Author : Queen Mamie Category : New Hausa Novels 2026
"Yawwa bari na tafi."
Haka Gwamma ta tafi,tana tafiya tana maijin dad'i.
Da misalin k'arfe Hud'u Maigari ya shiga gida Bayan ya huta Ladidi ta zo mai da maganar da Gwamma rltazo da ita, Murmushi yayi "wan nan ai magan- ganun Mutane ne" ita wan nan Matar dama bata son Yarinyar ,don haka abar Maganar kar ma kowa yaji."
Haka Ladidi ta hak'ura tabar maganar Amma abin na ranta.
k'arfe shida su Jummai suka dawo ba laifi sun sayo kaya da yawa, k'aramar motar d'aukan kaya da gado aciki na katako duk k'auyen Hansai ce Malam ya fara yiwa, duk a wanda akaiwa aure ba masu irin sa duk da wan nan d'in ma bamai tsada bane can,lalle ta cika yar gata littafin( Miemei bee) Malam yayi farinciki ganin kayan .
Gwamma kuwa sai dariyar Mugunta take ganin ta had'a gurmi, haka dai sukai ta shirye- shiryen su.
Bayan sati d'aya Gwamma taji shiru ba alamun cewa an fasa auren, sai ma shiri data ga anayi a irgen da tayi yau saura Sati Uku bikin,hankalin ta ya tashi. Yau ma da takasan ce ranar Laraba Gwamma na zaune ta rafka ta gumi zumbur ta mik'e cike da wani tunani, ta yafa mayafi ta fice bata zame ko ina ba sai Gidan Delu,ta shiga Delu na zaune tana cin Zogale ta taso tace "lalle daga ganinki ta ciyoki."
Gwamma tace "sosai ma ai mufita nake nema."Delu tace "ai Labarin Bikin Hansai ya karad'e K'auyen nan ,ina zaune a nan nace kinyi sake".
Gwamma tace "yo ai lokaci bai k'ure ba."
Delu tace "tabbas yanzu kawaii kizo muje Gidan Boka na gaban K'auyen nan, da Zafi-Zafi akan bigi K'arfe.
Gwamma tace "yo ai matsalar ta Kud'i ce."
Delu tace "ai ba damuwa kije ki had'a su Kud'ad'en ki ,sai muje.
Gwamma tayi shewa "shiisa nake sonki Delu haka kawai yarinya ta zame min sai kace 'yar kishiya"! haka suka gama Gwamma ta tafi.
Fafutukar samo Kud'in Gwamma tashiga yi ,kurd'a- kurd'a, kullum tana yawon rancen Kud'i har wata Akuyarta, ta sayar nan ta had'a dubu Goma ,ta shiga kuma neman cuko dak'yar da Sid'in Goshi ta had'a Kud'in a sati d'aya ,hakan yayi dai- dai da Sauran Bikin Hansai sati Biyu.
Da sas safe Bayan Malam ya fita ta fita ,dama bata tambayar sa unguwa, ba bata zame ko ina ba sai gidan Delu tana zuwa suka tafi Gidan Boka.
Sunyi tafiyar Awa d'aya San nan suka hau Mota ta aje su adede Dajin da zai kaisu Gidan Bokan, Surk'uk'in Daji ne gun. Amma haka suka Shiga.
Sallama sukai boka ya daka tsawa yace "ba ai masa Sallama( saboda tsabagen tab'ewa irin ta Boka) haka suka shiga Gwamma tace "Boka dama akwai wata Yarinya ce da mijina ya tsinta tunda tazo na shiga Matsala ayanzu hakan D.an Maigari zata Aura ,ni kuma ban so ,dalilan daya sa nazo ne akan a rusa Auren karya yiwu ,San nan Kishiya ta sai abinda nace Mata, shima Mijina ayi min abinda kome nayi bazai ga laifi na ba."
Dariya ya kwarara "tabbas kina da sa a azzaluma mai son kanta, wan nan Aiki Sam bashida wahala,Amma fa kin cika muguwa ki tuba" dariya ya kurma yayi surkulle nan Hayak'i ya fuuuu ! ya d'auko wani Garin Magani yace "gashi ki yi abinci kitabbatar Kishiyarki da Mijinki sun ci .
San nan kuma Aiki akan auren can Zanyi shi .Godiya sukai ya kwarara ihu "ba aimun Godiya tab'ab'b'u kawai, ni ai na gama shiga ha'ula'I gashi kuma kun biyo Layi ,dariya ya saka .(meemi tace sakarkaru kawai Allah dai ya kiyashe mu tab'ewa ya shiryi masu hali irin na Gwamma).Aje Kud'in sukayi suka tafi... .kubiyoni
*By Queen meemi*
.
[3:58pm, 18/01/2017] πMeemiπΈ: . β β£ β β£ β ββ£β£ ββ£β£ β β£