Author : Surayya Category : Home Of Novels
ta sashi cikin kekensa na zama.
Aliyu ya fito ya nufi arfat, ya daukeshi, Abbana ya
jikin? I luv u Abbana, ta zauna kusa dashi, yaya
barka da dawowa ga abincinka.
Bana ci.
Haba yaya don Allah kayi hakuri
meyasa bazaka ciba?
Ki kyaleni kawai zeey kin batamin rai, ki barmin
yaro da ciwo ki ki yimin waya, to da ya mutu
saidai na tarar da gawa kenan?
Ya tsaya bakin taga yana kallon Ahmad da ihsan
suna ball.
Via #Justice_Hamzat
[8:13AM, 07/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 4***16
Ya tsaya bakin taga yana kallon Ihsan da Ahmad suna ball
a harabar gida.
Yaji dadi a ransa, zainab ta taso ta daura kanta abayansa
tana magana, cikin sanyinta.
Kayi hakuri yayana ka gafartamin
naga baka dade da tafiya ba, kuma ka barshi lafiya lau,
saina kasa gaya maka, ina gudun tashin hankalinka.
Saina rasa ya zanyi da yaron, ga talatu ta tafi duba jikarta
ba lafiya, na rasa ya zanyi dashi, ni nasan bazan iya fita
bada izninka ba, shiyasa kawai nasa yaron a gaba ina
kuka.
Yaya ka yafe min, bada niyya nayi hakan ba.
Ya juyo ya rungumeta yana share mata hawayen, yaji
tausayinta, ya juyo da ita ya rungumeta yana rarrashinta.
Shikenan naji, ya isa daina kukan, na hakura muje ki bani
abincin.
**** *** ******
da yaje gida yake cewa Alh yana so zai rubuta takardar
neman alfarma a dawo masa da ofis dinsa kano, saboda ya
zauna cikin danginsa da iyalansa.
Alh yace wannan shawara tayi daidai, tunda ka fara tara
iyali dole ka zauna a waje daya, ko don kulawa da ilimin
'ya'yanka ma.
Hakan akayi kuwa baisha wata wahala ba, wajen amince
masa, aka bashi ofis a kano.
Ga harkokin kamfaninsa komai yana garawa yanda yake
so.
Zaman mansura da zainab babu irin kyara da wulakanci da
cin mutunci da mansura bata yiwa zainab, amma zainab
saita kwantar mata da kai tana binta a sannu, bata kuma
bari Aliyu ya sani, bare yayiwa mansura fada, ita dai zainab
ta dage da gayawa Allah basu zaman lafiya.
Cikin hukuncin ubangiji kuwa, Allah ya amsa addu'arta.
Ta shiga falon mansura arfat na biye da ita, watansa sha
biyar yanata yawonsa ko ina, amma bata yaye shi ba.
Tace aunty zanje dubo jikin hajiya, ga arfat nan kafin
Ahmad da Ihsan su dawo islamiyya.
Har zata fita, mansura tace ke dawo ki dauki danki.
Zainab tayi murmushi tace dana ko danki aunty? Ai kin fini
karfi akan 'ya'an nan dani dasu du mallakarki ne.
Mansura tace wai 'ya'yanki da kike turowa su wuni a
bangarena ke kina naki bakya tunanin na cutar miki dasu,
kona dakesu, ko nayi musu wani mugun abu?
Zainab tace haba aunty na dade fa da sanin halinki, tun ina
'yar shekara takwas nake hannunki, da kina da mugun abu
dani zaki fara yiwa.
Aunty kina da kirki da hakuri kullum dauriya nake yi, har
nake iya hada ido dake. Amma ina mai jin nauyi da kunyar
aure miki miji danayi. Tasa kuka.
Mansura ta taso ta rungumeta, kada ki damu zainab na
dade dayin nadaman irin abubuwan da na rinka yi miki, don
kin auri Aliyu
wanda wauta nayi da son zuciya, tun fil-azal Allah ya rubuta
ke matarsa ce, to ya zanyi da wannan rabon?
Tunda kika haifi Ihsan Allah ya cusa min kaunarta a raina,
haka arfat gani daya nayi masa naji kaunarsa ta ratsani.
Kiyi hakuri zainab da abunda nayi miki.
Ta rungumeta, wayyo aunty dan Allah ki bari ban taba
rikonki da komai a raina ba, na yafe miki aunty nima ki yafe
min.
Na yafe miki zainab.
Aliyu ya fito daga daki yana yi musu tafi, yace nagodewa
Allah da kuka hade kanku, ga cek na milyan biyar-biyar kuja
jari.
Suka yi tsallen murna suka rungumeshi, suna masu yi masa
godiya.
Sun hade kansu bame jin kansu, tare suke harkar business
dinsu.
Dubai zuwa kano suna harkar gwala-gwalai, mansura ta
samu ciki ta haifii 'yarta mace.
Ansha murna da bidiri, akasa wa jaririyar Ikram, Ihsan du
tafi 'yan uwanta murnar zuwan Ikram don gani take yanzu
ta samu abokiyar shawara.
A tsakanin mansura da zainab baka iya gane 'ya'yan, don
gaba daya sunfi zama bangaren mansura. Aliyu kullum
yana cikin godiyar Allah.
Kamar yau da kullum nima da nake cikin godiyar Ubangiji.
TAMMAT BI HAMDULILAH.
Sai wani jikon kuma @Khadija Idris ringing