TATTALIN SO Complete Hausa Novels by Surayya.txt

Author :  Surayya Category :  Home Of Novels

Chapter   2 / 18

3K to 6K   out of 51.6K words

soma rubutawa jiyane, amma gobe insha Allahu zanyi muku 3 times pr day, kuyi hkr
[1:17PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**6

BA AYARDA mace ta dauki abincin mijinta tayi kyauta dashiba saidai in dafaffe ne in tayi, gudun kada ya lalace, to sai a sadaukar dan gudun kada ya zamo almubazaranci. Shima idan miji ya dawo saiki sanar masa, ko gidanku zaki aika da abinci saiki sanar masa, bare ki bawa wani can daban. Wannan yana cikin cin amanar miji.
Manya mutane suka rinka mikewa suna yiwa zainab kyautar kudi, saboda yanda yarinya karama ta burgesu, Abba da daddy sai washe baki suke yi don jin kokarin 'yar tasu da kwazonta.
Mamanta kuwa tayi hamdala acikin ranta, tana mai jin dadin baiwar da Allah yayi wa 'yarta tun tana karama, kowane tebir mutum hudu ne a zagaye dashi, akayi umurni da masu sabis su fara rabon abinci, shinkafa ce fara da taliya itama haka, sai soyayyun kaji da gasashen nama, sai mitfy, samosa, sopringros, haka kowa za a tsira katon filet a dire a gabansa, mata masu wa'azi sun zo, wajen yayi shiru an nutsu ana cin abinci, yayinda aketa kwararo wa'azi akan zaman aure ga ma'aurata.
Washe gari akayi yini, ranar litinin akayi fati, a ranar kuma aka kai amare dakunansu. Burin mansura ya cika, yau ta auri gwarzon namiji cikakke, wato Aliyu.
Tasan sarai Aliyu miskili ne bai fiya
wasa da dariya ba, shi hasalima magana wahala take masa yi masa, don inzaka daka ta tashi sai dai kuyi ta zaman kurame dashi.
Aliyu mutum ne mai tsafta, dan gayu ne mai son kamshi, baya damuwa du tsadan turare zai saya indai kamshin shi yana da dadi. Aliyu yana ji da kansa, akwai iya jan aji, yana da tsananin iyayi da gwalli kamar mace, ya fiya kasaita da son girma kamar wani basarake.
Washe gari ranar talata gajiyar biki bata bar ni'ima da zainab zuwa makaranta ba. Tun asuba da aka tashe su suka yi sallah, suka sake komawa gado suka nade cikin bargo suna bacci. Karfe bakwai masu aikinsu sukayi ta tashinsu don su shiry su tafi makaranta, amma du sunki tashi.
Dole sai rabuwa suka yi dasu.
Karfe goma dai-dai Aliyu ya shigo gidan don gaishe da iyayensa. A farfajiyar gidansu mai gadi da direbobi suna ta risinnawa suna gaisheshi. Aliyu ya cewa malam idi direba, "ina 'yan makaranta , i ce kodai basu makara bako?
Malam idi yace ai basu fito ba, yau ban kaisu makaranta ba." a zuciye Aliyu ya shiga gidan, kafa kawai yasa ya daki kofar ta bude garam.
Ni'ima da zainab suka tashi a firgice, suna mitsike ido. Suna dago kai suka ganshi. Kafarshi daya akan gadon, dayar tana kasa, fuskar nan tayi kirtif da ita kamar bai taba dariya ba.
Zumbur suka mike suka diro kasa daga gadon, suka durkusa can nesa dashi, suka kama cewa "yaya ina kwana? Bai amsa musu gaisuwar ba, sai tambaya daya jefo musu cewar "meya hanaku zuwa makaranta? Gaba daya jikinsu ya hau bari suna in'ina da kame-kame abunda zasu ce, ya daka musu tsawa "ku tashi ku saka uniform dinku, ina jiranku a falo." suka mike da sauri kowacce ta nufi kwaba. Shikuma yayo falonsu yana tsaye. Mintuna kadan suka fito sanye da kayan makaranta da jakunkunansu a rataye, ya sasu a gaba har farfajiyar gidansu, ya kwalawa malam idi direba kira, ya taho jikinsa na rawa. Yace "daga yau du ranar daka kara kin kaisu makaranta abakacin aikinka."
malam idi ya rikice jikinsa yana bari, yace "kayi hakuri yallabai, wallahi ba laifi na bane sune basu fito ba." yace "daga yau idan kaga basu fito ba kayi min waya kawai ka gaya min. Yace "to yallbai." suka shiga motar direban ya jasu. Shikuma Aliyu yayi cikin gida. Zainab tace, "inbanda abun yaya, daga yin aure saika fito da sassafe. "ni'ima tace, "ai gwandake bangarenku ma na 'yan firamare ne, ni 'yar sakandare nasan wallahi sai an dake ni, daya kyalemu gobe basa muzo ba."
gidan Aliyu yana nan daga bayan gidansu ba nisa. Amma tunda aka kai mansura basu je gidan ba, saboda basu da wani lokaci sai dare, sukuma ba fita suka yi da dare ba.
Yau alhamis ana tashi daga boko gida suka yo, dan ba islamiya. Ni'ima da zainab tuni sun gama shiri, anko sukayi na wani dandatsesen material baki, ni'ima tana rike da hannun zainab suka tafi.
Suna zuwa gidan suka shiga, 'yan aikin gidan sai sannu da zuwa suke yi musu. Suka karasa babban falo inda matar gidan take, sukayi sallama, saida akayi musu izni sannan suka shiga. Mansura ta taresu da murna, a'a sai yau zaku zo, nayi fushi." suka rike hannunta suna cewa, "tuba muke aunty, kinsan kullum da makaranta.
Tace, "to amma gaskiya yau anan zaku kwana." suka ce wai kwana aunty? Ai baza a barmu ba a gida." tace haba don Allah, ya ya zasu hanaku kwana a gidan babban yaya." yayinda take kwalawa mai aikinta kira talatuwa, "na'am ranki ya dade, ta amsa da saurinta, ta durkusa a gabanta, mansura tace "bakya ga munyi bai ne baki kawo musu komai ba, nifa bana son shashanci, kirinka kula da aikinki fa."
talatuwa tace kiyi hakuri aunty. Ta fita da sauri ta shiga kicin ta hado musu lemuka da snacks taje ta durkusa a gbansu ta ajiye. Zata mike zainab ta bude jakarta ta dauko dari biyar ta mika mata. Talatuwa tasa hannu biyu ta karba tana godiya. Inna laraba tashigo ta durkusa a gaban mansura tana tambayarta hajiya me za'a girka?

Surayya Abubakar
[1:19PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**7

TA YAMUTSA fuska tana tsara mata abunda zata girka. Harta mike ta fara tafiya zainab tabita tasa mata dari biyar a hannunta, tsohuwa laraba tace, "auta me za a sayo miki? Tace a'a ki rike baki nayi. Laraba ta washe baki tana murna tana godewa zainab.
Yaya Aliyu ya shigo, da sauri zainab da ni'ima suka yi masa sannu da zuwa tare da gaishe shi. Ya wuce bangarensa. Mansura ta kwalawa talatuwa kira, tazo da saurinta. Mansura tace, "ki hadawa Aliyu abinci kikai bangarensa."
zainab kanta data ke yarinya tayi mamakin abun, bare ni'ima data fara zama budura. Sun san haka bai kamata ba, don ba haka ake yi a gidan su ba.
Wata mata ce da goyon 'yarta ta fita da hayyacinta kamar almajira, ta durkusa tana gaida mansura. Mansura ta hade rai tana ya musta, da kyar ta amsa gaisuwan matar.
Ni'ima da zainab suka gaishe da matar, zainab tace kwanto yarinyar, bata da lafiya ne? Matar tace "wallahi zazzabi ne da amai da kashi na hakori." yayinda take kokarin sakkota. Zainab ta mika hannu zata karbeta, mansura tayi karaf tace "ke zeey auta yarinyar ba lafiya kokarin daukarta kike? Saita yo miki amai ajiki." zeey tace to kije ki sai mata magani ta sha mana.
Matar ta girgiza kai cikin yanayi na tausayawa, tace, "aiba kudin ne, magani har dari tara da hamsin, banida kudin dazan sai mata, kudin yayi yawa, ko dari da hamsin bani da'ita bare har dari tara da hamsin." zainab ta bude jakarsu ta zaro gudan dubu daya ta mikawa matar, "ungo kije kisai mata maganin." matar ta karba bakinta yana rawa.
Mansura tace, "ke zeey kudin wa kika samu kiketa rabarwa haka? Zainab tace daddy ne ya bamu da zamu zo ko zamu sai wani abun.
Mansura tace to shine kike rabar da kudi baku sai komai ba." zainab tace aunty ai muna da komai me zamu saya? Ba gwanda mu bayarba." matar nan dai tanata sawa zeey albarka harta fice ta tafi.
Ni'ima ta fuzge jakar daga hannun zainab, ta bude ta leke bakomai aciki, ta harareta to kin rabar mana da kudin, to yanzu dame zamu sai ice-cream din? Ni shiyasa wallahi bana so nabar kudin mu a hannunki, du saiki rabarwa da mutane mu ki barmu haka. Nidai kawai kirinka bayar da iya naki, kada ki kuma bayarmin da nawa kudin."
zainab tayi murmushi, tace "haba yaya ni'ima, abunki ai nawa ne, zan iya iko da komai naki, Allah ya bamu rai da lafiya, muna da kudi a gida, ko an bamu ma tarawa muke yi idan bamuda abun siya. To ga masu bukata saimu hanasu." ni'ima tace, "to amma ai bakya bayar du ba, ai kinsan zamu sai ice-cream."
zainab tace bakomai yaya ni'ima, zaki ga Allah ya bamu wasu, don ranan malaminmu yace, "anaso mutum ya rinka ya waita sadaka, saboda tana juyar da bala'i.
A zamanin annabi sulaiman (a.s) akwai wani mutum a gidansa akwai wata katuwar bishiya, tsutsuwa tayi 'ya'ya akai. Sai wata rana matar ta gaya wa mijinta cewar, ya hau kan bishiyar nan ya debo musu 'ya'yan wannan tsutsunwar zasu ci suda 'ya'yansu.
Mutumin nan ya kwaso 'ya'yan, suka gashe shi, shida matarsa da 'ya'yansa suka cinye. Sai tsunsuwar nan takai karar wannan mutumin gurin annabi sulaiman (a.s), shikuma yasa aka kirawo mutumin yayi musu tsakani da wannan tsuntsuwar, mutumin yayi alkawari bazai sake ba.
Ana haka sai wata rana matar nan ya kuma gayawa mijinta ya hau bishiya ya kuma debo musu 'ya'yan tsunsuwa, mutumin yaki, yace "annabi sulaiman ya hana shi ya sake dibar mata 'ya'ya." sai matar tace kana ganin annabi sulaiman zaiyi maka wani abu danka kwashe 'ya'yan tsunsuwa, alhalin shima me shagaltuwane da mulkinsa? Matar dai tai ta rudarsa har ya hau ya debo.
Sai tsuntsuwar nan tasake kai kararsa wajen annabi sulaiman, annabi sulaiman yayi fushi, ya kirawo shaidanu guda biyu, daya daga gabas daya daga yamma. Yace sutafi kan bishiyar nan su zauna, idan mutumin nan ya sake zuwa wajen 'ya'yan tsunsuwar nan su rike kafafuwansa su watsoshi kasa.
Shaidanu suka je kan bishiya suka zauna. Shikuma mutumin ganin ya debo wa'yancan ba ayi masa komai ba, don haka sa wannan karon ma ya sake komawa domin ya debo 'ya'yan. Har ya taka kafarsa zai hau, sai yaji almajiri yana bara a kofar gida, saiya umurci matar nan data bawa almajirin nan wani abu. Sai matar nan tace bakomai awajenta.
Sai mutumin nan ya dawo ya samu lomar abinci ya bawa almajirin nan, sannan ya koma bishiya ya debo 'ya'yan tsuntsuwar nan, saita sake dwowa ta gayawa annabi sulaiman, sai yayi fushi mai tsanani, ya kirawo shadanun guda biyu daya tura kan bishiyar. Sai suka ce bamu saba maka ba, muna kan bishiyar koda yaushe, lokacin da mutumin zai hau kan bishiyar sai wani almajiri yayi bara ya koma ya bashi lomar abinci, sannan ya dawo ya hau. Zamu kama shi kenan sai ubangiji ya aiko da mala'iku guda biyu, daya ya kamani ta wuya ya jefar dani inda rana take bullowa, daya yakama abokina ya jefar dashi inda rana take faduwa.
To kinga dalilin sadakar da yayi ya kubuta daga sharrin shaidanu. Aliyu yana daga dakinshi yana jinsu, ya sake jinjina hankalin autarsu, yasan hakika akwai bawar da Allah yayiwa autarsu na musamman.
Ya fito daga dakinshi.

Surayya abubakar
[1:19PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**8
YA FITO daga dakinshi, yayi gyaran
murya, ya ciro dubu biyar a Aljihunsa ya
mikawa zainab, yace "zeey auta ga kudin
ice-cream." ta rissana ta karba tana
godiya. Yaya Aliyu ya wuce ya sake fita. Zainab tace yaya ni'ima kinga abunda
nake fadamiki ba, inka bayar da kadan
sai Allah ya baka mai yawa." ni'ima tace
nagani, amma bani su nan kada ki sake
bayar mana." ita kuwa mansura a
zuciyarta cewa takeyi, "wannan yarinyar da shegen iyayi take. Wajen mangariba
suka isa gida. Bangaren hajiya suka nufa
sukayi sallar mangariba, zainab ta mike
tayi bangarensu, saita tarar da mamanta
kwance tana juyi. Ta tafi da sauri ta
rikota, tana cewa menene mamana, meya sameki? Maman tace banida lafiya
zaina, marata da bayana ciwo suke yi.
Nan da nan sai zainab tasa kuka tana
cewa, "mama tashi muje asibiti kinji?
Mama don Allah tashi mu tafi asibiti ko
kya samu lafiya. Maman tace da kyar, saboda ta fara
galabaita "zainab asibiti babu abunda
zasu iya yi min, Allah ne kadai zai bani
lafiya. Ki kirawomin hajiya da umma da
ummi, tayi cikin gida da sauri, du ta gaya
musu gaba daya suka taho, a lokacin Aliyu yana gidan. Maman ta galabaita
sosai, ko hannunta bata dagawa.
Umma tana ta hado kayan haihuwar a
dakin. Umma tana rike da maman, hajiya
tana mata tofi a ruwa a kofi, zainab din
taje ta rike maman tana jijjigata tana kuka, tana cewa mama! Mama!! Ki bude
idonki kiga hajiyan fa na kirawo miki ita.
Ki bude idonki kifa tofi take miki, don
Allah mama ki bude idonki kiga umma da
ummi., kefa kika ce nakira miki su, don
Allah ki tashi." ta kama jijjigata tana gwale mata ido, tana cewa mama!
Mama!!. Aliyu yace "umma ku kamata mu
tafi asibiti."
a lokacin Aliyu yaiwa abba da daddy
waya, suka ce to suma sun wuce
asibitin." a can suka tarar dasu Abban har sun riga zuwa, aka shigar da mama dakin
haihuwa, zainab sai kuka take yi, ta tafi
ta rungume daddynta tana kuka tana
cewa daddy kana ganin mama bata da
lafiya sun shigar da ita can, daddy kazo
mu bita. Ya rungumota yana rarrashinta, "kiyi
hakuri zainab, ki kwantar da hankalinki,
mamanki haihuwa zatayi. Ko bakya so
tasamar miki kanwa? Tace ina somana
daddy." to kiy shiru ki daina kuka,
mamanki haihuwa zatayi kinji ko? Kita yi mata addu'a kinji? Tace "to daddy
zanyi mata. Abba yace, hajiya su koma
da zainab gida a ar umma da ummi a
gurinta.
Abba ya taho da hajiya da zainab gida,
zainab sai kuka take yi, suna zuwa gida suna ni'ima da sadik su ni'ima suka tare
su da cewa ta haihu? Hajiya tace musu
a'a ta dai kusa. Du rarrashin da hajiya
take yiwa zainab ta kasa yin shiru, sai
kuka take yi.
Su kuwa can asibiti sun kasa samun nutsuwa, saboda jikin mama da yayi
tsanani. Wajen karfe uku na dare ta haifi
'yarta mace, su umma da ummi suka ta
hamdala suna yiwa Allah godiya.
Karfe bakwai na safe gaba daya 'yan
gidan sun hallara, ganin yanda jini ya tsinkewa mama, hankalin kowa ya tashi.
Daddy mijinta yana rike da ita yana
salati, yayinda likitoci suketa iya bakin
kokarinsu. Sunyi mata allura jinin ya
tsaya, du 'yan uwa sun zagaye ta, harda
sadiya amarya da mansura, su sadik da ni'ima du suna wajen. Zainab kuwa
hajiya ta janye ta suna falon dakin da
aka kwantar da maman nata. Saboda
kuka da zainab din take yi.
Ita kuma mama jikin nata yayi tsanani,
sai wasiya take bayarwa, sai cewa take cikin dakushashshiyar murya, "ina zainab
autata, ki kirawo min zainab dina.
Sadik ya fita da gudu yana kuka ya kira
zainab, ta taho da gudu ta rike hannun
maman nata ta jijjigawa, tana cewa "gani
mama, tashi gaya min abunda zaki gaya min, kinji mamana?
Ta kwantar da kanta akan ruwan cikin
maman nata tana kuka, maman data ke
fitar da nishi da kyar ta dora hannunta
kan zainab din tana shafawa, a hankali ta
rinka motsa bakinta tana karanto kalmar shahada 'yan uwa sunata amsa mata,
tana ta shakewa. Su sadiya da ni'ima
kuwa gaba daya sun rikice da kuka.
Can mama tayi shiru, hamza cikin firgita
yace, "ta mutu! Iyayen suka dauki salati
ga daya da hawaye, yayinda yaran suka cika daki gaba daya da kururuwar kuka.
Zainab kuwa tana yin baya ba'a ankara
ba ta sulale ta fadi kasa ba numfashi.
Aliyu ya sunkuce ta aguje ya shiga office
din likitan da ita. Likitan ya karbe ta da
sauri ya dorata kan gado yana kokarin ceto rayuwrta. Aka tafi da mama gida
akayi mata sutura aka binneta, kowa yaji
ciwon mutuwar mama. Mama mutuniyar
kirki me kawaici da hakuri, daddyn zainab
karfin hali kawai yake yi, domin yasan
yayi rashin da da wuya ya mayar da'ita. Don rashin hajiya saude ba karamin gibi
rayuwarsa tayi ba.
Anata amsar gaisuwa shikuwa sai yayi
jigudin yana tunani, ga 'ya'yanshi 'yan
mazan faruk da sadik suna manne da
jikinsa, yaran sun kasa manta mutuwar, sai dai kawai kada suna sharar hawaye.
Faruk shine sa'a ni'ima mai shekara goma
sha hudu, sadik kuma shekararsa sha
daya. Kwana daya da rasuwar mama aka
sallamo zainab suka taho, da yake ummi
ce a wajenta. Yarinyar tayi wata irin rama sai kace wacce ta dade da ciwo.
[1:22PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**10

ABBAN yace "toh shikenan Aliyu, Allah ya tayaka riko." Aliyu yace amin Abba, nagode, Abban yace to ka gayawa daddyn naku? Yace "eh, saida na fara zuwa nayi shawara dashi tukunna."
yace, "to ai shikenan komai yayi dai-dai, Allah ya tayaka riko." ya amsa da Amin. Ya yiwa mahaifinsa godiya ya tashi ya nufi gidansu, ya gayawa kakarsu.
Hajiya murna tayi takara karfafa masa gwiwa daya rike 'yar uwarsa dakyau, ta hakane zumunci zai kara karfi a tsakaninsu."
don ita hajiya mace ce mai zumunci, tana so taga kan zuri'ar ta a hade, yayiwa hajiyar alheri, hajiya tanata godiya dasa masa albarka, ya fice ya nufi bangarensu. Ya tarar da umma da ummi a babban falo suna hira.
Yace musu, "ku hadamin kayan zainab da daddare zan zo na tafi da ita." gaba daya suka hada baki cikin razana suka ce, "zaka tafi da ita ina?
Gidana zata koma zan cigaba da rikonta.
Umma ta mike ta kama yi masa fada, " wato mu ka raina irin rikon da muke yi mata, shine zaka ce zaka dauketa saboda kafi mu sanin darajarta, ko iko zaka nuna mana akanta?
Yayi murmushi yace "kuyi hakuri, umma ba haka bane." iyakacin maganar kenan yayi musu shiru. Sun riga sun san bai fiya yawan magana ba, sai dai yayi atakaice. Inkin ji shi yana hira mai tsawo, to da iyayensa ne maza.
Ya mike yana ce musu, "umma bari na karasa gida." umma tace "saboda maganar tamu bata da amsa ko? Yayi murmushi ya dire musu kudi a gabansu, yace ummi kwasai goro." tace "to, mungode, Allah yayi albarka."
yana fita umma ta kama baki, tace, "ki gane min yaro, wai shi babba har ya fimu sanin abunda ya dace. Ummi tayi dariya tace "Aliyu kenan gadanga kusan yaki. Shifa zuwan da yayi yaga dazu bata je makaranta ba, gani yake kamar zamu kara sangartar da ita mu rika biyewa shagwabarta."
Aliyu yana isa gidansa yayi fakin ya shiga, a falo ya zauna yana karkade kafa. Mansura ta fito daga daki, tace "sannu da zuwa Aliyu, ga break dinka can, koda yake rana ma tayi kaine kayi fitar safe."
yace "nayi break a office din daddy bana tare da yunwa." yace kisa a share wancan dakin, zan dawo da zainab gidan nan zata zauna acikin dakin can.
Ta dafe kirji tace "haba Aliyu, ya zaka ce zaka dawo da zainab? Ai zaka takurawa rayuwarta. Don Allah ka kyaleta a gidanku, wannan shagwababiyar yarinyar in zamu iya da ita anan?
Ya doka mata harara yace ba shawararki nazo nema ba, idan zainab tazo kada ki barta ta zauna ki koreta."
tace, "haba Aliyu kai ka fiya zafin zuciya, daga 'yar wannan maganan saika hau tari, ba nufi na haka

2 / 18