Author : Surayya Category : Home Of Novels
rungumesu gaba dayansu yana me
jin farin ciki, da nishadi a zuciyarsa.
Ta karbi jakansa ya zauna kan kujera yana
rungume da ihsan, zeey ta cire masa takalman
kafarsa da safa ta cire masa kakin jikinsa, ta
barshi daga shi sai ves da gajeren wando. Ihsan
tanata tsallenta a jikinshi. Zainab ta kai masa
kayansa dakinsa.
Ta dawo ta dauke ihsan, tare da cewa, daga Abba
yaje yayi wanka.
Ya shirya ya fito cikin kananan kaya suka nufi
tebir, sai da suka gama cin abinci suka nutsu,
suna kan kafet suna wasansu, Aliyu ya daure ido
da farin kyalle yana bin ihsan da rarrafe, tana
gudu tana dariya.
Zainab ta taboshi yayi saurin juyawa baya, yana
lalume zai kamata, ta zille dayan gefen tanayi
masa dariya.
Ta rankwafo gabansa taja masa hanci, tayi saurin
zillewa, yakai hannunsa bai kamata ba, zata gudu
yasa mata kafa ta fado kansa, yayi saurin shafa
kanta yauwa na kamaki. Tace "a wlh ban yarda
ba wayo kamin.
Ihsan ta fado kansu tana gwarancinta, gaba daya
suka sa dariya.
Ya bude idonsa duk suka zube kan kafet din suna
maida numfashi.
Tace Abban Ihsan, yace na'am maman Ihsan.
Tace don Allah tunda na gama diploma, kafin na
fara karatun digiri, muje gida kano mu huta, yaya
rabona da gidan tun bayan arba'in din Ihsan.
Wallahi inason zuwa gida.
Yace haba zainab du fa sati ina zuwa, kuma ina
gaya miki sakon gaisuwar da suke yi miki.
Ga waya kullum kunayi kuna hira dasu kuna jin
dadi, ko yaushe fa kuna tare dasu a waya.
Ta langabe masa tanayi masa magiya, Abban
Ihsan don Allah kayi hakuri ka amince mana
muje, wallahi suna son ganin Ihsan, sunce
hotunan ta baya gamsar dasu, yaya kada fa Ihsan
ta tashi bata san dangita ba.
Yace "I gaskiya hakane da wannan ku shirya
wannan satin zamuje tare.
Ta rungumeshi tana mai cike da murna da farin
ciki, nagode yaya Allah ya saka da alkhairi,
ubangiji ya kara maka budi da son zumunci.
Amin zeeyta.
Ranar da suka sauka 'yan uwa sunyi farin ciki
sosai da ganinsu, kowa sai daukan Ihsan yake yi.
Ahmad ya rungumesu, yana cewa barka da zuwa
aunty mamina, nagode da kika kawomin 'yar
uwata.
Ta shafa kansa Amadina naji dadi dana sameka
lafiya ka girma ka kara wayo da hankali.
Gidan nasu ya kasance kullum a cike saboda 'yan
sanda zuwa.
Ranar da suka yi sati biyu da zuwa
sukayi wanka sukayi kwalliya ita da Ihsan, ta
shiga motarta ita da Ihsan da kanta tajasu zuwa
gidansu.
Ihsan tana da shekara biyu kenan, amma
wayonta da surutunta saika zata tayi shekara
hudu.
Ni'ima ce ta sake haihuwa, suna gidan sunan
Aliyu yayo wa zainab
waya, Ihsan tanata rigima ta hanata amsa wayar,
yanata yi mata fada wai ta shiga cikin jama'a da
ita zafi ya dameta.
Y kashe wayar mintuna kadan ya isa gidan
ni'ima, ya yowa zainab waya yace ta fito ta kawo
masa 'yarsa.
Ihsan tana ganinsa ta rungumeshi, tana murna,
Abba ka daina tafiya kana barina in ban ganka ba
kuka zanta yi.
To na daina Ihsan dita, dake zan rinka zuwa ofis
ko?
Ta daga kai. Yauwa bebyna.
Yai tafiyarsa da Ihsan din sai mangariba ya koma
gida, Ihsan tana rungume a jikinsa tayi bacci.
Mansura tayi sallama, ta shigo ya amsa mata
sallamar yace ina Zainab?
Tace, kajika da wani zance, motata daban tata
daban zance taho mu tafi ne, tare dai muka fito
daga gidan ni'ima, ban san yanda akayi ba nura
tsohon saurayinta yasan ana suna, sai ganinsa
mukayi a zaune akan motarsa yana ganin zainab
ya kama washe baki, ta tsaya suna gaisawa
nikuma nayi tahowata.
Yayi wata irin zabura ya mike yana huci, dai-dai
lokacin da zainab din tayi sallama ta shigo, a
fusace yace mata daga ina kike?
Cikin sanyita tace yaya wace irin tambayace
wannan?
Kafin ta karasa maganan ya dauketa da mari,
tuni ta dafe kuncin nata, ta wani durkushe a kasa
saboda gigitaccen zafin marin.
Ya nunata da yatsa uban waye ya baki damar
tsayawa da nura, har ku gaisa dashi?
Kanta yana sunkuye, tana jin haka da sauri ta
dago kanta ta kalli mansura, tace aunty kiji
tsoron Allah, wai me na tare miki a doron kasa ne
kike so kiga kinsani bala'i?
Ya kamata ku sani wannan duniyar ba matabbata
bace.
Aunty idan kin kashe aurena da yaya me kikayi
tunda dai kinsan dole a gabanku zanci gaba da
zama, har lokacin da zangama idda na samu
wani mijn da zan aura, kuma duk matsalar data
faru dani dole ku zan kwaso na gayawa.
Aunty duk matan arziki bazata bari mijinta yayi
fushi da ita ba, ni gashi kinsa ran nawa mijin ya
baci dani, yana fushi dani alhalin bada hakkina
ba.
Via #Justice_Hamzat
[8:05AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**9
kiyi hakuri aunty, gaba kike dani, kuma ke
auntyna ce, bazan taba bari wani batanci ya
shiga tsakaninmu ba, amma dan Allah ki rinka jan
mutuncinki da girmanki.
Tace, yaya kayi hakuri, amma ban aikata abunda
kake zargina dashi ba, rabona da nura tun ranar
da ka koreshi, ko labarinsa ban sake jiba bare na
ganshi.
Ta mike tsaye zata nufi dakinta jiri ya kwasheta,
tayi baya zata fadi, Aliyu yayi saurin tareta ta
fado hannunsa, ta shide, numfashinta ya dauke a
gigice sukayi asibiti,
saida likitoci sukayi ta gwaje-gwajensu, suka jona
mata karin ruwa ta farfado, sai dai takoma bacci.
Mansura kukan nadama takeyi, tana bawa Aliyu
hakuri, shi bakin cikin marin da yayiwa zainab yafi
komai daga masa hankali.
Likita ya shigo yace, yallabai saika kula da
madam sosai, ka daina bata mata rai, don tana
da karamin ciki na wata biyu a jikinta.
Wani irin farin ciki ne ya lullube zuciyar Aliyu, ya
rinka dariya yana nuna farin ciki da godiya ga
Allah.
Mansura ta rinka mamakin irin farin cikin da yake
yi, wai yana son haihuwa haka amma bai hanata
planin din data keyi ba, du da dai bashi yasa ta
tayi ba.
Amma ai wataran yana ji tayi waya asibiti, tace
zato zo allura, bai ce mata komai ba, to me yake
nufi da itane, ko bai dauketa wata tsiya ba?
Tayi waje da saurinta, ta zaro wayarta ta bugawa
yayarta saratu
tana dauka tace, hello kinji yarinyar nan ciki ne da
ita, kinga murnar da Aliyu yake yi kamar wanda
akayiwa bushara da gidan Aljanna, yanzu dama
mutumin nan yana son haihuwa ya barni inata
faman planin.
Au dama planin Aliyu ya saki kiyi shiyasa baki
sake haihuwa ba tsawon lokaci?
Tace wlh yaya saratu gaskiya ba Aliyu ne ya
saniba, don na taba gaya masa zanyi tsarin iyali,
yace ba ruwansa, kuma bada yawunsa ba, idan
kuma nayi bai yafe ba.
Ni kuma naga shi dan gayu, ga son ya huta, sai
nake ga kamar tara 'ya'ya zai iya zame masa
matsala, yaga baya samun yanda yake so
watarana yayo min kishiya, sai duk da haka ban
tsira ba. Amma tunda naji labarin zainab tana da
cikin Ihsan, na daina planin din, amma gashi
harta haihu ta kuma samun wani cikin, ni kuma
ba labari.
Saratu ta daka mata tsawa tare da cewa, ke kika
yiwa kanki, kin cuci kanki abanza a wofi.
Ga dukiya nan yana samu kamar kasa, ita kuma
taita tara masa 'ya'ya kya zama 'yar kallo ai,
yanzu ma ya fara baki kujerar makka biyar, kin
kawowa Alh, to gaba muka san me zaiyi mana,
bare ace kin cika gidan da 'ya'ya, ni bazan iya
sauraran takaicinki ba sai anjima.
Ta kashe wayar.
Mansura ta dawo dakin a sanyaye da ita.
Zainab ta farka Aliyu yace sannu zeeyta.
Ta dago kanta cikin sanyita tace yaya kayi hakuri
dan Allah ka yafemin, wallahi ba wani namiji dana
gaisa dashi.
Kayi hakuri yaya zuciyarka ta huce.
Ya shafa kanta zainab ki daina tuna wannan
magana dakin san yanda raina ya rinka suya da
tukukin bakin ciki, ina tuna ni na mareki da
wannan hannun nawa
sai nake tunanin irin hukuncin da zanyiwa hannun
ko zuciyata ta huce.
Zainab nayi abunda Allah ya hana, yanke hukunci
cikin fushi.
Zainab ba laifina bane, shirin mansura ne kawai
don ta bataki awajena.
Kiyi hakuri zeeyta.
Tayi saurin sa hannu ta toshe masa baki tana
murmushi, don Allah yaya ka daina bani hakuri,
wlh na yafe maka, ka gayawa aunty ma na yafe
mata.
Babban jin dadi na da zuciyarka ta huce, bakayi
fushi dani ba.
Zainab jiyan ma bacin raine da zafin kishinki, wai
har na mareki.
Tace don Allah yaya kadaina tuna zancen marin
nan, kaifa yayana ne, kayi min marin ne a
matsayinka na wana, ba miji ba ko yayana?
Mansura tana tsaye a gefe daya tayi shiru tana
jinsu. Aliyu kamar baisan tana wajenba, bare
zainab da bata san tana nan ba.
Zainab tace, dan Allah yaya kayi hakuri kada
kayiwa aunty wani abu, kasan dan adam ajizine,
kowa zai iya kuskure kayi hakuri yaya ka yafe
mata.
Ya daga kai shikenan naji na yafe mata, mansura
kawai saita juya ta fita daga dakin.
Likita ya rubuta musu maganguna na karin jini da
lafiyar dan tayin cikinta.
A daren suka dawo gida wani irin tattalin so da
sabuwar kulawa da yakeyi, kamar zai mayar da
ita ciki
ita kuma sai sangarta take zuba mai da
shagwaba ga cikin nata mai tsurfa ne du
daurewar data keyi, amma abu kankani sai ya
daga mata hankali yasata amai.
Hankalin Aliyu ya kasa nemansa akeyi awajen
aikinsa, ga zeey dinshi bata cika lafiya ba.
Amma dole ya dauketa su tafi Abujan, ta karasa
warware wa acan.
Yace wa zainab ki hada abunda zaki tafi dashi
don jibi litinin zamu tafi.
Yana fita yayi bangaren mansura, yace mata kiyi
lis din du abunda zaku bukata, don jibi zamu
koma abuja.
Tace, kaida wa?
Yace dawa muke tafiya?
Tace, kana nufin wai da zainab din zaka kuma
tafiya ne?
Yace ya wuce wai.
Ta mike tsaye tana tafa hannu, to wlh abunda
bazai taba yuwuwa ba kenan, na gaji da yi muku
gadin gida wlh, wlh bazan zauna ba, na gaji da
rashin adalcinka, ka rinka kwasar wadanda kake
so kuna tafiya.
Ya daga mata hannu, tare da cewa ya isheni,
kada ki kawomin maganar banza, haka nayi niyya
baki isa ki canjani ba.
Ya fice ya doka mata kofar, ta tabe baki dan
rainin hankali zaka gane kurenka.
Via #Justice_Hamzat
[8:07AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**10
Dan rainin hankali zaka gane kurenka, tauraruwar
taka dole ka barta, ko kuma ka tafi damu gaba
daya, don wlh bazan zauna ba, sai na bika.
A bangarenta ya kwana da safe ya sake yi mata
maganar ta bada lis din abunda zasu bukata.
Tace masa saidai ka nemi lis a wajen zainab, don
ni kaga akwatuna na can nagama shirin binka.
Ya daka mata tsawa ke baki isa ki raina min
hankali ba.
Ga cek nan ki rubuta abunda kike bukata a karbo
miki a banki, idan kinga zaki zauna ki zauna, idan
kinga bazaki zauna ba to ki tafi gidanku.
Ta dafe kirji ni zaka yiwa wannan wulakancin
Aliyu?
Ko kallonta baiyi ba ya fice ya bata waje, tana jin
fitarsa itama ta shirya ta fice, gidansu Aliyu.
Da suka gaisa da umma, sai tayi bangaren ummi
ta gaisheta, sannan ta shiga bangaren su zainab,
ta gaisar da maman sannan tace mata, don Allah
daddyn zainab yana nan?
Mama tace "I yana ciki.
Tace don Allah mama inason magana dashi.
Tace, to bari nayo masa magana.
Ta mike shiga bangarensa ta gaya masa.
Yace mansuran ta shigo, mansura ta rissuna ta
gaisheshi, saita fashe da kuka daddy yace, lafiya
menene, me suka yi miki, wani abu ne ya faru?
Tace daddy wai dan Allah Aliyu yace zasu koma
abuja da zainab, sai nace ya rinka kwatanta
adalci a tsakaninmu, mu ma yaje damu abujan
nan, shine ya hauni da fada wai bazamuje ba,
anan yaga damar ajiyemu, in zan zauna na zauna,
in bazan zauna ba na fice na tafi gidanmu.
Dady yace subhanallahi, me yayi zafi haka? To
kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da shirinki, zai
tafi daku kinji.
Tace to dady nagode Allah ya saka da Alheri.
Yace bakomai tashi ki koma gida.
Ta fito tayi musu sallama ta koma gida.
Dady yayi waya ya kira Aliyu, ya zo da saurinsa,
yace dady gani.
Bayan sun gaisa, yace haba Aliyu
kaifa yaro ne, amma me halin manyan mutane.
Haba Aliyu kada rudin duniya ya debeka, ka
kaucewa fadin Allah, kazo kana fadawa halaka.
Yata masa nasiha daga karshe yace to yanzu
tunda bata amince ba, to an shiga hakkinta, don
haka ka tafi da mansura abuja ka bar zainab
anan kano.
Aliyu ransa ya baci wato mansura kararsa ta
kawo kuma tasan inda bai isa yayi musu ba.
Yace to dady na tafi da itan.
Yace yauwa ko kaifa dana, nagode.
Aliyu ya taho gida ransa a bace saboda abunda
mansura tayi masa.
Magoronsa ya rinka daci na tukukin bacin rai, sai
yaji zazzabi yana neman rufeshi.
Ya shiga falon zainab ya zauna ya zuba tagumi
zainab ta fito daga kicin ta ganshi, ta karaso
gabansa da sauri tace lafiya yayana, meya faru,
meya sameka kayi tagumi?
Tasa hannunta ta cire mishi tagumin, ya akayi
yayana menene?
Ya danyi tsaki yace bana jin dadin jikina, ina jin
dan zazzabi ajikin nawa. Oh! Sorry yayana sannu,
ta dafashi tana lallaminsa kamar yaro.
A hankali ta zame masa kayan jikinsa, daga shi
sai gajeren wando.
Ta shiga kicin ta kawo mishi ruwa mai sanyi, da
lemu ta zuba a kofi tasa masa a bakinsa kadan
ya iya sha saboda bacin rai.
Ta debo ruwa a tasa ta dauko karamin tawul tazo
ta rinka dangwalar ruwan tana daddana masa
ajikinsa, yana lumshe ido a hankali ya fara jin
yana watsatsakewa, saida taji jikinsa ya huce
daga dumin, sannan ta bashi magani yasha.
Ya kishingida akan kujera, ta rinka yi masa tausa,
sannu a hankali yana lumshe ido tare da cewar
wash.
Bacci mai dadi ya ringa fisgarsa, ya kwantar da
zainab ajikinsa ya rungumeta, bacci ya daukesu a
haka.
50 min suka kwashe suna bacci, a haka zainab ce
ta fara farkawa, ta runkura a hankali zata zame
tabar jikinsa, ya kara kankameta, ya bude ido ya
sumbaci lebenta, dariya, yayana ka farka.
Tunda zaki bar jikina ai dole na farka.
Yaya lokacin sallah yayi hudu saura.
Ya mike da sauri, ta shiga toilet ta hada masa
ruwan wanka, ya shiga yayi wankansa a nitse ya
fito zuciyarsa wasai, ya manta da wani bacin ran
mansura, yayi saurin sa kaya ya fita masallaci
don sallar la'asar.
Lokacin daya dawo daga masallaci ya tar zainab
ta canja masa shiga ta kananan kaya, irin shigar
da yake so.
Ta tare shi tana murmushi, ta riko hannunsa suka
wuce tebir don cin abinci.
Ta rinka tattalinsa, tana bashi abinci abaki, sai
kace yaron goye.
Suna ci cikin nishadi da faranta ran juna, sai
santi yake zuba mata, yana sata kyalkyala dariya.
Tasa shi cikin farin ciki da walwala
kwata2 ya manta da bacin rai da mansura ta
dasa masa.
Ya dauki waya bari na bugawa ni'ima ta kawo
min Ihsan dita, bana jin dadi idan bana jin
karadin bebyna.
Zainab ta rike wayar don Allah yaya ka bari, tace
saida daddare idan zasu zo yi mana sallama zasu
taho tare.
Yayi wani dif saboda yanda zuciyarsa ta buga da
ya tuno fa bada zeey dinshi zai tafi ba.
Gashi du ta hada kayansu da abunda tasan
zatayi amfani dasu.
Ta kula da halin da yake ciki, tace wayyo yaya
don Allah kayi hakuri idan ranka ne ya baci bari
na tura direba ya dauko maka ihsan din kaji
yayana.
Ta mike ya riko hannunta dawo ki zauna, ba fushi
nayi ba, dani da ni'ima ai duk daya ne.
Tace to meye yayana nafa duk ka canja?
Yace kiyi hakuri zainab bada ke zan tafi abuja ba.
Ta dafe kirji yaya me nayi maka, saboda me
bazaka tafi dani ba?
Ya kwanto da ita jikinsa.
Via #Justice_Hamzat
[8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**11
Ya kwanto da ita jikinsa yana rarrashinta, kiyi
hakuri zainab ba a son raina ba, mansura ce ta
kai karata wajen dady yace na tafi da ita.
Tace shikenan yaya, saikun dawo Allah ya kiyaye
hanya.
Ta mike tayi cikin dakinta ta kwanta tana
hawaye.
Ya taso ya biyota, ya dagota "zeeyta menene
fushi kika yi? Kiyi hakuri nasan dole ranki ya baci,
amma ni nafiki cutuwa da rashinki kusa dani.
Zainab kici gaba da shirinki, saimu tafi gaba
daya, kinji.
Ta tashi tace haba yaya ya zanki jin maganar
mahaifana?
Dady abunda ya fada gaskiya ne, hakan shine
adalci yaya kuje Allah ya kaiku lafiya, zan tayi
muku addu'a daga nan.
Ta tashi ta shiga toilet shiru-shiru yana jiranta
bata fito ba, ya dafe kansa tabbas yasan zeey
dinshi fushi tayi, ya tashi ya fita daga dakin.
Lokacin ni'ima da sadiya suka zo musu sallama,
sannan Aliyu baya nan, zainab bata gaya musu
cewar ba tare da ita za a tafi ba.
Sai goman dare suka tafi, sunyi mamakin rashin
dawowan yayan nasu gida da wuri.
Sha daya na dare zainab ta kasa bacci, tana
tunanin ina Aliyu ya shiga ne?
Tayo alwala ta shimfida dadduma tana sallar
nafila, tana addu'a Allah ya bata hakurin jure
rashin mijinta kusa da ita.
Ya kuma hade kansu da mijinta da kuma abokiyar
zamanta, ya kuma kare su daga sharrin
mahassada da makiya.
Ihsan ta farka da kukanta tana kiran dadynta,
bata ganshi yau ba ta taso ta kwanta abayan
zainab tana kuka, tana cewa aunty mami ina
Abba na, ki kaini wajen Abba kinji aunty mami.
Zainab tana kan addu'a tana hawaye tana jin
ihsan a kwance a bayanta tana kuka.
Ya dade da shigowa yana tsaye yana kallonsu,
tsananin tausayinsu ya gallabi zuciyarsa.
A hankali yae ya durkusa a gaban ihsan ya shafa
kanta, ta dago ta ganshi, ta fada jikinsa tana
dariya
Abba na ina ka tafi ka bani?
Ya rungumeta sosai yarinya ta rinka ajiyar zuciya
ya rinka shafa kanta.
Tayi lamo a jikinsa har tayi bacci ya shimfideta
ya dawo wajen zainab.
Yace yanzu zainab haka zakiyi min kiki sakin
ranki ku rinka shiga kunci keda ihsan.
Keda zaki rarrasheta amma ke kina kuka ita
tanayi, a haka kike so na tafi na barku, taya
zuciyata zata samu nutsuwa, bayan nasan bakwa
cikin kwanciyar hankali.
Kayi hakuri yaya wlh ni ba haka bne, ni abunda
ya daga min hankali naga har sha dayan dare
baka dawo bane, yaya ba dole na damu ba?
Yaya ina kaje ka kai sha daya baka dawo ba?
Yayi murmushi yace ina zanje kuwa, ai kinsan
bazan iya fita wani waje a wannan lokacin ba, ina
falon saukar baki muna lissafi da su sadik yanzu
nan suka tafi.
Tayi murmushi ya kamo hannunta zo muje na
kwanta kada na makara.
Da safe ya fito falo shida zainab yana dauke da
ihsan, sunci kwalliya kamar masu shirin zuwa fati,
sunata murmushi da fara'a ke ba kyace da wani
kunci a ransu ba
mansura suka shigo falon ita da Ahmada sunci
kwalliya tana taunar cingam, Ahmad yayo wajen
zainab yana cewa aunty mami mu tafi gaba daya.
Ta shafa kansa kada ka damu yarona idan mun
gama shirinmu zamu biyoku, inkaje ka kula da
karatunka, kaga za a canja maka makaranta
saika kula sosai.
Yace to aunty mami naji.
Mansura ta kallesu ta tabe baki, takaicinsu da
bakin cikinsu ya isheta, wato du yanda taso ta
kuntatawa zainab donta ga bacin ranta, yarinyar
taki nuna damuwarta.
Har mota ta rakosu, Aliyu ya mikowa zainab
ihsan ta karbeta, ya shiga motar suna daga musu
hannu, direba ya fara jan motar tana tafiya, Ihsan
ta kwala wata gigitaccen kuka tana zamewa daga
jikin zainab.
Motar tana kokarin fita daga get Aliyu yacewa
direba ya tsaya, ya fito da sauri ya karbi ihsan ya
rungumeta, ta rinka cewa Abba jani.
Yaya to ku tafi da talatu, ta taho da ita.
To shikenan turo talatun.
So kuyi hkr wllh banda lpia ne
[8:08AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4**12
To shikenn turo talatun. Ta shige gida da sauri
talatu ta fito ta shige gaban mota kusa da direba,
ihsan na kwance jikin babanta, yana lallashinta
Ahmad yana tsunkuninta suna dariya.
Mansura takaici ya cikata, wai me zainab take
yiwa Aliyu ne da yake musu irin wannan kauna?
Kafin su karasa airprt Ihsan har tayi bacci. Suna
fitowa daga mota talatu ta karbeta, ta koma
motar direba yasu suka tafi.
Mansura kanta ya kwance da ganin gidansu na
abuja, du da dai na kano da suke ciki yafi shi
girma da kyau, amma tsarin wannan din ya
burgeta sosai, kamar gidan turawa.
Tuni Aliyu ya fice cikin sauri ya nufi ofis. Mansura
da Ahmad sun zagaye ko ina, bangare daya ne a
kulle, ta tabbatar wajen zainab ne, tunda bai bude
musu ba.
Sai dare Aliyu ya dawo abun haushi ga yunwa