TATTALIN SO Complete Hausa Novels by Surayya.txt

Author :  Surayya Category :  Home Of Novels

Chapter   6 / 18

15K to 18K   out of 51.6K words

babarta da yayarta suka shigo
suna tambayar meya faru? Mansura ta fada jikin
babarta tana kuka, tana cewa hajiya kinga
abunda suka yi min, kina kallon irin sakayyar da
sukayi min, du kyakyawan rikon dana ma zainab
yau sunga ta mike ta zama mutum, shine suka
aurawa Aliyu ita." ta karasa tana kuka. Hajiya da
saratu suka saka salati tare da cewar, amma
Aliyu da zainab sunci amanarki sun tozarta ki, sun
wulakantaki, amma kansu sukayi wa, yanda
sukayi miki Allah ya tozartasu, taho mu tafi, aure
ne bakya yi su rike dansu. Bayan zainab su kara
aura masa mata uku su zama hudu.
Daman munafunci daya sa aka kai miki zainab
din don ta gama ganin sirrin gidan, ta riketa
Amana tamkar uwarta, amma sakayyar da zakuyi
mata kenan. Don kanku ku rike Aliyu, Allah ya
bata wanda ya fishi, suka jata suka nufi nasu gidan sunata
sababi.
Tofa Littafi ya canja salo
[9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**5 & 2**6

SUKUWA maza 'yan daurin aure, ana gama daurin
aure suka nufu daula hotel, don cin abincin daurin
aure, wato walima ta zama kadai 'yan daurin
aure.
Aliyu ba abunda ya dame shi sai washe baki
yake, yana ta gaisawa da mutane. Da yawa
mutane sunata mamaki, don sun san miskilanci
da rashin yawan dariya irin na Aliyu, amma yanzu
ya kasa rufe bakinsa saboda fara'a da amsa
gaisuwar jama'a da masu sanyawa auren nasu
albarka.
Cikin gida kuw, masu gidan yaransu da manyansu
cikin farin ciki suke da wannan aure na Aliyu da
zainab, saboda kawunan su a hade yake.
Su sadiya dasu ni'ima kuwa sai murna suke suna
zuba shewa da tafi.
Zainab kuwa tana dakin umma kudundune cikin
bacin rai, duniyar tayi mata zafi, ta rasa mai yake
mata dadi. Ita bata ga laifin auntyn ta ba, dole
tace taci amanarta. Mai auntyn ta rage ta dashi?
Ta dauketa kamar 'yar cikinta, amma yau
sakayyar da zata yi mata kenan ta aure mata
miji? Ta sake fashewa da kuka.
Meyasa haka? Meyasa yaya Aliyu mata haka?
Tana ganin yaya Aliyu mai rikon gaskiya da
amana, ashe shima zai iyabin son zuciyarsa. Ya
aureta yaci amanar matarsa? Wayyo ni Allah!
Kaico da wannan rayuwar, ranta ya rinka kuna,
makogwaronta ya rinka daci, ta rinka jin wani
yuuu a kanta. Ta dafe kan tana jin wani sara
mata da yake yi, wasu duhu suka gifta ta idonta,
idanuwanta suka rufe tayi baya ta fadi
numfashinta ya dauke.
Umma da ummi suka shigo dakin a lokaci daya,
suka ganta a wannan halin. Gaba daya sukayo
kanta suka dagota suna salati, umma ta
rungumeta tana salati tare da nanata kalmar
innalillahi wa'inna ilaihi raji'un."
yayin da ummi tayi falo da sauri tana salati,
mutane suka yo caa akanta suna tambayarta
lafiya? Ta rude sai fadi take ku kirawo mana
direba, zainab ce ta suma."
sadiya da ni'ima suka saka ihu suka yi cikin
dakin. Dakyar aka samu direban aunty sadiya a
waya, don duka direbobin sun kwashi mutane
suna can daula hotel.
Aka dauki zainab bata san inda kanta yake ba,
suka tafi asibiti. Sunata neman wayar Aliyu gaba
daya wayoyinsa a kulle suke saboda jama'a.
Haka ta Abba da daddy ma du ba'a samu.
A asibiti kuwa gaba daya matan sun cika daki
sunata koke koke, su umma da ummi kuwa da
mama matar baban su zainab, sunyi jugum-
jugum sai salati suke suna hailala a zuciyarsu,
tare da nemawa zainab lafiya cikin zukatansu.
'yan nurse din duk suka korasu falon asibitin,
sannan likita ya fara yiwa zainab taimakon
gaggawa.
Cikin ikon Allah ta farfado, sai likitan yayi mata
allurar bacci donta samu nutsuwa.
Sai sha biyu aka tashi daga walima, sannan aka
samu lambar wayar Abba da daddy. Suna jin
zainab a asibiti suka ce subhanallhi, meya faru
kuma haka? Umma tace, "shidewa tayi ta zube a
sume." to Allah sauwake gamu nan zuwa." Abba
ya binciko Aliyu cikin abokansa yace kaifa muke
jira ka gama sallamar abokanka kazo muje wata
'yar anguwa. Aliyu ya amsa musu cikin
girmamawa, bai tsaya tambayarsu ina zasuje ba.
Aliyu yana gaba kusa da direba, Abba da daddy
suna baya. Direba ya kaisu asibiti, tunda suka
shiga gaban Aliyu yake faduwa, yake tunanin me
kuma ya faru?
Direba ya tsaya suka fito, suka nufi falon asibitin
jikin Aliyu a sanyaye,
yana hango su umma da ummi, ni'ima da sadiya
da hajiya ya fara karanto kalmar "innalillahi
wa'ina ilaihi raji'un.
Daga nan ya rinka tsintar bayanin da ummi take
musu, na abunda ya samu zainab, ran Aliyu ya
baci hankalinsa ya tashi. Bai tsaya sauraron
ummi datake gaya masa likita yace kada a shiga
inda take ba, da saurinsa ya nufi dakin da aka
kwantar da zainab din.
A hankali ya murda kofar ya shiga
da sallamarsa aciki.
Nurse din data ke gadinta tana zaune gefe daya
tana sauraron farkwanta, tana ganin Aliyu tasan
shi sarai, don haka ta mike ta fito.
Aliyu ya tasaya gaban zainab yana kallonta,
yarinyarshi zainab mai kyau da nutsuwa, lallai ta
shiga tashin hankali, yau daya kawai ta rame
haka. Yasa hannu ya shafi fuskarta, tayi fiyau da
ita. Saiya ga takara fari, dan bakinta lebenta
jajaye, siririn dogon hancinta mai tsawo, ga zara-
zaran gashin idonta, baki lafiyayyen gashin girarta
daya kwanta das kan girar.
Ya zame dan kwallin kanta, bakin gashinta mai
tsawo da sheki wanda kullum yake kasancewa
cikin gyara, yaita walwali yana sheki, shiyasa bai
taba hanata zuwa salon ba, yanzu du sati biyu
take zuwa salon, dan ya fuskanci bata damu da
kitsoba saide kalba.
A hankali ya rankwafa kanta ya hada fuskarsa da
tata, cikin kyakyawan lafazi muryansa can cikin
makogwaronsa yace "zeeyta
ki soni don Allah ki kaunaceni, bani da buri
kullum saina yanda zan mallakeki. Zainab kece
rayuwata, tun ranar da kika fado duniya ina
ganinki Allah ya dasa min kaunarki a zuciyata,
kullum kwanan duniya karamin kaunarki akeyi.
Zeeyta ba kya ceto rayuwar yayanki ba, ki
tsamoni daga cikin damuwa ba? Haba zeeyta, ke
kadaice farin cikin rayuwata." aka taba kauren
kofar ya dan ja baya. Likita ne zai shigo, yayi
saurin gyara mata dan kwalinta ya rufa mata
maya fi, wai don kada yaga jikinta.
Likitan yayi sallama, yace, ta farka ne? Yace
mishi a'a ya mika masa hannu suna gaisawa..

YACE kada ka damu idan ta farka normal zaka ganta.
Sai dai don Allah adinga kiyaye wa abunda zai bata mata
rai."Aliyu ya gyada kai, yace "insha Allahu za'a kula.
Abba da daddy suka shigo suka tsaya akanta
suna yi mata addu'a da fatan Allah ya bata lafiya.
**** *** ****
saratu da lawisa sun saka mansura a gaba
sunayi mata fanfo zuga iri-iri, lawisa tace, "don
haka nake gaya miki, ki kula da yarinyar nan,
mutum mai shiru-shiru abun tsorone, kinga yanzu
ta kaiki ta baro. Ta gama sanin sirrinki kaf gashi
yanzu ya aureta ta zamo kishiyarki, wallahi ko
kadan kada ki saurara mata, kada ki barta ta
zauna don ba gidan zama tazo ba.
Kuma wallahi ki fito da kudi mu shiga malamai ki
samo kansa, ki mallake shi tsab. Dai-dai da
uwarsa da ubansa ki rabasu dashi, ya zamo babu
wanda yake gabansa saike da yaronki.
Mansura tace, "um! Wannan uban 'yan taurin kan
zai mallaku ne, tun kwanakin baya fa na kashe
kudi akansa, amma inda kika san dutse haka
yake, kwata-kwata baya lankwasuwa. Kuma
halinsa ne bawai ni kadai yake yiwa hakan ba, ita
kanta yarinyar baki ga yanda yake takura mata
ba. Inta jin tausayinta. Ashe shidai akwai abunda
yake kullawa ransa.
Kiga mutum kullum kicin-kicin dashi ba fara'a shi
ba zai zauna ayi wata hira mai dadi dashi ba
ballantana kiga dariyarsa. Wallahi na gaya miki
sai muyi kwana biyu dashi bama magana, don
haka ma tsani naga yazo garin gwanda yana can.
In nayi magana yace wai dan Allah na rabu dashi
ban iya soyayya ba. Du wayewata yana cewa ban
iya soyayya ba, yanzu daya auri wannan
gidahumar kifin rijiyar aina ga ta yanda zasuyi
soyayyar.
Saratu yayarta tace, to inbanda ke da abunki
wannan ai du shi zai koya mata." mansura tace,
tabdijam wannan, wannan dinne zai zauna yana
koya wa mace wani abu, ai shi inbanda isa da iko
da gadara babu abunda ya iya. Shifa ason ransa
komai saide kayi masa yana daga kwance, tunda
naga sangartar tasa tayi yawa kai tsaye inya ce
inyi masa abu nake cewa bazan iya ba.
Lawisa tace wallahi na gaya miki namiji ba dan
goyo bane, ko uwarka ka yanka ka bashi inya
tashi mantawa zaiyi ya zuba ma rashin mutunci."
saratu tace to ba gashi ya mata ta gani, ta rike
'yar tamkar cikinsu don yankan kauna ya tashi ya
aureta.
Mansura tace shekara takwas ina rikon 'yar nan,
ko shekara banyi gidan miji ba ya tattaro min
rikon 'ya, karshe abunda ya sakamin dashi
kenan? Ai duk zasu ci buhun ubansu, mun saka
kafar wando daya dasu. Wallahi saina rushe
zamansu, basu bajin dadin rayuwar, mu zuba su
gani.
**** *** ****
kwanan zainab biyu a asibiti, tayi bacci ta huta
sosai, don data farka take komawa baccin
zuciyarta ta huta ta samu nutsuwa, ta manta da
abunda ya faru.
Dakin cike yake, da mutanen gidan, zainab ta
farka ta yunkura zata mike, umma ta dagota a
hankali tana yi mata sannu. Zainab tayi salati
tace, "umma meye na ganni a asibiti? Tace ishiru
bakida lafiya ne, zo muje ki wanke bakinki."
ta kamata takaita toilet ta wanke mata bakinta
da fuskarta. Ta dawo da ita ta zauna a bakin
gado 'yan uwanta da iyayenta suna mata sannu.
Ummi ta hada mata shayi mai kauri tana bata da
kofin, mama ta zubo mata farfesun kaza ana bata
tanaci, taci dayawa.
Aliyu ne ya turo kofa ya shigo da sallamarsa, tayi
kur ta zubo masa ido tana so ta tuno wani abu,
shikuwa murmushi yake yi, ya daga hannunsa
sama yana yiwa Allah godiya.
Ta kura masa ido tana kallonshi ko kiftawa
batayi, a hankali abun ya fara taro mata cikin
kwakwalwarta, tabbas abunda taji ba mafarki
bane gaskiya ne, yanzu ita matar yayanta Aliyu
ne da gaske? Hawaye ya fara zubowa a idonta,
ta mike a hankali tana takawa sannu a hankali ta
nufi inda Aliyu yake a tsaye, ta durkusa a
gabansa cikin kuka, ta rike kafafuwansa tasa
kanta ajiki tana kuka, da sheshsheka tana cewa,
yaya, haba yayana yaza kayi min haka? Haba
yaya kaine fa uwata? Yaya yaza ka rikide ka
zama mijina? Yaya du abunda uwa take yiwa
'yarta tunda na rasa mamana kai ka fansheta, ka
juye ta a wajena, ka hanani maraicin rashin uwa,
ka zama kaine uwar tawa. Ya zakayi min haka
yayana? Kaifa mijin auntyna ce, matar da na
dauketa kamar 'yar uwata da muke ciki daya, ta
rikeni da gaskiya da rikon amana, zumunci ne mai
karfi tsakanina da ita.
Yaya ya zakayi sanadiyyar rugujewar wannan
zumuncin? yaya don Allah, yaya don girman zatin
Allah ka taimake rayuwata ka sauwakemin
aurenka ka bani ko waye kaga dama."
dakin shiru yayi bakajin motsin komai sai
kukanta, mahaifinta ya taso yazo ya dagata, yace
"haba zainab ina ganinki da hankali da ilimi, ashe
sun zamo na banza tunda zaki iya cewa mijinki
ya sakeki." tace kayi hakuri daddyna
bazan iya zama da auren nan ba, naci amanar
auntyna, da wani ido zan kalli auntyna? Na
yaudareta naci amanarta, naso kaina daddy,
bazan iyaci amanar auntyna ba."
daddyn yace yau, "zainab yau zan gaya miki
abunda baki saniba, tun kafin Aliyu ya san zai
san mansura mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke." ta
juyo a razane ta kalli mahaifinta. Ya daga mata
kai yace kwarai hakane.
Bazan taba mantawa bayan mamanki ta haifi
sadik da
banda lpia ina fatan zky hkri
[9:15AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**7

Bazan taba mantawa ba bayan mamanki ta haifi sadik da
faruk, tana so ta haifi 'ya mace, ita da Aliyu har nafilan dare
sun sha yi da rokon Allah ya bata 'ya mace mai hankali da
nutsuwa da hakuri da baiwar ilimi.
Saboda tunda na auri mamanku Allah ya hada jininsu da
Aliyu, komai nasa a gurinta yake.
Shawararsu daya bakinsu daya. Lokacin da mamanki ta
samu ciki kusan tare sukayi laulayin cikin nan, idan tayi
amai shi zai kwashe ya gyara
wajen, du abunda take son ci shine dan aiken
sayowa.
Ranar da aka haifeki kuwa kiri-kiri Aliyu ya hana
daukanki wai kada asa miki datti da ciwon jiki, du
sanda akace Aliyu ya samu hutu bashida wajen
tarewa sai wajen mamanki yana rainonki. Kina da
shekara daya ya shirya miki birthday. Kina kan
kafadarsa yana yawo dake. Lokacin da ya yanka
cake din yasa miki abaki aka dau tafi, yace Allah
yasa na miki na aurenmu watarana."
mamanki tace, "haba Aliyu, yaushe zakayi jiran
karamar yarinya haka? Yace wallahi mama tun
ranar da aka haifi zainab Allah ya dasa min
kaunarta araina, ni dai dan Allah mama inaso
kimin Alkawari zaki auramin zainab inta girma."
mamanki tace na dau alkawari, in dai har Allah
yayi kai mijinta ne, to ba mai aurenta sai kai, na
baka zainab tundaga yanzu ta zama taka.
To kinji yanda mahaifiyarki ta bawa Aliyu ke, tun
kina 'yar shekara daya. Abunda ya tashi aurenku
kuwa yanzu, yazo mana ne ransa a bace yace
"shidai dan Allah a taso da alkawarin mamanki a
aura masa ke, don yana tsoron samarin da suke
yi miki tururuwa, yaga har kin fara zance. Shiyasa
ya nemi alfarma a hade aurenku data ni'ima.
To yanzu mahaifiyarki tana karkashin kasa ta
rasu, baza kiyi kokari ki cika mata alkawarin data
dauka ba, kinfi so kita barinta da nauyi akanta?
Ta dago kanta tana kuka tace, daddy ko wane
irin alkawari mamana ta dauka akaina zan iya
cika mata shi, na hakura daddy. Kayi hakuri ka
yafe min bata maka da nayi." yace bakomai
zainab, tsakanina dake kullum sai albarka."
***** ****** ****
kwananta uku a asibiti aka sallameta, don taji
sauki. Amma du shigowar da Aliyu zaiyi tana
asibiti nan bata iya dago kanta ta kalle shi bare
tace zatayi masa magana kota gaisheshi,
kunyarsa take ji sosai. Bama inta tuna haidar
shine Aliyu, du tes din kalamomin soyayyar da ya
rinka turo mata da wayar da suka rinka yi ashe
du yayanta ne Aliyu, ita ya zata yi da wannan
abun kunya?
Ita kuwa mansura data ji zainab tana asibiti,
addu'a ta rinka yi Allah isa kada taji sauki a fasa
aurenta da Aliyu.
Da Aliyu yaje dadadare gidansu mansura zai
dauketa su tafi gida, sai tace ai ita ta gama
zaman gidansa, mayaudari maci amana, Allah ya
isa tsakanina dakai! Tunda kaci amanata."
abun ya konawa Aliyu rai, yace ni kike gayawa
wannan maganar? Tace ana gaya maka din
azzalumi! Yace to ya isheki, kada ki sake bakinki
ya kuskure ki zageni, zaman gidanku kuwa kiyi
tayi, randa kika gaji kya dawo." yaja motarsa ya
tafi ya barta nan tsaye.
Saboda kwanciyar zainab a asibiti, an fasa bikin
da kaisu acikin wannan satin sai asabar mai
zuwa za'ayi wuni akaisu dakin mazajensu.
Zainab ta zamo bata da sakewa ko yawan
magana, ko yaushe ka ganta tayi shiru tana
tunane-tunane. Aliyu daya fuskanci kunyarsa take
ji sosai, saiya daina shigowa inda take. Sai dai da
safe d daddare yayo mata tes yace kici abinci fa,
kinsan bana son zama da yunwa.
Ya karashe mata tes din da kalaman soyayya
masu sanyaya zuciya. Takan girgiza kai tace, "kai
namiji, ba ruwanshi da kunyar abunda yake so.
Wai yayanta Aliyu shine yake mata irin wannan
kalaman soyayyan, baya jin nauyinta bare
kunyarta.
Yaita aiko mata da cimarta ko yaushe, abubawa
da yasan tafi so,
suna zaune a falo ita da ni'ima, wayarta tayi
kara, ta duba ta gani saita kyaleta taita burarinta
harta gaji ta tsinke don kanta, amma sai aka
sake bugowa.
Ni'ima ta dago kai ta kalleta, tace ki dauka mana
dan Allah, nasan bazai wuce yaya ba." ta girgiza
kai tace bashi bane." ni'ima tace to ki dauka
mana."
ai ban san mezan ce masa bane.
Ni'ima tace ki gaya masa abunda ya faru kawai
kada yaga kin yaudareshi."
tana daf da katsewa ta dauka, a sanyaye tace
"hello! Daga can nura yace ai dole kiki daga
wayata, kunya ma ai ta isheki.
Wato zainab ina ganinki simi-simi kamar ma
hankali, ashe azzaluma ce ke, kin yaudareni.
Kinsan saurayinki ne aurenki zaiyi kika binneni a
cewar yayanki ne a hannunsa kike, ashe
masoyinki ne.
Zainab idonta ya fara zubar da hawaye, tace ba
haka bane, don Allah nura ka saurareni kaji.
Karaf a kunnen Aliyu daya shigo dakin a yanzu,
tuni hanjin cikin zainab ya hautsina, tuni ta rikice
ta kasa cewa komai, wayar tana manne a
kunnenta tanaji nura yana gaya mata
maganganu.
Aliyu ransa ya baci, ya rinka wani huci ya karaso
inda hankalinra ya tashi, ta rintse idonta tana
jiran saukar mari. Yasa hannunsa akan nata
hannun da yake kange a kunnenta, ya zare wayar
, ya daka masa tsawa kai wawa shasha! Kana
sane da matar aure kake waya? Wallahi kayi na
farko kayi na karshe...

Bakwa comments ko likes don haka zanyi daina wahalar da kaina may be littafin bai muku bane shiyasa nayi typing kadan ma.
[9:16AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**8, 2**9 & 2**10

DU sanda ka sake yiwa matata waya saina daureka bbu
beli. Kuma yanzu ma ka saurari zuwan kana nan sojoji,
zasu zo su koya maka
hankali." ya cire wayar da kunnansa yayi cilli da ita ta daki
bango ta tarwatse, ya karasa gurin ya ciro sim card din ciki
ya kakkarya shi gutsi-gutsi ya
watsar a wajen. Ya dago kansa yana mata wani
irin kallo, yace wannan ya zamo na karshe, idan
na kuma gani kina waya ko kina magana da wani
sai ranki ya baci." ya juya ya fita.
Ta dafe kanta tana kukanta. Ni'ima ta dawo
dakin da tun shigowar yaya Aliyu data ga sababin
da yake yi ta zame jikinta ta gudu, don kada ya
huce akanta."
ni'ima ta zauna kusa da ita ta dafa ta, tace meye
na kuka, ke matsalarki kenan saurin kuka."
tace, haba yaya ni'ima, kin san sarai yaya Aliyu
ya fiya saurin fushi da zafin zuciya, ni kuma bana
so naga bacin ransa balle kuma ace ni na bata
masa, taya za ayi zaman aure a haka?
Ni'ima tace haba zainab kefa mai hakuri ce zaki
iya zama da yaya Aliyu, don kinfi kowa iya gudun
bacin ransa. Ni sai yanzu ma na fahimta ashe du
tsanani da yaya yake yi miki soyayya ce da
kishinki da yake yi, ni wallahi ban taba ganin
amarya da ango da suka dace da juna ba irin ke
da yaya."
idonta yayi narai-narai hawaye ya sake zubowa
tace, "ke yaya ni'ima haka zaki rinka yi min?
Ta fashe da kukanta. Ni'ima ta rungumota tana
rarrashinta, "to shikenan kiyi hakuri na daina, ba
zan kuma ba."
du wayanci kawayen zainab ta gayyace su bikin
ni'ima, to da abun ya zamo haka ya hade da
nata, sai babbar kawarta hauwa Rabi'u ta rinka
yiwa kawayensu waya tana sanar musu tare da
basu hakuri na rashin ganin kati. Du da haka
saida Aliyu ya sanar a gidajen radio, saboda na
nesa kawayenta da basu sani ba.
Ranar jumma'a akayi mata kamu, kamun da ya
bada mamaki saboda cikar kawayenta da 'yan
uwanta suka yi, sai da aka fara saukar Qur'ani
sannan aka kamata."
daga nan wata malama ta bude filin da dan
wa'azinta (kusan hakkin miji akan matarsa ne
wa'azin kuma inaga munyi a baya basai na
maimaita ba).
Malamar nan tai ta wa'azi da fadakarwa akan
aure, wanda tunda aka fara zainab take kuka, dan
jikinta har rawa yake yi. Du da tasan hakkokin
miji akan matarsa babu abunda malamansu na
islamiya basu koya musu ba, amma wa'azin
malamar nan ya shigeta.
Yanzu taya zata hada jiki da yayanta Aliyu harta
kwanta gado daya dashi? Ya salam! Allah kaika
san abunda kake nufi da auren nan, Allah ka bani
ikon biyayya ga mijina.
Ranar asabar tun asuba akayi wa zainab da
ni'ima gyaran jiki, inda jikinsu ya fara laushi da
tsantsi, fuskarsu kuwa kamar kwan lantarki dan
kyau.
A wajen walima shiga iri daya akayi musu, wani
dankareren abu me kyalli da walwali pink, da
gwagwaro pink, dutsen da suka sa a hannu da
wuya duk pink, takalmi da jaka duk pink, sunyi
kyau sosai.
Walimar ta tara kyawawan 'yan mata gogaggu
masu takama da ayar Allah.
Domin ayau ma wani wa'azin aka kuma yi mai
shigarwa, daga nan wani babban malami yayi
lakca wadda ya ladftar da zuciyar mai saurare, ya
dasa tsoron Allah a zukatan wanda suka saurara.
Daga karshe aka rufe da addu'a, aka yiwa
angwaye da

6 / 18