kai kawai Ilham ɗin tayi ba tare kuma da ta tanka mata ba, ta miƙe tsaye ta zura takalmanta ta wuce ɗaki tana mai tsananin takaici da baƙin cikin halin kwaɗayi da son abun duniya irin na mahaifiyar tasu da Auntyn su.


Ita kuwa Mama ko bi ta kansu ma ba tayi ba tana can gurin hidimar lissafa kuɗin da Fadwa ta shigo dasu, zaro idanu tayi tare da kama hanci lokaci ɗaya ta saki guɗa, kafin kuma cike da tsananin farin ciki tace "Kan uban nan kai..kinji inda ake harkar arziki, Lallai yau munyi gamdakatar..." Ta faɗa lokaci ɗaya tana barbaje kuɗin a gabanta tana kallo, ganin yanda kuɗin sukai wani caa agabanta ne yasa ta ƙara zaro idanunta waje tace "Kiga tsabar kuɗi dan Allah kiga irin wannan abun arziki..? Wuri na gugar wuri naira na gugar naira har naira dubu ɗari cif cif, ga kuma wanda ya bani dubu hamsin sai wanda yabawa su Amatu suma dubu ashirin, dubu ɗari da saba'in fa kenan a daren nan..? Kai!! Amma wannan mutumi yayi wallahi yayi ba ƙarya..." Ta faɗa cikin fara'a da tsananin farin ciki tana washe baki.


Tashi Amatullah tayi itama ta bar gurin tana mai musu addu'a da fatan shiriya a zuciyarta ta wuce ɗakinsu.


Su ko su Mama da Fadwa ko a jikinsu babu wanda yabi ta kansu, haka sukai ta murnar kuɗinsu suna jin daɗi. Kafin daga bisani Mama da taga lokacin dawowar Abba gida yayi ta tattare kuɗin ta shige dasu ɗakinta taje ta ɓoye a cikin kayanta sannan ta dawo suka cigaba da tattaunawa akan sabon saurayin a Fadwa.








**********




Washegari


Misalin ƙarfe 4pm. Dai-dai na yamma zaune yake a tsararren falonsa dake cikin gidan Abba yana latsa tsadaddiyar wayarsa ƙirar iPhone 12pro max.
Sanye yake da wata tsadaddiyar shaddar Bazan mai kyau da yarari kalar ruwan toka, sai rufaffen takalmin ƙafarsa daya kasance baƙi, haka hular kansa zanna bukar mai zanen baƙi ce.


Sai kyakkyawan haɗaɗɗen agogon baƙin fatan dake ɗaure a hannunsa na kamfanin Rado, sosai shigar tayi masa bala'in kyau, dan shi karan kansa daya gama shiryawa kafin ya fito, sai daya kai dubansa ga madubi ya ɗan murmusa, domin shi a karan kansa sai daya yaba da tsantsar kyau na musamman da yaga shigar tayi masa.
Sannan ga wani irin masifaffen ƙamshi na musamman da daɗin shaƙa da yake fitarwa a jikinsa, lallausan sajen nan nasa kuwa ya kwanta luf luf sai ya ƙara fito da ainihin kyaun fuskarsa da zallar haiba da kwarjininsa, sai sheƙi yake kamar wani sabon ango.


A hankali ya gyara zaman hular dake kansa yana duba agogon dake hannunsa, kafin ya saki tsaki lokaci ɗaya yana miƙewa tsaye da wayarsa riƙe a hannunsa yasa kai ya fice daga falon.


Direct sashen Fahad dake can wani ɓangare daban a cikin gidan ya nufa, cikin takunsa na isassun maza masu ji da kansu, da sassarfa ya ƙarasa ƙaramar ƙofar gate ɗin gidan ya tsaya yana ɗan ƙwanƙwasawa.
Jin shiru ba'a buɗe bane yasa ya tura ƙofar a hankali ya shiga kai tsaye yana ƙarewa ɗan madaidaicin ƙaramin filin tsakar gidan da aka ƙayatasa da shukar furanni masu ƙamshi da ɗaukar ido.


Yana isa dai-dai ƙofar da zata sadashi da shiga falon gidan ne kuma ya fara jiyo dariyar Fahad ɗin daga can cikin falon yana faɗin "Pls pls pls Baby..kiyi haƙuri bazan daɗe ba yanzu zan dawo kinji...?"


Kansa ya ɗan girgiza tare da lumshe idanunsa, kafin kuma a hankali yasa hannu ya fara ƙwanƙwasa ƙofar falon.


Buɗe ƙofar falon da Fahad ɗin yayi ne yasa ya tamke fuska yana harararsa kafin juya yana faɗin "Idan ka fasa zuwa ne ai da tun tuni ka sanar dani in wuce abuna, amma saboda ka maidani ɗan iska shine zaka wani shanyani ka barni ina ta zaman jiranka, kai kazo ka wani rashe ka miƙe ƙafafu ka barni acan inata kiranka ma ka ƙi ɗauka..." Ya faɗa da alamun gajiya da zaman jiran nasa da yayi.


A karkace Fahad ya kallesa kafin yace "Kasan abinka dame iyali, wallahi hanani fita tayi sai dana lallasheta na lalaɓata tukunna. Kuma lokacin da kake kira ina kallon kiran naka amma bani da lokacin ɗagawa ne saboda ina kan lallashi iyalina..." Ya faɗa cike da tsokana yana ɗaga masa gira.


Sakin baki galala kawai Ya Azeez yayi yana kallonsa, kafin ya kaɗa kai ya juya ba tare da ya tanka mai ba ya kama hanyar ficewa daga cikin gidan, saboda yasan halin Fahad idan ya biye masa yanzun nan zai fara mai terere yana mai gorin bai da mata dan haka ya barshi ya kula da tashi matar, tunda shi yanzu gwauro ne baida mai lallaɓasa.


Shiko Fahad ganin ya fice ne bai ce mai komai ba, yasa ya bi bayansa da sauri yana ƙoƙarin danne dariyar dake taso masa.


Koda ya ƙarasa ya iske har ya buɗe motarsa ya shiga ya zauna, yana ƙoƙarin tada motar, da gudu ya ƙarasa ya buɗe ɗayan ɓangaren ya shiga ya zauna, ko gama rufe ƙofar kuwa bai yi ba Ya Azeez ɗin yaja motar da gudu ya tunkari gate, zaro idanu Fahad yayi cike da tsoro yana faɗin "Aboki meye haka ne wai...?" Ya faɗa da mamaki yana kallonsa, hararansa Ya Azeez ɗin yayi kafin yace "Sauka ka hau taka motar, sai mu haɗe acan tunda kasan gidan..." Ya faɗa tare da taka motar a guje bayan maigadi ya buɗe masa gate ya fice daga cikin gidan.


Kallonsa Fahad yayi kafin yace "Wai meye na duk wannan fushin ne kake ta wani cin magani, daga faɗar gaskiya kawai sai cibi ya zama ƙari...?"


Kai tsaye Ya Azeez yace mai "Nima ka jira lokaci ka gani yaro, na kusa in baka mamaki. Kai ƙaramin ɗan iska ne sabon shiga..."


Kallonsa Fahad yayi kafin yace "Kan uban nan kai, ni kake kira da yaro..? Ina shirin zama Daddy amma saboda tsabar tsaurin ido irin naka shine kake kirana da yaro...?"


Ko kallonsa Ya Azeez bai yi ba yace "Kaji dashi dai..."


Wani kallo Fahad ya watsa mai kafin yace "Gwauro kawai..." Ya faɗa cike da jin haushin kiransa da yaro da yayi.


Bai tanka masa ba yayi banza dashi, ya ci gaba da tuƙinsa cikin ƙwarewa a haka har suka shiga tsararriyar unguwar ta Nasarawa Gra.


Suna isa dai-dai tangamemen gate ɗin gidan Alhaji Bello Ɗan Ƙwarai, Ya Azeez yayi horn da hanzari maigadi ya taso ya wangale musu gate, cikin natsuwa ya sako hancin motarsa cikin gidan kafin a hankali ya ƙarasa inda aka tanada domin ajiye motoci ya faka motar.


A kuma Dai-dai lokacin ne direban Alhaji Bello Ɗan Ƙwarai ya zuba horn a bakin gate ɗin gidan nasa, inda da sauri maigadin ya tashi yaje ya wangale masa ƙofar gate ɗin kafin a hankali direban ya silalo motar ya shigo cikin gidan.


Bayan ya gama daidaita parking ne kuma maigadin ya ƙaraso da sauri ya buɗe masa murfin motar yayinda lokaci ɗaya kuma ya ɗan rusuna yana yi masa barka da dawowa, a hankali ya fito daga cikin motar yana mai kallon motar su Ya Azeez dake fake a kusa da tashi, wanda kuma har lokacin suna ciki basu fito ba.


Ganin Alhaji Bello Ɗan Ƙwarai ɗin ne kuma yasa Fahad saurin buɗe motar ya fito yana ƙarasowa gabansa ya rusuna yana gaishesa, ganin haka ne kuma yasa Ya Azeez buɗe motar shima ya fito cikin natsuwa ya ƙaraso gabansu ya ɗan rusuna yana gaishesa.
Da fara'a Alhaji Bello Ɗan Ƙwarai ya amsa musu, kana kuma cikin tsananin farin ciki da jin daɗin ganinsu ya ɗago su atare yana riƙe da hannayensu suka nufi cikin gidan kai tsaye.


































*Ya Allah ka gafartawa mahaifina da sauran Musulmi baki ɗaya🤲*
[12/23, 10:19 AM] Janafty: *WADATAR ZUCCI*




*Wattpad: Aishaalto09*








3️⃣3️⃣






A tare dukkansu suka shiga cikin falon yayinda Alhaji Bello Ɗan Ƙwarai ya sake riƙe hannun Ya Azeez ƙam a cikin nasa, wanda kuma a zuciyarsa yaje jin wani irin tsananin nishaɗi da tsantsar farin ciki mara misaltuwa.


Suna ƙarasowa tsakiyar falon kuwa Alhaji Bello Ɗan Ƙwarai ya shiga kwallawa Ummi kira yana faɗin "Khadija..! Khadija..!! Ina kike ki fito mun yi baƙi..." Ya faɗa cikin ɗan ɗaga murya ta yadda duk inda Ummin take zata jiyosa.


Kasancewar kuma suna kichin ne ita da Zahra yasa cikin hanzari suka bar abinda sukeyi suka fito a tare da sauri zuwa babban falon.


Ummi ce akan gaba sai Zahra dake biye da ita a baya, tana faɗin "Ko daga ina kuma baƙin suka zo da yamma nan oho..." Ta faɗa cikin ƙagara da son ganin baƙin nasu.


Da Fahad ta fara arba zaune a saman kujera yana sakin murmushi, kafin kuma idonta ya sauka akan Ya Azeez dake zaune shima a gefen Fahad ɗin hannunsa riƙe da makullin mota da wayarsa yana kallonta.


Tsayawa tai cak tana kallonsa kafin ta washe baki lokaci ɗaya ta taho da gudu tana faɗin "Laaa Ya Abdul kaine..dama kasan gidan mu ne yaushe kazo...?" Ta jero masa tambayoyin duka a tare cikin matsanancin farin ciki da mamaki tana kallonsa.


Ya Azeez kuwa dake zaune fuskarsa ɗauke da tsananin farin ciki da kuma mamakin ganin Zahran da yayi a gidan, ya sake faɗaɗa fara'arsa yana kallonta still kuma fuskarsa ɗauke da murmushi yace "Dama nan ne gidanku..ina Auntynki...?"


Rausayar da kai Zahra tayi kafin tace "Aunty Shatu tana ɗaki yanzu ta haura sama, bari inje in kirata tazo ku gaisa..." Ta faɗa kai tsaye tare da juyawa da sauri ta haura sama zuwa ɗakinsu domin kiran Shatun.


Murmushi Abbie da Ummi sukayi tare da juyawa suna kallon Zahra data ƙarasa haurawa saman da gudu tana kwallawa Shatu kira, kafin kuma lokaci ɗaya su dawo da kallonsu kan Ya Azeez wanda shima Zahran yabi da kallo yana sakin wani lallausan murmushi daya ƙarawa kyakkyawar fuskarsa kyau da haiba.


Sake kallonsa Abbie yayi fuskarsa ɗauke da fara'a yana faɗin "Au ashe kama sansu tunda gashi naji kai tsaye Zahra ta ambaci sunanka...?"


Jinjina mai kai Ya Azeez ɗin yayi, kana ya buɗe baki kenan zai bashi amsa.


Dai-dai lokacin kuma Shatu da Zahra suka sauko a tare zuwa cikin falon, yayinda ganin fitowar Shatun kuma tasa gabaki ɗaya hankali da tunanin Ya Azeez ɗin sukutum ya tafi gareta, wanda a ɓangaren ta itama hakan ce ta kasance.
Idanunsu gaba ɗaya suka zubawa juna, yayinda lokaci ɗaya Ya Azeez yaji wani irin abu ya daki ƙirjinsa, sakamakon kallon kyakkyawar fuskar Shatun da yayi.


Wani irin tsantsar mamaki ne ya lulluɓe Fahad, yayinda yaga yadda Ya Azeez ɗin ya tattara gabaki ɗaya hankali da natsuwarsa kacokan ya ɗora akan Shatu wacce gaba ɗaya itama ta shagala da kallonsa lokaci ɗaya tana sakin wata ɓoyayyiyar ajiyar zuciya.


Matsawa kusa dashi Fahad yayi kana cikin dabara ya zunguri gefen kafaɗarsa yana galla masa harara, kafin kuma cikin yin ƙasa ƙasa da murya yace "Dalla Malam ka natsu ka dawo hayyacinka..ka wani saki baki da hanci kamar gaula sai ƙarewa ƴar mutane kallo kake sai kace wani maye, kai ko kunyar iyayenta ma bakaji ba..." Ya ƙarashe maganar lokaci ɗaya yana yi masa nuni da Abbie daya zuba musu ido yana kallonsu.


Wani kallon banza Ya Azeez ya juyo ya watsa mai kafin ya ɗauke kai yana faɗin "Ina ruwanka dani...? Kai uban me ya kai idonka kanta da har kasan ina ƙare mata kallo in banda tsabar gulma da shegen sa idonka...?" Ya faɗa tare da haɗe rai yana zafga masa harara.


Dariya ce taso kufcewa Fahad amma sai bai bari ta fito fili ba, yayi sauri ya haɗiyeta kafin yace "Allah ya huci zuciyar gwarzon mazaje angon Hajiya Fadwa..."
Ya faɗa cikin tsokana yana cigaba da danne dariyarsa, banza dashi Ya Azeez yayi bai tanka masa ba, saboda ya fahimci take takensa so yake ya biye mai su raba hali a gidan mutane, shi kam bada shi ba.
Ba zai yarda ya barshi da jin nauyi da kunyar mutanen gidan ba, duk da bai san dalilin Abba na turo su gidan da yayi ba, kawai yace suzo ne su gaishe da Abbie da Ummi, sannan ya gaisa da babbar ƴar Alhaji Bellon kuma ya ganta idan tayi masa.


Ita kuwa Ummi tuni ta koma kichin da hanzari domin ta kawo musu abun motsa baki.
Ba jimawa kuwa sai gata ta fito riƙe da wani ɗan madaidaicin farati ɗauke da juices da ruwan gora mai sanyi sai wani ƙaramin filet data zubo fruit masu sanyi akai tazo ta ajiye a gabansu kana ta koma kusa da Abbie ta zauna, tana kallonsu Zahra da Shatu da sukai cirko cirko a tsaye, Zahra sai faman washe baki take kamar wacce aka yiwa bushara da gidan aljanna, Shatu kuwa juyawa tai da sauri ta wuce ɗakinsu da hanzari yayinda a zuciyarta kuwa har lokacin take cike da matsanancin mamakin ganinsa a gidan nasu, wanda kuma hakan yasa har ta manta da yanayin shigar da ke jikinta ta fito a haka.
Inda take sanye da wasu tausasan riga da wando masu kamar sleeping dress marasa kauri, sosai kayan sukayi masifar bin jikinta musamman ma wandon daya bayyana shape ɗin cikakkun hips ɗinta masu faɗi, sai kuma rigar data kasance mai ɗan faɗi kaɗan wacce ta ɗan kamata ta bayyana tudun cikakkun ƙirjinta.
Gaba ɗaya sha'afa tayi ta manta lokacin da Zahra taje kiranta ta biyota a yadda take gashi kanta ko ɗankwali babu sai lallausan baƙin dogon gashinta dake ta sheƙi daya zubo har kan kafaɗarta, domin ita duk a zatonta ƙarya kawai Zahran take da tace mata Ya Abdul ɗin yazo gidansu shiyasa ta fito da sauri dan taga zahiri.
Bin ta sukayi da kallo dukkansu har sai data ɓacewa ganinsu kafin Ya Azeez ya iya ɗauke manyan

29 / 38