Author : Surayya Category : Home Of Novels
da
jaka kala bibbiyu.
Ya bawa ni'ima da zainab da sadiya
super holland biyu su uku, ya karawa zainab da galila anyi mata haddaden
dinki aikin sama mai tsalelen kyau.
Da mangariba Aliyu yana dakinsa,
mansura ta shiga da jaririn, Aliyu ya
karbeshi yana murmushi, sai shafashi
yake yana murmushi. A zuciyarsa kuwa godiya yakewa ubangiji daya bashi
kyautar da duk duniya babu wanda ya isa
ya baka kyautar da sai Allah.
Mansura tace Aliyu nazone akan
maganan shirye-shiryen suna. Yace uhm!
Me da me zaku yiyyi? "inaso da yamma ayi walima, da daddare
mu fita fati a daula hotel, sai bokitai da
manyan robobi da kalanda, du za'a
rarraba a wajen.
Yace za'ayi komai amma banda fati." ta
wani harzuko, haba don Allah don Annabi, wallahi ka fiya yawa, ya zaka ce
ba za'ayi fati ba, alhali ni inaso na burge
saboda kawayena zamu kakko makadi
don kawata fatin, kuma zaka kawo min
matsala.
Yace albarka nake nemarwa 'ya'yan, bana so su taso akan harkar shaidanci.
Ta mike ta kama masifa, kai dai kawai
kana so ka wulakantani a gaban kawaye
na, haka wai haihuwar fari dan kwaya
daya amma bazaka saki kudi ayi
bushasha ba, don kasan bakai kasha wahalar haihuwan ba.
Ya daga mata hannu yace, ya isheni
haka fita ki bani waje." ta fito tana
kunkuni tare da bakaken maganganu. Ya
dafe kai don jin kansa yana sarawa,
mansura zata haddasa masa ciwon kai, shi baya son hayaniya.
Ta dawo daki tana kunkuni da fadar
maganganunta. Saratu yayarta tace,
meye kuma?
Mansura tace kinji wai baza ayi fati da
kida ba. Saratu tace, ai wannan wulakanci ne, ya
mayar damu kananan mutane bayan ni
har na buga kati na fara rabawa?
Lawisa kawar mansura tace, kawai inba
zai bari mu tafi ta nan ba, ba saiki ce
masa zaki je kiyi sunan a can ba, inyaso da daddare muyi tafiyarmu fatin, ai mun
riga munyi dai ai shikenan." saratu tace
ita wallahi jeki ce masa zaki tafi gida
zamuyi sunan acan.
Mansura tace wallahi yace na fice na
bashi waje, idan na koma nasan halin zuciyarsa, sai ya iya marina.
Saratu tace tabdi ya mareki? Ai kuwa
wallahi daya mari aurensa.
Lawisa tace, tunda kuwa kika nuna kina
jin tsoronsa kinsha wulakanci iri iri.
Nan suka hadu sukaita aibata shi, suna fadar maganganu son ransu. Zainab
kuwa ranta ya baci, kawai saita sa kuka.
Saratu da lawisa suka hau yi mata
masifa. Kinji yarinya da munafunci, dan
uwanki yayi ba dai-dai ba zaki hanamu
fadane munafuka? Kiyi kukan jini bana hawaye ba." zainab ta mike tayi dakinta
tana kuka. Lawisa ta rike baki, tace ahaka
kike zaune da wannan yarinya mai
miskilancin tsiya, har wani kuka take don
anfadi laifinsa.
Mansura tace kuma wallahi baki ga yanda yake takura mata ba, ni har
tausayi ma take ban, don inyana gari
bata da sakewa" saratu tace "ai wani irin
mutum ne, shiko fuska baya saki don
kada akawo masa raini." ranar suna dole
mansura ta hakura da maganar fati, akayi taron suna da yamma akayi walima ta
burgewa da bajinta, mai jego sai shiga
take tana fita tasa wannan ta cire tasa
wancan ta cire.
Yaro yaci suna Ahmad, sadiya da ni'ima
da zainab, les din da Alh ya dinka musu suka saka, da yamma a wajen walima
suka sa super ta wajen Aliyu. Can
jimawa zainab ta canjo da shaddar da
Aliyun ya dinka ma, sadiya tayi mata
daurin gwagwaro akanta, tayi kyau,
kamar ka saceta ka gudu. Sadiya da ni'ima sun cancanja shiga,
suma dai shadda ce amma kalar ta kowa
daban. Sadiya ta rinka raba kalanda mai
hoton zainab tana dariya rungume da
jariri, kaandar tayi kyau
kowa ya karbi kalandar ya kalla saiya yaba da ita.
Haka su saratu da lawisa su kaita raba
robobi da 'yan kananan bokitai. Da haka
taro ya tashi lfy, kowa yana san barka.
Kayan barka da atamfofi data samu, da
rigunan jarirai kamar wadda zata bude shago.
Ba ruwanta kibarta kawai take yi, taci mai
kyau tasha mai kyau, ta hau gado ta
mimmike ba ruwanta da harkar Ahmed,
yana wajen masu rainonshi su zasu hada
masa madara su bashi yasha, su bashi ruwa, idan ya koshi su goya shi.
Shan nononsa sai lokaci lokaci, saidai
idan ta jiyo kukansa ta kirawo 'yan aikin
nata ta balbalesu da masifa, mai suke yi
masa yake kuka? Suyi ta faman rantse
rantse cewar, wallahi basu yi masa komaiba, sannan zata karbeshi ta bashi
nono, tasa su goya shi suyi ta faman
jijjiga har sai yayi barci.
[1:25PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**15
TASA su goya shi suyi ta faman jijjiga shi
har sai yayi barci.
Sai dai fa du sanda zainab ta dawo daga
makaranta, tana yin sallah zata karbo
ahmad daga wajen masu rainonsa, taita yi masa
wasa tana tarairayarsa, tai
tayiwa mansura naci da magiya dole
saita karbe shi ta bashi nono ya sha ya
koshi.
Ahmad yayi wayo sosai, yayi mugun sabo
da zainab, don har yafi ganeta akan mamanshi
don zainab har ta iya yi masa
wanka, ta shirya shi cikin kaya masu
kyau, tasa mishi turare yaita kamshi. Har
mansura taita sha'awarshi, abinda ita
lalacinta da son jikinta bazai barta ta iya
ba. Du da zainab din ba wani lokacine da ita
ba, inta fita tun takwas na safe sai shidda
na yamma take dawowa, idan sun taso
data dawo gida inta ci abinci tayi sallah,
tayi wanka tasa kayanta, saita dakko
yaronta ahmad taita yi masa wasa tana
lallabashi, har lokacin bacci ta kaiwa
mansura shi ta bashi nono yasha ya
koshi ta taho dashi dakinta ta kwantar
dashi a gado, ta canja kayan barci tayi
musu addu'a taja bargo ta rufe su, ta
rungume ahmad a jikinta suyi barcinsu. Talatuwa
data ke tayaa kwana idan ya
farka cikin dare, ita zata dakko shi ta
bashi madara da ruwa, tasa shi shi
akafada ta jijjiga shi yayi gyatsa ya koma
baccin shi, saita shimfida shi a gaban
zainab ta rufe su. Itama ta koma baccinta du
sanda Aliyu yazo weekend, yana kula
da abinda yake faruwa da yaronshi da
yake kokarin zama marayan karfi da yaji.
Sun sha fada da mansura akan sakarwa
masu aikin dansa data keyi. Yasha korota
intaje kwana dakinshi, yace saita dakko mishi
dansa. Saita rabu dashi ta tafi
dakinta tayi kwanciyarta.
A hankali ya fuskanci tsananin son da
zainab take yiwa ahmad, ya gano zainab
ce take kwana da ahmad ba yan aiki ba,
sai ya samu nutsuwa a ransa, yayi wa Allah
godiya, don yasan zainab tafi
mansura tarbiya da sanin ya kamata,
yasan danshi zai taso da tarbiya matukar
yana tare da zeey autarsu.
Yau asabar, Aliyu yana gida, zainab babu
makarantar boko, wajen tara na safe tayi wa
ahmad wanka a bahon shi, Aliyu yana
kallonta yana yaba baiwar da Allah yayi
wa yarinyar, 'yar da har yanzu bata cika
shekara goma sha uku ba, amma tana da
nisan hankali da tunani wanda 'yar
shekara ashirin da biyar bata dashi, wato
mansura.
Ta gama yi masa wanka, ta nade shi a
tawul tana yimi shi wakar data ke yi masa
inyana rigima. Wayar falonce tayi kara,
zainab ta daga tace "hello yaya ni'ima."
daga can ni'ima tace yau ne fa yinin kawata
murja sule, kizo da wuri muje."
zainab tace don Allah yaya ni'ima kiyi
hakuri, ba zan samu damar zuwaba."
ni'iman tace saboda me?
Zainab tace, yaya ni'ima wallahi ban
tambayi yaya ba, kuma kinga yau nadan samu
hutu ba boko, ina so na wuni da
ahmadina, ba zan iya fita waje na barshi
ba.
Ni'ima tace kinfiya shirme zainab, ina
uwarsa ko zaki zama mai rainonta ne? Ita
ba unguwa take ficewa ta barshi ba, sai ke zaki
zauna ki rinka yi mata wahala
dashi? Tace "haba yaya ni'ima kada ki
manta ahmad dana ne gudan jinina ne,
don wallahi basu da maraba da abunda
zan haifa, tunda dan yaya nane. Ina
ruwana da halin uwarsa, tsarina daban nata
daban. Kiyi hakuri wata rana na
rakaki, kinji yaya ni'ima?
Tace to shikenan auta, ba komai ki
shafamin kan ahmad ki sumbace shi, kice
masa inji momynshi."
zainab tayi dariya tace, "to bar kiji ma nayi masa
kafin ki kashe wayar." ta
suabcin kumatun ahmad tace yarona
momynka tace nayi maka, tana kuma
gaisheka, inta dawo daga gidan biki zata
zo ganinka." ta ajiye wayar tana dariya.
Ta zauna ta gama gogewa Ahmad danshin
jikinsa, ta shafa masa manshi, ta
shafa mashi farar hoda, sannan ta daga
wuyarsa da hammatarsa ta zazzaga
masa, ta shafa masa kasan wuyansa da
hammatarsa, tasa masa kwalli, tasa mai
pampas, tasa masa farar ves, tasa masa safa da
dan takalminsa, ta shafa masa
turarensa. Shirin yaron yayi kyau, gashi
yana ta kamshi.
Ta dama mishi madararsa a fida daidai
cikinsa, tasa masa abaki ya kama zuka,
ya shanye tas, ta bashi dayan fidar mai ruwa a
ciki ya sha, ta dora shi a kafadarta
tana shafa bayanshi, yaron har yayi
gaytsa.
Ta dago shi tana yi masa wasa yana
dariya, daga bayanta taji ance " bani
yaron naki na taya ki raino." ta juyo da sauri tace
"lah! Yaya yanzu ka shigo?
Don ita kwakwata dazu bata ganshi ba,
don ita inta na tar da Ahmad bata
tunanin komai sai yanda zata kula da
yaronta. Ta durkusa ta mikawa Aliyu shi,
ta gaisar da Aliyun ta mike tayi dakinta itama ta
shiga wanka. Tana fitowa ta
goge jikinta da tawul, ta zauna gaban
madubi tana kalkale jiki.
Zainab tun tana karamarta 'yar iyayi ce
da son kwalliya, gata da son kamshi, da
kudinta ma sayan turaruka take yi bare yaya
Aliyu yana sai mata, hakama
Abbansu ko daddynsu suna bata.
Ta tsara kwalliyarta cikin wani fine les
mai fulawoyi, bashida nauyi, riga da siket
ne filet, ta kafa daurin dan kwalinta daya
kara fitowa da kyanta, ta fesa turaruka sai
kamshi take zubawa.
Ta fito falo har yanzu Aliyu yana zaune
yana lallaba Ahmad da yayi barci, tace
yaya yayi barci kawo shi naje na
shimfede shi. Ta dan marairaice masa
cikin shagwabarta tace....
Next episode by 6pm
via #Justice_hamxat
[1:26PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**16
TA DAN marairaice masa cikin
shagwabarta, tace don Allah yaya
kabarni naje gida.
Yace meyasa kike so ki koyi karya ne, ba
inaji ni'ima tayo miki waya zakuje gidan biki
bane?
Tayi kasa da murya cikin shagwaba tace,
wallahi yaya ba gidan biki zanje ba, aina
gaya mata bazan jeba, tunda ban gaya
maka ba. Daman su hajiya zan kaiwa
Amadina su ganshi." ya gyada kanshi, "kuje
direba yana waje sai ya kai ku." tayi
murmushi, yauwa yaya nagode." ya
gyada kanshi ya jingina da kujera yana
ta kallonta, tana ta hada fidar Ahmad ta
ruwa data madara, da dan fulas dinshi na
ruwan zafi, ta debo masa kaya kala biyu da
pampas guda biyu ta zuba acikin jakar
goyonshi.
Wannan page ya dan samu matsala yayi
baki
kwanci tashi ba wuya, zainab ta zama
budurwa, tana da shekara goma sha bakwai,
yanzu tana aji shidda a
sakandare. Zainab kyanta ya kara fitowa,
tana da iyayi da kwainane, akwaita da
tsabta dason gayu, don du wata saita je
salon, bata gajiya da kunshin tafin
kafanta ko zanen fulawa ta lalle. Ta fiya sanyi
magana da marairaita; saiki
zata sangarta ce da shagwaba tayi mata
yawa. Idan tana magana mace ma
burgeta take yi bare namiji, akwaita da
iyayi da yauki da yanga.
Abinda yafi fisgar maza da hura wutan sonta a
ransu, inhar zata shiga waje
saita samu maza masu sonta. Amma
bata iya tsayawa ta sauraresu, domin
tana tsoron yayanta, tana gudun abunda
zai bata masa rai, bata so tayi masa laifi.
Don waya ma ya hanata rikewa, sai wata rana
data je gida Abba ya bata wata mai
kyau, amma ta rinka dari-dari da tsoron
gaya masa. Sai Ahmad ne ya dauka da
gudu ya kai masa yana gaya masa
Abbanshi ya bawa aunty maminshi waya.
Saida ya mata gargadi sosai akan in ta sake yaji
ta bawa wani saurayi numbar
wayarta sai ranta yayi mummunan baci,
don haka take kiyaye wa. Ni'ima anzama
babbar budurwa sosai, tana karatun
diploma har ansa mata ranar aure har ma
ankusa bikin. Aunty sadiya tanada 'ya'ya biyu,
hafiz da
sajida. Mansura kuwa tun daga Ahmad
bata sake haihuwa ba, tace dama saiya
shekara biyar, toh gashi yanzu ya
shekara biyar din. Zainab yarinya mai
hakuri, ga hankali da nutsuwa, tana da kwazo,
don tayi saukar qur'ani yanzu ta
juya hadda. Yau asabar tana tasowa a
daga islamiya ta ware kitson kanta tana
son zuwa salon, harta fara tunanin ta
yanda zata tambayi yayan nata fita, bata
son yayi mata fada. Zainab tayi murmushi tace
don Allah
aunty gayawa yaya zanje salon. Tace
"bazan je inda yake ba munyi fada." tace
haba aunty, don Allah kije ki lallabashi ki
bashi hakuri, ki tambayo min nidai na tafi.
Ta tabe baki tace hakuri? Hakuri fa kika ce? Don
ya kara wulakantani." zainab ta
kalleta cikin mamaki, Ahmad ya fito da
gudunshi da hijabin nata a hannunshi
yana cewa "aunty mami gashi mu tafi
kinji. Tace jeka gayawa Abbanka cewar
zanje salon. Dai-dai lokacin Aliyu ya shigo,
Ahmad yaje ya rike hannunshi
yana gaya mishi "Abba inji aunty mami
wai zamuje salon. Ya dago kai ya kalleta,
"saida kika dauki mayafin tafiya sannan
zakice a gayamin."
ta durkusa cikin marairaice warta, tace don Allah
yaya kayi hakuri, tun dazu nake
jiran fitowarka, ba mayafin tafiya
nadauka ba."
ya gyada kanshi kuje Allah kiyaye.
Tace yaya na gode. Ya bawa Ahmad
kudin salon din, suka tafi direba yakaisu. Suna
yin fakin a gaban shagon salon din,
suna fitowa daga kanta da zata yi karaf
idanuwanta suka hade dana wani dan
kyakyawan saurayi daya zuba mata ido,
tayi saurin kawar da kanta, taja hannun
Ahmad suka shiga ciki, a gurin suka wanke mata
kai suka gyara mata shi,
suka yanke mata farce, suka goge mata
kafa, du da karfa tata sumul take kamar
ta jarirai. Ta fito da youghot da biski ta
bawa Ahmad don kada yaji yunwa.
akayi mata kunshi kunshi sarka a hannu da kafa,
nan da nan ta canja ta kara yin
kyau kamar tauraruwa. Tana fitowa daga
wajen idanunsu suka sake haduwa, yayi
mata murmushi ta dauke kanta da sauri,
ya taso ya tari gabanta. Yace "don Allah
ki taimakamin ki saurareni ki gaya min inda
gidanku yake nazo na sameki a
gida."
ta mika masa katin yayanta, tayi saurin
shigewa motar direba yaja suka tafi.
Saurayin nan ya sumbaci katin data
bashi yana mai jin dadi da farin ciki haduwarsa
da wannan beb
din.
Suna tafe tana tunanin saurayin data
gani, gaskiya ya hadu, itace da tsayawa
yau harda bawa saurayi katin yayanta,
wyarta ce tes ya shigo, tayi mamakin waya turo
mata tes. To kodai ni'ima ce?
Ta bude tes din, bakuwar lambace bata
san mai lambar ba, ta fara karanta sakon
kamar haka.
"i 've been lucking 4 a chance to tell u my
message, i luv u." mamaki ya kamata bata
ankara ba ta
kuma jin shigowar wani sakon, ta bude ta
fara karantawa.
This secret has been in my heart enough
now i want to make it.
Ta bude dayar da suka shigo tare, i told you that
i want u to be my wife" a'a
wannan wane irin kalamomi ne masu
rikitar da zuciya, waye wannan? Ta sake
dubawa ta maimaita karantasu gaba
daya. Ba suna to waye wannan? Ita dai
tasan ba wanda suka hadu dazu bane, donshi
bata bashi lambar wayarta ba.
Kuma tasan ba wani namiji data bawa
lambar wayarta, to ko waye?
Next episode by 9pm
via #Justice_hamzat
[1:26PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**17
Har suka karaso gida zuciyarta tana cike
da tunane-tunane, waye wannan?
Meyasa ya boye mata kanshi bai fadi
sunanshi ba?
Ahmad yayi barci, ta saboshi akafada ta kwantar
dashi kan kujera. Mansura ta
kalleta tace ammafa kinyi kyau, saide kin
dade." ta zauna tace "hum! Kedai ki bari
aunty, saurayi fa nayi a wajen, kuma
harna bashi katin gidan nan, ina tsoro
kuma kada yazo yaya yayi min fada. Mansura
tace a haba wane irin fada
kuma? Ai yanzu kin wuce wannan ajin.
Don ma keba wayayyi bace kanki a duhu
yake, amma yanda kike kyakyawar nan
gaki danyar budurwa shine dai-dai fara
wankar samari, toke sai rashin waye wa, kullum
kina like a gida, idan zaki fita ki
zurma hijabi saika ce gyatuma. Don Allah
ki waye.
Tace, to aunty wai ya kike so nayi ne,
wace iri ne ce wayewar?
Haka dai ta ringa ce mata tanasa matsatsun
dinki ita kuma zainab tace ba
haka Allah yace ba, ka waye akan
addininka shine wayewa, aunty sadiya ce
ta shigo da sallama da kanwar mijinta
yasira, a'a auntyn mu barka da zuwa.
Zainab taje ta rungumeta, tace yasira rabon goron
harda aunty kuke yi ne?
Tayi dariya tace to ya zanyi tace da ita
za'a kawowa zeey autarsu na fati.
Zainab tace fati yasira, anya zan dai zo
miki yini, yaya bazai barni naje miki fati
ba. Sadiya tace haba don Allah, ke bari zakiyi
yasan zakije? Kice masa gidana
zaki zo, ni'ima ma nan zata zo saimu tafi
tare, nayi muku ankon fati da
gwagwaronsa, harda takalmi set din
kayan."
zainab tasa ihu, "sai auntyn mu, kedai kina son
fito da 'yan kannenki.
A to inbanyi muku ba wa zanyi wa, ku
kenan fa kannen nawa mata, ai dole na
gyaraku.
Mansura tace, "ai wannan autar taku
saikin dage mata don taki wayewa, kullum kanta
a duhu yake.
Sadiya tana dariya tace ai laifin mijinki
ne, bakina kallo yke takura mana auta ba,
ki rinka hanashi kin barin ta da yake ta
sake.
Mansura ta kama baki tace rufamin asiri da
yayanku, idan nayi magana tawa ce
take yin zafi, ranar jumma'a wato ranar
fatin, mansura ta shigo dakin zainab
tace, "bazaki je ki fada masa maganar
fatin ba saiya fito? Tace don Allah aunty
gaya masa." tace kinsan in ni na gaya masa cewa
zaiyi inason koya miki yawo.
Ta mike bari naje, aunty kiyi min addu'a
Allah yasa ya barni." tace "to Amin."
yana shirin fita mansura ta kawo masa
jakarsa, zainab ta fito ta durkusa tace
"yayana. Bai kulata ba yace "uhm! Ya akayi?
Yaya dan Allah zanje gidan aunty
sadiya? Me akeyi a gidan?
Bikin kanwar mijinta ake yasira, shine
nake neman alfarma dan Allah yaya
kabarni naje. Ya daga kai kada ki dade. Tace to
yaya
nagode." yana fita ta tafi gidan sadiya,
direba ya kaita. A can ta tarar da ni'ima
suka rugume juna suna murna. Kinyi sa'a
'yar uwa ya barki."
kinganni dai, yayan namu ne sai a hankali. Amma
yau ba laifi fuskar tasa a
sake take. Hu! Aunty wannan material din
fa? Tana daga su tana yaba kyansu.
Tace Abban yasir ne ya kawomin su
tsaraba, amma naga sun zo akaya zan
sai muku. Yauwa auntyn mu kina burgemu fa.
Suka
gama tsra shirinsu na zuwa fati, wani
hadadden material ne da aka sake fito da
kyansa da wani dinki mai kyau.
Gaba daya su ukun sunyi kyau amma ba
kamar zeey da kamar don ita aka yoshi. Suna
bayan motar sadiya da mijinta suna
gaba. A gidan fatin suka bi bayan amarya
da ango suka rakata har mazauninta.
Yaron sa'adu bori yanata kida da waka
'yan mata sunata rawa daga baya aka
tsaya da kidan, babban kawar amarya tazo ta yi
addu'a tareda yiwa bakin da
suka zo barka da zuwa. Daga nan ango
da marya suka tashi suka ja zugar
kawaye da abokai suna biye da bayansu
har wajen masu sabis. Kowa shiyake
sabis din kansa. Zainab duk inda tyi idon mutane
ne akanta, ita kallon ya isheta,
don bata saba da irin wannan shiga ba,
ta saba kullum tana hijabi, to ita abunda
yafi damunta ma sha daya har tayi, tana
jin soron yaya fa.
Amma yaya sadiya da mijinta sunce har dakinta
zasu rakata su bawa yaya
hakuri.. Wata kawarta tazo taja
hannunta, dole saita yi rawa. A hankali
take juyawa, kusan maza hudu ne suka
rufa kanta suna mata liki.
Kamar daga sama yaya Aliyu ya diro wajen, saiji
tayi an damki hannunta. Ta
juyo a tsorace dan ta razana, ganin
yayanta ya hade rai kamar wanda bai
taba dariya, saita firgice ta tsorata. Ya
funciki hannunta yayi waje da ita, ya
bude mota ya turata ciki shima ya shiga. Ta
takure a tsorace take, saboda tasan
halin yayanta sarai, akwai zafin zuciya.
Aliyu ransa ya baci sosai ganin maza
suna yiwa zainab liki, ba dai sonta suke yi
ba? Wani abu ya soki kirjinsa, ya rinka
ganin bibbiyu a idonsa, yayin da motar ta fara
tangal-tangal kamar zata kifa.
Zainab ta fara salati ta baro kujerarta ta
rungume Aliyu tana ihu tana salati.
Tirkashi! Mu hadu a littafi na biyu,
waishin menene ya soki zuciyar Aliyu?
via #Justice_Hamzat
[9:14AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**1 & 2**2
A hankali ya dawo hayyacinsa,
yaci gaba da maimaita salatin daya ji zainab tanayi. Saida
taji ya samu nutsuwa sannan itama tafita daga tsoron data
shiga, tayi saurin komawa
wajenta. Yaci gaba da tukin a