Chapter 46 Reading Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt Arewa Novels

Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt

Author :  Nimcyluv Zeey Kumurya Category :  A Books

Chapter   46 / 78

135K to 138K   out of 231.7K words

ƙaramin bakinta cikin muryarsa mai nutsuwa da kamala wacce girma da samartaka suka ƙara kamata ya ce.

"Yaya"
Ya faɗa yana kallon Fuskarta sai kuma ya ce "Akwai matsala yaya, na kasa samun nutsuwa me ya sa kike zuwa cikin baccina kina kiran sunana tare da yi min kuka? Why Angel ko akwai abin da ya ke damunki? Bai kamata ki damu ba, kina tare da wanda kike so kika zaɓa matsayin abokin Rayuwar ki. Uba ga yaranki kin samu abin da ki ke so. Nima kuma zan maki tawa rantsuwar yanzu"

Miƙewa tsaye ya yi hannunsa zube cikin Aljihu gashin ƙirjinsa ya kwantar lub sai sheƙi yake a saman farar fatarsa abin ka da farin bafulatani. Da ɗan sauri-sauri yake duba cikin wata box har ya samu sabuwar reza jikinsa na rawa ya ɗauki reza ɗin tare da tsayawa akan photon Abra ya ce.

"I, Salman Khamal Khamis, promise you if I don't find you as my wife... Ni ba ɗan halak bane Abra" yana faɗin hakan ya tsaga tafin hannunsa da rezar nan ta ke jini ya fara zuba, Murmushi ya yi yana zubawa photonta ido ganin jinin da ke zuba a jikinsa yana sauka a photon ya ce.

"Ban damu da shekara nawa za kuyi tare ba, ban damu da yaran da zaku haifa tare ba, ban damu da girma ko tsofan da zaki kafin na dawo gareki ba, ke nake buƙata a cikin rayuwata. IDAN BA KE babu ni Abra, I love You, I love, I love Abra Khamal Khamis" Yana faɗin haka ya sake tsaga hannunsa da rezar ga wani gumin azaba dake tsastsafo masa a tsakiyar goshinsa. Kamar yana magana da photon nata ya ce "Yaya, I promise to love you unconditionally.
Darling, you are the love of my life, I promise never to break your heart as it will also break mine. I love you so much. I promise to be with you forever.
Honey, I know life has many challenges, but I promise to be dedicated to you. For better or worse I will always stand by your side until death separates us"

A hankali wasu hawaye Masu zafi suka shiga fitowa daga cikin idanunsa, amma a hakan bai sare ba ya ƙara sakin Murmushi wanda ya fidda zallar kyansa cikin wata kalar Murya wacce babu tsoro ko rauni a cikinta ya ce.

"Every day when I wake up, the first thing that comes to my mind is you. You know, how only a few things in this world make you happy with the fact that they are there and make your life great. You are one of those very few things. Thank you for being my destiny.
You are my destiny. You are my dream come true. I can’t imagine myself with anyone else. I love you and just want to thank you for every single thing you do. You are the reason why I live, the air that I breathe and the love of my life!Wherever you go, whatever you do, I want you to know that you are my destiny"

Ƙirjinsa ya buɗe jikinsa na rawa na tsananin azaba amma a haka ya rubuta alphabet letter na A. Nan take jini ya fara zuba kamar daga sama wani abokinsa mai suna Sunday ya shigo ganin Salman cikin wannan hali ya sa Sunday faɗin.

"What happened to you Friend?" Shiru Salmanun-faris ya yi yana kifa kansa a jikin photon Abra. While jini na zuba daga ƙirjinsa zuwa hannunsa. Sunday ya matsa kusa da Salman ya ce.

"你怎么了?你的情况呢? Nǐ zěnmeliǎo? Nǐ de qíngkuàng ne?" Ma'ana "Mene ya sameka? Kalli halin da kake ciki fa?".

Salman was speechless, hannunsa ɗaya dafe da ƙirjinsa ɗayan kuma ya rungome photon Abra a jikinsa idanuna rufe. Ganin Salman yaƙi magana ya sanya Sunday matsawa tare da ƙoƙarin taɓa Salman a hargitse cikin zafin zuciya ya ce.

"Don't torch me, i Said get out of my room".

Abbi da Adnan na zaune a gefen gadon da aka kwantar da Abra, har lokacin bata ta shi ba. Abbi da hankalinsa ke kanta a hankali yaga tana motsa bakinta kamar mai yin magana, sai hannunta da yake ɗan fisga, ganin yadda bakin ke motsawa sosai ya sanya Abbi matsawa kusa da ita, tare da ranƙwafawa daidai saitin bakinta. Ga mmakinsa babu abin da take cewa Maybe zafin ciwo yasa take haka.

"Innalillahi Faris, Faris mene wannan, mu gani" da sauri wannan kalaman suke fita daga cikin bakinta a kuma bayyane, Adnan dake zaune ya gyara zama yana binta da masifaffun idanunsa, wanda kuma zallar kallo ne na taƙaici musamman ganin yadda Abbi yake da riƙeta shi ba muharraminta ba, ga wannan ban zan Salman da take kira ba dare ba rana ba kullum bakinta cikin ambaton sunansa yake.

Kama hannunta Abbi ya yi cikin kulawa ya ce "Sweetheart kin farka?" A hankali ta buɗe idanunta bakinta har lokacin yana motsawa. Kallon Abbi ta shiga yi wani Irin kallo mai kama dana tuhuma, Murmushi yayi yace "Sannu Sweetheart sannu Kinji" kafin tai magana Adnan ya tashi da sauri ya zo inda take gaba ɗaya kan gadon ya hau ya ce.

"Naji tsoro Angel, i can't life without you ki daina suma irin haka please Angel zuciyata ba zata ɗauka ba" ya ƙare maganar yana ɗora kanta a kan cinyarsa, ya shiga shafa kanta. Da ace tana da ƙwarin barin jikinsa tabbas da tayi haka domin babu abin da zai sanya ga Abbinta wannan mugun azzalumin ya riƙe tare da nuna mata soyayyar ƙarya. Maganganun Abbi ta tuna wanda ya sanya ta fara zubar da hawaye ba tare data shirya ba. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wacce kalar rana yau ta zame mini? wacce rayuwa zan fuskanta a nan gaba, mene aikata a gare su da suka zaɓi haihuwata ta wannan sigar tare da yardani? Laifina ne, ni nace su aikata abin da suka aikata su waye iyayena mene yasa za suyi mini haka wayyo Allah" Wani irin raunataccen kuka Abra ta saki hadda shassheƙa kamar numfashinta zai bar jikinta,da Yadda take ji a cikin zuciyarta gwara ace bata zo duniya baki ɗaya ko kuma aci gaba da ɓoye mata Asalinta.

"Ka kula da ita bari na kira Likita" Abbi na faɗin haka ya fita daga cikin Room ɗin. Baya son Abbi ya fahimci wani abu wannan dalilin yasa ya jawota jikinsa tare da Rungometa yana faɗin "Kee, Shiitt dalla Malama kin daman" ƙoƙarin sauka take daga jikinsa ya hanata ta hanyar ƙara matseta a jikinsa yana jan tsaki kamar an masa dole. Suna zaune Abbi ya shigo likita na bin bayansa. Dubata ya sakeyi ya tabbatar musu komai lafiya ya ƙara jaddada gudun Abin da zai ƙara sata cikin wannan halin.

Gaba ɗaya suka nufi gida tun a mota Abra take maƙale da Abbi tana faɗin zata bisa, amma ya yi mata shiru har suka isa gida babu wanda ya samu zarafin yin magana. Abbi ya kalli Abra ya ce.
"Abra baki da ikon bina, a baya nike kula da Al'amarin ki, amma yanzu ragamar rayuwar ki ta tattara ne a hannun mijinki, ki sani babu kyau abin da bakin ki ke furtawa. Shi aure ɗan haƙuri kiyi ta addu'a nima zan tayaki kuma In sha Allah daga wannan rana zan fara bincikar asalinki har mu gano iyayenki na gaskiya, naso riƙe ƙi roƙa na har abada, amma Abin da ka tsara bashi Ubangiji ya tsara ba. Ni nayi kuskure domin nasan komai jimawa dole wannan ranar zata riskemu, Kiyi haƙuri ki yafewa Abbinki na rashin faɗa maki gaskiya da ya yi, amma dake da Salman abu guda a zuciyata soyayya ɗaya nake muku. Bake kika tsara yadda zaki zo duniya ba, kuma mu duka bamu da tabbacin cewa kina da Iyaye ko kuma ke ba halattacciya bace, lokaci da bincike shi ne zai tabbatar da ainihin wace ke"

Shiru ya yi yana sauke numfashi ƙara riƙe hannun Abra ya yi wacce take ta kuka kamar ranta zai fita kafin ya numfasa ya ce. "Kimin wannan alfarma don darajar Allah ki daina saka damuwa a ranki, ina kasa sukuni bana samun nutsuwa. Kin samu miji mai tsananin son ki da ƙaunar ki na imani da Allah zai tallafi maraicinki ya riƙeƙi da amana"

"Abbi don Allah ka tafi dani, idan har farin ciki kake so nayi idan ina nan wata rana zaka iya samun ganganar jikina a matsayin gawa" kafin Abbi ya yi magana Adnan ya ce.

"Ina son duk abin da Angel ɗina ke so, Abbi idan tafiyar zai sanya tai farin ciki na amince ka tafi da ita, ni zan dinga zuwa" da sauri Abra ta ce "A'a ba sai ka zo ba" Murmushi kawai Abbi ya yi ganin tsakani da Allah Abra ke duka maganganun ta. "Adnan ta ya ya ɗan kwali zai ja hula? Abra akwai tarin ƙuruciya da kuma rashin sabo a tattare da ita, shi ya sa take cewa haka. Ka kula da ita a yanzu kai take buƙata zuwa next week zan zo tare da Farouk haɗi da duk bayanan binciken da mu kayi zan sanya Private investigator In sha Allah komai zai zo cikin sauƙi"

Jinjina kai Adnan ya yi kafin ya ce "Mun gode sosai Allah ya saka da alkairi, zan kula da Angel kulawa da ko a wajanka bata samu ba, nima a matsayina na Police zanyi ƙoƙarina wajan bincika asalin Real parent's ɗinta"
Ganin da gske Abbi tafiya zai ya barta yasa Abra ƙankame jikin Abbi tana rusa kuka wanda duk wanda yaji kukan da take dole ya tausaya mata. He couldn't feel yadda hawayenta suka jiƙa masa jiki. Shi kansa idanunsa sunyi jajir Na'ima ta gama cutarsa itace silar komai da duk wani abu ɗaya faru ta ya ya zai yafe mata? Har Abada.

Da ƙyar Adnan ya janye Abra daga jikin Abbi ya mayar da ita nasa jikin, tare da rungometa sosai yana faɗin. "Me ya sa ki ke gudana Angel? I'm your husband ni ki ke buƙata a yanzu, the you know how much I love you?" Girgiza kai kawai Abbi ya yi tare da juyawa ya fita zuciyarsa cike da so da tausayin Abra.

Cilli Adnan ya yi da Abra yana nunata da hannu ya ce "Idan kinso ki mutu babu ruwan Sp Adnan Aliyu Matawalle, ko kin faɗawa Uban riƙon naki ba zai taɓa sawa na sakeki ba, domin na fishi iko da ke useless.." goge hawayenta tayi tsaf tare da kallon Adnan cikin dauriya tace. "Ba zan taɓa mutuwa sbd kai ba Sp Adnan Aliyu Matawalle, abubuwan da kke min idan ka haifu kada ka fasa" tana faɗin haka ta juya da sauri ta nufi Bedroom ɗin ta. Mamakin martanin da tayi masa yasa Adnan kasa motsawa balle yayi tunanin ɗaukan mataki akanta me hakan ke nufi? ta daina shakkar sa ko yaya ne?.Ya daɗe tsaye a wajan kafin ya nufi bedroom ɗinsa zuciya cike da tunanin abin da zai mata.
Abra taci kuka ta ƙoshi harta dan gana haka ta raya daren tana kaiwa Allah kukanta akan ya shiga lamarinta ya kawo mata mafita cikin abin da ke damunta ya kuma bayyana mata iyayenta, daga ƙarshe ta roƙi Allah akan ya haɗata da Salmanun-faris cikin gaggawa.

Washegari tana kwance tayi wanka wata simple duguwar riga ce a jikinta iya qwiwa sai fararen ƙafarta da suke a waje. Tai lamo jikin bed rungome da pillow gaba ɗaya tunaninta ya tsaya komai nata ya tsaya tana nan kamar wata statue. A hankali ta ji an murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin nata, Ƙamshin Pur oud da taji ya sa ta tabbatar da shi ne ya shigo ƙara haɗe fuska tayi ba tare data amsa Sallamar sa ba.
Tsaye ya yi a kan yana harɗe hannayensa a ƙirji Looking at her daga shi sai trousers babu ko singlet dai murɗaɗɗen jikinsa da yake a buɗe. "Where's my breakfast?" Shiru not respond domin yi tayi kamar bata ji Abin da yake faɗa ba.

"Ni sa'an mugun Ubanki ne da zan dinga magana kina jina? Ko kuma mugun halin uban naki kika fara wanda ban san da shi ba?" Sai a lokacin ta buɗe idanunta ta kallesa tare da mirginawa wanda ya sanya duguwar rigarta tattarewa zuwa can sama, har farin pant ɗinta ya bayyana cikin ƙasa da murya ta ce. "Daman ance ai kyan ɗan ƙwarai ya gaji iyayensa,babu laifi dan na ɗauki halin mahaifina" a fusace yayi kanta zai daka tayi saurin zillewa wanda ya sa gaba ɗaya rigar jikinta barin jikin tai naked! Cak Adnan ya tsaya domin it's the first time daya ganta naked haka nan cikin haske, notin kansa ya nemi kuncewa domin idan akwai abin da ke saurin raunata zuciyarsa bai shige buƙatarsa zuwa ga matarsa ba, Abin da yake kwaɗayi a kullum wanda yake sanyaya zuciyarsa.

Takawa ya shiga yi zuwa inda take sai da sukai dab da juna ya ce "Ubanki mugu ne Abra, Azzalumi,Macuci, Ma yaudari, mai baƙar zuciya kona bar shi Ubangiji ba zai bar shi ba. Domin Ubanki kura da fatar Akuya ne!"
"Ka sani Uba, Uba ne ba'a taɓa sauyawa tuwo suna, duk lalacewar shi, shi ne ya yi sanadiyar zuwana duniya. Ka saurara da aibata min shi duk da ban san abin da ya aikata a gare ka ba, zuciya nake gudu kada haƙurina ya gaza" Zuciyar Adnan na tafasa ya ce "Well-done Abra Khamal Khamis. Well-done barewa ba tayi gudu ɗanta ya kasa rarrafawa ba, yanzu ne wasan namu zai fara bada citta tunda har kin zamu zarafin mai da min da martani haka nake so muje zuwa shege ka fasa" banza tai masa da sauri ta juya zata shige bathroom. Bata san mene ya faru ba, sai jinta tayi kane kane a jikin Sp Adnan Aliyu Matawalle yayi mata wata iriyar ƙyakkyawar runguma wacce da iya zuciya ɗaya yayi mata ita, domin gangar jiki bata iya ɓoye ainahin abin da zuciya ke buƙata.

He started kissing her from her mouth to her neck. It was a kiss that he had never given her before, babu wutar ɗaukan fansa ko ta ƙiyayya. It is something that shows what the heart wants and needs. Now Abra needs it in his body. Nan take ya nuna mata buƙatar miji zuwa ga matarsa.

Abra ta rasa yaya zatai, a kullum faɗo mata yake kamar jaka ba tare da so ko tattali ba, yana sauke buƙatarsa shi ke nan. Daga baya kuma ya ci mata mutuncin da ko maƙiyinta ba lallai yayi mata ba. Tana karatun novel dan haka zai wani tunani ya faɗo jikin ranta. Taya shi abin da yake tayi sai da yazo gangara ta tsakanin buƙata ta hankaɗa shi gefe da gudu tai bathroom tana haki. Adnan ji yayi kamar zai mutu ko hannunsa ya kasa motsawa sbd ciwon da mararsa ke masa, zai zufa dake yanko masa idanunsa yayi jajur ya ƙorawa ƙofar bathroom ɗin idanun, zubar da aji ne yayi begin nata akan wani abu na jikinta.

Ta daɗe cikin bathroom ɗin kafin ta fito, ga mmakinta sai taga ɗakin nata yayi duhu sosai kafin ta motsa taji an cillata kan gado, duk yadda taso ƙwace kanta kasawa tayi sai da ya tara masa gajiya tare da jifatanta da maganganun masu ɗaci kafin ya fita yana faɗin. "Ba kyauta aka bani ke ba, kuɗi nasa na aureki kuma dole nazo maki aduk sanda nai niyya Ubanki ma yake abin da yaga dama balle ni da nake miji a gareki, mara galihu baiwata!" Ashe kuka ma cikin rahama yake domin kasa yinsa tayi a yanzu Zuciyarta tai mata nauyi sosai.

Misalin ƙarfe huɗu na yamma tana zaune a Parlour sanye take da duguwar riga mara nauyi sosai, gashin kanta duk a cukurkuɗe tai zururu a hankali taji an murɗa handle ɗin ƙofar parlourn an shigo, bata motsa ba domin ta san shi ne ba kuma ta mara ba dawowar shi. Idanu taji a jikinta alamar ana Kallonta haka kawai taji gabanta ya faɗi da sauri ta ɗaga kanta, Innalillahi wanda ta gani tsaye ya shammaceta bata taɓa zato ko tunanin ganinsa a wannan lokacin ba. Jikinta na rawa ta miƙe tsaye tana binsa da kallo cikin wata murya ta ce "Faris.." sai kuma ta kwasa da gudu tai kansa......

LITTAFIN DARE DA DUHU, na kuɗi ne biya 300 ta wannan acct ɗin 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank. Idan katin waya ne zaka biya 500 kai Mgn ta wannan number. 09047871750/08081012143
[10/20, 7:45 PM] Abk: Da sauri Salman ya shiga girgiza mata kai, alamar kada ta ƙaraso wajansa domin ya san abin da zai faru idan ta zo. Ita ta haramta a garesa kamar yadda ya haramta a gareta. Da sauri ya yi baya ganin yadda ta yo kansa gadan-gadan, hawaye na bin fuskarta ga wani irin kuka da take tamkar wacce akai wa mutuwa.
Juyawa ya yi da sauri ba tare daya shirya ba da nufin barin parlourn yama fita daga cikin gidan baki ɗaya. Ƙyakkyawar rungomar da Abra tayi masa ta baya ita tayi sanadiyar ɗaukewar wutar kan Salman, cak ya tsaya zuciyarsa na bugawa da ƙarfin gaske, shi kansa ya san ya azabtu da rashin Yayar tasa, amma ba shi da iko da ita a yanzu mummunar ƙaddara tai musu shamaki da juna.

Gaba ɗaya ya kasa motsawa sbd yadda Abra ta ƙankamesa ta baya hannunta ɗaya a ƙirjinsa ɗaya kuma ta riƙe ƙugunsa dashi, wani irin kuka take wanda yake ratsa zuciyar Salman, saurare ɗaya yayiwa kukan yasan cewa bawai Iya na farin cikin ganinsa bane, akwai abin da yake faruwa a ƙasa.
Idanunsa da sukai jaa ya buɗe a hankali cikin nutsuwa ya saka hannunsa tare da zame hannayenta dake rungome da jikinsa da ƙyar. Juyawa yai ya fuskance ta ƙanta a ƙasa yana kallon yadda take kuka kamar zata haɗiyi zuciya. Tun daga sama har ƙasa yabi jikinta da kallo babu abin da ya bashi tsoro sai ramar da yaga tayi ba haka ya tafi yabar Angel ɗinsa ba.

Inda take ya matsa tare da sanya hannunsa duk biyun ya tallafo haɓarta fuskarta ta samu gurbi a cikin hannunsa, kasa magana ya yi sai binta da idanu kawai da yake, Eyeballs to Eyeballs suke kallo juna, Abra na shassheƙa ta ce.

"Faris"
Kasa amsata ya yi yana son tantance muryar data kirasa da ita, hannunsa ya zame kaɗan yana

46 / 78