Author : Queen Mamie Category : New Hausa Novels 2026
Hansai kuwa ta b'angaren iLimi sai nace Masha Allah ,duk k'auyen ayaran Mata,domin ta dage kullum Malam na k'arfafa Mata Gwiwa Musamman na Addini sai san barka.
Sam bazaka ce Hansai daga K'auye take ba,tun Bayan da malam ya dakatar da Gwamma sai ya ce Dije ta Koma gun Jummai haka Dije ta fara nutsuwa ,gashi Hansai Ke koya Mata karatu Sun saba sosai ,sab'anin da sai de ta tsaya k'ofar d'akin su tana hararar Hansai duk da yarinya ce mai Shekara Hudu.
Gwamma kam tana gani ba damar magana don Malam yace duk randa takarya doka inta bar Gidan to har abada bazata dawo ba. shiisa tai shiru saboda tana k'aunar zaman Gidan domin tabbs tasan Malam yana da kyautatawa da yawa.